Downloaded from GNOVELS.COM.NG This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG For feedback and support Facebook : https://facebook.com/gnovels Twitter : https://twitter.com/gnovels Telegram : https://t.me/gnovels [30/08, 3:45 pm] +234 906 084 2867: Cikin tsananin tsoro da mamaki. Maryam ta rumtse idanunta da azaban k'arfi tare da cewa. "Innalillahi waInna'ilaihirajiun. Zaleeha kashe kanki zakiyi baki da hankali ne?." sai kuma duk falon ya ricab'e sabida. Ihun da Zahira keyi tanayi tana tsalle da burburwa tare da cewa. "Shike nan ai an huta." Aunty Lubna kuwa da Ziyada ruggume juna sukayi tare da rumtse ida nunsu, Ganin yadda Zaleeha tasa knife d'in ta yanke wuyan hannunta tare da kurma ihu mai gigitarwa, tuni jini yaketa tsiyanyowa yana zubowa har k'asa. Cikin wani irin tsoro da al'ajabi da firgici ya Ahmad yayi sauri ya k'arasa gabanta, tare da sa hannu ya fizge knife d'in data saitashi kan jijiyar mak'ogoronta. Ihun Mama da Yayarta Ruda da Zahira ya cika gidan gaba d'aya. Mamy da Aunty Lubna da Ziyada ma kukan sukeyi mai cike da tsoron ganin Zaleeha zata aikata kisan kai. Ga kuma ihun da itama Zaleehan takeyi tanayi tana tsalle tana. "Wallahi zan kashe kaina! gwara in mutu kowa ya huta! In yaso in na mutu a raba gawata biyu a kai musu dukansu biyu kowa a bashi tsagi d'aya." Ya Ahmad kuwa hannunta data yanke yaketa kamowa dan ganin yadda jini ke zuba alamun ta yanke sosai. Baba Malam kuwa tun sanda yaga ta yanke kanta, ya juya ya bar wurin yana tafe jiri na fizgarshi sabida tsananin tashin hankali da b'acin rai. A gabanshi a gidan shi ƴarshi ke kirari da tutiyar kashe kanta, a kan mijin da itace tace ya turo iyayenshi. Gaba d'aya idanunshi basa gani, sabida wani fitinennen duhu daya mishi k'awanya kan kwayar idanunshi, babu abinda yakeyi sai sunan Allah yake ambato, Wai yau shi Malam Bashir Sulaiman Dukku shine za'ayi kisan kai a cikin gidanshi, kuma yarsa ce ta cikinsa, lallai fulani sunyi gsky da sukace, (Te'ud'o laddefu and'i dayan sabere) kowa ya auri daji tofa yasan tabbas wata rana zai haifi Saura/lampo. Jiki na rawa ya zauna dirsham a bakin gadonshi tare dasa hannu duka biyu ya tallabe kanshi kana yaci gaba da zancen zuci. "Eh tabbas yau dai yaga zahiri, ashe ba banzaba Fulani keda k'abilanci a fagen neman aure da bada aure, yau gashi yaga illa da kuma dafin gwamutsa zuriya, sabida ai dai kowa ya sani abinda d'iyarshi Zaleeha take inkarin zata aikata koma yace ta aikata kafurcine wanda addinin musulunci yayi tir dashi, kisan kai ko kashe kai al'adace ko d'abi'ace ta kafurai marasssa imani da tawakkali wanda basuyi imani da Allah da manzonsa ba, bare suyi imani da k'addara mai kyau ko akasin haka." Wani irin fitinennen kukane mai cushe zuciya da numfashi ya kwabcewa dottijon nan mai cikar haiba da kamala, mik'ewa yayi cikin tsananin kuka ya d'auki yar karamar jaka, Qur'an da wasu littafan ya saka a ciki, sannan yasa ATM nashi da carbinshi kana ya d'auki car key d'inshi. A hankali ya nufi cikin gidan inda yake jiyo ife-ifen na k'ara tsananta, Dib-dib-dib haka zuciyarshi ke bugawa da tsananin k'arfi da firgita Kardai ta kashe kan nata ne?. Yana isa ya samesu gaba d'aya suna tsaye a tsakar gidan, sai Zaleeha daketa kwaso akwatunan da yan uwan Abdussalam suka kawo tana ta watsosu tsakar gida, gaba d'aya tayi kaca-kaca da komai ta birkice ta zama kamar mai shafar al'janu. Ya Ahmad ne keta kamota tana zillewa duk ta birkice gashin kanta yayi biji-biji ya hargize ta zama kamar zarerriya Wani k'aton akwati ta jawo wanda wlhi ko maza zai sunyi da gaske zasu jawoshi sai gashi ta figoshi ta turoshi waje, Ahmad ne yayi sauri tareta cikin gigita da kid'ima ya kamo hannunta dake zubda jinin tare da cewa. "Wallahi al'janine a jikinta, sune suke sata yin komai." Da sauri ya sake hannunta ya kalli Ziyada data ruga a guje ta nufi mahaifin nasu, tana zuwa ta durk'usa gaban Baba malam hannu duka biyu ta d'ago cikin tashin hankali ta saki kuka mai sauti tare da cewa. "Dan Allah Baba Malam kayi hak'uri, kada ka tafi, in ka tafi ka barmu ya zamuyi, dan Allah Babana kayi hak'uri, wlhi gwara ka kori ita Zaleeha tunda bazatayi maka biyayya ba." sai kuma ta kifa kanta bisa rumfar sawunshi cikin neman al'farma. Hakama Maryam da gudu tazo gabashi ta durk'ushe murya na rawa cewa. "Wayyo Allah na wayyo Ya Ahmad ka bar Zaleeha kaga zata kashe mana mahaifinmu da bak'in ciki." Sai kuma ta matso gab dashi cikin tsananin kuka take magiya. Tuni Ahmad ya mance da Zaleeha bare matsalarta yazo tsakiyar k'annenshi suka durk'usa gaban Mahaifin nasu suna kuka mai tada hankali. Zaleeha kuwa sam bata cikin nitsuwarta bare tasan illar abinda take aikatawa asirin da uwarta tayi mata ya shafe nitsuwarta burinta kawai ta firgita kowa a fasa batun aurar da ita. Ido Baba Malam ya rumtse ganin Mamy ta motso gareshi cikin kuka take cewa. "Kada laifin mutun d'aya ya shafemu baki d'ayanmu, idan ka tafi ya zanyi da rayuwata? ina zan shiga? Me ya rage min da zaman gidannan? Dama d'ana kwaya d'aya tak Allah ya bani, shi kuma ba'a gidan yakeba, dan k'ashin Kanka ne da aurenka nake zaune a gidan nan, ni banyi maka laifiba Maryam batayi makaba hakama Ziyada da Habu da Zakiriyya to meyasa zakayi nesa damu akan laifin da bamu aikata ba?." ta k'arishe mgnar tare da durkushewa gefenshi kana ta kamo hannunshi murya na rawa tace. "Duk in da zakaje sai ka tafi damu, in kuma laifinsu ya shafemu ne, wlhi kana fita nima zan bar gidan nan." kalamam Mamy sunyi matuk'ar k'ara gigita su Maryam kawai sai suka saki sabon kuka. Mama kuwa da Ruda da Zaleeha ihu sukeyi wai bak'in ciki ya haukata Zaleeha. Daga bakin Gate Habu ke jiyo ihu da hargitsin dake cikin gidan nasu, Ko parking bai gama dai-dai tawa ba ya fito cikin motar, a guje ya nufi cikin gidan nasu gaba d'aya jikinshi kerma yakeyi. Wani irin tsayuwa yayi tare da zaro idanunshi baki d'aya, kuka da magiyar dasu Maryam keyi ya ganar dashi abinda ke faruwa. Wani irin tafasa da harzuk'a zuciyarsa keyi, juyowa yayi tamkar zautacce, Zaleeha da ta Kikimo wani akwatin ne ta harboshi, dai gaban Habu, kana ta juya tayi hanyar shiga parlour da niyar kwaso wani. Wani irin razanannen k'ara ta saki jin wani irin azabebben naushi da Ya Habun nata ya d'irka mata a tsakiyar gadon bayanta har saida tayi tangal-tangal zata fad'i k'asa, bata gama gigitar naushinba taji yasa k'afarshi ya tareta daga fad'uwar da zatayi ya naushi k'irjinta wanda saida ta bada sautin hak. bata ida tsayuwarba tayiji yasa k'afarshi ya tad'eta ta yi k'asa, ji kake gib ta bugi k'ofar parlour tayi gaba ta dawo baya, sai kuma ya zaro belt d'in k'ugunshi ya juya kan belt d'in dai-dai inda k'arfen yake ya fara tsula mata tamkar Allah ya aikoshi. Ihu da karaji ta sake tare da fara mirginawa tamkar macijiya tana. "Wayyo Ya Ahmad ya Habu zai kasheni! Wayyo goshina ya fashe! Wayyo k'uguna ya karye, wayyo Allah na na mutu na lalace". Shi kuwa binta yakeyi a baya yana had'a mata naushi da gula da zana tare da magana cikin haki dake nuna tsantsar tafasar da zuciyarsa keyi. "Shegiyar yarinya. tsinenniya mara amfani a doron duniya, kiyi ihu da kyau ki fad'a da k'arfi kasheki zanyi, tun kafin ki kashe mana mahaifinmu, kasheki zanyi koda ma rage mugun iri, shegiya mai zuciyar arnan kan duwatsu. Shegiya mai gadon bak'ar zuciya." Ina Ahmad, Maryam, Mamy, Ziyada su bata Zaleeha sikeyi ba bare su ceceta daga bugun gardi da Ya Habu keyi mata. Ganin alamun habu zai kasheta ne yasa Mama tayi tsalle tare da shiga tsakaninsu, da k'arfi ta ingiza Habu baya tare da cewa. "Dan ubanka kai farar zuciyarce da kai? Nace kai ɗin farar zuciyar ce da kai? da kake cewa tayi gadon bak'ar zuciyar a ina ta gado kenan?." Kan Zaleeha ya kumayi sunkuyowa yayi yasa hannu ya damk'o wuyanta tare da shak'ewa da k'arfi kana ya kalli Mama tare da cewa. "Eh nima bak'ar zuciya gareni kuma, data kashe mana uba gwara na kasheta, bak'ar zuciyar kuwa a ina zamu gada banda wurin bak'ak'en arnan iyayenkin can dake bautar gumaka." Aunty Lubna ce tayi k'arfin halin kamo hannun Habu da niyar cotar rayuwar Zaleeha daketa kakarin mutuwa tuni idanunta sunyi zuru-zuru a woje, sai kuma ya jiyo muryar Baba Malam na cewa. "Abubakar ka dawo haiya cinka, kisan Kai ya sab'awa addinin musulunci." jin haka yayi matuk'ar sace mishi zuciya hakan yasa ya hankad'e Zaleeha, kana yazo ya durk'usa gaban mahaifin nasu cikin rauni yace. "Dan Allah da al'farman manzon rahma Baba Malam kayi hak'urki ka gafarcemu ka rufa mana asiri kada kayi nesa damu." Ita kuwa Zaleeha wani irin azabebben tari takeyi tun sanda Habu ya sake mata wuya tarin takeyi tare da kuka, Aunty Lubna ce ta ruggumeta sukaci gaba da kuka a haka, Ruda kuwa tunda Habu yazo ta silale ta bar gidan dan tsoron yaron take. Ita kuwa Mama akwatuntan su Abdussalam d'in ta fara tattarewa tana maidasu parlournta. Shi kuwa Baba Malam kanshi ya jujjuya tare da rab'awa gefen su da nufin zai fita, ganin hakane yasa fargabansu ya ninku sama da sau d'ari, Maryam ce ta kife kanta a k'asa cikin kuka tace. "Kaito na! Kaiton rayuwata da bani da damar share hawayen mahaifina, Yau da ace bani da aure wallahi da na sharewa maka hawayenka baba malam Kodako Saifuddeen kurmane makahone gurgune kuturune wallahi matuk'ar zakayi farin ciki tabbas da zan zauna dashi. Inama ana rabuwa biyu wallahi da na kasu biyu." Ziyada ma kukan takeyi tare da kamo hannun Baba Malam cikin rauni tace. "Baba kada ka tafi ka barmu, in yana sona ni zan zauna dashi." Gaba d'aya sun rud'e da kuka hatta habun kuka yakeyi bare kuma Maryam da Ahmad masu rauni. Wani irin Murmushi Ahmad yayi still hawayenshi na kwaranya, kai ya jinjina ganin Zaleeha na rarrafe tamkar yarinya k'arama a hankali ta isa gaban Baba Malam hannu ta had'e wuri d'aya cikin yanayin neman gafara, murya na rawa jikinta na kar-kar-wa numfashinta na ficewa ba komawa, cikin shak'k'k'iyar murya a disashe tace. "Na amince Baba Malam na yarda ayi auren ka aura min Saifuddeen d'in na amince. Ka yafe min Babana ka gafarta min ka rufa min asiri kada in hallaka sabida fushinka na amince ayi auren na yarda." Da sauri Maryam da Ziyada suka ruggumeta. Ahmad da Habu kuwa ruggume juna sukayi, Mamy kuwa kamo hannun Baba Malam d'in tayi ta nufi side d'inshi dashi, shi kuwa ba musu ya bita. Ahmad da Habu sukabi bayansu, Aunty Lubna kuwa kamo hannun Zaleeha tayi ta nufi Side d'in Mamy kana Ziyada da Maryam sukabi bayansu. Zahira kuwa da sauri tabi bayan Mama. A gidan Saifuddeen kuwa, Ummi ce zaune a parlournta ita da. Su Bappa Ali da Malam Ashiru. Cikin nitsuwa tayi musu bayanin dalilin nemansu da tayi ta k'ara da cewa. "Hankali na ya tashi tun zuwansu na forko, yarinyar ta nuna bata son auren da Saifuddeen ta gaggaya musu bak'ak'en maganganun da suka gigitasu suka tayar musu hankali, anan Ahmad ya dawo yana kuka cur-cur da hawayenshi dan wulak'ancin da tayi musu ita da aminanta. basu b'oye min komai ba, sai dai shi Saifuddeen baiso su sanar min ba sabida tsananin son yarinyar yakeyi ita kuwa bata sonshi ina tsoron kada tazo ta cutarmin shi." Ta k'arishe maganar cikin yanayin tsantsar karaya da tsoro. Bappa Ali ne ya gyara zama tare da fuskantarta da kyau kana yace. "To yanzu me kike so ayi?." Nannauyan ajiyan zuciya ta sauk'e tare da cewa. "Ni dai auren ya fita raina, ku kira Saifuddeen ku taushi zuciyarshi ya rabu da yarinyar ya janye batun auren, kana kuje ku sanarwa iyayenta cewa an fasa batun auren tunda yarinya bata so gwara a bari kawai, magnin bari kadama a soma." Baba Ashiru ne ya katseta da cewa. "A,a sam bamu da hujjar janye batun auren nan, da girmanmu da mutuncinsu munje munyi magana gemu da gemu sannan dan zancen baya muce zamuje muce mun fasa auren. Sannan keda kankifa kika ce mana Saifuddeen yana son yarinyar matuk'a gaya." Cikin sanyi ta girgiza kai tare da cewa. "Ba zancen bayan kadai bane. Ko shekaran jiya Hayatuddeen yaje gidan kakarsu wurin Abokinshi k'aninta ya sameta can tanata kuka, wai ita bata son auren gurgu kurma. Tayi al'washin in dai aka aura mata shi zata kashe kanta. Kuma jiya ma dasu Saifuddeen d'in sukaje nanma ta ciccimusu nutunci sun dawo nan suna mgnar basu san na jisu ba." A hankali Bappa Ali yace. "Ba komai! In sha Allah babu abinda zai faru sai al'khairi! Ke dai kiyi ta addu'a kin san addu'ar uwa karb'eb'b'iyace domin bata da hijabi, Tunda kin sani mun sani Saifuddeen yana sonta tofa mu bisu da addu'a. in har bata so ai iyayenta zata sanarwa kuma in bata sonshi baza bashi izinin turamu ba." kasake tayi tana jinsu, suna bata k'arfin guiwa, cikin kula Malam Ashiru yace. "Kinga fa du-du-du kwana biyar ne ya rage bikin ta yaya zamu fito da wata matsala ta b'angarenmu, muyi hak'uri in har bata so d'in su sa fito da matsalar." Kai ta jinjina tare da cewa. "To tunda kunce haka ba matsala, amman ni naso Saifuddeen ya nemi matar aure a cikin tarin matan dake bibiyarsa da soyayyarsu. Amman ba komai Allah yasa hakan shine mafi alkairi." Amin Amin sukace baki d'aya, kana sukace to su zasu koma dukku. nan suka sallemi juna suka tafi. A can gidansu Zaleeha kuwa, shiru gidan ya koma kamar gidan zaman makoki, kowa da abinda ke ransa, su Ahmad da Mamy da Maryam dai sunyi ta magiya da rok'on Baba malam da bashi hak'uri. Har saida suka ga alamun ya samu sassaucin tashin hankalin da yake ciki. Bayan anyi sallan isha ne. Malam Adam da Ya Aminu suka shigo gidan a jere. Kai tsaye parlour Baba Malam suka nufa, Bayan sun gaisa ne ya musu bayanin abinda ya faru. kwaffa ya Aminu yayi dan tabbas da yana nan to da tuni ya karya Zaleeha. Shi kuwa Malam Adam kai ya jinjina cikin tsananin mmki da tsoron yaran zamani yace. "Aminu je ka kirawo min Zaleehan." To yace kana ya mik'e ya nufi part d'in Mama. Ita kuwa Zaleeha zuwa yanzu dai tayi kuka har hawayenta sun kafe. Da kyar Aunty Lubna da Maryam suka sata tayi wonka kana tayi salla, sannan suka bata magani ta sha, domin tuni wuyanta ya kumbura haka fuskarta ,gaba d'aya jikinta ciwo da tsami yake mata duk farar fatar nan tayi jazir ga tsami da yankan da tayiwa kanta yayi duk da anyi mata dressing. Rumtse idanunta tayi lokacin data rab'a jikin Ya Ahmad da yanzu ya shigo, wasu zafafan hawaye ne masu k'una suka kwaranyo mata. sosai ta zama abar tausayi dan duka iya duka Habu ya jibga mata gashi ita da kanta can ƙasan zuciyanta take jin zafin abinda ta aikatawa mahaifinta. cikin sanyin murya da tausayawa tare da lallashi Ahmad yace. "Zaleeha!." bata amsa ba sai wasu sabbin hawaye ne suka fara sintiri a fuskarta. Lubna ce tasa tafin hannunta ta share mata hawayen, yayinda Maryam ma idanunta sukayi rau-rau alamun zasu zubdo kwalla, muryar Ya Ahmad d'in nasune ya katse musu shirun nasu. "Dan Allah Zaleeha na rok'eki da girman Allah kiyi biyayya ga umarnin mahaifinmu, kiyi koyi da Maryam, ki kare mana mutunci da martaba da darajar gidanmu dana mahaifinmu." A hankali ta bud'i baki cikin disashewar murya tace. "Ya Ahmad bana sonshi wallahi na tsaneshi ji nakeyi kamar zan mutu in na tunoshi." kanta ya shafa tare da cewa. "Zaki soshi, zaki daina jin komai, in kin rabu da aljanin dake jikinki. Ni nasan Zaleeha tana son farin cikin Babanmu." Shiru tayi dan ta fahimci ya Ahmad dai ya maidata mai aljanu so bazai tab'a fahimtar matsalarta ba, shi kuwa d'agota yayi suka fuskanci juna cikin tausaya mata yacee. "Dan Allah Zaleeha kiyi biyayya ga auran da Baba Malam zai miki ki zauna d'akinki, nayi miki al'k'awarin zan miki duk wani abu da kikeso a duniya matuk'ar baifi k'arfina ba, kuma bai sab'awa shariya ba, ki gaya min duk abinda kikeso zan miki shi k'anwata, ni dai fatana a miki auren ki zauna lfy da mijinki." cikin zubda hawaye tace. "Ka saya min sabuwar mota, motocina su zama biyu." da sauri Maryam tace. "Ai yanzuma motocinki biyu ne, ai kayan aurenma da motarki sabuwa fil Saifuddeen ya had'o miki." Ido ta rumtse da k'arfi dan wani d'aci da takaicin jin sunanshi da Maryam ta kira cikin had'e fuska tace. "Bana son wannar, abin gori abin dangin miji". murmushi Ya Ahmad yayi tare da cewa. "Zan saya miki k'anwata sabuwa fil zan saya miki, motocinki su zama uku." sosai taji dad'in amincewar da yayi zai saya mata mota, ganin taji dad'i yasasu jin dad'i suma. Ahmad ne ya rik'o hannunta tare da cewa. "Da me kuma kike so?." cikin jin dad'i tace. "Sabuwar system." cikin jin dad'i fa da ganin yarintarta yace. "Kin samu." kayan d'aki kuma wanne iri kikeso." jim ta d'anyi tare da cewa. "Ko wannema." a tunaninta me zata ce a kan kayan d'aki abinda ko sun kashe kud'i sun mata bazata soshiba. haka fa sukayi ta lallab'ata. Ya Aminu kuwa yana isa parlour Mama ya samu, Habu cikin had'e fuska yace. "Ina Zaleeha tazo, Baba malam na kira." "Tana part d'in Mamy." "Je ka kira min ita." to yace kana suka nufi parlour Mamy, daga bakin k'ofa ya tsaya tare da cewa. "Ke Zaleeha maza ki zo, Baba Malam na kira." jin muryar habu yayi masifar razanata, da sauri ta mik'e ta nufi parlour. Ahmad d'inne yabi bayanta. ganin Ya Aminu da Ya Habu a parlour'n ya k'ara firgitata. nur-nur tayi gaba sana suka bita a baya, tana tafe tana d'ingisa k'afarta. har suka isa parlour. kana Ahmad na biye dasu a baya, A hankali ta isa gaban Baba Malam d'in jiki na rawa ta durk'usa ganin yadda ya Aminu ke watsa mata harara yasa tayi maza tayi k'asa da kanta, murya na rawa tace. "Baba Malam gani." shiru yayi yana k'are mata kallo, gaba d'aya jikinta rawa yakeyi, Malam Adam ne ya kalleta tare da gyara murya wanda sai lokacin ta ganshi, cikin rawan murya tace. "Daddy ina wuni." ido ya lumshe tare da cewa. "Lafiya lau Zaleeha." daga nan sukayi shiru na tsawon 55 seconds sannan Malam Adam ya kira Zaleeha wacce tsoro ya hanata salama. "Na'am". A hankali ya fara magana. "Naji abinda kikayi, da kuma abinda kike Al'washin yi na cewa zaki kashe kanki ko?." shiru babu mgna sai wata zazzafar zufa data keto mata, "To yanzu gaya min cikin mutun biyu da kika sa suka turo mana iyayensu wa kike so?." kai ta jujjuya alamun babu. Cikin fad'a Aminu yace. "To uban wa yasa zaki had'a mana kayan mutun biyu, kin san aurenki saura kwana biyar meyasa zakisa Abdussalam turo iyayenshi." da sauri tace. "Bani bace nace su kawo kayansu bafa." a hatsale Habu yace. "Waye to." cikin tsoro tace. "Mama ce." shiru sukayi sai Baba Malam ne yace. "Uhummm". Malam Adam kuwa yace. "To yanzu dai gwara mu zare hannunmu a kanki, gwara mahaifin naku ya tafi ya barku kiyi duk yadda kika ga dama ko." cikin raunin murya tace. "Dan Allah, Baba Malam kayi hak'uri na tuba, ku gafarceni, Kayi hak'uri kada ka tafi, na yarda ayi auran." cikin jin dad'i Malam Adam yace. "Allah ya miki al'barka, tashi kije." jiki na rawa ta mik'e ta tafi. daga nan suka ci gaba da tattaunawa. Nan Baba Malam ya bawa Habu umarnin cewa gobe da safe ya kwashe kayan su Abdussalam ya mayar musu. Ita kuwa Zaleeha d'akinta ta wuce, kana ta d'auki wayarta. 10:15 pm ta gani, zuciyarta cike da bak'in ciki ta kwanta, text tayi ta rubutawa da mugayen kalamai tana tura mishi har kashi uku, sannan ta kira Bilkeesu ta gaya mata duk abinda ya faru, nan bilkeesun tace. Tana zuwa gobe dan mgnar bazata yiwu a waya ba. Saifuddeen kuwa, kafin ta tura mishi texts d'inma yayi bacci sabida a gijiye yake. Washe gari tun da sanyin safiya, Ahmad da Salisu suka shigo da masu gyaran gida, dan sabunta fentin gidan. Kai tsaye sashin wannan part guda biyun nan wanda yakeda ciki da parlour da dinning area, a tsakanin part d'in da komansu iri d'aya suka nufa. In da nan Raliya da Ahmad suke a d'aya part d'in. Nuna musu duk gyaran daya dace sukayi kamar farfasa steps d'in tsakanin parlour da dinning area, yadda wheelchair D'inshi zaibi ko ina a part d'in har zuwa cikin parlour'n nan mai 2 beedroom dan nanne zai zama turakarshi. Suna gama nuna musu suka fara aikinsu,. Su d'in kuwa kai tsaye cikin gidan suka nufa, jin shiru parlour ba kowa yasa suka wuce parlour Saifuddeen, suna shiga suka hangoshi kan wheelchair d'inshi mai azabar kyau. Ya bawa k'ofar shiga baya. Ba jin takunsu zaiba bare yasan akwai mutane a bayanshi, Wayarshi ya zubawa ido yana maimaita karanta text d'in da Zaleeha ta turo mishi a karo na barkatai. Wani irin zaro ido Ahmad yayi lokacin da idanunshi sukayi arba da abinda ke rubuce a wayar, wani irin zazzafan numfashi ya sauk'e da k'arfi tare da...! Littafina na kuɗine in kin karanta na sata kin san sauran in kina ɓuƙata turo katin mtn na raɗi uku kacal ta wannan number 09097853276 ko kuma ki biya ta asusuna na 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. By *GARKUWAR FULANI* [30/08, 3:46 pm] +234 906 084 2867: Zazzafan numfashi ya sauƙe, da ƙarfi ya fusge wayar daga hannun Saifuddeen, sosai hankalinshi ya tashi ransa yayi mummunan ɓaci dan ganin kalaman da Zaleeha ta rubutawa Saifuddeen tacikin text message, wani irin ɓaƙin ciki da ɓacin raine suka tokarewa Ahmad maƙoshi, shikam baisan meyasa Saifuddeen ya maƙalewa Zaleeha ba, yarinyar da bata ganin mutumci da ƙimarsa ko kaɗan, yarinyar da ta maida rashin kunya man shafawanta. Ɓata fuska Saifuddeen yayi tare da miƙowa Ahmad hannu, alaman ya bashi wayarsa. Fuska Ahmad ya haɗe sam babu alaman wasa akan fuskarsa haka ya juya ya nufi hanyar fita daga ɗakin, da kallo Saifuddeen ya bishi, wani ɗan guntun murmushi ya sake, haƙiƙa yasan Ahmad sam bayason aurensa da Zaleeha, ya kuma san dalili, amma yasan nanda wani lokaci kaɗan Ahamad ɗin zai fahimta. Cikin   zafin zuciya haɗi da fusata Ahmad ya nufi ɓangaren Ummi. Zaune Ummi take akan kujera gefenta kuwa Raliya ne zaune tana ta yabawa da koda d'inkunan zafafan laces ɗin dake gabanta, wanda Saifuddeen ne ya saya musu donyin fitan biki. Murya can ƙasan maƙoshi Ahmad yayi sallama, inda ya kutsa kansa cikin falon, fuskar Ummi cike da fara'a ta amsa masa, saidai kuma yanayin yanda taga fuskarsa yasanya taji ba daɗi, domin Ahmad mutum ne me yawan fara'a, baƙaramin abu bane zai sanya kaga ya ɓata fuska. Raliya kuwa ji tayi gabanta ya faɗi, sakamakon ganin mood ɗin mijin nata. Zama Ahmad yayi akan sofa tare da tanƙwashe ƙafafunsa. Dubansa Ummi tayi cikin sanyin murya haɗi da bayyanar da damuwarta tace. "Ahmad lafiya kuwa?." Ɗago idanunsa wanda sukayi jajur yayi ya kalli Ummin tare da miƙo mata wayar Saifuddeen dake hannunsa. Amsan wayar Ummi tayi tare da kai dubanta ga screen ɗin wayar, wanda har yanzu screen ɗin keda haske bai ɗauke ba, wanda shi Saifuddeen azatonsa Ahmad baisan security ɗinsa ba, shiyasama yabar Ahmad yatafi da wayan, shikuwa Ahmad dama tun tuni yasan securityn Saifuddeen ɗin, don ranan agabansa Saifuddeen yacire wayartasa a security. Idanu Ummi ta ƙurawa rubutun dake kan screen ɗin wayar, sannu ahankali take karanta saƙon, lokaci guda jikinta ya ɗauki wani irin rawa, take yanayin idanunta suka sauya daga farare zuwa ja,  aƙalla ta maimaita karanta saƙon yafi sau uku, batare da ta sani ba, sosai zafafan baƙaƙen maganganun da aka rubuta cikin saƙon ke yawo acikin brain ɗinta. Babu abun dayafi ɗaga mata hankali kamar inda Zaleehan ta rubuta cewa. ```"Ka turo iyayenka su janye batun aurena da kai! Su zo su kwashi wannan tarkacen da kasa aka tarkato aka kawo mana jidali. In kuma kaki yin hakan ka kuskura ka bari akayi auren nan aka kawoni mushen gidan kunnan to. Wallah Allah kenan``` Saifuddeen, in ka bari akayi auren nan cikin biyu za'ayi ɗaya ko in mutu ko ks matu!!!." Sosai tunanin Ummi ya tsaya cak, wani irin matsanancin tsorone ya daki zuciyarta, sosai kalaman Zaleeha suka ɗaga mata hankali, tabbas tanayiwa ɗanta Saifuddeen tsantsar so, bakuma tason wani abu da zai cutar dashi,  tayaya ma amatsayinta na Uwa zata zuba idanu tana kallo ɗanta yakai kansa ga inda ake neman halakasa, tabbas acikin kalaman na Zaleeha tagano cewa bata ƙaunar Saifuddeen ko kaɗan,  sam bazata taɓa bari Saifuddeen ya auri macen da take da bushashshen zuciya ba. Hawayen da suka cika idanunta tasoma ƙoƙarin shanyewa, cikin raunin daya bayyana akan fuskarta ta dubi Ahmad. Shi ɗinma Ahmad dubanta yayi, cikin rauni yace. "Ina takaicin tsananin son da Saifuddeen kewa Zaleeha, bata sonshi Ummi sam bata ƙaunarsa, bata ganin ƙima da darajarsa, tun awaje tana faɗa masa mugayen kalamai irin wannan inaga kuma idan anyi auren? ba fata nake ba Ummi amma sam banason abun dazai wargaza mana farin cikin mu, Saifuddeen kamar jigo yake agaremu baki ɗaya, bazan iya zuba idanuna naga ya jefa kansa cikin mawuyacin hali ba, Ummi zuciyar Zaleeha tayi zurfi sosai wajen tsanar Saifuddeen, saboda haka zata iyayin komai idan ya aureta." Ɗan tsagaitawa da maganan yayi tare da maida ƙwallan da suka cika idanunsa, ci gaba yayi da cewa. "Ai Nakasa Ba hauka bace bare tace baida hankali bazata iya zama da shiba, kuma Nakasar Saifuddeen bashi yake nuna cewa ya kasa ba,   mene aibun Saifuddeen Ummi? shin laifine don Allah Ya jarrabeshi da nakasa? ko kuwa laifine don yazamo kurma kuma gurgu, shi nakasashshe ba mutum bane kenan? Wallahi Ummi Saifuddeen bai dace da Zaleeha ba, saboda bata yarda da ƙaddara ba, hartanajin cewa ita watace, wacce ajinta ya ɗara nakasashshe, ta manta cewa da me lafiya da kuma nakasashshe duk halittar Allah Ne." Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe tare da sakin wani murmushi wanda yafi kuka ciwo. Cikin tsananin tausayin ɗannata Saifuddeen da irin ƙaddaran da Allah Ya ɗauro masa tace. "Inajin tsoro Ahmad, Inajin tsoron abun da zai faru nan gaba, bana fatan yarinyarnan  Zaleeha ta cutarmin Saifuddeen cutarwa mafi muni." Still ajiyar zuciya ta kuma sauƙewa, tare da miƙewa tsaye,  duban Ahmad takumayi cikin sanyin murya tace. "Ahmad zanyi abun da ya dace, abunda  kowacce uwa zatayi dan kare rai da lafiyar danta zanyi abinda ya kamata ace  tayi a matsayina na uwa!." Tana gama fad'in haka ta juya ta nufi hanyar ɗakinta. Tuni hawaye sun wanke fuskan Raliya, duk da cewa bata karanta saƙon da Zaleehan ta turowa Saifuddeen ba amma tabbas ta fahimci duk abun dake faruwa, daga cikin kalaman na Ummi da kuma mijinta Ahmad. Dubanta Ahmad yayi, itama kallonsa take, yayinda hawaye ke tsiyaya daga cikin idanunta, shin menene aibun Hamman'ta don yakasance gurgu kuma kurma? shima mutum ne kuma Namiji kamar kowa, yana da cikakkiyar lafiyansa na ɗa namiji, sannan gurguntan sa bazai zama kasawa agareshi ba, don meyasa Zaleeha zata ƙisa? Kai Ahmad ya girgizawa Raliya alaman ta daina kuka. Kasa jurewa tayi, hakan yasa ta faɗa cikin jikinsa tare da sakin kuka mai sauti. Rungumeta yayi ƙam tare da sake jawota jikinsa,  nan yamiƙe tsaye tana ajikinsa suka nufi hanyar barin falon. Suna fita suka yi karo da Hayatuddeen wanda shigowarsa cikin gidan kenan, sanye yake da white t shirt da kuma 3 guater jeans, hannunsa riƙe da wayarsa ƙiran Samsung yayinda kunnensa ke saƙale da earpiece,  yana ganinsu yaɗan yi turus tare da turo bakinsa gaba, har acikin ransa shikam yagaji da ganin Yayar tasa Raliya da Ahmad manne da juna sunashan soyayyarsu kamar tattabaru, kullum haka yake ganinsu liƙe da juna kamar wasu tif da taya. Hararansa Raliya tayi da jajayen idanunta,  sake kwaɓe fuska yayi yana shirin yi musu halinnasa na shagwaɓa ne, Ahmad ya miƙo masa wayar Saifuddeen, batare da Ahmad ɗin yace komai ba yaja Raliya suka nufi ɓangarensu. Da kallo Hayatuddeen ya bisu har suka ɓacewa ganinsa,  bakinsa ya taɓe ƙasa-ƙasa yace. "Hegu fitinanu, kuyi dai nima dana ƙara girma, ai dai zanyi auren nan ehe, don haka duk wani me ɗagamin kafaɗa ma gwara ya daina, nima ai zanyi auren bawai ba zanyi ba." Haka ya nufi ɓangaren na Saifuddeen yanata ƙunƙuni aransa. Koda ya ƙarasa part ɗin a parlour ya had'u da Salisu dake saurin fita, dan sunyi mgna da Saifuddeen kam batun Rashida na son su kai musu kud'in walima, so shine ya fita da sauri dan kai mata kud'in, cikin girmamawa yace. "Ina kwana Ya Salisu." "Lafiya lau Auta ya sakalci." Salisu ya amsa mishi ba tare da ya tsaya ba, Murmushi Hayatuddeen yayi tare da cewa. "Manyan angwaye sai b'are-b'are suke uwa hanji a langa." yana musu tsiya ya wuce ya nufi bedroom d'in Hamma Saifuddeen din nashi zaune ya sameshi akan wheelchair ɗinsa, inda ya tasa laptop ɗinsa agaba ƙiran company'n apple yana dannawa. Akan cinyar Saifuddeen ɗin ya ɗaura wayar tare da yin super ya faɗa kan lallausan gadon na Saifuddeen, lumshe idanu yayi yana me shaƙan daddaɗan ƙamshin na Hammansa, aransa yana fata ace watarana shima yazama kamar hamman nasa. Saifuddeen kuwa murmushi kawai yayi tare da ɗaukan wayar tasa ya duba, ganin still akan message ɗin Zaleeha yake, yasanyashi sakin murmushi, domin jikinsa ya basa cewa Ahmad bai cire wayan a security ba balle yayi amfani dashi. Cigaba yayi da aikinsa,yayinda time to time yake sipping exotic juice ɗin dake gefensa. A wunin ranan masu gyarannan suka gama komai na side d'insu Saifuddeen kafin azahar sun gama komai na side d'in masu buga kitchen cabinets ma sunzo sun shirya komai ras. masu fenti kuwa sun fento ko ina na gidan luggu da sak'o da yake sunada yawa kuma akwai kayan aiki kafin magrib dai sun gama komai gidan ya zama sabo fil yayi ras sai shek'i yakeyi da k'amshin sabon fenti. In da akayiwa gidan fentin Coral color iya rabi daga k'asa kuma dama tayis ne manne royal color hakan yayi masifar kyau ya haska gidan, cikin gidan kuwa Side d'in Ummi pumpkin color akasa daga saman pop d'in daga k'asa kuma navy blue mai shek'i, hakama saman inda Hayatuddee yake, inda Saifuddeen yake kuwa ba'a tab'abashi ba dan bai jimaba, Sai inda Raliya take mai mak'otaka da inda za'a ake shirin sa Zaleeha, mint green and white akayi mata komai yayi ras, sai wojen part d'in duka da aka fente da dark brown and daga d'an k'asan kuma tayis ne manne a jikin ginin, sai farfajiyar wurin da yakeda d'an zagayeyyen ma dai-daicin lambun da yakeda yabanyar grass carpet wanda yayi kore shar, sai bishiyar mangoro mai fad'i da tsananin duhu wanda yake baje kan bishi yoyin dabino da ayaba da gwaiba dake gefenshi dan bishiyar mangoron bata da tsawo sosai, a k'asan kuwa fulawowi ne jere wanda sune suka zama garkuwan wurin sai ya zama in kana cikin wurin baza'a hangoka ba, cikin wurin kuwa sai wasu fulawi masu halittar tim-tim in ka gansu kamar kujeru, kana ga kan pompoms guda biyu wanda dasu akeyiwa wurin ban ruwa, daga tsakiya ciluk kuma wani k'arfe ne mai tsawo wanda yake manne da fitilar sola mai d'an karen haske. sai irin kujerun silver nan da ake ajewa a asibitoci da wuraren shak'atawa, kujerun ne suka zageye wurin da k'asanshi ke wadace da koriyar ciyawar, ga sanyin tsirrai gana ruwan dake gudana a wurin ga na inuwar bishiyar mangoro dana dabino da gwaiba, uwa uba ga sanyin bishiyoyin ayaba kusan guda biyar da suka zagaye wurin, daga cikin wojen wurin kuwa an lailayeshi da intalak, sai babban baranda mai fadin da aka laileyeshi da tayis fari k'al. kana cikin parlour kuwa yasha fenti purple and cerise color sosai parlour yayi kyau hakama cikin two bedroom d'innan, kitchen d'inta kuwa an k'awatashi da durowowi masu kalar pink and white sosai aka k'awata kitchen d'in. komai fa yayi ras sai shek'i da k'amshi gidan keyi, hakama fulawin gidan duk anbi an musu sassariya an dai-dai tasu, garden dake bayan part d'in Ummi ma an gyarashi sosai, gida dai ko yanzu amarya tazo... Juyi take tayi akan makeken gadon nata,  gaba ɗaya damuwa ya cika zuciyarta, wani irin zafi takeji acikin ƙirjinta,  rumtse idanunta tayi, take wasu irin hawaye masu zafi suka kwaranyo daga cikin idanunta, ya zatayi? wazata kaiwa kukanta ya share mata hawaye?  burinta shine koda mutum ɗaya ne ya fahimceta, amma ankasa samun hakan,  sosai zuwa yanzu ƴan uwanta keyi mata kallon wanda aljanu suka kama,  laɓɓanta ta ciza tare da sakin wani marayan kuka mai sauti, ta lura shi wannan nakasashen jikinshine a nakasashe zuciyarsa cike take da jarumta, dan ta fahimci duk baraza da ihu da hargowar da take mishi akan ransa da rayuwarshi a banza, babu alamun karaya bare fargaba ko d'igon tsoro, asalima sai tsoronshi dake cika mata idanu muddin ta kalli kwayar idanunshi koda na one second ne. Juyi ta kumayi tare taune lip d'inta na k'asa ayanzu tafi buƙatarsa fiye da dacan baya, fatanta burinta, muradinta duk sun ta al'laƙane akansa, sam soyayya batayi mata adalci ba da ta jefata cikin mawuyacin hali,  hannunta ta sanya ta dafe dai-dai saitin zuciyarta dake bugawa, tanajin sonsa na fusgarta, wani irin maganaɗisun ƙaunarsane ke ƙara janta akowacce rana,   yaya zatayi da soyayyarsa dake ƙoƙarin fasa mata zuciya? Ƙaddara tazo mata ayanda bata taɓa zata ba, ƙaddara ta zautar mata da tunani, har takai ga tanayin komai cikin zaucewar hankali. Sosai tayi hugging pillow, ahankali taci gaba da rera kukanta, saida tayi kuka sosai kafun wani wahalallen bacci ya ɗauketa. Washe gari. Zaune suke su dukansu akan babban dinning table ɗin dake  cikin falon, Saifuddeen, Hayatuddeen da kuma Raliya, sai Ahmad wanda shigowarsa cikin falon kenan. Ahankali Saifuddeen ke tsakalan abincin yana kaiwa bakinsa,  gaba ɗaya hankalinsa naga wayarsa dake riƙe ahannunsa, sosai yashiga busy tunda aka fara shirye-shiryen bikin, dan ma yanada tarin aminai dake ji da komai wani abinma sai dai kawai yaga anyi sosai suke shiryawa bikin inda ya kama yau saura kwana uku bikin. Tunani yakeyi akan tirelar dake can harabar gidan nasu wanda aka kawo kayan Zaleeha. Tirelan cike yake dam da kayan Zaleeha wanda Ya Ahmad yayi mata komai na duniya wanda amare zasu buk'ata. Wanda Habu ya bada shawaran kada a sauk'e kayan a gidansu a wuce dashi gidan Saifuddeen d'in acewarsa k'arin jidaline. to koda ya gayawa Ahmad sai suka bawa driver'n tirelar hak'uri akan zasu biyashi abar kayan a ciki sai an gama gyaran side d'in amaryar sai su sauk'e kayan to su kuwa jin za'a biyasu yasa suka amince. to an gama gyara a bisa tsarinsu dai gobe za'a zo a sauk'e kayan sannan tuni Salisu ya nemi masu had'a kayan su shirya za'a biyasu dubu saba'in kud'in aikinsu kana Maryam da Aunty Lubna zasu zo su kimtsa komai duk a goben... Ummice ta ƙaraso cikin falon, cikin shirinta tsab, sosai tasha ado irin wanda ya bayyana cikar kamalarta, tana ƙarasowa cikin falon gaba ɗaya kallon ƴaƴan nata ya dawo gareta. Ahankali Saifuddeen ya ɗago da kansa ya kalli Ummin nasa, ganin yanda tayi masa kyau yasanyashi sakin murmushi, tare dayi mata duban tsab, domin yaga alaman cewa fita zatayi. Ƙarasowa dinning area'n Ummi tayi, hannu tasanya ta shafa kan autanta Hayatuddeen dake ta faman zuba wa cikinsa, spiring roll. Fuska Saifuddeen ya kwaɓe tare da karyar da wuyansa gefe, Matsanancin tausayinsa ne ya cika zuciyar Ummin, don sarai ta fuskanci abun da yake nufi, alamune dake nuni yanada yar damuwa can k'asan zuciyarshi wanda kuma baya son ta sani, ita kuwa in taga hakan bata matsa mishi kan ya sanar mata sai dai takanyi k'ok'arin sashi farin ciki, sai dai tasan yanzu koma menene aransa baya rasa nasaba da Zaleeha, hannu tasa ta shafa kansa shima. Murmushi yayi inda cikin body language ɗinsa yayi mata alaman da ina zataje. Itama murmushin tayi tare da gyara tsayuwarta, duban ƴaƴan nata tayi dukansu, tare dayi musu bayani akan zuwanta Dukku da ta tsarashi yau da safe, sannan kuma ayau ɗin zata dawo, sosai suka ɗanyi mamaki sai-dai kuma sanin cewa ana tsaka da shirye-shiryen hidiman biki ne yasanya basu damu ba, don atunaninsu wani uzurine wanda ya shafi bikin zai kaita Dukkun. Haka Ummi tayi sallama da su, inda dukansu suka rakota har compound ɗin gidan. Saida suka ga tafiyarta kafun su dukansu suka koma cikin gida. Kusan ƙarfe shabiyu da wasu ƴan mintuna Ummi suka iso cikin garin na Dukku me al'barka. Kaitsaye gidan Bappa Ali suka sauƙa. Sosai Aunty Mina tayi murnar ganin Ummin, nanfa lokaci ɗaya tacika mata gabanta da kayan ciye ciye, hadda dangin su fura da nono, Sosai Ummi da Auntyn ke shan hiransu, kasancewar Bappa Alin bayanan, sunje gaisuwan wani abokinsu wanda bashida lafiya, shida Malam Ashiru. Cikin ikon Allah Kuwa Ummi na idar da sallan azahar saiga Baffa Alin ya shigo, koda yaga Ummin yaji daɗi, saidai kuma zuciyarsa ta basa kan cewa ba lafiya ba, domin lafiya ƙalau babu abun da zaikawo Ummi Dukku ana tsaka da shirye shiryen bikin Saifuddeen kana kuma jiya-jiya nan sukaje amsa kiran nata. Bayan sun gaisa da Bappa Alin ne Ummi ta gyara zama, lokaci ɗaya damuwa ya bayyana akan fuskarta, dubanta Baffa Ali yayi cikin sanyin murya yace. "Lafiya kuwa? badai wanine bashida lafiya acikin gidan ba?." Kai Ummi ta girgiza cikin ƙunan zuciya tace. "Akan maganan auren Saifuddeen da yarinyar nanne, kamar yanda na faɗa muku kaida Malam Ashiru jiya cewa yarinyar nan batason Saifuddeen, tana masa barazanar matuƙar ya aureta zata kasheshi, to fa yanzu abin k'aruwa yakeyi dan bata daina ba, awancan karon kun tausasheni ta hanyar cewa nayi haƙuri nabari ayi auren, na haƙura badon raina yana soba, saidai ayanzu bazan iya haƙura ba, inamatuƙar jin tsoron abun da zai faru anan gaba, inatsoron rasa Saifuddeen, Bappa Ali kasan yanda Saifuddeen yake awojenmu dan Allah Kayi wani abu!." Nan ta kwashe duk kan abun daya faru da kuma text message ɗin da ta karanta wanda Zaleehan ta turowa Saifuddeen ta faɗa masa. Ajiyar zuciya maiƙarfi Bappa Ali yayi, tare da sanya hannu ya ɗan dafe kansa, tabbas zuwa yanzu yakamata yabita maganan Ummi, don kuwa tabbas ayanda Zaleehan ke faɗa da kuma bayyana tsanar Saifuddeen afili tabbas zata iya aikata koma miyene don ganin ta cutar dashi, tabbas shima zuwa yanzu kam yafara tsorata da al'amarin. Ɗan jim yayi tare da gyara zamansa, cikin kulawa yace. "Insha Allahu Ayau yau ɗinnan zan ɗauki Malam Ashiru mu tafi Gombe tun lokaci bai ƙure mana ba, haƙiƙa wannan lamari yayi tsaurin da dole sai manya sun shiga cikinsa, ki kwantar da hankalinki, Insha Allah zamuje mu samu shi Malam ɗin, zamuyi magana ta fahimta dashi, bakuma zamu ɓoye masa komai dake faruwa ba, tabbas nasan zai fahimce mu, shi kuma Saifuddeen Allah yabasa wata mace tagari wacce ke ƙaunarsa!." Ajiyar zuciya mai ƙarfi Ummi ta sauƙe tare da cewa "Ameen!." Har cikin ranta taɗanji sanyi, haka dai suka ɗan taɓa hira kaɗan kafun daga bisani tace zata koma. Haka suka rakota har wajen mota inda Sule driver ke jiranta. Haka Ummi suka kama hanyar shigowa cikin garin Gombe zuciyarta wasai, tanajin kamar ta raba Saifuddeen da ƙaya. Tafiyar 1 hour ne kacal ya kawosu Gombe, inda ta koma gida zuciyarta cike da salama, saidai kuma ta wani ɓangare, cike take da tausayin Saifuddeen, domin kuwa koda sau goma zata kalleshi, to akowani kallo ɗaya, saita hango zazzafar ƙaunar da yakeyiwa Zaleeha acikin ƙwayan idanunsa. Amma addu'a bata bar komai ba. Zata tayi masa addu'a akan Allah Ya musanya masa da mafi alkhairi. Su Bappa Ali kuwa ƙarfe biyar dai-dai suka kamo hanyan zuwa garin Gombe shida Malam Ashiru, daga cikin abun da Ummi ta faɗa masa, ko ɗaya bai rage ba, haka ya labartawa Malam Ashiru komai, shikansa Malam Ashiru saida yaji zuciyarsa tayi masa ba daɗi, tabbas yasan sharrin ƙiyayya, ƙiyayya bata da daɗi sam, kuma takan rufewa mutum ido, yayi duk abun dayaga dama, musamman ma ga mace da auren mijin da bata so dan haka shima ya yarda baza'ayi wannan aurenba. Ƙiran sallan Magriba acikin garin Gombe tayi musu, nan suka tsaya sukayi sallah, inda suna idarwa suka nufi gidan Dirankaɗi, wato Baban Ishaq kenan, kasancewar tunkan su taso sunyi masa bayanin komai sun kuma sanar dashi zuwansu, inda shikuma ya ƙira Baba Malam ya shaida masa cewa da anyi sallan Isha za su zo. Koda suka ƙarasa gidan na Dirankaɗi, anan sukayi sallan Isha, daganan suka wuce zuwa G.R.A wato unguwar su Zaleeha. Tarba me kyau suka samu daga Baba Malam, inda ya sauƙesu acikin babban falonsa, nan yasa aka cika musu gabansu da kayan ciye ciye, hira kaɗan suka ɗan taɓa, kafun Dirankaɗi ya gyara zama inda ya fuskanci Baba Malam, cikin nutsuwa haɗi da halin dattako yashiga labartawa Baba Malam abun dake faruwa, da irin saƙon text message din da Zaleehan ke turawa Saifuddeen wanda suke ɗauke da barazana haɗi da baƙaƙen maganganu, inda ya ɗora da cewa. "Kayi haƙuri Malam, amatsayinmu na manya masu hankali, baikamata ace mun zuba ido hakan na faruwa ba, haƙiƙa duk auren da akace akwai ƙiyayya acikinsa to mafi al'khairi shine barinsa, tabbas babu wani uba dazai so ɗansa ya rasa iri awannan gida naka mai cike da kamala haɗi da tarbiya, saidai kuma babu yanda zamuyi ɗaukan ƙaddara ya zame mana dole, saboda hakane mukazo baka haƙuri, kayi haƙuri Malam bisa dole munjanye nemawa Saifuddeen auren Zaleeha da mukayi, fatanmu shine Allah ya bawa kowannensu abokan zama nagari!." Ajiyar zuciya Baba Malam ya sauƙe tare da ɗanyin jigum, tabbas Zaleeha nason dasa masa ciwon zuciya, sannan tanason zubar masa da ƙima da kuma mutumcinsa a idanun jama'a, saidai kuma yayi al'ƙawarin bazai taɓa bari hakan ya faru ba, gyara zamansa yayi tare da duban su Baffa Ali, cikin dattako haɗi da tausasa zance yace. "Babu wani abu dazan faɗa muku face haƙuri, kuyi haƙuri, haƙiƙa nine nan mahaifin Zaleeha, sannan nike da ikon bada aurenta ga koma waye, tuntuni nakuma bada aurenta ga Saifuddeen, kamar yanda Zaleeha take ƴa awajena, hakama Saifuddeen, shi ba iya ɗalibina bane kaɗai, inajinsa kamar jinina, saboda haka kuyi haƙuri, kujanye batunkun fasa auren, Zaleeha ƴatace kuma inada ikon tanƙwarata duk yanda naga dama, kuyi haƙuri ku ɗauka cewa duk waƴannan abubuwan da takeyi yarinta ne kuma zata daina watarana, tabbas nasan yanzu giyar ƙuruciya ne ke ɗibanta, nan gaba kaɗan bazatayi abun da tayi yanzu ba." Ɗan jim yayi tare da cigaba da cewa. "Kuyi haƙuri dan Allah, Amatsayina na Uba agareta na baku haƙuri, kuma kamar yanda kuke sha'awar haɗa zuri'a dani, haka nima nake sha'awar haɗa zuri'a daku, musamman Saifuddeen daba kowani uba bane zaiƙi son zamowarsa suruki agaresa, kamar yanda na faɗa muku tun daga farko babu abun da zan faɗa daya wuce nace kuyi haƙuri insha Allah aurennan ba fashi." Da sauri Malam Ashiru ya fara jujjuya kai a hankali tare da cewa. "A a Malam kayi hak'uri abar batun auren nan mu kam mun janye.....! BY *GARKUWAR FULANI* [30/08, 3:46 pm] +234 906 084 2867: Murmushi Baba Malam yayi irin nasu na manya, kana ya ɗanyi jim, haƙiƙa fasa auren Zaleeha bazai rage komai ba face mutuncinsa da kimarshi, mutuƙar kuwa aka fasa auren to tabbas ita da mahaifiyarta sun samu abun da suke so, sam shikuma bazai lamunci hakan ba, gyara zamansa yayi tare da kai dubansa ga su Baffa Ali da Malam Ashiru. Cikin nutsuwa haɗi da kamala yace. "Haƙiƙa nafahimci me kukeji agame da wannan auren, saidai kada ku manta mu daku ɗin kamar ƴan uwa muke,  dukanmu tsofaffine masu dattako da sanin ya kamata,  amatsayina kuma na mahaifi ga Zaleeha zan ƙirata na zaunar da ita nayi mata nasiha, insha Allah nasan zata fahimta, dan Allah kuyi haƙuri, rashin tunanine kawai irin na yaran zamani!." Ajiyar zuciya su Baffa Ali suka sauƙe, cikin sanyin murya haɗi da fahimtar Baba Malam ɗin, Baffa Ali yace, "shikenan Malam Basheer babu komai, Allah yasa auren ya zama al'khairi agaresu, Allah kuma ya sawa Zaleeha so da ƙaunar Saifuddeen acikin zuciyarta, don shikam yana sonta sosai, fatan mu shine auren nasu yayi al'barka!." Da "Ameen Ameen!." suka amsa su dukansu,  inda Baba Malam ya sauƙe ajiyar zuciya, sosai yaji girman na iyayen Saifuddeen ya ƙaru acikin idanunsa, nan suka ɗan tattauna maganganu masu muhimmanci, daga nan kuwa su Baffa Ali sukayiwa Baba Malam ɗin sallama,  har bakin motarsu Baba Malam ya rakosu, inda bai dawo cikin gida ba saida yaga tafiyarsu. Zama yayi akan ɗaya daga cikin tausassun royal chairs ɗin da suka ƙawata haɗaɗɗen falon nasa, bayansa ya jingina da jikin kujeran tare da lumshe idanunsa,  cikin ransa haka yakejin ba daɗi, tunda yake baitaɓa sanya ranan auren ɗansa ko ƴarsa daga baya kuma akazo da maganar fasawa ba sai akan Zaleeha! duk kuma a dalilin taurin kai irin nata, tabbas Zaleeha tanason sashi yaji kunya a idanun mutanen da suke matuƙar ganin ƙimansa, amma babu komai zaiyi abun tubkar hanci tunda wuri,  wayarsa dake cikin al'jihun rigarsa ya laluɓo inda ya dannawa nombern Mama ƙira, bugu uku ana huɗu Mama ta ɗauki ƙiran, batare daya jira komai daga gareta ba yace. "Kituromin Zaleeha." kitt ya kashe wayan, don sam baison abun dazai ɓata ransa da daren nan. Bayan kamar minti shida dai-dai Mama tashigo cikin falon hannunta ɗauke da ɗan madaidaicin tray wanda samansa ke ɗauke da flask da kuma ƙananan cup guda biyu,  bakinta ɗauke da sallama ta ƙaraso cikin falon, inda ta jawo wani babban table dake tsakiyan falon ta kawosa har gaban Baba Malam ɗin, nan ta ɗaura ɗan ƙaramin tray din akan table ɗin,  duban Baba Malam tayi fuska ɗauke da Murmushi tace. "Barka da hutawa!." Shima Baba Malam ɗin fuskarsa ɗauke da murmushi, ya jinjina mata kai alaman ya amsa. Su Baffa Ali kuwa koda suka isa gidan nasu Saifudden kai tsaye ɓangaren Ummi suka nufa,  zaune suka isketa ababban falon nata, gefenta kuwa Hayatudeen ne wanda keta faman buga game ɗin Drok Stack Ball awayarsa. ganinsu yasa Hayatuddeen ya gaishesu cikin ladabi, don kuwa hadda Dirankadi akazo,  nan ya miƙe ya haura sama zuwa ɗakinsa. Ummi kuwa tashi tayi ta kawo musu drinks masu ɗan sanyi,   nan ta zauna suka shiga ɗan gaisawa, musamman da Dirankaɗi wanda suka jima basu haɗu ba. Bayan sungama gaisawa ne, Dirankaɗi ya gyara zamansa tare da fuskantar Ummi'n, sanin cewa ita ɗin mai yawan haƙuri da sauƙin kai ne yasanyasa tausasa lafuzansa, tayanda zata fahimcesa sosai, ahankali yace. "Kamar yanda kika buƙata da muje gidan su Zaleeha, munje munkuma sanar musu cewar mun janye batun auren!.". Ajiyan zuciya sauƙe a hankali tare da cewa. "Alhamdulillah". murmushi suka ɗanyi, sai kuma Dirankadi ya ɗan numfasa tare da cewa. "Kiyi haƙuri Hajiya..  kisa aranki cewa auren Saifuddeen da Zaleeha haɗine na Allah bawai yin kanmu ba, sannan kada ki manta ance matar mutum kabarinsa, sannan idan Allah Ya nufa cewa Saifuddeen sai ya auri Zaleeha bamu isa hanawa ba." shiru tayi jiki a mace taci gaba da sauraronshi. "Tabbas nasan mekikeji nakuma fahimci irin fargaban da kike ciki, ƙwarai kowacce uwa bazata taɓa son wani abu dazai cutar mata da ɗanta ba, nasan kina gujewa Saifuddeen auren Zaleeha ne badon komai ba saidan, kina jin tsoron abunda kaje kazo, da kuma irin tsananin ƙiyayyar da Zaleehan ke nuna masa,  ƙwarai hakan abun tsorone to amma kada ki manta, babu wani abu dazai samu bawa me kyau ko akasinsa,  face dama tuntuni anrubuta acikin littafin ƙaddaransa." Kai ta gyaɗa tare da cewa . "Haƙƙun". Cikin jin daɗin tana gamsuwa yaci ga da cewa. "Wani baya taɓa iya cutar da wani harsai Allah Ne ya tsara hakan,  saboda haka inaso ki kwantar da hankalinki, munyi magana ta fahimta da mahaifin yarinyar, mutum ne shi mai tsananin dattako da kamala, kema kinsan hakan tuntuni, ya ƙasƙantar da kansa ya bamu haƙuri, ya haɗamu da Allah cewa kada a fasa auren! yakuma taushemu da lafuzza masu daɗi, saboda haka mu dai mun aminta cewa Saifuddeen zai auri Zaleeha, saboda haka yana ɗaya daga cikin ƙaddaransa, komai zai wuce kuma watarana sai labari, kema inaso kisa aranki cewa Insha Allah auren Saifuddeen da Zaleeha al'khairine mai tarin yawa, wanda zaisa dukkanmu farinciki anan gaba,   mudai addu'an al'khairi yadace munayi musu ako da yaushe!." Baffa Aline yaɗan nisa tare da amsawa da cewa. "Ƙwarai kuwa, abun da Dirankaɗi ya faɗa gaskiyace, haƙiƙa dukanmu nan munsan cewa ke uwa ta gari ce,  munsanki da haƙuri Ummi, dan Allah inaso ki ƙara akan nada, ki-kumayi duba da irin tarin soyayyar da Saifuddeen keyiwa yarinyarnan tunfa suna ƙanana, kuma rauninki zaisa Saifuddeen fasa auren nan!." Malam Ashiru ne yace. "Ƙwarai kuwa, ayanzu dai fatan al'khairi da sa al'barka kawai suke buƙata daga garemu." Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe tare dayin ƙasa da kanta, sosai taji zuciyarta tayi mata nauyi, yayinda matsanancin rauni ya bayyana acikin idanunta, haƙiƙa ita abu ɗaya take gujewa Saifuddeen shine halin dazai faɗa bayan aurensa da Zaleeha, matuƙar bata sanja hali ba, tasan Saifuddeen bazaiji daɗin zaman auren ba, wanda ita kuma duk wani fata da burinta baiwuce Saifuddeen ɗinta ya samu mace tagari, mai share hawayensa. Hawayen dake ƙoƙarin cika idanunta ta shanye tare da ɗan sakin murmushi, cikin sanyi tace. "Babu komai, duk yanda kukace shikenan, dama ni baƙin Zaleeha nake ba kawai dai munanan kalamai da ƙudurinta akan Saifuddeen shine ke bani tsoro, amma zantayi musu addu'a Allah yasa auren yazama alkhairi, wanda kowa zai amfana dashi!." Cikin jin daɗin sauƙin kai irin na Ummin dukansu suka amsa da "Ameen Ameen." Nan Dirankadi yace acigaba da shirye shiryen biki kada afasa komai da akayi niya, baiwani jima agidan ba yashiga motarsa inda ya nufi gida, su kuwa su Baffa Ali can cikin BQ suka sauƙa, saboda dare yayi babu yiyuwar komawarsu Dukku aranan, saidai gobe da safe zasu kama hanya. Jin ƙiran da Baban nata keyi mata yasanya taji gabanta ya faɗi, take tsoro ya shigeta saidai kuma babu yanda ta iya dolenta ta amsa ƙiran nasa, zumbuleliyar hijab ɗinta ta zura, kana tanufi ɓangaren mahaifin nasu. Da sallama ɗauke abakinta ta kutsa kanta cikin falon,   cikin sanyi Baba Malam ya amsa mata,   ƙarasowa tayi inda ta zauna akan lallausan carpet ɗin dake malale bisa tsakiyan falon, duƙunƙune jikinta tayi acikin hijabin, cikin ƴar siririyar muryarta dake rawa tace. "Barka da dare Baba Malam!." Kansa kawai ya jinjina mata alamar "Yauwa." Aƙalla ta ɗau sama da mintuna 5 baice da ita komai ba, nanfa bugawar zuciyarta ya tsananta, don amatuƙar tsorace take. Gyara zama Baba Malam yayi tare da fuskantar ta,  cikin kulawa yaƙira sunanta. Ɗagowa tayi ta kalleshi tare da amsa masa murya na rawa jiki asanyaye. Ajiyar zuciya Baba Malam ya sauƙe tare da yi mata duban tsab, cikin son tausasa lafuzansa agareta dan yi mta nasihar da wala Allah imaninta zai sabunta cikin kula yace. "Haƙiƙa kowani uba yana al'fahari da ƴarsa ko ɗansa matuƙar sukayi masa biyayya,." Sosai lafazinshi ya ratsa jikinta, Shi kuwa cigaba yayi da cewa.   "Bazance bana al'fahari dake ba Zaleeha saboda ke jininace, sannan kuma ko ba komai kin amshi zaɓin dana baki, kin kuma yi na am, saidai kuma labari yazo kunnena akan cewar kina rubuta saƙo irin na ɓaƙaƙen maganganu da kuma gargaɗi da barazana da kisan kai kina turawa Saifuddeen". Tuni jikinta yake tsuma.   "Kada ki watsamin ƙasa a ido Zaleeha! Dan in kikamin haka ,wallahi Allah zan barranta dake, kada kimin fuska biyu. tabbas nasan cewa rashin sanin wanene Saifuddeen agareki shiyasa kike wulaƙantasa, yanunamiki ƙauna da gata tun kina ƴar ƙanƙanuwan yarinya, haka kuma har kawo yanzu bai janye ƙaunarsa daga gareki ba,  Saifuddeen maganarci ne wanda nayi imani samun kamarsa nada matuƙar wahala, ba'akowani gida ne ake haihuwar irin Saifuddeen ba haka kuma irinsu basu da yawa acikin al'umma, nazaɓa miki Saifuddeen amatsayin mijine saboda nasan bazaki taɓa danasanin aurensa ba, Saifuddeen bazai barki kiyi baƙinciki ba Zaleeha." Tuni hawaye ke kwaranyo mata a ranta take faɗin. "Wannan musakin wanne farin ciki zai samar min,mutun da bashi da bakin da zai furta min kalaman so, mutumin dake kamar dutse duk daɗin kalmar da zan masa ba ji zaiba, haka zan rayu dashi babu so bare soyayya da ƙauna! muryar baban natane ya katse mata hasashenta. "Zaleeha kina ganin nakasasshe ne ko, to Saifuddeen da kike gani shi zai zame miki GARKUWA sannan bongo majingina na rayuwarki,  shin Zaleeha menene aibun Saifuddeen dan yakasance Nakasashshe? saboda shi nakasashshene shiyasa kawai kike gudunsa? Baki san cewa Nakasa Ba Kasawa Bace Zaleeha, kuma babu nakasasshe sai kasasshe musamman nakasa irin ta Saifuddeen da bata shafi lafiyarsa ba, sannan nakasar zuci itace nakasa ba wai ta gangar jiki ba,  Saifuddeen yana da kyakkyawar zuciya, kyawawan ɗabi'u, kyawawan halayya, ga  wadatan zuci  duk ya haɗa in kuma kyau ne tako ina Allah ya mishi kyau da haiba, haƙiƙa amatsayina na uba mahaifinki, ina matuƙar yi miki kwaɗayin samun managarcin miji kamar Saifuddeen, sanin cewa miƙa aurenki ga Saifuddeen danayi bazaisa nayi dana sani ba, shiya zuciyata ta aminta da shi sosai,  dan Allah Zaleeha, ki nutsu ki dawo cikin hankalinki, ki watsar da duk wani buri ki rungumi auren Saifuddeen amatsayin ƙaddarar rayuwarki,  kin kuma san idan kikayi haka Allah bazai bari ki taɓe ba,  ni mahaifinki ne Zaleeha, idan ban nusar dake ba, babu wani wanda zai nusar dake, saboda haka maganan tura ɓaƙaƙen maganganu ga Saifuddeen banasonshi dan Allah ki daina kinji ko Mamana?." A hankali ta gyaɗa kanta alamar to yayinda cikin zuciyarta kamar ta mutu dan baƙin ciki. "Saura ƴan kwanaki kaɗan yazamanto miji agareki saboda haka yazama dole ki girmamasa kamar yanda kike girmamani harma fiye da haka domin shi mijinki ne kuma al'jannarki tana ƙarkashi diga-diginshi ,sai ya ɗaga zaki shiga". A ranta take cewa. "Wannan gurgun kam ai ɗaga ƙafarma ba iyawa zaiba." hannu tasa tana share hawayenta jin Baba malam ɗiɓ yaci gaba da cewa. "Saboda matsayinsa na miji agareki yazama dole kiyi masa biyayya da ɗa'a, koda wasa kada kice zaki bijirewa umarninsa, ƙin bin umarninsa tamkar saɓawa Allah Ne saboda haka ki kiyaye!." Tuni hawaye sun wanke fuskar Zaleeha, sosai zuciyarta keyi mata ƙuna so take tasaki kuka mai sauti, hakan yasa tasanya hannuwanta duka biyu ta toshe bakinta, gudun kada kukan ya fito, kai kawai taketa gyaɗawa kamar Ƙadangaruwa. Ganin haka yasa Baba Malam cewa. "Tashi kije, sannan koda wasa kada ki taɓa mantawa da maganganu na, domin kuwa idan akace yau bana raye babu wani wanda zai faɗamiki makamancinsu." still kai ta gyaɗan Da sauri ta-tashi ta fice daga cikin falon, tana rufo ƙofar falon tashiga tafiya cikin yanayi na gudu-gudu sauri-sauri, koda ta shiga falo, tsaye ta samu Mama tanata kaiwa da komowa,  Mama naganin Zaleehan tayo kanta, cike dason tambayarta me Baba Malam ɗin yace mata, saidai me tuni Zaleeha ta shiga ɗakinta inda ta rufo ƙofar tare da murza mata key, sulalewa tayi ajikin ƙofar tare da sakin kuka mai sauti,   galala haka Mama tasaki baki tana kallon ƙofar ɗakin Zaleehan, kana daga inda take tsaye tanajiyo sautin kukan da  Zaleehan keyi, rantane yayi matuƙar ɓaci, domin tasan babu wani abu dazaisa Zaleeha kuka haka, idan ba maganar auren wancan nakasashshen ba, gashi tanaji tana gani aka kwashi kayan Abdussalam aka meda, tsuka tayi cike da baƙin ciki haɗi da takaici ta wuce ɗakinta. Kuka sosai Zaleeha tayi harsaida muryarta ta dashe, lokaci guda wani irin zazzafan ciwon kai ya kawo mata ziyara, gaba ɗaya ƙwaƙwalwarta ta toshe harta rasa ma tunanin me zatayi, kullum kwanan duniya soyayyarsa ne keyi mata tsaye acikin rai da zuciyarta, sannan gefe guda kuwa ga yanda rayuwa keneman juya mata baya, tahanyar haɗa ta aure da wani wanda takejin tsanarsa acikin zuciyarta fiye da kowa. Da ƙyar ta iya tashi daga jikin ƙofar, haka ta nufi bathroom, ko gani sosai bata iyawa saboda yanda idanunta suka kumbura sukayi luhu-luhu dasu,  wanke fuskarta tayi tare da dawowa ta kwanta luf akan lallausan gadonta,  sosai kanta ke ciwo kamar zai rabe gida biyu haka takeji, gawani irin zazzaɓi daya sauƙar mata, babban blanket ta jawo tare da rufe jikinta, kanta ta tura acikin pillow, sannu ahankali take fitar da sheshsheƙan kuka, cikin haka wani bacci wanda sam batayishi cikin daɗin rai ba yazo ya ɗauketa. ** Yau ya kama saura kwana biyu biki, inda ake ta hidima haɗi da shirye-shirye daga ɓangarori guda biyun,  gidan su Saifuddeen sosai ake hidima inda tuni ƴan uwansu dake nesa sun zo, nanfa shirin biki ya ƙara armishi, ɓangaren Ango Saifuddeen da abokansa kuwa sunshiga busy sosai, babuma kamar yashi Saifuddeen, gaba ɗaya yanzu bashida wani lokaci koda na hutawa ne, yadage tuƙuru wajen ganin yaƙawata bikin nasa, inda yaketa ɓarnatar da kuɗi wajen ganin ya ƙawatar da kansa da kuma amaryarsa,  gudumawa yake samu sosai takota ina, wanda abun har mamaki yake bashi, sam shi baison mutane suna wahalar da kansu akanshi, musamman ma akan auren nasa yafiso yayi komai da kanshi, haka ƙungiyarsu ta Jonapwd ma ta basa gudumawarta mai tarin yawa, wanda bisa dole ya amsa, don ƙa'idar ƙungiyanne dazaran abu ya samu mutum na hidima, walau farin ciki walau akasinsa, to fa saisun bada nasu taimakon suma. Birnin gombe da kewaye duk sun cika sun ɗauka batun auren Zaleeha da Saifuddeen wanda aketa tallashi a dukkan gidajen Radio kama daganan FM Gombe, PROGRESS, RAYPOWER, AMANA uwa uba, vision FM gidan radio su Zaleeha, yan uwa ƙawaye maƙota ,duk anji labari, Bilkeesu kuwa da gangan ta sanarwa duniya mijin da Zaleeha zata aura nakasasshe ne, wannan abun ya ƙara tada hankalin Zaleeha. Rashida kuwa tuni ta gayyato ƙawayensu baki ɗaya harda waɗanda sukayi aure, haiƙan gadaran suketa shiryawa bikin ita da sauran ƙawayen nasu. Kamar yanda ake ta shirye shirye shiryen biki agidan nasu Saifuddeen cike da farin ciki, aɓangaren gidansu Zaleeha kuwa abun ya banbanta, domin kuwa Baba Malam da Mamy haɗi da su Ya Ahmad ne kaɗai suke shirin auren, sai kuma Mamy wanda tazama kamar itace uwar amarya, don Mama kam fir tamaƙi zama agidan hakanan ta tsiro da tafiya garinsu, tayi hakanne kuma don bazata iya juran tarin baƙin cikin dake tunkarota ba, sam Baba Malam baihanata ba, dan yasan hanatan ma wani babban bala'i zai zama, kuma tama tafi ta basu fili ayi komai ba fitina, shiyasan tunda Mamy nanan bai da muwa da tafiyar Mama. Ita kuwa Mama bazama tayi gidan bokayenta. Yau Baba Malam yace aje ayiwa Amarya Zaleeha jere, saboda haka tun safe Aunty Lubna da kuma Maryam, sai wata Aunty Aseeya wacce take ƙanwar Mamy sai Aunty Shatu suka kimtsa don zuwa yin jeren,   cikin motar Aunty Aseeyan suka shiga, inda aka haɗasu da ƙatuwar motar dake cike da kayan na Zaleeha wanda su Baba Malam ne ya ƙara matasu duk dan wai ta kwantar da hankalinta, daga gefe kuwa musamman Ya Ahmad yayiwa wani babban company magana, wanda suke da ma'aikata wanda suka iya tsara ɗaki, nan yaɗauki hayan ma'aikata guda biyu wanda sune zasu tsarawa Zaleehan ɗakin nata. Koda suka isa gidan nasu Saifuddeen wanda sosai ya amshi gyaran da akayi masa, Ummi da kanta ta amashesu, inda tayi Musu tarba me kyau, sosai sukaji daɗin hakan, inda Maryam tacika da farin ciki, domin kuwa sosai taji daɗin karamcin Ummin, dan tasan Zaleeha ta dace da uwar miji, sannan tasan Ummi bazata bar ƴar uwartata ta wulaƙanta ba,   Raihana mutan Kd da Adda Rahma matar Dr Ummi tasanya su kaisu zuwa ɓangaren Zaleeha,   koda sukaje part ɗin da Zaleehan zata zauna sosai suka cika da mamakin yanda aka ƙawata part ɗin, sosai part ɗin yayi kyau, anyi masa tsari mai ɗaukar hankali, inda aka ƙawata komai dake cikinsa,  tabbas sun yaba da haɗuwar part ɗin na Zaleeha, sunkuma yarda cewa Saifuddeen masoyine agareta, don ko ba a faɗa musu ba sunsan sosai ya ɓarnatar da dukiyansa wajen ƙawata wajen,    tuni ma'aikatan da Ya Ahmad ya turo suka haɗu da maikatan da Salisu ya ɗauko sun shiga aikinsu na shirya wajen don kuwa har sun gama kimtsa falo,  sabida su biyarne dan haka aikin ke gudu, sosai falon ya tsaru haɗaɗɗen falone wanda aka ƙawata gaba ɗaya jikin bangon da wani haɗaɗɗen magic paint me tsananin kyau, yayinda aka watsa wasu   haɗaɗɗun royal chairs atsakiyan falon, kujerune ƴan ubansu wanda aka narka kuɗi sosai wajen sayansu, asalin royal ne masu kyau da tsada, inda kalansu suka kasance milk colour and light sky blue sai kuma ratsin golding ash dake jiki,  sosai kujerun sukayi kyau, yayinda aka malale wani lallausan carpet mai taushin gaske a tsakiyan falon, wanda dazaran ka takashi ƙafafunka zasu nutse aciki saboda tsabar laushi,inda shima yake da kalar milk, and sky,   da wasu irin tsadaddun cottings aka ƙawata jikin window da kuma ƙofar falon, kalan cottings ɗin sun kasance ligh blue irin mai hasken nan,  sannan gaba ɗaya cottings ɗin simples suke basu da wani ado, sai ɗan ratsin golding ash kawai dake jikinsu, cotting ne masu azabar kyau da tsada, wanda suka ɗai ma sun isa ƙawata kyawun ɗakin,   can gefe kuwa wani irin ƙaton tv plasma ne wanda saboda tsabar girmansa yasanya ba'a kafasa ajikin bango ba, kan wani haɗaɗɗen table na glass aka ɗaurasa, wanda kalan table ɗin yakasance sky blue, sai kuma adon jikinsa daya kasance golding ash mai walwali,  gefe da gefen tv'n wasu irin haɗaɗɗun flowers aka sanya guda biyu, ƴan madaidaita, inda flowers ɗin suka kasance kowanne da kalansa, ɗaya milk ɗaya kuma sky, sosai haka ya ƙara ƙawata haɗuwan falon, can gefe kaɗan kuwa, rantsatstsen dinning area ne wanda aka ƙawatasa da haɗaɗɗen decoration mai masifar kyau, inda aka shirya wasu haɗaɗɗun royal chairs wanda suke kalan kujerun dake cikin falon saidai kuma yanayin tsarinsu baizo ɗaya ba, tsakiyan kujerun kuwa wani babban table aka sanya me masifar kyau,  gaba ɗaya falon walwali dake sheƙi yake inda yake fidda ƙyallin haɗuwa, sam ba acika shirgi acikin falon ba, komai antsarasa ne cikin nutsuwa da wayewa, sosai su Aunty Lubna ke yaba falon, saboda ko ƴar gwamna sai haka, sosai Yaya ahmad ya kashe maƙudan kuɗaɗe wajen sayan kayan furnitures ɗin, saboda yana matuƙar son Zaleeha taji daɗi ta zauna ɗakinta shiyasa zai iya kashe ko nawane akanta. Koda suka ƙarasa zuwa bedroom nansuka samu tuni angama shirya komai, inda acikin ɗakin ma aka zuba wani haɗaɗɗen furnitures mai azaban kyau,  don kuwa haɗaɗɗen royal bed mai kalan white and golding aka kafa mata, inda saman kan gadon ya kasance light blue colour,  sosai gadon ya tsaru da ado haɗi da ƙyale ƙyale irin na zamani, yanayin tsarin gadon kaɗai ya isa nusar dakai cewa ba ƙiran Nigeria bane, inda ajikin gadon akayi wasu haɗaɗɗun bedsite masu kyaun gaske,  gefe da gadon kaɗan kuwa wani tangamemen drawer ne wanda aka cika jikinsa da wani irin zanen ado mai masifar kyau haɗi da wani irin mirror glass me matsanancin kyau, kana can gefe kuwa wani haɗaɗɗen dressing mirror ne me kyaun gaske,  sai kuma stool ɗin sa wanda shima aka ƙawata jikinsa da ado mai ɗaukar hankali, again kuma wani dressing mirror ne ɗan madaidaici mai kyau aka aje aɗan gefe kaɗan,   tsananin tsaruwan da ɗakin yayi yasanya gaba ɗayansu suka shagala, tabbas ɗakin Zaleeha ya ƙawatu iya ƙawatuwa ko aturai al'barka,  komai dake cikin ɗakin abun so da burgewane, tabbas idan za a ƙiyasta kuɗin furnitures ɗin a iya ɗakima kaɗai banda parlour kayan sunkai na 4 million,  domin kuwa kayane masu masifar kyaun gaske,  haka suka dinga yaba kayan, koda suka buɗe bathroom kuwa mamakine yakusan kashesu, sosai aka ƙawatasa kamar ba bathroom ba,  inda wajen wanka ma na glass akayi mai masifar kyau wanda shi kaɗai ya isa ɗaukar hankalinka, sannan gefe ga wani haɗaɗɗen jakuzzie wanda aka ƙawatasa sosai, koda suka fito daga ɗakin na Zaleeha ɗayan ɗakin dake gefen nata suka shiga, don dama 2 bedrooms ne acikin falon,  shima sosai aka zuba masa wasu haɗaɗɗun furnitures masu kalan grey, sosai shima ɗakin yayi kyau, fitowa sukayi daga ɗakin inda suka ƙarasa zuwa cikin kitchine ɗin dake cikin falon, hmmmm wani kaya sai amale, anan fa haɗuwar take, komai dake cikin kitchine ɗin light pink and white colour ne,  sosai aka ƙawata kitchine ɗin, inda aka shirya komai na amfani acikinsa tsab,  da wasu zafafan food flask aka ƙawata jeren kitchine ɗin wanda aƙalla kowanni food flask ɗaya yakai 100k wato dubu ɗari, wani kamma harda ɗori, kaya masu kyau da inganci aka zuba acikin kitchine ɗin, tabbas Zaleeha kam anyi mata auren gata, Ya Ahmad da Baba Malam sun kashe mata kuɗi na fitan hankali wai duk dan su faranta mata rai ko sa samu ta zauna ɗakinta tayiwa mijinta biyayya,  haka dai suka dinga zagaya part ɗin suna yabawa da kyawun komai, inda Aunty Lubna ke ɗaukar komai awayarta, saboda haɗuwan kayan ya zarce misali. A sashin Saifuddeen ma a ranar aka shirya mishi sabbin kayan gadonshi masu masifar kyau, abundai sai wanda ya gani. Basu sukabar gidansu Saifuddeen ɗinba sai da sukayi sallan la'asar, bayan sun cika cikinsu da daddaɗan girkin Ummi, inda tayi musu haɗaɗɗiyar fried rice wanda yaji chicken, sai kuma kunun aya mai masifar daɗi,  ga kuma dambun kifi wanda yaji kayan ƙamshi, sosai sukaci abincin don yayi musu masifar daɗi, haka sukayi sallama da Ummi cikin girmamawa kana suka kamo hanyar dawowa gida. Itadai Zaleeha duk wannan wainar da ake toyawa babu idanunta aciki, don tun jiya takulle kanta aɗaki, bata fita koda cikin falo ne, hasalima zazzaɓi ne ke ɗawainiya da ita kwana biyun. A dare randa akaje akayi mata jeren ne, tayi mafarkin wai tana ɗakinta na gidan Saifuddeen ɗin tana zaune kan gadon, sai ta hango wani ƙaton maciji baƙiƙƙirin dashi yazo bakin ƙofar ɗakin nata yayi zuɗuɗuɗu ya shige ƙarƙashin gadonta, tana ganin har ya gama shiga ta kasa ihi ko neman taimako, saida taga binɗinshi ma ya shigene, sai kawai ta miƙe a guje ta fita daga ɗakin ta bar gidanma baki ɗaya, tanata gudu bata san inda zata jeba sai Mamanta da Bilkeesu da Ruda ta nuna mata bakin kogi, kawai sai ta nufi cikn kogin har ta fara nisa cikin ruwan da zai iya cinyeta sai taga wani farin dottijo bafulatani ya riƙo hannunta sun fita. To anan ta farka daga baccin kuma sai ta tashi da zazzafan ciwon kai. hakan yasa sam batason hayaniya. Musamman Mamy ta sa aka ɗauko mata ƙwararriyar mai zanen lalle da kitso don tazanawa Zaleehan, amma haka Zaleeha ta tubure tace sam ita babu wani lalle da za ayi mata, koda taga Mamy ta matsa kawai saita sa kuka, dan dole haka Mamy ta ƙyaleta, duk wani gyaran amarya kuwa dasuka shirya yi mata haka taƙi basu haɗin kai duk wani abun da za'a bata ace tasha ko taci sai ta buɗe musu shafin kuka, bisa dole suka ƙyaleta, itakuwa Zaleeha shawaran Bilkeesu ne ke yawo acikin ƙwaƙwalwarta, don kuwa Balkeesu ce tayi mata huɗuba akan kada ta yarda ta amince da komai na hidiman bikin, aure ne dai tabari a ɗaura idan yaso bayan an ɗaura auren an kaita gidan musakin plan ɗinsu da suka shirya zai soma aiki. Koda Rashida dasu Aunty Lumbna da Maryam a Mommy matar Malam Adam sukazo mata da zancen walima ƙi tayi fir taƙi yarda akayi ganin zata kunyatasu yasa suka shereta. Yau takama ranan jumma'a inda gobe take asabar wato ranan ɗaurin aure kenan, sosai su Saifuddeen suka shiga busy fiye dako yaushe,  hidiman ɗaurin auren na gobe kawai suketayi. Ɓangaren su Hayatuddeen da abokansa suma ba'abarsu a baya ba, don musamman suka ɗinka zafafan shaddodi wanda zasuyi fitan bikin dashi, inda Saifuddeen da kansa ya saya kowannensu haɗaɗɗen getzner wanda zasu saka wajen dinner inda kalan kayannasu ya kasance daban dana abokan ango. Tunda aka fara hidiman bikin har kawo yau Saifuddeen bai nemi Zaleeha ba koda awaya ne, duk wani abu na hidiman biki da  Rashida da Amira ƙanwar Ya Aminu a sauran ƙawayenta naa gari sukeyi don sunbasu haɗin kae sosai, Bilkeesu kuwa sai tsula rashin ɗa'a takeyi. Adaren na Jumma'a ne zazzaɓi mai zafi ya rufe Zaleeha, haka taƙi sanar da kowa saima ɓoye kanta da tayi inda ta duƙunƙune acikin bargo tana rawan sanyi, fatanta ɗaya shine Allah yasa ma zazzaɓin yazamo sanadin mutuwarta ta huta da baƙin cikin rayuwa. Ɓangaren Dalla kuwa aranan yaransa sukazo masa da labarin gano gidansu Zaleeha, harma da wajen aikinta, nan Dalla yacika da matsanancin murna, sai-dai kuma murnar tasa taso komawa alokacin da suka sanar dashi labarin aurenta da ake shirin ɗaurawa gobe, inda suka sanar masa cewar wani kurma kana gurgu zata aura, dariyan mugunta Dalla ya fashe dashi, inda yace.   "Ta kwana gidan sauƙi" nan yatsara irin rashin mutumcin da zaiyi mata,  nan ya ƙudurta aransa cewa dazaran an ɗaura mata aure da gurgun mijinnata ayayin da ake ƙoƙarin ɗaukan aure alokacin shikuma zaisa yaransa su ɗauko masa ita, tabbas shine zaisha wannan romon budurcin, al'ƙawari yaƴiwa kansa cewa saiyayi mata dalla-dalla tayanda bazata sake moruwaba. Saturday. 26/january/2019 Rana bata ƙarya. Ranan yau takasance wata muhimmiyar rana awajen Saifuddeen da duk wani mai ƙaunarsa, haka ranan tayau takasance wata rana wanda Zaleeha bazata taɓa mantawa da itaba a iyaka tsawon tarihin rayuwarta, ayau ne baƙin cikinta yafi na koyaushe ninkuwa acikin zuciyarta, ayaune takejin tsanan kanta da rayuwa fiye da kullum, ayau tanaji tana gani zata zama mata ga ga wani ba wanda ya taimaketa ba zata zama matar wancan mutumin da kyawawan manyan idanunshi ke bata tsoro. Federal lowcost. 9:30 am, gaba ɗaya gidan nasu acike yake da jama'a, ƴan uwa maza da mata haɗi da abokan ariziki, ko ina dake cikin gidan cike yake da mutane kowa ka gani fuskarsa ɗauke take da zallan farinciki. Can ɓangaren Saifudden nake jiyo hayaniyan mutane hakan yasa natafi don na duba meke tafiya acan, gaba ɗaya falon nasa cike yake da abokansa maza su, Ahmad, Jabeer, Ishaq, Saminu mijin Raihana, Wareesu, Saleesu, Mudassir, ibrahim, Rabi'u, Hisham, Jabeer da kuma abokanshi da sukayi karatu tare Hashim, Jafar,Abdulhakim. Gaddafi, Aziz da dai sauransu gaba ɗaƴansu sanye suke da tsadaddun shadda ƴan ubansu yayinda kowanne daga cikinsu yayi kyau sosai, gaba ɗayansu cike suke da farin ciki, domin dama ganin auren Saifuddeen ɗin shine cikar burinsu. dan duk da suna tare da taraddadin kar dai nakasar Saifuddeen tashiafi mazantakanshi to shiyasa ganin aurenshi shine burinsu. Ahankali yake murza wheellchair ɗinsa, inda ya ƙarasa zuwa gaban dressing mirror, cikin nutsuwa yake shafawa haɗaɗɗiyar surar jikinsa body lotion, koda ya kammala cumb ya ɗauka inda yashiga taje lallausan sumar dake kansa, wanda ya kwanta luf-luf kamar ƙawataccen sajen dake kwance akan fuskarsa, body spray ya fesa ajikinsa me daɗin ƙamshi, kana ya tura wheelchair ɗinsa zuwa kan gadonsa, inda anan ya aje kayan da zai sa. Cikin yanayi na nutsuwa da alamun gajiya da ɗan kazar-kazar ɗinshi kamar yanda ya saba ako da yaushe ya zura dogon wandon haɗaɗɗiyar getzner mai kalan white ajikinsa, yana gama saka wandon ya sanya rigar wacce ta kasance half jumper, cikin nutsuwa ya ɗauko babban garen kayan wanda aka yajiwa wani irin fitinannen aiki da surfani blue colour mai masifar kyau, cikin nutsuwa ya zurata akan rigar tasa, lokaci ɗaya yayi wani irin azababben kyau mai tafiya da zuciya, ahankali ya zura wasu haɗaɗɗun toms ƙiran Italy aƙafafunsa masu azabar kyau da tsada, yayinda takalman suka kasance blue colour, wato kalan aikin garen jikinsa kenan, wasu tsadaddun links masu tsadan gaske yasanya ahannuwan rigar, kana yaciro wani tsadadden wrist watch mai tsananin kyau da tsada daga cikin wani ɗan ƙaramin box, agogon rolex ne me masifar kyau, ɗaura agogon yayi ahannunsa na dama tare da ɗaukan haɗaɗɗiyar hulansa mai tsada wacce take da kalan blue ajikinta yasanya, tare da dai-dai-ta zamanta akansa. Tabarakallahu ahasanul khaliƙiyn! wani irin fitinannen kyau Saifudeen yayi wanda tunda yake bai taɓayin irinsa ba, gawani azababben kwarjini da yayi, wani irin ƙyalli da walwali fuskarsa keyi, sajen nan nashi yayi lib-lib akan farar fatar kekyawar fuskarshi, jajayen laɓɓansa sai sheƙi sukeyi tamkar ya shafa musu mai, gashin girarshin nan ya kwanta lib gwanin ban sha'awa, yayinda getzener ɗin jikinsa kuwa keta shinning, getzner ne me masifar tsada da kyau, wanda aƙalla kuɗinta yakai 95k, sosai kuma kayan suka amshi jikinsa. cikin nutsuwa ya ƙarasa gaban dressing mirror, kallon kansa yayi acikin madubin tare da sakin murmushi, shi kansa ya aminta da kyawu haɗi da cikar halittan da Allah yayi masa, shiyasa akullum yake gode masa, tabbas Allah abun godiya ne, sam bazai iya fasalta matsanancin farin cikin dayakejin kansa aciki ba, yau zuciyarsa zata samu cikar muradinta, wani haɗaɗɗen parfumed mai ƙamshi ya fesa. Kana ahankali ya danna madannin kekensa, kaitsaye ya nufi hanyar fita daga cikin ɗakin, buɗe ƙofar yayi ya fito ahankali, idanu su Ahmad suka zuba masa, baƙaramin kyau yayi ba, wanda sukansu maza ƴan uwansa sun ƙyasa da gayun nasa inaga mata kuma? sosai suka shiga yaba tsantsar kyawun nasa, inda Ishaq keta tsokanansa, shidai Saifuddeen sai murmushi kawai yakeyi don kuwa yau yana cikin farin ciki, nanfa dukansu suka shiga yi masa hoto, bayan sun gama yi masa hotonne kuma suka shiga ɗaukan selfie dashi, inda sukayi kyau sosai, zuwa lokacin ƙarfe 10 har da kusan rabi tayi hakan yasa suka ɗunguma sukai waje, don kuwa ƙarfe 11 dai-dai ne za a ɗaura auren. A falon Ummi kuwa tana ganin fitowansu ta ratso gefe tana zuwa Adda Rahma da Raihana da Raliya suka