Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Hakan ammata turata sabida mugunta.


Matafiya

Tsaye suke acikin babban filin makarantar MAYE BALWA wadda tajima dawatsewa bakowa aciki kuma ba komai na anfani takoma tamkar kango, sunjima suna zagayen makarantar kafin su samu wani wuri daga gefen makarantar suka zauna suna tattaunawa da hakimin garin, bayan suyi magana da wani company gine,gine dake cikin garin Yola, suna jiran ƙarasowarsu domin suɗamƙa kwangilar gyaran makarantar hannunsu..basu jima awurinba manager company yazo, Hakan yake nuna musu tsare tsaren ginin makarantu dasuke dashi a laptop ɗinshi suna dubawa..shikuwa yarima sameer ya lumshe kyawawan idanuwanshi masu launin ruwan madara, yana sauraren bugun zuciyarshi dayakeji tamkar zata tsinke wani irin fargaba da faɗuwar gaba yakeji wanda besan daliliba kuma abin seƙara kusantoshi yakeyi...sukuwa sunacan suna aikinsu hankali kwance domin nema sukeyi suyi sugama subar unguwar domin babu alamun ko sunsan miye hotel balle suyi tunanin samunshi Anan kusa, sesun koma cikin gari tukkunna.


Danejo


Taje inda innawuro ta aiketa tadawo tana tafe tana tana tsilla sandarta sama gaya duk tazubo sumar kanta tarufe mata rabin fuska da ƙirjinta ɗaya har zuwa cibiyarta sabida tsawon sumar dakuma tsantsinta, tafiya takeyi ita kaɗai awurin domin kamar jeji hakan wurin yake sabida anfita daga cikin gari kuma ba'a ƙarasa cikin rugar Fulanin dake maƙwabtaka fawirinba,tayi tafiya menisa kafin tazo Dede inda motocinsu suke, da mamaki take kallon motocin bawai ɗan bata taɓa Ganin mota ba a'a kawai de tayi mamakin ganinsu awurinne, ahankali taƙarasa wurin cikin sanɗa tana leƙensu....Sukuwa basuma sanda akwai mutum awurinba. Tajima tana kallonsu basusaniba harta juya zata tafi sekawai idonta yasauka akan yarima sameer dake lumshe da Ido yasaka hannu ɗaya yaɗage setin zuciyarshi dayakeji kamar zata ɓalle tafoto waje...ido tawaro cikin tsananin fatin ciki dajin daɗi taƙarasa gunshi sam bata damu da mutanen dake wurinba cikin ɗauki tariƙo hannunshi tana faɗar "pappi cikin sweet voice ɗinta me daɗin sauraro...wani irin zabura princes yayi sabida wani mugun shuck dayaji lokacinda hannunta yasauka anashi, tareda buɗe lulu eyes ɗinshi akan kyakkyawar fuskarta, wanda yayi sanadiyyar tsanantawar bugun zuciyarshi.

Sukuwa duka ido suka waro musamman brothers ɗinshi dasukasan waye yarima sameer dakuma yadda yake ƙyamatar mata, amma imam, Hakimi, da manager company duka kallon mamaki ne suke mata gatadai kallo ɗaya zaka mata kasan cewar ƴar fulanice ta asali wanda akasani da kunya da kawaici amma gaya tariƙe hannun namiji kuma babban mutum me daraja irin yarima sameer agansu batareda taji kunyarsuba.


Shi kuwa wani mugun kallo kawai yakebinta dashi amma kasa cewa komai kowani dogon motsi yakasayi...cikin mamaki danejo kebinshi da kallo tunda tabuɗe ido aduniya take Ganin pappi ɗinta bata taɓa yimai maganaba yashareta se yau, atake gabanta yafaɗi tsoro da fargaba duk suka rufeta dara daran idanuwanta masu masifar haske suka canja kala atake suka cikoda ƙwallah, dasauri ta russuna wurin ƙasan ƙafafunshi taƙara kamo hannunshi ɗaya muryarta na rawa take faɗar "pappina bakada lafiya ne? Miyasa kayi shiru? Ko wani abun wannan mutanen sukayima? Miyasameka pappi? Kayi magana dan Allah. Taƙarasa zancen tana saka Mishi kukan dake fita har zuciyarta..

