Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da ruwan titi.
Yadda taga ina yi sai ta tsaya tana kallo na kafin ta mayar da fadan akan su Binta da zainab din tana fadin zamu hadu da kune wallahi don nasan da sanin ku take min hakan.
Nace wai kun san wanan banzan ce da kuka tsaya tana fada maku maganan banza saman hanya haka ?
A harzuke tace nice banza nace an fada maki idan ba banza kike ba may kike zaki tsaya kina ma mutane son raki ke gaki mai kudi ki takamu ki wuce lafiya kin taki banza ko ?
Zaki gane kurenki wallahi wani kallon banza na watsa mata nace sai dai mu gane kuren mu amfada maki don kina da kudi zanji tsoron ki ne ko may kudin ki bai damay ni ba tunda ban taba zuwa wurin ki neman wani abu ba.
Matar da take cikin mota ne taji abin yayi yawa kuma dukkan mu munki bari ta bude mota ta fito tana jan ta tana fadin haba Nafisa zaki tsaya kan wanan karamar mara kunya kuna raba hali a saman hanya ai sai ta ja maki raini ga jama, a.
Kuta tayi ta watsa min harara na mayar mats ta shiga mota tana fadin zaki san kin shiga hurumi na nace inga alheri .
Fisgan mota tayi sai da yayi wani irin kugi suka nufi hanyan cikin gari zainab tace wai Khadija kin san kowacece ita din ?
Wacece kuwa banda kila matar wani ko wata kusan gwaunati shike nan don muna kasa sai ta rena mu Binta ce ta katse ni da fadin matar yayan mi ne kishiyar anty Fati.
Inda motar yabi nabi da kallo nace yanzu wanan matar matar dan uwan ku ne wallahi na dauka irin matan bariki din nan ne masu zaman kasu nima ban san yaya akayi idona ya rufe haka ba naci mata mutunci.
Nan nake fada masu abinda tayi muna da zamu shiga gidan su yanzu kuma ta sake maimaita muna shiyasa raina ya baci don naga kamar da gaiyya tayi hakan amma kuyi hakkuri don Allah.
Binta tace ai mu yau kin muna daidai wallahi don ba karamin dadi naji ba da kikaci mata mutunci nan a gaban mu.
Mun da jima a tsaye dasu karshe mukai sallama muka shige gidajen mu har lokacin ina da zafin matar nan a raina.
Nafisa ko sai fada take kawar ta na bata hakkuri tana fadin ban son ki biye mata ba tunda kinga kannen mijin ki a wurin may yuyuwa tasan ki ke baki santa ba.
Zanyi maganin ta wallahi sai ta rena kanta zata san ba a taba ni a zauna lafiya ko wacci tuwo dani miya ya sha na san dai ba yar gidan uban kowa bane ita.
Su zainab na shiga gidan su suka fara bada labarin arangaman mu da matar yayan nasu nan mutanen gidan suka fito suna sauraren su.
Mommy tace kai amma wanan yarinyar wallahi ta burge ni sosai yau da haka Fati ke daurewa ta mayar mata da martani da abin nata ya rage.
Anty amarya tace ai ba zata iya ba ne don ta riga tasa mata tsoron ta a zuciya kuna ganin a banza ta bar mutane ne haka da kowa ke shayin ta.
Ummi tace kwarai ai irin su ba a banza suke barin gida ba sai sun kama bakin kowa sun daure yadda ba mai iya motsawa a kan su.
Sai lokacin mama tayi magana tace aini wanan yarinyar ta gama shereni wallahi tayi min daidai yanzu zata san in ta daure bakin wasu bata iya daure na wasu.
Nikan da muka shiga gida ya Amina tana daki mika mata sakon nayi a cikin wani dan leda wanda ban san abinda ke ciki ba dakina nakoma na fara rage kayan jikina.
Na mayar da dan riga mai karamin hannu da bujen body hook dana cire sai hula dana dora a kaina kitchen na nufa don dora abincin dare saboda yamma yayi.
Kafin wani lokaci har na kammala na gyara wurin na mayar da kauan da nayi aiki a inda suke daki na kofa nayi wanka kafin a kira sallah na fito na canza kayan jikina.
Kananan kaya na kara sawa a jikina don idan ina gida sune kayan sawa na wayata na jawo ina duba sakon dana samu daga abokaina da muke karatu dasu.
Lokacin sallah yayi na mike na gabatar da sallah ban daga ba sai da na yi har isha,i na nike abin sallah na fito din in ba yaran anty na abinci.
