Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register


Downloaded from GNOVELS.COM.NG




This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG
to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/gnovels

Twitter : https://twitter.com/gnovels

Telegram : https://t.me/gnovels

BAƘIN SHAFI


oumyasmeen


HILUX aguje suke shigowa layin Alhaji Hussain me tangaran da kuma mayan motoci a babban masallacin da ke gidan za a iya daurin auren jikokinsa har guda biyu tuni kusoshin gwamnati sun cika maƙil da kuma attajirai cikin masallaci kuwa wani ne ya matso kusa da mahaifin sabeer kai mahaifin sabeer jin jina kai yayi ya dubi waliyin amarya yace


'' a dakatar da daurin auren nan na fasa..,


da sauri uncle Yusuf ya ɗago da tsoho me ran ƙarfe Alhaji Hussain me tangaran da kyar ya iya haɗeye yawun baƙin sa wanda yayi mai ɗaci yace


'' me ya faru...?,


tashi yayi ya dubi sabeer yana cewa tashi mu tafi mun fasa ashe damar yar su bata da uba sannan yar iskace shine soyayya ta rufe maka ido zaka dauko mana abin magana a family din mu tashi yayi haka yan uwansa suka fara zarewa da dadde dadadde gumi ne ya shiga karyowa yan uwan nasreen da kyar daddy yace


'' baffa ya zamu yi tun da nake ɓan taɓa ganin tozarci irin na yau ba..,


ran baffa ya ɓaci iya ɓaci idanuwansa yayi yaja yace


''komai aka faɗa mata ita ta jawa kan ta bani da ikon hana mutane abin da za su faɗi amma idan har khadijatou bata gyara halinta ba wallahi zan zartar da hukunci da ba zai mata dadi ba karo na biyar a fasa auren ki amma ba zaki hankali ba ...,
baffa hakuri za a yi


cikin cije leɓe yace


...a daura na ALTAB ba wanda aka sanarwa nan take aka daura auren ALTAB da rufaida akan sadaki dubu dari biyu nan da nan basu shela suka fara




Cikin gida kuwa har labari ya isa kunnen nasreen zubewa tayi a ƙasa hawaye na bin fuskarta babban takaicin ta shi ne sai Da komai ya zo ƙarshe yayi mata wannan cin mutuncin ina ma ya bari a daura ko wata ɗaya tayi karo fa na biyar da fasa auren ta ko wanne daga an kawo kuɗi Sai abin ya rushe amma wannan fa ranar daurin aure aka fasa me wannan shegen zai ce tashi tayi


ta goge hawayenta gyara fuskarta ta shiga yi adda asma ce ta shigo tace




''nasreen ya na ganki haƙa...?,


juyowa tayi tana murmushi wanda ya fi kuka ciwo tace


'' adda asma meke nan ban fahimce ki ba...,


shigowa ta kara yi tace


'' an fasa daurin auren ki amma kina cikin kwanciyar hankali ga su abban Sultan nan duk ransu a ɓace Please nasreen ki canja halinki ke ce kaɗai da muwar wannan family din namu...,


ranta ne ya ɓaci ta ɗaga mata hannu tana cewa adda asma ina mutunta ki da ganin darajar ki wallahi idan baki kiyaye kalaman ki ba zan cire duk abin da nake ganin ki dashi nayi miki ba dad'i duk wanda zai damu barin ni ce sau fa biyar to s kuke na mutu anyi na farko na suma har da kwanciya a asibiti na biyu iya suma nayi na uku na rame na fita hayyacina na hudu na damu har hakan ya sakani na dinga cuta na biyar kenan so kuke na mutu


to ba ai wannan namjin nan ba wallahi dan haka ga hanya nan


kama haɓa tayi ta fita wallahi gwara da kikai musi haka dame zaki ji


Please humy ki fita ina buƙatar hutu idan an jima tayi mu haɗu a club




sakar baki tayi ta ɗauki jakarta tace


''ni kike kora...,


a fusace tace


''ki ɗauka haka ne zo ki fita ƙiiii ta jata kaciɓis sukai da abokanan Altab suna shigowa sun ci babbar riga haɗiye wani yawu tayi me kauri garin irin kallon da ya jefe ta dashi mazaiwa tayi cikin iya barikanci tace




''sannun ku da zuwa ya hidima..,


mamakine ya ishe shi be taɓa zaton shedancin yarinyar nan ba ya kai haka yau a fasa auren ki kuma ga tanan normal har tana da kwarin gwuiwar shiga mutane


