Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

wani ruwa mai daɗin ƙamshi, ga wasu fulawoyi da suka bai baiye saman ruwan, cikin natsuwa da kuma salo yake mata wankan, yayin da Ma'u take jinta kamar wata sarauniya...
Haka aka gama wankan nan cike da soyayya, na ɗo ta yayi a towel, ya fito da ita daga bathroom ɗin, shimfiɗeta yayi akan bed ɗin dake cikin ƙayataccen ɗakin, shafe jikinta yake ta ko ina, a haka wani ɓarawon bacci mai ɗan karan daɗi yayi awon gaba da ita....
Bayan Haidar ya samu mutsuwar da yake so ya samu da ita, sai ya mirgina gefen ta yana ƙare mata kallo, cike da tsantsan so da ƙaunarta...

Koda Ma'u ta tashi, idonta da Haidar ya fara tozali, murmushi ta sakar mai, shima martanin murmushin ya mayar mata, sa'annan yace

"Fatan kin tashi lfy! Gimbiyata kuma sarauniyar da take mulkar zuciya ta."

Murmushi Ma'u tayi ta sunkuyar da kai, matsowa Haidar yayi kusa da ita yace
"Meye matsalar ki! Yanzu na miki maganin ta, dan zan iya komai akan ki hasken idaniyata.."
Ɗagowa Ma'u tayi sannan tace

"babu komai! Kawai na tuna mafarkin da nayi jiyane, kana sawa wani gida wuta, kuma da safe a kace gidan Alh Tanko ya ƙone, shin hakane da gaske kai kasa! Ko kuma mafarkin ne kawai..?"

Gira ya ɗaga mata alamar eh hakane, sannan yace

"Tabbas ni nasawa gidan sa wuta, kuma da ace bai janye maganar aurenki ba, to yau da shi zan ƙona, saboda danni kaɗai aka halicceki, ina ji ina kallo bazan taɓa barin wani namijin bil'adama Ya raɓeki, ke ko al'jani ne ya zo wucewa ta inda kike muduk ya kalleki, to sai na hukunta shi ko waye shi ɗin, kuma ko ɗan waye acikin jinsin al'janu....✍️





*Ina jin koken ku na cewa ya kamata akawo, wanda zai yi maganin haidar*

*To koken ya iso gareni amma saide fa kusani Haidar shine lbrn in ba haidar to ba lbr*👌😄





