Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Ni ka ga tafiyata, kada ka sake ka zo min gida in ba takardar Rayha ka kawo min ba, babu gardin da zai zauna min a gida, ‘ya’yana sun girma kuma duk mata ne. A toh! Allah ya bamu alkhairi”.
Ya juya ya fita yana kara fadin,
“In ma aljanar ce za ta aure ka ku yi ta auren, kai ta ga ka yi mata, tunda tuzuru ne, sama da shekara talatin babu mai kiranka saurayi, ba Khalipha mai iyali abin burgewa ba”.
******




Juyi yake a matsakaicin gadon, lullube cikin zanin atamfar Rayhanah. Sai yanzu ya gane turaren ba wani bane ‘Makhmariyyah wa lamsa nectar’ ne wanda ake durawa a wani kanti a Jiddah. Shima Sapna ce ta gaya masa wata rana yana rungume da ita yake tambayarta wane irin turare ne mai sanyi da kwantar da hankali ta shafa a tufafinta haka?
Me yasa take amfani da abubuwa irin na Sapna?Is it a coincidence or what? (Arashi ne ko minene?) Ta san abubuwan da yasa yake son Sapna har da ire-iren wadannan abubuwan? Gayun Sapna cool ne and cooly ba na tashin hankali ba. She's a designer baby.
Tukunna ma, wace ce Rayhanah? Shi fa ya san wannan sunan, amma ya manta inda ya san shi. Ko Daddy zai tsire shi, ba zai taba yin sakin nan ba, ko ba don ji da ya yi ita ce Juman da ya so a murya ba, sai wannan furuci da ta yi na cewa za ta jira shi da aurensa har abada saboda Daddy. Koda har abada bazata ganshi ba. Ba don komai ba sai don cewa duk mai darajja Daddy abin so ne da girmamawa a gare shi.
Shima zai koyawa zuciyarsa bajinta, zai sota zai zauna da ita har abada saboda Daddy ko da a fili (a zahiri) ba ta yi masa ba. In yaso nan gaba sai ya je ya auro Sapna ya kara idan tana da rakin da ba za ta iya dauke shi a shimfidarta ba.
Ya tara bukata mai yawa ga duk macen da tai kasadar aurensa, shekarunsa talatin da uku bai taba sanin ‘ya mace ba. Ya killace kansa ne (insha Allahu) only ga matar aurensa, wadda yake fatan ta zama itace tubalin iyalinsa.
Ya kuma yarda ya baiwa Rayhanah da bai sani ba wannan babban matsayin tunda zabin Daddy ce. Addu’a yake har a fili Allah yasa RAYHANAH ba irin wadannan ‘yan lagwai-lagwai din bane kamar tsada irin matar Yaya Khalipha.
Bakar mace yake so ‘yar’uwarsa fully Nigerian. Ba kyale-kyalen gashi da farar fata ba. Shi kadai kuma ya koma yiwa kansa dariya duk da yana cikin tension din da Daddy ya hada masa wai ya rubuta saki. Abin da ya ba shi dariyar shine tambayar da zuciyarsa ta yi masa.
“Daga ganin sarkin fawa sai miya ta yi zaki? Tun ba a ga matar ba an ga kyau ko muninta, an ga yankan bakinta har an fara kissima yadda ake son ta a shimfida? Man! Kwanciyar aure ba ita ce kawai abin kissimawa a cikin aure ba, akwai wasu abubuwa masu muhimmanci ko da a ce basu kaita muhimmanci ba, to suma suna da nasu.
Shakuwa da juna, kusancin zuciya da zuciya, soyayya, tausayi da jin kai a tsakanin ma’aurata, fahimtar juna, nuna kulawa da bakin cikin ko farin cikin juna, planning a kan tarbiyyar ‘ya’ya da yanayin yadda ta dauki addininta da yadda take gudanar da ibadarta.
Idan ta dauki nauyinka yadda kake so a shimfida, ta kuma rasa wadannan qualities din she’s not enough wallahi auren ba zai dore ba.
Ga kuma kasancewar dan adam tara yake bai cika goma ba, da wuya a samu wadda ta hada dukkan wadannan din, a wurin Ibraheem idan irin haka ta faru to saki ba shine solution ba.
Dubo wata wadda ba ta da wancan take da wannan ka hadasu, sai rayuwa ta fahimta da soyayya ta dore. Tunanin Himu kenan har barci mai karfi ya dauke shi, mafarkin yadda zai ga Rayhanah yake, saboda yasa abin a ransa.
*******








