Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ayi mana ba ko wannan faɗan daka ganin fin karfin mu akai,


jameel yace


"Insha Allahu zamu kiyaye muma musulmene,


Masha Allah jalaluldeen yace yayin da kowa ya koma gurinsa samin sukai suka zauna yayin da abrar ta kwanta a jikin tareek cike da tausayi jalaluldeen yace


"Wannan yarinyar abar tausayi ce mahaifinta amini nane a yanzu bata da kowa ba ko wanne lokaci muke samin abinci ba sama da shekar arba'in ba musan mene kwanciyar hankali ba ana kashe mu yawa kiyashi yara ƙanana sun zama marayu tun da abun nan ya faru ina lura da yarinyar nan yau ne ta sami lokacin yin bacci,


Dan ya mutsa fuska yayi domin shi bega abin da ya hada shi da labarin yarinyar nan ba duban sararin samaniya talaluldeen yayi yace




"Ɗana dan Allah wata alfarma nake nema a gunka ko wanne lokaci muna cikin bara zanar Isra'ila nima balalle in rayu ba inaji ajikina ko basu kashe mu na yunwa zata hallaka mu dan Allah da Manzonsa zan baka aurar abrar ka ruƙeta amanah kazama gatan ta bata da kowa in yan uwan mahaifiyar ta su kasan tana raye to tabbas zasu kashe ta .....,




da sauri ya ɗago kyawawa idanuwan sa cikin firgice jameel girgiza mai kai yayi runtsai idanuwansa yayi yace..........


*Tur ƙashi ga auran safna yar lelan sitti ga abrar wanne zance su bily suke ɓoyewa..? wanne abune ya faru shekara da shekaru...? mene ne maso min ƙaddarar abrar da tareek wanne bom ne zai tashi a family ɗin NADER..?*


Duk amsar tana gaba ku biyo ni yanzu taken ƙaddarar ta fara




DESTINY LOVE




Arewabooks@oumyasmeen


Pinterest www.oumyasmeen.com


Watt pad@Aminaoumyasmeen




Kar Ku manta kuyi following ɗina nadena posting complete a group


Ban yarda yan YouTube channel su daukar min littafina su mai damin audio ban yarda a mai damin da shi document ba in kunne yaji jiki ya tsira


Wannan shafin na kune


Aunty kainat


Aunty nainarh kd




Masoya ina godiya mara a dadi ina jin dadin saƙon son da kukewa littafina destiny love


Chapter 41-42




Kasa magana yayi sakamaƙon hannunsa da jalaluldeen ya kama yace


"Kai min wannan alfarmar na aminta da kai na yarda da kai dan hunin nan da nayi tare kai na kula da dabi'un ka insha Allahu ba zakai da nasanin aurar abrar ba nasan na miƙa ta a hannun na gari ba zayi kukan rashin mahaifiba,




Yawa me koyar magana yace....


"Na amince,


godiya yayi mai inda be kasa a gwuiwa ba ya haɗa mazan da suka rage a gun aka daura aure sosai jameel yayi murna ko ba komai yasan zai tallafi rayuwar yarinyar wasu kuwa jin haushin auran suke a ganin su jalaluldeen be dace yayi haka ba


washegari


cikin sauri sauri yake shirin sa ganin suna hada kaya da sauri abrar ta taso duk ta bushe ta rame da alama ma yau ba za'a kawo musu abinci ba ganin ko tayi magana basa gane me take faɗi dan haka ta tsaya tana kuka tafi so duk inda zasu sutafi da ita da hulya da jalaluldeen tausayi yarinyar ne ya kamshi ya dan rage tsayin sa cikin salon maganar kurame dan a ganinsa sai tafi fahimtar haka yake mata nuni da hannu aiki za su tafi zasu dawo


Kai ta ɗaga mai alamar ta fahimta biscuit ya ɗauko ya ɗan ƙa mata amsa tayi daman yunwa take ji kallon jameel yayi yace