*MORE COMMENT*
*MORE TYPING AKAI AKAI*✍️👌

*PLS SHARE*











~MATAR KHAMIS CE 🥰💃~
[6/7, 12:41 PM] Matar Khamis,: 👄👄👄👄


*NAMIJIN DARE*
_aljanin soyayya_✍️



```story and writing```



*by*
*_ummy mrs khamis_*
09137879957


________________________________________________________________________________


*WOMEN WRITERS ASSOCIATION*📚

_(Domin Marubuta Mata)_

✨(W.W.A)✨


https://www.facebook.com/106752595253176/posts/107924965135939/




*short story*



*TSOKACI* :
```Wannan lbri ne ƙirƙirare ban yishi dan wata ko wani ba idan yayi kaman ce ceniya da rayuwar ka/ki afuwan akasi aka samu💁‍♀️```



```bissimillahir rahamanur rahim```



*_dukkan yabo da godiya su tabbata ga Allah ( s w a ) aminci da tsira su tabbata ga Annabi Muhammadu {s.a.w}_*



______________________________________



SADAUKARWA!!

ZUWA GA DUK MASOYA NA🥰💃




*bissimillahir rahmanir rahim*


____________________________________________________________




*26 & 27*




____________Zuba masa ido kawai Ma'u tayi, tana matuƙar mamakin furucinsa da yake cike da alwashi....
San sanyar ajiyar zuciya Ma'u ta saki a hankali tace
"To meyasa zaka aikata hakan..?"
Saida yaja dogon numfashi sannan yace

"Saboda ina sonki kuma ina ƙaunarki, Wallahi duk duniyar nan babu wanda ya kaini sonki da kishin ki, shiyasa ban ƙaunar inga ko wani ɗa namiji naga ya raɓeki koda kuwa shi waye.."

Ita dai Ma'u ido kawai ta zuba mai tana mamakin son da Haidar yake mata, gashi kuma wani ɓangare na zuciyar ta, yana kwaɗaita mata son yin aure ko dan hankalin innarta ya kwanta...
Haidar kamar yasan abinda take ayyanawa a ranta, hannunta ya kamo sannan a hankali yace

"Husnah ni ban isheki ki ƙare rayuwar ki dani ba?, Zan baki duk wani farin cikin da bil'adama bazai iya baki shiba, zaki kasance a cikin zuciyar da bazata taɓa yi miki kishiya ba, zan nuna miki soyayyar da ba'a taɓa yiwa wata ƴa mace ita ba a cikin duniyar masoya, ki cire tunanin auren wani bil'adama, ni nan kaɗai na isa na baki farin cikin da babu wani mahaluki da zai iya baki shi..."

Lumshe ido Ma'u tayi yayin da hawaye yake kwaranyowa daki daki, rungume ta Haidar yayi, yana bubbuga bayanta a hankali alamar rarrashi...
Cikin raunin murya Ma'u tace.
"Haidar nasan kasan cewa, innarmu bata da wani buri da ya wuce taga nayi aure, kuma gashi.....
Yatsar sa yasa a leɓenta yace
"Shishhht! Nasan komai basai kin gayamin ba, amma ga tambaya ɗaya zuwa biyu da zan miki, idan na samu amsar ta dai-dai yadda nake so naji to zan yanke hukunci da ya dace.."
A hankali Ma'u ta ɗago tana kallon cikin idonsa, duk da dai har yanzu bata iya kallon cikin idonsa, sunkuyar da kanta tayi tana kallon ƙasa....
Ɗago da kanta Haidar yayi sannan yace
"ki kalli cikin idona mana, pls mana masoyiya ta."
Kallo shi take cikin ido, yayin da take ji duk tsigar jikin ta tana tashi, yanayin salon kallon da Haidar yake mata, sai ya jefata cikin wani yanayi jinta take kamar ba ita ba, Saida ya ɗau wasu ƴan sakanni sannan yace,

"Kina sona! Kuma zaki iya rayuwa dani.?"

Girgiza kai Ma'u tayi alamar eh, hannunta Haidar ya kamo sannan cikin wani irin salo yace.
"Da bakinki nake so naji kin amsa min."
Eh kawai Ma'u tace a taƙaice .
Cikin murna da zumuɗi Haidar yace
"Da gaske! Kuma kinyi alƙawari.?"
Ma'u tace "eh mana." Ta faɗa tana murmushi..
Rungume ta Haidar yayi, yana jin farin ciki marar misaltuwa, a ganin sa tunda Ma'u itama tana sonshi to dukan matsalolin sa sunzo ƙarshe..
Haidar bai maida Ma'u ba sai gabda magribah, kai tsaye ɗakinta ya ajje ta...

Bayan ta gama shiryawa tsakar gida ta fito, samun zahrah tayi har ta gama girkin dare, kasancewar inna gwana ce wajen koyawa yara girki, ko kaɗan bata so taga yaro ya taso bai iya girki ba...
Dundu Ma'u ta kaiwa zahrah a baya, sannan tace
"autar mu! ina innarmu take ne".
Inna dake fitowa daga cikin ɗaki, fuskarta da alamun bacci tace

"Gani wake nema na?".

Ma'u tace
"nice innarmu."

"Ohh Wllhi nasha baƙuwa nayi,"
Inna ta faɗa tana ɗaukar buta...
Zahrah dake durƙushe tana dariya tace "innarmu ina ga baccin bai isheki ba."
Guri Ma'u ta samu ta zauna tana cewa
"da alama kuwa gaskiya."
Haka rayuwa tayi ta tafiya kullum soyayyar Ma'u ƙara lunkuwa take a zuciyar Haidar, musamman yanzu da yake ganin bashi da wani abu da ya shige masa gaba.....

Ta ɓangaren Ma'u kuwa saide muce subhanallah, Dan yanzu babu wanda yake zuwa yace yana sonta, ita dama ko a jikin ta dan duk namijin da ta kalla, saide taga ya zaman mata abin tsoro ko taga muninsa, Haidar shi kaɗai take ganin farinsa a doron duniyar s nan, sai ƴan uwanta maza wanda suka kasance muharramanta, amma sauran maza ita dasu *hai hata-hai hata*.......✍️






*More comment*
*More typing*
*Pls share*








~MATAR KHAMIS CE 🥰💃~
[6/8, 8:48 AM] Matar Khamis,: 👄👄👄👄


*NAMIJIN DARE*
_aljanin soyayya_✍️