Da asubah bayan ya yi sallah a masallacin dake kusa da gidansa wajejen karfe shida na safe, ya zauna ya shiryawa Daddy (text msg) na ban hakuri da neman afuwa. A ciki yace da Daddyn
“Aurensa da Rayhanah na har ranar busa kaho ne. Ya yi hakuri ya yafe masa ba zai iya ko da kwatanta abin da ya umarce shi ba, ya ba shi RAYHANAH....... akwai uzurin da ya janyo bai neme shi a waya ba shima ya kasa samunsa.
Ya rufe wayar ne kwata-kwata a dalilin jinya mai tsaho da ya yi a SanFrancisco, ya tambayi Mami ita ai ya gaya mata. Ya kare da cewa,

“Daddy I’m sorry........ Luv u Dad!”

Shima fitowar shi kenan daga masallacin asibitin wayar dake aljihunsa ta sanar da shi shigowar sakon. Ya dauko ya karanta, sai jikinsa ya yi sanyi. Amma bai ba shi amsa ba.
Mota ya dauka ya nufo gida da yake aikin kwana ya yi. A farfajiyar gidan ya cimma motar Ibraheem, jikinsa ya kara yin sanyi da ya shigo falo ya ganshi zaune cikin kujera yatsunshi goma cikin sumar kanshi kansa a sunkuye. Kayan jikinsa na barci ne.
Duk sallamar da Daddyn ya yi bai ji ba, ya yi nisa cikin tunani mai zurfi, kawai so yake ya ga wannan Rayhanah da ta tokare masa a kahon zuci. Yasa hannu ya mikar da dansa tsaye, sannan ya rungume shi.
“Jeka dauko passport ayi biza in sadaka ga Rayhaanah, amma don Allah Ibraheem ka rike min Rayhana amana, domin amanar Allah ce a hannuna. Idan ba ta yi maka ba, ka bani ‘yata kar ka wulakanta min ita yadda uwarku ta wulakantata......!!!”
Hannu ya kai ya toshe bakin Daddyn don ganin yana so ya tuno tsohon bacin ran da Mami ta dasa mishi.
“Past is past Daddy........ just the present!”
Dacta Mansur ya girgiza kai, wato ya yarda da shi. Ibraheem a dan nauyaye da nauyin harshe ya ce,
“A ina Rayhanah take?”
Daddy ya ce,
“Informatics - Singapore”.
Fiddo idon da Ibrahim ya yi ya baiwa Dr. Mansur dariya.
“Ita da wa Daddy? Da aurena?”
Daddy ya ce,
“Ita da budurwarka Juma, da kuke soyayya a waya”.
“Kasa tsage in shige!”.
In ji Ibraheem........ sai ya rufe fuskarsa da tafukansa. Wai ya ji kunya kenan. Dacta ya wuce ciki yana dariyar Ibraheem.
Idan yana tare da Dr. Mansur (mahaifinsa) bai san sanda yake mai da kansa kamar yaron goye ba. And the Dad likes it..... shi har gobe Ibrahim da Khalipha hangosu yake suna ‘yan digwui-digwui a Al-Muntada da Al-Falah (Children Islamic Schools) a Birtaniya.
Sanda yake kama hannun daya, Asma’u ta kama daya su tsallaka titi. Su shigar dasu makaranta.
Don haka shi har gobe yaran goye ne a idanunsa baya sakar musu ragamar rayuwarsu sai a bisa hanya madaidaiciya, ba kuma takura musu yake ba, tsaka-tsaki. Ayi raha lokacin raha, ayi discipline in sun karkace, sannan ayi musu abin da suke so
[12/26/2019, 21:08] Takori: *****


HADUWAR AMARYAR DA ANGON!