"Ikon Allah ke baiwar Allah sakeshi mana aina kika sanshi dazakiga mutum kawai kizo kiriƙeshi kinamai kuka? Cewar imam cikin mamaki...banza tayi dashi domin burinta kawai pappinta yayi magana amma shiru se ido kawai dayake binta dashi...shikuwa imam agarzuƙe yayo kanta yana masifa "waifa wannan wani lokacin Fulanin nan naruga ba hankaline dasuba tashi kibarnan kona tattakaki yanzu Wlh. "No karka daketa Cewar Ameer yana tasowa daga inda yake zaune yaduƙo kusan inda take gurfane riƙeda hannun yarima sameer yace "ƙanwata sakeshi muyi magana kinji, Yafaɗa cikin alamun rarrashi...dagowa tayi da jajayen idanuwanta masu masifar girma tawatsamaisu tareda girgiza kanta duka sumar data rufe rabin fuskarta tayi baya atake asalin fuskarta ta bayyana. Azabure ameer yayi baya sedai yayi ƙarfin halin hana kanshi faɗuwa, hakama duk wanda ke wurin seda yarazana Ganin tsananin kyawun wannan yarinyar gakuma gashi har gadon baya kana ƙwatar idonta kaɗai ta isa tashedama tabbas aljanace sabida kasan cewar ƙwayar idonta lite blue sedai acikin ido farine ƙal amma yanzu yakoma ja sabida kukanda tayi. Duk wanda ka kallah awurin natsuwa ta ɗauke Mishi amma Banda zaratan samarin dasukayi ta maza suna kallonta... ɗan seta kanshi yayi kana yaƙara cewa a'ina kikasanshi ƙanwata? Domin yaga dai taƙi ta sakeshi kamar yadda yabuƙata...ƙwallar dasuka cika idonta ne suka ƙara zubowa kana tace "pappina ne...!



Book ɗin AL'AJABI Paid book ne akan 1k kacal complete ga duk me buƙata domin a complete yafito duk wanda keson posting kullun 700 ne zaki iya tura kuɗinki ta wannan account ɗin 👉2276776261 sha'awanatu ƙasim UBA bank, kana kitura Shedar biyanki a wannan nomber 👉 07037092176 on whatsapp.










Autar alheri ✍️

🪐🐦‍🔥🪐 *AL' AJABIN*🪐🐦‍🔥🪐

🪐🐦‍🔥 *MASARAUTA*🐦‍🔥🪐



🪸🪸🪸🪸🪸🪸 Daga💪Alƙalamin👇🪸🪸🪸🪸🪸🪸


Dr Yasmeen Ahmad😚


Autar alheri ✍️


Al'ajabi, hummm

Book ɗin al'ajabi wani sabon kabcene me matuƙar al'ajabi da ban mamaki, kabcene wanda ya banbanta da sauran books na masu ban al'ajabi kamar irinsu ( MEJO NAJEEB,,, SOLDIERS FAMILY,,,,IZZAR MULKI,,, JEJI GIRL,) inaga sune Books masu ɗauke da abin al'ajabi to wannan kabcen dabanne sam ba irinsu bane, idan kuna so kukashe ƙwarƙwatar karatu to kigarzayo domin samun damar karanta book ɗin AL'AJABI.

ROMANTIC LOVE STORY 💋 KAMAR YADDA AKA SABA HUMMM MY LOVELY SISTERS ABUNFA BA'A MAGANA KAWAI MUTSUNDUMA ACIKIN WANNAN LABARI ME TAKEN AL'AJABI 💃


Book 1

Page 17 & 18


"Kana tace "pappina ne kuma inasanshi banaso wani abun yasameshi, kace yayi magana dan Allah kowani abun kuka masa ne? Tafaɗa cikin yanayin tausayi domin duk zuciyarta ta karaya Ganin pappinta yaƙi cewa komai...ajiyar zuciya Ameer yasauke kana yadubi yarima sameer daya lumshe kyawawan idanuwanshi tun lokacinda kalamanta suka fara dukan dodon kunnenshi, kana yace "princes kasan wannan yarinyar ne? Yatambaya badan abashi amsaba domin yasan ba abinda yarima sameer zece Mishi idan kuwa zasu kwana awurinne, sedai ga mamakinshi yaji cool voice ɗinshi yana faɗar "I no her, yafaɗa kamar meciyon baki, kafin yaƙara motsa laɓɓansa cikin gajiyawa yake faɗar
"please just sey her get from my saint, Yafaɗa, zuciyarshi ada gule.

