Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

za'a rage.
       Ya sake jan numfashi dayin rubutu kaɗan a takardar gabansa ya tura tsakkiyar table ɗin yana bin fuskokinsu da kallo a ransa dariyar mugunta yake musu. “Zan yarda bisa sharaɗin nine zan zabi speaker na majalissa. Idan kun amince kuyi singing, nima zanyi”.
       “What!!”.
Suka faɗa kusan su dukansu suna waro idanu dayin zallo.
    Cikin ɗage kafaɗa na I don't care ya miƙe abinsa, guard nasa yayi saurin ja masa kujera baya.
      “Duk shawarar da kuka yanke ina saurarenku”.
    Ya faɗa yana nufar ƙofar da zata sadashi da office ɗinsa kai tsaye batare da yabi hanyar fita ɗakin meeting ɗin ba ta waje..
      Kallon-kallo kawai aka komayi kowa ya kasa magana, dan kuwa shugaban ƙasa Ramadhan ya dakesu ne a kan jijiyar wuya dake kawo numfashin kila wa kala.

        Shigarsa office ɗin baifi da minti biyu ba kiran Gimbiya Su'adah ya shigo masa. dole ya danne ɗaci da fushin dake a zuciyarsa har maƙoshi ya karɓa mata da girmamawa. Har yanzu haushinsa takeji, dan haka cikin kaushin murya ta sanar masa su Lubnah zasu zo musu hutu. Ba zuwansun bane ya bashi mamaki koya damesa. Jin har su biyar zasu zo da sunan hutu, bayan a cikinsu akwai wanda ke aiki da karatu.
        “Okay Maa, amma kuma su su Lubnah aikinsu fa? Sannan Basma duka yaushe ta fara zuwa school da zata fara sakaci da shi?”.
      A zafafe gimbiya Su'adah tace, “To sai akace maka bazasu iya zuwa daga nan ba ne? Zanje ganin likita na ne london, idan kuma baka buƙatar suzo ɗin sai su wuce Bina”.
     “Am sorry Maa ba haka nake nufi ba. Insha ALLAH nima zan shigo gidan cikin weekend ɗin nan”.
    Bata amsashi ba, sai ma yanke kiran da tayi. Ya rumtse idanu da ƙarfi, tare da tura lip ɗinsa na ƙasa cikin baki ya hau tauna da ɗan ƙarfi. Waɗan nan takaicin ya hanashi yin komai yau a office, duk da dai dama aikin bawani mai tsauri bane duk tsare-tsarensane akan ayyukan da yaga ya dace ya fara shimfiɗawa kodan tukuyci ga talakawan da suka tsaya a rana domin zaɓensa.

*______________________________*

        Tun bayan tashin shugaban ƙasa a meeting ɗin wasu a cikin yaransu suka sanar musu da sharaɗin daya kawo na yarda da 50-50 akan cabinet saɓanin 70-30 da suka tsara. Ransu ya ɓaci suma matuƙa, basuyi ƙasa a gwiwa ba wajen miƙa zancen ga nasu god fathers ɗin. Suma da ga can hankalin nasu a tashe yake, kuma ransu a ɓace yake. Duk da kasancewarsu a mabanbanta gari a wannan ranar suka nufo Bingo gaba ɗayansu suka haɗu domin tattaunawa. Sai dai zaman nasu bai samu akan lokaci ba sai wajen sha ɗaya na dare. Tsabagen ƙwarewa a siyasa kuma kusan ƙarfe huɗu na yamma sai da suka kaima shugaban ƙasa Ramadhan gaisuwa har office.
       Yayi farin ciki da zuwansu, ya kuma girmamasu matsayinsu na manyan ƙasa kuma kakanni a garesa, dan dukansu zama su iya girmar Bappi, wasu kuma sa'anni da shi. Su ɗin kowa yasan manyan mutanene a ƙasar kuma dattijan arziƙi da sukai hidima ma ƙasa shekaru masu yawa da suka shuɗe. Sannan mutanene masu dattako da bazaka taɓa jin bakunansu akan mulkin ƙasar ba har sai idan ta ɓaci. Sai dai abinda ƴan ƙasa dama shuwagabannin basu sani ba, waɗannan dattijan lulluɓin biri ne kawai a jikin kuraye, sune ke juya ƙasar NAYA bisa table tamkar mulmulallen ƙarfe bisa ƙarfe. Duk wani shugaba da zai hau a gwamna ko shugaban ƙasa sai da yardarsu, sannan duk wani mai taimaka masa da zai naɗa sune da kaso mafi yawa a ciki, shiyyasa a kowanne mulki, a kuma kowacce jaha yaransu ne akan madafun iko.
      Kamar gaske shawarwari masu daraja suka bama shugaban ƙasa Ramadhan. Wanda yaji daɗinsu kuma yay farin ciki dasu, barin office ɗinsa kuma bai wuce da awa guda ba har zuwansu gareshi da shawarwarin da suka bashi sun watsu kafafen yaɗa labarai dama yanar gizo. inda kowa ya samu damar tofa albarkacin bakinsa. A mafi yawan Comments ɗin kuma ya ta'allaƙa ne ga yabonsu da jinjina mutuncinsu a idanun al'ummar ƙasar NAYA.