"Malam za mu iya tafiya lokaci na kurewa?,


Dariya jameel yayi yace


"Sai da ka gama shan soyayya sannan zaka tuna dani,


Tsaki ya ja ya miƙe ganin sun fara tafiya tasa kuka hulya ce ta rungumeta tana lallashinta


cikin garin Gaza




Ga war wakin mutane suka fara cin karo da su daukan video suka shiga yi da sauri suka shiga wani tsauni suka ɓoye kuka jameel yake domin Beta ɓa ganin wannan rashin imani ba tareek kuwa da yake yana da taurin zuciya sai dai na zuci wanda yafi na fili tare wata mata sukai da mijin ta suka kashe ya'yanta guda biyu da mijinta saboda da tashin hankalin da ta shiga a take anan ta haihuwa ɗaukan dan sukai suka kashe ihu tasa tana bin su tana kuka itama su kashe ta dariya suka dinga yi kafar tareek ce ta zame da sauri jamee ya ruƙo sa ƙaddara ta ruga fata dukkan su sukayo kasa


Chak suka tsaya ganin wasu mutane daba yan kasar ba yunkurin guduwa suka sai ta su sukai da bindiga alamar suna daga ƙafa zasu harbe su hannu wansu suka daga sama ƙara sowa gunsu sukai dayan yace




"את עיתונאית? (At itonait?)


Ma'ana kai dan jarida ne


Dayan ne da bindiga a hannunsa yace


אתה סוכן חשאי? (Atah sokhen khassai?)


ku jami'an liƙen a sirine


shiru su tareek sukai musu domin basu iya Hebrew ba wani naushi dayan ya kawo wa tareek kaucewa yayi da sauri ya dauko ID card ɗinsa amsa yayi ya duba cikin harshen Hebrew yace




"Lior (ליאור) maƙiyan mune musulmai ku kashe su sunan sa Muhammad,


Innalillahi wa'inna'ilaihir raji'un


haka fa ke faruwa duk wani arni ya tsani musulmi musamman me sunan Annabi Muhammad (S.A.W) duk hanyar da zasu bi su musgunawa me suna sai sunbi in da dama ma kashe mutun za suyi Allah ka daukaka musulunci da musulmi Allah ka kawo wa kasar Palestine sauki Allah ka kawo kasar shen tashin hankalin da suke cikin


ya Ubangiji Allah ka tarwatsa Isra'ila da duk mutumin da ke da sa hannu gurin rusa Palestine ya Allah ga kasar mu Najeriya...


Allah duk wani matsala da muke fama da shi Allah kai mana maganin sa ina taya yan uwana musulme barka da shigowar sabuwar shekara ta musulunci


kansu suka nufa da sauri tareek ya durƙusa ya dauki ID card ɗinsa suka fita aguje binsu suke sai ta tareek dayan yayi da bindiga cikin rashin sa'a bata same shi ba sun lura da cewa wannan farin shike nadar bayanai dan haka suka dinga sai tashi da bindiga gaban wani tabkeken kogi cikin rashin sani tareek ya waɗa ihu jameel ya saki cikin sauri suka ƙara so gun da sauri jameel ya rufe bakin sa ya maƙale a cikin wani kogon bishiya yana kallon su


dariyar arna ɗayan ya saki yana kallon cikin ruwan yace




"Yuval (יובל) Yair (יאיר) Tamir (תמיר)ku zo mu tafi nasan ba wanda zai rayu a cikin su.....,


juyawa sukai kuka jameel ya fito yana yi zaman dirshan yayi yana kuka duba wa yake ba tareek ba labarin sa


shima waɗawa yayi cikin ruwan duk kuwa da girman ruwan be iya ruwa ba dan haka nutsaiwa yayi ga igiyar ruwa na janshi......


