Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

mishi hakan dan ya
rabu dani. Duk da yanzu ina na damar hakan. Na dubeta
sosai yanzu bana jin kunyar in furta ina son Abubakar,
don bansan ina sonsa ba sai yanzu da na koreshi.
Rahama tace kila kiga ya dawo, amma in yazo kada ki
kuma kuskuren da kikayi a baya. Nace, Rhama na rokonki
dakada kimin karya don hankalina ya kwanta, na tabata
ko Abubakar yana shaye shaye ba zai dawo gareni ba.
Tuni na dangana dashi, tun ranar da na tura mashi wani
sako da dadare, kin ga amasar da ya bani nan acikin
wayata. Na sauke ajiyar zuciya tare da share wani
hawaye da ya biyo kan karan hancina yayi min dan
maimayi. Rahama na gane kuskurena da nasani nabi
innata nasan ba zan tozarta ba, zasuyi hakuri dangin
uwata zasu rikeni da ko na hadu da Abubakar bazanji
komai ba. Lallai barin gaban iyaye matsala ce katuwa.
Rahama tace, ita dama mace guri 3 yakamata ta
kasance, in bata gidan ubanta to a sameta a dakin
mijinta. Idanto ya kasance baki can to a sameki a kabari,
ta cigaba da cewa, duk inda mace take a sameta a
karkashin wani uba ko miji, ko wa, ko kani, ko daki. Idan
aka sami mace bata kar kashin ko 1, lallai ba wanda zai
ganta da kima ko daraja. Kare da doki suna iya kawo
maki hari tunda ke yar kanki ce, don haka duk lokacin da
Allah ya kawo maki miji to kiyi aure zafin da kika dauka
kan maza ba inda zaya kaiki, tunda sune a bokan
rayuwa.Rahama tayi wa abubakar text din kwatancen da
na ambata cikin hiran mu don haka washegari suka
dunguma suka nufi kaduna har da sagir inata yi wa
rahama mitar sallama in likita yazo ta fada mishi saboda
sagir na kashe kudi wanda a zatona shine me kashewa
ta ce min in nutsu in warware tas,sun isa kaduna
shekaru masu yawa bai tsaya a garin kaduna ba tun
daya bar ta sai de ya wuce ta a mota tambaya suka yi
aka nuna musu rigasa haka ma abuja road sai dai sun
sha wahala da ta sama suka yi mamakon ta kasa sun
shiga layi na ukusun tambaya gidan yawa amma babu shi
sun zaga sun gaji har sun fita daga abuja road sun fada
makarfi road
Abubakar ya ce mu dai koma kan abuja raod din mu sake
yin tambaya daga bisani suka yi tambaya a wani
masallaci da ke layin na ukun bayan sun idar da sallah
nan mutane suka basu shawaran suje ta kasa Ikon Allah
suna shiga layi na uku Abubakar ya gane gidan su Hafsa
domin tsawon shekaru gidan yana nan yanda yake baa
kara komai ba saidema kara lalacewan da yayi suka
tsaya kusa da gidan yara nata wasa a kofar gidan cikin
kasa sagir yace kana da tabbacin cewa nan ne gidan
yaya ma akayi ka sani abubakar yace nazo shekaru da
dama bayan fitowar yarinya daga gidan yasa su yin
shuru yar doguwa marar jiki tana sanye da doguwar riga
ta farin yadi da kore kalar tutar nigeria gadukkan yan
kaduna duk wanda ya ganshi yasan cewa yadi ne na
makarantar primary ta gwamnati tana rataye da yar jaka
ta buhu mai dauke da littattafanta na makaranta kafarta
sanye cikin sandal na roba wanda igiyoyinsa suka
ciccire,Abubakar gabanshi ya fadi, tamkar hafsat a
shekarun baya. Yace yanmata zo mu tambaye ki mana.
