Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

shi nayi a waya akan cewa in ba ya komai ya same ni a gida, akwai maganar da nake son mu tattauna dashi.

San da ya k’araso ne ya kira ni a waya yana waje.

Hijab na san a fito na wuce gurin Ummu na mata k’aryar cewa zan je gidan su Anisa in dawo yanzu.

fatan a dawo lafiya ta min kana tace in gaishe da su Anisa da Momi.

Ina fitowa na shiga motar nace mai ya tuk’a motar mu bar layin.

Kallo na yayi da alamar tambaya, amma ganin yanayin da nake ciki yasa bai ce min komai ba ya ja motar mu ka bar layin.

Sai da naga mun bar layin mun shiga wani layin sannan na ce ya tsaya a nan.

Sai a lokacin naji zuciyata ta karye na fara kuka wanda nima ban san dalilin yin kukan nawa ba.

Bi na yake yi da kallo ganin yadda nake kuka bil hakk’i yace "Wai Zarah me yake faruwa ne kike wannan kukan, ki fito ki fad’a min me ke faruwa dake ne".

Cikin kuka nace "Sadik an kusa raba mu, za a sa almakashi a datse soyayyar da ke tsakanin mu, na kasa danne halin da nake ciki a yanzu, shi yasa na ga gwara in fito in fad’a maka halin da nake ciki a yanzu".

"Ban gane me kike nufi ba, wai waye zai raba mu?" ya tambaye ni.

"Sadik aure za a had’a ni da yaya Faruk, yanzu haka bikin bai fi saura wata biyu ba" Na k’arashe maganar cikin shashshek’ar kuka.

Wani irin takaici ne ya kama shi jin wai an kusa bikin ta da Faruk, ba ta fad’a mishi ba, sai da ta ga komai ya rinca’be sannan za ta fad’a mishi.

Shi yasa da tace mai Faruk d’in ya hana ta tsayawa zance yasa alamar question mark, yasan daman yana da dalilin yin haka, abin ta fi yi mishi ciwo a ranshi shine yadda a lokacin ya tambayeta ta nuna mishi ba wani abu dake tsakanin su.

Cikin fad’a yace "Yanzu Zarah da kike wannan kukan miye amfanin shi, bayan sai da kika bari komai ya gama ‘baci sannan za ki fad’a min, gashi har ana maganar biki, yanzu mai ki ke so in yi akai".

Cikin kuka nace "Dr dubarata ta k’are, plss ka samo mana mafita, wallahi in dai ba kai na aura ba zan shiga wani hali, lai zuciyata take so da muradi".

Ganin yadda take kuka yaji duk jikin shi yayi sanyi, shi kanshi yasan Fatima na son shi.

Cikin lallashi ya ce "Wipe your tears Zarah, ki ba ni hakalin ki muyi magana ta fahimta".

Ina jin haka nayi saurin share hawayen dake fito wa daga fuska ta, na maida hankali na gare shi.

"Zarah, kin yi kuskure da tun farko ba ki fad’a min me ke tsakanin ki da wannan yayan naki ba, duk yadda muke son junan mu, ba mu da wani power tun da har an yi fixing d’in bikin ku, ina ganin mafita a gare mu shine mu yi hak’uri da yadda k’addara tazo mana mu hak’ura da juna".

Wani irin kallo na mishi na alamar tambaya akan abin da yace.

Maganganun da Sadik ya fad’a sun k’ara sa ni a rud’ani ganin yadda yayi saurin mik’a wuya ga al’amarin, duk wani bijire wa da halin da nake ciki a yanzu duk akan shi ne, amma shi gashi a lokaci d’aya ya nuna ya hak’ura da ni.

"Ban fahimci inda maganganun ka suka nufa ba, kana nufin har ka hak’ura dani, bayan duk fad’i tashin da nake yi duk a kan ka ne, Dr kar ka sa in fara zargin ko ba so na kake yi ba" Na fad’a cikin fushi.