Cikin jirgin ‘Turkish Airlines’ da sukeciki, bairin tunanin da Ibraheem Mansur Takai bai yi ba, ya gaza ko da kurbar dan jusin dake cike da kananan kankara da suka mishi a dan kofin su dan kankani dake hannunshi.
Wace ce wannan Rayhanan? Ya take? Wace irin tarba za ta yi masa? Shima wace iri ya dace ya yi mata? Zai so ta? Zai iya ba ta matsayin mata a gare shi? Zai iya hada rayuwarsa har abada da yarinyar da bai sani ba bai taba gani ba? Bai taba yin wata mu’amala da ita ba balle ya san kamanninta ko halayenta?
Tunaninnikan da suka addabi kwakwalwar Ibraheem kenan, yayin da a bangaren mahaifinsa Dr. Mansur Takai, babu abin da ya dame shi, daga ya sha jus sai ya bude shafukan jaridar ‘Daily Tribune’ dake hannunsa, in yaso ya yafito ma’aikatan jirgin su zo su ba shi abinda yake bukata da yake a first class seats suke.
Lokaci-lokaci ya kan saci kallon Ibrahim ta gefen idonsa, sarai ya san tunaninnikan da ke damunsa, amma bai ce masa komai ba, bai ma nuna ya san halin da yake ciki ba.
A lokacin da aka ba da order a daura belt jirgi zai sauka a ‘Changi-Airport’, Ibrahim bai ji ba. Sai ji ya yi Baban yana makala masa, bayan ya makala nasa. A lokacin ne Ibrahim ya gane ‘he is lost...... (ya yi nisa a tunani).
Ya kalli uban, shima ya kalle shi, sai suka yi ‘yar dariya a tare.
Bayan sun sauka motar hotel din da Daddy ya yi booking tun kafin su taho (Mandarin Orchard Singapore) already tana jiransu, ta kwashesu da ‘yan jakunkunansu marasa nauyi zuwa otel din.
Tun a hanya Daddy ke kiran wayar Rayhanah ana gaya masa a kashe take. A lokacin ita Rayhanah tana aji suna wata jarrabawar gwaji (test) domin gab suke da fara jarrabawar karshen shekara. Kuma dama karatun na shekaru biyu ne kacal, da yake tana da diploma tare dasu.
Karfe shidda na yamma ta baro cikin institute din nasu ta kamo hanyar gida, ta tsaya ta sayawa Inna roasted KFC, ita kuma ta sayawa kanta ‘wantanmee’ ko ‘wonton’ (yadda suka fi kiransa), ‘chili crab’ da ‘fried hokkien mee,’ duka suna daga cikin (40 Singapore foods Singaporeans cannot live without) abincin mutanen kasar Singapore guda arba’in da baza su iya rayuwa basu ba, saboda ta ce da Innar yau kada ta yi musu girki za ta yo take away don ta wayi gari ba ta jin dadi, sauri ma take ta isa gida don ta kaita clinic a duba ta.