biyo bayanta, kanshi ta dafa tare da cewa. "Allah ya bada sa'a Babana , yau kayi kyau sosai irin kyan da ban taɓa ganin kayiba." Amin Amin sukace baki ɗanyansu, shi kuwa Saifuddeen alama ya mata da ya gode, su Adda Rahama kuwa selfie suketayi dashi. gannin zasu ɓata lokacine Salisu yace. "Adda Rahma ku barmu mutafi". to tace kana suka barsu. Acan compound ɗin gidan kuwa su Hayatudden da abokansa ne tsaye, sosai matasan yaran sukayi kyau cikin shigarsu ta shadda sky blue wanda yayi masifar amsarsu, dukansu cike suke da farin ciki inda suketa ɗaukan hoto da sabuwar wayar ta Hayatudden iphone 7+ wanda Saifuddeen ne ya saya masa, fitowar su Saifuddeen yasa dukansu suka maida hankalinsu garesu, tuni Hayatuddeen ya shiga santin irin kyawun da Hamman nasa yayi, nan yashiga ɗaukan Hamman nasa hoto, daga bisani kuma yashiga yi musu selfie. Cikin yanayi naɗan sauri sauri kowanne ya nufi mota don kuwa lokaci nata ƙurewa, wata zazzafar RANGE ROVER black colour sabuwa dal mai azabar kyau da sheƙi da ƙyalli Saifuddeen ya shiga, wanda musamman ya sayeta saboda da ita yakeson yin hidiman biki, Ishaq ne yashiga gefensa ya zauna, su Ahmad kuwa kowa motarsa ya shiga hakama sauran abokansa baki ɗaya dan babu ƙaranta, yayinda aka warewa Hayatuddeen da abokansa motarsu guda ɗaya zazzafa wanda suma da ita zasuyi chilling ɗinsu wajen bik. su Baffa Ali da Malam Ashiru kuwa wata haɗaɗɗiyar mota ƙiran mercedes suka shiga don sune suke matsayin iyayen ango, Dirankaɗi ma yazo da abokansa, inda su Alhaji Khabeer da Alhaji Ibrahim, haɗi da Alhaji Ishaq Ba miskila, San Husssain Alhaji Yawale Alhaji Aliyu mai dilan leda Malam Habu dama sauran manyan ya kasuwa duka Ya Rabi'u ma yayan Ishaq na Abuja yazo haka Dr Aliyu .Ya Adnan da abokan shi hakama bappa Ali da abokanshi da abokan Abbansu Saifuddeen suma sunzo don halartan ɗaurin auren, gaba ɗaya haka motocinsu sama da talatin da biyar suna jera reras akan titi line by line haka suke tafiya cikin nutsuwa. Duk inda jeren motocin suka wuce sai anbisu da kallo ahaka har suka isa cikin unguwar NEW G.R.A, can gefe sukayi parking motocinsu, don kuwa ƙofar gidan su Zaleeha cike yake da mutane maƙil, manyan malamai, manyan ƴan kasuwa, da kuma ƴan siyasa duk sun samu zuwa ɗaurin auren, saboda Baba Malam mutum ne da sunansa ke yawo acikin Nigeria, kusan kowa ya sanshi, kana ga Yaya Ahmad da sanadinshi yasa pilot suka rinƙa dirowa birnin gombe da jiragensu dan halartan ɗaurin auren ga kuma sojojin da ys Aminu suma sun gayyato nasu mutanen. Raveel ma ya gayyato duk abokan aikinsu. Isowar su Saifuddeen yasanya gaba ɗaya kallo ya dawo kansu, kowa kallon Saifuddeen yakeyi, wanda nagarta haɗi da haiba da kwarjini da kamalarsa ya cika idanun mutane, sam basai an faɗa maka ba da kallonsa zakagane cewa shine angon, sai-dai kuma da yawa suna mamakin kasancewarsa gurgu. Cikin mutunta juna Baba Malam da tawagarsa suka amshi su Saifuddeen, kamar yanda lokaci baya jinkiri wajen zuwa 11:00 am dai-dai dubbanin jama'a suka shaida ɗaurin auren SAIFUDDEEN Muhammad Ahamad Dukku da kuma ZALEEHA Bashir Sulamain Dukku akan sadaki naira dubu ɗari...! Littafina na kuɗine duk wanda ya fiddamin shi aradun Allah yaseeeeeeeen doooooooguwa buluƙutu baƙar mutuwa! *BY* *GARKUWAN FULANI* [01/09, 10:05 am] +234 803 620 1562: *Wannan shafi nakine kyauta gareki kekyawar ƴar jaridar vison FM Gombe inai miki fatan al'khairi Zaleeha Babangida Hari mai shirin Babu Nakasasshe sai rago, dake da jonapwd gombe inai muku fatan al'khairi godiya ta musamman gareka malam ishaq* _ZAIBA MASU KARATU KADA KU SAKE A BAKU LABARI BIYA ƊARI 200 KACAL ki samu littafin Zaiba na Ummee Garkuwa littafi ɗaya maidarrusa da dama karanta Zaiba kisha dariya tausayi shauƙi bege ƙauna karanta Zaiba kisha barkwanci Sufi ga masu buƙata ku nemi Ummee Garkuwa 08037251895 ta wannan number_ Wani irin matsanancin farin ciki ne mai tarin yawa ya cika zuciyar Saifuddeen, haƙiƙa yau takasance rana ta mussaman agaresa ranan da bazai taɓa mantawa ba acikin ƙuɗɗin tarihin rayuwarsa, cikin ikon Allah yau gashi Zaleeha ta zamo mata agaresa, zata rayu cikin ƙarƙashin iko da damansa, zata zama itace aƙasansa ta tabbata matar nakasasshe, wani irin ƙayataccen murmushi kawai Saifuddeen ke sakewa, hakanan yakejin kansa dai-dai da kowani cikakken namiji,  cikin son tayasa murna Mutane suka dinga bashi hannu suna musabaha, kowa sai Allah yasanya al'khairi yakeyi masa,   haka yadinga amsar hannun mutane masu tayasa farinciki, hatta Ahmad da bawani son auren yake sosae ba yau yayi farinciki saboda auren Saifuddeen babban abune awajensu. Kasancewar al'adan ƴan Gombe ne yin receiption bayan an gama ɗaurin aure to hakanne takasance ga Saifuddeen domin kuwa tuni sun tsara haɗaɗɗen receiption wanda zasu koma gida shida abokansa da kuma wasu daga cikin jama'ar ɗaurin auren don suyi, haka suka shiga mota aka nufi gidan nasu Saifuddeen. Zazzafan zazzaɓine ajikinta har zuwa yau ɗin, yanzuma duƙunƙune take acikin blanket gaba ɗaya jikinta sai faman rawan ɗari yake, tun daga ɗakinnata tana iya jiyo sauti da hayaniyan mutane, wanda hakan shike ƙara affecting ɗinta, hartanajin kanta kamar zai rabe gida biyu, kwata kwata batason hayaniya,  turo ƙofar ɗakinnata akayi, Aunty Lubna da Maryam, da kuma ƙawarta Rashida ne suka ƙaraso cikin ɗakin, ganinta still a duƙunƙune cikin blanket yasanya su ƙarasowa daɗan sauri, Maryam ne taɗan yaye blanket ɗin tare da kai hannunta jikin Zaleehan nan taji zafi jau,  "Subahanallahi! dama bakida lafiya ne Zaleeha?". taƙare maganar tana me ƙara taɓa jikin Zaleehan. "Zaleeha!." Aunty Lubna taƙira sunanta, ahankali ta ɗan buɗe rinannun idanunta ta kalli Aunty Lubna'n, murmushi Aunty Lubna tayi mata tare da zama agefen gadon,  ganin haka yasa Zaleeha ta haɗo duka ƙarfinta tashi tayi taɗan zauna tare da jingina bayanta da jikin saman gado,  hannu Aunty Lubna tasanya ta dafa kafaɗan Zaleehan cikin kulawa da kwantar da murya tace. "Ki daina sa damuwa aranki Zaleeha, musamman a irin wannan ranan, yakamata ace yau kin aje duk wani makamen yaƙi da auren nan da kika ɗaura, sannan kin kori damuwa daga gareki,  ayanzu damuwar da zaki sa kanki bazai taimakeki da komaiba Zaleeha, babu amfanin wannan ƙuncin, yanzu lokacin da zaki bari zuciyarki ta huta ne, ayau kuma ayanzu an ɗaura aurenki da Saifuddeen, zaifi kyau ki rungumesa amatsayin miji bawai maƙiyi ba, saboda duk yanda kikakai ga ƙinsa, yanzu kin zama mallakinsa, zaki zauna aƙarƙashin ikonsa, yanzu komai zakiyi saida izininsa, saboda Allah yace girman miji ya zarce na iyaye, haka ku girmama mazajenku tamkar yanda zaku girmama iyayenku, harma fiye da haka, dan Allah Zaleeha kiyi haƙuri hakanan damuwar nan kibarta!." Aunty Lubna taƙare maganar cikin lallashi. Kuka Zaleeha tasanya tare da rumtse idanunta, wani irin ɗaci takeji amaƙoshinta, yayinda zuciyarta keyi mata zafi,  tabbas anyi mata abunda bataso, an aurar da ita ga wani ba mutumin da tafi so fiye da kowa ba,  take taji matsanancin tsanar Saifuddeen ya ƙara ninkuwa acikin zuciyarta, hartanajin zata iyayin komai don ganin ta nesanta kanta dashi, sannan kuma ta tozarta igiyar aurensa dake kanta, al'ƙawarine saita wulaƙanta aurensa, sam bazata zauna da nakasashshe ba!. Cike da tsananin tausayinta Maryam ta kamo hannunta, cikin yanayin sanyinta tace. "Zaleeha ke ƙanwatace, jini ɗayane ke yawo ajikinmu, tabbas inason duk wani abun da kikeso, haka kuma inaƙin abunda kike ƙi, saidai kuma Saifuddeen ba abun ƙi bane, irin Saifuddeen mata da yawa ke fata da burin samu amatsayin miji, kada ki taɓa dubansa da nakasarsa, domin NAKASA BA KASAWA BACE, haka kuma nakasa bata zama ciwo matuƙar ba nakasar zuciya bace, tabbas ina tayaki farincikin samun Saifuddeen, saboda inaji ajikina ko anan gaba koda bayan raina nasan cewa ƙanwata tasamu managarcin mijin dazai zame mata garkuwa, na tabbata koda ace yau kowa namu zai ƙare abarki ke ɗaya, bani da kokonto akan saifuddeen saboda nasan zai riƙeki da amana, bakuma zai taɓa bari ki wulaƙanta ba, nasan ayanzu kina ganin laifin Baba dama su Ya Ahmad da Ya Ameenu saboda sun aura miki wanda bakyaso." Ɗan tsagaitawa da maganan maryam tayi tare da sakin murmushi,  ahankali ta cigaba inda tace. "Watarana zakiyi alfahari da Baba Malam Zaleeha, zakuma kiji cewa yayi miki zaɓi irin wanda kowani uba ke fatan yiwa ƴarsa, tabbas nasani komin jimawa saikinyi al'fahari da zaɓin Baba Malam, sannan kuma kada kimanta cewar duk wanda yayi biyayya ga Iyayensa to har abada baya taɓa taɓewa." Duk wannan maganganun da Maryam keyi Zaleeha bata buɗe idanunta ba haka kuma hawaye basu bar tsiyaya daga cikin idanun nata ba,  zuciyarta tayi tauri, ɓacin rai ya cikata, tsana ƙiyayya masu tsanani, sun riga da sunyi tasiri acikin jikinta da ƙarfin sirin da Ruda ke zuƙa Mama suna banka mata, saboda haka babu wani magana daza a faɗa don atausasata da zaiyi aiki acikin ƙwaƙwalwa da zuciyarta, hasalima ji take kamar ana ƙara mata yawan tsanar Saifuddeen ɗinne. Duban Rasheeda Aunty Lubna tayi cikin kulawa tace, "Rasheeda kiyi abun daya dace, tasamu tayi wanka bari naje nakawo kayan da zata sa." "To" Rashida ta amsa zuciyarta cike da tausayin Zaleeha, saidai kuma ta wani ɓangare wautan Zaleeha kawai take gani. Su Aunty lubna na fita, Rasheeda ta kamo Zaleeha, da ƙarfi Zaleeha ta fusge hannunta daga na Rashida, cikin yanayi na faɗa-faɗa zaleeha tace. "kada ma kice zaki faɗamin komai Rashida, babu abun da zaki faɗa min wanda zan fahimta, sannan kowani kalma zaki faɗa, zakiyi asaran yawun bakinki ne kawai, dan koda wasa bazan taɓa ɗauka ba." Murmushi Rashida tayi tabbas tasan Zaleehan tana cikin ɓacin rai da baƙinciki, hakan yasama bazata biyeta ba, tasan tanajin haushinta ne saboda tabawa Saifuddeen da abokansa haɗin kai   wajen ganin antsara abubuwan biki sun tafi dai-dai. Dawowar Aunty Lubna ne ta lallaɓa Zaleehan inda ta haɗa mata ruwan wanka,  ko acikin toilet ɗin da ƙyar Zaleehan ta iyayin wanka, domin gaba ɗaya jikinta babu kuzari, tana fitowa daga wankan aunty lubna ta kamata inda ta zaunar da ita akan stull,  da ƙyar ta iya shafawa jikinta mai,  aunty lubna dakanta taɗanyi mata light meckup akan fuskarta kasancewar tasan ba isashshen lafiya bane da ita,  yimata meckup me yawa kaman takurata ne,  doguwar rigar bababar  atamfar chiganvy  me kalan ja aunty lubna ta bata tace ta sanya, kanta yafara ciwo sosai hakan yasa batayi musuba ta amsa, ta zura ajikinta, sosai ɗinkin rigar tayi kyau yayinda tabi jikinta ta lafe, rigar irin A shape dinnan ne me faffaɗan hannu, an ɗameta daga ƙirji zuwa ciki yayinda daga ƙasa kuma aka faɗaɗata, haka hannun rigar akayishi mai faɗi, sosai yayi wa Zaleehan kyau musamman ma idan ka haɗa da kalan atamfar da takasance ja mai ratsin green colour,   dogon gashinta da akullum yake cikin gyara aunty lubna ta tubke mata shi akusan wuyanta, jan ribbom aka maƙala ajikin gashin, aunty lubna dakanta tayi mata ɗaurin ɗan kwali mai kyau, hakannema ya ƙara ƙawata shiganta, kama daga kan sarƙa ɗankunne, harma da awarwaro.duka na gold aka samata masu kyaun gaske,  aunty lubna naƙoƙarin yafa mata mayafi ajikinta ta shagwaɓe fuska tare da turo baki, hawayene suka cika idanunta, ganin haka yasa Aunty lubna sakin murmushi tare da kamata ta kwantar da'ita akan gado,  komawa aunty lubna tayi tasanarwa da ya Ahmad halin da Zaleehan ke ciki, nan take Ahmad yayiwa family doctor ɗinsu waya, babu ɓata lokaci kuwa sai gashi yazo,  sanin cewa batason allura ne yasanya likitan bata magunguna bayan ya auna yanayin jikinnata, magunguna masu ƙarfi ya bata, tare da ɗaura mata drip, don kuwa shima zai taimaka wajen bata ƙarfin jiki da kuzari. Ko mintuna 20 ba ayi da samata drip ɗinba bacci ya ɗauketa. Acan gidansu Saifuddeen kuwa receiption aka gabatar me rai da lafiya inda akayi ɓarin nairori wajen ƙawata haɗaɗɗen abinci da drinks ɗin da akasha, bayan anci ansha ne kuma aka bawa kowa takeaway wanda ke ɗauke da kayan ciye ciye dana shaye-shaye, kowani ledan takeaway kaza ne guda aciki anyi raping ɗinta da poil paper abun dai sai wanda ya gani, nan fa Saifuddeen da abokansa suka shiga ɗaukan hotuna kala-kala,  haka sukayita bidiri basu suka samu kansuba saida aka ƙira sallan azahar nanfa masu tafiya masallaci suka tafi masu tafiya gidama suka tafi, inda wasu sun koma gidane don suɗan huta kafun lokacin ɗauko amarya da kuma diner. Gaba ɗaya gidan nasu Saifuddeen babu masaka tsinke, jama'ane takota ina, hatta ɓangaren saifuddeen dinma mutanene acikinsa maƙil. Su Ahmad da ishaq ne suke zaune afalon sunata hiransu, wasu kuwa na kallo, kowadai da abunda yakeyi, Saifuddeen na cikinsu inda gaba ɗaya hankalinsa kekan laptop ɗinsa, da alamun wani aiki mai tsananin mahimmanci yakeyi, dan gaba ɗaya hankalinshi na kan System ɗin gaba ɗaya idanunshi sai yawo sukeyi a jikin fuskar laptop ɗin, ganin hayaninyar abokan nashi yayi yawa ne suna katse mishi hamzarine ya sashi sarrafa kekenshin ya shiga bedroom ɗinshi. Abuja. Kuka sosae Amina keyi hakan tatashi yau batajin daɗi wani irin abune takeji ya toshe mata maƙoshi, tabbas babu makawa tasan kishin Saifuddeen ne ke ɗawainiya da zuciyarta, har wani zafi zafi takeji aƙirjinta, tanason Saifuddeen so mai tarin yawa tana kuma kishinsa sosai, bata san dacewa soyayyar Saifuddeen yayi ƙarfi azuciyarta ba sai yau daya kasance ya auri wata ba'ita ba,  ahankali take fitar da sautin kukanta, wayarta ta ɗaga tare da kunnawa, take hoton Saifuddeen wanda akayi masa ɗazu inda Hayatuddeen ya ɗaura a status ɗinsa ya bayyana akan fuskarta, don tuni ta sauƙe hoton zuwa wayanta, sosai yayi mata masifar kyau acikin farar shaddan dake jikinsa, fuskarsa ta ƙurawa ido, tabbas kowa yagansa yasan yanacikin matsanancin farinciki,   rumtse idanunta tayi tare da sakin wasu zafafan hawaye, tabbas ta barwa Allah itakam, ta fawwala masa dukanin lamuranta, tasan zaiyi mata jagora, idan tana darai da kuma rabo tabbas tasan watarana zata mallaki saifuddeen amatsayin mijinta. Kaduna, Asma'u Ahmad matawalle kuwa tun jinya da taga batun auren Saifuddeen sosai hankalinta ya tashi sai dai tasa a ranta babu wani na ƴa macen da zata hanata mallakar Saifuddeen a matsayin mijin aurenta, shiyasa daren jiya harda mafarkinta wai auren da ita aka ɗaura. Ahmad ne yabi bayan Ishaq da ya shiga bedroom ɗin Saifuddeen, akan gado suka sameshi, yana zaune kana abokinshi Aziz Wanda ya kasance babban SS shima yana zaune gefenshi duk sun zubawa laptop ɗin idanu bisa dukkan alamu wani abun Saifuddeen ke nuna mishi, kana da alamun tashin hankali a fuskarsu. Ahmad ne ya kalleshi da kyau kana ya zauna kan durowar gefen gadon, ganin hakanne yasa Saifuddeen gyara zamanshi kana ya jingina bayanshi da kan allon gadon. Wayarshi ya ɗauka text ya turawa Umminshi cewa yana jin yunwa kuma ya gaji. yana turawa ya ajiye wayar sannan ya ɗan miƙawa ishaq hannu suka yi irin gausuwarsu sanna ya kuma kalli Ahmad daketa mishi kallon tuhuma. Da Sallama Ummi da Adda Rahma suka shigo falonshi dake cike da abokanshi gaisawa sukayi sannan suka wuce cikin uwar ɗakan, yana ganin Umminshi ya ɗan kwaɓe fuska tare tanƙwashe kanshi bisa kafaɗunshi yayi rau-rau da manyan idanunshi da suke cike da tashin hankali da tarin gajiya, da sauri Ummi ta zauna gefenshi, murmushin jin daɗi yayi tare da raɓawa jikinta, hannnta tasa kan goshinsa sai kuma tayi saurin sunkuyiwa ta leƙa fuskarsa tare da cewa. "Meke damunka?." rumtse idonsa yayi da ƙarfi, sanna ya buɗesu, Adda Rahma kuwa murmushi kawai taketayi a ranta take cewa. "Hmmm shaleleln Ummi wannan ɗan shagwaɓan inaga randa duk ya kusanci matarma sai anyi jinya biyu mutun sam shi baya son wahala abu kaɗan sai yazo yayi ta narkewa Umminshi yana shogoɓa." a fili kuwa ajiye kulolin abincin da suka kawo mishi tayi tare da zama ƙasa kan carpet ta kamo hannunshi alamun tausasawa, sai kuma ta ɗan leƙo fuskar wayarshi da yake nunawa Ummi inda ya rubuta, "Ummi sacemin ita akeson ayi, meyasa? me tayi musu? wayake shirya sacemin matata ranar da za'a kawo min ita gidana? me nayi musu?." cikin kaɗuwa da tsoro Rahma ta mike tsaye tare da cewa. "Su waye ne Saifuddeen meyasa zasu saceta?." Ummi kuwa wani irin fargabane da tsoro ya rufeta jiki a mace ta kalli Ahmad da ishaq da Aziz ta musu bayanin abinda ya rubuta mata sosai Ishaq da Ahmad suka shiga ruɗani Aziz kuwa kai ya jinjina tare da cewa. "To ai da sauƙi tunda mun gano shirinsu, tun a zuwa ɗaurin aure Saifuddeen ya gano akwai baƙin ayarin motocin da suka shiga sahunmu kana ya ɗauki numbers ɗin motocin ya kuma bi diddigin inda aka sai motocin ashema a kamfanin Salisu ne, to yanzu bincike yazo mana da sauƙi dan Salisu ya bamu komai na masayin motocin harma da number wayarsa, shine ya bawa Saifuddeen damar bibibiyar kiran wayar dama motsinsu munji shirinsu na son sace Zaleeha." wasu siraran hawayenesu ka zubowa Ummi murya a raunace tace . "Aziz ku nemo hukuma a lamarin." kai Saifuddeen ya jujjuya mata alamun a a, shi kuwa aziz gyara zama yayi tare da cewa. "Uhmmm Ummi kenan to ai su kansu Hukumar Saifuddeen ne idonsu, tunda duk wani tantirin daya gagaresu gane inda yake Saifuddeen suke miƙawa aikin bin diddiginshi ta na'ura mai ƙwoƙwalwa yake gano musu komai, to yake binciko tantiran da basu shafeshi bama bare wannan dake son sace mishi amarya, yanzu haka ya tsara komai ya kuma haɗe kiran wayar waɗancan da wayata, yanzu haka hatta motar da ya saya dan ɗauko amaryarshi suma sun sayi irinta, dan su samu damar sacetan, rashin sanin Saifuddeen yana ɗaya daga cikin tawagar UPSC, ne ya sasuyin wannan gangancin." Adda Rahma kam gaba ɗaya hankaƙinta ya tashi, sai dai ganin yadda Saifuddeen ke basu ƙarfin guiwa yasa hankalinsu ya ɗan konta, Adda Rahman ne ta kalli Aziz tare da cewa. "Wacce tawaga ce kuma UPSC?." Cikin fidda nufashi yace. "Ma'ana tawagar Union public service commission! sai dai sirrance yake musu aikin, ƙarƙashin jagorancin DSS." Jinjina kai Adda Rahma tayi dan ta fahimci sirri Saifuddeen ke yi wanda ba'a cika son mutane su saniba, duk da sunsan yana tare da DSS amman basuyi zaton matsayin aikinshi ya kai nan ba. nan suka ɗan sashi yaci abinci sannan suka fita suka tafi. Ƙarfe 4 dai-dai kamar yanda al'adan gombawa takasance da yamma suke ɗauko aure kuma hakan ya samu asaline tun lokacin da ƙungiyar ƴan kalare suka fare da sace amare in za'a kaisu gidajen aurensu da dare shiyasa aka dawo da al'adar garin kai amarya gidanta da yamma ido na ganin idop. Hakan yasa gaba ɗaya abokan saifuddeen sun shirya tsab don zuwa ɗauko amaryarsu, motoci ne masu uban yawa suka tanada don zuwa ɗauko auren, tuni su Ahmad, Ishaq, Salisu, Wareesu, Saminu, Mudassir, Jabeer, Hisham, ibrahim, Rabi'u, Aziz, Aryan, Gaddafi,duk sun kammala komai, kowa yasanja shiga irin ta alfarma. Ahankali Saifuddeen yake tuƙa kekensa, har ya ƙaraso harabar gidan, sanye yake da ɗanyar shadda blue mai masifar kyau, sai shinning take yayi kyau matuƙa, saidai awannna karon baisanya gareba, hasalima rigar half jumper ce,  su Adda Rahama da suka fito don zuwa ɗauko aure tana ganin ƙaninnata taƙarasa garesa da sauri, yanaganinta ya sakar mata murmushi tare da shagwaɓe mata fuska kaman wanda zaiyi kuka,  murmushi Adda Rahama tayi tare da ƙarasowa ta shafa gefen fuskarsa, cike da ƙaunarsa tace. "To sakalallen Ummi na farko yanda naga ka shagwaɓe fuskarnan so kake kace kagaji ko? ehem ai duk wata shagwaɓa Hayatuddeen awajenka ya koyota." Murmushin daya bayyana fararen haƙwaransa yayi tare da ɗan lumshe idanunsa, hannunta ya kama inda ya ɗaura adai-dai saitin heart ɗinsa, dariya me haɗe da murmushi tayi, cikin jin daɗi ta dubesa inda tace. "Kamar yanda kake cikin farinciki Saifuddeen haka muma muke, farincikinmu nayau bazai misaltuba angon Zaleeha!." Yanzunkam dariya sosai Saifuddeen ɗin keyi saidai babu sauti, sosai maganan addan nasa tafaranta ransa, ganin yanda yake dariya yasa Adda Rahama lumshe idanunta tana mejin daɗi acikin ranta,  ita da kanta takoma bayansa inda ahankali take ɗan tura kekennasa, harsuka ƙarasa gaban wata hamshaƙiyar ƙatuwar mercedess benz 2019 mai azabar kyau da tsada, sabuwace dal sai shinning take tana ɗauke ido,  shida kansa ya shiga motar kamar yanda ya saba, inda Ahmad ya naɗe kekensa ya tura masa cikin both, nanfa kowa yashiga mota,  inda ƴan ɗauko amarya ma suka shiga tasu motar, ajere haka motoci ashirin da shidan ke tafiyan gwano akan babban titin, kasancewar Gombe akwai manyan tituna sannan kokusa babu ƙazanta akan gaba ɗaya titunansu, cikin motoci ashirin da shidan nan tsakiyarsu ta Saifuddeen take wanda cikintane za a ɗauko amarya. Tunda ta kwanta bacci ba ita ta tashiba sai 3:40 cikin ikon Allah kuwa jikinnata yayi sauƙi sosai don koda tatashi babu abun da takeji,  don taɗan samu kuzari ajikinta, still  Aunty Lubna da Maryam da Aunty Shatu ne suka tsaya kaida fata inda sukaga tasake sabon wanka,  to fa yanzukam meckup aka tsantsara afuskartata ta musamman,  kayan da tasa kuwa ya banbanta dana ɗazu, duk da kasancewarsu duka dogin riguna ne, saidai wannan na wani tsadadden shadda lace ne me matsifar kyau, shima ɗindai akwai ratsin ja ajikinsa, sosai yayi bala'in yi mata kyau, ɗauri ɗankwali aka zizara mata tare da yane mata jiki da babban mayafi, wasu tsadaddun sarka da ɗan kunne aka sanya mata, turare kuwa kusan ma wanka akayi mata dashi, don wani irin masifaffen ƙamshi take. Gefe kuwa Rashida da Balkeesu ne zaune, balkeesu sai washe haƙoran munafurci take, yayinda take ta saƙa sharri acikin zuciyarta, bakomai yasama tazo ɗaukan auren ba face matsanancin gulma dake cinta tana son taje taga gidan kurma gurgun tunda Mama ta hanasu ganin kayan auren kam. Cikin nutsuwa tarin motocin suka ƙaraso ƙofar gidan nasu Zaleeha, su Adda Rahama waƴanda sune zasu shiga gidan don fito da amarya suka fiffito, kaitsaye suka nufi cikin gidan. Shi kuwa Saifuddeen ido ya ɗan lumshe tare da yin murmushi ganin wata benzz irin tasa tazo kusa dashi ta tsaya kana yaga a ƙalla yanzu motocin sun kai talatin banda guda biyar wanda sukazo suka samu a cikin ƙaton harabar gidan duk da girman wurin saida ya tsuke ya musu kaɗan wata motar har tana gogar wata, lips ɗinshi ya ɗan lasa gano harda motocin masu sun sace Zaleeha ne a wurin. A cikin gida kuwa Aunty Lubna ce ta shiryata tsab inda ta rufe mata fuskarta da mayafin laffaya mai tsananin tsada da ƙyalli dake jikinta, Goggo Maryama ƙanwar Baba malam da Aunty Aisha ƙanwar Mama ce suka kamata harzuwa falon Baba Malam, inda Ya Ahamd, Ya Aminu, Malam Adam harma da Mamy ke zaune, nasiha sosai Baba Malam da yayunnata sukayi mata, inda suka gargaɗeta sosai akan zaman auren nata, nasiha sukayi mata irin mai ratsa zuciya da jiki, nasihace irin wanda ke nutsar da duk wata ƴa mace, saidai kuma ko kaɗan Zaleeha babu abu ɗaya data ɗauka daga cikin nasihartasu, hasalima kukan baƙinciki kawai takeyi, sukuma take suka cika da tausayinta domin kuwa duk atunaninsu nasihar tasuce ta tsumata har take kuka. Ganin kukan nata yaƙarune yasanya Aunty Aisha da goggonta ƙanwar Baba Malam suka kamata, domin kuwa tuni Maryam itama tasa kukan rabuwa da ƴar uwartata, haka Zaleeha take kuka sosai, yayinda ayanzu take kukan mai dalilai biyu, dalilin farko shine auren ta da aka ɗaura da wanda bataso, dalili na biyu kuwa shine dalilin dake sa ko wacce amarya kuka da zubda ƙolla tanajin bege da kewa da zafin barin gidannasu da zatayi, tabbas tasan zatayi matsanancin kewar yayu da ƴan uwanta, hakanan takejin duk ba daɗi, haka Aunty Lubna da Goggo suka riƙota har zuwa compound ɗin gidan, kuka take sosai, tanamejin tsananin baƙinciki aranta don kuwa kowani taku ɗaya da zatayi zuciyarta tafasa takeyi, yayinda wani irin malolon baƙin ciki ke cika zuciyarta, sosai takejin takaicin kaita gidan Saifuddeen da za'ayi. Haka suka nufi wajen motocin tare da tarin zugar ƴan rakiyar amarya wanda dama tuntuni su ake jira, Balkisu da Rasheeda ne tafe wanda dama mota ɗaya sukeson shiga da amarya, babuma kamar balkeesu don ita da biyu ma takeson zama kusa da Zaleehan, dan so take taƙara zugata sosae. a cikin motocin kuwa text