Ido danejo tazuba Mishi kawai tana kallonshi yayinda idon ke ƙara cikowa da ƙwallah...shikuwa Ameer jin kalaman ɗan uwan nashi yasa yadubeta kana yace "please ƙanwata inaga wannan Bashine pappin dakike magana akaiba kiyi haƙuri kije gida kinji zakiga pappinki acan yana jiranki amma wannan bashi bane, yaƙarasa zancen cikin rarrashi. Ita kuwa tunda taji saukar kalamanshi idonta suka ƙara zuba tamkar panpo, cikin kukanda keson kuɓuce mata tasaki hannayenshi wanda yaji tamkar lantarki ce tarikeshi amma yanzu tasakeshi sewani zutt,zutt yakeji acikin lallausan tafin hannuwan nashi. "Ni zakace akora my pappi ni HUSNAR KA? danejo ce fa? yau nikake kora? minayima dazafi Hakan? Ni pappi? Humm sabida kaga banada kowa danake raɓa naji sanyi sekai? Karka manta pappi kaine uwata, kaine ubana, kaine yayana, kaine ƙanena, kaine abokina, amma yau kaida kanka kake korana? Hum shikenan I'm going to all your life my pappi sedai zan zauna zaman tsimayen

"When you're call me
"when you're missing me😥
"When you're coming back to me my happiness
"When you're coming back to me my everything all my life,
I'll waiting for you any time my pappi. Tana gama faɗar Hakan tamiƙe tsaye tareda saka bayan hannunta tashare ƙwallar idonta, kana tajuya kawai tabar wurin.

Sukuwa gabaki ɗaya sunyi mutuwar zaune tunda tafara magana domin sam basuyi tunanin zataji abinda princes yaceba balle har ta iya maida Mishi amsa da turanci ba, hartabar wurin basu saniba, sunlula duniyar tunanin ya akayi ƴar fillo ta iya Turanci kuma ƴar cikin ruga Fulanin jeji? Amma ba wanda ze basu amsar wannan tambayar tasu Hakan yasa suka ƙara gaskatawa ransu Cewar gamo sukayi da aljana... firgigit Hakan Anwar yayi yana kallon inda take gurfane da zimmar yabata haƙuri amma seyaga wayam bakowa Hakan yasa gabanshi ƙara mugun faɗuwa cikin kaɗuwa yake faɗar "kai ameer taɓace fa Wlh ajanace innalillahi wa'innailaihiraji'un...arazane Ameer ɗinma yamiƙe tareda riƙo hannun yarima sameer daya koma tamkar wanda aka zarewa lakka ajiki yamiƙar dashi tareda janshi suka fara tafiya gun motocinsu sedai duk yadda Ameer yaso sutaka dasauri abin yaƙi samuwa domin yadda yake tafiyarshi yanzuma Hakan yakeyinta cikin izza da ƙasaita tamkar yadda yasaba yin abarshi ga dukkan alamu dai hakanne tafiyar take bawai yanayi bane sabida kuɗi ko mulkinsu ba... hakama su imam tuni sun mara musu baya...hakimi kan se haƙuri yake basu domin ya ɗauka sun fasayin aikinne tunda yaga Manager company gini yacika bujenshi da iska, aranshi kuwa se tsinewa wannan aljanar yarinyar yakeyi...sukuwa dogaransu nahangosu tafe sukayi saurin buɗe musu motar, suna isowa suka shiga hakama excout ɗinsu suka shiga cikin sauri aka tada motocin sukabar yanki baki ɗaya.