Alhamdullah haka suka ce ido ya mujaheed ya kora mata murmushi ta sakar mai shima martani ya sakar mata ya matsa kusa da ita hannunsa ta kama idanuwanta suka ciko da kwalla ƙasa ta tayi da ido tace




'' blood line kaga abin da sabeer yayi min...,


kama hannun ta yayi suka matsa duk abin da ke faruwa altab ya na lura da komai be san me khalil zai yi da wannan yar iskar yarinyar ba zama sukai a guarding tace




'' ko zaka iya faɗamin dalilin da yasa ka sabeer ya fasa aure na ko dai akan magana ɗaya ce da na sani da...,




NASREEN bazan ɓoye miki ba akan dayan ne amma yace wai yar iska ce dafe kanta tayi kallon hannun ta yayi da yaci uban farata har da tattoo bayan kunshiin da tayi innalillahi kinga ko wallahi idan har ba zaki canza dabi'un ki ba to kina tare da kalubale kala kala daga yau sai yau kar na ƙara jin kin tafi club dole ki canza idan har kina neman miji na gari...,


ya khalil dame zanji kanaga yau tace zata dawo daga cairo amma me ta dawo a gaban ta na haɗata da Allah akan daurin aurena ka ɗai idan ta halarta ta gama yi min komai amma me tazo ya khalil dame zanji kowa laifina yake gani sannan maganar barin kawayena Please mubar maganar nan idan shawara kake bani to tayani da addu'a fakat ta faɗa tana tashi sakar baki yayi yana fatan Allah ya shirye ta


sosai yan biki ake gutsiri tsoma musamman ma ɓangaren amarya rufaida ta taji wannan labari har rawa ta taka basa ga muciji da nasreen saboda a komai tayi mata fintinkau ko ina nasreen hakan ba karamin dad'i yayi mata ba yanzu dole ta ajiye wannan shegen girman kan nata


da yammaci kowa ya fara shirye-shiryen tafiya dinner idan dangin mai tangaran da na rufaida kowa zai halarci dinner nan


a bangaren nasreen shirin fita take taci uwar doguwar riga fitted gown peach colour da adon stone white colour da blue sosai rigar take kwallil ha wani uban kamshi da take bazawa Kai kace ɓarin turare akai daman ko ɗaya bata dinka lefenta ba tana da shago a zooroad komai order tayi ban da na abbanta da ya bata necklace ta saka irin me tsayawa a makoshin nan tuni tattoo din da tayi a huyanta ya fito daura veils tayi blue Black sannan ta ƙara fashe jikinta da turare kiran sallar magariba da kai ta ɗan dakata ta zauna jakarta ta dauka da wayar ta ta kunna sakon sabeer taci karo da su har guda bakwai ba tare da ta duba ba ta goge su ajiye wayar tayi ta zuba ta gumi wayar ta ce tayi ringing alamun shigowar sako dubawa tayi ta kurawa sakon ido tsaki ta ja kamar ba zata duba ba sai ta duba ga abin da aka ce mata


Assalamu alaiki kiyi hakuri aiki yayi min yawa so bani da time din da zan zo kano ina taya ki murnar auren ki


tsaki ta ja ta goge ji tayi kamar ta jefar da wayar saboda takaici ganin an idar da salla ta saɓa jakarta ta fito ba kowa a floor a farfajiyar gidan ce ta haɗu da mutane ana ƙoƙarin tafiya dinner kowa sai kallonta yake ko a jikinta gurɗewa tayi da yake hil ta saka ga kallon mutane tsaki tayi ta gyara tafiyar ta danna remote tayi motar ta ta buɗe shiga tayi ta yi mata key a hankali ta fara tafiya horn tayi me gadi ya buɗe mata ai kuwa a guje ta fita har tada kora take tafiya take da gudu har ta isa kan titi sannan ta dena gudun da take




ta fara tafiya a hankali zuciyar'ta duk ba dadi idan tace abin nan be taɓata ba tayi karya sai ta nutsuwarta tayi gudun samin matsala wayar ta ce tayi ringing ganin me kiran gabanta ya waɗi parking tayi a bakin titi ta ɗaga kiran tace