*11:00pm*

        Su dukansu biyar zaune suke a cikon falon gidan ɗaya daga cikinsu mai ƙarancin haske kasancewar an kashe mafiya yawan fitulun. Sai yaransu huɗu irin su shugaban jam'iyya, da Alhaji Yaro glass sai shugaban ƙasa mai sauka Usama S. Hamada da Mr Mike Bando vice president ɗinsa.
      Bayan sun gama sauraren ƙarin bayanai daga bakunan yaran nasu oga kwata-kwata mai shugabantar tawagar dattijan ya ajiye kofin shayin hanunsa yana wani shegen murmushi da faɗin, “Da alama yaron nan bazaiyi tsahon ran cika 2years ba, kamar yanda mukai masa fata”.
     Sauran dattijan huɗu sukai ƴar dariya, yayinda su su Alhaji Yaro glass basuga abin dariyarba anan. Dan har cikin rai sun fara jin fargaba akan taurin kan shugaban ƙasa Ramadhan.
       “Amma ranku ya daɗe kenan zamu yarda da sharaɗinsa?”. Forma Vice president Mike Bando ya faɗa cikin jin ɗaci.
         Wanda ke kusan tsakkiyar dattijan zaune ya ɗan taɓe baki da faɗin, “Well! Zamu iya yarje masa zakuma mu iya jayayya da shi. Sai dai ku sani dukansu biyu sunada haɗari. Yarje masan, da kuma yin jayayyar”
        Cikin takaici Alhaji Yaro glass yace, “Kenan ranka ya daɗe wannan ƙaramin alhakinne zai zamar mana ƙadangaren bakin tulu, ya ringa juyamu yanda yake so? Wai mizai hana ya mutu ne a wata shida?”.
       A tare dattijan suka kwashe da dariya. Sai kuma suka gimtse fuska. “Haka tunaninsa ke ayyana masa, shiyyasa har ya sharɗanta abinda ke a zuciyarsa. Shi yaro ne, baisan siyasa ba, bai san komai nata ba, bai san wahalar rayuwa ba dan cikin dukiya ya tashi. Dan haka wannan ba tunaninsa bane...”
       Da mamaki suka dubi oga kwata-kwata da yay maganar. Murmushi ya sakeyi batare da damuwa da kallon da suke masan ba. Yakai yatsunsa biyu ya ɗan ɗalli bowl ɗin gabansa mai ɗauke da fruits. “Tabbas ba tunaninsa bane, wannan tunanin Alhaji Hameed Taura ne. Dan haka shine zai fara mutuwa kafin yaron”.
    Ya ƙare maganar cikin kaushin murya da ɗaure fuska. A take su alhaji yaro glass suka shiga kallon-kallo. Dan su kam bama su hasaso hakan ba a ransu, tunda sun san shima Ramadhan ɗin gwanine na taurin kai da rashin mutunci. Har cikin rai wannan abu yay musu daɗi, kuma sunyi na'am da shi. Dan kuwa mutuwar Alhaji Hameed Taura suma shine burin ransu..........✍