DANEJO


Tafiya kawai takeyi batamasan ina take jefa kafartaba wani irin ɗaci takejin zuciyarta namata wanda bata taɓa jin irinshiba,,,yau ta ɗanɗani baƙin cikin dabata taɓa tunanin samuba, wai itace pappinta zece akora wai besantaba wannan wacce irin ranace me muni tazo acikin rayuwarta? tabbas wannan abin yayi mata zafi bakuma dan bata taɓa fuskantar Hakan bane a'a kawai dai ɗanta riski hakanne a inda batayi tunaniba, domin koda mutanen duniya zasu mata Hakan bazataji zafiba, amma agun pappinta kam bazata iya juraba, Hakan taketa zancen zuci harta isa gida tafaɗa babuko sallama gabaki ɗaya a hargitse take kamar wata zararriya... innawuro naganinta tataso cikin bala'i tana faɗar "ke dan ubanki nizaki wulaƙanta, tunyoshe nake jiranki amma kikayi zamanki seyanzu zaki dawomin kuma hannu rabbana, tukkunna ma ina aikenda namiki? Ko kina nufin ƙin tsayawa kikayi ki ƙarbo kika dawomin Hakan hannu rabbana? Taƙarasa zancen tana zuwa inda danejo take tsaye....Ita kuwa sema yanzu da innawuro ta tambe aikenta tatuna, dan ɗaukin Ganin pappinta yasa tayasarda saƙon.

Cikin tsawa taji saukar muryar innawuro tana faɗar "wai badake nake maganaba kinwani shareni sekace wata sa'ar uwarki....ɗib tayi tare da haɗiye sauran kalamanta Ganin yadda danejo taɗago azabure tana watsa mata waƴannan idanuwan nata dasuka gama komawa abin tsoro sabida ɓacin rai wanda yanayinta yamaidata aljanar ƙarfi dayaji. Tsorontane yashiga innawuro lokaci ɗaya Hakan yasa tazuba mata ido kawai tana kallonta domin inda ada ne dasedai taji saukar ruwan duka tako'ina ajikinta amma yanzu kam tana shakku...iskace tafara kaɗawa tayi baya da sumar kan danejo tana kaɗata sama, Hakan yaƙara ta azzara sauyawar halittarta daga mutum zuwa siffar aljanu...dasauri innawuro tanufi ɗakinta tareda maida ƙyauren tarufe gam tana faɗar "aikin banza wannan yariya ko dangin ibilisai ni wuro inaganin jarabawar duniya mlm yaɗauko mana jaraba dabe ɗauko uwar aljanar nanba daba abinda zesa tazame muna fitina kataɓa ta kuma wani bala'in yabiyo baya, Hakan innawuro keta mitarta ita kaɗai acikin ɗakinta.


Danejo kuwa nasu ɗakin tashiga tareda zubewa akan katifarta tana rushewa da matsanancin kuka metaɓa zuciya, sam takasa danne abin aranta


Wani irin ɗaci ke taso mata azuciya, tarasa ina zata saka kanta, taɗauki tsawon lokaci tana kukan kafin taji ana shafa lallausar sumar kanta....dasauri taɗago tana kallonshi cikin mamaki domin tasan dudduniya mutun ɗaya kemata Hakan kuma sam batayi tunanin ganinshi ba yanzu..aiko sukayi ido huɗu dashi yana sakar mata lallausan murmushi wanda yaƙara fitoda asalin kyawun fuskarshi ga dimple ɗinshi duka biyu sun lotsa abinda ke bala'in ɗaukar hankalinta gareshi kenan...dasauri tajuye fuskarta tana turo baki gaba kawai taƙara rushewa da matsanancin kuka.
"Ya salam shine abinda pappi yafurta ahankali yaname dafe kanshi, kafin yariƙo hannunta cikin sigar rarrashi yake faɗar"please my husnah stop crying mana, sata kigayamin miyasaki kuka, yafaɗa cikin Cool voice ɗinshi sak irinna yarima sameer domin basuda banbanci ko ƙwayar zarra ne tsakaninsu daga murya har kamanni na fuska da jiki har yanayi komai nasu iri ɗaya ne. Hakan yasa danejo keyiwa yarima sameer kallon pappinta. Shiru tayi taƙi Magana kusan minti ukku, kana tabuɗe baki cikin muryar kuka take faɗar "nikatafi bayan ɗazu ka wulaƙantani kakoreni daga wurinka dan kawai kana tareda wayancan mutanen shine yanzu zakazo min, haba pappi miyasa zakamin Hakan dan Allah? Karka manta fa Kaine ummana yayana kuma malamina idan kagujeni yazanyi? Tafaɗa tana ƙara sakin wani sabon kukan me tsima zuciyar mesauraro.