Ta tsaya nesa dasu, abubakar yace nan nan gidan su
hafsat? Ta maimaita sunan hafsat? Yace, eh. Tayi shuru
tana son tunano wacece hafsat a cikin gifan nan? Ta
dubeshi karama ce? Yace, baba ce, suman mamanta
inna ta zaro ido inna? Yace eh. Duk yan dakinsu suna da
labarin hafsa yayarsu, duk da itace karama kwarai a
lokacin da abubuwan suka faru ba zata mance da sunan
hafsa ba. Sai dai kamanin hafsat sun bace mata. Inna
kuwa ai uwarsu ce, wace babansu ya kora sanadin abin
kunyar da akace hafsat tayi. Ta dubeshi tace, hafsat
bata nan, hakama inna. Yace, ina suka je? Cikin kagara
tace, nima ban sani ba. Inna dai tana funtuwa. Yace, to
baba fa? Ta nuna gida da yatsa, yana ciki bashi da lafiya,
sagir yasa baki. Kice masa yana da baki. Tace, saidaifa
ku shiga, don baya iya fitowa. Hashim yace, to fada
masa sai mu shiga. Tana juyawa, sagir yace, wanan
yarinyar tana matukar kama da hafsa. Abubakar yace,
donma baka santa tana karama ba, da cewa zakayi
itace. Tafito tace, yace in shugo daku. Suka rufe mator
suka bita. Lallai gidan yawa ta sunan nanshi inji sagir.
Kansu a kasa saboda yawan matan gidan da yaransu,
wasu kuma suna wasu ayyukan. Sun dan gaisa da
wadanda suke bakin hanyar zuwa dakin, yarinyar da ta
shugo da tabarma ta shinfida musu a gefe suka
zazzauna suna fuskantar tsohon. Yana kwance kan
tsohuwar katifar shi, wadda ta lakume. Suka gaisa, dakin
yayi shuru lokacin yarinyar ta kara dawowa da kwanan
sha na silba mai dauke da ruwa ta dire masu. Baba yace,
kai cema babarku ga baki. Itama ta shugo su gai sa.
Baba yace, kin shaida su? Tace, a a yace samari daga
ina? Abubakar ya zunguri sagir, nan take sagir
yace."Baba mu baki ne daga Kano."
Baba yace, "Kano gurin wa kenan?" Ya ce, "Ba za ka
shaida mu ba, ni sunana Sagirn wannan kuma Abubakar.
Sai kuma wannan Hashim." Sagir yayi dan shiru saboda
tunanin ta inda zai fara maganar.
Can ya ce, "Wato Baba za ku ji mamakin cewa mun zo
neman auren Hafsat ne."
Baba ya yunkura ya zauna wanda baisan lokacin da yayi
hakan ba, domin in zai irin wannan zaman sai an kama
shi.
Ya ce, "Hafsatuna?" Hashim ya ce "Ita" A rude Baba ya
ce, "A ina kuka ganta? Don Allah ku fada min, kun ganta
ne?"
Tausayi da kaunar tsohon ya ratsa zuciyar Abubakar, ya
ce "kada ka damu Baba, Hafsat tana nan lafiya."
Ya ce "Alhamdulillah, Allah yasa ba irin mafarkin da na
saba yi bane, tare kuke da iata?
Hashim ya ce "Ba mafarki bane Baba, kuma ba tare
muke ba." Ya nuna Abubakar. "Ga mai sonta da Aure
nan, mun zo ne mu sanar da kai magabatanmu za su zo.
Sai dai matsalar da muke tunani kada su zo kuma wani
ya basu labarin cewa ta bar gida. Kila sanadin hakan
iyayen mu suki amincewa."
Baba ya ce "Wannan ba matsala ba ce, in sha Allahu,
Amma kafin nan ina son Hafsat ta zo gida, yarinya tafi
daraja idan tana gaban mahaifanta."suka ce To Insha
Allah za su kawota, ko kuma su tafi da wani ya ga inda
take.