Haka nan ta tsinci kanta da faduwar gaba a lokacin da ta doso gida. Sai da ta tsaya a kan wani dan tudu ta zauna ta zube ledodin hannunta a kasa tana dan hutawa tana hango kofar gidan nasu da bakuwar motar otel din (Mandarin Orchard) fara sol. Ta san hotel din da Daddy ke sauka kenan, don haka jikinta ya ba ta Daddy ne ya zo.
To amma wannan faduwar gaban da ta samu kanta a ciki ta mece ce? Ta so ta kunna wayarta, sai ta tuna a gidan ta barota.
Sai kawai ta mike da dan kuzari tana cewa a ranta bari in karasa gidan, daman dai kuma ta kwan biyu basu yi waya da Daddyn ba, har Inna kan tambayeta kwana biyu Baba Likita bai kira ba, lafiya?
Ta kan ce lafiya sumul insha Allahu, kin manta Baban nawa busy doctor ne?’
Inna ta ce, “Allah yasa buzu ne ba busy ba, ki kira min shi kawai”.
Ta yi dariya ta ce,
“To ai ni yanzu bani da lokacin kunna waya idan ban gama tsarge tests din nan da suka sako ni a gaba ba, na yi na yi ki koyi operating din waya da kanki kin ki saidai ki dameni in kira miki wannan in kira miki wancan, yanzu sai ki yi zuciya ki koya”.
Duka Inna ta kai mata ta fice da gudu tana dariyarta. A haka suka rabu yau.
Ta mike ta ci gaba da tafiya a gefen titi a hankali don yunwa take ji sosai, ledodi da hand bag dinta kamar ta watsar dasu don nauyin da su kai mata, musamman kwalin kazar Inna kaji biyu ne a ciki. A haka ta daure ta ci gaba da tafiya at the same time, faduwar gabanta na kara tsananta.
Ba wata kwalliya ba ce a jikinta, amma da ka ganta kai tsaye za ka kirata black-American. Shigar jikinta usul shiga ce ta matan Singapore (Belted-Waist-Shirt) dark blue mai dogon hannu. As a Muslim, sai ta sanya bakin dogon wando a ciki, ta kuma sanya karamin hijab na Larabawa a kanta wanda ya tsaya iya kafadunta.
Also kayan jikin nata are not expensive.....kuma basu nuna komai na jikinta ba, daka ganta kasan Musulma ce cikakkiya. Singapore is very modern but dressing very sexily will not be acceptable in certain places.... don haka matan kasar musamman musulmin can basu fiya yin shiga ta tsiraici ba balle ita Rayhanah.
Kafafunta rufe cikin bakin cover kuma flat takalmi Melissa (brand din ZALORA). Rahane ba zuwa take ta sayo kayan nan ba, Dr. Mansur ke zuwa ya sayo da kansa a shaguna duk zuwan da ya yi ya zo ya zube mata su, illa dai yana karbar size dinta har ya rike. Zamanta cikin dalibai ‘yan’uwanta musamman haifaffun Singapore shi yasa yau da gobe ta iya shigarsu.
Fuskarta ko powder (hoda) babu, haka lebbanta babu danshin mai, but they are soft and supple kamar tana basu wani extra care ne, amma babu ko daya. Babu gumi a fuskarta, fuskarta tas fresh and choculate. Ba ta da dogon hanci, gashin nan dai dan madaidaici a tsakanin idanunta. Gashin kanta a tsefe yake, baki mai karfi amma ta matse karshensa da ribbon, hakan bai hana ya yi dan tudu ba, da yake ba ta taba sanya masa relaxer ba, haka yake da karfi kamar reza na asalin Hausawan Kano jikokin barbushe da tsimbirbira.
Da wannan shiga, da wannan fuska, da wannan yanayi Rayhanah ta danna kararrawar shiga falonta.
*****