''assalamu alaika baffa barka da dare...,


Khadijah duk ida kika tafi ki dawo aje gurin dinner din nan da ke


gumi ne ya wanke ta tace


'' bani da get pass...,


kije altab ya baki yana faɗar haka ya kashe wayar sanin shi din magana ɗaya yake jikinta yayi sanyi ta juya zuciyar'ta na mata soya har ta isa gida bata dena mita ba a waje tayi parking ta fito kai tsaye shashin altab ta nufa wanda kaf duniya ta tsane shi bata kaunar ganinsa ba tayi wahalar knocking ba a bude yake tana iya jiyo muryar abokanan sa shiga tayi bakin ta dauke da sallama


amsa mata suka wayar ta ce tayu ƙara daidai fitowar altab sanye da ash din shadda tayi bala'in amsar sa ɗagawa tayi ta ƙara a kunne tace


'' jazz gani nan zuwa amma bazan dade ba kuyi duk abin da ya dace...,bata jira me zai ce ba ta kashe wayar altab nunawa yayi kamar be ganta ba ya dauke kansa yace




'' rufa'i kamar lokaci yayi ko..,


eh wallahi amma sai munyi isha ma je mu dauko ta


okay gurin ka nazo


wani kallo yayi mata ya buɗe baki zai magana ta tari numfashin sa tace


''yanzu ba lokacin sa'insa bace ka adana ta a kwai ranar ta bayin kaina ne ya kawo ni nan ba girgiza kai tayi ta kalli gefen ta ganin yadda suka tsura mata ido kallon su yayi ƙasa ƙasa yana cewa


ke yanzu baki ji kunya ba kalli tufar da ke jikin ki ko da yake duk inda dan iska yake bashi da kunya ba abin da ba zai iya aikatawa ba sannan wallahi kijin na rantsai miki ko tuba kikai idan har ba zaki canza halin ki ba ba me auren ki mace me daraja da rufe jikinta ake kai aura ban da ƙaruwar da take banzatar da jikin ta ko wanne dan iska ya zo ya taɓa...




🤔 🤔


BAƘIN SHAFI


oum yasmeen


EPISODE 2


Mayafinta ne ya zame daga kanta da sauri ya kalli wuyan'ta yaga star ta tattoo jinjina kai yayi ransa duk a ɓace yace


'' fice min daga daki tunka fin nayi miki ba dad'i...,


da sauri ta ɗago kaf duniya bata da maƙiyi sama da Altab kallo ɗaya zakai wa fuskarta kaga tsagwaran tsana da yayi mata me yayi zafi kuma dada ce wa take tana yarinya ya bauta mata amma yanzu fa ba wanda ya tsana sama da ita wayar ta ce ta ƙara ringing da sauri ta kalli screen ɗin wayar sai neman agaji take ganin sunan humy chairlady ɗagawa tayi tare da barin gurin ,


zama yayi ya saki gauran numfashi gaskiya abin da kai be dace ba ya zaku haɗa mata biyu dan dai tana da dakakkiyar zuciya ce da tuni wallahi wani zancen ake ba wannan ba..


Rufa'i ya faɗa ransa a ɓace


a'zafafe altab ya ɗago yace


'' mene abin daga hankali akan yarinyar nan ba ita ta siyawa kanta ba mutum shi yake saiwa kansa da kansa daraja shekaran jiya ba a hotel muka ganta ba munje kamawa baƙin mu da za su zo ita da ƙawayenta nifa wallahi na tsani yar iskar yarinyar nan gani yayi ba zai iya zama da ita ba shi ya saka yace ya fasa...,


toshe kunnan ta tayi wayar ta ta waɗi species ko wanne ɓangare yayi nasa guri tuni idonta ya ƙada yayi ja abin ka da farar fata ɗurƙusawa tayi ta ɗauki layinta da sauran species din wayar ta fita tayi ta bugo mai kofar zuciyar ta duk a jagule zama tayi akan fafaren kujerun da ya zuba su a farfajiyar shashin nasa zuba tagumi tayi tun da take bata taɓa ganin cin mutunci irin na yau ba amma ba komai duk iyayenta ne sula zata zama abin da suke zargi sai a faɗa da hujja




da wannan tunani ta tashi ta bar gurin dakin ta , ta shiga lokacin ba kowa sun tafi dinner kwanciya tayi ba tare da ta cire komai ba duniyar na juya mata kallon species din wayar ta tayi ta ja tsaki


bacci ne ya kwashe ta ba tare da taci re komai ba


Wannan kenan


sosai guri ya ci ka dam ƙam da abokanan arziki rufaida sai murmushi take baki yaƙi rufewa sosai adda asma ke baza ido ko zata ga nasreen amma ba ita ba alamar ta kardai fa ta jawa kanta daman baffa ciki yake da ita shiru tayi tana tunani ji tayi an taɓa ta da sauri ta juyo dan murmushin karfin hali tayi tace