Baaba ta ce, "Kai amma wannan abu ya yi dadi, amma
ku jira wanta yanzu sai ku gaisa, batun zuwa kuwa nice
zan biku, ko kuma muje tare da Umar wansu din." Suka
ce A kira shi. Sagir ne ya dauki lambar, bugu daya ta
shiga ya dauka tare da Sallama, Sagir ya amsa ya ce,
"Mu baki ne daga Kano, gamu nan gurin Mahaifinku,
zamu samu ganinka?" Ya ce, "Lafiya?" Sagir ya ce,
"Lafiya lau." Umar ya ce, "To gani nan zuwa, zan shigo
layin da fasinja." Sagir ya ce, "To."Suna zuwa kan layin
Umar ya cema kwandastansa ya kara dasu shi zai shiga
gida, ya basu hannu suka gaisa sannan ya yiwa Baba
sannu da Jiki. Cikin doki Baba ya ce, "Jiki da sauki, sun
zo ne da labari akan Hafsatuna, abin dadi har da mai son
aurenta, gashi nan tsakiya." Da tsananin mamaki ya ce,
"Da gaske kun ga Hafsa? Allahu Akbar!!! dama tana
raye?" Sagir ya ce, "Tana raye." Umar ya ce, "Ikon Allah!"
Baba ya yiwa Umar bayanin komai da yanda suka yi.
Umar ya ce, "Baaba ki zauna ni zan je naga inda take
kafin, in yaso kwaje daga baya." Baba ya ce, "Haka ma
yayi Umar." Umar ya ce, "Shawarata anan ko za a ce
bakin suje can Funtua wajen Inna a karbi auren?" Sai
Baba ya ce, "Ba komai nan ma yayi Umar. Allah shine
mai yanda ya so."Umar ya shiga motarsu, inda suka je
gidanshi suka ci suka sha, sun huta sosai, sai karfe 5
suka ce zasu tafi.
Abubakar ya kasa hakuri ya ce, "Yarinyar can tana kama
da Hafsa." Umar ya ce, "Ummi, 'yar autarmu ce." Ya ce,
"Masha Allah." Duk yaga sauran kannanta yanzun saura
Inna, suna gidanma Umar ya kira wayarta, bayan sun
gaisa ne yake fada mata cewa cewa Wadansu bayin
Allah ne suka zo da labarin Hafsatu, cikinsu har da
wanda zai aureta. Cikin tsananin mamaki ta ce, "Da
gaske kake?" Ya ce, "Gasu nan ma." Ta ce, "Harda
Hafsat din?" Ya ce, "A'a, zan dai bisu muje in ga gurin da
take." Ta ce, "Ko zaku biyo mu je?" Ya ce, "Kada ki
damu Innarmu ni kadai na isa, tunda gida zata dawo."
Inna ta ce, "To."Biyar da rabi suka dauki hanyar Kano su
4 ne. Suna hira a nan Umar ya samu wadan su labaran
game da Hafsat, nan ne ya ji cewa bata san sun zo ba,
bata da lafiya don haka ya ce, "To in mun je ku bari in
fara shiga."Kusan karfe 8 suka iso Kano, sai da suka yi
Sallar Isha'i sannan suka isa gidansu Rahma. Tana ganin
Umar ta gane dan'uwan Hafsa ne, saboda kama ta jini.
Da sun ce a bari sai da safe a je gurinta, Umar ya ce shi
kam yanzun yake son zuwa. Dole suka tafi, daga bakin
kofa suka tsaya Umar ya shiga da sallama.Mama tana
sallar Isha'i, ni kuma ina bakin gado. Ina jin a jikina
tamkar wani bakon al'amari zai same ni. Muryar Yaya
Umar ta katse ni, da sauri na dubi kofar, zumbur na mike
tsaye jikina yana kyarma na ce da sauri, "Yaya Umar!
Yaya Umar kai ne ko mafarki ne?" Ya yi murmushi, "Ni ne
Hafsa." Na zuba masa ido, ya sake zama magidanci, ya
tako ya rike hannuna, na ce, "Kai da wane ne? Wa yace
maka ina nan?" Ya zaunar da ni a bakin gado ya ja kujera
ya zauna dai dai lokacin da Mama ta idar da Sallah.Na
ce, "Mama ga Yayana Umar." Ta juyo suka gaisa, su
Sagirr suka shigo har da Abubakar. Shi na zuba ma ido
tamkar wadda na warke makanta. Shi kuwa ya hade rai
kamar wanda zai fadi sakon tashin bom.