Wanda ya bude kofar wani matashi ne baki mai tsayi sambal, mai wasu irin idanu masu lumshewa da kansu, da budewa cikin nutsuwa cikin umartar kansu da yin hakan, cikin kwayar idonshi akwai wani abu mai sheki kuma ba farare ne tas ba, ga dogon hanci kamar Dacta Mansur, fatarshi ta nuna haifaffen Nigeria ne, gashi nan kamar Dr. Mansur (choculate in complexion), duk da Dr. Mansur ya fishi haske.
Ya tara suma mai dan tudu a kanshi, ba kuma nannadaddiya ba ce ta ‘yan asalin Northwest-Nigeria ce wato mai karfi, amma ta sha taza ta sha mai mai tausasa gashi (ArganaVita) da ba a samun shi sai a kasashen ketare.
Sanye yake da farar shadda kal hilton dinkin Mohammed, rigar ta kusa kasa sai wandon a ciki, kanshi babu hula, daure a damtsen hannunsa agogon ‘Calibre de Cartier’ ne da ya kwanta cikin tattausar fatar hannunsa wadda lallausar bakin gashi ya kwanta a ciki.
Babban abin jan hankali a halittarsa, wannan tsagar bakin nasa ne da bakaken lebbansa marasa kauri, sai kuma lallausar sajen da ya kwanta a gefen kunnuwansa bai iso habarsa ba, wadda dan lotsawar nan na tsakiyar haba (cleft) ya bayyana a fili ko da bai motsa bakin don cin abinci, dariya ko yin magana ba.
Kallon-kallo ake tsakanin Rayhanah Rashid Takai da matashin da ya amsa sunan Ibraheem Mansur. Kallon da bai da ma’ana at all. Kallon da kai tsaye za ka fassara shi da kallon zakuwa a tantance juna kawai, ba na so ba, na kauna, ko akasin haka ba, kawai ‘eager to see each other,’ kuma ba tare da sun bar kallon ya tsawaita ba tunda ko da kalma ba ta shiga tsakani ba kowa ya gane kowa, kuma kowa ya yi ‘quenching’eager dinsa.
Don haka Rayha ta yi saurin sadda kai wani abu yammmm! Na bin ilahirin jikinta, wanda ya fi karfin tashin tsigar jiki sai circulating din jini abnormally da yadda ya saba aiki, domin bukatarsa nason ya isar da sako ta kowanne hali (by all means) daga zuciya zuwa cikin gangar jiki da kwakwalwa.
Duk wadannan mintunan da suka kwashe a tsaye, Dr. Mansur da Inna na kallon su, addu’a kowannensu ke yi cikin zuciyarsa Allah ya daidaita. Cikin Dr. Mansur ya fi na Inna Juma durar ruwa, idan Ibraheem ya ce Rayhanah ba ta yi masa ba ina zai sa kansa? Amma ga HIMUN, abin ba haka yake ba.

Kallon da ya yi mata na farko, eager look ne na neman tantancewa da kauda curiosity. Amma as his eyes enter her’s much more deeply..., (da kwayar idanunshi ta shiga cikin tata sosai), kokari kwakwalwarsa ta shiga yi wajen farfado masa da shekaru goma sha daya a baya.
Tabbas ya san fuskar, yasan wadannan idanun masu rauni da sanya kasala, ya san ‘yar yarinyar nan ce RAHANE, data shigo cikin rayuwarsu daga asibitin Malsm Aminu Kano, mai kula da ubanta a bargar dawakin Hakimi, mai yiwa ubanta wanki, yanke farce da taya shi feeding horses (baiwa dawakin Hakimi Abdulqadir abinci).
‘Yar yarinyar nan ce da Daddy ya dauko daga Takai..... wadda ta rasa jinta dungurungum, ‘yar yarinyar nan ce mai amfani da HEARING AID....... wadda ta sa shi barin gida ba don ya so ba, sai don ya ceci kansa ya ceci zuciyarsa daga fadawa soyayyah a inda bai dace ba, a kuma lokacin da bai kamata ba.

Yana ‘referring’ kowanne ‘motion’ na zuciyarsa a kanta da KARYA........ bayan kuma sau tari tsoron kar zuciyarsa ta ce ya yi karyar yake kidima shi ya yi mata KARYAR......
Ya bar gida saboda kar zuciyarshi ta wulakantashi da kauna da soyayyar kwaila ‘yar kauye mai lalurar JI, hade da wasu ‘extraordinary charismatic features’ (baiwarwaki da karama) da ake kira ‘Rahane.’ A girl with a great mind!
To yaushe ta koma RAYHANAH? (Daddy ne ya canza mata suna), zuciyarsa ta yi saurin tuno masa........

“Mene ne sunanki......?”
“Rahane”.
“Rayhanatu kenan ko?”
“A’a, Rahane.......”
“To ni ba zan iya kiranki Rahanen ba, don baida ma’ana at all sam-sam....... Rayhanah....!!!”
Ya tuno tattaunawar farko da mahaifinsa ya yi da ita a ranar da ta fara samun kanta daga hatsarin da suka yi, a kuma ranar da Baban da abokinsa Dr. Imam suka makala mata ‘hearing aid’. As soon as da suka fahimci she's hearing impaired!
Kafin Rayhanah ta ankara Ibraheem ya kai hannu gareta ya cire hijabinta yana duba kunnenta da bayan kunnen, babu komai sai dan karamin dan kunne mai barima na farin dutse. Ta saki ledodi da jakar hannunta kasa saboda razana.

