Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kara yayyafa ma wutarsa petrol take, amman babyn Nennen bata gane ba. Wannan childishness dinnata yana kara burge shi.
Hamma yace "Ayshaaaaa…" tace "na'am Hamma" yace "ba bacci nake ba, I am just in a mood!" Ya fada yana mata wata kallo, mai shiga rai da sanya kasala.
Har sai da Aisha ta tsargu don ya kara jawo ta jikin sa sosai, this time around juyo da ita yayi tana facing dinsa gabagadi. Aisha tayi shiru, yace "baza ki tambayeni what mood ba?" Tace "toh Hamma bacci kake ji, kuma ka kafe kai baka ji" ta dan turo bakin ta gaba, tana fada cikin shagwaba 'yar gaske.
Ai kuwa Prince ya sa ido yana kallon bakin da take turowa so soft and luscious, bai san sanda yace "I really really want to kiss you saddiqa… "ya matso dab da fuskar ta, har suna jin numfashin juna, ya kalle ta, cikin idonsa kadai ta ga tsantsar al'amuran dake cin zuciyarsa da gangar jikinsa. An yi sa’a itama ta juyo kenan sai kawai Hamma ya hade bakinsu wurin guda ya soma kissing Aisha-Siddiqah in a serious tone and passionate manner.
Da kyar Aisha ta samu ta zame daga Hammah, ta mike jikinta yana rawa a daburce tayi hanyar kitchenette. Hamma da kyar ya iya mikewa yanakokarinsaita kansa. Yabi bayanta yana cewa cikin basarwa,
“you know what? Jeki shirya kawai ki bar girkinnan, we are going out, ma ci a waje”.
Tace “toh”, sai ga Nenne ta sake kira.
Tace “ni Hammansu dazu maganar bikinsu Princesses na kira zan maka na manta, an saka rana, kwanaki goma masu zuwa. Don Allah ka taho da Aisha, kuma kuzo da wuri. Asabar ne daurin aure wato ranar addu’ar arba’in din Sarki”.
Prince ya ce “toh Nenne, in sha Allah”.
Itama Aisha sai murna lokacin da Hamma ya gaya mata zasu tafi gida Lagos sati mai zuwa, tace “bikinsu Firdausi za’a yi?”
Yace “eh, za’a hada da addu’ar arba’in na Emir. Shine babban burinsa kafin rasuwarsa wato auren twins din gidanmu”.
Siddiqah tayi ta murna har ‘yar rawa ta shiga takawa a wajen, ta manta shaf a gabansa take, irin murnar zata gida dinnan, after a long while.
Hutun Prince ya dade da karewa, zuwan Siddiqah ne yasa ya kai har wannan lokacin a Argentina.
Sun fita a daren sun shakata, suka ci abincin dare a wani Arabian Cuisine sannan suka dawo gida.
Aisha ta nufi dakinta tayi wanka ta sha rigar barci mai dan kauri purple ta fesa turarukanta masu dadin kamshi ta nufi dakin Prince.
Nan ta tadda shi daga shi sai short nicker akan sofa yana shan ‘chamomile tea’ kafin ya kwanta. Ta na shiga Hamma ya dago yana dubanta da wani kallo da bai taba yi mata ba, domin sha'awar matarsa ce zallah yau cikin idanunsa da duk abinda yake yi. Aisha ta juya da sauri zata koma ganin ba suttura a jikin Hamma sai gajeren wando, ga kunya data kamata sai ya aje kofin hannunsa, yace Aisha wait, ya taso ya isa gareta ya kamo hannunta ya shigo da ita cikin dakin yana cewa.
"Ya kinzo turakar miji neman albarka kuma zaki koma?"
Aisha duk ta daburce ta rikice tarude, sabida yanayin da Hamma ke mata magana yau ya sha banban dana koyaushe. Ba don ta kasance mai karfin ji bama, da bazata ji shi ba.
"Dama-dama... zuwa nayi ince maka Hamma saida safe".
Hamma ya dora hannuwansa biyu bisa kafadun Aisha hagu da dama yana murzawa. Ya dan mutstsuka jijiyar wuyanta cikin wani salo na tasowar muguwar sha'awar da baisan akwai a tareda shi ba, saida Aisha ta runtse ido sabida tasowar tata sha'awar ta diya mace, kafin hannunsa ya kai kansa saman kirjinta.
Yace "saida safe dinma ai irin haka ake fadarsa Ayshahhh, ba da fatar baki ba. You my dear I want to kiss you again today!".