Bakin tabkeken kogin Israel wanda an ƙawata shi sun mai da shi gun shaƙatawa


wasu kyawawan yan mata ne a tsaye a bakin beach ɗin duk kan su ba me kayan arzuki rungume dayar tayi tana tsotsar bakin ta basu damu da yarda mutane ke shige da fice a gun ba sosai suka shagala gurin aikata masha'arsu dayar ce ta so ta kama tausasan breast dayar ta fara sha kai kace tana kan cinyar mahaifiyar ta ko ƙarin biyawa kan su bukata suke da sauri dayar ta dubi cikin ruwan nan tace


"Ayelet (איילת) מים - mayim),


Ayelet kalli cikin ruwan nan ganin sun yi nisa da abin da duke ta matso kusa da su ta cire su ganin sun makalle juna ta nuna musu cikin ruwan da sauri suka nufa siririyar cikin su tace


"Batya (בתיה) אתה יפה (Atah yafeh,


Ma'ana kalli wani kyakkyawan mutumi


Wacce aka kira da batya ta yi sauri waɗawa cikin ruwan yawo take yawa wata kifi har ta ƙara sa gun ta rungumu Shi ta fito da shi za gaye shi suke Ayelet tace


,אתה יפה מאוד (Atah yafeh me'od"
Duk inda me kyau yakai ya kai


te mako suka fara bashi sai dai me sai da sauri nao ta dago ganin wani shima da sauri ta nufi cikin ruwan shiga tayi ta dauko shi jere su sukai tace


"Duk yarda akai wani abu suka gujewa suka fada cikin ruwan nan wannan ruwan kunsan har Palestine,


da sauri batya tace




"Palestine...?,


NAO tace




"Ehmn wannan mutanan daga yankin Palestine suke ko baki ga daga kudu maso gabashin Jordan suke ba ,


AYELET tace


"Wallahi da nasan daga yankin makiyan mu suke bazan temake su ba haka kurum kin katsai mana jin dadi,


Tsaki NAO tayi tace


"zargi nake ban tabbatar ba baki ga wannan ba black ne....?




Batyet barin gun tayi ta nufi wani tamfatsaitsan gu ga baki dayan SA glass ne towel ta nauka ta goge jikin ta wani matashi ne ya rungume ta tabaya yana mammatsa mata breast ɗin ta numfashin tane ya dauke na hucin gadi ture shi tayi tace


"Na gashi yanzu bani da wani sauran feeling,


dago runannun idanuwansa yayi ya kama mota haɗe bakin su yayi cikin zafi zafi yake romantic da ita har ta fara mayar mai yawa wasu tsunmokara haka suka zube akan hadaddan luxury bed ɗin dakin....






*Kano unguwar gadon kaya*


*Karfe 9:30pm GMT*


"Heartbeat tunfa jiya nake kiran number su jameel a kashe Allah isa lafiya amma wallahi jikina yana bani a kasin haka kasan da gun nan ba shi da kyau balle ga irin aikin da suka je hi ,


Tissue ya yago ya goge bakin sa yace


"Allah isa lafiya nima na bibiye su amma shiru na duba shafin su naga tun da jameel yayi posting a bin da ke wakana a Palestine be ƙara ba haka tareek,


Lushe idanuwanta tayi tace




"Nasir ,


da sauri ya ɗago ya dubeta tun da suke ya manta rabonsa da yaji takira sunan sa ɓoye mamakin sa yayi yace




"Na'am ,


Tashi tayi ta juya bayan tace


"Wace baby nice,


cikin hanzari ya tashi yace


"baby nice kin santa ne ..? nima ita nake nema,


cikin shashekar kuka tace..




"yau naga sako ta email ɗina wai ina so insan wanda ya kashe Sultan san nan kar indamu ba wanda ya isa ya cutar da tareek duk da yanzu masu neman ransa suna ci gaba da aikin su duk inda yake suna tare da shi ...,


ma tsowa kusa da ita yayi ya juyo da ita yana kallon ta yace


"Nima naga saƙon nan kar ki damu insha'Allah komai zai huce,


Kuka tasa ta rungumesa tace


"Sai yaushe Nasir bani da wani ɗa yau naje asibiti likita yace min ko anjuyo min da mahaifa balalle ta ƙara daukan ciki ba Nasir na cuci kai na ya'ya sai dai inga ana haifa..,


Cikin lallashi yace


"Aysha irin ranan nan nake guje mana tun farko kika ƙi ganewa ina mutukar son yara amma ba yarda za muyi wannan ita ce kaddarar mu ba mu isa mu chanzata ba ,




Ruke hannuta yayi suka hau sama


Ko ina shiru tsit baka jin motsin kowa a hankali take saukowa taka staircase take yana bada sauti dena tafiyar tayi dan jin sautin takun da take daban sautin abin da take ji daban ji tayi kamar an taɓa mata ƙeya juyowa tayi da sauri ta saki wata iriyar ƙara sai dai me ...?