Tunda tafara magana yake kallonta tamkar yasamu tv aranshi yana ayyana Cewar ta haɗu da princes Sameer ne kenan duk yadda akayi domin duk faɗin Afirca shine kawai keda kama dashi wanda za'a iya gani ayi tinanin shine, bece mata komaiba harta gama zancenta taɗora da kuka..hannunta kawai yariƙa tareda hura mata iskar bakinshi a ido domin bayaso wani daga cikin gidan yazo yaji abinda suke magana akai, aiko suka ɓace bat kafin su bayyana bakin wani ƙaton teku, buɗe idonta tayi taga inda suke, amma batace komaiba kuma bataji tsoroba kasan cewar sun saba irin wannan tafiyar da pappi, kusan minti 15 suna ahakan kafin yajiyo gareta cikin tausasa harshe yace

"My husnah kitsaya kinutsu ki saurareni kinjiko..kai kawai taɗaga Mishi amma batace komaiba...Hakan yasa yaci gabada faɗar"kiyi haƙuri abisa korarda yarima sameer m habibullah yayi Miki, domin banine na korekiba yarima sameer ne, Shima kuma ba'ason ranshi yakorekiba sedan kasan cewarshi yatsani mata suraɓeshine da irin halayyar Ameer M habibullah yakeda Ita sam baze korekiba sabida Hakan kidena fishi da pappinki kinjiko ƙanwata, yaƙarsa zancen cikin kwantarda kai yadda zata fahimta....amma ina tun lokacinda yace bashi bane yakoreta ƙwaƙwalwarta tadena gane komai, tunani kawai take aranta to bashi bane waye? Waye takeda kama irinta pappinta? tayaya mutun biyu zasu kasance iri ɗaya? Kodai su ɗin twins ne? To koma twins ne aikamarsu tayi yawa kuma miyasa shi batasanshi ba se pappi kawai? Miyasa kuma bayason mace taraɓeshi? Miyasa ze koreta bayan ita batasan ba pappinta bane? Kuma tayaya ma zata yadda ba pappi bane? Hakama tayaya zataƙi yadda bayan pappinta betaɓa mata ƙarya ba...duk acikin ranta take jerawa kanta waƴannan tambayoyin da batada amsarsu, sedai abinda batasaniba afili take zancen zucin nata kuma koda azuci tayi pappinta ze iya sanin abinda take saƙawa....muryarshi ce takatse mata tunani inda yake fadar "duka zaki samu amsoshin wannan tambayoyin naki my husnah sedai bayanzuba dasannu Zaki fahimci komai, abu biyu saki sani ayanzu sune na ɗaya muba ƴan biyu bane hasalima bajinsinmu ɗaya ba inafatar kinsan Hakan, Sena biyu zaki bawa zuciyarki nutsuwa da bani bane kika gani ɗazu sabida zankaiki har inda yake kiganshi amma bazan bari yagankiba kin yadda? Yaƙarsa zancen yana kallonta...kai kawai ta iya ɗagawa amma takasa cewa komaiba sabida mamaki da al'ajabi. Sunjima aruwin yanata rarrashinta kafin yasamu zuciyarta taɗan nutsu yamaidata gida.


MASARAUTAR MAHAR

Sedare lis suka dawo garin MAHAR sedai agajiye liƙis suka dawo domin daga Adamawa ko ina basu tsayaba se masarautarsu, motar data ɗauko imam ce kawai tatsaya taraba ta ajiye shi kana suka ƙaraso..suna fitowa daga cikin motocin kowanne pert ɗinsu yanufa domin dare yayi sosai, koda yashigo general parlor gidansu bakowa kuma duka ankashe fitilun parlor, Hakan yasa ya haura kawai pert ɗinshi batareda yanemi mammi ba, yana shiga tun a perlor yafara fatali da kayan jikinshi harya shiga bedroom ɗin ƙarasa cirewa kawai yayi yafaɗa bathroom yasakarwa kanshi ruwa tareda lumshe kyawawan idanuwanshi, sedai arazane yabuɗe su jin saukar sweet voice ɗin danejo inda take fadar "kaine uwata, kaine ubana, kaine yayana, kaine ƙanena, kaine abokina, amma yau kaida kanka kake korana daga gareka,