Mama kadai ya gaisar, bai kalli inda nike ba ya ci gaba
da karanta wata takarda da aka lika a jikin bango, ta
masu gargadin ciwon kanjamau. Hankalina ba ya tare da
su, don haka ban san me suke tattaunawa ba, yau wane
irin mafarki nake yi? Ga Yaya Umar ga Abubakar?
Mutumin da na cire rai da sake ganin shi, ya dawo ne?
Ko kuma daman yana nan? Ashe wai a fili nayi zancen,
sai na ji Sagir ya ce, "Wa?" Na dube su cike da damuwa
ina zare ido. Na kalli Abubakar, "Don Allah ku fadi min
ina mafarki ne?" Sagir ya ce, "Hafsa mune muka zo da
Umar." "Kun je gidanmu ne? Wa ya kaiku?"Nan take na
mike don watsa ruwa na fito na jawo jakar Rahma na
murza hoda. Ta ce, "Iye! Har da su hoda? Kina son birge
Abubakar." Na ce, "Ina ruwana da shi?" Mama ta ce,
"Sauki ya samu ta 'ki saka hoda? Har da kwalli radau
kayanki." Na ce to. Sannan na ce Rahma ta dan hada
min tea.
Lokacin da Sagir ya isa masaukin nasu, ya same su suna
karyawa, hira suke yi inda Umar ya basu labarin barin
Hafsa gida, ya ce kowa ya sha mamakin faruwar
matsalar saboda Hafsa nitsatstsiya ce, ko yawace-
yawacen nan na 'yan mata bata yi, bata ma da kawaye,
son bokonta ne yasa wannan saurayin ya yaudareta har
ya kai ga yi mata ciki, kasan mata da karamar
kwakwalwa, idan saurayi na kashe musu kudi babu wuya
an yaudaresu. Hashim ya ce, "Labarin da Rahma ta
bamu fyade yayi mata shi saurayin." Umar ya ce, "Ta
yiwu haka ne, don lokacin da abun ya bayyana Babanmu
bai kwantar da hankali an ji yadda lamuran suka faru ba,
kawai ya kore su ne."
Abubakar ya ce, "Ta bakin Umar ne mace idan tana son
namiji ta hadu da Shaidani, to ba zata yi wuyar bada kai
ba." Sagir ya ce, "To duk dai komai ya wuce. Allah ya
tsare mana zuri'a kuma ya rabamu da rudin shaidan."
Ameen ya Rabbi, suka amsa.
Ran Abubakar fa a bace yake amma bai nuna ba, a nashi
ganin ba wani fyade, ita dai dan tana son shine taje don
sakarci ta bashi kanta, har saida yayi mata ciki sannan
za tace yayi mata fyade, dan ta kare kanta ne kawai, wa
ma yasan adadin kwanciyar da tayi da shi. Ya ja
tsaki.Sun shigo ina shan tea, na ajiye ina kallon Yaya
Umar na ce, "Ina kwananku?" Suka amsa amma ban da
Abubakar wanda ke latsa wayarshi, a raina na ce,
"Mutumin nan fa har yanzu bai huce ba." Na dubi Yaya
Umar na ce, "Ina Baba da su Baaba?" Ya ce, "Suna nan...


Zaharaddeen Shomar
whatsapp 08168575100




Sanadin Boko 3-03
Posted by ANaM Dorayi on 09:35 PM, 27-Sep-15
Under: SANADIN BOKO
Ya ce, "Suna nan, Baba ne dai ba lafiya, ya fi shekara
baya fita." Idanuna suka ciko da kwalla na ce, "Allah ina
zaton halin da na saka su a ciki ne ya sa shi rashin
lafiya." Umar ya ce, "A'a lalura ce kawai." Na ce, "Ina
Ummi?" Ya ce, "Ummi ta yi tsawo, sai kin ganta." Na ce,
"Inna fa?" Ya ce, "Inna tana Funtua." Na tsura mishi ido,
"Me take yi a can? Ko suna da dangi ne?" Ya ce, "A'a,
tayi aure can da Yaranta ma 2." Nan take na dafe kirji,
kuka ya kuma kwace min na ce, "Ban yiwa Iyaye na
adalci ba, sun soni, sun min dukkan abinda iyaye kewa
dansu daidai karfi, amma ni sai na tarwatsa su." Yaya
Umar ya ce, "Komai mukaddarine kada ki damu." Tsaki
Abubakar yayi tare da tabe baki, ni dai na kauda kaina
gefe.