Ba'a jinta sai wata dariya da yake amsa kowa a tabkeken floor ɗin ta kifawa tayi domin wani irin duka da a kai mata da sauri ta fita bata tsinci kanta a ko ina ba sai a wani daji ba gida gaba ba baya ga bishiyoyi sai zaga yeta suke kai kace mutane ne ke dawafi a gaban ka'aba


Wani ƙaton mutum ta gani a gaban ta bata iya ganin karshen sa cikin wata iriyar murya yace......












DESTINY LOVE


OUM YASMEEN




43-44


A gigice ta farka tana wai waye da sauri ta kunna lamp ɗin datake kusa da gadonta haske ne ya mamaye dakin zuciyar ta na wani irin bugu yawa ta waɗo zuru kafafuwan ta tayi kasa domin wallahi baza ta ci gaba da kwana a dakin nan ba haba wannan masifar har ina ta yau daban ta gobe da ban wayar ta ce tayi ƙara da sauri ta dauka ganin me kiran dafe kirji tayi tace


"Innalillahi bily ta mutu ,


Wayar ce ta sulale a hannunta tabbas mun taɓowa kan mu a bin da ba'za mu iya ba na shiga uku sauran ni


kuka take yawa ranta zai fita bata san safiya tayi ba sai ganin haske ta window ɗinta tayi ya shigo yawa wata mahaukaciya ta tashi ta shiga toilet a gurguje tayi wanka shafshaf tayi sallah ta ɗauki key ɗin motarta ta fita a ji tayi an bigeyta juyowa tayi ta dauke nasreen da mari ai bata dure hannun ta ba ta shararara mata mari cikin mamaki tace


"Nasreen Ni kika mara...?,


kallon tara sauran kwata nasreen tayi mata tace


"Au tantama kike ko in ƙara miki..?,


Wani kallo tayi mata na zamu gaura ya tayi gaba tace


"Bani da lokacin ki amma kin ɗauki bashi,


Dariya Nasreen tayi tayi gaba tana yar waka


shiga motar ta yi cikin sauri take tuƙi sai kotu road a bakin kofar gidan su bily ta faka da sauri ta fito ta shiga gidan gwuiwoyin ta kasa ɗaukar ta sukai lokacin da taga bily a shinfiɗe ko wanka ba aimata ba


sa hannu tayi ta buɗe gawar zaro ido tayi ganin irin kisan da akai mata


shaƙe ta akai har ta mutu zubewa tayi tana kuka har haka hada ta bata dena kuka ba


ga su nucy suna zo har da tafida ko kallon safna basuyi ba ganin mutane sun fara raguwa safna ta fito sa'a taci garo da nucy da tafida suna tare kusa da su ta tsaya tace


"Yanzu shawara daya ta rage mana ko ku ɗauka ko karku ɗauka amma ita ce mafitar halin da muke ci inba haka ba to lashakka za'ai tayi mana zari dadde kuma kunsan baza mu iya tsare mai ba bubuwan nan sun isheni haba yau ba bayijjah ba bily jibi fa.....,


Kallon hadarin kaji tace


"Ci gaba muna sauraran ki...,


yar ƙaramar dariya tayi tace


"NUCY TAFIDA hmmm ku naga har yau bakuyi nadama ba to wallahi kuna gamai mai aiki kashe ku zaiyi kamar yarda ya..... Sai tayi shiru bata ƙarasa ba saka maƙon ganin NAZEER da tayi sallama NAZEER yayi musu tafida ya meƙo mai hannu suka gaisa yace