```story and writing```



*by*
*_ummy mrs khamis_*
09137879957


________________________________________________________________________________


*WOMEN WRITERS ASSOCIATION*📚

_(Domin Marubuta Mata)_

✨(W.W.A)✨


https://www.facebook.com/106752595253176/posts/107924965135939/




*short story*



*TSOKACI* :
```Wannan lbri ne ƙirƙirare ban yishi dan wata ko wani ba idan yayi kaman ce ceniya da rayuwar ka/ki afuwan akasi aka samu💁‍♀️```



```bissimillahir rahamanur rahim```



*_dukkan yabo da godiya su tabbata ga Allah ( s w a ) aminci da tsira su tabbata ga Annabi Muhammadu {s.a.w}_*



______________________________________



SADAUKARWA!!

ZUWA GA DUK MASOYA NA🥰💃




*bissimillahir rahmanir rahim*


____________________________________________________________




*28 & 29*




____________Haidar ne zaune a cikin wani lambu mai cike da furanni, iskar dake kaɗawa agurin da ƙamshin furannin sai suka haɗu suna bada wani ni'imtaccen yanayin dake sanya nishaɗi....
Babu abinda zuciyar sa ke hararo masa irin masoyiyar sa Ma'u, hannunsa ya shafa abun mamaki sai ga ma'u ta bayyana, ajikin hannun nasa kamar tv, kallon ta yake cike da shauƙi yana murmushi, gani yayi tana cokano baki kamar wata ƴar ƙaramar yarinya, hakan kuma yana matukar birge Haidar, sumbatar ta yayi ta jikin hannun nasa yana cigaba da kallon ta...
Ma'u kuwa da taji an sumbaceta sai ta ƙara cunno bakin nata kamar wacce take jiran tsammani.......

Haidar da yake kallon ta yana ƙara faɗaɗa murmushin sa, jinsa yake yafi kowa Sa'a a duniya, dan idan yana kallon ta mantawa yake da komai, jin motsi a ta bayan sa yasa da sauri ya shafi hannun sa, tuni hoton Ma'u ya ɓace a hannun nasa....
Abokinsa ne I'liyas, ya ƙara so yana cewa

"Toh Mijin bil'adama ashe kana nan! Ko bil'adamar taka kake tinani?."
I'liyas ya faɗa cike da
tsokana da kuma shaƙiyanci......
Haidar dake kallonsa yana hararar sa yace

"Mai zai sa inyi tunanin ta bayan ko da yaushe ina tare da ita, yanzu mah ina cikin ganinta, kazo ka katse min jin daɗi na.."
Baki kawai I'liyas ya saki yana kallon sa sannan daga bisani yace

"Ni ba wannan ba! ko zaka iya nuna min masoyiyar taka, naga wani irin kyawu gare ta da har ya ja hankalin ka."

Shiru Haidar yayi kamar mai tunanin wani abu jim kaɗan kuma sai yace

"Gaskiya bazan nuna maka ita ba.."
"Saboda me?."
I'liyas ya tambaya cikin mamaki,
Haidar yace "Saboda ina matuƙar kishin ta sosai, banso inga kowa yana kallonta indai namiji ne.."
I'liyas yace "lalle abin naka azimin ne, amma har ni da nake a matsayin abokin ka, baza ka nuna min ba.."
Tashi i'liyas yayi zai bar gurin kamar yayi fushi, ganin haka da Haidar yayi sai ya riƙo hannun sa yace
"yi haƙuri abokina zo in nuna maka ita."
Dawowa i'liyas yayi ya zauna, hannunsa haidar ya shafa sai ga ma'u ta bayyana, sakamakon ɗazu tana bacci yanzu kuma idonta biyu kawai dai tana kwance ne, kamar yadda yace kallo ɗaya i'liyas zai mata, hakan kuwa ta kasance yana kalla Haidar ya janye hannunsa....
I'liyas a ransa yace ba laifi tana da ɗan kyau, amma a fili sai yace wa Haidar
"Gaskiya na yarda da ake cewa so makaho ne, to tabbas haka ne! So babbar makanta ce, na farko ni banga wani kyawun da zaija hankalin ka zuwa gare ta ba, wanda har ace babu matan da suka fita kyau ba acikin jinsin al'janu, sannan ƙari wata makantar shine da har idonka ya rufe, ka kasa sanin dai-dai da kuma akasin haka.."