Cikin cool voice d’in shi da yake k’ara sace zuciya ta yace "try to understand me Zarah, maganar ba a son ki ma bai taso ba, ke kan ki kisan ina son ki, in har da ba na son ki, bazan tsaya ‘bata ma kaina time ba, kema kuma ba zan ‘bata miki lokacin ki ba, abin da yasa ki ka ga nace haka saboda na rasa wace hanya za mu bi mu shawo kan matsalar, yanzu gashi kin ce bai fi saura 2 month bikin ba".

Sai yanzu na ji sauki a raina ganin shima Sadik ya nuna damuwar shi akan maganar, nasan yanzu zan samu relief a raina.

Da haka muka ci gaba da tattaunawa akan matsalar, mun yi da Dr zai neme ni a waya mu samu mafita akan maganar.

Fitowar da zan yi naga motar yaya Faruk ta shigo layin, da alama daga wani gurin yake tun da har ya biyo wannan layin.

Shi kuwa yaya Faruk tun da ya ganni na fito a motar ya tabbatar da cewa tare muke da Dr.

Kusa da motar Dr yazo yayi parking.
Fitowa yayi daga cikin motar ya nufo inda nake, ni kuwa jiki na in banda rawa ba abin da yake yi, hakan da nayi ne yasa Dr ya lura da halin da nake ciki.

Shima fito wa yayi daga side d’in driver ya kulle motar.

Kallon kallo ake yi tsakanin yaya Faruk da Dr Sadik, da alama kowa da abin da yake sak’awa a zuciyar shi.

*MAKAUNIYAR SOYAYYA*💝💖💞


🤦🏽‍♀🤦🏽‍♀🤦🏽‍♀🤦🏽‍♀🤦🏽‍♀🤦🏽‍♀🤦🏽‍♀🤦🏽‍♀🤦🏽‍♀


*STORY & WRITTEN*


*BY*


*MARYAM AHMAD PAKI*




*🌈KAINUWA WRITERS ASSOCIATION*🤝🏽




*Wannan shafin sadaukar wa ce ga dukkan fans d’in Brigadier Faruk*
*Lallai Faruk ya ciri tuta a wannan littafin da yafi kowa samun mabiya, ni kaina Bregadier Faruk na burge ni, kuma fans d’in sauran jaruman ina mik’a gaisuwa ta a gare ku, wani shafin kuma zai zama sadaukar wa gare ku*

*Ina godiya ga dukkan d’aukacin masu bin wannan littafin*

*Allah ya bar mu tare*🤝🏽🤝🏽🤝🏽



_A wannan shafin nake sanar da makaranta wannan littafin cewa na tsayar da wannan littafin har sai bayan sallah in Allah ya kaimu saboda kusantowar azumi_

_Allah muke rok’o yasa mu fara azumin nan cikin kwanciyar hankali, ni’ima, lafiya da wadata_

_Ya Allah kasa muna daga cikin wad’an da z aka ba ma aron rai da za mu ga wannan watan mai alfarma, idan kuma kwanan mu ya k’are kasa mu cika da Imani_

_Allah kasa mu fara azumin nan lafiya, mu gama shi lafiya_




59&60

Yaya Faruk ne ya tako cikin takun k’asaita ya tawo gurin da nake, ni kuwa in ban da addu’a baa bin da nake yi a raina saboda ban san wani mataki zai d’auka a kaina ba.

Hannu na ya rik’e cikin d’aurewar fuska, yana min wani irin kallon da ni kaina bazan iya fassara shi ba.

Dr ne ya fara min wani hautsinannen kallo ganin hannu na a hannun yaya Faruk, hakan da na fahimta yasa na fara k’ok’arin k’wace hannu na amma ko alamar sake wa bai yi ba, ganin in na ci gaba da jan hannu n azan iya ja ma kaina ciwo yasa na hak’ura.