Hamma ya fada admiringly idanunsa akan siraran lips din Aisha, yana musu wani inviting looks. Aisha ta kusa narkewa bakidayanta domin a lokacin Hamma ya matsota sosai ne a jikinsa, ya isa cikin nutsuwa ya hade bakinsu wurin guda ya soma sumbatar Aisha a tsanake, sannan ya koma kissing hungrily.
Ashe namiji duk dadewar sa babu aure, ba sai an koya masa sumba ta auratayya ba? Ko da kuwa ya fidda rai da ita, ko bashi da sha'awar ta, sanda zata sameshi zai ji tane tana sarrafashi.
To hakan ce ta faru da Prince Abdulrasheed yau. Da ya samu kissable lips din Aisha yau ya dinga tsotso tamkar Allah ya aikoshi, saida ya ajiye kishirwar shekaru masu yawa na kuruciya dana shiga girma.
Aisha kyale Prince tayi ya yi yadda duk yake so yau, ya jagwalgwala ta iya son ransa a duk ta inda yake so. Ya tsotse duk abinda yake so. Kuma shi da kansa yayiwa kansa limit. Don yana ganin in ya kauda budurcinta any moment zata iya conceiving, shikuma yana ganin kamar bata yi kwarin da zata haihu ba. Tunda har ya samu wannan access din zai iya karawa Aisha lokaci.
A kwanaki goma da suka biyo bayan wannan ranar, wata wawuyar shakuwa ce ta shiga tsakanin Hamma da Aisha. Suna kwana a gado guda, Hamma saida ya san yadda yayi ya fara raba Aisha da dukkan sittirun jikinta in zasu kwanta, yana rabar Aisha da dabara da wayau da simple hugs, da light kiss masu sawa ta saki jiki da shi, su yi barci manne da juna. Tun Aisha matukar jin nauyi da tsoro har ta soma sakewa da Hamma sosai. Don ta lura ba shi da nufin abinda take tsoro. Kusan sati biyu kenan irin rayuwar da suke yi a cikin gidan kenan, full of understanding, intimacy and love, Hamma ya zama baya iya barci bai raba jikinsa dana Aisha ba, bai sumbaci bakinta da kirjinta yadda yake so ba amma bai taba wuce hakan ba yake takawa kansa birki, don a ganinsa har lokacin Aisha bata yi girman data isa ya dora mata hidimar dake cikin aure yanzu ba kada tazo haihuwa ta samu matsala.
Amma me? A na I gobe zasu tafi Lagos komai kwace masa yayi, ya kasa controlling kansa yadda ya saba duk kuwa da yana tausayawa Aisha, da kyar da roko da magiya harda kuka Aisha ta kwaci kanta a hannun Prince domin kuwa gani take duk ranar da hakan ta faru ba wata wata mutuwa zatayi, in tayi la'akari da irin yanayin da Prince ke shiga a irin wadannan lokutan akanta.
A satin dasu Prince zasu dawo Lagos Dade yasa aka je aka shirya gidan Prince na Banana Island, wanda ke daura da gidan mahaifinsa, Prince ya jima da sayen gidan bai taba amfani dashi ba, tun kafin saukarsu Dade ya gayawa Nenne in sun zo a gidansu zasu sauka. Yasa aka gyara gidan aka shigar komai da zasu bukata.
Tun saura kwana uku daurin aure suka sauka a Lagos. Gidan ya debi murnar zuwan su ba babba ba yaro, kowa murnar zuwan Hamma yake yi, ga ‘yan biki sun soma isowa daga sauran jihohi. Kiki ce kawai bata samu zuwa bikin Aunties dinta Princesses ba, don tana shirin rubuta jarrabawarta ta karshe a Informatics a lokacin.
Aunty Murjanatu Taiwo tana Ilorin, sai bayan addu’a zata taho Lagos tare dasu Nenne in sun je. Dade yace su Hamma su fara sauka a Lagos su huta kwana biyu, in yaso sai su dunguma duk gidan zuwa Ilorin su samu adddu’ar Sarki ranar asabar, wadda ta kasance kuma ranar daurin auren su Fatima.