"A'a kaga dan jarida duk inda aka ji anyi wani abun sai kunzo ,


dariya yayi yace


"Wannan shine aikin mu kuma hanyar samin abincin mu ,


NUCY tace


"Hakane Allah yasa ba da wata a kasa ba ake bibiyar rayuwar mu,


Satar kallon SAFNA yayi yace


"in ba rami me yakawo rami ko aikwai wani abu da kuka sani akan mutuwar SULTAN BAHIJJAH BILY..?


saboda mutuwar su tana da a bin mamaki ko wanne da irin salon da aka kashe shi in kunsani baku faɗa ba tofa wallahi Allah gaba kan ku za'a dawo ku faɗi me kukai ake bin ku ana kashewa ke ankashe miki dan uwa


da alama wani aka zo kashewa ba asami wanda aka zo kashewa ba aka kashe shi ko ya ji wani abu wanda zai iya faɗa shine aka kashe shi ɗan kar ya tunu asiri mutuƙar baza ku faɗi ba wallahi kun shi ga ku Uku da kuka rage tofa kuma kuna kan hanya ,


Gumi ne ya wanke safna da sauri ta matsa ta buɗe murfin motar ta shiga ta tada ta a gushe ta fita


kallon kallo aka shiga tsakanin tafida da nucy sun fara fa zargin ba iya jarida NAZEER yake ba harda bincike to aikuwa za suyi maganin sa...








*ISRAEL*


*Assuta Hospital*


20 Habarzel Street Ramat Hachayal


*neighborhood in north Tel Aviv, Israel*


Tsakanin su da Ben Gurion international airport ba nisa


Buɗe idanuwansa yayi tuni abin da ya faru ya dawo mai sabo yawa yanzu yake faruwa da sauri ya tashi ajiyar zuciya yayi ganin suna tare da tareek cire ƙarin ruwa yayi ya ƙara sa gunsa sai akai sa'a shima ya tashi godiya yayi wa Allah ganin be mutu ba gasu a tare yace


"Tareek ya jikin ka ?,


Cikin yana yi na rashin lafiya duba da irin lalurar sa yace


"Da sauki kai ma yana ka ..?,


Duban dakin da suke cike yake yace


"Alhamdullahi da sauki tareek yaka mata mubar ƙasar nan in har muna son ran mu da lafiyar mu,


miƙewa yayi ya zauna yace


"To muna barin asibitin nan sai airport,


da sauri Jameel ya kalle sa yace


"ABRAR fa ka manta da ita?,


dafe kansa yayi da yake sara mai da sauri suka dubi kofa ganin anturo likita ne da wata budurwa sanyi da mini skirt da riga mara hannu murmushi ta sakar musu tace


"Allah na gode maka sun sami sauki,


duban ta likitan yayi yace


"Za mu iya sallamar su inna duba su naga sun sami sauki ba wata matsala,


zama tayi kusa da tareek tace


"Okay thank you,


kayan da ta gani a jikin su ta miko wa tareek da sauri ya amsa ya buɗe ya fito da Flash ɗin sa zuciyarsa na wani irin bugu in suka rasa komai wannan abun ya lalace sun sha huya abanza da yake yana cikin wata jaka ko ruwa be shiga ba ganin tana jin turanci yace


"Nagode,


NOA tace


"bakomai nayi dan Allah ne tsakanin mu ba godiya amma ku yan wacce ƙasa ne?,


da pillow ya jin gina yace


"Nigeria,


dan ya mutsa fuska tayi ta dubi jameel tace


"Ya jikin ka kai nafi yarda da ɗan Nigeria ne amma ban da kai ta nuna tareek,


kau da kai tareek yayi likitan duba su yayi ganin basu da wata matsala ya sallame su NOA tace


"Sai mun ƙara haduwa ga number ta kuban taku suna na NOA YUVAL RON ku fa ?,


Gyara tsayuwa jameel yayi ya amshi wayar ta yasa mata numbers su domin tayi musu halacci yace


"JAMEEL UMAR TAKAI,


murmushi tayi tace


"Wow nice name,


ganin tareek yayi shiru tace


"Miskili kai ya sunan ka ?,


dan basar wa yayi yace


"TAREEK BN NADER,


dan jim tayi tace


"Nice name amma ina da wata shawara kar ka bari mutanan mu su san sunan ka Muhammad ka dinga cewa sunan ka isa har kabar garin nan yana da hadari sosai musamman aka san kai dan Palestine ne,


dan murmushi yayi ya yace


"Nagode,


Sallama sukai suna fitowa suka nufi hanyar da zata mai da su palestine har gaɓar teku mota ta kai su sauka sukai suka bada kudi suka hau jirgi isar su palestine suka tatda tashin hankali.....