*_(Hummm🚶🏻🤦🏻)_*


*_Ku garzaya AREWABOOKS ta link ɗin dake sama farkon page, domin samun pages fiye da wanda kuke gani a WhatsApp⛹🏻‍♀️⛹🏻‍♀️😘_*



*_ZAFAFA BIYAR (5) ZAZZAFAR TAFIYA🔥🔥👇👇👇_*


*1*~ *_KUFAN WUTA_*🔥
_Safiyya Huguma_

*1*~ *_BAQAR INUWA_*💥
_Billyn Abdul_

*1*~ *_RAYUWAR MACE_*💅
_Hafsat Rano_

*1*~ *_MASARAUTA_*💪
_Miss Xoxo_

*1*~ *_NOOR ALBI_*❤‍🔥
_Mamuhgee_



Guda 1👉300
Guda 2👉400
Guda 3👉500
Guda 4👉700
Guda 5👉1k


*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya👇🏼

*_09032345899_*


*KATIN MTN*👇👇

09166221261
__________________

*_JAMA'AR JIGER zaku iya biyan kuɗin littatafan ZAFAFA BIYAR kuma ta nan👇🏼_*



Guda daya=300F
Guda biyu=400F
Uku=500F
Hudu=700F
Biyar=1000F


*ZAKU TURA KATIN WAYA NA (MOOV ko AIRTEL) ZUWA WANNAN NUMBER,TARE DA SHAIDAR BIYA*👇🏼

+227 95 16 61 77



*_TEAM ZAFAFABIYAR🔥🔥🔥🔥_*



*_BAƘAR INUWA...👇🏻_*


Da ɗumi-ɗuminsa💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

Please
*_Follow me_*
*_Share_*
*_Comments_* akan abinda ya shige maka duhu.

_AREWABOOKS, dan zaku dinga samun sabbin pages galla-galla akan lokaci insha ALLAH. Maza garzaya ka karanta naka hankali kwance. Ka kuma yi following ɗina ko dan kar ayi babu kai, da a baka labari gwara ka bayar🥰🥰🤝🏻👇🏻_


*YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS*

Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: -

*Enter your name:* (Cikakken sunanki)

*Enter your mail:* (Email ɗinki)

*Enter an username* (Sunanki)

*Enter your password:* ( misali 12341234)

*Confirm password:* (misali 12341234)

Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂.

*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.

*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.


*_AREWABOOKS LINK kai tsaye_*

https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3


Masu iPhone

Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com

*_Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App... Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine_.*


*_MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER_*

+234 903 177 4742


_Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan😍😘😍🥰😍😊_.




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
[6/17, 1:36 PM] NANA: *_Typing📲_*