Haidar da izuwa yanzu ya fara fusata da abinda I'liyas yake ce mai, cikin fushi yace
"to ai bakasan wani abu ba! duk duniya babu wanda nake so yace Nurul aini tana da kyau, hakan da ka faɗa shine daidai, dan da ace cewa kayi tana da kyau to Wallahi da zan iya jin haushin ka, amma da ka faɗi akasin haka naji daɗi sosai, ni kaɗai nake so in yabeta kuma naga kyawunta.."

I'liyas yace "lalle kam."

"To da kake cewa ma na kasa sanin dai-dai da rashin sa kuma, to ai saika faɗa min mai na aikata na rashin daidai ɗin.."
Numfasawa i'liyas yayi sannan yace
"Gaskiya baza ɓoye maka ba, kai abokina kuma mai faɗa min gaskiya idan nayi kuskure, ka auri jinsin da ba naka ba kuskure ne abokina, ka killace ta, ka hanata kula kowa, ka ƙi bari jinsin ta ya aure ta, ya kamata kasan cewa hakan da kayi kuskure ne abokina, lokaci yayi da zaka farka daga barci da kake ka fita a rayuwar ta haka nan, ka barta tayi au...."
Wata gigitarciyar tsawa da Haidar ya daka mai Saida gurin ya amsa haɗe da bada wata iriyar girgiza, ba shiri, i'liyas yayi shiru daga nasihar da yake mai, wanda hatta tsuntsayen dake gurin Saida suka tsorata da sauran wasu halittu da ke gurin....
Cikin tsantsar fushi Haidar yake cewa
"Ba ina sonta bane dan in cutar da ita, ina sonta ne da in bata da farin ciki, kuma ba ina sonta bane dan in haɗa soyayyar ta da kowa ba, haka kuma bazan taɓa jurar na ganta ta haɗani da wa ni ba..."
Idanun sa ya Lumshe da suka rine suka koma baƙiƙirin, cigaba yayi da cewa "I'liyas ina so kafin na kefta idanuna, ka ɓacemin da gani, kayi nisa da inda zan iya hangowa, muduk ka bari na ganka sai nama lahanin da har ka ƙare rayuwar ka bazaka manta da shi ba..."
Ɓacewa I'liyas yayi kamar yadda haidar ɗin yace, Saida yayi nisa daga inda haidar yake sannan ya bayyana a gurin, saƙa da warwara kawai yake can kuma sai yayi murmushi yace "Wallahi Haidar saina rabaka da bil'adamar da kake iƙirarin cewa matar kace.."

Shi kuwa Haidar ganin iliyas ya bar gurin, sai shima ya tashi da niyar barin gurin acewar sa iliyas ya ɓata mai rai bari yaje inda zaiji dama dama......


★★★
Ɓangaren su Ma'u kuwa zaune suke a tsakar gida, sun shimfiɗa tabarma suna ta hira abin su cikin kwanciyar hankali, kasancewar ƴan uwanta mata sunzo musu ziyara yau, sai hirar su suke gwanin birgewa, Ma'u dake tsakiyar su baza ka taɓa cewa itace yayarsu ba, zakayi tunanin duk sun girmeta...
Inna dake gefe tare da ƴan jikokinta, sai wasan su suke abinsu, ɗagowa inna tayi ta kalli Ma'u a ranta ta ayyana cewa Allah sarki kema da kinyi aure da kina nan da ƴaƴan ki, Allah ka dubi wannan baiwa taka ka fito mata da mijin aure nagari tayi auren ta....✍️