Anty ce ta fito daga dakin kwanan ta muryan ta naji daga baya na tana fadin har kin fito eh kawai nace mata ba tare da na juya ba ina zuba abincin a plate na mika ma yaran dake zaune suna jirana.
Juyowa nayi inda nake tsanmanin take zaune nace in zuba mata abincin yanzu ne kallo na naga tanayi cikin mamaki tambayan da ta jefo min a lokacin ban zaci ji ba.
Khadija may ya hada ki da buzuwa yau kin ko san waye buzu kin san ko matar waye don Allah ki rufa min asiri tunda nake unguwan nan ban taba fada da wani ko wata ba ina jin tsoron rashin tsoran nan naki wallahi.
Kara daure fuska nayi nace ina ruwa da wata buzuwa ko baturiya take ba zan yarda ta wullakantani ba ga banza don tana takama tana da kudi tunda ba kudin ta nace ta bani ba.
Don Allah dai ki bari ban son irin haka ni na dauka kin bar halin nan naki yanzu da kika girma ashe halin na nan baije ko ina ba.
Mijin ta fa na iya sakawa a kore mu a unguwan nan wallahi don suke fada aji yanzu a garin don Allah dai ki bari.
Kamar zan yi magana sai nayi shiru ranan banci abinci ba saboda haushin buzuwan nan dake ci min rai haka na kwana da tunane kala kala a raina.
Hajiya mama haka ranan itama ta kwana tana tunane a ranta kan yadda zatayi da danta akan buzuwan da ta zama masu fitina da masifa a cikin zuri,an su.
Dan ta ya zubar mata da mutunci da kimar da mutane ge gani nata duk a kan auren wanan matar da bata darajja mutane da halin ta.
Da safe nafito na hada breakfast har na gama ya Amina bata fito ba tana daki na gyara ko ina na gidan sai na koma na shiga wanka na fito na shirya tare da hayewa gado in dan huta.
Sai lokacin na fara jin hayaniyar su a falon gida alaman sun tashi ke nan daga barci hakan baisa na fito ba sai kara lafewa danayi saman gadon barci ne ke son dauka na a lokacin.
Muryan ya Amina naji na bude idona a hankali ina kallan ta daga inda nake kwance nake mata ina kwana murshi tayi ta karaso gare ni tana fadin.
Har kin gama kin kwanta yau barci ne ya dauke ni tana fadi tana kaiwa zaune a saman gadon da nake kwance jin banyi magana sai naji tayi murmushi .
Tace khadija fushi kike yi akan maganan da nayi maki jiya akan buzuwan nan bata da mutunci ne khadija shiyasa kowa ke tsoron shiga tsabganta don mijin ta zai iya keta ma kowa a kanta yadda yake son ta.
Dagowa nayi nace OK shike nan don mijin ta na da kudi ko mulki ba zanyi fada akan dama na na dan adam ba murmushi naji tasake yi tace khadija ina raba ki da shiga tsabgan irin mutanen nan.
Kai na kawar gefe ina hade miyau takaici da yazo min a lokacin haka abin yai ta cina har na gaji na sake na manta da wata can a zuciya.
Jin shiru da su Binta sukayi yasa su ranan biyo ni gida a falo suka samay mu dukkan mu nan muka zauna har anty muna hira suna min korafi wai kullun ina gida kumshe ban fita.
Zainab tace kodai kina tsoron haduwan ki da Nafisa ce nace waye Nafisa kuma tace matar yayan mu mana da kuka kwasa ranan .
Oh kuce mi buzuwa mana ai sai in gane ba Nafisa ashe sunan ta ke nan ni na fi gane ma buzuwa ai Binta tace ai bata son a kira da buzuwa shiya sunan ya mutu a bakin mu.
Ranan da ra kai kara wajen yayan a gidan bakiga irin fadan da yai muna ba ni tun lokacin gidan ya fita raina wallahi.
Ashe ya zama mijin buzuwa ke nan yar sani in fika wai agola da rabon gida ina kika san yar sani in fika ne ai sai kin ga yadda ta mayar da anty Fati a gidan.
Ita da mijin ta yanzu ta koma yar kallo a gidan ko dan aikin gidan yafi ta daraja a gidan kwanan fa sai da ta fito aka maida ita kin san may ?
Da ta koma bata gidan tana dawowa sai cewa tayi wai uban wa yace ta dawo gidan sai ta kama kitchen da komai tarufe na gidan ta hana ma anty Fati da yaranta.
Sai lokacin anty dake gefe ta saka baki a hiran da mukeyi a falon tace amma samun wurin nata yayi yawa wallahi nace wai wace anty fati kuke magana haka ?