*_BAƘAR INUWA👉🏻AREWABOOKS👇🏻_*


https://arewabooks.com/chapter?id=62aafdab52e2996a61a92f3d




*_Episode 29_*


...............*_GOVERNMENT HOUSE_*

Tattaunawar sa da dattijan ya bashi ƙwarin gwiwa sosai. Dan yaji matuƙar daɗin shawarwarinsu. Da wuri yau ya shigo gida, dan haka yana ɗan watsa ruwa ya fito falon upstairs ɗin domin yin wani ɗan aiki. Da kansa ya buɗe fridge ya ɗauka fresh furarsa da Anne bata gajiya da aiko masa duk bayan kwana biyu. Da ga can gefen falon kujerune guda biyu dake gab da wawakeken glass ɗin dake tamkar matsayin window, sai dai shi zaka iya fita ta cikinsa zuwa barandar upstairs ɗin, daga nan cikin falon kuma zaka iya hango kai kawon kowa dake a ƙatuwar harabar gidan. table ne tsakkiyarsu, sai fitila doguwa dake tsaye wadda zaka iya amfani da ita idan baka buƙatar hasken falon da yawa. Zama yay da bismilla kafin ya buɗe furansa da kilishi dake a cikin kwali. Daga haka ya kunna apple lap-top ɗinsa ya fara aiki a nutse cike da ƙwarewar iya sarrafa keyboard. Sosai ya shagala a aikin dake masa matuƙar dadi, dan tsare-tsarene da suka shafi ayyukan da zai ɗora cabinet ɗinsa a kai. Lokaci-lokaci yakan ciri kilishi ya kai bakinsa koya ɗan zuƙa fura.
Cak yatsunsa da ɗan sakewar fuskarsa suka dakata sakamakon jin kamar shashshekar kuka. Sai dai kuma bai ɗagoba har kusan sakanni talatin. Tabbatar da da gaske kuka ake a kusa da shi ya sakashi sake nutsuwa yana sauraren inda sautin ke fitowa, kafin ya ɗago da ƙyar tamkar an masa dole ya kai dubansa ga inda sautin kukan ke tashi.
Babu yalwataccen haske a falon, amma hakan bai hanashi hango Raudha dake zaune can steps na sauka downstairs ba, ba dukanta yake hangowa ba, iya kafaɗarta ne kawai zuwa kanta, saboda tana zaune ne a steps ɗin kusan tsakkiya ta masa ƙasa da yawa. Ɗauke idanunsa yay da ga kanta, ya maida ga agogon dake jikin lap-top nashi, ƙarfe ɗaya saura na dare. Cigaba yay da aikinsa tamkar abin bai damesa ba, sai dai acan ƙasan zuciyarsa kukan nata na sukarsa. Bai cika san kuka ba, musamman irin nata mara sauti sai jan ajiyar zuciya. Duk yanda yaso cigaba da aikin cikin shauƙin daya fara sai hakan ya gagaresa, dole ya ɗauke hannayensa ya gyara zamansa a kujerar tare da harɗe ƙafafunsa ɗaya kan ɗaya ya jingina bayansa da kujerar ya lumshe ido yana cigaba da sauraren fitar sautin kukan nata mai haɗe da jan ajiyar zuciya.
Tun yana lissafa sakanni ya koma mintuna, har takaisa ga kusan mintuna talatin babu alamar zatai shiru. Takaicin tsayar masa da aiki ya sakashi jan siririn tsaki ya buɗe idanunsa. A ɗan harzuƙe ya miƙe zuwa makunnar wutar falon ya dannasu baki ɗaya. Warr haske ya gauraye ko'ina.