Nenne ta rasa ina taka saka ina taka aje da surukarta Aisha, wata sabuwar kauna da soyayya Nenne take yiwa Siddiqah musamman data gane suna zaman lafiya itada Hamma, Aisha ta samo kansa shima ya samo nutsuwarta, Nenne bata taba jin Hamma cikin farin ciki da nishadin data ji shi ciki ranar da suka yi waya itada su, tana tsammanin Siddiqah ciki gareta ba. don haka tun kafin saukarsu a Lagos yau Nenne da kanta ta shiga kitchen ta shirya abincin tarbar Hamma da Aisha, ta hada dana Dade, girki tayi masa na musamman data tabbatar Hamma ya dade bai samu irinsa ba, wato (Locust Beans Stew) da suke kira Dindin da (Ofada Rice).
Bayan saukarsu da kadan Dade yace ma Prince a gidansu zasu tare, yasa an shirya musu komai da zasu bukata. Don haka ana gama cin abincin dare Dade yace Firdausi ta dauko keys din gidan ta baiwa Hamma, ta yiwa Aisha rakiya kuma.
Anan Nenne tace “a’ah Dade, ita kam Aisha ta zauna ta huta anan, a bari sai bayan biki sannan ayi tarewar. Ta jima bata nan akwai bukatar ta huta tukunna”. Ai kuwa nan da nan Prince ya canza fuska. Domin a yau kam yayi niyyar angwancewa da amaryarsa Siddiqah babu daga kafa. In yaso idan ciki ya samu ya tayata nakudar. Yanzu kuma Nenne tana wani zance wanda zuciyarsa ta gaza dauka, wai Aisha ta zauna da ita har bayan biki, duk kokarinsa na rainon da yayi tayi wata da watanni ba’a gani ba, sai rana daya da ya saka ran hutawa.
Har dai rashin jin dadin hakan ya gaza boyuwa a fuskarsa, ‘yar damuwa ta nuna a fuskar Prince, amma dai bai yi magana ba. saidai tuni Dade da yake shi namiji ne ya ramfo shi.
Lura da yanayinsa da Dade yayi, sai yace.
“Kehinde kodai kafi so ku tafi tare yanzu ne?” Zuruf! Aisha tayi tace “Dade ayi hakuri don Allah ni nan zan zauna gun Nenne har a gama biki, nayi kewar Nenne for long”.
Taki dago ido balle Prince ya kalli kwayar idanunta. Domin ta riga ta san Prince ya gama kaiwa kul a a dalcinsa. Daren tahowarsu da yaya ta tsira? Balle yanzu a gidansa na gado? Takaicin abinda Ausha tace yasa shima ya hadiye, yace “a’ah Dade, ba wata matsala a kyaleta ta sha zamanta”.
Amma Kai da ji kasan shagube ne yayi. Ya ajje spoon ba don ya koshi ba, sai don bazai iya cigaba da ci ba’a gane ransa ya baci ba, da abinda Aisha tayi masa a gaban kowa ta nuna bata damu dashi ba, ya mike yace zai je gidansa ya huta. Bai sake kallon inda Aisha take ba ya nufi hanyar fita falon.
Anan ne Nenne ta dubi Aisha tace “raka shi zuwa mota mana Aisha” Hamma, wanda a lokacin har ya kai bakin kofa cikin matukar kulewa zai fice, yace.
“A’ah Nenne na yafe, ta zauna kawai, na gode”.
Wannan gwasalen da Hamma yayiwa rakiyar Aisha, duk ya faru akan idon amare Princess Fatima da Princess Firdausi, don tare aka zauna cin abincin har dasu gabadaya.
Abin yayi matukar yiwa Fatima dadi, na yadda Prince ya nuna bai damu da Aisha a gaban kowa ba. ita bata fahimci haushi yaji don Aisha tace da bakinta bazata bishi ba. Har ta samu abin adarwa a gaba.
Fatima na komawa dakinta ta kira Aunty Taiwo, tana mayar mata da yadda aka yi, da irin gwasale tayin binsa gidansa da Prince yayi ga Nenne da Aisha, sai Taiwo tace da Fatima, “ewo, to dama nifa na san Kehinde sarai, nafi kowa saninsa, saninda ko Nenne bata yi masa ba, ba son zama da yarinyar nan yake ba, biyayya yake yi musu don a rabu lafiya da kafaffun iyayenmu da basa shawara, su Nenne ke faman cusa masa ita kamar dusa, kamar ance lafiyayyun mata ‘yan asali na manyan gida sun gama karewa a duniya.
Na rantse idona idonta a Lagos ko Ilorin in ta sake tazo, sai nayi mata wulakanci da kaskancin da bazata kara kuskuren zuro jiki cikin zuri’ar Akanni ba, balle ta wani kwashi siraran kafafunta tazo mana biki irin wannan na girma”.