Wanan da ta taba haihuwa har mukai fati daku a baya dan tunane nayi nace nagane ta itace mijin ta ya auri wanan matar wallahi itace inji Binta zainab dai sai dakilan wayanta takeyi tana charting.
Anty ce tace yanzun yaya akayi akan abincin nan dai take fada muna yadda suka kwashe da suraj anty ce ke dariya ni banga abin dariya ba tunda ba dukan ta naji yayi ba.
Sun kai wani lokaci suka ce zasu tafi na mike na dan taka masu har bakin get din gidan anty na na dawo ciki.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
Yau ta tashi tana ta farin ciki maigida yace zai dawo garin sai abubuwan taron shi akayi ita da kawayen ta a gidan.
Fati bata san abinda ke wakana ba sai dai gani tayi mata da maza suna ta shige da fice a cikin gidan nasu wanda duk girman shi bai hana a jiyo ihun da suke yi ba a lokacin wai duk cikin murna ne hakan.
Hajiya ce ta aiko gidan a tambayi Fati mai ke faruwa ne gidan nasu amce anga mutane na ta shige da fice a gidan.
Fati tace itama ba ta sani ba itama dai haka ta gani suna shiga suna fita kawai a gidan amma bari ta tambayi laraba taji ko ta sani zuwa tayi ta kira Laraba take tambayan ta abinda ke faruwa tace wai maigidan ne zai dawo shine ake shirin taron shi.
Mamaki Fati taji a lokacin tace yanzu dawowan na yaya Abdul shine shine akewa wanan hiddimar haka ikon Allah ikon gaskiya.
Hajiya mama ma da taji fada tai tayi tana zage zage sai da hajiya ummi da mommy suka ce ta sa masu ido ga duk abinda take yi wani abin saboda neman baki take yin shi.
Ran hajiya ya baci sosai daki ta shige saboda bata son yawan surutu abin kunya abin takaici wai dan da ta haifa da cikin ta a gaban idon su tantirai ke wanan wasan a gidan shi.
Yau ina tarbiyan da tai mai a matsayin dan ta na fari a matsayin shi na jikokin malaimai bu sanadin mace ya samu raini a rayuwan shi macen ma shu,umar mace da tafito yawon barki.
Muryan mommy ya katse ma mama tunane tace nazo ne in ji haka zamu kyale Fati ita kadai a cikin tantiran matan nan.
Mama ta nisa tace may zanyi hajiya karima mommy tace ni a gani na yaran nan suje suma su zauna a dakin Fati din kin ga ko suna da niyar mata wani abinda ba daidai ganin idon su zai sa su fasa.
Abinda kuka yi shawara akai sai ayi ni banda abincewa don wanan yaron ya gama bada tako ina mommy tace kada kice haka yaya kowa yasan ba halin shi bane juya shi akayi ya koma haka.
Murmushin takaici mama tayi tace haka dai kuke cewa amma har da raayi kin san shi tun farko da son farar mace ai doguwa.
Shine dai abinda ke rudin dan naki kawai ba wani asiri wallahi yaya mudai bishi sannu har a samu ma fita yaran ta kwala ma kira duk suka hadu nan take fada masu tana son su shirya gobe idan yayan su zai dawo su je su zauna da Fati a part din ta sai ta sake cewa ina ganin zamu biku ni da antyn ku amarya zan buga waya sauran uan uwanku suzo ba zata zamuyi mata kamar yadda tai muna bazata itama bata fada wa kowa da shafe shi ba.
Nan dai suka taru sukai ta shawaran abinda zasu yi bada sanin buzuwa ba don su rama abinda take shirin masu din na iza masu takaici ta nuna masu su ba kowa suke gare shi ba yanzu.
Muna falon antyna zaune karatu muke da yaranta ita kuma tana duba littafinta na islamiya don tana hadda a wata makarantar matan aure dake unguwar su.
Wayan ta ne yai kara tace dan ta dake kusa da wayan ya miko mata jin ta ce hajiya karima mun wuni lafiya yasa na gane da mommy take waya don aminiyar ta ne sosai mama kuma a uwa ta dauke ta a gidan tafi shiri dasu su biyun.
Bandai ji may suke fadi ba bayan gaisuwa da sukayi sai ji nayi antyna tana fadin kwarai kuwa hakan yana da kyau sosai mommy in Allah ya yarda goben zan shigo dani da khadi tunda tana nan sai muzo a cika taro da mu muma.
Dagowa nayi na kalli antyn nawa don jin abinda tace bayan sun gama waya ne take ce min ikon Allah wai dan gidan hajiya mama ne ya samu karin girma bai fadawa yan uwan shi ba sai gani sukayi matar shi tana ta shirin buki ita da kawayen ta.