Likita ya shigo a nata 'yan hirarraki ya bani sallama.
Daga nan Sagir ya kwashemu mu 6 banda Abubakar, don
yace muje kawai, muka fice zuwa gidana.
Mama dama ita bata shiga ba gidansu ta wuce, sai ga
Shadad ya rugo da gudu, Mama ta ce mishi na dawo
shine ya taho. Mama tana barinshi gida ne saboda rigima
da yake yi a asibiti, ya fada jikina yana min oyoyo Aunty.
Umar ya zuba mishi ido, shi kam sai yanzu ya tuna fa
ashe da ciki na bar gida, ya ce, "Dan da kika haifa
kenan?"nace shine, sunansa shadad, idanuna suka soma
kawo ruwa, nace jeka gurin kawunka, yamike yaje gurin
umar, umar yace tabbas wannan dan munnir ne, kamarsu
ta baci, kinga ko dolensa ya amshi danshi, nace ai yaya
wlh baxan bashi yaron nanba, koshi ya bukata, inkuma
kunsan zakuce in kaishine tobazan koma gdaba, daganan
gabama zanci.... da sauri umar yace, toshikenan anbar
maganar, kusan karfe 1 har sagir da hashim sunyi mana
sallama, sai kuma gasu sun shigo da kayan abinci,
karamin buhun shinkafa ne da taliya, sagir ya mikoma
rahma kudi batare da yayi mata mgn ba, yafita. sannan
ya kirata a waya, wai tabani inji abbkr ne, amma tace inji
sagir, rahma kuwa tabani tace inji sagir, nace kaiba zan
amsaba kashe kudin yayi yawa, dubi kwanciyata a
asbitifa, tace a'a asbitinki ina ganin hashim ne, na amsa
tare da cewa, ko wanene ma dai nagode.Rahma ce
tadafa mana abinci mukaci, misalin karfe 3 yaya umar
yashirya tafia kd, nace yasakebi ta gidansu maman
rahma yayi mata godia, don tun bayan fitarsu sagir na
bashi labarin komai, tundaga tafiyata har iyanzu har
tsakanina da munnir ban boye masa komaiba, yacemin
yana ganin munnir shima a wata jibgegiyar mota lkc
zuwa lkc, yafadamin dukkanin abubuwan da suka faru
bayan barina gda, nayi kuka sosai, yace karna damu
komai yafaru da mumini daga Allah ne, kuma sakayya
tana nan tafe tsakanina da munnir, insha Allah sai kowa
yagane fyade ya miki, nidashi da rahma mukaje gdansu
mama inda yayi mata godia bisa godiya bisa rkon
datayimin, yayi addu'a ga likita hindu wadda tamin gata,
munayi masa rakiya saiga sagir da abbkr, yace da umar
yadan jirashi.suka shigo gurin rahma ashe sallama yayo
mata, suka kira umar gefe sukayi sallama dashi, sannan
abubakar yabashi kudi tare da tabbatar mishi da cewa
tsakanin gobe zuwa jibi iyayensa zasuzo, don haka
yasanar dasu, bansan mesuke tattaunawaba, yazo dai
yacemin zasu saukeshi a gareji, nace to saimunyi waya,
don nakarbi lambarshi, yasoma yakira inna muyi mgn
nace mishi a'a baxan iya mgn awayaba, washe gari naje
skul, ashe na danji sauki, kuma yanzun na rage kuncin
zucia kamar da, ina zaune ina krt wata baiwar Allah
tayimin sallama, nakalleta tanamin murmushi tare da
sallama, na amsa mata nima cikin sakin fuska, tace
nadaina ganinki kwana 2 lfy, naga kindan rame, nace
banda lfy ne, har na kwanta asbiti, taxauna tare da cewa
eyya, Allah yasauwake, saita danyi shiru daga baya kuma
tacemin sunana sa'adatu sulymn, kekumafa? nace
sunana hafsa, tacemin inaso muzama kawaye inba