Direct motar shi ya nufa dani ya zaunar dani a kujera mai zaman banza sannan ya kulle motar.

Gurin motar Dr ya nufa wanda tun a lokacin da yaya Faruk ya rik’e hannu na yake kallo na.

Wani irin murmushi yaya Faruk yayi ya ci za gefen le’ben shi, kana ya kalli Dr da wani irin d’aurewar fuska ya ce "Dr Sadik ko?" ya tambaye shi.

Shiru Dr ya mishi bai bashi amsar tambayar da ya mishi ba, sai ma k’ara tamke fuskar shi da yayi.

Yaya Faruk bai damu da rashin amsawar shi ba, ci gaba da yayi da maganar shi.

"Warning nake so in maka, na ga alamar kamar ilimin addini bai gama wadatar ka ba, idan ba ka sani ba, ina so ka sani, ba kyau neman aure akan nema, hakan haramun ne kuma ya sa’ba ma addinin musulunci, ina so ka sani bikin mu da ita bai fi 2 month ba, ka fita harkar ta, idan kuma ka k’i… hmmmm" ya k’arashe maganar yana girgiza kai.

"Duk wannan maganganun da kake yi kana nufin zai sa in tsorata ne, ko in ja baya da neman Zarah, hakan bai girgiza ni ba, sai ma k’ara min k’arfin gwiwa da yayi, abin da nake tutiya dashi shine Zarah tawa ce, tun da ni take so, ka ga ni ke da power akan ta".

Jin wannan kalamen Dr yasa yaji wani irin ‘bacin rai ya ziyarce shi wanda yafi na da, yana ganin gwara ya koya ma Dr hankali yasan shi bat saran shi ba ne, don haka cikin fushi ya cakumo shi, Dr wanda ya ji hannun soja da kyar yake numfashi, har ya duk’ule hannun shi zai kai mishi naushi, ko me ya tuna ya sake shi ya bar gurin.

Dr kuwa tun da ya samu yaya Faruk ya sake shi, ya shiga motar shi ya ja ta da gudu ya bar unguwar.

Ni kuwa tun da na ga abin da yaya Faruk ya ma Dr, na ji kamar ni aka ma wa, tun da ni na janyo mishi hakan, kuka kawai na fara yi mai tsuma zuciya.

Yaya Faruk na shiga cikin motar ya ji sautin kuka na ya cika mishi kunne, duk da kukan na ta’ba mishi zuciya hakan ba zai hana ya hukunta ni ba, gani yake yi in ya bar ni haka zan k’ara ganin lagon shi ne in raina shi.

Wata irin juyowa yayi ya kalle ni da idon shi da ya canza launi, ya daka min wata irin tsawa da na ji kayan ciki na sun kad’a.

"Fatima fitar min daga mota kafin in illata ki" ya fad’a cikin tsawa.

Saboda tsoratar da nayi yasa na kasa bud’e k’ofar, sai rawa da jiki na yake yi.

Tsawar da ya k’ara min ce yasa na fara k’ok’arin bud’e motar ko ta wani hali, ni dai in samu in fita daga motar, a yanayin yaya Faruk, in akwai abin da yafi illatawa, nasan zai iya.

"Ki fita nace…" Ya k’arasa maganar yana buga hannun shi a sitiyarin motar.

Ai ni ban ma san yadda aka yi na bud’e ba, ji na kawai nayi na fad’o daga motar, ban damu da buguwar da nayi ba na mik’e na fara tafiya da sauri ba tare da na juyo na kalli inda yaya Faruk yake ba.

Haka na ci gaba da tafiya har na k’araso layin mu, jiki na kuwa sai ciwo yake min saboda fad’uwar da nayi lokacin da na bud’e motar.

Lokacin da na kai gate d’in gidan mu, tsayawa nayi na goge hawayen da ke fuska ta nayi, ba na son kowa ya fahimci halin da nake ciki.