'' zeena har kun zo...?,


eh wallahi daman tun ɗazu nake neman ki ya taro


zama tayi akan kujera zeena ta ja itama ta zauna adda asma tace


'' wallahi alhamdulillah...,


haka abu kuma ya zama abin gaskiya be mun dadi ba na tausayawa nasreeen yawa wacce aka saka mata hannu yan iskan nawa ne suke auro wa


shiru adda asma tayi tana danna wayar ta ba tare da ta tofa komai ba tasan halin zeena tas ta iya munafurci sannan aminiyar umman yaya ce


uhmm nace ba


ɗagowa tayi tace


'' Please bana son wannan zancen kama yayi muyu addu'a koma mene Allah ya kawo karshen abin idan kuma da wanda ya saka mata hannu insha Allahu dan sa zata aura..,


uhmm Allah ya kyauta


amin ya Allah


Sai ƙarfe ɗaya taro ya watsai kowa ya ɗauki motarsa ya tafi gida lokacin nasreen ta farka jin hayaniyar mutane tashi tayi tana ya tsuna fuska shaf ta manta da zata je club dafa kanta tayi gashi ba waya a hannun ta dole gobe ta je ta siya waya ,


tashi tayi ta cire kayanta ta saka na bacci ta koma ta kwanta ji tayi an turo kofar ta kunna bedside blam tashi tayi tace


'' lafiya kuka shi go min daki...?,


aunty nasreen gurin yayi kaɗan har guestrooms sun cika shine dada tace muzo dakin ki


wata uwar harara ta zabga mata tace


'' to ba guri maza ku fitar min daga daki ina za ku zauna a nan..?,


ke yanzu nan dakin har abin alfaharin kine wai yau she zaki hankali ne..?,


ya jero mata tambayar ajere tashi zaune tayi ta yaye blanket din da ta rufe jikinta da shi dafe kanta tayi ta cusa hannu wanta cikin gashinta tace


'' ku fitar min daga daki saboda tsabar raini a ina zaku kwanta ni bana son matsuwa...,


amma kin iya
da sauri ta ɗaga mai hannu tace


'' kana faɗamin magana iya son ranka narantsai da Allah ka jirayi sakamako zo ku fitar min da ga daki bawai tsoranka nake ji ba altab kaddara ce bata wuce faɗawa kan ka ba idan ba zakai wa mutum fatan shiriya ba be kamata ka dinga jefan shi da mugayen kalamai ba wallahi wata ran sai kai dana sani mara amfani zo ku wuce ku barmin daki kowa da inda ya tashi da shi yake alfahari...,


kallon su basma yayi yace


'' ku jira ni a waje....,


sum sum suka bar gurin suna mamakin nasreen da bata jin tsoransa kowa na gidan tsoransa yake ji musamman ma yaran gidan da yake shi ne babban jika a gidan takowa yayi har ida take tsaye ya zura hannuwansa a aljihu yana jefa mata wanni irin kallo me cike da fassara kala kala


danne tsoransa da yake shiga zuciyar ta tayi musamman ma da taga iya kirjinsa ta tsaya dogo ne sosai amma kibar sa ta shanye tsayinsa bawai kiba sosai ba wacce zatai mai muni aa daidai da kirar jikinsa cikin dar dar tace


'' malam fuce min daga daki...,


shiru yayi mata ba amsa ratsawa tayi zata fita ta bar mai dakin ya riƙo mata hannu fisgewa tayi tana cewa bana bukatar ganin ka nace maka ka fitar min daga daki wannan wacce irin kaddara ce ba za a bar zuciyar mutum ta huta ba daga wannan sai wannan


ba ruwan Ubangiji ke kika saka kan ki a ciki


zama tayi a ƙafa tayi shiru zuciyar ta na tsananin bugawa daguwa tayi taga ya fita jan tsaki tayi ta rufe kofar ta dakyar ta samu tayi bacci


washegari wanka tayi ta shirya cikin riga da wando amma wandon falazo ne Golding colour da riga milk colour stocking dinta gashi wuyan rigar
up-shoulder ne ko yaya tayi motsi ana iya hango kirjinta ɗaukan jakarta tayi ta riƙe a hannu ta yafa mayafi a kafaɗa takalmin kafar ta hil ne shafa kanta tayi shaf ta manta da wula kawai sai ta saka mayafin ta a ka tafiya take tana taku dai-dai har ta fito Parlour kallon rashin fahimta dada take mata tace