damuwa, nace bakomai, mun danyi hira, sannan tatafi,
abinda yafi cizon raina yanzu a wane matsayi abk ya
ajiyeni? da nayi zaton yabarni har abada, amma sai gashi
yazo asbiti, duk dabaimin mgn ba, kuma naganshi a
layinmu yazo gidan mama yakira yaya umar, kenan har
yanzu yana sona? bari in isa gda in kirashi, ta gidan
rahma nabiya, ban boye mata komaiba abinda ke raina,
itama ta amince da cewa inkirashi mu gaisa na masa
godia, donfa gaskia shine ya nauki nauyin asbitinki, tace,
hatta jinin da aka karamin nashine yabada, amma baisan
cewa su sagir sun saniba, tace keko shinkafar nan da
kudin nan shine yakawo nace sagir ne don kada kiki
karba, bayan tayi shiru, sai kuma takara da cewa, abk
yana sonki, matsalar karuwancin dakika dorawa kankine,
kinsan maxa sunada kishi, kuma gaskia yana kishinki,
yakuma ki sauraron kowa cikinsu sagir bare suyi masa
bayanin danayi musu, nace, kinbasu lbr komai game dani
ne9 tace, sun bukaci nafada musu, shine kawai yaki
sauraro, na jinjina kai nace, toba ance shima bashida lfy
ba? tace eh, saidaya bada jini ko sallamarshi ba'ayiba,
wani sanyi naji cikin raina, jinin abk yana gauraye da
nawa? na sauke ajiyar zucia na kalli rahma, anjima zan
kirashi, to waima in nakira nace masa me? rahma tace
kirashi yanzun, nacije nace to bari nakira, nalatsa
lambarshi ta tafi, nace to rahma mexance masa ne don
Allah? wayar tasoma ringing, daidai lokacin yana zaune a
babban falonsu, yana tare da wasu daga cikin danginsa
sunzo dubashi, aciki harda fadima, ya kalli number dake
jikin wayar, tamkar yashare, amma saiya kasa, don
lokacin ma itace azuciyasa, ya amsa sallama ta bayan
ya daga wayar, na kalli rahma mexance? ( amma da
hannu nayi mata alama) ta harareni, ku gaisa mana, ta
fada a hankali, nace ina yini, ka isa gda lfy? ba zato naji
yaja tsaki, sannan yakashe wayar, na dubi rahma nace,
tsaki yaja sannan yakashe, tace duk kece kika jama
kanki, yaxa'ayi ki dora ma kanki halin daba nakiba? nace
magana zarar bunu, na riga nafada ta fito bamai iya
maidata, wasu zafafan hawayen son abk tsantsa suka
soma sulalomin, ina sonshi rahma, idan yabarni dakyar in
zan moru, bansan hakaba sai bayan dana furta kalmar
datajamin tsana a gurinsa, tace kidaina kuka, duk abinda
yasamu bawa daga Allah ne, kuma abk yana sonki, na
tabbata zai aureki, na sauke ajiyar zucia tare da share
hwy, koba gaskebane zancenki nadanji sanyi, kitayani da
addu'a, rahma tace, tuni nake tayaki, nace ngd, Allah
yabar zumunci, bari inje in dauko shadad in wuce gda,
nasan yana jirana, tace to saimunyi waya, na daukoshi
sannan na nufi gda, raina cunkushe, kunnuwana basu
daina amsa kuwwar tsakin da abk sadiq yaminba, duk da
tsananin son danake masa amma baxan juri wulakanciba,
ban taba tunanin wata rana zatazo da namiji zaimin
hakaba, domin banmayi tunanin cewa zan kalli namiji a
matsayin mutum ba, tun bayan abinda munnir yayimin,
ina yan aikace aikacena, lkc zuwa lkc inajan tsaki sbd
abinda abk sdq din yayimin, dakuma tunanin cewa
nidashi mun rabu kenan?