*More comment*
*More typing*
*Pls share*








~MATAR KHAMIS CE 🥰💃~
[6/8, 7:45 PM] Matar Khamis,: 👄👄👄👄


*NAMIJIN DARE*
_aljanin soyayya_✍️



```story and writing```



*by*
*_ummy mrs khamis_*
09137879957


________________________________________________________________________________


*WOMEN WRITERS ASSOCIATION*📚

_(Domin Marubuta Mata)_

✨(W.W.A)✨


https://www.facebook.com/106752595253176/posts/107924965135939/




*short story*



*TSOKACI* :
```Wannan lbri ne ƙirƙirare ban yishi dan wata ko wani ba idan yayi kaman ce ceniya da rayuwar ka/ki afuwan akasi aka samu💁‍♀️```



```bissimillahir rahamanur rahim```



*_dukkan yabo da godiya su tabbata ga Allah ( s w a ) aminci da tsira su tabbata ga Annabi Muhammadu {s.a.w}_*



______________________________________



SADAUKARWA!!

ZUWA GA DUK MASOYA NA🥰💃




*bissimillahir rahmanir rahim*


____________________________________________________________




*30 & 31*



*KATSINA CIKIN GARI*

___________A wata ƙasaitacciyar anguwa da tafi kama da ta masu mulki, dukkanin gidajen dake jere a wannan anguwa gaba ɗaya su haɗaɗɗune, idan ka kalli wannan zaka yi tunanin wancan yafi wannan kyau da tsari, amma sai dai kana kallo zaka hango wanda ya fisu....
Wani gida da yafi jan hankali na shi naga an buɗe get ɗin gidan, yayin da motoci na alfarma ke shiga kamar an rako shugaban kasa filin jirgin sama...
Bayan motocin sunyi fakin a inda ya dace, ma'aikatan gidan suka taho da hanzarin su, har rige-rigen buɗe Bayan motar suke, wanda hakan ya nuna alamun suna farin ciki da zuwan sa, a hankali aka buɗe murfin motar, tare da zuro ƙafafuwan sa waje, sai ya ɗau wasu ƴan sakanni sannan ya fito gaba ɗayan sa...
Alhaji Ibrahim naga ya fito daga cikin tare da wata mata, da dukan alamun dai matar sa ce, sai wasu matasa guda biyu dake binsu a baya, tahowa suke cike da tsantsar farin ciki da murnar ganin juna...
Suraj kenan matashi kuma baƙin fata na farko da yake tuƙin jirgin sama, a ƙasashen ture, kyakkyawa ne shi ajin farko ga kuɗi ga jin daɗin duniya duka Allah ya bashi.....
Ganin iyayen nasa lafiya hakan ya sashi nishaɗi da farin ciki, jikin ladabi da biyayya ya tsugunna har ƙasa ya gaishar dasu, dan suraj akwai ɗa'a, ƙannen sa suma suka gaishe shi cikin girmamawa suna mai sannu da dawowa.....
Ɗunguma sukayi gaba ɗaya suka shiga cikin gidan, a falo suka yada Zango nan suka zauna aka sake wata sabuwar gaisuwar yaushe gamo, haɗe da ƴan hirarraki kaɗan kaɗan....
Momy ce ta kalli mubarak tace
"ka cewa yayan ku yaje yayi wanka sai ya fito muci abinci."
Shi kuwa Suraj jin tace haka sare yasan dashi take, kawai dai ta fake da mubarak ne, sai yaji bai ji daɗin hakan duk da cewa ya saba da wannan ɗabi'ar ta Hausa Fulani, ace wai uwa baza ta iya kallon ɗan ta na fari ba, bare har tayi doguwar magana dashi....
A sanyaye ya tashi ya shige ciki domin ya watsa ruwa, suma sauran tashi suka yi kasancewar magribah ta gabato, Alhaji Ibrahim ya kalli Momy yace
"Wai ina jiddah take ne! Bata zo taga babanta ya dawo bane.."
Momy tace "ni Wallahi nama manta in tashe ta Barci take, gashi yamma tayi yanzu, tun ɗazu take jiran dawowar tasa har ta gaji da jira bacci yayi awon gaba da ita.."
Daddy yace "to gaskiya je ki tashe ta, daga nan sai ki faɗa mata babanta ya dawo.."