A dakinta na baya wato dakin Kiki aka sauketa, kafin ta kwanta saida ta kira Ummanta ta gaya mata saukarsu lafiya a Lagos, sannan ta kira Hamma don tayi masa saida safe ta kuma bashi hakuri da kalamai, amma sai ta samu ya kashe dukka wayoyinsa.
Haka ta kwana da tunani da damuwar Hamma a ranta.
Washegari da safe ita da Nenne ne suka shirya abin karin Dade da Hamma, sai wajen karfe goma na safe Prince yazo gidan kuma a gurguje suka karya shida Dade zasu fita, bayan yabi Nenne dakinta sun gaisa, yanaso ya tambayi Aisha amma ya dake. Sai gata tana shigowa dakin Nennen dauke da lemun tuffah da sassanyar madarada tanbulan na tangaran akan karamin tray, ta gefensa ta wuce zuwa ciki, taci ado har ta gaji gabadaya ta saje da ‘yammatan amarya da suka cika gidan tun jiya.
Ta ajiye a gabansa, don tun safe take dakon shigowarsa duk ta damu, tace a ladabce “Hamma ina kwana?” Yayi mata wani kallo yace “lafiya kalau, yaya gajiyarki?” Nenne aka kirata a waya sai ta fita daga dakin tana amsa wayar.
Aisha bata yi aune ba taji Prince ya kamata ya mikar daga durkuson data yi a gabansa ya jata zuwa kusurwar dakin ya matseta sosai a jikinsa, sannan ya manne ta a kirjinsa da wata zazzafar hug, ya rage tsaho ya sumbaci lips dinta lightly, yace,
“Aisha jiya banyi barci ba isashshe saboda rashin ki a gadona Aisha, I missed you and your sweet lips, me yasa kika yimin hakane wai?”
Ya yi mata wani kallo na so da sha'awar da baisan yaushe ya fito daga idanunsa zuwa nata ba, saida Aisha taji tasirin kallonnan har spine dinta, tsigar jikinta saida ya tashi yarrr, Hamma ganin haka ya sake manne bakunansu wuri guda yana kissing lips dinta hungrily, wannan karon zazzafar kiss yake extending Wanda ya rikita Aisha bakidayanta. Duk da haka tunanin a inda suke ya hanata nutsuwa ta amshi sakonnin nasa. Aisha ta soma kokarin kwatar kanta tana fadin.
“Please don Allah Hamma ka bari, ka sakeni kada Nenne ta dawo. Dakin Nenne ne fa!”.
Hamma yace “I don’t care, ai gara ta gani ta san yadda kuka taru kuka kwareni jiya, I missed your warmth, shine jiya kika ce nan zaki zauna ko? Don kawai kinga ina shirin angwancewa? Wannan ai mugunta ne Aisha.
Hummm! Ni na manta ma I am pissed at you na tsaya Ina romancing dinki”. Aisha tayi wani murmushi kawai ta kalleshi “ni dai don Allah Hamma ka sakeni kunya nake ji” ya sake mata kiss a kasan wuyanta sannan ya saketa jin kamar motsi a bayansu. Ashe Firdausi ce ta shigo neman Aisha, ganin abinda ke faruwa tayi maza tayi excusing kanta da gaggawa ta juya tana murmushi.
Firdausi na fita Nenne ta dawo, sai Aisha ta gusa ta basu wuri. Har Hamma ya gama gaisawa da Nenne ya fita daga gidan, wanda ya soma dinkewa da baki musamman kawayen amarya dana Nenne, bai kara ganinta ba. Kuma a washegarin ranar first flight ya tashi dasu zuwa Ilorin, shida Dade, Nenne, Aisha da amaren domin su samu addu’ar arba’in kuma a dauro auren a fadar Ilorin.