Saifuddeen ya turawa Aziz na numbers ɗin motocin da suke zargi, amsa ya tura mishi da cewa. "Ba matsala duk nabisu na sace iskar tayun bayansu, sai ta motar dake kusa damu nan na barta amman naja tamu mutar na matsesu basuma da damar motsawa, na kuma gayawa Ahmad ya fito cikin motar taku yayiwa amarya jagora ,zakaga gefen hagu da daman ku akwai mata uku uku sojojine cikin farin kaya." murmushi mai cike da nasara Saifuddeen yayi. Shi kuwa Ahmad yana ganin fitowarsu yayi saurin ƙarasawa garesu, shiyayi musu jagora zuwa motar da za'a sanya amarya wato wanda Saifuddeen ke ciki, shida kansa Ahmad ya buɗe mata ƙofar motar, Aunty Lubna ne ta sata cikin motar, ganin Saifuddeen zaune acikin motar yayinda hankalinsa gaba ɗaya kekan laptop ɗinsa, yasanyata sakin murmushi, lallai tajinjinawa ƙauna irin na Saifuddeen da sauri ta kamo hannun goggo Maryama dake shirin shiga tace. "Tsaya Goggo angon yana ciki, shi yazo ɗaukan amaryarshi da kanshi." Ahmad ne ya ɗanyi murmushi tare da cewa. "Sabida tsarone babbar yaya ba don tsoro ba." dariya sukayi cikin happy Balkeesu ne tay kamar bata jisuba tasoma ƙoƙarin shiga motar, da sauri ta ɗan dawo da baya ganin Saifuddeen hakimce acikin motar haibarsa da kimarsa da kwarjinta sun bugi zuciyarta shakkarshi mai yawa ta rufeta, bisa ɗole taja da baya, Ya Ahmad da Adda Maryam ma dake gefensu murmushin jin daɗi sukayi sabida sunga tarin so da kulawar Saifuddeen a kan ƙanwar tasi, dan ya gayawa ya Ahmad duk abinda ke faruwa na son sace amarya, ya faɗa mishine da kashedin karfa wasu suzo su basu amarya su jira sai sunzo da kansu .Su Bilkeesu kuwa bisa dolensu suka shiga wata mota ta daban. Ahankali duka motocin ke tafiya a jere a jere. Sosai hankalin yaran Dalla yayi matuƙar tashi ganin duk motocin sun fice sun barsu sai nasu kawai ,nasun kuma duk sunyi faci, sai ƙwaya ɗayar nan, koda suka shaidawa Dalla hankalinshi yayi masifar tashi to waya gano shirinsu, waya ɓata mishi tsarin sace matar wannan gurgun kurman, dole a tsorace suka fita da motocin a haka suka lallaɓa suka isa wurin mai sa iska, yayinda duk abinda sukeyi Saifuddeen na ganinsu a system ɗinshi ta sanadin na'urar bibiya da ya bawa Hayatuddeen ya liƙa musu a jikin motar da take irin tasa. Tunda tashiga cikin motar ta cusa kanta atsakankanun cinyoyinta kuka take sosai har kaman zata shide, samma batasan dawa take tare ba acikin motarba, ta gefen ido yake kallonta, hakan ne ya tabbatar mishi kuka takeyi. Sosai yakejin kukan nata na taɓa masa zuciya da jiki dan jikinshi ya bashi kuka take ga kuma alamu yana ganin yadda ta takure tana shessheƙa, saidai kuma tun shigowarta motar ko ɗago kansa baiyi ba, gaba ɗaya ya maida idanunsa akan system na laptop ɗinsa, saidai kuma duka hankalinsa na gareta, ɗan ɗagowa yayi tare da numfasawa, cikin nutsuwa ya rufe laptop ɗin bayan ya saita abinda zai naɗe mishi diddigin yaran Dalla sai dai akasi kaɗan da aka samu lokacin da yasa yayi ƙarancin binsu har inda zasu isa, ido ya zuba mata cikin jin tausayinta yasan halinda mata kan shiga lokacin da suke barin gidan iyayensu zuwa gidan mazansu, dan bai mance auren Raihana ba da Adda Rahma ke badu labarin daga cikin gombe har suka isa Kaduna Raihana bata bar kukaba sai ta ɗanyi shiru sai kuma taci gaba har suna mata dariya wai hutawa takeyi bare da dama sun san Raihana saurin kuka gareta, ido ya lumshe tare da buɗesu ya zuba mata su, ahankali ya sanya duka hannuwansa akan kafaɗunta, ɗan ɗagota yayi kaɗan, ita kuwa Zaleeha jin anriƙe kafaɗunta ne yasanyata yin tunanin Aunty Lubna ce, hakan yasa batare data buɗe idanunta ba, haka bata yaye mayafin dake kanta ba, tafaɗa jikinsa, sakin sabon kuka tayi tare da sanya hannuwanta duka ta zagaye cikinsa, cikin kukan fitar hayyaci tace. "Dan Allah Aunty Lubna ku maidani gida, wallahi bana son barin gida,karku kaini cikin bare ban sansuba basu sanniba, wlh bana sonsa, natsanesa, ko ganinsa banason yi, mutuwa zanyi matuƙar kuka kaini gidansa, dan Allah Aunty ki taimakeni, taƙare maganar tana me cusa kanta cikin ajikinsa. Ahankali ya lumshe idanunsa, tare da sanya duka hannuwansa ya ƙara jawota jikinsa, wasu irin tagwayen ajiyar zuciya ya rinƙa sauƙewa take wani irin zazzafan shauƙi ya shiga ratsa zuciyarsa da jikinsa. Jin wani masifaffen ƙamshi mai azabar daɗin ji da shaƙa wanda bata taɓa jin irinsa ba na shiga cikin hancinta wanda ba ƙamshin Aunty Lubna bane yasanyata ɗan jan jikinta baya, ahankali ta ɗago kanta, azabure tawani irin jan jikinta baya, kallon fuskarsa da yayi masifar kyau wanda ita da kanta sauda ta ganshi kamar balarabe, ganin shinne yasanya komai ya ƙwace mata, wani irin baƙin ciki ne ya cika zuciyarta take tasaki kuka tare da maida kanta ƙasa, wani irin tafasa zuciyarta keyi mata. Ƙawataccen murmushi Saifuddeen yayi tare da maida bayansa ya jingina da jikin kujeran, lumshe idanunsa yayi yayinda yake shaƙan dadaaɗan ƙamshinta, runguman da tayi masa yasanya yaji wani abu na tsargawa ta cikin jikinsa, sam baiyi yunƙurin sake taɓa ta ba, haka kuma bai hanata kukan da takeyi ba, ahaka har suka iso cikin katafaren gidannasu. Nan fa ƴan kawo amarya kowa yacika da mamakin haɗuwar gida, masu son auren sai masha Allah kawai suketa cewa, Goggo Maryama ce ta riƙeta inda tace tashiga gidan da ƙafar dama haɗi da bismillah, ranta aƙuntace haka tayi bismillah duk da cewa bawai ganin gabanta takeyi ba, zuwa yanzu tama daina kukan, jira kawai take Saifuddeen yace da ita wani abu ta sauƙe masa kwandon bala'i. Baƙaramin mamaki kyan ɓanagaren na Zaleeha ƴan uwanta sukayi ba, don kuwa komai yayi harma ya zarcewa tunaninsu, koda Balkeesu taga uwar dukiyar da aka kashewa Zaleeha, dakuma irin tsaruwan gidan al'afarma part ɗin nata, saida taji wani abu kaman mashi ya caki zuciyarta, sam bata ɗauka haɗuwar wajen zaikai har haka ba. Acan cikin ɗaki aka zaunar da Zaleeha. Sannu ahankali jama'a ke watsewa don nan da wasu awanni za a gudanar da diner, Rasheda ma tatafi don zuwa taho da me meckup ɗin da zatayiwa amarya, hakanne yabawa Balkeesu daman ƙara hurewa Zaleehan kunne, sam tace da ita tadaina asaran hawayenta, tabari idan hidiman biki ya kammala plant ɗinsu da suka haɗa sai ya fara aiki, sosai Zaleeha kuwa tahau kan maganan na Balkeesu ta zauna wanda zugan bilkeesu da asirin mma yazo iri ɗaya. Kamar yanda al'adan Gombawa yake aduk sanda aka kawo amarya gidansu ango, to fa akan tarbesu da kayan ciye ciye dana shaye shaye, hakance takasance agidansu Saifuddeen dan kuwa sosai aka cikawa su Zaleeha kayan ciye ciye, komai cikin wadata akayisa, abun ma har mamaki yake bawa wasu daga cikin dangin Zaleeha don kuwa kuɗi sosae gidan su Saifuddeen ɗin ke kashewa wajen ƙawata komai nasu, kamar basajin ciwon kuɗin. Ya Habu kuwa da ya Aminu har cikin ɗakin suka shigo suka gargaɗeta akan batun diner muddin tayi abinda zai kunya tasu Habu yace. "Wlh rabaki gida biyu zanyi kin sanni ba mutun cine da niba, ni ba irin ya Ahmad bane." Dolenta ta nitsu koda suka tafi ko motsin kirki bata kuma yiba. Kasancewar ƙarfe 8:00 pm dai-dai za a fara gudanar da diner'n hakan yasa amarya Zaleeha tana idar da sallan isha aka soma tsantsara mata meckup akan fuskarta, musamman aka ɗauko ƙwararriyar meyin meckup inda tazo ta baje basirarta akan fuskar Zaleeha, wani irin haɗaɗɗen meckup aka tsantsara akan fuskar Zaleeha wanda yayi bala'in fito da kyawun fuskarta, dakanta ta zura wata haɗaɗɗiyar fitted weeding gown mai azabar kyau, jifa jifa aka sanya ratsin fari ajikin rigar, rigace irin doguwa ɗinnan wanda har sharan ƙasa take, sosai rigan takama jikinta tazauna ɗas, inda gefe da gefen waist ɗin rigar aka sanya wani irin yadi mai sharara wanda yake da masifar tsawo, haɗuwar rigar ya zarce misali, musamman ma yanda ya zauna ajikinta yayi ɗas, tabbas ko ba a faɗaba kallo ɗaya zakaiwa rigar kasan da cewa taja maƙudan kuɗaɗe wajen tsarata, haɗaɗɗen ɗaurin ɗan kwali irin na amare aka kafa mata akanta, bayan anyi parking dogon gashinta atsakiyar kanta, inda aka sanya mata wani haɗaɗɗen sarƙan gold mai tsananin kyau da tsada, dagakan ɗankunne har zoben dake hannunta duka na gold ne, masu masifar tsada da kyau, wani irin takalmi mai masifar tsini ta sanya aƙafafunta, bakaɗanba tayi kyau nafitar hankali, harwani ɗauke ido take, turare kuwa kamar ɓarinsa akayi ajikinta, sosai Zaleeha tayi kyau cikin shigarta ta diner, inda kowa ke yabawa da tsantsar kyawun da Allah yayiwa Zaleeha, ita kanta Zaleeha tasan cewa ayau ɗin tayi kyau. Gombe International Hotel Sosai aka ƙawata babban falon wanda ananne za a gudanar da diner ɗin, anyiwa wajen ƙawa naban mamaki tare da haɗaɗɗen decoration na peach and white, sannan kuma daga sama adon decoration blue akayi mai masifar kyau, gurin acike yake da jama'a , inda kowani team da kalan shigarsu, gabaki ɗaya abokan Saifuddeen shigar shadda blue colour ce ajikinsu, inda gefe guda kuwa su Hayatuddeen ke sanye da peach colour ɗin shadda, daga gefe kuwa su Adda Rahama suka tsantsara ado cikin wani tsadadden farin lace mai adon blue, gurin tuni yacika da jama'a zuwan ango da amarya kawai ake jira. Ɓangaren Zaleeha kuwa ana gama tsantsara mata kwalliya Rasheeda ta sanar dasu zuwan ango, hakan yasa aka ƙara ƙawata mata adon nata, Balkeesu da Rasheeda na riƙe da ƙasan rigarta dake jan ƙasa suka nufi compound ɗin gidan. Saifuddeen ne zaune acikin wata rantsatstsiyar mota yabala'in yin kyau acikin farar shadda mai peach colour ɗin aiki dake jikinsa, yayi kyau fiye daduk wani tunani mai tunani, idanunsane suka sauƙa akan tauraruwar amaryarsa wanda tsananin kyawun da tayi yaso zautar dashi. A hankali suke taku tamkar wahainiyoyi, suna isa gab ɓakin motar Saifuddeen ya...! Littafin nan na kuɗine in kika ganshi a woje to na satane kuma yaseeen doguwa aradu in kina buƙata turo katin mtn na 300 kacal ta wannan number 09097853276 ko kuma kimin transfer ta 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. By *GARKUWAR FULANI* [01/09, 10:38 am] +234 806 596 1552: _Shafinga ƙyauta ne gareke babana, Ali Wambai, inai maka fatan al'khairi a rayuwarka, yaro mai sunan manya Allah yasa ka samu nagarta irin na masu sunan naka_ A hankali ya lumshe Kyawawan idanunshi, tare da furta. "Masha Allah!." a cikin zuciyarshi sosai tayi masa kyau acikin shigar wedding gown ɗin nata, har wani ƙyallin kyau take kamar wata tauraruwa, komai nata yazama wani na musamman,  cikin nutsuwa haɗi dajan aji irin na amare suka ƙaraso wajen motar Saifuddeen ɗin, da sauri Sule driver ya ƙaraso inda ya buɗe murfin motar da kansa, idanunta dake cikin wani ɗan siririn mayafi ta rumtse sakamakon ƙamshinsa da yadaki hancinta, sakamakon buɗe marfin motar da akayi, da taimakon Balkeesu tashiga cikin motar, ƙasa-ƙasa Balkeesu ke kallon Saifuddeen, sosai yayi bala'in yin kyau, saikace wani balarabe, komai nasa is perfect, sosai Saifuddeen ya haɗu, haƙiƙa musamman a irin wannan rana ko maƙiyinsa bai isa kushesa ba. Zaleeha na gama shiga cikin motar Sule driver ya maida murfin motar ya rufe. wata muguwar hararan Balkeesu ta abkawa Sule driver, cikin takaici tabi Rasheeda suka shiga wata mota ta daban. Ahankali Sule driver ke tafiya dasu acikin motar,   idanu Saifuddeen ya lumshe tare da jingina bayansa da jikin kujeran motar, sosai yake shaƙan daddaɗan ƙamshinta, hakanan haɗewar ƙamshin turarensa da nata  suka ba da wani irin yanayi me daɗin gaske, irin yanayin ƙamshin nan mai sauƙar da kasala uwa uba ga sanyi Ac da motar ke busa musu,    cikin nutsuwa ya ɗaura hannunsa ɗaya akan nata hannun, take haɗuwar lallausan fatar jikinsu waje ɗaya ya ƙara sauƙar masa da kasala, cikin ƙunan rai da hatsala Zaleeha tayi yunƙurin janye hannunta baya, amman sai ta gaza hakan jin ya rumtse tafin hannunta cikin nashi sosai zuciyarta ke tafasa, gefe guda kuwa ga ƙamshin turarensa wanda gaba ɗaya yabi ya cika mata hanci yana birkita mata kwanya sai shaƙar daddaɗan ƙamshin nashi takeyi, wanda tsabar tsanan da tayiwa mai turaren yasa take ta son cusawa ranta tsanan ƙamshin turaren nasa har wani abu me ɗaci-ɗaci take rayawa kanta takeji acikin maƙoshinta, zuwa yanzu har rasa yanda zata misalta tsanarsa aranta takeyi,  komai bayayi mata daɗi, tana daurewa ne kawai don plant ɗinsu da suka shirya yakai ga ci, ga kuma gargaɗin ya Habu wanda tasan ba mitunci ne dashi ba, bacin haka babu wani abu da zaisanyata zuwa wannan banzan diner'n toma da wanne angon zata taka ta shiga. Ganin tajanye hannunta daga cikin nasa yasanyashi maida kansa jikin lallausan kujeran motar, numfashi yake fitarwa ahankali, yayinda wani irin kasala ke sake lulluɓe masa jiki. Kowannensu zuciyarsa ɗauke take da tunani kala-kala shi ji da gani yake kamar bata tsiraba daga sharrin masu son saceta da haryanzu hidimar bikin bata barshi ya gama bincikosu ba, ita kuwa ji take da zama kusa dashi gwara zama kusa da bakin kura. A haka suka ƙaraso babban wajen wanda aka ƙawatasa iya ƙawatuwa, wato Gombe International Hotel, sosai wajen ya haɗu komai gwanin burgewa ga kuma tsaron da dole yasa yaran Dalla barin wurin. Acan cikin babban hall din da za'a gudanar da diner ɗin kuwa, kowa zuwan ango da amarya kawai yake jira,  gaba ɗaya mutanen dake wajen zuciyarsu awanke take da farinciki, yayin dasu Hayatuddeen keta ɗaukan pictures, suma zuwan ango da amarya kawai suke jira kafun nan abasu filin cashewa, don al'ƙawarine yau sai gaba ɗayansu sunnu nawa Hamma Saifuddeen ɗin gata, wannan rana itace ranan da Hayatuddeen dakuma gaba ɗaya dangin da abokan Saifuddeen ke jira, hakan yasa suke fata da burin faranta ran ɗan uwannasu tahanyar ƙawata masa bikin nasa yanda zaiyi armashi. Labarin isowar ango da amarya da MC yajine yasanyashi soma labartawa jama'an wajen cewa. "Allah yayiwa ango da amarya isowa." Nanfa kowa ya zubawa ƙofar hall ɗin ido, gaba ɗaya mutanen wajen sun zaƙu dason ganin amarya da angon. Ishaq wanda yasha dakakkiyar shaddarsa blue tare da wani haɗaɗɗen glass, wanda idan baka san shiba bazaka taɓa shaida cewa makaho bane, don kuwa komai nasa irin na masu gani yakeyi,  Ishaq da kuma Ahmad haɗi da Hisham da kuma Aziz wanda yana ɗaya daga cikin abokan Saifuddeen wanda sukayi Gombe State University tare sune suka fita don zuwa taro ango da amarya, wanda dama tuni su Balkeesu da Rashida suna da ƙannan Ya Aminu yaran Yayan Baba malam da yara Goggo Maryam da dai sauran ƴan uwan amarya waje, don kuwa sune suka riƙewa amarya Zaleeha ƙasan rigarta dake da matsanancin tsawo, wanda dole ya zama sai an riƙe mata shi. Sule driver ne ya ya buɗewa Saifuddeen ƙofar motar tare da ware masa sabuwar kekensa mai azabar kyau, har wani ɗauke ido da ƙyallinta keyi Cikin azama da alamun iya sarrafa kai da cikar nitsuwa ya hawa kan keken Saifuddeen ya dai-daita zamanshi hakan kuwa sai yayi bala'in ƙarawa kwalliyar tasa armashi, don kuwa wani irin kwarjini ne yasake bayyana atattare dashi, zamansa akan  wheelchair ɗin nasa sai ya ƙara masa girma da wani irin kima, ya fito tamkar jinin sarauta sule driver ne ya buɗewa Zaleeha murfin motar, ahankali ta zuro da kyawawan ƙafafunta wanda sukaji tsadaddun takalma masu kalan pitch,  tana gama fitowa daga cikin motar, su Rasheeda suka tattaro ƙasan rigar nata inda suka riƙe mata shi, ahankali Saifuddeen ya danna madannin wheelchair ɗin, take yasoma tafiya dashi, cikin nutsuwa yaƙaraso inda Zaleehan ke tsaye, kasan ceqarshi dogo, kuma wheelchair ɗin yafi sauran tudu, kana tanada maddan da za'a ƙara tunda ko a rage sai ya zama yayi tsawo in ka hankosu zakayi zaton a tsaye yake hannunshi yasa ya kamo nata ya ɗan haɗe tafukan hannunsu ya rumtse. Ahankali suka soma takawa inda yake sarrafa wheelchair ɗinsa cikin nutsuwa, wani irin haɗuwa da burgewa tsarin tafiyan tasu ya bada, duk dacewa shi yanakan wheelchair ne, amma kuma sai hakan yaƙarawa kwalliyar tasu armashi, don kuwa zamansa akan wheelchair'n ya bayyana tsantsar ajinsa da kuma kwarjininsa da kima da kamala uwa uba ƙasaita, hakan yasa mutane da yawa zasuyi masa kallon zallan ajine da kasaita yasanyashi naɗewa akan kujeran, wanda saima ka lura sosai zaka iya gane cewa wheelchair ne don kuwa kujera ce mai tsananin tsadan gaske, musamman aka kawo masa ita daga Germany. Ishaq da Ahamad ne ke biye dasu, saikuma su Rashida dake riƙe da jelan rigarta, bayansu kuwa Aziz da wasu matasa wanda sune zasu bada tsoro a wurun dan yanzuma akwai mashunan UD da suke zargi a wurin. Jabeer ne da kuma Hisham ke biye dasu Ahmad ɗin a baya, sosai tsarin nasu yayi kyau,  cikin nutsuwa suka kutso kansu cikin hall ɗin. Lokaci guda mutane suka somayin hanmdala sakamakon ganinsu, dan sunyi bala'in burgesu, nanfa Diamond Photograpgy suka soma aikinsu na ɗaukan hoto, sosai akeyi musu hoto, ga wani sassanya kiɗa dake tashi. Ahmad da ishaq da Salisu da Aziz kuwa da yayyafin kuɗi suka biyo bayan ango da amrya, yayinda rashida kuwa ke fesa wani abu mai ɗan karen ƙamshi kana yana bada kalan wal-wali. ɗaukansu hotuna tako ina, don sun bala'in yin kyau da dacewa, yanayin yanda Saifuddeen ke hakimce akan kujeransa shiya ƙara zautar da mutane, don hakan ya masifar ɗago ajinsa, sosai yayiwa kowa kwarjini, take ƴan matan da suka samu halartan wajen diner'n suka mato akansa, sosai dayawan mutane ke hamdala da godewa Allah, don kuwa tabbas Saifuddeen ya cika cikakken namiji kuma ingarma, maiji da tashen kyau haɗi da kwarjini,  haka kuma mutane da yawa ke yaba tsananin kyawun da amarya Zaleeha tayi, don kuwa kowa na iya hango beauty face ɗinta ta cikin wani ɗan abun da aka ɗiga mata akanta wanda yaɗan rufe gefen fuskarta kaɗan, sosai su Adda Rahama ke yaba kyawu da haɗuwar Zaleeha, tabbas sai yanzu suka tabbatar da cewa bawai abanza Saifuddeen ya nace akan cewa sai ita ba, haƙiƙa Zaleeha tacika mace abunso ga kowani irin ɗa namiji, sannan kyawunta ya isa kyau,  sosai kowa yaga dacewarsu da Saifuddeen ɗin, don kuwa kyaune ya gauraya da kyau. Wani irin cool music  na Ed sheeran mc ya sakar musu irin mai taɓa zuciyar nan, hakanne ya ƙara bawa tafiyar da sukeyi armashi,  Hayatuddeen da abokansa ne suka zo sunayi musu live vedio,  Ahaka har suka ƙarasa wajen da aka ƙawata domin zaman ango da amarya, wajene wanda aka ƙawatasa da decoration mai kyaun gaske, wanda akayi amfani da colours irin na kayan dake jikin ango da amarya,  cikin nutsuwa Saifuddeen yayunƙura ya sauƙa daga kan kekensa cikin nutsuwa haɗi da salon mai armashi ya hau kan wata rantsatstsiyar royal chair wanda tagaji da haɗuwa,  Rasheeda ne ta zaunar da Zaleeha agab dashi har takai ga jikinsu naɗan gogan na juna. Kamar yanda aka saba ango da amarya na zuwa wajen diner ake fara gudanar da shagulgula hakanne yasanya babu wani ɓata lokaci MC yabuƙaci da babban abokin ango akan yazo yaɗan basu biography na ango. Ishaq wanda fuskarsa ke ɗauke da murmushine yataso inda ya ratsa cikin yawan jama'an tamkar wanda yake gani haka yaƙarasa gaban MC, mike  ya karɓa inda yayi gyaran murya, cikin nutsuwa haɗi da kamala yasoma bada ɗan taƙaitaccen tarihin Saifuddeen ɗin, sosai biography'n na Saifuddeen ya taɓa zuciyar kusan gaba ɗaya mutane dake wajen, duk da cewa in brief Ishaq ɗin yayi komai, amma tabbas rayuwar Saifuddeen cike take da al'amura masu sosa zuciya, dayawan mutanen da basusan Saifuddeen ɗin ba, sai alokacinne ma suka san da cewa shiɗin kurmane, koda Ishaq yagama bada ɗan taƙaitaccen tarihin na saifuddeen, take jama'an wajen suka soma tafi,  sosai aka jinjina gwarzantaka irin na Saifuddeen don haƙiƙa yacika Namiji. Ishaq na komawa, still Mc yasake buƙatan babbar ƙawar amarya don tazo ta bada biography na amarya. Tsulum Balkeesu tasoma ƙoƙarin miƙewa zuciyarta cike da mugunta, don kuwa dama tuni tagama kitsa kalaman da zata faɗa agame da amaryan, haka kuma tashirya gasawa Ango magana afakaice, saidai kafun ta farga  sai tsintar muryar Rasheeda tayi acikin kunnuwanta, wanda sanin halin Balkeesun da mugun nufinta ne yasanya Rasheeda rigata zuwa, don tabbas tasan balallai abun da Balkeesu zata  faɗa yazamanto al'khairi ba, wannan ranan kuwa ta farinciki ce, sam batason aɓata ran kowa, sudai da suka ɗaukawa kansu dala ba gammo sai suyita fama. Cikin nutsuwa Rasheeda ta ɗan bada taƙaitaccen tarihin Zaleeha, wanda kuma iya abun da ta sani ta faɗa, nan mutane da yawa suka ƙara gaskata cewa lallai Amaryar Saifuddeen ɗin ƴar ƙwalisa ce, don aɗan biography ɗinnata da Rasheeda ta bayar, zaka fahimci cewa, itaɗin ƴar ƙwalisa ce, sannan mai aji da kuma wayewa, uwa uba ƴar gidan hutu ce, sam bata wani san baƙin cikin rayuwa ba kuma ƴar gidan mutunci ce. Koda aka gama gudanar da biograpy nanfa mc yasake musu music mai daɗi da taɓa zuciya,  inda aka ɗan soma ƴan ciye ciye wanda aka kashe maƙudan kuɗaɗe wajen tsara abunci dana sha. Haka suka shiga gudanar da diner ɗin cikin nutsuwa, bayan ankammala ciye ciye ne, mc ya sanya wata waƙa mai daɗin gaske, nanfa ya buƙaci da ƴan uwa suzo don nunawa amarya da ango ƙauna. Aunty Rahama, Raleeya, da kuma Raihana, Aunty Kubra sune wanda suka fara miƙewa tsaye, don filin nasune na musamman,  cikin yanayin taku haɗi da ɗan rawa mai burgewa suka ƙarasa kan step ɗin da ango da amarya suke,  sosai suka burge kowa musamman shigar alfarman dake jikinsu tunkan su ƙaraso Saifuddeen ya miƙowa Adda Rahama hannunsa, cikin nutsuwa Adda Rahama takamo hannun nasa ta riƙe tana murmushi, hannu tasa ta shafi gefen fuskarsa take ta buɗe wata ƴar purse ɗinta, fararen ƴan dubu-dubu miƙaƙƙune suka cika cikin jakan,  haka suma su Raihana da Raleeya da Aunty Kubra gaba ɗayansu jakakkunansu suka buɗe, kuɗaɗen suka ciro inda suka soma yiwa ɗan uwannasu da amaryarsa ɓarinsu, kuɗi suke zuba musu sosai har kaman basason kuɗin, yayinda wajen ya cika da kiɗa haka masu vedio da kuma photo sunatayi, abun sosai yake ƙayatarwa, shikansa Saifuddeen saida yasha mamakin yanda ƴan uwannasa ke ɓarar da kuɗi wajen yi masa liƙi, suna cikin yi musu liƙinne, Dr Adnan da kuma Ahmad, haɗi da Saminu da General Abbas mijin Aunty Kubra suka ƙaraso. Hohoho idan bakwayi kuban waje, domin kuwa sosai suka shiga taya matansu likin, nanfa abun yaƙara girmama mutane da yawa sai sakin baki sukayi suna kallonsu, Ahmad kuwa har kamo Raleeya yake suna ɗan taka rawa atare, sosai suka nunawa Saifuddeen ɗin ƙauna, kafun daga bisani mazajensu suka janyesu inda sukabar kan dandamalin,  nanfa mc yabawa gaba ɗaya abokan ango dama. Nanfa akeyinta rigiji rabgi , domin kuwa gaba ɗayansu da rawa suka shigo cikin filin, hakanne yasa gaba ɗaya hall ɗin aka ɗau sowa, don sosai abun ya ƙayatar, babuma kamar ishaq, Aziz, Ahmad, Salisu, Warisu tumbuleƙe, Mudassir, Jabeer, Hisham, kai baki ɗayansu dai wanda suke rawa sosai, babu wani kunya ko ɗar, acewarsu ranan da suke jirane tazo, Ibrahim, Wareesu, Saleesu, Saminu, da kuma Aziz da sauran school friend ɗin Saifuddeen ɗin kuwa suma sosai suka taka,  Ishaq ma da ba gani yake ba haka ya gwada basirarsa wanda ya burge kowa,  Ahmad ne ya jawo Saifuddeen zuwa cikinsu, har tsakiyarsu ya jawosa bisa kan wheelchair ɗinsa,  nanfa suka kewayesa sukayi mishi zube suna rawa tare dayiwa junansu ɓarin kuɗi, ko ina dake cikin hall ɗin tafi haɗi da shewane ke tashi, domin sosai salon na abokan Saifuddeen ya tafi da kowa, sun bala'in burgewa. Koda suka gama bidirinsu suka koma, nanfa mc yayi gyaran murya tare da ƙiran masu gayya da aiki, ginshiƙai kuma ƙannen ango. Hohoho inji hausawa sukace abu namu maganin akwaɓemu. Su Hayatuddeen da Zakariyya Imran da Sulaiman kana isma'il da Faruq ɗan Adda Rahma. Manyan ƙanne, yara matasa masuji da ƙarfi ajikinsu, ƴan matasan da suke ji da tashen tasowarsu, salon rawar tasuma ta dabance don kuwa saida ango da kansa yashiga tafa musu, don da wani irin ƙayataccen rawa suka shigo cikin filin, nanfa aka somayi musu ihu ana ƙara zugasu kansu na ƙara girma, harta Isma'el ɗan Alhji Kaburu dayake kurma saida ya taka,  sosai Hayatuddeen da abokansa Imran, Sulaiman, Isma'il da ƙanin amarya Zakariyya rawa irin ta zamani sukeyi mai ɗaukar hankali, hakanan jama'an wajen sukaji kwaɗayin yi musu liƙi, don kuwa rawan nasu yayi kyau sosai, nanfa jama'a suka soma yi musu ɓarin kuɗin. Ango