Da yaya Khalil na had’u a gurin shak’atawa yana waya, gani na da yayi ne yasa ya katse wayar da yake yi tawo guri na.

Cikin tsokana yace "matar Soja daga ina kike ina ta neman ki".

Ban ce mai komai ba, nasan idan na bud’ e baki zan mishi magana, kuka ne zai fito.

Ido ya tsura min yana kallon yanayi na.

Hannu na ya kamo ya kai ni gurin shak’atawa ya zaunar dani akan jurera, shi ma kujerar dake kallo na ya zauna.

"Fatima me ya same ki na ga idon ki yayi ja".

"ciwo idon yake min".

"Fatima nasan akwai abin da yake damun ki, tun dawowa ta daga service na lura da kin canza, da kina fad’a min damuwar ki, amma yanzu ban san me yasa kike so ki ‘boya min ba, baki san in na gan ki a damuwa ba, nima ina shiga damuwa, ki daure ki fad’a min kin ji Auta".

Maimakon in fad’a mishi abin da ke damu na, sai ma kuka da na fara yi mai ban tausayi.

Da ina da hali da na fad’a ma yaya Khalil damuwa ta kamar yadda ya buk’ata, nasan shi zai ba ni shawarar da ta dace da ni, amma a yanzu ina ganin ba bu wani amfanin fad’a mai tun da har na bar maganar ta kawo wannan lokacin da komai yazo k’arshe.

Tun da na fara kukan yake kallo na, yadda ya lura ina da buk’atar yin kukan a yanayin da ya lura ina ciki, sai da ya bari na gama kukan sannan ya taso ya zo gun da nake.

Farin handkerchief d’in shi yasa yana goge min hawaye, a lokaci d’aya yana girgiza min kai alamar kar in ci gaba da kukan.

"Fatima wannan kukan da kika yi, shi ya tabbatar min da kina cikin damuwa, amma ba zan matsa miki ki fad’a min a yanzu ba, yanzu ki tafi d’akin ki huta, anjima zan zo in same ki muyi maganar".

Tashi nayi na bar gurin, yayin da yaya Khalil ya bi ni da kallo yana k’issima abubuwa da yawa a ranshi.

Yaya Khalil mik’e wa yayi ya shiga motar shi ya tafi gidan su Anisa.

San da ya isa gidan, bai shiga ciki ba, parking yayi a harabar gidan ya kira wayar ta ya sanar da ita zuwan shi..

Ba a fi mintuna 5 ba sai ga shi ta fito cikin shigar material kalar milk, ta yafa k’aramin gyale a kanta.

Da murmushi ta k’arasa side d’in kujera mai zaman banza tana murmushi.

Shima murmushin yake sakar mata yana ci gaba da kallon ta ganin kayan yanda suka amshi jikin ta.

"Sannu da zuwa yaya Khalil".

"Yawwa Anisa, sannun ki gimbiya ta".

Rufe ido tana dariya kana ta ce "kai yaya kana sa ni jin kunya".

Shima Dariya yayi yace "Au kunya ta kike ji, gwara ki daina wannan kunyar taki, dan b azan yarda da haka ba".

Sunkuyar da kai tayi tana ci gaba da murmushi.

Hira suka ci gaba da yi kafin ya canza akalar zancen da cewa "Anisa dama akwai tambayar nake so in miki, ina so ki ba ni gaskiyar amsar".

Mai da hankalin ta tayi gare shi tana sauraren shi.

"Anisa me kika fahimta a yanzu game da Fatima, nasan tana cikin damuwa amma in na tambaye ta sai tace min ba komai, ina son in kin san wani abu ga me da halin da take ciki, plsss ki fad’a min, nasan ba za ta rasa fad’a miki ba".