Sallamar mamansu Rahma naji nafito daga kitchen ina
amsawa turus na tsaya na tsaya ina kallon matar da
suke tare, itace ko kuwa dai mafarki ne? bakina ya
furta Inna! sai kuma na juya daki da gudu na zauna
ragwaf,na kifa kaina cikin cinyata, kuka na saki wanda
ya farkar da shadad daga bacci Mama tace ji wani
sakarci shigo daga ciki" ta umarci inna,inna ta shigo ta
zauna itama ta zauna shadad ya taso yazo ya dafa
bayana yana son yayi kuka yana cewa Anty wanene ya
dukeki? mama tace kyale wannan antyn taka mai kukan
tsiya harsai an doketa? mama ta ci gaba to wannan
kukan na menene? inna tace na rashin son gani nane,
don haka ma yanzun zan tafi Da sauri na fada kanta ina
cewa inna ki yafeni inna ban kyauta miki ba, inna na
tuba natuba" inna kawai sai tasa kuka, mama tace
haba maman hfsa, yaya kuma zaki taya ta?Da kyar ta
lallashe mu. Na kasa hada ido da inna,duk da dadin da
naji na ganinta. shadad na zaune a cinyarta, muryata a
dusashe nace "yaya umar ne ya kawoki? tace ehh shine
amma ya juya sbd suna da bakin da zasuje kd din
gobe. Lkcn da muka zo kina mkrnta, shine yace bari ya
kaini gdan maman taku" Na sauke a jiyar zucia, ina su
kawu?tace kowa lpia. ina nan ina malumfashi kika ki
nemanmu shekara da shekaru? Ina cikin bakin cikin
kunan rai yanda kika gudu yafi bata min rai abisa cikin
da kikayi. abinda ya kona min rai dake kenan Allah
yasani hfsa banso kika guje min baNace inna bazan iya
hada ido dake bane abnda kike min fada akanshi kullum
na kiyaye ban kiyayeba. Amma wlh ba da gangan na
aikataba munir fyade yamin ta karfi inna " inna tace
umar ya fada min komai,Allah zai fidda ke ta shafa kan
shadad Allah yayi maka Albarka ya tsareka da hali irin
na munir, shi kuma Allah shine yasan yadda zaiyi da
shi, mama tace komai dama mukaddari ne ga bawa
Allah ya shige mana gaba. sannan game da yaron nan
mai sonta kuyi mata fada,dan mutuncine tayi auranta
tare da yin karatunta adakinta. Aure da haihuwa basa
hana neman ilmi, yanzun baga rahma ba! da bamu bata
goyon bayan taci gaba da karatu ba Amma yanxun da
tayi aure mijin yace shifa matarsa fa makrnta zata
koma, Nace dama rahma nason karatu gashi ta samu"
mama dai ta tafi gda ta barmu. ranar kwana mukayi
hira nida inna hirar bayan rabuwa, munyi kuka mun gaji.