"when you're coming back to me my everything.
Wani irin mugun faɗuwa gabanshi yayi yana ƙara ganin kyakkyawar fuskarta me ɗaukar hankali a ƙwayar idonshi, "hasbinallah "innalillahi wa'innailaihiraji'un wannan wacce irin yarinya ce ? Yafaɗa asaman lips ɗinshi kafin yayi sauri yayi wankan shaf'shaf yafito, kayan bacci shi kawai yazura taredayin addu'a yakwanta, sedai baccin yaƙaura cewa idonshi sam muryarta kawai yakeji tana mishi gizo idan kuma yarufe idonshi ita yake gani, yaɓata tsawon lokaci ahakan yarasa abinda yake mishi daɗi daƙyar bacci ɓarawo ya ɗauke shi, sedai ko minti 40 beyi dayin baccinba yafarka arazane yana salati, saka makon danejo dayariƙa gani acikin baccin shi tana kuka kamar ranta ze fita akan korar daya saka ayimata ɗazu, cikin wani irin yanayi yadafe kanshi yana maimaita....!


Book ɗin AL'AJABI Paid book ne akan 1k kacal zaki iya tura kuɗinki ta wannan account ɗin 👉2276776261 sha'awanatu ƙasim UBA bank, kana kitura Shedar biyanki a wannan nomber 👉 07037092176 on whatsapp.










Autar alheri ✍️

🪐🐦‍🔥🪐 *AL' AJABIN*🪐🐦‍🔥🪐

🪐🐦‍🔥 *MASARAUTA*🐦‍🔥🪐



🪸🪸🪸🪸🪸🪸 Daga💪Alƙalamin👇🪸🪸🪸🪸🪸🪸


Dr Yasmeen Ahmad😚


Autar alheri ✍️


Al'ajabi, hummm

Book ɗin al'ajabi wani sabon kabcene me matuƙar al'ajabi da ban mamaki, kabcene wanda ya banbanta da sauran books na masu ban al'ajabi kamar irinsu ( MEJO NAJEEB,,, SOLDIERS FAMILY,,,,IZZAR MULKI,,, JEJI GIRL,) inaga sune Books masu ɗauke da abin al'ajabi to wannan kabcen dabanne sam ba irinsu bane, idan kuna so kukashe ƙwarƙwatar karatu to kigarzayo domin samun damar karanta book ɗin AL'AJABI.

ROMANTIC LOVE STORY 💋 KAMAR YADDA AKA SABA HUMMM MY LOVELY SISTERS ABUNFA BA'A MAGANA KAWAI MUTSUNDUMA ACIKIN WANNAN LABARI ME TAKEN AL'AJABI 💃

Book 1

Page 19 & 20

"Yana maimaita innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, yanajin gabanshi na tsananta faɗuwa, yajima zaune kafin yamiƙe yanufi bathroom yaɗauro alwala yafito yatada sallar nafila domin ayanzu kusanci da mahaliccinshi kawai yake buƙata yarigada yagama gasgata cewar gamo yayi, hakan yaraya wannan daren har aka kira asuba kana yafice zuwa masallacinsu dake cikin masarautar, yana fitowa yasamu yan uwanshi duka sun fito domin wannan al'adace agun ahalin wannan masarautar muddin kana cikin masarautar to doline da asuba kafito ahaɗu domin shiga masallaci, daga iyayen nasu maza har memartaba sarki habibullah dawazirinshi kuma ƙane agareshi, baba tsoho kenan, har galadima wanda yakasance shima ƙane ne agunsu, kuma dukansu sun manyanta, kowanne datashi zuri'ar,,,ahakan suka nufi masallacin dukkansu.