Da hantsin ranar suka shiga Ilorin Emirate, Aisha tana like da Nenne duk inda tasa kafa nan take mayaswa. A yanayin kalar fatar jikinsu da kamanninsu na Fulani sai suka fita dabam a gidan, kamar ‘ya da uwarta. Wadanda basu san matar da aka aurawa Prince bama a gidan a ranar suka ganta, masu yabawa nayi haka masu gatsinen yarbawa na kankantar Aisha. Amma maganar rashin wayewa ya fara barin jikin Aisha ta yi fes da ita ta kara cikowa ta fara cika idanun mai kallonta. Prince yana can fada tareda Uncles dinsa do a ranar ne ake shawarar wanda za’a bawa sarauta a cikin ‘ya’yan Emir. Idris Akanni y ace a’ah, ko dama Emir ya dade yana gaya musu su cire Idris da dan sa daga sha’anin sarauta. Basu kara yarda da hakan ba sai yau da Dade ya fitittike yace bazai karba ba, baida ra’ayin sarauta ko kankani, don haka ya barwa kaninsa mai bi masa wato Abdulyaqeen Akanni wanda shine Turaki of Ilorin.
Da wannan aka bar zancen cewa washegari bayan addu’a arba’in din za’a zarce da bikin nadin sarautar da daurin aure.
Da farko a dakin da Nenne ta sauka Siddiqah take amma da Aunty Taiwo tashigo yiwa Nenne barka da zuwa, suka gaisa, ta tambayeta Hakeem tace yana fada, tana kallon Siddiqah a kaikaice, taga alamar a dakin Nenne take nufin zata sauka sai tace da Nenne cikin yarbanci da tayi tsammanin Siddiqah bata ji sam.
“Nenne keda surukar taki daki daya zakuyi sharing ne? Ai ba’a yin haka a gidannan, ta tashi ta koma cikin matan ‘ya’ya, haba Nenne don Allah ki dinga jan ajinki akan yarinyar nan”. Nenne tayi sakatoto tana duban ‘yarta Taiwo kafin ta samu abin cewa Aunty Taiwo tace da wata baiwa dake gefe ta dauko kayan Aisha ta kai dakin da ta sauka.
Jin tace a kai dakin da take yasa Nenne tayi shiru bata tanka ba, koba komai zata so a samu shakuwa da fahimta tsakanin Murjantu da Aisha, bata son yadda Taiwo ke treating matar kanin nata.
Taiwo tace Aisha ta biyo ta, kamar kada ta mike don ba tun yau ba jikinta ya gama bata Aunty Taiwo bata sonta ko kowa bai gaya mata ba. Amma jin Nenne bata ce a’ah ba, kuma Taiwo dinnan diyar Nenne ne da bata da maraba da Hamma, sannan Maman Kikinta sai kawai ta zari hand bag din ta da mayafinta tabi ta nata dakin.
Babban bedroom ne a wani sashe na cikin gidan sarautar, dakuna ne a jere wasu na fuskantar juna duk iri daya, yawanci matan Uncles din Abdulrasheed da matan ‘ya’yansu in suka zo sha’ani duk anan suke sauka, dakin da suka shiga da Aunty Taiwo ya ji kayan alatun rayuwa na gargajiyar sarauta dana zamani, ga iya kwandishin mai ni’ma nata aiki, akwai tafkeken gado da wardrove, Aunty Bola matar wani Cousin dinsu da Aunty Iyabo matar Turaki da Fatima da Firdausi ne a dakin suna hira lokacin da suka shiga dakin. Jikin Aisha a sanyaye matuka don yarbanci kawai kake ji yana tashi a gidan da sauran dakunan, koda suka shigo ma duk ta tsangwami kanta duk da Firdausi na tsokanarta da fulatanci tana cewa duk ta wani takure, tafi son koyaushe gta like da Nenne, tace ta saki jikinta nan duk iyayen Hamma ne sai su kannensa. Fatima ta Harari Firdausi tace da turanci don kowa yaji “in taga dama ta daure jikin don Allah, kinsan bata son shiga cikin yarbawa kada su cinyeta, ba abin raini a wurin yarinyar nan irin Bayerabe. I wonder yadda na jita shiru kamar an aiki bawa garinsu tun isarta gidan Hamma kuma”. Ifedayo ta zaro ido tace “kamar yaya bata son yarbawa? Ewoo! Bata son kabila ta auri dan su, dan ma babban jikan sarkin Ilorin da muke fatan ta zama uwa ga kowa namu watarana?”
Aunty Bola tace “ke ko Ifedayo! Ai ‘yammatan hausawa ba don so suke aure ba, kwadayin su ba inda baya kaisu. Balle taji sarauta zam, taji Prince na kasashen turai ai nan ‘yammatan hausawa dana fulani suka fi kauri. Sai an yi auren kiga ba soyayyar da zata dauwamar da farin ciki a cikinsa”.