Saifuddeen kuwa sai wani ƙasaitaccen murmurshi yaketayi hannunshi rike da hannun Zaleeha daketa mutsutsun kwacewa, yayinda hawaye ke zubo mata tabbas taron ya haɗu iya haɗuwa irin haɗuwa na kece raini da nunawa sa'a taso ace da wanda take sone take zaune a yanzu ,domin har tsikar jikinta tashi yakeyi yadda hall ɗin ya ricaɓe aketa ɓarin kuɗi, ita da kanta tasan babu ƙaranta a bikin ta kuma yarda komai na alfarma akeyi ta gamsu da ranta mijinta kuma kekyawane irin kyau na kece raini da nunawa sa'a ta kuma gamsu mai cikekkiyar tsabta ne da gayu, kuma masoyine na gaskiya dan taga salon zazzafar soyayyarshi to amman mijinfa bashi da maraba da ginennen taɓo kuma duk haka tasan yazo a ƙirerren lokacine wlh da yazo kafin haɗuwanta da wanda ya taimaketa tabbas yanada nagartar da dole ta soshi to amman a makere yazo, kuma sai takeji can cikin zuciyarta kamar wani abu ke sarrafa mata zuciya, bata dawo daga duniyar tunaniba taji sauƙan tattausan yatsunshi kan haɓarta da sauri ta ɗan juyo ta kalleshi sai kuma tayi maza ta lumshe idanunta ganin ya ɗaga mata girarshi ɗaya tare da kashe mata ido kana ya ɗan kaɗa mata harshe alamun, ya dai, kana ya ɗan nago hannunta dake tsarke da nashi bayan hannun nata ya juya tare da manna mata wani irin sassanyan kiss. wow nanfa masu hoto suka koma kansu. Cikin farinciki Hayatuddeen yaƙarasa wajen Hammansa nanfa yasanja salon rawarsa, hannun Hamman nasa ya kamo, ahankali yake juya kujeran Hamma Saifuddeen ɗin nasa, hakan yasa abun yaƙara armashi, murmushin farinciki kawai Saifuddeen ɗin keyi, haƙiƙa ƴan uwa da abokansa sun nuna masa tsananin gata, nanfa Hayatuddeen da abokansa suka ciro kuɗaɗen al'jihunsu suka soma zubawa Saifuddeen da Amarya Zaleeha, Zakariyyane yaƙarasa jikin ƴar uwartasa ahankali ya kamo hannuwanta tare da jawota tsakiyan filin, tayi matuƙar mmkin ganin Ya Aminu Ya Ahmad Ya Habu Aunty Shatu Aunty Lubna da Adda Maryam dasu Amira ƙannen ya Aminu sun mata zobe ita da ango Saifuddeen suna mata yayyafin kuɗi, Zakariyya kuwa nan ya riƙe duka hannuwanta, cikin tsananin ƙaunar ƴar uwartasa yasoma ɗan jijjigata hakanne yasa Zaleeha taɗan saki murmushi, nan taɗan soma ƙafafunta, ganin haka yasa gaba ɗaya su Hayatuddeen suka ke wayeta suna rawa, bisa dole Zaleeha ta biyesu suka ɗan soma takawa,don kuwa ansanya musu wata daddaɗan waƙa, wanda ko baka da niyar yin rawa saika taka, bare ita Zaleeha uwar son waƙa da kiɗi haka yasa taɗan saki jikinta bayan anyi musu ɓarin kuɗi sosai takoma kan kujeran ta zauna tana me maida ajiyar zuciya. Haka dai akayita shagulgula masu ƙayatarwa yan ƙungiyar jonapwd sunyi matuƙar bada mmkin irin kuɗaɗen da suka liƙawa ango, nairori kam awannan rana sunyi kuka sosai, an ɓarnatar dasu baɗan kaɗan ba, sai wajen ƙarfe 10:00 pm, aka kammala gudanar da diner'n, nan kowa yasoma ƙoƙarin tafiya gida, don dayawan mutane amatuƙar gajiye suke, babuma kamar Saifuddeen, wanda dama shi sam bai iya jure wahala, abu kaɗan ke gajiyar dashi, sai yaji duk yazama very weak bare kuma ga hidimar da yasha, yanzuma babu wani abu dayake buri da fatan gani kamar Umminsa, so kawai yake yaje yayi mata complain ɗin gajiyar dake damunsa, kamar yanda sukazo amota ɗaya haka komawarsu ma takasance amota ɗaya, saidai har suka iso gidan ko ƙala baice mata ba, gaba ɗaya gajiya ke damunsa, itama Zaleehan agajiye take hakan yasa ta lafe jikinta ajikin kujeran motar tare da lumshe idanunta da suke cike da bacci. Jin isowarsu yasanya dakanta ta buɗe murfin motar ta fice, ko tsayawa batayi ba, riganta na sharan ƙasa haka tanufi ɓangaren nasu, don ta zaƙu da ta cire rigan, sam bata wani iya zama da kaya mai nauyi ba, musamman ma wannan dayake wedding gown. Shima Saifuddeen saita wheelchair dinsa yayi tare da hawa kai, kaitsaye yanufi cikin gidan nasu. Kasancewar darene babu wani hayaniya, dayawan mutane bacci suke, waƴanda suka dawo daga wajen diner kuwa tuni kowa ya shige ɗaki don ya ɗan huta,  ahankali yake tura wheelchair ɗinnasa har yaƙaraso cikin falon, idanunsa ne sukayi masa tozali da Umminsa dake zaune acikin falon, yana ganinta yaɗan lumshe idanunsa tare da shagwaɓe fuska, murmushi Ummi tayi tare dayi masa duban tsab, tabbas tasan da cewa Saifuddeen bazai taɓa dawowa har ya kwanta  batare daya neme ta ba, tasan dolene zaizo gareta hakanne ma yasa tazauna afalon zaman jiransa, ahankali ya ƙaraso tare da ɗaura kansa akan kafaɗan Ummin, cikin yanayi na zallan shagwaɓa ya ɓata fuska tare da taɓe red colour lips ɗinsa. Hannu Ummi tasa tashafi lallausan sumar kansa, cikin kulawa tace. "Ka gaji ko?." Kansa yajinjina mata alamar "Eh." Tare da ƙara maida kansa jikinta, tamkar wani yaro ɗan shekara shida haka ya koma mata, sakalci haɗi da shagwaɓa kawai yake zuba mata, komai ta cikin body language ɗinsa yakeyi mata,  sosai Ummin ke lallaɓinsa, sarai dama tasan ɗanta bayason wahala, gashi da ɗanbanzan shagwaɓa, abu kaɗan ke wahalar dashi sai dai jarumtar zuciyarshi na danne sakalcinsa, lallaɓasa Ummi tayi tare da cewa. Yaje yayi wanka, tun tuni dama tasa anshirya musu abinci akan dinning area. Da ƙyar Ummi ta iya lallaɓasa yabar part ɗin nata, yana fita yasamu su Ahmad da su Ishaq wai zasuyi masa rakiya zuwa wajen amarya, nanfa yace musu ya gode, ganin cewa dama suma sungaji yasa suma basu matsaba, nan kowa yanemi inda zai huce gajiyarsa, Ahmad da Saminu kuwa kowa matarsa ya kama suka ƙule aɗaki. Cikin nutsuwa Saifuddeen ya kutsa cikin ɓangaren nasu, babu kowa acikin falon sai daddaɗan ƙamshin turaren wuta, dubansa yakai ga ƙofar bedroom ɗin na Zaleeha, nan yagansa agarƙame, baiwani damu ba yanufi ƙofar dazata kaisa zuwa falonsa, don kuwa  dole sai yabi ta falon Zaleehan kafun yasamu kansa cikin nasa falon. Yana shiga haɗaɗɗen falon nasa kai tsaye ɗaki ya nufa, kayan jikinsa ya shiga ragewa, saida ya rage dagashi sai gajeren wando sannan ya nufi toilet, shida kansa ya haɗawa kansa hot water acikin bathtube, kwanciya yayi lub aciki tare da lumshe idanunsa, sosai yaji daɗin ruwan don ahankali yaɗanji gajiyan jikinsa naɗan warwarewa,  wanka yayi insa ya fito daga cikin bathroom ɗin bayan ya ɗauro alwala, koda ya fito wata marroon ɗin jallabiya ya sanya, duk da akwai gajiya ajikinsa ko kaɗan hakan bai hanasa yin sallah raka'a biyu ba yana idarwa ya shafa addu'oinsa sannan yabi lafiyar gado, light off na wutan ɗakin yayi tare da jawo blanket ya rufa ajikinsa, lumshe idanunsa yayi, sannu ahankali tunanin matarsa ke mamaye zuciyarsa,  ahaka bacci mai nauyi ya ɗaukesa. Washegari Ƙiran sallan asuban fari ya farka, nan yatashi tare da faɗawa bathroom yayi wanka haɗi da ɗauro alwala, koda yafito dogon wandon jeans da kuma white crazy shirt yasanya ajikinsa, sosai kayan sukayi masa kyau, kan kekensa ya hau inda ahankali ya buɗe ƙofar ɗakin ya fice. Cikin nutsuwa yake tafiya da keken nasa har yakawo cikin falon na Zaleehan, ɗan shiru yayi ganin wutan ɗakin a kunne da kuma alamun motsi acikin ɗakin nata yasa kansa tsaye yafice daga cikin falon, don ya tabbatar da cewa tatashi sallan asuba ne. Direct masallacin dake gefen gidannasu ya nufa. Zaleeha kuwa fitsarine ya tasheta koda taga lokacin sallan asuba yayi kuwa shine taɗauro alwala, nan tazo tayiwa Zaheera dake kwance akan doguwar kujeran dake cikin ɗakin tashin duniya amma Zaheera taki tashi, sabida gajiyan hidimr daren jiyan hakan yasa dole Zaleeha ta ƙyaleta, nan ta shumfuɗa sallaya inda ta tayar da sallah,  tana idarwa ta soma gabatar da azkar ɗinta, koda ta gama, wayarta ta jawo inda ta shiga Qur'an app nan ta buɗe suratul baƙara ahankali cikin zuciyarya take karatun sai dai tana farawa kasala da wani gyangyaɗi mara tushe ya rufeta ta rasa meyasa haka cikin kwanakin nan duk sanda zatayi niyar yin karatu sai taji wannan yanayi da kyar take iya farawa dai. Ɓangaren Saifuddeen ma kuwa tunda yayi sallan Asuba yana nan zaune acikin masallacin, karatun Al'Qur'ani yayi sai 7 dai-dai yabar cikin masallacin, kaitsaye ɓangaren Umminsa ya nufa, dan zuwa gaisheta, kamar yanda ya sabar mata kowacce ranan duniya. Yana shiga yasameta tana zaune afalo, yayinda gidan yayi shiru duk ana maida baccin da ba'ayiba Daren jiyan shiyasa ita da kanta ta shiga kitchin, hannunta riƙe da carbi tana ja,  rusunawa yayi agabanta cikin girmamawa yagaisheta cikin body language kamar yanda ya saba. Ko gama dai-daita zamansa baiyiba fitinannen ƙamshinta yayi masa sallama a hanci, lokaci guda kuma saigata tashigo cikin falon, sanye take da hijab wanda takawo har zuwa ƙasa, sosai hijab ɗin yayi mata kyau, cikin nutsuwa taƙaraso cikin falon Ummi naganinta tasaki murmushi tare da miƙo mata hannu, gefenta ta zauna, har ƙasa ta durƙusa cikin tsananin ladabi da girmamawa tace da Ummi "Ina kwana?." da "Lafiya Ummi ta amsa tare da tambayarta ya kwanan baƙunta? ɗan murmushin daya ƙara bayyana zallan kyawunta tayi cikin nutsuwa tace. "Alhamdulillah!." Da "Masha Allah!!." Ummin ta amsa, still fuskarta ɗauke da murmushi, hakanan taji wani irin daɗi ya ratsa zuciyarta don kwata-kwata bataiyi zaton haka yarinyar keda ladabi ba, shiru tayi tana kallon yatsun ƙafan Ummi haka nan taji son Ummi cikin ranta, cikin kula da sonta Ummi ta ɗan sunkuyo ta kalleta cikin sanyi tace. "Ngd ɗiya Allah ya muku al'barka ya bamu zaman lfya." cikin tsunkuyar ds kai da alamun jin kunya murya can ƙasa tace. "Amin Ummi." cikin kula Ummi tai murmushin jin daɗi tare da cewa. "Tashi kije ki kwanta kiyi bacci ki huta gajiyan biki." Cikin jin daɗi ta gyaɗa kai kana ta miƙe hankali tare da ficewa daga cikin falon, ko kallon inda Saifuddeen yake batayi ba, hasalima yi tayi kamar batasan da wani abu waishi mutum awajen ba, ita kuwa Ummi bataji wani abu akan rashin kula Saifuddeen ɗin da Zaleehan tayi ba, domin azotonta sunyi nasu gaisuwar a ɗaki, domin duk atunanin Ummin Saifuddeen ɗin aɗakin Zaleehan ya kwana. Zaleeha na tafiya Saifuddeen yaɗan zubawa Ummi shagwaɓansa sannan ya nufo part ɗin nasu. Koda ya shigo cikin falon zaune ya iske ƙanwarta Zaheera ta ƙurawa tv ido, inda take kallon wani series film a mbc bollywood wato (حب خادع) nasu tara da deep, kasancewar sosai dukansu ita da Zaleeha keson series film ɗin. Tana ganin Saifuddeen taɗan zamo daga kan kujeran gaishesa tayi, yayinda shi kuma ya amsa mata cikin jinjina mata kai, fuskarsa ɗauke da ɗan murmushi, kai tsaye ɗakin Zaleehan ya nufa, don rashin ganinta afalo da yayi ya tabbatar masa cewa tana cikin ɗakin, ahankali yakai hannunsa inda ya murɗa handle ɗin ƙofar, kana ya shiga, tsaye take agaban gado tana ƙoƙarin zuge zip ɗin rigarta dake a wawage, yayinda white skin ɗin bayanta keta shinning, jin motsin anshigo ɗakin yasanya batare da ta juya ba tace. "Zaheera zoki zuge min zip ɗin nan please." taƙare maganar tana me watsa dogon gashin kanta akan wuyanta. Ahankali ya danna madannin wheelchair ɗinsa, take keken tasoma tafiyu as slowly, yana ƙarasawa gab bayanta ya tsaya cak, hannunsa yakai kan lallausan skin ɗinta, jin sauƙan wani lallausan hannu abayanta wanda sam baiyi kama dana ƙanwarta Zaheera ba yasan yata juyowa da sauri. Idanunsune suka faɗa cikin na juna take kuma losing balance ya kamata nanfa ta faɗo kansa, hannayensa duka biyu yasa inda ya rungumota jikinsa, azabure cikin matsanancin tsoro ta turesa tare da tashi tsaye, cikin fushi tace. "Waya baka izinin shigomin ɗakina, har takai ka gayin azarɓaɓin taɓa mini jiki? ko an faɗa maka cewa na nemeka ne." tura baki tayi tare da dubansa cikin shakkarsa da takaicin aurensa da tayi tace. "Ni jikina na mutum ɗaya ne, kuma zan cigaba da adana masa kaina, sannan jikina bana musaki bane, jikina na cikakken namiji mai lafiya ne, halan ko kamanta cewa kai Nak...." Batare daya bari ta gama magananba ya wani irin fusgota ta faɗa jikinsa, hannunsa yasa inda yayi mata wani irin tsastsauran riƙo, cikin tsoro da fargabar zuciya ta ɗan kalato tsiwa tace. "Da Allah ni kasakeni, na tsani haɗa jiki da kai!." Ahankali yaɗan lumshe idanunsa wanda suka ɗan sanja launi, laɓɓan bakinsa yaɗan cije, "wato shi nakasashshe ne saboda haka bazai iyayi mata komai ba ko? hmmm zaiyi maganinta ne." yafaɗi maganar acikin zuciyarsa. hannunsa ɗaya yasanya ya tallafo fuskarta, ganin haka yasa Zaleeha waro idanunta, cikin mamaki ta ɓuɗe baki tare da da cewa. "Kai Malam da Allah miye haka zaka...." Kamar amafarki haka taji sauƙan bakinsa acikin nata, yayinda yasa hannunsa ya riƙe kanta da ƙarfi, tayanda bata iya ƙwacewa ba, idanu Saifuddeen ya lumshe tare da kamo sweet lips ɗinta yana tsotsa, cikin son ladabtar da ita ya shiga tsotsan bakinnata da ƙarfi ƙarfi, inda har teeth ɗinsa yake sanyawa akan lips ɗinta yana ɗan cizonsu, harshensa yasa ya naɗo nata harshen tare da kanainaye mata harshen take yashiga musanya yawunsu, firgici da takaici haɗi da tashin hankali Zaleeha kam tashigesu, sosai take son ƙwace kanta daga azabar tsotsar lips ɗinta dayakeyi amma takasa. Idanuntane suka ciko da ƙwalla, take tasoma dukan ƙirjinsa da duka ƙarfinta amma ina Saifuddeen ko gizau, saima ƙara zafafan tsotse laɓɓanta da yakeyi da ƙarfi. Azaba kuwa da zafi har cikin kanta, dan kansa ya janye bakinsa daga nata tare da hankaɗata kan gado, baya yayi da kekensa tare da dubanta giransa ɗaya ya ɗage mata tare dayi mata alaman to ya? Kuka mai cin rai tafashe dashi cikin matsanancin takaici haɗi da sabuwar tsanarsa tace. "Allah Ya isa na bazan taɓa yafe makaba mugun mugaye kawai, wanda babu abun daya sani sai son kai dana zuciya." hannu tasa tana goge harshenta data ɗan zaro kana idonta na zubda siraran hawaye tace. "Allah ya isana kuma Allah zai saka min" Murmushin daya bayyana tsantsar kyawunsa yayi ahankali ya ɗage kafaɗunsa alaman ko oho, madannin kekensa ya danna tare da juyawa ya fice daga cikin ɗakin, tana ganin fitarsa ta silalo daga kan gadon zama tayi aƙasa tare da sakin kuka, cikin matsanancin takaici tashiga harba ƙafafunta tamkar ƙaramar yarinya ƴar shekara 6, ji take kaman tayita zabga ihu na baƙin cikin abunda yayi mata, ga kuma bakinta dake masifar yi mata raɗaɗi harshenta kuwa har jinsa take kaman baya cikin bakinta, laɓɓɓanta sai wani zut-zut sukeyi, kuka takeyi tsakananinta da Allah tana harba ƙafafunta, cikin kukan tace. "Bazan taɓa yafe maka ba, mugu nakasashshe mai zubin ƴaƴan ruwa, wallahi ayau plant ɗina zai fara aiki bama sai gobe ba, don in na zauna da kai zalina zakayi taci." A garin Doho kuwa Mamace da yayarta Ruda ke zaune gaban wani shirgegen kasurgumin bokansu na arnan kan dutse bayan ya gama jin baya nansu sun gama tattaunawa, zuru-zuru yayi da ida nunshi tare washe wawakeken bakinshi cikin amo mara daɗin ji yace. "Kada ku damu, bazata zaunaba dan sihirin ya kamata, munyi sa'a lokacin da mukayi aikin bata salla, sihirin yana ƙarƙashin gadonta bazata iya zama cikin ɗakinba dole, zata gudu zata bar gidan babu zama da wannan gurgun, dan tuni mun gama aikinmu babu wanda zatayiwa biyayya akan zama a gidan, dan ji zatayi kamar cikin kushewarta take, mutanenmu zasu sa mata tsanan gidan da mijin sosai." cikin jin daɗi Ruda tace, "Yauwa boka bashallu mun gode." Mama kuwa kai ta jinjina tare da cewa. "To amman ya batun aurenta da Abdussalam?." kai ya jujjuya mata tare da zaro idonshi yace. "Ki bari kiga mun samu mun raba wannan aurenma tukun, dan shi yaron da wuya mu sameshi." jin haka Ruda tace. "Mun gode a gama wannan ɗin kafin a fara wani." itama Mama godiya tayi kana suka ajiye mishi kuɗin aikinshi suka tafi. ~Wasa farin girki~ Ahankali ta murɗa ƙofar toilet ɗin ta fito,  sanye take da wani pink ɗin bathrube yayinda gaba ɗaya gashin kanta ke jiƙe da ruwa, da dukkan alama dai, daga wanka take,  fuskarnan tata akwaɓe take sam babu alaman fara'a asamanta, sosai abunda Saifuddeen ɗin yayi mata safiyar jiya yake cinnta tare da ƙara sosa ranta, inda yake ƙara motsa duk wani ɓacin ranta,    ƙarasawa gaban dressing mirror tayi ta zauna, dai-dai lokacin aka turo ƙofar ɗakin aka shigo,  azabure ta juyo don ganin kowaye yayi gangancin shigo mata ɗaki babu sallama. Idanunta ne sukayi mata tozali da Balkeesu, ganin Balkeesu yasa ta sauƙe ajiyar zuciya, tare da juyawa tasoma ƙoƙarin shafa mai ajikinta, don acikin yanayin ɓacin ran da take ciki batajin zata wani iya nunawa Balkeesun cewa tayi farinciki da zuwanta. Cikin yanayi na tsantsar mamaki Balkeesu ke kallon Zalihan, ba abun daya ɗaga hankalinta kamar ganin gashin Zaleehan ajiƙe da tayi, cikin mamaki haɗi da tsantsar gulma dake cinta tace. "Zaleeha badai barinsa kikayi yayi ba?." Juyowa Zaleeha tayi tare da ɗan dubanta, cikin rashin fahimtan maganan Balkeesun fuska a haɗe tace. "Yayi me?." Hararanta Balkeesu tayi tare da cewa. "Meyasamu gashinki naganshi ajiƙe? inafatan ba kanki kika mallaka masa ba dai ko?." Wani irin harara Zaleeha ta bankawa Balkeesu, tare dayi mata kallo, irin na baki da hankali ɗinnan. Cikin hasala ta furzar da iskan bakinta, inda tace "Allah ya sauwaƙe ni Zaleeha nabawa wani wanda ba zaɓin raina ba jikina,  ke koda ma zan iya mallakawa wani kaina, to kidaina tunanin zan mallakawa wannan mugun virginty ɗina. To wai ma kina tunanin ayanda yake always akan wheelchair zai iya amsan virgin ɗin macene, chab shirme ma kenan, mutumin da kullum yake bisa kujera kamar wani sarki."  taƙare maganan tana me taɓe bakinta. Murmushin jin daɗi Balkeesu tayi tare da cewa. "Nasani ko zai iya karɓa abu a duhu." Tsuka Zaleeha tayi tare da cigaba da shafa body lotion ɗinta. Tana kammalawa taɗan murza powder akan baby face ɗinta,  tashi tayi tare da ƙarasawa gaban makeken drawer ɗinta,  wani yadi mai laushi wanda yaji ɗinkin riga da sket ta ciro tare da sanyawa, sosai kayan yayi masifar amsar jikinta, sosai surar jikinta ya bayyana, musamman ma hips ɗinta, dogon gashinta ya kama atsakiyar kanta, inda tayiwa kanta wanka da wani turaren oud mai ƙamshin gaske. Duk abun nan da takeyi idanun Balkeesu na kanta, sosai Zaleehan tayi mata kyau,  tarasa meyasa hakanan Zaleeha kowani kaya tasa sai sunyi mata kyau, wannan yana ɗaya daga cikin abun da yasa, akullum kishin Zaleehan ke ƙara ruruwa acikin ranta, akusa da ita Zaleeha ta zauna tare da dubanta, cikin takaicin abun daya faru jiya tsakaninsu da Saifuddeen ɗin tace. "Bazan zauna ba Balkeesu, inajin kamar ana huramin wuta aƙasan zuciyata, sam bazan iya cigaba da zama agidannan ba, wlh ji nake kamar ana korata daga ɗakin, akullum tsanarsa ƙara yawa take acikin zuciyata, banajin zan zauna har zuwa lokacin da muka tsara in sashi ya sakenin, idan ban gudu yauba to tabbas zan gudu gobe." Murmshin gefen baki Balkeesu tayi, take zuciyarta tayi haske, dajin maganganun Zaleehan saitaji kaman an ɗauke mata wani nauyi dake kan ƙahon zuciyarta ne. Gyara zama tayi tare da duban Zaleehan cikin ƙara ƙarfafa mata taurin zuciya tace. "Bazan ce kada ki gudu yau ko gobe ba Zaleeha, saidai kuma guduwarki da gaggawa, zai iya haifar da rugujewar plant ɗinmu, tunda ai in guduwa kikayi da aurensa a kanki zaki gudu ko, ni kuma nafi son ki sashi ya sakeki inma zaki gudun kinga kin fita rayuwarsa salim alim, sannan kadafa ki manta da cewar shekaran jiyannan aka kawoki, kibar maganan guduwan nan har sai lokacin da muka tsara ya cika please ki tsurfa musu rashi mitunci gidan gaba ɗaya ta yadda dole ya sakeki." Kai Zaleeha ta rinƙa jujjuya mata cikin sanyin sauti tace. "Bazan iyaba, me mutanen gidan sukayi min da zan musu rashin ɗa'a? Ina son Umminshi dan tanada kirki hakama ƙannenshi suna sona, kuma nima ina sonsu musamman Ummi da autanta, Kuma shima ɗin ya za'ayi in mishi rashin kunyar bayan tsoronshi nakeji yanada kwarjini da yawa, ko idanunshi bana iya jurar gani, kuma dai ko yaya zanyi yanzu yana matsayin mijina ne, ya zanyi mishi tijara Allah yayi fushi dani in tarawa kaina zunubi. Gwara kawai in gudu yafi min al'khairi, bazan iya zaman ɗakin nanba da gidan Allah ji nake kamar korata akeyi." Wani irin mugun harara Bilkeesu ta watsa mata kana tace. "To mai imani da miji da tsoron Allah ai sai ki gudun kifi ruwa gudu in kinga dama ki dai sani in kin gudun nema tofa da aurenshi a kanki." Shiru Zaleeha tayi tare da kawar da kanta gefe, tarantse bazata zauna da Saifuddeen ba, tagwanmace ta tabbata babu aure datai ta zauna dashi, tana ji a jikinta da zuciyarta cewa zata jira abun sonta, koda nan da shekara ɗari ne,  sam zama da Saifudden banata bane. Saifuddeen kuwa, hakanan yakejin zuciyarsa wasai tun jiyan,   sosai murmushi ke bayyana akan kyakkyawar fuskarsa, musamman ma idan ya tuna da mood ɗin Zaleehan na jiyan tsantsar tsoronshi ne da fargaba ya hango acikin ƙwayan idanunta can ƙasan tsiwar da take mishi,  kaitsaye banɗakinsa ya wuce,  wanka yayi sannan yafito inda ya kimtsa kansa cikin wata ɗanyar purpule ɗin shadda mai masifar kyau, sosai yayi kyau, yayinda farar fatarsa taƙara bayyana acikin kayan,  shaddan irin ɗinkin nan na half jumper akayi mata,kasancewar haka nan shiyake bayason full jumper yafison half, duba da yanayinsa wanda ko yaushe azaune yake, so bayason duk wani abu dazai takurasa. turarensa mai daɗin ƙamshi ya fesa, tare da sanya Cumb yaƙara taje kwantacciyar suman dake kansa, ƙarasawa gaban mirror yayi tare da ɗan duban kansa, shikansa yasan cewa yayi kyau, cikin nutsuwa ya danna madannin kekensa, wayoyinsa kawai ya ɗauka, inda ya fice daga cikin ɗakin, koda yazo falon na Zaleeha bai iske kowa cikinsa ba, hakan yasa kaitsaye yafice daga sashin nasu. Direct ɓangaren Umminsa ya nufa, tundaga bakin ƙofar falon na Ummi yakejin hayaniya na tashi, koda ya shiga nan ya iske su, Ahmad, Ishaq, Wareesu, Saminu da kuma Saleesu, Mudassir harma da Hisham da Jabeer, Aziz gaba ɗayansu sun baje, yayinda aka cika musu gabansu da kayan ciye ciye, Ahmad da Salisu ba kunya haka suke lodawa cikinsu abinci, sam baruwansu da wani surkuntaka, saboda sunaganin duk suɗin ƴan uwan junane, haka kuma Ummi mahaifiyace agaresu, saboda haka babu wani batun noƙe-noƙe, duk da cewar ansan fulani da kunya, saidai sabo da kuma zumuncin dake tsakaninsu ya goge wannan kunyan. Cikin mamaki yake kallonsu don sam basu sanar dashi zuwansu ba. Ƙarasowa cikin falon yayi,  inda yakai hannu ya zunguri Ishaq wanda ke  ta faman suɗe hannunsa wanda yaci masa dashi, bakomai yasashi suɗe hannunba kuwa face daɗin miyar masan, shikam har yau baiga macen da takai Ummin Saifuddeen iya girki ba. Ishaq kuwa cikin gane wanda ya zungureshi yace. "Banason wulaƙanci fa Saifuddeen, wato wulaƙanci zaka mana saboda mun riga mun damƙa maka amaryarka a hannunka ko?." Gaba ɗayansu sukayi murmushi inda Saminu yace. "Manta dashi da Allah, nasan bazai wuce haushinmu yakeji ba, kasan dai Saifuddeen sakaline baison wani ya raɓi masa Umminsa, kuma mumadai Ummin nan nasonmu." Saminu yaƙare maganar yana me kai loman gandar fatan saniya, wanda yaji haɗi sosai, sai ƙamshin su kanumfari yake. Kai Ahmad ya girgiza tare da duban Saminu cikin yanayi na tsokana yace. "Surkinka nefa Yayan matarka." Hararansa Saminu yayi tare da cewa. "Kamanta tare mukai wasan ƙasa." Dukansu suka saka dariya, banda Saifuddeen wanda shi kullum murmushine aikinsa, da haka yasaba kuma hakan yafi yi masa kyau, aduk sanda yayi murmushi idan kumatunsa da tsakiyar gemunshi da goshinsa suka lotsa, sai yayi wani irin fitinannen kyau. Dai-dai lokacin Ummi da Goggo Dada suka fito daga cikin kitchine, bayansu kuwa Raliya ce riƙe da plate, wanda samansa ke shaƙe da yankakkun kayan fruits, agabansu ta dire musu plate ɗin, duban Ummi Saifuddeen yayi tare da shagwaɓe fuskarsa, cikin body language ɗinsa yayi mata alama da cewa. "Shine kika wahalar da kanki wajen haɗawa waƴannan ƙattin abun karin kumallo ko bayan ga matansu!." Gane abunda yake nufi yasanya Ummi sakin murmushi,  ƙarasowa cikin falon tayi tare da sanya hannu ta shafi lallausan suman kansa, cikin kulawa tace. "Ae duk al'barkacin aurenka sukeci." Jin abun da Ummin nasa tafaɗa yasanyashi sakin murmushi, idanunsa ya ɗan lumshe, ahankali ya dubi Goggo Dada nan yayi mata alamun gaisuwa, da fara'a ɗauke akan fuskarta ta amsa, tare da ƙarayi masa murnar biki. Nan suka zauna inda suka shiga ɗan taɓa hira kaɗan, su Hisham na gama kammala cin abincin