DESTINY LOVE














Arewa books@Oumyasmeen


Watt pad@ Aminaoumyasmeen


Perfectly pen's








Episode 45-50




TAREEK POV


Cikin kiɗima yake duban gun duk gawarwakin mutane da'alama da asubayin ranar aka sa musu bom ƙafafuwan sa kasa daukan sa sukai lokacin da yayi arba da gawar jalaluldeen da hulya zai iya rantsaiwa wannan tashin hankalin da yake ciki yafi na mutuwar SULTAN tabbas kuka samin sauki ne idanunsa sunyi ja wai yaushe za adena kashe musulmi ne ..? rayukan su yazamo tamkar ran kiyashi......


Jameel ne ya kara dubawa ana haka yaga gano abrar duk jikinta jini sai numfar fashi take da sauri ya dauke ta miƙawa tareel yayi be jaba ya amsheta ana haka sai ga jami'an tsaro na kasar cikin fushi tareek ya tashi ya tare su yace


"Me kuka zo kuyi bayan angama komai kunzo ku binne kawarwakin wayan da basu ji basu gani ba tur da halinku me yasa baza ku kawo musu dauki ba a lokacin da suke tsananin bukata yanzu mene amfanin zuwan ku..?,


Jikin sune yayi sanyi...


besan cewa basu da ikon dakatar da cutarwar da Isra'ila ke musu ba wani abun sukan faki numfashin mutane suyi musu tabbas komai yayi farko zai ƙarshe suma ba'a son ransu hakan ke faruwa ba basuyi zargin shi ba dan ƙasar bane duba da irin launin fatar shi dan haka suka kashe wa'yanda suka mutu wa'yanda suka jinyata suka kawo masu duba lafiyar su...


Bayan an gama sallatar wa'yanda suka rugamu gidan gaskiya daman likitoci sun fara aikin kola da wa'yanda suka sami rauni ciki har da abrar ansamu ta farfaɗo dan haka tareek yace...


Tafiaya zasu yi sarah bata ji dadi ba ganin yanzu bata da kowa mijinta jalaluldeen ya mutu cikin muryar kuka tace...


"Zan ƙara jaddada maka amanar Abrar Ibrahim kesar a yanzu bata da kowa sai Allah sai kai kaji tsoron Allah ka kula da ita kabata ilimin addini da na boko ka tarbiyantar da ita kamar yarda Ubangiji ya fada wata ran ka dawo ka kawo ta taga a halin ta


yan uwan mahaifinta suna Jordan da zama can suka koma nasan koman daran daɗewa zasu dube ta zasu dawo gare ta,






jikinsa ne yayi sanyi zuciyarsa tayi rauni....


yawa me ciwon baki yace


"Insha Allahu zan roƙe amana ko baku bani amanarta ba ni bazan iya Cutar da kowa ba.,


Farin ciki ne ya mamaye zuciyarta tace


"Nagode Allah ya yi muku albarka,


Amin yace jameel ya dauki kayan su


shi kuma ya dauki abrar saboda raunin kafarta akafada yasa ta haka ya juya ya fara tafiya jameel ya mara mai baya lub abrar tayi hawaye na bin kunci ta garin da aka haife ta yau zata barsa lumshe idanuwan ta tayi har suka zo gabar teko Palestine da Jordan ba wanda yace da dan uwansa kala kowa da irin tunanin da yake...


Jirgin ruwa suka shiga da zai sada su da kasar Jordan daga nan kuma in sukai kwana biyu su huce kano dole sai yayi wa abrar viza tunda bata da shi shiga sukai


a hakali jirgin ya fara tafiya abrar gyara kwanciya tayi a jikin sa Allah yayi mata son jiki da yake da abin da ke damunsa be damu da yarda take shige masa jiki ba......