A matuƙar tsorace Raudha tai saurin miƙewa tare da juyowa. Gabanta yay matuƙar faɗuwa saboda tozali da tai da shugaban ƙasa Ramadhan tsaye jikin ƙarfen benen hannayensa duk biyu zube cikin 3quarter wandonsa. Fuskarsa kicin-kicin yana watsa mata wani irin kallo da batasan a wane aji zata fassarashi ba.
Saurin maida kanta ƙasa tai da ga barin kallonsa, yayinda ruɗanin da kunyar kayan dake a jikinta suka hadu suka dabaibayeta, ta naɗe duka hannayenta a ƙirjinta tana shafa damtsen hannunta dan son bawa jikinta kariya. Kayan barci ne masu santsi da taushi baby pink color. Wando iyakarsa gwiwar ta, hakama rigar mai kamar best sai dai hanunta nada faɗi, ba wata babba bace, dan ta mata ɗas a jiki tamkar saida aka gwadata akayita, sai gashin kanta dake ɗaure a tsakkiya da ribbon yana reto. Raudha tanada gashi mai ƙyau, duk da kuwa bawai yanada tsaho kalar da za'a ce masa irin na indiya ko turawa ba. Sai dai a cikin mutane irinmu dole ne a kirata mai baiwar gashi musamman a yanzu da ya samu gyara na musamman da kulawa wajen Feena a gidan aunty hannah lokacin training ɗin da akai mata, sai ya kara ƙyau da zama abin kallo dalilin halittarta nada alaƙa da jinin larabawa, dan kafin auren bata taɓa sakama kanta relexer ɗin ba.
Kokawa yake da zuciyarsa da idanunsa da ga barin kalonta amma ya kasa, damin kuwa ALLAH ya azurtata da abinda yake matuƙar so ga diya mace. Tun Ramadhan na yaro yana matuƙar son gashi, dan yana ɗaya daga cikin abinda ya ƙara shaƙuwarsa da Anne cikin ƙanƙanin lokaci a wancan lokacin. Anne nada gashi sosai, haka zai zauna yayta jagwalgwala mata shi wai yana mata kitso ko tsifa. Har ya shiga secondary school bai daina zaman taya Anne tsifar kai ba dan kawai ya samu damar wasa da shi........
“In... Ina yini”.
Raudha ta katse shi da ga shagalar kallonta. Komai baice mata ba, sai dai ya janye idanun nasa a kanta. Bata taɓa jin ya amsa mata gaisuwa ba, dan haka yanzu da bai amsa ɗin ba bata damuba ta fara hawowa steps ɗin cike da tsoro da kunya da nufin komawa ɗakinta. Tazo gab da shi zata gitta a bazata taji saukar muryarsa cikin kunnenta babu zato.
“Mike damunki?”.
Duk da ahankali yay maganar bata hanata jin tasirinta cikin zuciya da ɓargon jikinta ba. Kanta dake ƙasa ta girgiza masa, cikin ƙoƙarin danne kukan dake taso mata tace, “Babu komai”.
Komai bai sake ce mata ba, sai ma raɓawa da yay ta gabanta ya koma inda ya baro. Bata cigaba da tafiyar ba har sai da yakai zaune da kusan minti biyu.
Sum-sum ta nufi hanyar bedroom ɗinta batare data yarda ta dubesa ba hawaye na rige-rigen sake sakko mata saman kumatu. Daga inda yake zaune, ƙwayar idonsa ta bita da kallo harta shige. Idanun ya maida ya lumshe tare da sauke nannauyar ajiyar zuciya ya lafe jikin kujerar yana kokawar danne abinda ke taso masa....