Goggo Dada tasanar dasu cewa zasu buɗe kan ango da amarya tunda dai jiya bata samu taje wajen diner ɗinba,  nan dukansu sukayi na'am, inda Aunty Meenat ma da fitowarta daga ɗakin Ummi kenan tace itama zata yiwa ango nasa liƙin,  su Adda Rahama da Raihana ne suka firfito falon, nan fa Ummi tace da Raihana taje ta ƙirawo amarya. Zaleeha kuwa har zuwa yanzu suna tare da Balkeesu, inda Balkeesu ke ƙara fomfata tana kuma kunnata akan kada ta gudu ta tsaya ta fetsarewa mutanen gidan ta yadda uwarshi da kanta zatasa ya saketa shi kuma ta nuna kasheshi zatayi,  ita dai Zaleeha abun daya dameta ne ya isheta don wannan karon dai zugar bilkeesu ba abar ɗaukar mai hankali bane, to bare kuma asirin Mama ya riga zugar tasiri. Ƙoƙarin kwanciya take, sukajiyo knocking door,  azaton Zaleeha Zaheera dake kallo afalo ne hakan yasa tace. "Yes come in." Ahankali Raihana tatura ƙofar ɗakin tashiga, ganin Raihana yasa Zaleeha ɗan sakin fuskanta, duk da batasan wacece ita ba, amma kallo ɗaya tayi mata ta hango matsanancin kaman da sukeyi da Aljanin gurgun da tsanarsa tayi mata tsaye acikin rai sosai ta yaba da kyan Raihana kuma har ranta taji tana sonta. Balkeesu kuwa baki tasake tana ƙarewa Raihanan kallo, gaba ɗayama hankalinta yatafi ga tsadadden zanin dake jikin Raihana'n, domin kuwa babban Chiganvy ne ɗan ubansu. Murmushi Raihana tayi tare da duban Zaleeha cikin kulawa tace. "Idan babu damuwa muna buƙatarki afalo, za'a ɗanyi muku buɗan kai ne!." Dammm haka Zaleeha taji ƙirjinta ya doka, sam batason abun dazai ƙara haɗata dashi, musamman idan ta tuna da abun daya shiga tsakaninsu jiya saitaji kanta kamar zai buga gaba ɗaya tsoro lamarinshi ke bata. Cikin baƙinciki da takaici Balkeesu tace. "Mezai hanamu zuwa kuwa, ai zamuzo yanzun nan." tafaɗa tana me miƙewa tsaye dan samawa Zaleeha mayafi, ɗan murmushi Raihana tayi tare da cewa. "Badamuwa, ai bama sai kunzo ku dukanku ba, itaɗin dai kawai muke buƙata!." ta ƙarishe mgnar cikin yatsina fuska dan sam ita da Bilkeesu bata konta mataba, Zaleehan kanta a fakaice take sonta tunda ance bata son Hammanta ita kuwa duk wanda yace baison Hamma Saifuddeen ɗinta itama bazata sotaba. Ƙasake Balkeesu tayi tare da watsawa Raihana harara ƙasa-ƙasa, tabbas maganace afakaice Raihanan ta faɗa mata, amma dai koma menene ta rantse saitaje anyi buɗan kan da'ita. Wani tsantsareren mayafi laffaya Zaleeha ta yafa aduka jikinta inda ya sauƙo ya rufe har fuskarta, wani flat shoe kalan yadin jikinta ta sanya aƙafafunta,  Raihana da kanta taƙara fesa mata turare nan Balkeesu uwar gulma tariƙe Zaleehan, Raihana na gaba sukuma suna biye da ita abaya haka suka nufi cikin gidan. Sunanan zaune afalo suna ɗan taɓa hira, daddaɗan ƙamshin daya ziyarci hancinsa shiyafara sanar masa da zuwanta, juyawan dazaiyi kuwa ya hangota cikin wani light orrange ɗin mayafin laffaya mai tsananin kyaun gaske, sai walwali da sheƙi yake, Raihana da kanta ta kamo Zaleehan, inda ta zaunar da ita akan kujeran dake facing na Saifuddeen ɗin, tsulum Balkeesu daketa faman ƙarewa falon kallo tazo ta zauna akusa da ita, sosai Balkeesu tasha mamakin haɗuwan falon, wanda kuma yake mallakin Ummi, sam abubuwan mutanen suna shammatan ta, kwata-kwata bata taɓa tunanin yawan arzikinsu har yakai haka ba, duk abun da sukayi takan ɗauka, ƙaryane kawai da fafa, wani abun kuwa takanyi tunanin sunayinshi ne kawai don su mallaki Zaleehan, saidai kuma tunaninta ya fara sauyawa ne tun lokacin da aka kawo Zaleehan gidan,  yanzu kam tagama yarda cewa suɗin masu arziki ne, duba da irin kuɗin da aka kashe wajen ƙawatawa Ummin nasu falonta, uwa uba ga ƴan uwan Saifuddeen ɗin da ako yaushe suke cikin sutura mai kyau, da shiga ta al'farma domin kab cikinsu babu wacce take sanye da ƙasa da  kayan dubu ashirin, saima yayi sama, kowa kagani acikinsu masha Allah, Gaba ɗayansu cikin jindaɗi da rufin asiri suke rayuwarsu gasu kyawawane ajin forko, duban Adda Rahama wanda ke sanye da wani jan leshi mai shegen tsada tayi, taɓe baki tayi, cikin ranta tace "Ƴan iska, kowa kagani cikin farinciki yake, badai Saifuddeen shine farincikin ku ba, hmmm ai na gano lagonsa, rashin Zaleeha shine baƙin cikinsa, kukuma baƙin cikinsa shine tashin hankalinku, to kuwa kushiryawa tashin hankali, don wallahi al'ƙawari nayi sai nasa Zaleeha tasa ya saketa saki mafi muni kafin insata ta gudu daga gidannan."   ƙasa-ƙasa tayi ƙwafa, tare da cigaba da ƙare musu kallo. ita kuwa Zaleeha shiru tayi kanta a sunkuye ta cikin mayafin ta zubawa ƙafafun Saifuddeen ido, wanda suke ƙal-ƙal kana daga ganinsu zasuyi tsananin laushi da taushi kodan hakan bazai rasa nasaba da rashin takawarsuba daga ganin fatar tiɓis zatayishi laushi, yatsunshi ta zurawa ido tana kallonsu tamkar ka taɓasu jini ya tsallo kan faratun yatsun nashi ta maida idanunta ganinsu ƙal-ƙal yasata ɗan kauda idonta, a ranta take tajjudin yawan tsabta na wannan nakasasshen aljanin yakeda shi sabida ita fa tana alaƙanta kyan Saifuddeen da iska, takalmanshi dake gefe ta kalla wanda suke na Gucci a tsiwace cikin ranta tace, "Hmmmm gurgu kafi mai ƙafa iya shege, shi komai nashi mai tsada, wannan da lafiyarsa lau, alla'anɗi iya ƙasaitar da zai zuba. Shi kuwa Saifuddeen kota kanta baibiba hira yake da abokanshi. Bilkeesu kuwa sam bata tsinke da al'amarin nasu ba saida taga yanda Ummi da kuma Goggo Dada ke yiwa Saifuddeen ɗin ɓarin kuɗi, sosai suka zuba masa kuɗi, inda Aunty Meenat ma tazuba masa nata, nanfa kuma suka dawo kan Zaleeha,  Goggo Dada ne tasa Raliya ta buɗe mata mayafin, nanfa suka shiga zuba mata kuɗi itama, sosai suka zuba mata nairori, Ummi ne ta dubi Raliya inda tace taje ɗaki akwai wani gift da ta ajiye akan gado ta ɗauko mata, babu ɓata lokaci kuwa saiga Raliya ta dawo, hannunta ɗauke da wani ƙaton gift wanda aka masa ado da pink flowers, sosai yayi kyau, hannun Zaleeha Ummi takamo inda ta sanya mata babban gift ɗin cikin nutsuwa tace. "Wannan tukuici ne agareki na zamantowa matar ɗana da kikayi, Allah Ubangiji yayiwa rayuwar aurenku al'barka, sannan yabaku zuri'a ta gari tare da zaman lafiya mai ɗorewa." Gaba ɗaya jama'an wajen suka amsa da Ameen, saidai banda Zaleeha, sai kanta data sunkuyar alamun jin kunya, kana tanata wasa da yatsun hannunta. Sosai Ummi taji ƙaunar ƴarinyar a ranta komai da nitsuwa da kunya take yinshi. Balkeesu kuwa da ƙarfi tafaɗi Ameen ɗin, wanda hakan kuwa da biyu tayishi, sam bataso sugane cewa itaɗin munafukace, don tafuskanci cewa kamar, Raihana ta ganota. Haka suka gamayi musu buɗan kaiɗin cikin nuna ƙauna, Balkeesu ne tajata suka koma part ɗinta bayan duk an haɗa mata kuɗin. Su kuwa su Saifuddeen anan falon Ummin sukaci gaba da zama. Suna shiga cikin ɗaki, Balkeesu wanda jikinta ke mazari ta amshi gift ɗin, hannunta har rawa yake wajen ƙoƙarin buɗewa. Zaleeha kuwa mayafin dake jikinta ta yaye, cikin ƙunan zuciya tayi wurgi da mayafin, faɗawa kan gado tayi tare da lumshe idanunta, sam batajin tsanar kowa dake cikin gidan saishi kaɗai haka nan taji tana so duk mutanen gidan sabida ta lura sunada karamci da mutunci kuma sunfi ƙarfi tijara koda da ƙwayar zarrane a wurinta. Ihun da Balkeesu tayi shiyasanya Zaleehan ɗagowa da sauri ta dubi Balkeesun, cikin yanayin mamaki haɗi da firgita Balkeesu tace. "Gold, Zaleeha Gold ne fa aciki da kuma turaruka masu tsada ga kuɗin duk ke akabarwa." Wani haɗaɗɗen kwalban turare Balkeesun ta zaro tare da cewa. "Zaleeha kinkuwa san kuɗin wannan turaren?, oh my God ashe waƴannan mutanen masu kuɗine sosai har haka!!." Wani dan ƙareren agogo da sarƙan gold Balkeesun ta ciro, wanda aka ƙawata gidansu da wani farin glass, cike da mamaki tace. "Lallai kuwa mutanen nan sunshiryawa auren nan, what a surprise."  Kallon sarƙa da agogon Zaleeha tayi, wanda lokaci ɗaya sukayi bala'in yi mata kyau, amma ayanda takejin zuciyarta yasa bata  nuna ba, maida kanta jikin pillow kawai tayi tare da lumshe idanunta, abun daya dameta shine aranta ita kuɗinsu baya gabanta. Balkeesu kuwa kaman Zararriya haka ta dinga yaba kayan, saida tagaji don kanta sannan tayi shiru, nan kumafa zuciyar hassadan nata ta motsa, take taji wani danƙareren baƙin ciki ya cika zuciyarta, inama da ace itace tasamu wannan kayan more rayuwa haka? wai ma shin maiyasa ita rayuwa bata zuwar mata da garaɓasa haka? lallaima dole ne taraba Zaleeha da wannan gidan, idan bahaka ba tanaji tanagani zasu maida Zaleeha millionaire girl, ita tananan zaune Zaleeha zata shiga cikin sahun manyan mata, wanda kokaɗan kuwa ita bata fatan haka, dole ne ma taƙara zuga Zaleeha akan batun a sakin kafin guduwarta, don kuwa ayau ɗin ta hango irin tsananin soyayyar da dangin Saifuddeen ɗin keyi masa, tabbas ayanda tafahimta ayanda suke masifar sonsa, to zasu iya ɓatawa da duk wani wanda ya ɓata masa, dakuwa zasu tsani Zaleeha da tafi kowa murna. Saboda tsananin ƙyashi da hassadan dayaci Balkeesu kasa cigaba da zama agidan tayi, lokaci guda tayiwa Zaleehan Sallama inda takoma gida, zuciyarta cike da saƙe-saƙe kala-kala. Tun wannan fitowan da Zaleeha tayi na zuwa buɗan kai, daganan bata sake fitowa ko falo ba, abincin da aka kawo mata ma har ɗaki, Raliya takawo mata ta ajiye, sam kasa cin abincin tayi, Zaheera ce taci inda tacika cikinta, itakam babu abun daya shallaketa, tanajin daɗin zaman gidan, babu wani takura, dagaci sai kallo, dama ita tanan tafi kauri, aiki ko na misƙala zarratinne basonshi take ba, wannan dalilin ma yana ɗaya daga cikin abun dayasa ta ƙi komawa gida, domin tasan da zaran takoma tofa aiki za'aita sakata kamar jaka, itakuwa sam bason hakan take ba, ga shi Ziyada ba zama take ba, always tana gidan Hajja ga Zaleeha dake yawan yin wasu aiyukan kuma an aurarta. Saifuddeen kuwa gaba ɗaya wunin yau dasu Ishaq yayisa, don sosai suka zauna don ɗebe masa kewa, kasancewar acikinsu babu wanda baisan matsayin auren Saifuddeen da Zaleehan ba, kowa yasan baso takeyi ba, dan haka nan suka wuni sai dare suka tattafi. Koda Yadawo sallan Isha, kai tsaye falonsa ya wuce, koda yazo falonta ko ƙofar ɗakinta bai kalla ba, dan shima yau ƴan jan ajinnasa suna kusa, duk dacewa yana da buƙatar jinta ajikinsa, amma dole haka zai daure, dan yasan koda yaje ma tofa faɗa zasuyi, shikuwa bayanzu yakeson yafara gwada mata ƴar ƙarfi ba. Koda yashiga haɗaɗɗen bedroom ɗinsa wanka yayi, inda ya kimtsa kansa cikin kayan baccinsa, kwanciya yayi tare da jawo laptop ɗinsa, nan yayi ƴan danne danne, a hankali ya zubawa system ɗin ido, yana kallon motar nan da yasa Hayatuddeen ya liƙa mata na'ura tana tafe har gidan da ta shiga, yaga matasan baki ɗaya sai kuma duk sukayi cikin gidan hakanne ya hanashi damar ganin abinda ke faruwa a cikin gidan. bincike yaci gaba da yi akan gidan da matasan har saida ya samu iya abinda zai samu to amman har yanzu babu ƙwaƙran laifin da za'a kamasu dumu-dumu a ciki haka dai ya haɗa abinda ya samu, kafun daga bisani bacci ɓarawo ya ɗaukesa. A cikin gidan Dalla kuwa,koda yaranshi suka gama yi mishi bayanin abinda ya faru, cikin tsananin tashin hankali yace. "To meyasa!? Waya ɓata min tsarina!? ya akayi haka ta faru?." sai ya kuma shaƙo wuyan Lado dake gabanshi cikin rashin imani yace. "Shekara ɗaya cur ban fatattaka ƴar kowaba, nace muku babu ƴar da zan taɓa a kanta nakeso na gwada lafiyata, meyasa zakuyi min kuskuren da har wani ya gane ya bata tsaro, nafa ce muku a buƙace nake." ingiza Lado yayo ganin yana kakarin mutuwa, shi kuwa Lado tari ya rinƙayi ba sassauci. yayinda gaba ɗaya sauran yaran suka sha jinin jikinsu, shiko Dalla safa da marwa ya farayi a kansu yana wani irin numfashin masifa da tijara da ƙwarewa a dabanci cikin yaƙini da kansho murya a hargitse yace. "Wallahi wallahi sai na girgiza zuƙatan gombawa sai kowa yaji kwatankwacin baƙin cikin da naji, na rantse da ubangijin dake busan numfashi sai na keta haddin ƴan mata huɗu a wuni ɗaya shine fansar budurcin shegiyar yarinyar nan da a kanta wannan sojan yamin dandatsan ɗan akuya." wata iriyar wawuyar tsawa ya tamfatsa musu tare da cewa. "Dole ku nemo min zuƙa-zuƙan ƴan mata huɗu dan na gwada lafiyata a kansu." cikin biyayya da tsoro sukace, "An gama." shi kuwa Dalla a harzuƙe yace. "Ku nemo min su daga yau zuwa mako biyu rak, ita kuwa shegiyar yarinyar nan dan nasan ba namijin da za'a kaiwa ita ya kwana da ita ɗaki ɗaya bai ratsa budurcinta ba, dan haka na ɗage neman har sai nanda wani lokacin zan nemeta in mata fyaɗe mafi muni irin fyaɗen da ban taɓa yiwa ƴar kowaba, zan kwana akanta, kuma kuma kowa sai yayi awa biyu a kanta wannan ganimar samotane." cikin jin daɗin ganimar daya alƙawaranta musu, suka sallameshi suka tafi. A can ɗakin Zaleeha kuwa, duk yanda taso bacci ya ɗauketa abun yaci tura, tayi juyin harta gaji amma bacci yaƙi ɗaukarta, gaba ɗaya zuciyarta cike take da tunani kala-kala,  sosai soyayyarsa ke ƙara yawaita acikin zuciyarta, duk wannan rububin da akeyi da sonsa take kwana take tashi, har zuwa yau batacire rai da samunsa ba, tasa aranta cewa komin daɗewa watarana zata gansa. Tashi zaune tayi ji take kamar korata akeyi daga cikin ɗakin sam bata samu tayi isshen bacci, gyara zamanta tayi tare dakai dubanta ga Zaheera wacce ke kwance akan kujera tanata sharar baccinta, inda tayi ɗai-ɗai da ƙafafunta, ahankali ta dawo da dubanta ga jikinta, sanye take da wata fitinanniyar sleeping gown, irin mai fitar da surar jiki ɗinnan, sosai rigan dake da kalan coffee ta amshi farar fatarta, daga wuyan rigar har zuwa kan ƙirjinta gaba ɗaya net ne irin mai  showing skin ɗinnan,  yayinda kwata-kwata tsayin rigar yakasance iya cinyarta ne, hannu tasa taɗan shafi dogon gashinta dake baje bisa kafaɗunta,   ahankali ta zuro da ƙafafunta ƙasa, tashi daga kan gadon tayi tare da miƙewa tsaye. gaba ɗaya jin ɗakin take ya mata ƙunci, ahankali take tafiya harta ƙarasa jikin ƙofar fita daga ɗakin, ahankali ta murɗa handle ɗin ƙofar tare da sanya key ta buɗe ƙofar,  cikin nutsuwa tafito zuwa falo, ahankali take ɗan takawa harzuwa tsakiyan falon nan taɗan shiga ƙarewa falon kallo, sai alokacinne ma take yaba tsantsar kyawun kayan da Yaya Ahmad ɗin ya saya ma, taga masifar tsaruwar ginin falon, amma saboda yakasance mallaki ga Saifuddeen yasa, ko kaɗan bataji zata yaba tsarin falon da gidan ba, ƙarasawa jikin window'n falon tayi ta tsaya, ahankali taɗan buɗe glass ɗin window'n, take wani irin ni'inmtaccen ƙamshi haɗi da sanyin shuke shuken dake wajen suka daki fuskarta, lumshe idanunta tayi tare da sake manna jikinta da bango tana shaƙan ƙamshin... Saifuddeen kuwa wani iri fitinannan ƙishine ya tasoshi gaba cikin baccinsa. Ahankali Yake buɗe kyawawan idanunsa, hakanan yaji wani irin sanyi na ratsa zuciyarsa, sake buɗe idanunsa yayi tare da sauƙesu akan agogon bangon dake saƙale cikin ɗakin. 1:40 am agogon ya nuna, hakanne yasashi ɗan tashi ya zauna, mamakin farkawarsa adai-dai wannan lokacin yake, jin masifan ƙishirwa na damunsa yajawo kekensa inda ya hau, ya zauna ɗas a kai ya tura kansa har zuwa gaban ɗan madaidaicin fridge din dake cikin ɗakin, koda ya buɗe fridge ɗin gani yayi babu ruwa, gaba ɗaya drinks ne suka cika fridge'n, dolensa haka ya murɗa handle ɗin kofar ɗakin inda yanufi falonsa. Gaban fridgen dake cikin falon ya ƙarasa, inda ya buɗe ya ɗauki goran ruwa, ahankali ya ɓalle murfin tare dakai goran bakinsa,  sosai yasha ruwan saida yaji ya ƙoshi kafun ya aje goran,  aƙoƙarinsa na komawa ɗakinsa ne idanunsa suka gane masa haske acikin falon Zaleeha,  kansa kawai ya girgiza, har zai koma ɗaki kuma, saiya tuna da cewa baya son abar ƙwan wuta akunne matuƙar za'a kwanta yana da kyau adinga kashe ƙoyayen wuta. Ahankali yaƙarasa jikin ƙofar falon nasa ya buɗe,  kekensa ya danna inda yaƙaraso zuwa falon nata, idanunsa ne sukayi masa tozali da bayanta, inda har yanzu take tsaye jikin window. Kallonta yasomayi tundaga ƙasa, santala santalan fararen cinyoyinta ne  suka cika masa idanu, ahankali yasauƙe idanunsa akan shape ɗin bayanta,  inda kyawawan hips ɗinta suka bayyana sosai,  still idanunsa ne suka sauƙa akan dogon gashinta dake baje bisa bayanta. Idanunsa ya lumshe tare da shaƙan daddaɗan ƙamshinta dake shawagi acikin falon, sake buɗe idanunsa yayi inda ya ƙurawa shape ɗin bayanta ido, take yaji gaba ɗaya tsikar jikinsa sun mimmiƙe, lokaci guda wani irin fitinanniyar sha'awa ya taso masa. Take yaji wani abu na harbawa acikin jikinsa. Zaleeha kuwa ɗan gajiya da tsayuwan tayi hakan yasa ta juyo dan dawowa cikin falon, kanta aƙasa dan kwata-kwata bata tsammaci ganin wani awannan lokacin ba. Kusan numfashin Saifuddeen ne yaso ƙwacewa alokacin da idanunsa sukayi masa tozali da cikakkun breast ɗinta, wanda suka bayyana kansu ta cikin rigar hartakai ga ana iya ganin kusan rabinsu ta saman rigar, uwa uba ga shatin nipples ɗinta daya bayyana raɗau tacikin lafaffiyar rigar dake jikinta. Wani irin yaarr yaaarr haka yaji ajikinsa, take wani abu ya mamaye gaba ɗaya ilahirin jikinsa, batare daya saniba wani irin numfashi ya ƙwace masa. Jin fusgar numfashin mutum yasa Zaleeha ɗago kanta atsorace, ƙara tasake, sakamakon ganinsa da tayi, tare da saurin ja da baya, sam bata tsammaci ganinsa awannan lokacin ba. Da sauri ta sanya hannu ta dafe ƙirjita, cikin tsoro haɗi da bugun zuciyarta daya tsananta bugawa,  ajiyar zuciya take sauƙewa, sosai ganinsa ya tsoratata, shikuwa Saifuddeen tsuke fuska yayi tare da kafeta da mayan idanunsa, wanda lokaci guda suka sanja launi, inda suka tashi daga fafare zuwa wasu kalan na daban. a fakaice yake kallon ƙirjinta, wanda yake ɗagowa ahankali- hankali yasa, tabbas tsoratan da tayine yasa hakan,  laɓɓansa ya cija tare da yamutsa fuska kana ya sanya hannu ya ɗan shafa kekyawan sajenshi da ya kwanta lib-lib, cikin wani irin yanayi yasake kallonta, saidai wannan karon bai yarda yasauƙe idanunsa akan beautiful breast ɗinta dasuke mugun rikirkitashi ba, musamman ma shatin nipples ɗinta, wanda idan ya kalla sai jijiyar jikinsa ta harba. Shiyasa ya kauda kanshi dan bafa yason raini, kada tayi zaton sha'awarta ke rinjayarsa kada kuma ta ɗaukeshi mayen mace. Ɗan janye hannunta daga kanta tayi tare da dubansa, lokaci guda ta haɗe fuska tare da sanya hannu ta kama waist ɗinta. Cikin faɗa da tsiwa wanda dama tuntuni suke kwance aƙasan zuciyarta ga kuma tsoro baki ta murguɗa mishi tare da cewa. "Ae bai kamata bama nayi mamakin ganinka at this time ba, because aljani koda yaushe yana nan kuma zaije ko ina kuma zaiyi abinda yake so!." Hararansa tayi tare daɗan juya idanunta cikin halin ko inkula tace. "Meye kake wani kallona? idan ma kai mayene wallahi saidai kaci kanka domin nidai nafi ƙarfinka, kurwata kurrrr  ni wallahi ka dena tsareni da waɗannan mayatattun ida nun naka." Taƙare maganar tana jujjuya masa idanu, haɗi da kama ƙugunta, sam tagama mantawa da shigar dake jikinta kwata kwata. Shikuwa Saifuddeen murmushin ƙasan zuciya yayi kana ya lumshe idanunsa tare da buɗewa yakuma watsa mata su, da sauri ta ɗauke idanunta daga kallonsa tare dajin wata irin faɗuwar gaba ya rusketa kwarjininshi da haibarsa suka mamaye fuskarsa a take taji shakkarshi da shayinshi. Lokaci guda taji wani irin abu yana bi ta cikin jikinta har zuwa cikin zuciyarta dake harbawa da sauri-sauri. Ahankali ya danna madannin kekensa inda yasoma nufowa gareta, ganin haka yasa tasoma ja da baya baya, still shikuma baidaina biyota ba, babu abun dayaso gusar da tunaninta kamar yanda ƙwayan idanunsa suka sanja launi daga farare zuwa ja, sannan gaba ɗaya sun rikiɗe sun canja launi zuwa yanayin bacci. Saura baifi taku uku tsakaninsu ba, ta juya inda ta buɗe ƙofar ɗakinta ta faɗa ciki da gudu, tana shiga da sauri ta murzawa ƙofar ɗakin key. Ganin alaman saka key aƙofar yasanyashi lumshe idanunsa tare yin murmushin mugunta da sanya hannunsa ya dafe goshinsa, ahankali yajuya yanufi ɓangarensa, idanunsa tuni sun rufe wani irin masifaffen sha'awa ne ke taso masa irin wanda bai taɓa ji ba kuwa. A ranshi yake cewa. "Farar kura ba ga tsoro ga son bada tsoro, wai ita in an barta ni zata razana, fitinanniya mai bakin tsiwa, yarinya zanyi mgninki bakin zai mace." Adaddafe yasamu yahau kan gadonsa, lumshe idanunsa yayi tare dayin kwanciyar rubda ciki, sosai yakejin wani matsanancin feeling, yayinda dazaran ya kulle idanunsa, hoton haɗaɗɗen surar ƙirjinta dana bayanta keyi masa gizo, tabbas  shikam ya yaba da kyawu haɗi da cikar surar Zaleeha, ƙam haka ya ruggume pillow, sosai yakejin matsananfin feelings ɗinta, tunowa da yanda ya tsotsi laɓɓanta jiya, shiya sanya ya ƙara rikicewa, sosai yake sonjin ɗuminta acikin jikinsa, saidai kuma bashi da wani zaɓi wanda ya wuce haƙuri, dan shi tunani ma yake duk randa ya kusan ceta yaga ta kanshi dan yaga alamun tara mishi jama'a zatayi. Ɓangaren Zaleeha kuwa tana murzawa ƙofar key, da gudu ta haura kan gado tare da shigewa cikin blanket, ƙam haka ta kulle idanunta gaba ɗaya jikinta karkarwa yakeyi, sai alokacinne ma tatuna da irin shigar dake jikinta, take wani irin abu ya tokare maƙoshinta, tashi zaune tayi tare da duban kanta, ganin rabin ƙirjinta awaje, yasa ta cije baki, cikin takaici haɗi da kishin kanta tace. "Sam baicancanci yaga surata ba, wayyo ni maiyasama nafita ne?." Tsuka tayi tare da komawa ta kwanta, baccin tsorone ya ɗauketa batare da ta shiryawa hakan ba. Shikuwa Saifuddeen saida yasha artabu da jikinshi da zuciyarshi sosai kafun ya iya maida bacci. Washe gari. Kamar yanda takeyi tun da tazo gidan haka yauma tayi, tana gama idar da sallah tatafi ɓangaren Ummi inda tagaisheta. Yau ɗinma Ummi cikin so da ƙauna ta amsa mata gaisuwarta, a falo ta haɗu da Saifudddeen da Hayatuddeen bisa dukkan alamu daga masallaci suke, cikin sakin fuska Hayatuddeen yace, "Barka da safiya Aunty Zaleeha." ɗan tsayawa tayi fuska a sake tace. "Barka dai autan Ummi." murmushi yayi tare da cewa. "Ya amarci da gajiyan biki." hararansho taƴi cikin sanyi ta ratsa gefen Hamma Saifuddeen ɗin harara ta cillamishi, sai kuma tayi wuf ta wuceshi kamar dai tsoro take kar ya cabketa abinma dariya ya basu kana suka bita da ido. daga ɓangaren na Ummi kaitsaye part dinsu ta  dawo, komawa tayi tanaɗe akan gado inda tacigaba da baccinta. Acan gidan su Zaleeha kuwa sai jiya Mama tadawo daga tafiyanta da tayi, Baba Malam dai ko sannu baice da ita ba, koda ya lura cewa Zaheera bata gidan, tana can gidan Zaleeha, sosai ransa ya ɓaci, nanfa yasa Ya Ameenu Habu akan su kwashi kayayyakinta na aure da motocinta su kai maita kana su ɗauko Zahira sannan su ƙara yiwa Zaleehan nasiha inda yaje. Hakan kuwa akayi, tuni Ya Ameenu da Habu sukatafi dan ɗauko Zaheeran bayan duk sun lodo kayan aurenta a motocintan. Koda sukaje gidan nasu Saifuddeen sai Ya Aminun ya bawa Habu kuɗi yacewa Habu ya hau keke napep ya koma ya ɗauko motarshi su samu wacce zasu koma da ita tunda duk motoci biyun da suka zo dasu na Zaleehan ne ɗaya na cikin kayan aurenta ɗaya kuma wacce Ya Ahmad ɗinta ya saya mata, Ya Aminu na fitowa cikin motar ya nufi wurin maigaɗinsu akan yaje ya mishi sallama da masu gidan a nan suka haɗu da Ahmad, inda suka gaisa cikin girmamawa da mutum ta juna, Ahmad ne yayi masa jagora har cikin gidan, saida Ya Ameena yafara zuwa ɓangaren Ummi tukunna, cikin mutum tawa ya gaida ta, sannan yayi mata bayanin cewa yazo ɗaukar Zaheera ne,  sosai Ummi taji daɗin karramata da yayi, nan tasake aminta da tarbiyan gidan Baba Malam ɗin, Ahmad ne yayiwa Ya Ameenu jagora zuwa ɓangaren Zaleehan, don kuwa Saifuddeen bayanan, sun tafi meeting ɗin ƙungiyarsu na Jonapwd shida Ishaq. Sosai Zaleeha taji daɗin ganin yayan nata, saidai kuma jin cewa Zaheera yazo ɗauka, yasanya taɗan ɓata fuska, saidai kuma bata isa cewa komai ba, sanin cewa Ya Ameenun nada zafi sosai, babu ruwansa yanzu saiya solleta soso da sabulu. Haka Zaheera ma ranta baiso ba, don dai kawai Ya Ameenun ne yazo da kansa, amma da wanine bazata bisa ba, don ita ke gadin Zaleeha a cewarsu a yadda suka tsara kenan wai ai duk nacinsa bazai zo inda takeba in Zahira nan kuma da ita aketa plant ɗin yadda Zaleeha zata gudu, Haka dole ta haɗo kayanta, Gyara zama ya Ameenu yayi, cikin kulawa haɗi da kwantar da