SHATTIMA BABA GANA






Ƙanta ne ke wani irin sara mata cikin karfin hali tace


"Yagana yanzu ya kikeso inyi da raina kinfi kowa sanin damuwata,


gauran numfashi tasaki ta jin gina da luxury sofa tace


"Ya kaltum tun farko gabaki ɗayan mu mun kasa sarrafa zukatan mu mun kasa ɗaukan kaddara da mun rungumi ƙaddara wallahi da yanzu wani zancen ake ba wannan ba duba ki ga komai na shirin jagule mana ..?,


ɗaga kanta sama tayi ta ƙurawa p.o.p ɗin dakin ido cikin raunin zuciya tace


"Yagana wallahi har yanzu banyi danasanin hukuncin da alanguburo ya dauka ba ,


Dan murmushi yagana tayi ta gyara zaman ta tace..


"Hmmm ya kaltum kenan,


glasses cup ta ɗauka ta kai bakin ta duk daɗin tatatcan pineapple and coconut juice wani irin ɗaci take ji yana yi mata a bakin ta wai sai yaushe ƙaddara zata dena wala gigi da'ita..?,


aguje nur ta shigo tace




"Auntin barno..,


Cikin fara'a ta ware hannunta tace


"NUR,


Ƙara'sowa tayi ta rungume ta tace


"Aunty ina lubna...?,


Lubna tana gidan hajja kaka


Aisar ne ya shigo farin ciki ne ya mamaye shi ganin aunty sa yace


"Sannu da zowa aunty,


Yauwa tace masa nan fa hira ta farke a tsakanin su kowa na nan nan da antin barno


BN NADER FAMILY


Ran Alhaji Abdullah ne ya ɓaci cikin faɗa yace


"Wanna ai shashancin banza ne in zaku farka tun huri Ku farka saboda rashin hankali kuna so ku zautar damu wacce irin fatalwa ana zaune ƙalau ke Rahama zan laminci wannan ƙageggen zancen naku ba...
namasu taɓin ƙwaƙwalwa..?,


cije leɓen ta tayi domin wallahi ita ganauce ba jiyauba dan haka dole fa malan me turakar yasin yayi mata addu'a a gidan nan ba fashi mom Amina tace


"Amma ai...,


ɗaga mata hannu yayi yace


"Ƙar ki ɓatan rai nide na gama magana tun huri kisa wancan mashiriki ya barmin gida..,


tashi tsaye tayi tace..


"Yanzu kai min adalci kenan kasan kuwa irin tashin hankalin da jiya nashiga..? yanzu malam me turakar yasin ɗinne mashiriki..?


To wallahi a iya bakin ka har da aljanu faɗa yake kabi shi a hankali kar ya shanye maka ruwan ƙwaƙwalwa


da'katawa yayi daga tafiyar da ya fara yace


"Rahama naga kina so ranki ya ɓaci to ki bar wannan mutumin ya ƙara hour daya a gidan nan saboda kin rainani ni zai shanyewa ruwan ƙwaƙwalwa yana faɗar haka yasa kai ya fita


Gyara ɗaurin kanta tayi tace


"Wallahi saina yi ai bakai ake tsoratawa ba..,


Ba ko sallama ya shigo yana rawa da'katawa yayi ganin wani uban carɓi a huyan wani tsoho cikin mamaki yace


"Kai lafiya me ya kawo ka..?,


Malam me turakar yasin yace


"Hattara dai yaro ka iya bakin ka ko yanzu in maida maka da bakin ka huya..,


haɗa rai Salim yayi yace


"Kai anfaɗa maka wannan kurarin naka zasu tsoratar dani..? wallahi tun huri kwashe wayan nan matattun ƙafafuwan ka kayi gaba ko yanzu in nuna maka zamani ,


Cikin sauri mom Amina ta ƙara so tace


"Na shiga uku Salim kanka ɗaya kuwa

Please Login or Register in order to submit comment