Bayan an idarda sallah kowa yafito ananne suka fara gaisawa da juna wato samarin gidan dakuma yayunsu domin memartaba da tawagar ƴan uwanshi tuni sunyi gaba. "Good morning yaya Naseer, cewar yarima sameer domin duk acikin yayunsu yafi ƙaunar yaya Naseer wanda baya iya shareshi kamar yadda yake share sauran. "A a morning my lovely bro yoshe agari? Naseer ɗin ya amsa yana rungumeshi. Bece komaiba yadda shima Naseer ɗin yasan bazece wani abinba, daga wannan gaisuwar, hakan duk suka gaisa da junansu kana kowa yanufi pert ɗinsu amma ameer da anwar pert ɗin mammi sukabi princes.

Bara nabaku ɗan bayani kaɗan daga cikin wannan ahalin yadda zaku fahimta.


Sarki habibullah yanada yara biyar kamar yadda kuka sani, Mansoor shine babba wato baba wanbai, yanada yara ukku Naseer, Abdul, kabeer, kuma kusan sune manyan yara agidan wato Abdul wanda suke kira yaya Abdul, sekuma yaya Naseer, da yaya kabeer, Muneer, shine kebinshi shine suke kira abbey, yanada yara ukku, Yarima Sameer, affan, Safnah, jabeer kuwa shisuke kira dady, yaronshi ɗaya Anwar, sekuma Mubarak, wanda suke kirada abba ciroma, yanada yara biyu, Ameer da Amerah, sekuma Autansu Abdullah, wanda sunanshi yaya Abdul yaci, shi bemada aure ayanzu hakan tun shekarun baya da matarshi tarasu beƙara aureba, hakanan yake zaunenshi, kuma bayama zama ƙasar yana US acan yake aikinshi, kuma shine suke kirada abban yarima ko abban princes domin tunda aka haifi yarima Sameer ahannunshi yataso shine yake kiranshi da yarima har Sunan yabishi to acan US basa cewa yarima sedai suce princes shine sunayen suka haɗe mishi...sarki habibullah kuwa matanshi ukku mebabban ɗaki itace uwar gida yaranta ukku, mansoor da jabeeer, se abdallah, se Fulani abu itako yaranta biyu mubarak da muneer, sa'annan Fulani huraira itako bata taɓa haihuwa ba,

Kunji yadda suke barana barku hakan zuwa gaba saku fahimci komai domin akwai waƴanda se gaba sunayensu zasu fito dakuma rawarda zasu taka aciki.


Suna isa general parlor mammi suka samu abbey zaune yana aikin a laptop ɗinshi, mammi kuma nagefenshi tana zuba mishi coffee, dukkansu rusunawa sukayi suna gaida iyayen nasu bayan sun amsa ne abbey yace "yaran abbey yagajiyar tafiya? Naga kunyi saurin dawowa kwana ɗaya duk nisan wurinnan. Murmushi Ameer yayi kana yace "wlh kuwa abbey domin akwai abubuwan damukeso muyine idan mundawo kafin bro yakoma US shiyasa muka dawo karmu ɓata lokaci acan.

Jinjina kai abbey yayi kana yace "shikenan badamuwa sedai babu zancen komawa US ayanzu domin memartaba yabada umurnin dukkanku kufitarda matan aure kafin yatafi sabida akwai muhimmin abu dayakeso aiwatarwa agareku kuma acikin wannan lokacin yakeso kuyi aure, yaƙarasa zancen yana kallon yanayinsu. Seyaga Anwar ne kawai yaɗago aɗan razane yana dubanshi sekuma Ameer dayace "aure kuma yanzu abbey? Amma shi gogan ko ɗagowa beyiba ga dukkan alamu bemasan akanme ake maganarba domin yalula wata duniyar, fuskar waccan aljanar kawai yake gani a idonshi hakama muryarta kemishi gizo acikin kunnenshi kuma cikin sautin kuka....da mamaki abbey ke kallonshi yana karantar yanayinshi, hakama yan uwan nashi, kusan minti 15 suna ahakan domin abbey zuba mishi ido yayi koda zece wani abu. Amma shiru, hakan yasa yataɓoshi yana faɗar"Muhammad lafiyarka kuwa? Yatambaya da mamaki kwance akan fuskarshi.

Mammi ma shitake kallo mamaki fall ranta..arazane yaɗago yana faɗar "na'am abbey. Dukkansu zaro ido sukayi yadda sukaga idonshi suyi luhu,luhu kamar wanda yasha kuka yagaji kokuma wanda beyi bacciba, abinka ga me manyan idanuwa.