Tashi Momy tayi tana dariya tace "yanzu kuwa kaga tsalle tsalle a wajen jiddah.."
Hayewa tayi saman bene da shi kuma Daddy ya fice masallaci...


★★★
Bayan magribah kuwa Momy ce ke ta ciku-cikun haɗa musu dinner akan darduma, dan Daddy baison hawa danning ya fison cin abinci a ƙasa wannan yasa har iyalen gidan sa sun saba da hakan....
Wata yarinya ce da baza ta wuce shekara biyar ba, ta fito daga cikin ɗaki da gudu, yarinya sak Suraj kamar yayi kaki ya zubar, cikin Muryar ta ta ƴan yara tace
"momy ina Daddyna yake! Kin ce inayi sallah zan ganshi yana ina..?"
Momy tace
"to Sarkin tambayoyi! Kije yana ɗakinsa, kuma ki tafi a hankali.."
Taku uku tayi a hankali sannan ta zuba da gudu. Ɓangaren Daddy nata tayi tana kiran sunan shi...
Suraj dake zaune kan sallaya yana zikirin yamma, dan suraj Masha Allah akwai son ibada....
Shigowa tayi da gudu ta, faɗa jikin sa tayi tana ihun murna, rungume ta yayi yana ƙara jin son ƴar tasa da kuma ƙaunar mahaifiyarta,
da ta rasu wajen tsawon shekaru biyar kenan, ranar da ta haifi jiddah Allah ya karɓi ranta tun daga nan Suraj bai ƙara yin aure ba, dan ko zancen auren aka mai sai yayi kuka, a ganin sa bazai samu mace tamkar mahaifiyar jiddah ba.....
Jiddah ce ta katse masa tinanin da yake wajen cewa
"Daddy ka taho min da tsaraba ta.?"
"Eh mana sarauniya ta! Yanzu muje gurin momy muci abinci sai mu dawo, na nuna Miki tsarabar ki.."
Ɗaukar ta yayi suka wuce babban falon gidan, kasancewar anan suke cin abincin.....
Bayan an gama cin abincin ne Alhaji Ibrahim ya kalli Suraj yace

"Am!! Suraj ya maganar mu da kai kan ka tafi U.S. , akan zuwa ganin ƴar aminina Salisu, fatan dai baka manta ba.."

"Eh Daddy ina sane! Amma yanzu ina ganin kamar za'a iya mata aure, tunda kaga yanzu shekara biyu kenan dayin maganar.."
Daddy yace "tabbas hakane insha Allahu gobe sai muje can batsarin, in yaso in an mata aure to dama can ba rabon ka bace ita..."
Suraj yace "to Allah ya kaimu.."
ya faɗa cikin ladabi, hira suka cigaba da yi ciki nishaɗi har lokacin sallar isha'i yayi, sallar isha'i kuwa kowa yayi nasa gun.....
Washe gari kuwa da shirin su, suka tashi sai ƙaramar hukumar batsari........


★★★
Ɓangaren Ma'u kuwa yau tunda ta tashi take jin faɗuwar gaba, tun tana daurewa har ta gayawa inna halin da take ciki, inna kuwa sai ta kwantar mata da hankalin cewa INSHA ALLAHU alkairi ne Ma'u karki damu kedai kiyi ta addu'a, nima ina miki fatan alheri.
A haka har bacci yayi awon gaba da ita, cikin baccin ne take mafarkin wani mutum ya ɗaure Haidar yazo ya jata sun tafi, shi kuma haidar dake ɗaure sai kiran sunan ta yake amma mutumin yaƙi sakar mata hannu, tayi ƙoƙari taga fuskarsa amma ta kasa, a daidai lokacin ne Ma'u ta farka a zabure, tana mamakin wannan mafarkin da tayi, a ko da yaushe saide tayi mafarkin Haidar yana cutar wasu amma yau shi aka cuta......✍️





_alhmdllh yau dai nayi post sau biyu a rana hakan ya faru ne sakamakon comment ɗinku musamman facebook ina yinku ƴan facebook da ace zan iya dana ambaci sunayen ku saide ba lokacin haka amma insha Allah zan ƙoƙarta hakan_





*More comment*
*More typing*
*Pls share*









~MATAR KHAMIS CE 🥰💃~
[6/9, 12:37 PM] Matar Khamis,: 👄👄👄👄


*NAMIJIN DARE*
_aljanin soyayya_✍️