Ita kanta ba za ta iya cewa ga abin da yake damu na ba, tun da ban fito na fad’a mata ainihin matsalata ba, amma tasn duk wani halin da nake ciki, ba zai rasa nasaba akan magana ta da yaya Faruk ba, ba ta son a ce ta bakin ta za a ji komai, gwara ya gano me ke damuna da kanshi, don haka tace "gaskiya yaya Khalil ni ban san me yake damun Fatima ba, ni kaina na lura da canzawar ta, lura da nayi kamar ba ta son kowa yasan halin da take ciki, yasa nima ban matsa mata da tambaya ba, amma ni kaina ba na jin dad’in canzawar Fatima".

"Shi kenan Anisa, insha Allahu zan gano ko ma me yake damun ta, ba ri in k’arasa gida, sai mun yi waya, ki gaida Momi".

"Za taji, ka gaida Fatima da Ummu".

Motar yayi wa key, yayin da Anisa ke d’aga mishi hannu.

Yaya Faruk kuwa, tun san da na bar motar ya kwantar da kanshi a jikin sitiyari, wani irin zafi yake ji a k’irjin shi.

"Me yasa Fatima take son d’aura mishi damuwa da hayaniya, idan bai wasa ba zai iya kamuwa da wani ciwon duk a dalilin son Fatima, So ya zamar mishi babbar cuta a gare shi tunda wacce yake so ba ta damu da halin da zai shiga ba".

Sai da ya kusan kwashe mintuna 10 a gurin kafin ya ja motar ya nufi gida.

Yana shiga gidan ya wuce side d’in shi ba tare da ya shiga side d’in Momi ba.

Kwanciya yayi ya d’aga kan shi sama yana tunanin makomarshi a guri na, abin da yake k’ara d’aga mishi hankali bai wuce yadda bikin yake k’ara matsowa ba a lokaci d’aya kuma al’amura suna k’ara rinca’be wa.

Da yana ganin matsalar mai sauk’i ce, sai yanzu yake ganin abin ya wuce tunanin shi.

Yanzu wani mataki ya kamata ya d’auka? Wannan tunanin shi yafi mishi yawo a zuciyar shi.

Momi ce ta fito daga kitchen ta kalli Anisa da take faman buga game a wayar ta.

Kiran sunan ta Momi tayi ta amsa mata.

"Anisa yayan ki bai shigo ba, na ga motar shi ya dawo, nasan halin shi ba lallai ba ne in yaci abinci, d’auki food flask d’in nan ki kai mai".

"To Momi bari in je in kai mai".

San da ta shiga d’akin, samun shi tayi yayi zurfi a cikin tunani.

Tsayawa tayi tana kallon shi, yayin da wani irin tausayin shi yake k’ara mamaye zuciyar ta.

A hankali ta k’arasa kan center table ta ajiye food flas d’in kana ta wuce gurin shi.

Kusa dashi taje ta zauna tana kiran shi, amma ko alamar amsawa bai yi ba.

Ganin hakan ne yasa ta rik’o hannu shi.

D’ago kanshi yayi yana kallon ta.

Sanin ba zai mata magana ba a halin da yake ciki yasa tace "yaya Faruk me yake damun ka, plsss yaya Faruk ka fad’a min ko nima zan ji sanyi a raina". Ta k’arashe maganar hawaye na zuba a idon ta.

Yadda Anisa take damuwa da lumuran shi, yana ganin ba zai iya ‘boye mata komai ba.

Don haka yace "Fatima ce matsala ta".

Da sauri ta tare shi da cewa "Me ta maka yaya Faruk".

Zayyane mata komai yayi na abun da ya faru yanzu tsakanin shi da ni.

Wani irin haushi na ne ya kama Anisa, tana ganin lokaci yayi da ba za ta iya zuba ido yayan ta ya fad’a wani hali ba, za ta fito ta fad’a mata tasan me yake wakana.