Haushi naji a raina nace shiya sani mana duk wanda ya wullakanta iyayyen shi ai kan shi yai wa wasu ma suna can suna neman iyayyen ido rufe basu samu ba.
Shi ya samu Allah ya bar mashi nasa a raye shine zai wullakanta su antyna tace ai shi na gani nima wallahi.
Shi fa dama haka yake kamar mai tsoron mutane yake hadewa da buzuwan nan da yayi sai abin ya kara bulakucewa mai.
Yanzu hajiya karima ta kirani ne tana fada min wai gobe tana gayyatan mu zuwa gidan nashi don suma zasuyi nasu taron a part din Fati.
Kai amma suma dai basu da zuciya wallahi akan may ba zasu saka mashi ido suga iya gudun su ba ai mutum baiyi sai da nasa.
Ni dai ba zan je sai kun dawo don babu komai wurin nan sai tarin takaici tace a a don may bazaki ba ba gaiyyatan mu sukayi ba muje mu mara masu baya a cika taro da mu muma.
Ban iya bata amsa ba sai ma cewa da nayi da yaron ta kana jina ko muci gaba da karatun mu dajin wanan abin takaicin.
Duk abinda muke sai na gaza yi sai cewa nayi da ita wai mashi wani irin mutum ne haka wai tace ai zaki ganshi gobe idan munje gidan.
Washe gari ko da wuri anty tasa muyi aiyukan da muka saba a gida muka gama komai akan lokaci.
Tace mu shirya zuwa karfe uku mushiga gidan su mommy din raina bai so ba haka na shirya dole cikin wani buje dariga na atampha da nayi dinki shi a abuja atamphan pink ce don haka shirgan pink colour nayi na ni kaina nasan kayan sun karbe sosai don sun fitar min da sura na fili.
Muka fito muka rufe gidan muka nufi gidan da kafa saboda ba nisa sosai abin mamaki sai samu mukayi duk yan uwa da abokan arziki sun hadu a family house din nasu.
Mun dan shiga dakin mommy ita kirjin abin nikan ganin duk matan aure ne a ciki yasa naja yaran anty muka wuce dakin mama wurin su zainab.
Ba wasu mutane a dakin sosai sai ita da yaran ta kuma da alama kamar wani magana mai muhiamci suke a lokacin sai naji na tsargu ga yadda na gansu din a lokacin saboda kar na takura masu dana gaida su sai na mike zan fice daga dakin.
Muryan mama din naji tana cewa a a dawo abinki ki zauna ai ba wani magana muke yi ba cikin muryana da yake kamar sallo da yanga nace No bari kawai na tafi daga waje ai.
Binta ne ta fito daga cikin daki tace muryan ki naji yasa ni fitowa yanzu wai rangas wanan irin kwalliya haka ai sai ki sa kallo ya koma kan ki.
Guntun murmushi nayi nace da ita silly girl ina zainab ashe tana kusa da mama zaune saboda cika min ido da sukayi ne banganta ba tace gani nan bakiji ina cewa khady ba da kika shigo.
Binta ne tace mu shiga daga ciki mu zauna sai maman tace a a tazo nan ta zauna abinta ki sakata ciki kamar kunshi matsa min take yi wai nazo na zauna a kusa da ita ban hau kujeran ba sai na zauna a kasa kusa da kafafuwan ta.
Ina zama tace da yaranta masu aure mutum biyu kun ganta nan ranan ta burge ni da ta tsaya taci wa yar iskan yarinyar nan mutunci ido rufe akan titi taso ta kawo masu rainin hankali a saman hanya ita ko ta wanke ta tas wallahi.
Anti fauziya tace kin min daidai wallahi dama ai ganin ana daga mata kafa ne yasa takewa mutane iskanci wai ita a dole matar mai kudi.
Nan dai suke ta maganganun su a wurin kamar daga sama muke jiyo haya niya wata ta leko tana fadin ga yaya Abdul nan ya iso kuma nan ya fara shigowa.
Fita suka kama yi a raina nace ashe shiyasa yake maku abinda yaga dama saboda hakan da kuke mai nidai ina zaune a kusa da hajiyan tasu.
Ganin yaran nata sun fita yasa ta mayar da hankalin ta a kaina tana fadin dada dai yanzu khadija gudun mu kikeyi baki ko son shigowa gidan nan in kin zo na dan yi murmushi nace no mama ba haka na bane kawai dai daurowa ne.