'' Khadijah sai ina kuma...?,


kallon a gogon hannun ta tayi tace


'' zooroad...,


ban gane zaki tafi zooroad ba


dafe kanta tayi tace


'' ya Allah dada zanje na bude shagona fa..,


gutsurar tufa tayi tana ci tace


'' Allah ya shirye ki haka kurum kin zamar da kanki na miji in banda zamani ina mace ina buɗe shago ta zauna...,
ɗago wa za tayi suka haɗa ido da altab yana cin wainar shinkafa da miyar a gushi kau da kanta tayi daga shi har rufa'i wallahi ba wanda zata gaisar tace


'' Dada ba laifi bane mace ta nemi halak ɗin ta kinga Allah ya sakamin albarka na har shagon saloon na bude...tun ina yin online na buɗe shago..,


wallahi kuwa da ace miki zaune gari banza gwara ki nemi abin yi cewar rufa'i


ya tsuna fuska tayi ɗagowa tayi jin sallamar blood line hugging din sa tayi tana cewa good morning blood line


morning beautiful lady


cika shi tayi yace


'' beauty me ya samu wayar ki ina ta kira a kashe..,


ta sami matsala yanzu ma wata zani na siyo kafin na buɗe shagona


a'a nasreen ina zuwa haka zuwa fa anjima za a kawo amarya cewar adda asma


murmushi tayi me cike da ma'anoni ta samu damar kuntatawa altab tace


'' yanzu aunty me ya hadani da kawo amarya na tafi neman arziki ko da yake duk neman da kake baya cire ka daga zargin mutane ba..,


hannunta khalil ya kama yace


'' muje na siya miki wata special gift happy birthday to you..,


zaro ido tayi shaf ta manta da yau birthday din ta tace


'' wallahi na manta abubuwan sun min yawa nagode sosai..,


idanuwanta duk ya ciko da kwalla karki damu aini ina sani ummi ma tace '' na taya ki murnar zagayowar ranar haihuwar ki...,


da sauri ta kallesa cikin mamaki tace '' anya kuwa...,


Wallahi da gaske nake kinga sakon da ta turomin


ture wayar tayi tace '' basai na gani ba da motar ka za mu tafi ko da tawa...?,


farin cikin ki shine nawa


murmushi tayi tace '' nima haka..,


fita sukai a tare suna hira adda asma ce tace




'' Allah sarki khalil komai yana yi domin ya kawar mata da damuwar ta..,


taɓe baki dada tayi tana cewa kinga alamun ta damu ne kike faɗar haka


dada abin fa zai mata ciwo wallahi kawai dai tana kawar wane dan ma duk tarin kawayenta ba wanda ta gayyata wasu ma basu san za ayi bikin ba...


Wannan shine rufin ashirin da Ubangiji yayi mata da fita ma sai ta gagareta dada ta faɗa cikin takaicin abin


addu'a nasreen take buƙata Allah ya kawo karshen abin nan


cewar adda asma


tabe baki altab yayi yana tashi binsa rufa'i yayi yace




'' dada sai anjima..,


kun gama cinye mata waina ai dole kuce zaku tafi


dariya rufa'i yayi yana cewa adda asma kenan kuɗi muka bata tayi mana tambaye ta idan karya muka yi


a'a abin harda sharri ni ko ficika ba su bani ba


Dada wane be san halin su ba sai addu'a


barin kar wannan mutumin yaji labari wallahi ni tausayawa yarinyar nan nake auran soja ba dad'i wallahi daman gashi ga halinsa


wallahi kuwa kawai dai Allah ya saɓa hali
cewar adda asma


Wannan kenan


wani shu'umin murmushi take saki tun ɗazu ko banza ta nuna mata ƙarfin ikon ta wace mata barno gabas ce kaɗan ta fara gani wallahi


mamy da sauri ta jiyo tace


'' basma lafiya kika shigo min ba ko sallama...,


wallahi nayi kece dai baki ji ba kina tunani


ajiyar zuciya ta sauke tace


'' to me kika zo yi...nan ..?,


wani ne yazo a baƙar mota yace '' na ƙira ki...,


cikin sauri tace '' okay na gane ce ne mai muyi magana ta waya..