"Yaya Faruk, ina ganin wannan maganar ya kamata a ce su Dadi sun san halin da ake ciki, ka ga bikin ku na matsowa, in ba an shawo kan matsalar da wuri ba, komai zai iya rinca’be wa, barin wannan maganar zai iya jawo maka wata damuwar".

"Kar ki damu Anisa, ni kaina ina tunain yin hakan, amma zan ci gaba da yin k’ok’ari na dan in ga komai ya zama normal, ba komai ba ne nake son in fad’a ma su Dadi su dinga ganin laifin Fatima, ina sa ran komai zai daidaita".

Anisa jinjina irin son da yaya Faruk yake min ta ke yi, tasan idan ya rasa ni zai iya shiga wani hali, fatan ta Allah yasa komai ya daidai ta.

Haka su ka ci gaba da tattaunawa akan matsalar.

Sai da ta tabbatar yaci abinci kafin ta mishi sallama ta bar d’akin.

Tana zuwa d’aki ta ga ba za ta iya jurar ganin halin da yaya Faruk yake ciki ba, shawara ta yanke akan taje ta nemi izinin zuwa gidan mu, tana ganin ta hakan ne za ta samu sassauci a yadda ta ke jin zuciyar ta.

Da zuwan ta, ta fad’a ma Momi tana son zuwan gidan mu, Momi ta ba ta izinin zuwa.

A lokacin da Anisa tazo gidan mu, ina d’aki na, ni kaina a lokacin ba zan ce ga abin da yake min dad’i.

Gaisawa da Ummu na ji suna yi kafin ta shigo d’aki na.

Da shigowarta ta nemi kujerar mirrow ta zauna tana kallo na.

Cikin murmushi na ce "Ashe manya ne a gidan namu, Anisa ya su Momi?".

"lfy lau" Ta ba ni amsa a tak’aice.

Lura da yadda ta ke kallo na da kuma yadda ta amsa min yasa na zargi ko akwai wata a k’asa.

"Fatima ina son mu yi wata magana da ke" Anisa ta fad’a.

"Ina jin ki" Na ba ta amsa.

Anisa cikin damuwa ta ce "Fatima ban ta’ba zaton hakan daga gare ki ba, tuntuni na lura da canzawar ki, ban san canzawar taki tana da alak’a da yaya Faruk ba, ban tsammaci za ki ‘boye min me ke tsakanin ki da yaya Faruk ba, Fatima yadda na d’auke ki, ashe ke ba haka ki ka d’auke ni ba, sai daga baya duk na samo amsar da nake buk’ata a gurin ki, shine kin min haka ne saboda kina ganin yaya Faruk d’an uwa na ne, zan goyi bayan shi, tabbas hakan ta ke a guri na, zan iya yin komai dan ganin yaya Faruk ya samu abin da yake buk’ata, ina gani ko da a ce yaya Faruk ba d’an uwan ki ba ne, ya ci a ce kin so shi saboda irin soyayyar da ya nu na miki na tsawon lokaci da ya d’auka yana rainon soyayyar ki, amma ke sai ki ka za’bi son zuciyar ki na ganin kin samu abin da kike so, ba tare da kin lura da halin da zai shiga ba, shawarar da zan ba ki shine yaya Faruk shi yafi dacewa dake ba Dr da kika d’aura ma so ba, wannan shawarar da nake baki ita, ina fad’a miki ne ba wai dan yaya Faruk yana matsayin d’an uwa na ne, sai don ina duba amincin da ke tsakanin mu dake, ko da yake nasan canzawar ki duk yana tattare ne da son da kike ma Dr, nasan za ki iya yin abin da yafi wanda ki ke yi, Dr shi ya janyo har ki ka canza, dan ni kaina nasan ba halin ki ba ne".

Duk da nasan abin da Anisa ta ke fad’a min gaskiya ne, yau da alama Anisa na kai ta k’arshe ne tun da ta fito tana fad’a min wannan maganar, kasancewar ta ba ta da fad’a, amma hakan ba zai sa in mata shiru ba ganin yadda take ba ma Dr laifi a maganar.