“Where's your hearing aid?”.

Abin da ya tambayeta kenan da wata murya mai sanyi, harshensa da accent dinsa (American), wato na Amurka ba na Birtaniya da ya fi saukin furtawa ba.

Hannuwanta biyu ta kai kan nata tana son rufe gashinta da ya tsiraita. Sai ya russuna yana kwashe mata ledodin ta da jakarta da ta zubar ya bata hanya tareda yi mata alamar ta wuce, sai ta rabe ta gefensa ta shige ciki.
Babu kowa a falon, Inna da Baba Dacta sun shige kicin tun sanda Ibraheem ya cizge hijabin Rahane.
Ai ganin ba kowa a falon sai ta kara da gudu ta yi dakin barcinta ta rufo kofar ta jingina da ita tana numfarfashi kamar wadda ta yi gudun mita duba. Idanunta ta lumshe tana ambaton
“Yaa Wahhabu......... Yaa jamilal munzarrr (Ya mafi kyawun masu gani)!”

Ya Himu ne, tabbas shine....Daddy ya kinkimo ya kawo mata tana zaman-zamanta lafiya, ita ina ruwanta da wani Ibraheem. Tun can bai son ta, kyankyaminta yake, kalma wannan ba ta taba shiga tsakaninsu ba tun saninta da shi a gidan Dacta Mansur, kawo barinsa gidan don ba ta ishe shi ko da kallo ba.
Ita fa wannan auren kawai ta dauke shi suna ne, biyan bukatar ran Daddy bata taba tunanin zai zama reality ba.
Ta yi zaton haka za ta kare rayuwarta cikin kwanciyar hankali da neman ilmi da taimakon Babanta Mansur da Innarta Juma. Ba ta taba kawowa ranta Ibraheem din zai shigo cikin rayuwarta ba.......
Ta shiga uku....... wannan gundamemen Ba-amurken ne mijin nata da har Inna da Baba Dacta za su fita su barta da shi a gida akan saninsu? To tace masa me? Ko tayi masa me? Tayi yaya da shi?
Watakila ma dubawa ya yi in da hearing aid ya ce baya son ta. Duk Khalipha shi ya janyo mata....... da sunyi aurensu na so da kauna da ganin mutunci da kimar juna ai da Daddy bai yi mata AUREN HUCE HAUSHI da Ibrahim ba.
Sai ji ta yi hawaye na bin fuskarta. Bokon nashi har ya zarta misali, tsoro yake bata, kwarjinin shi razanata yake, ba ta san inda Daddy ke nufi ta kai shi a matsayin life-partner ba. Wannan gandamemen baqin bature haka wanda zai iya hadiyeta baki dayanta?
Ya yi biyun Yaya Khalipha a girma da tsayi, ba wai kiba ce da shi ba (physique).
Kuma ita bata taba yiwa kanta sha’awar rayuwa da wani Da namiji ba bayan Khalipha, shine dai-dai ita, domin ta kowanne bangare bai tsaurara ba...... ga boko ga addini, ga simplicity bai dauki kansa a bakin komai ba.
Rana daya wannan iftila’i ya ratsa, ta karbi zabin Daddy don biyayya da yakinin da take da shi na cewa a haka za su kare rayuwar tasu ita da Innarta da Daddy Ibrahim ba zai zo ba. Yau gata ga IBRAHIM MANSUR TAKAI.

Kokarin bude kofar ake, kofar da take jingine a jikinta. Ai da ta yi wata zabura guda daya sai ganinta ta yi a toilet dinta na bedroom ta kulle kanta.
Inna ta shigo tana cewa,
“Yau na ga abin da ya isheni ni Juma, mijin kike gudu haka? Lallai kin hada kanki da aiki.
Fito ki ci abincin da kika siyo shi Ibraheemu ma ya dade da fita a gidan nan.......”
Ai kuwa ta bude kofar ta fito idanunta sun ci kuka sunyi jawur. Haka Inna ta yi ta lallamin

Please Login or Register in order to submit comment