Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

'Yan-Adam.
Saboda haka ni ma ina mana fatan alkhairi tare
da fahintar juna."
Sageer ya jinjina kai, ya ce,"Amin.
Naseer ka ji, ko kuma in bari in ba ku wuri ku
gaisa."
Ya dan muskuta ya ce,"Ina jin ma idan ma za
kayi zaman ka, babu damuwa, ai ni da kai ba
bambanci.
Duk abinda ka fadi tamkar ni ne na fade shi."
Ya riga ya gano shi, don haka ya ce,"Haka ne,
amma waka a bakin mai ita, ta fi dadi, ko
Malama Nusaiba?
Ta ce,"To ni me zan ce?
Ya mike ya ce,"Bari dai na jira ka a mota.
Malama a fito lafiya."
Ta ce,"Kuwa ba ka zauna shiru kai kaidai a mota.
Ta mike, "Zo mu je." Ta fice ya bubbuga kafadar
Naseerr, sannan ya bi bayan ta.
Wata kofa ta bude, sai ga su a wani matsaikaicin
falo. Ta ce ya zauna ta kunna masa T.V. "Wane
( Channel) Ka ke so? Ya ce,"Bar min labarai, na
gode."
Ta fita, jimawa kadan suka dawo tare da Mariya,
dauke da kayan abinci da na sha, ta aje masa."
Duk ni kadai?
Tayi murmushi," Duk kuma na ke son ka cinye."
To na gode."
Ta sa kai ta fita.
Sageer yayi kishingide a kujera, ya cigaba da
kallon sa.
Tana sallama babban falon. Naseer na daukan
waya, "Yaya B, ya aka yi ne? Ka na wane gari ne
yanzu?
Ya ce,"Tafiyar nan bata yuwu ba B. Sai dai mun
hadu, ka ji labari. Ina ma Kaduna a halin
yanzu.......
Takaici yasa Naseer B, ya kashe wayar sa. Jin
shiru. Shi yasa shi ma ya cire ta a kunnan sa.
Ya gama 'yan latsen-latsen sa tsawon lokaci,
kafin ya dubi inda Nusaiba ke zaune. Kanta a
sunkuye yake, don haka ya ci gaba da hararar ta.
Jikinta ya bata ana kallon ta, saboda haka ta dan
dago ba zato suka hada ido.
Yayi sauri ya janye na sa...................
______________________________
Masu karatu, yaya za ta kaya ne? Wace badakala
za ta faru a wannan labari? Ga Naseer Ga
Nusaiba, cikinsu wa zai ci gari? Na yi gaba a
dangaraman jirginmu na (MAIZAR AIRLINE). Mue
je zuwa, wai mahaukaci ya hau Kura.




Zaharaddeen Shomar


Whatsapp 08168575100 Downloaded from GNOVELS.COM.NG




This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG
to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/gnovels

Twitter : https://twitter.com/gnovels

Telegram : https://t.me/gnovels


Please Login or Register in order to submit comment