har ta juya zata tafi da sauri tace '' mata tsaya kawai tafi na ki guri za mu yi magana ta waya


amma mamy wane shi...?,


basma bana hana ki irin wa'yannan tambayar ba maza maza zo ki wuce ki bani guri


fita basma tayi batare da tace komai ba wayar tace tayi ringing da sauri ta dauka tace


'' aminiya ta wallahi ban taɓa zaton wannan shirik namu zai yi ta siri ba sai gashi lokaci ɗaya mun burkita zuri'ar me tangaran...,


wata shu'umar dariya kawar tata tayi tace


''ai idan har zaki ci gaba da ɗaukar shawarata to wallahi kowa sai kin gyara masa zama...,


limshe ido tayi tace '' ai kuwa dana fi kowa murna wallahi...,


sallama sukai sannan ta kashe wayar shaf ta manta da batun me jiranta a waje


Wannan kenan


Cikin nishaɗi suka fito daga wajen saida waya tsayawa yayi yace


'' ni zan koma akwa wanda zamu haɗu dashi anan ga shi can yana jirana...,


langwaɓar da kai tayi tana cewa gaskiya naji dadi sosai wallahi Nagode Allah ya bar zuminci


amin ya Allah ya faɗa yanayin gaba buɗe motar ta tayi ta shiga a hankali ta fara tafiya har ta isa zooroad fito da mukulli tayi ta buɗe shagonta tana shiga jazz da shi da pretty suka shigo kallon su tayi tace




'' Allah ya rufa muku asiri baku daki gurbi ba ban dade da zama ba..,


zama sukai jazz tace


'' lallai kam jiya nai ta kiran wayar ki switch up me ya faru bayan mu gama tsara guri har 2:49 ina club...,


BAƘIN SHAFI


oum yasmeen


EPISODE 3

Previous to the last page


'' lallai kam jiya nai ta kiran wayar ki switch up me ya faru bayan mu gama tsara guri har 2:49 ina club...,


Continue


ajiyar zuciya ta sauke tace '' wayata ce ta lallace..,


fito da syrup pretty tayi ta buɗe tace '' Allah ya kiyaye gaba..,


amin ya Allah amma dan Allah kar ki sha ba zai yiwu ba customer's su zo min ba ana kallon ki ki ta tun ɓele..
haba nasreen ya kike mana yawa ne yanzu ni nake tunɓelen yawa wata akuya ko tinkiya


Pretty ta faɗa tana kai Syrup bakin ta tunda ta saka shi tas sai da ta shaye shi ta wurlar da kwalbar fashewa tayi da sauri nasreen tace


'' wallahi sai kin share min anya kuwa ina cikin nutsuwar ki..?,


ina fa take cikin nutsuwar ta sunyi faɗa da bash


Jazz ya fada yana dariya


tashi nasreeen tayi ta cire mayafinta tace '' ya kake mata dariya..yau dara fa ba dad'i wallahi tama yi kokari da ba faɗi ba an kwashe ta..,


Nasreen kenan ya ali yaga ali fa akai ya fito daga dakin hotel ta fito ina abatun damuwa shine fa har da marin budurwar indai takaice miki labari kaca kaca akai har sai da yan sanda suka shiga cikin lamarin yanzu bashi ba ita shine fa ta shiga cikin wani hali


to mene abin damuwa tunda ke kin aikata shima ya aikata ga ani na gaskiya ba abin daga hankali ko ki damu


baza ki gane ba wai mutumin nan fa yan sanda ya faɗa suyi mana tsakani da shi kin ji fa wani rainin hankali


tashi tayi ta zauna kusa da jazz ta kwashe da dariya shima dariyar yake yace


'' wallahi ban taɓa ganin original yan iska ba irin bash da pretty yau ya saba kai ta gurin yan sanda nifa gani nake kamar fa ya raina su wallahi..,


buɗe fridge tayi ta ɗauko lemoka ta miƙa musu itama ta buɗe tana cewa gaskiya nima ban taɓa ganin haka ba kar kai mamaki dan da wani watan su koma su jone

Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6

Please Login or Register in order to submit comment