Da safe muka je makaranta nida shadad muka bar
inna,duk wanda ke makarantarmu yau yasan ina cikin
farin ciki, shi kuwa Abbkr lkcn dana kira dinnan ya min
tsaki, yana kashewa ya mike ya nufi dakinsa ya kira
umar suka gaisa. yace, umar don Allah idan iyayenmu
sun zo gobe kada ka bar wata baraka da zata nuna
cewa yarinyar nan ba a gda take ba" umar yace To
insha Allahu ba wata matsala yace sannan ku amshesu
da karamci suna son haka" umar yace insha Allahu,
haka nan da dare suna tare da hashim yana sake fada
masa cewa "Don Allah in sunje kada ya bada wata kofa
da Za a gano yarinyar nan ciki tayi" hashim yace Haba
nawa, Insha Allahu komai zai zo da sauki, ka kwantar
da hnkalinka, babu wanda zai fahimci komai, Tunda
yaya umar ya dawo daga kano ya sanar da baba zuwan
baki, don haka baba yace ya kira masa Amininsa
Malam garba da malam mamman. suna zuwa ya shaida
musu komai,suka ce To insha Allah goben bazasuyi
nisa ba, sannan sukayi masa murna da dawowar yar'sa
HAFsat.Sun shawarta a amshi bakin A shagon gdan
malam garba ,don yana da girma,don haka tun ranar
yasa ya'yansa su gyara shi,umar kuwa kaji ya siyo da
cefane akayi sa'a matarsa murja tana 'yan karance2
ltattafai don haka taiya grki. ya siyo lemuka kaloli aka
zuba a ckin frdge.tun safe Babah ta kimtsa
baba,yanxun ma yakan dan kokarta wanka da kanshi
tun baya n da akaga hafsa ta fito masa da kayan sallar
da umaryayi masa lkcn yana cikin ciwo bai sasu ba, yar
ciki da malum malum yasaka an shimfida manya
manyan tabarmi. umar yakawo chines carpetdinshi aka
shimfida. Babah kuwa harda turaren wuta ta zuba a
kasko tace akai shagon da za a sauki baki,Tun asubahi
Abbkr ya rbuta txt ga baffa sa'adu, bayan gaisuwa ta
girmamawa yace"Baffa ina fatan zakuyi hkri da yanda
zaku samu gdansu hafsa, ina nufin talakawane.Da
fatan wannan ba zai zama matsala ba,ka yafeni innayi
rashn kunya" murmushi baffa yayi lkcn da ya karanta
sakon,yayi kiran layin Abbkr. ckin grmamawa ya dauka
tare da gaishe shi ,Baffa yace "Hamma kada ka samu
damuwa, talaka da mai kudi duk dayane a gurn Allah,in
talaka yafi mai kudi tsoransa ma to yafi mAi kudi
agurinsa, Lura da cewa kudi ba komai bane face
jarabta,duk da mafi rnjaye cikin zurarmu masu kudine
amma muna da talakawan,so kada kadamu" Abbkr
yace, Na gode BaffA Allah yakai ku lpia ya dawo da ku
lpia" shi kuma yace ameen, shi yasa yake son baffa sa
adu akwai saukin kai ba irinsu Baffa magajiba. Hashim
yazosunyi sallama a inda ya sake sanar da shi
damuwarsa, bayason suji cewa tayi ciki, ko ta bar
gda,Hashim yace kada ka damu" tun da suka tafi yake
cike da fargaba,tafiyarmaitsawo ce tsakanin yola zuwa
kd. duk da sammakon da suka doka sai kusan mmagrb
suka iso, don haka baFfa sa'adu yace da hashim bari
ya kira amininsa dake zaune kd don su sauka gurinsa.
washe gari sai su shiga gdan da suka zo,Hashim yace
to. A nan take baffa ya kira abokinsa, basu samu
matsalaba don yace gashi nan zai zo ya taho dasu da
kansa. direba ya jawo shi har zuwa by-pass,shi ne ya
gano su dai dai inda yace su tsaya. baffa da abokinsa
sunyi murna da ganin juna,don sunfi shekara goma
basu hadu ba sai dai waya sbd yanayin aikin
kowannensu, Tare suka yi karatu a jami'a (ABU) a gdan
shi da ke makarfi road ya saukesu a sashin baki, umar
ya kira HAshim yace to "to yanzu ya zamuyi da
abincinku? ko ka sanar daniunguwar da kuke sai na
kawo maku"Hashim yace makarfi road dai naji ance
amma bari in tmbyi yaran gda ya fada wa su baffa sai
baffa yace.To ba laifi, in ankawo din dama su nan ba
su san da zuwanmu ba,Baffa ya sanar da abokinsa sai
yace haba dai su barshi yanzunnan za

Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3Chapter 4Chapter 5

Please Login or Register in order to submit comment