Kamar an yiwa Aunty Taiwo kunni, ko kuwa allura akan gyambon ta, ta dubi Aisha ta kyabe baki, tace “ku bar ganin laifinta, iyayenta ne manyan kwadayayyu da basu san darajar kansu ba balle na abinda suka haifa, amma ba ita ba, tunda ita batama san shi ba ko kafin a auro ta, su da suka dauki wannnan teenager suka aurawa Kehinde wanda a haife ya haifeta sune suka fiddo kwadayinsu da zalamarsu fili, ta yaya zaka aurawa danka wanda baka ko taba gani a zahiri ko a hoto ba? Sai kawai don jin su waye iyayensa.
Wai daga haduwar kan hanya aka baiwa Nenne sadaqarta ta aurawa danta saboda an ga mamora a jikinta.
Ni tunda nake ban taba jin aure na rashin mutunci irin haka ba, ban taba ganin auren rashin sanin darajar Da irin naki ba, ai a al’adarku ana lefe, ana yiwa amarya kayan hana gori, amma ke ko lefen bana jin an yi miki, ke suturar da zaki saka ma a gidanmu mu muka yi miki, da tsummokara kikazo, ko wanka babu, aka bi aka asirce mana uwa, bata zance sai naki, amma ku duba kuga daga shan jar miyar Ewedu har ta fara washewa, ku kuke kayan daki amma ke haka aka daukoki zikau! Aka kawo mana.
Mun miki komai domin mu suturtaki, mai nuna sadaqarki suka baima Nenne ta likawa Kehinde ta karfi da yaji.
Kuma shi ba so yake ba, ya fada ya kara bashi da lokacin soyayyah, bazai taba son ki ba saboda ya dade da gama soyayya tun a kuruciyarsa, akwai wadda yayi shekara da shekaru yana so tun samartakarsa har girmansa bai aureta ba. kuma har gobe ita zuciyarsa ke so.
Ni nasan Kehinde wallahi, babu kuma wanda zai gaya min waye Kehinde, ko a kafa aka daura masa ke nan gaba kadan zai kwance ya yar.
Kawai kun ga arziki da sarauta kun nace, watakila ma kuna tunanin Kehinde zai yi sarauta ne, to in gaya miki gaskiya inma wanan kukewa keda iyayenki to kije ki gaya musu Kehinde bazai yi ba.
Da aka aura masa ke aka kawoki guidanmu saida ya jingineki kusan shekara guda, saida su Nenne suka gaji da ajiyarki a daki ne suka tattara ki suka danna masa ganin wankin hula zai kaisu dare.
Da zuwanki gidansa na fahimci kun soma juya masa kai, iyayenki nata surkulle ga dukkan alamu, har wani dora ki yayi a status baya ko jin faduwa a ganshi dake a matsayin mata.
Nayi rantsuwa ni Taiwo abokiyar tagwaitakarsa, inma asirinku ne ya fara cinsa ko zan daina barci sai na warwareshi da karfin addu’a, in asiri kuke shiga jeji kuna jefa masa mu addu’a muke kwana yi, yadda kuka ganshi haka zaku kyaleshi. Kakan kakanmu Shehu Alimi, ya dade da tofe zuri’ar shi da kul’aquzai, daga duk wani sharri na masu nufin Kehinde da wani surkulle na magauta da irinku makwadaita”.
Duk maganar nan Taiwo na yinta ne cikin sassaukan turanci da fulatanci ziryan, don ma Aisha ta fahimta sosai.
Siddiqah dai tana zaune banda kallon bakin Taiwo ba abinda take yi. Kirjinta yana harbawa zuciyarta na matsewa. Fuskarta na rinewa daga yellow zuwa jazir.
Saida Aunty Taiwo ta gama cin mutuncinta tas, su kansu su Fatima da Firdausi wadannan maganganu na Yayarsu Taiwo sun san firgitasu domin sunji sun yi zafi da tsauri sosai. Firdausi jikinta rawa ya fara yi ta soma cewa “haba-haba Aunty Taiwo? Haba ke kuwa don Allah Maman Kiki? Wannanba girmanki bane”. Ganin yanayin da Aisha ta shiga ya firgitasu. Babu ko digon hawaye a fuskarta amma tsigar jikinta duk ta tashi yarr, tsokar fatar bakin ta har raurawa takeyi amma ba kuka ba.
Taiwo zata wuce toilet ta bar su a wurin suka ga gabadaya jikin Aisha ya dauki kyarma, idon nan ya koma kamar

Please Login or Register in order to submit comment