★★★

Tun daga wannan ranar Raudha da shugaban ƙasa basu sake haɗuwa ba. Sai dai kamar kwankin baya, takanji shigarsa da fitarsa gida. Dan takan jima batai barci ba. Takai ko dare ya raba bai shigoba sai taji shigowar tasa.
A haka suka kuma shanye satin ya zam satinau uku da aure da kuma shiga gida gwamnatin. A safiyar juma'a kusan 12pm na rana sai ga su Aunty Hannah a bazata harda Hajiyar birni sun kawo mata ziyara. Harga ALLAH taji matuƙar daɗi da yin farin ciki, duk da tsananin tsoron al'amuran aunty Hannah a yanzun. Sun samu tarba ta mutuntawa a gareta dama ma'aikatan gidan. Dan Mama Tambaya ce tsaye kan komai har sai da taga kuku ya wadata gabansu da abinci na musamman da abin sha. Bakin Hajiyar birni har kunne tanata zuba santi yau gata a fadar shugaban ƙasar NAYA. Kuma jikarta ke amsa sunan matar gidan, ƴarta matar vice president, kai wannan daɗi ya mata yawa. Ta kama Raudha ta rungume tanata saka mata albarka ko damuwa da ramar datai babu wanda yayi.
Raudha taji daɗin ganin Yasmin da yayunta su Fatisa. Har su fatisan ke faɗa mata aunty Halima zata wuce da su gidanta a Bina su koma makaranta. Hakan ya mata daɗi, dan dama bata son zaman su Fatisa a Bingo hannun su Hajiyar birni gudun kar a saka rayuwarsu a garari kodan rawar kansu, saboda mummynsu bata da wani ƙarfin iko akan komai. Babu abinda zaman nasu zai amfana musu sai ƙara lalacewa duk da taga kamar sun ɗan nutsu yanzu tun sakin da Abbansu yayama Mummy.
Batai ƙasa a gwiwa ba wajen roƙon Hajiyar Birni a bar mata Yasmin anan. Babu wanda yace mata komai akan hakan, sai ma hajiya mama data wani taɓe baki da hararta.
“Oh saboda ita kaɗai kuka haɗa uwa da ita? Yanzu Raudha har idonki yayi buɗewar raba ɗayan biyu tsakanin Yasmin da su Noor?”.
Kai Raudha tai saurin girgizawa, “Lah a'a wlhy Hajiya mama ba haka bane, dama so nake naji idan za'a barmin Yasmin ɗin sai nace itama Noor a bani tunda Asim shi namiji ne”.
Hajiya Mama zata sake magana aunty Hannah ta katsesu. “To inaga mubar maganar haka sai munje gida ma tattauna. Sai itama Asabe a kirata idan ta amince”.
Badan Hajiya mama taso ba tai shiru. Daga haka suka cigaba da hirarsu har lokacin salla yay Raudha ta kaisu ɗakinta dan suyi. Wasun su sunyi alwala wasu na ƙoƙarin yi Asim yace mata zai ƙara shan lemo. Da to ta amsa masa tana ɗan murmushi. Taja siririn gyalen jallabiyar jikinta ta yana ta fito domin ɗauka masa.
Yau ne karon farko da tun zuwanta gidan ta nufi hanyar kitchen, badan ta tabbatar nan ɗinne kitchen ɗin ba. Sai dan taga tanan kuku ya dinga fito musu da abinci ɗazun. Tana ƙoƙarin ɗaura hanunta a handle ɗin ƙofar dake a rufe taji kamar ana magana a hankali, kuma kamar muryar Aunty Hannah data fito a ɗaki tun shigarsu tana amsa waya. Nutsuwa tai ta kasa kunnenta, sai ko tajiyo aunty Hannahr na faɗin,
“Waɗan nan sune kalolin abubuwan da yafi sha kenan?”.
Kuku ya amsa mata da faɗin, “Eh ranki ya daɗe. Amma kamar yanda na sanar miki har yanzu bai taɓa cin abincin gidan nan ba. Amma kullum akayo sharar sashensu nakanga alamar kwalayen anci nama musamman kilishi, sai kuma fura da naga yana shigo da ita da kansa duk bayan kwana biyu”.
“Fura kuma?”.
“Eh ranki ya daɗe”.
“Okay hakan ba matsala bane. Zamuji daga ina ake kawo masa furan da naman ba damuwa. Yanzu dai daga yau duk bayan sati za'a dinga kawo waɗannan kalolin drinks ɗin zuwa nauyin kowanne milk cikin cefanen gidan nan idan zakayo. Sai ka kula sosai wajen zubasu a iya fridge ɗin da yake mu'amula da shi. Maganar abinci kuma zan saka matarsa ta kula da shi akan cinsa dan muna buƙatar ya dingaci ɗin, dan muna buƙatar waɗan nan abubuwan su dinga tasiri a cikin jininsa a hankali yanda babu wani likita da zai iya fahimta da wuri sai dai a ɗauka diabetis ɗinsa ce”.
“Okay Ma baku da matsala da hakan, dan ɗazuma nayi magana da Aunty (forma first lady, ƙanwar mahaifiyarsa ce, uwa kenan take a wajensa, kuma tun yana ƙarami itake tsaye kan karatunsa saboda mahaifiyarsa ta rasu wajen haihuwarsa, a hanun mamarsu first lady ɗin ya tashi ma. Aikine dake buƙatar sirri, shiyyasa ta ɗorasa akai gudun kar aci amanarsu ko a samu matsala. A haka ma akwai abinda ya sani da ita aunty Hannah ɗin bata sanshi ba). Ta ƙaramin bayani sosai dama akansu ɗin da yanda zai dinga amfani da shi a abincin nasa musamman ma shayi. Amma na mata complain akan matarsa, tace babu damuwa itama koda taci”.
Ɗan jim Aunty Hannah tai, sai kuma ta ɗan ɗaga kafaɗa da taɓe baki alamar ko'a jikinta inhar burinta zai cika na ganin mijinta a kujerar shugaban ƙasa wataran. “Ba damuwa idan tacin itama kamar yanda first lady ɗin ta faɗa. Sai dai ka kula, ba kowanne ma'aikaci bane namu a cikin ku, sannan wanda suke namun ma da ga kai sai Tambaya kuka san sirrin aikin da kukeyi”.
“Okay Maa. I promise bazaku taɓa samun matsala daga gareni ba kuma kun sani, Aunty Bushira tamin komai a rayuwa, miye amfanina idan ban saka mata da buƙatarta ba.”