```story and writing```



*by*
*_ummy mrs khamis_*
09137879957


________________________________________________________________________________


*WOMEN WRITERS ASSOCIATION*📚

_(Domin Marubuta Mata)_

✨(W.W.A)✨


https://www.facebook.com/106752595253176/posts/107924965135939/




*short story*



*TSOKACI* :
```Wannan lbri ne ƙirƙirare ban yishi dan wata ko wani ba idan yayi kaman ce ceniya da rayuwar ka/ki afuwan akasi aka samu💁‍♀️```



```bissimillahir rahamanur rahim```



*_dukkan yabo da godiya su tabbata ga Allah ( s w a ) aminci da tsira su tabbata ga Annabi Muhammadu {s.a.w}_*



______________________________________



SADAUKARWA!!

ZUWA GA DUK MASOYA NA🥰💃




*bissimillahir rahmanir rahim*


____________________________________________________________




*32 & 31*




____________Haka ta tashi tana al'ajabin wannan mafarkin da tayi, ji tayi wani sanyi yana ratsa mata zuciyar ta, sakamakon ɗazu da gabanta yake faɗuwa...
Tashi tayi ta fito waje, samun inna tayi zaune tana gyara wake, sai kuma auta zahrah dake wankin uniform ɗinta, sannu da hutawa tayi musu sannan ta zauna, waken da inna take gyarawa Ma'u ta karɓa, cigaba tayi da gyaran suna ɗan taɓa hira jefi-jefi.......

Ƙarfe 12:00 daidai suka ji sallamar kawu Salisu da wasu baƙi, ganin Alhaji Ibrahim da inna tayi yasa da sauri ta tashi tana "lale marhaban! sannun ku da zuwa, ku ƙara so ciki.."
Cikin ɗakinta inna ta kaisu, tare da shimfiɗa musu ƙatuwar dadduma, nan suka zauna aka fara gaishe gaishe cikin mutunta juna, Alhaji Ibrahim ya gabatarwa da inna Momy da ƴaƴan sa maza guda uku, inna tace "masha allah! Allah yayiwa rayuwa albarka." Gaba ɗaya suka amsa da ameen....

Ma'u dake tsakar gida tana shirya abincin rana, sai kaiwa da komowa take, Dan ma'u gwana ce wajen girki, zahrah ce ta shigo da katan ɗin ruwan gora a hannun ta da ta siyo a shago, da hanzari Ma'u ta karbi ruwan ta ɗauki ƙaramin tire ta ɗora kofuna akai, ta shiga dashi ɗakin da suke......

Koda ta shiga cikin taga sun zuba mata ido, Ma'u dama gata da tsoron mutane Musamman ma taga akwai maza a gurin, a dabur ce ta tsuguna ta gaisher dasu amsawa sukayi gaba ɗaya, suna kallon ta...
Shi kuwa Suraj da bai ɗago ba kallon ta yake ta ƙasa ƙasa, idonsa ya faɗa kan ƙafar ta, da take fara sol, kamar bata taka ta a ƙasa, ji yayi ƙafar ta burge shi dan shi yana son yaga ƙafar mace kyakkyawa koda kuwa bata da kyawun fuska...
Sauri yayi ya kawar da tunanin da yake a ransa, yana fatan Allah yasa yarinyar da za'a haɗa shi da ita tana da hankali.....
Tashi Ma'u tayi ta fita daga ɗakin ta barsu suka cigaba da hirar su da su inna, ganinta da Alhaji Ibrahim yayi sai yaji daɗin hakan, dan haka kurum ta kwanta mai a rai, kuma yana da tabbacin zaman su zai zo ɗaya da Suraj....

Kiran sallar azzhar ne yasa kawu Salisu yaja su zuwa masallaci, a hanyar su ta dawowa ne Alhaji Ibrahim yake cewa kawu Salisu
"wannan yarinyar Asma'u! Da nagani yanzu shin maganar mu da kai ta kwanakin baya da suka wuce, tana nan Ko kuwa an mata miji..?"
Kawu Salisu yace
"ah ah! Ba'a yi mata ba."
Nan kawu Salisu ya kwashe dukan abinda ya faru bayan rabuwar su ya faɗa mai, shima Alhaji Ibrahim labarin dalilin da yasa ba su zoba yaba shi, sannan ya ɗora da cewa "yanzu haka ma a shirye suke, dan sunzo da Suraj ne yaga Ma'u, su shirya kansu in sun daidai ta ayi musu aure.....
Kawu Salisu yayi murna da hakan, har suka ƙarasa gida kawu Salisu yana murna, bayan sun shigo ne, sannan Ma'u ta gama girkinta zubo musu tayi a kula ta kawo musu, haɗe da kawo musu fulet ɗin da zasu ci tayi

Please Login or Register in order to submit comment