"Anisa ina ganin duk maganar da za ki yi, ki tsaya a iya kaina, Dr ba ruwan shi a wannan maganar, hasalima sai yau ne yasan me yake tsakani na da yaya Faruk".

Wani irin murmushin takaici tayi sannan ta ce "Ai ke ba za ki ga laifin shi ba, tun da kin yi nisa a son shi, duk yadda za a fad’a miki gaskiya ba d’auka za ki yi ba, dan haka bazan ga laifin ki ba, abin da nake so in tunasar dake, yaya Faruk kamar matsayin miji yake a gurin ki, tunda duk an yi abin da musulunci ya tanada, shaidu ne kad’ai ba su shaida ba, ya kamata ki san da haka".

Katse ta na yi da cewa "Ashe kin san ba a d’aura ba kenan, kin ga bai da damar hana ni kula Dr in ma shi ya turo ki".

Cikin ‘bacin rai Anisa ta ce "Yaya Faruk bai san zan zo nan gidan ba, bare har ya umarce ni da na zo na miki magana, ke kanki kin San Yaya Faruk ba zai aikata haka ba, ni da kaina na ga ya dace na zo".

"Anisa kar ki ga laifi na, ni kaina na rasa me yasa na kasa jin son yaya Faruk a raina, na san ya kuma cancanta da in so shi".

Wani irin kallo Anisa ta min kana ta ce "Son zuciya shi ya jawo miki haka, ba wai zuciyar ki ce mai laifin ba, Fatima ina guje miki ranar danasani a lokacin da ba ta da amfani a gare ki, Makauniyar Soyayya da ki ke ma Dr shi zai jawo miki hakan".

Kalamen Anisa sun min zafi, amma nasan ni ce mai laifi, ci gaba da tanka mata zai iya sa rai ya 'ba ci.

Ci gaba tayi da cewa "In har Yaya Faruk ya shiga wani hali, ke ce sila, da ma ai kin ta'ba fad'a min shi ba ya cikin tsarin Wanda kike so ki aura" Anisa ta k'arashe maganar tana mai zubar hawaye.

Kalamen ta sun sa jiki na yayi sanyi, nasan tun da ta fad'i hakan, ba zai rasa nasaba da halin da Yaya Faruk yake ciki a kaina.

Ba abin da ya dace da nayi a lokacin da ya wuce nima in zubar da hawayen ko na samu sassauci a halin da nake ciki a yanzu.

Duk wannan maganganun da suke yi Yaya Khalil yana bakin k'ofa yana jin me suke cewa, tun dawowar shi Ummu ta fad'a mai Anisa ta zo tana guri na, shi yasa ya taso ya tawo d'akin, wajen shiga d'akin ne yaji maganganun da Muke yi.


Ganin shi kawai muka yi a d'akin ya shigo yana min wani irin kallo da bai sa ba yi min irin shi ba.

Ganin irin kallon da yake min ne yasa jiki na ya k’ara sanyi, nasan yaya Khalil na ‘bata mishi rai, ba kasafai ka ke ganin ‘bacin ranshi ba, amma in ranshi ya ‘baci bai iya nuna fushin shi ba.

Anisa da ta lura da shigowar yaya Khalil yasa ta mike’ tana goge hawayen ta da niyyar tafiya.

Ta fara tafiya ne yaya Khalil ya kira ta cikin sanyin murya.

Juyowa tayi ta kalle shi kafin ta ci gaba da tafiya, da alamar ba za ta tsaya ta saurari mai zai ce mata ba.

Ci gaba yayi da kiran sunan ta, ko alamar juyowa ba tayi ba ta bar d’akin.

Shi kanshi yaya Khalil yasan yau Anisa ran ta ya ‘baci, kuma ko waye aka ma d’an

Please Login or Register in order to submit comment