Da sauri Raudha taja da baya wani irin kuka na neman kufce mata, jitai bama zata iya ƙarasa ji ba, babu abinda kanta keyi sai sarawar tashin hankali. Bayan poison na ac bai ishesu ba sai sun haɗa da matakan ingiza ciwonsa, ya kamata tasan wane ciwo ne ke damunsa ma. Bata da tabbacin yunƙurin da tai akan matsalar ac ta karɓu, amma tana addu'a da fatan hakan dan tasan ta tura saƙonta inda da wahala a ɗaukesa shirme. Jin za'a buɗe ƙofar kitchen ɗin tai azamar rugawa karkashin ƙafar bene ta lafe har sai da aunty Hannah ta shige bedroom ɗinta na ƙasa da ta kaisu dan suyi alwala. dan bata kaisu upstairs ba sanin nan ɗin kamar sirrine na shugaban ƙasa.
Sai da tayi ɗan kukanta mamakin aunty Hannah da dalilinta na son aikata duk wannan abubuwan na ƙara kumeta. Dan a iya hasashenta tarasa minene alaƙar aunty Hannah da shugaban kasa da har take gaba-gaba wajen yin haɗin gwiwa da wasu domin kashesa. A gefe kuma zuciyarta na ƙara ninƙaya wajen tunanin zancen farko na sakama shugaban ƙasa poison a cikin ac. Ga wani zasu dinga basa a abinci da drinks? Kai mutanen nan sam basu da imani wlhy. Amma insha ALLAHU ALLAH bazai taɓa basu nasara ba. Zatai iya bakin ƙoƙarin ta na ganin burinsu bai cikaba akan shugaban ƙasa kodan kyakywar zuciyar kakanninsa.



Da ƙyar Raudha ta iya danne komai dake a ranta har lokacin tafiyar su yayi, shatara ta arziki ta haɗama kowannensu daga kayan lefenta. Dan sune kawai take takama da su a gidan matsayin nata. Hakama Mummy da Aunty Halima ta haɗa musu tasu tsarabar.
Ta rakasu har harabar gidan tana sharar hawaye. A dai-dai lokacin da motarsu ke fita a harabar farko na gidan motocin shugaban kasa da securitys nasa ke shigowa. Ko ba'a faɗa ba tasan shi ɗinne, dan haka tai shirin juyawa cikin gida tana ƙoƙarin amsa gaisuwar wasu a hadiman gidan da sai yanzu suka ganta.
Shugaban ƙasa Ramadhan da tun tsayuwar motar tasu idonsa ya ganta ya bita da kallo a kaikaice batare da waɗanda ke a wajen zasu iya gane hakan ba. Zuciyarsa ke masa wasuwasi da tambayar su waye ɗin waɗancan da har zata fito rakkiyarsu har harabar gida?. Rashin mai amsa masa hakan ya sashi ɗauke idonsa a ƙofar data shige ya maida ga agogon hanunsa. Ƙarfe huɗu na yamma da wasu mintuna. Ya dawo gidane saboda yana son su fita ita da shi zuwa Taura house gaishe da su Anne. Wannan lokacin kawai ne da shi, gobe idan ALLAH ya kaimu zai bar ƙasar wani taron shugabannin Africa da za'ai a ƙasar Nigeria.


Buɗe ƙofar ne ya saka Raudha dake kwance ɗagowa da sauri har gyalen kanta na zamewa ya faɗi, duk da shi ɗin ta tsammaci gani sai kuma duk ta ruɗe. Cikin in ina take masa barka da dawowa da gaishesa. Kamar kullum yauma bataji ya amsa ba, sai dai idonsa na kanta da har ya sata kasa kallonsa.
“Nanda mintuna talatin zamu fita can gidan gaishe su.”
Daga haka yaja jikinsa baya zai rufe ƙofar, dan dama tsaye yake a jikinta riƙe da handle ɗin. Yana gab da rufewa kuma sai ya

Please Login or Register in order to submit comment