Nan take dan jana da hira cikin rashin sakin jiki nake dan bata amsa a hankali ganin dandazon mutane sun nufo dakin nata ne yasa na mike zan bar wurin tace dani koma ki zauna abinki yanzu fita zasuyi idan mun gaisa.
Wani farin mutum ne ya dumfaro kofan zai shigo kamshin turaren shi kawai ya isa ka dago kai kaga ko waye maishi nan dandazon yan uwa suka dare a kofan dashi da wani suka shigo dakin kawai ba wanda ya shigo bayan su sai ni da mama da yaron anty na da muke zaune a dakin a lokacin.
Mayar da hankali na na nayi ga wayana dake hannu na a lokacin ban daga na kallesu ba suka zube kasa suna gaida mama din cikin girmamawa.
Tace dashi bayan sun gaisa ashe kana tafe baka fadawa kowa ba harda samun abin arzikin da kayi bamu kai girman da zaka sanar damu hakan ba a yanzu sai dai muji ga shanun talla ana fadin wai ka samu karin girma a ma aikatar ku.
Yace ba hakkana bane mama bari nayi sai nazo in fada maku dama ashe ma kun riga da kunji abinda ba a ko rantsar dani ba tukun .
Daidai lokacin na dago kai cikin jin haushi na watsa mashi wani irin harara ban sani ba ashe idon shi yana kaina a lokacin cikin rashin sani na nayi saurin dukar da kainanajigina da kujeran da mamake zaune tare da mayar da kaina ga wayana da nake duba.
Wanan wata yarinyace haka miskila har da zata iya hararana da nuna min ko in kula yace a ranshi in dai zaka sake hali wallahi kasake mudin dai mune iyayyen ka ba wasu ba.
Yanzu ka duba fadin gidan nan kaf yan uwa ne da abokan arziki da mommyn ku ta gaiyato suka zo don ka idan ba a zumunci waza ka gani a nan yanzu kai hakan ma da sukai maka bakaji dadin shi ba.
Ace mutum babu nashi wanda ya ja a jiki sai dai yan duniya masu maka rudi da duniya kaina na kada alaman fada mashi dai mama na tabe baki na.
Wayana ne yai kara a lokacin baba nane ya kirani da sauri na dauka cikin kashe murya nace daddy yau kaji ban kiraku ba ka kirani yanzu nake son kiran ka a yanda nake magana da mahaifina cikin sakewa da walwala kamar ina magana da wani sa a na sai mutum ya saurara zai iya jina don kada in damay su in hana su maganan da suke yi din.
Muryan su naji yana fadin mama zan shiga gida in huta don ban isa can ba nan na fara shigowa in gaida ku.
Har lokacin yanayin ta ba dadi Allah ya sauwaka naji ta fada masu tace Yusuf ashe kuna tare yusuf din da ya dukar da kan shi tunda mama ta fara mai fada sai a lokacin yayi magana yace eh mama tun da ya bugo min zai dawo ai naje abujan taron shi.
Mikewa sukayi zasu bar dakin tace kaji an mayar da Fati dakin ta ko hakan yasa shi tsaya yace naji mama.
Wani sabon hararan na dago in aika mai still muka kara hada ido yasha toka a lokacin yace zamu tafi Allah ya tsare ta kara maimaita mai suka fita dakin.
Ajiyan zuciya na sauke bayan fitan su mama din tace kin ga yayan ku ko yau khadija nasan kila baki san shi ba.
Murmushi kawai nayi mata nan sauran diyan suka shigo suna fadin su mommy sun fita ance gidan ya cika da mutanen Nafisa don haka mu zamu wuce can.
Kafin ya gama ganawa da baba su zainab suka fito suka ce in tashi mu tafi Allah ya gani da zasu bar ni in zauna wurin mama da zai fi mun dadi don ban son hayaniya da yawa ga matar gidan da mai gidan da nake kule dasu a raina.
Ganin mota zamu shiga yasa na dauka gidan yana da nisa sosai ashe ma ba wani nisa muna shiga mata yan duniya ne birjit a farfajiyan gidan zazaune saman kujeru farare sai kidan dj dake tashi kamar wani buki akeyi mai muhinmanci a gidan.
A raina nace kudin banza a bazan suke tafiya mommy na gaba ita da anty amarya muna biye da yawan mu a bayan ta muka shige gidan.
Nan naga duniya a cikin gidan sai kace ba a garin kaduna muke ba part din Gatin muka shiga a sama suke dukan su mun samu tayi kwalliyanta ba laifi nikan a nan falon ta na zauna zainab ma da namu yazo daya

Please Login or Register in order to submit comment