Dukkansu shiru sukayi suna kallonshi kafin abbey yace "Muhammad Mike damunka? Bakada lafiya ne? Kakoma hakan? Damamaki shima yake kallon mahaifin nashi jin tambayar dayake mishi amma yakasa cewa komai, cikin ɗan tsawa abbey yace "ya inama magana kamin banza wai yoshe zaka ajiye wannan miskilin nakane Sameer? Humm toni bazan juri wannan sakarcinba kaji da kyau ina buƙatar kakawomin matar aure acikin wannan watan kafin ka koma US kuma umurni ne yanzu yajanye daga umurnin memartaba nawane kuma doline kowa yakawo idan ba hakanba toni zan nemawa mutun dakaina, yana gama faɗar hakan tamiƙe kawai yabar parlor sefamar faɗa yakeyi domin aganinshi duk laifin Abdullah ne dake biyewa shirmen sameer ɗin shiyasa yake yiwa mutanen renin hankali.


Shikuwa gabaki ɗaya mutuwar zaune yayi tunda yaji kalimar aure jinshi ya ɗauke, auren kawai kemishi amsa kuwa cikin kunne..mammi ma batace musu komaiba tamiƙe warta domin idan tatsaya zata tausaya musu ne awannan gaɓar kuwa basa buƙatar tausayi domin kuwa inba hakan aka musuba bazasuyi aurenba duka yaran gidan maza sunyi aure sune kawai sukaƙiyi dan sunga anzuba musu ido...mammi na ɗagawa suka Miƙe jiki asanyaye suka nufi pert ɗinshi kowannensu zuciyarshi na luguden tara,tara musamman princes da babu zancen aure yanzu atsarinshi.


A parlor suka zube cikin tashin hankalin da yakasa ɓoyuwa agaresu anwar yace "brother's yazamuyi da wannan zancen na abbey plesse aure fa, yafaɗa cikin alhini..."humm aini namarasa abin faɗa wlh dan banmasan ta ina zamu faraba, amma ni inaga Indai abbin yazo da hakan to kawai Nawwara zanfitar dama ita nakeso kawai banyi niyyar yin auren bane ayanzu, cewar ameer...dasauri duk suka kalleshi sedai kuma zancen ameer ya sanyaya ran anwar hakan yasa yasaki wani lallausan murmushi kawai yana shafa sumar kanshi. Da mamaki ameer yace "yadai bro? Ko kaima abin yazo maka dasauƙi ne? Humm kawai Anwar yace amma bebawa ameer amsaba, balle shi gogan dagabaki ɗaya baya cikin nutsuwarshi, fahimtar hakan yasa suka sakashi agaba da tambayar Mike damunshi amma yakasa cemusu komai, ahakan sukawini ranar a pert ɗinshi sallah kawai ke fidda su sedai yanayinda princes yake ciki yaƙara tada musu hankali hakan yasa suka yanke shawarar kiran abbanshi su sanar dashi.


DANEJO


Tunda abbey kemusu zancen aure har kawo firar dasukeyi tsakaninsu tana tsaye itada pappinta tana kallonsu cikin mugun mamaki ta kalli yarima sameer kuma ta kalli pappi, tabbas ba pappi bane amma ba wanda ze yadda da hakan idan ba yagansu hakan tadata gansuba. Seda pappi yaga tagamsu dacewar wanda tagani dai bashi bane kana yasake ɗauketa yamaidata rugarsu, shikuwa yayi tafiyarshi, amma hakan danejo takasa samun saƙat domin kuwa tunanin abubuwan datagani acikin wannan masarautar da pappi yakaita yahanata sukuni gakuma wannan dake Kamada pappi datake ganin kamar yana cikin tashin hankali kuma duk yadda taso tayiwa pappinta tambaya akan abubuwan data gani yaƙi bata damar hakan, wannan lamarin shine yamayarda danejo wata irin sukuku.

Su jauro

Tun lokacinda suka tare danejo suka shiga taitayinsu domin seda sukayi kusan mako ɗaya akwance suna jinyar abinda idonsu yagane musu sedai daga lokacinda suka tuna kalaman danejo agaresu inda take cewa duk wanda yaƙara

Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3

Please Login or Register in order to submit comment