murya, yashigayiwa Zaleehan nasiha, dayi mata nuni akan tabi mijinta, idan ya umarceta da yinnabu matuƙar bai saɓawa shariya ba yace tayi to koda bataso tayi, domin hakan shine dai-dai domin al'jannarta na ƙarƙashin diga-diginsa . Itadai Zaleeha jinsa kawai take, amma bata ɗauƙa, koda yazo tafiya har compound ɗin gidan ta rakosu, nan kuma yasa Hayatuddeen da Imran dasu Zakariyya kwashe kayayyakinta kab suka shigar mata, sannan ya bata car keys ɗinta duka biyu a hannunta, godiya tayi tare da cewa ya gaishe mata da Ƴar uwarta Maryam. Haka Ya Ameenu yatasa Zaheera suka bar cikin gidan, shikansa ya yaba da tsarin gidan, musamman ma part ɗin Zaleeha wanda yayi matuƙar kyau, shida kansa ya ƙyasa, ya kuma yabawa Saifuddeen sosai, don bakowani namiji bane zai iya ɓarnatar da dukiyarsa wajen ƙawata gida mai kyau kamar haka ba. Tafiyan Zaheera yasa Zaleeha duk taji gidan bayayi mata daɗi, hakanan taji komai ya tsaya mata, batasan dacewa motsin Zaheeran na ɗebe mata kewa ba, sai ayanzu da Zaheeran tatafi, haka ta koma ɗaki ta kwanta, zuciyarta cike da saƙe-saƙe kala-kala. Tananan ƙule aɗaki har akayi sallan isha, Nanfa wani irin tsoro yashiga diro mata, take fargaba ta cika zuciyarta, sam batajin zata iya kwana itakaɗai aɗakin batare da wani nata ba, sosai tsoron sa yashiga zuciyarta, tabbas ayanda taga cikin idanunsa jiya to idan tayi wasa komai zai iya aikata mata, abanza saiya rabata da virginty ɗinta, shikenan kuma daganan yagama cutanta, dan tasa aranta cewa bamakawa daga ranan daya yayi disvirgin ɗinta tofa shikenan itakam ta sallama rai da rayuwa, don baƙinciki ne zaiyi ajalinta tabbas. Tashi tayi daga kan sallayan tare da kai dubanta jikin ƙofar ɗakin, ganin babu key ajikin ƙofar yasa gaba ɗaya hankalinta ya ƙara tashi,  atsorace tashiga neman key ɗin amma bata gani ba. Ƙirjintane yatsananta bugu alokacin da taji motsin mutum a falonta. Shikuwa Saifuddeen lokacin dawowansa kenan daga masallaci, kaitsaye ɗakinsa ya wuce, dan yanaso yaɗan watsa ruwa, kafun ya ya ɗa ci abinci. Jin motsin buɗe kofar falonsa, dakuma rufewa yasanya taɗanji zuciyarta tayi sanyi, cikin hanzari ta ɗauki blanket da pillow, saikuma phone ɗinta, saɗab-saɗab tafito daga cikin ɗakin, ahanzarce tayi hanyar fita daga cikin falon, tana samun kanta aɗan compound ɗin shashin nata kuwa ta saki ajiyar zuciya,  kaitsaye garden ɗin dake cikin part ɗin nata ta nufa wanda yake cike da sanyi da sauraye, kan wata kujera dake ɗan cikin garden din ta kwanta, tare da jawo blanket ta rufa jikinta, ɗaura kanta tayi akan pillow tare da sauƙe ajiyar zuciya, ta dai gwammace kwana awajen da dai ta tsaya aciki ya illata mata rayuwa, zata jure komai amma bazata iya jure abinda zai iya mata ba, hakanan bata tsaya wani mugu yayi disvirgin ɗinta ba tunda ta duba ɗaya ɗakinma babu key sai tayi zaton shine ya zaresu dan karta rufe ƙofa ya samu damar shigowa ya mata fyaɗe injita da faɗi. Raliya kuwa wacce tazo rufe window'n ɗakinta dake abu ɗe ne taga kaman wulgawan mutum ya shiga cikin garden, kanta tasake zurowa ta cikin window'n, nan idanunta suka gane mata Zaleeha dake ƙoƙarin kwanciya akan wata kujeran ƙarfe. Mamakine yakusan  kasheta awajen, sosai abun ya ɗaure mata kai, komawa cikin ɗakin nata tayi ta zauna tare dayin jigum, me hakan yake nufi kenan? tsanar da Zaleeha tayiwa ɗan uwanta har yakai wanda zataƙi haɗa shumfuɗa dashi? har ta gwammaci kwana acikin sauro da ciyawi da sanyi a kan kujerar ƙarfe akan ta kwana dashi. Kanta ta jinjina tare da rumtse idanunta wanda suka ciko da ƙwalla, sam bahaka ta ke wa ɗan uwannata fata ba, babban burinta shine yasamu ingantaccen kulawa daga wajen matar tasa amma meyasa Zaleeha ke gudunsa? kwaffa tayi tare da cewa. "Ko ya zakiyi wlh in sha Allah sai dai ya raɓi jikinki in Allah ya yarda duk iskancinki kin shiga hannu kenan mutu ka raba, ato sai yaci sadakinshi." Tana faɗin haka sai kuma ta miƙe da sauri ta nufi.....! Cikin bedroom ɗin ta da nufin zataje ta sanarwa Ahmad, ko meye ta tuna kuma, oho sai ta koma ta zauna tana nazari. Sosai abun yayiwa Raliya ciwo, koda Ahmad ya fito ganin meya tsareta,  kamar zata faɗa masa saikuma tayi shiru, shi kuwa da bai san meke faruwaba sai janta yayi suka koma bedroom ɗinta dan yana tare da begenta. Ɓangaren Saifuddeen kuwa kwata-kwata ma bai nemi Zaleehan ba, yana fitowa daga wanka kwanciya kawai yayi,  sam bayaso yaje gareta, harma yaga abun da zai rabasa da nutsuwarsa, dan shikaɗai yasan irin azaban dayasha jiya, saboda haka baya sake fatan shan wani azaban kalan wannan, kasancewar agajiye yake hakan yasa yana kwanciya bacci ya ɗaukesa. Zaleeha kuwa gaba ɗaya tatakura akan kujeran da take kwance, sam kujeran bata da daɗin kwanciya bare daɗin bacci, cikin mintuna ƙalilan har jikinta yasomayi mata ciwo, gawani irin masifaffen sanyi dake busawa acikin garden ɗin, mutsutstsuka jikinta kawai takeyi, sosai takejin wuyanta ya ƙage amma kuma bata da wani zaɓi, wanda ya wuce yin haƙurin kwana awajen. Atakure haka bacci ɓarawo yasamu nasarar ɗaukarta. Ƙiran sallan asuban fari da akeyine ya ratsa jikinshi ya bashi lokacin salla yayi, ahankali ya buɗe idanunsa,  ɗan miƙa yayi tare da haɗawa da salati a zuciyarsa, nan yatashi zaune, kekensa ya jawo tare da hawa kanta, cikin nutsuwa da ɗan sauran kasalan bacci yakai kansa banɗaki, wanka yayi tare da ɗauro alwala, kaitsaye yafice daga ɓangaren nasa. Har yaƙarasa jikin ƙofar na Zaleehan saikuma wani tunani yazo masa, take yafasa shiga tada'ita da yayi niyya, sai ya ƙonƙasa mata ƙofar, kana ya juya ya tafi, kai tsaye yawuce masallaci. Zaleeha kuwa dama gaba ɗaya batayi wani ishashshen bacci ba, dan sanyine awajen sosai, jin motsi alaman cewa yatafi masallaci yasata tashi zaune, cikin sauri ta ɗau bargon haɗi da pillow'n ta, ahanzarce tanufi ƙofar falon nata, dai-dai lokacin Ahmad yafito daga ɓangarensu dan zuwa masallaci, idanunsa ne suka gane masa Zaleeha, fuskarsa ɗauke da ɗan mamaki yabita da kallo, ganin fitowarta daga cikin garden gashi hannunta riƙe da bargo da kuma pillow alamun nan ta kwana kenan yasanyashi girgiza kansa, cikin ransa yace. "Allah Ya shirya ki, ae dama mai hali baya taɓa fasa halinsa, saidai in ba'a zauna ba kuma dai duk tsaurin wayon amarya to wlh sai ansha manta anci sadaki an suɗe ki dai gama ɓoye-ɓoyenki." Nan yawuce masallaci. Itakuwa Zaleeha sam-sam ma bataga Ahmad ɗin ba, kaitsaye ɗakinta ta wuce, cikin hanzari tasoma rage kayan jikinta, ruwan ɗumi ta haɗa inda tayi wanka, tana fitowa daga wankan ta zura wata farar jallabiya mai kyau,  hijab tasanya tare da ta da sallah, koda ta idar da sallan bata tashi akan sallayan ba saida tayi azkar, nan ta ɗauko ɗan ƙaramin Qur'aninta tasoma karatu,  ba'ita ta rufe Qur'anin ba saida taga gari yaɗan somayin haske, wasu bedroom slippers masu kyau ta zura aƙafafunta, inda tasake feshe jikinta da turare me daɗin ƙamshi. Koda tafito daga ɓangaren nasu kai tsaye part ɗin Ummi ta  nufa, bakinta ɗauke da sallama haka ta kutsa cikin falon, wanda ke cike da jama'a, Raihana ne da Saminu waƴanda zasu koma Kaduna asafiyar ta yau, saikuma Goggo Dada da Aunty Meena wanda zasu koma Dukku, Aunty Rahama ma yau zata koma, don tunjiya Dr.Adnan keyi mata waya, kan cewar yayi kewarta gashi weekend  yana gida shiyasa yace zaizo da safen ya ɗauketa. Cikin yin ƙasa da kai haɗi da nuna tsantsar ladabi taƙaraso cikin falon,  har ƙasa ta durƙusa inda ta gaishe da Ummi, cikin fara'a haɗi da sakin fuska Ummi ta amsa mata gaisuwan nata, tare da miƙo mata hannu ta kamo nata, cikin kulawa Ummi tace. "Taso kizonan kusa da Umminki yarinyar kirki, kema ai ɗiyatace, tunda kika shigo cikin mu kuwa kinzama jininmu." Tasowa tayi daga inda take tare da ƙarasowa kusa da Ummi, Ummi ne tajawota inda ta zaunar da ita agefenta, sadda kai ƙasa Zaleeha tayi tana murmushi, hakanan itakam Allah ya samata son matan aranta, sosai take ganin ƙima da kuma darajan Ummi'n,  su Raihana ne suka gaishe da Zaleehan, amatsayinsu na ƙannen Saifuddeen,  haka ta amsa musu fuska asake, ɗan zamowa ƙasa tayi inda tagaishe da Goggo Dada dakuma Aunty Meena, sai kuma babbar yaya wato Adda Rahama, da kuma Saminu wanda ke zaune gefen Saifuddeen, da fara'a akan fuskarsu duka suka amsa gaisuwar nata,  komawa gefen Ummi tayi ta zauna a ƙasan carpet dan tana matuƙar ji da ganin darajar Ummi, shiru tayi yayinda ko kallon inda Saifuddeen yake batayi ba, shikuwa har acikin ransa mamakin irin tsantsar ladabinta ga ƴan uwansa yake, tanason kowa acikin ahalinsa tana mutuntasu da girmamasu, amma wato shine marainin wayonta sam bata ganinsa da gashin ido, murmushi yayi wanda  shi kaɗaine yasan ma'anonin murmushin ransa yace.   tabbas kuwa zanyi maganinta ne, very soon zankashe bakin tsiwan, badai ni ta raina ba?." hmmm yasha alwashin duk randa ya kamata kuwa zataji ajikinta. Saminu ne yace da Raihana su hanzarta sutafi, bayason tafiyar da bata safiya ba, saboda alokacinne yakejin karsashi ajikinsa, nan kowa yatashi don yi musu rakiya zuwa compound ɗin gidan, ciki kuwa harda Zaleeha wanda ta kamo hannun Daddy yaron Bappa Ali wato Junior mai sunan Abbandu Saifuddeen kenan,  kasancewar yaron kyakkyawane yasanya sosai yashiga ranta, gashi nan da wayonsa irin yaran nanne masu shiga zuciya, haka suka fito compound ɗin gidan inda yaketa zuba mata surutu, itakuwa murmushi kawai take tayi masa, har bakin mota suka rako su Raihanan, nan sukayi sallama da juna, cikin yanayi na tsokana Raihana ta dubeta, tare da cewa. "Kikulamin da Hammana da kyau da kyau, dan ko ƙuda bama son ya taɓa manashi." Dariya sukayi gaba ɗayansu, itakuwa Zaleeha ɗan guntun murmushi tayi, yayinda taji wani malolon abu ya tokare maƙoshinta, cikin zuciyarta tace. "Lallai kuwa zai mutu, indai nice zan kula dashi!. Yo ni me haɗina dashi kunamai ma su sauƙa ajikinsa mana ba ƙuda ba ni me yadameni." Motar su Raihana baigama fita daga gidan ba saiga Dr.Adnan nan shima yazo ɗaukar matarsa, nanfa suka gaisa, inda Zaleeha tagaishesa cikin mutuntawa,  Farouq da Adam kuwa sai tsalle suke dan sunga babansu, duk girmansu baigani ba haka yasasu ajikinsa,  babu yanda basuyi ba akan cewa Daddy yazo su tafi ba amma yaƙi,  waishi ala dole yasamu sabuwar Aunty yace shi Dukkunma bazai komaba, kusan saida yabawa kowa dariya haka suka tafi anata raha. Daddy kuwa da ƙyar  suka iyayi masa wayo yabi iyayen nasa da karatunshi,  Ahmad ne yazo da motarsa wanda dama shine zai mayar dasu Goggo Dada gida, lokaci ɗaya fa gaba ɗaya jama'an baƙin biki  suka watse gida yayi shiru. Ummi Raliya da kuma Zaleehan kawai aka bari, dama Saifuddeen yana part ɗin Ummi, kasancewar shi baifito rakiyan ba, shikuwa Hayatudden sarkin bacci, yanacan tun dawowansa daga sallan asuba daya koma bacci shine haryanzun baitashi ba. Direct Zaleeha part ɗinta ta koma, inda su Ummi da Raliya suka koma wajen Saifuddeen. Tana shiga cikin ɗakin nata ta cire hijabin dake jikinta, kan gado ta faɗa tare da ɗan lumshe idanunta, sosai takejin wani sabon bacci naƙoƙarin ɗaukarta. Can ɓangaren Ummi kuwa, Saifuddeen naganin dawowansu, ya sakawa Ummin nasa shagwaɓa, sanin halinsa na sakalci kaman wani ƙaramin yaro yasanya Ummi da kanta tashiga kitchine inda ta haɗa masa coffee, sosai yaji daɗin haɗin coffee ɗin da Ummin tayi masa, ɗaukan mug ɗin yayi tare da bar musu falon, kai tsaye yanufi sashinsu. Saifuddeen nafita, Ummi tayi murmushi cikin jin daɗi tace. "Allah kenan maiyin yadda yaso a lokacin da yaso, kafun auren nan kowa yasan cewa yarinyar nan bason auren nan take ba, amma yanzu cikin ƙuduran Allah gashi suna zaune lafiya, kinga ta saki ranta." Murmushin gefen baki Raliya tayi tare daɗan muskutowa, cikin jimamin abun dake damun zuciyarta tun daren jiya tace. "Hmmmm hakane kam Ummi, amma nikuwa jiya naga abun daya ɗauremin kai ya bani mmki, dan nima da fari da naga ta saki ranta naji daɗi." Dubanta Ummi tayi tare da cewa. "Mene kuma yafaru?." Gyara zama Raliya tayi tare da cewa. "Ummi kinsan kuwa cewa jiya awaje cikin garden ta kwana? wallahi Ummi abun yabani mamaki sosai, inata tunanin dalilin da zaisa ta kwana cikin garden, idan har zatana gudunsa haka, meyasa ta amince da aurensa?." Cikin matsananci mamakin jin maganan da Raliyan ta faɗa Ummi ta sauƙe wani irin ajiyar zuciya, jiki amace tace. "Raliya kin tabbatar da abun da kike faɗa kuwa?." Kai Raliya tajinjina tare da cewa. "Wallahi Ummi da idanuna naganta jiya a garden ta kwana, kuma koda natashi sallan asuba dana leƙa naganta, alokacin tana ƙoƙarin barin wajen, kuma tabbas nasan babu makawa itace dan Abban Farida ma ya ganta dayazo tafiya masallaci." Ɗan jim Ummi tayi tare dajinjina kanta, take taji zuciyarta tayi mata wani irin ba daɗi, hankali ya tashi fargaba ya cika mata zuciya wato har ƙiyayyar ta kai haka, jiki a mace tace. "To Allah dai ya kyauta." Amin Amin Raliya ta amsa jiki a mace. Haka dai zaman yaci gaba da gudana har tsawon kwanaki, Kullum  in gari ya waye Zaleeha na idar da salla zataje ta gaida Ummi a mutunce, lokuta da dam takan samu Saifuddeen a wurin Ummi, amman tsakaninta dashi sai harara da murguɗa baki, tana son kowa na gidan yayinda suma duk suke matuƙar sonta musamman Raliya da takanje har ɗakin Zaleeha su ɗanyi hira, dan itacema ta tayata shirya tarin akwatunan kayan aurenta da kimtsa mata duk abinda zata buƙata a durowa, sauran akwatunan suka kaisu ɗaya ɗakin, Hayatuddeen kuwa dama akwai sabo a tsakaninta haushinta da yaji kan cewa da tayi bata son Hammanshi yanzu babushi tunda yanaga har ta yarda da auren ta zauna lafiya dashi. tana matuƙar girmama Ummi wanda hakan yasama mata soyayya a idanunsu, tana mutunta Ahmad a cewanta mai sunan yayanta ne dan Yaya ma take kiranshi tun tana gaidashi yana amsawa a yatsine har dai ya fara ɗan sasaautawa. Har yau kuma a woje take kwana cikin gardin, wannan abun shine yasa Ahmad yake matuƙar jin baƙin cikinta, shi kuwa Saifuddeen  da fari baisan bata kwana a ɗakintaba dan baya shiga kuma da safe yana ganinta a wurin Umminshi, To tun shekaran jiya daya dare ya ankara da bata ɗakin, ya dudduba ko ina na cikin part ɗin nata babu ita ba dalilinta, falonshi ya koma wayarshi ya ɗauka tare da yin mgnar zuciya, "To ina take zuwa ta kwana yau kwana biyu kenan bata kwana a nan." Kanshi ya ɗan jingina da jikin kujerarsa tare daci gaba da mgnar zuci. "To waya sanima ko ta daɗe da barin kwana a nan." sai kuma yayi ajiyan zuciya tare da cewa. "ko dai part ɗin Ummi take kwana? kai Anya kuwa Ummi zata barta ta kwana a side ɗinta, to ko dai part ɗin Raliya take kwana." Text ya rubutawa Ahmad, "Kayi bacci ne?." Ahmad da ke zaune a falo shida Raliyya suna mgnar Zaleeha dan hango wucewarta da sukayi, murya a sanyaye Raliya tace. "To wai ko dai Hamma Saifuddeen bai san bata kwana a ɗakinba?." Ajiyan zuciya Ahmad ya sauƙe tare da cewa, "Ina zaton bai saniba, kinfa san shi da miskilanci, in kuwa yasan bata kwana a cikin to yasan inda take kwanan shiyasa bai kulataba ai jiki magayi." da sauri ya ɗago wayarshi ganin saƙon Saifuddeen ne ya sashi cewa. "To ina ga dai bai san bata kwana cikiba sai yanzu dan ga text ɗinshi wai nayi bacci ne." ido Raliya ta zuba fuskar wayarshi tana ganin amsar da yake rubuta mishi. "A a banyi bacci ba, lfy dai ko?." jim kaɗan sai ga wani saƙon. "To lafiya dai zance,amman Zaleeha na wurinku ne?." murmushi Ahmad yayi tare da cewa Raliya, "Hmmm zanyi mgnin yarinyar nan." sai kuma ya rubuta mishi amsa. "A a Zaleeha kuwa, bata nan." a take sai ga wani saƙon. "Kasa Raliya ta dudduba nan wurinku, taje Side ɗin Ummi ma ta duba ko tana can." yana gama karan tawa yace. "Lafiya dai kam ko?." tsaki Saifuddeen ya ɗan ja kana ya rubuta mishi, "Nima ban saniba lafiya ko ba lfy ba, ina dai zargin yarinyar bata kwana a gidan nan, dan tun shekaran jiya na lura babu motsinta, sannan yanzu na dudduba ko ina bata ciki side ɗin." cikin nuna fargaba Ahmad yace. "Innalillahi, to ina take zuwa ta kwana, gani nan fitowa." sai ya kuma miƙe ya kalli Raliya tare da cewa, "Maza kije side ɗin Ummi ki gaya mata, ana neman Zaleeha ki kuma ce karta nuna tasan inda take kwana zanyi mgninta." to tace tare da juyawa ta nufi side ɗin Ummi, kana shi kuma Ahmad ya nufi ƙofar falon Zaleehan nan yayi kicibis da Saifuddeen daya fito, "To wai ina ta shigane, mufa mun dudduba wurinmu babu ita." kai ya jujjuya mishi alamun shimafa ya dudduba wurinsu babu ita. dai-dai lokacin kuma Ummi da Raliya suka iso, nan fa suka haɗu suka nuna basu san inda takeba. ita kuwa Zaleeha tun fitowan su Ahmad ta buɗe ido, jin ita ake nema yasa ta zame a hankali ta konta a ƙasan kujerar fulawi ke zagaye da ita. Ahmad kuwa yana hangota hakan ya sashi cewa. "Hmmmm zaki gane kurenki." wayarshi ya zaro lallatsata yayi ya nemo number Ya Aminu, ya kirashi kana ya kara wayar a kunnenshi. Can cikin bacci Ya Ameenu yaji wayarshi nata suwa, a hankali ya ɗan zare Maryam daga jikinshi, hannu yasa ya ɗauki wayar time ya duba ƙarfe ɗaya na dare. "Ahmad kuma a daren nan lfy kuwa?." sosai yaji fargaba ,kar dai Zaleeha nacan na tarfa musu rashin ɗa'a, jiki na rawa ya amsa kiran cikin sauri yace. "Salamu alaikum ,Ahmad lfy kuwa?." cikin nuna tashin hankali yace. "Ya Ameenu Zaleeha ce bamu ganiba mun nemata ko ina a gidan babu ita ba dalilinta, kuma Saifuddeen yace tun shekaran jiya bata kwana a side ɗinsu, to sai yayi tunanin wai ko side ɗinmu take shigowa ta ɓuya ko na Ummi, to shine yanzu ya sanarmana zatonsho tana wurinmu,mun duba kab gidan bata, nan shine nace bari in kiraka ko ta dawo gidane?." cikin kaɗuwa Ya Ameenu ya miƙe tare da cewa. "Zaleehan to ina take zuwa?." a taƙaice Ahmad yace. "To ko tana gida ne?." rai a ɓace Ameenu yace. "Kai anya kuwa sam bata gida, to ina take zuwa ta kwana, yi haƙuri bari in kira Baba malam." to Ahmad yace kana ya katse kiran sannan ya gaya.musu yadda sukayi da Yayanta Ameenu, kana yace su shiga ciki kafin Ameenun ya kirashi. Shi kuwa Ya Ameenu wani irin tashin hankali ne da ɓacin raine mai tsanani ya rufeshi to ina Zaleeha take zuwa ta kwana ina take tafiya ta bar ɗakin mijinta me haka yake nufi? kiran Baba Malam yayi bawan Allah yana zaune bisa sallaya yana karatun qur'an kiran Ameenu ya shigo wayarshi, har wayar ta katse bai ɗaukaba duk da yaga Aminune so yake yaje ƙarshen surar Arrahaman da yake karantawa, yayinda wani fargaba ya rufeshi lfy kuwa kira da tsakiyar daren nan. Yana zuwa ƙarshen surar kira na uku na shiga wayar, da hamzari ya amsa kiran, "Barka da dare Baba Malam kayi haƙuri na tada kai daga bacci." Ameenu ya faɗa a ladabce, murya a ɗan harɗe Baba Malam yace. "Ameenu lfy kuwa meke faruwa?." cikin sanyi Ya Ameenu yayi mishi bayanin da Ahmaɗ yayi mishi, ya ƙara da cewa. "Ko dai ta taho gida ne?." lumshe ido Baba Malam yayi yana jin wani irin suya da zuciyarshi keyi me Zaleeha ke nufi zubda mishi mutunci da kima  a idanun mutane ko? a hankali ya cewa Ameenu. "Ameenu bana zaton tana cikin gidana ,bazata zo nanba, amman dai bari in bincika." to Aminun yace kana y katse kiran. shi kuwa Baba Malam fitowa yayi da kanshi yayi tabin luggu da saƙo na gidan ya duba ko ina kab babu ita, koda ya titse Mama da tambayar ina Zaleeha ke zuwa ta kwana, rantse-rantse tayi ta mishi akan ita bata san ina Zaleeha ke zuwa ta kwanaba. a daren Ameenu ya kira goggonsu Maryama da duk inda suke zaton zataje ko ina sai ace musu bata zoba. Wannan abu yayi matuƙar tada hankalin Baba Malam ya Ameenu kuwa ji yake in yaga Zaleeha zai kusan karta, dole ya kira Ahmad yace, wlh bata wurinsu amman tunda da safe tana dawowa zai zo ya sameta, har ɗakinta. Da  wannan kowa ya koma ɗakinshi, Ahmad kuwa ranshi ƙal yasan Zaleeha zata gane kurenta. Washe gari kamar yadda ta saba, suna tafiya masallaci ta koma ɗakinta wonka tayi da ruwan ɗumi wai ko tsamin cizon sauro da  jikinta keyi zai ragu, wanka da al'wala tayi, kana ta fito tazo tayi salla koda ta idar  azkar tayi sanan ta miƙe ta kimtsa jikinta cikin wata doguwar rigar mai ɗan karen.kyau wanda duk na kayan aurene, da mayafinshi ta yane kanta ,kana ta nufi sashin Ummi. a falo ta samesu, dukansu, cikin nitsuwa ta isa gaban Ummi dake mata murmushi tare da cewa. "Gari ya waye ko ɗiyata?." murmushi tayi tare da rusunawa gaban Ummi cikin ladabi da sanyin lafazi tace. "Ummi Ina kwana?." cikin kula Ummi tace. "Lafiya lau ya  baƙunta?." kai a sunkuye tace, "Alhamdulillahi." "Masha Allah." cewar Ummi kenan Hayatuddeen ne ya gaidata ta amsa fuska a sake, kana ta kalli, Ahmad dake zaune kusa da Saifuddeen bisa alamu lissafi sukeyi, cikin sanyin sauti tace. "Yaya ina kwana?." a taƙaice yace. "Lafiya lau." daga nan kuma sai ta miƙe tare da cewa Ummi . "Raliya na kitchen  ko?." cikin jin daɗi Ummi tace. "A a tana sashinta yau wai kanta ke ciwo." a hankali tace, "Ayyah ban saniba Allah ya bata lfy." Amin Amin Ummi tace, Kana sai ta ɗan rusuno tare da cewa, "To Ummi bari in shiga kitchen, me zan  haɗa  mana breakfast?." sosai Ummi take jin daɗin yadda take sakewa da Raliya su shiga kitchen tare, gashi yanzu har tana shiga ita ɗaya ma tayi musu girki. cikin kula Ummi tace. "Bari inzo mushiga tare to." da sauri tace . "A a Ummi ki bari zan iya ki huta." sai kuma ta kalli Hayatuddeen daketa murmushi tace, "Zo muje kitchen ka tayani hira." da sauri ya miƙe yabi bayanta, yana cewa. "Yauwa muje ki min dege-dege." da ido Ummi ta bisu har suka shiga kitchen ɗin. koda suka ƙarasa cikin kitchine ɗin, hayewa kan wata kujera Hayatuddeen yayi ya zauna, wayarsa ya fiddo daga aljihunsa tare da soma latsawa, ita kuwa Zaleeha, direct wajen fridge ta nufa, buɗe cikin firjin dake shaƙe da kayayyakin abinci tayi, nan ta zaɓo manya manyan kaji guda biyu,  sake wankesu tayi sannan ta ɗaura akan wuta tare dasa kayayyakin ƙamshi dana danɗano. nan ta ɗibo irish patatoe tasoma ƙoƙarin ferewa,  Hayatuddeen ne ya taso tare da soma taya ta,  haka suka cigaba da firan, yana ta zuba mata surutu,    mayafin dake jikinta ta ajiye, tare da soma yin aikinta cikin nutsuwa, yayinda Hayatuddeen gaba ɗaya ya sakota gaba da surutunsa,  cikin abun da bai wuce awa ɗaya da rabi ba, ta kammala haɗa barbecued chicken da kuma patotoe balls,  sai kuma bread Pizza, wanda gaba ɗaya ƙamshinsa ya cika kitchine ɗin, Hayatuddeen dake zaune agefe sai haɗiye miyau yake, dan har ya tsara irin cin da zaiyiwa bread pizza ɗin, da ƙamshinsa ya cika masa hanci, spearmint tea ta haɗa, sannan ta juyesa acikin flask, nan ta kimtsa gaba ɗaya kayan akan wani babban tray, duban Hayatuddeen tayi tare dayi masa alama akan yazo ya tayata ɗauka, aikuwa shi ya kwashe komai inda ya jere musu break fast ɗin akan dinning table, ita kuwa Zaleeha har yanzu tana kitchine, fruit salad ta haɗa, inda ta zubashi cikin wani babban glass bowl, tunanin haɗa chocolate fudge cake ne yazo mata, nan ta duba taga akwai komai na buƙata, kanta ta jinjina, sannan tashiga ƙoƙarin haɗawa, cikin mintuna ƙalilan kuwa ta kammala, ita kanta saida tayaba da ƙamshin chocolate fudge cake ɗin, Hayatuddeen dake falo kuwa koda ƙamshin yaje masa, saida yakasa haƙuri ya biyota zuwa kitchine ɗin, ganin, fudge cake ɗin yasan yashi cewa. "Wow fantastic, Aunty Zalee dama wai kin iga girki har haka ne?, na ɗauka a faɗa da masifa chart da zuwa wurin aiki kawai kika iya." Hannu tasa takai masa bugu, da sauri ya kauce yanayi mata dariya, hararan wasa ta watsa mai, tare da cewa. "Kaɗauka yanda kuke sakarkaru kaida Zakariyya haka kowa ma yake ne baku da aikin sai yawo a gari dama tsokana da ci." Taƙare maganar tana me miƙo masa, wani haɗaɗɗen tray wanda ciki tashirya chocolate fudge cake ɗin, amsa yayi yana wani malau malau da baki, tare da cewa. "Hmmm ai yanzune ma zakuga tashen jami'a zakusha mmki bari dai in gama sabawa da jami'ar kin san banfi sati ɗaya da fara zuwa ba." Dariya ta ɗanyi tare da cewa. "Yo ai da an ganka ansan kanka na fizga da igiyar iskar sabin shiga jami'a ka dai yi a hankali yaro dan ita jami'a gidan ban kashine." Murmushi ya ɗanyi tare da cewa. "Gobe zan kawo miki sabon abo kina Khamis ku gaisa. kiga irin salon takun mu, yaseen ki kuma cewa mijinki ya saya min mota. Dan ni ba yaro bane da za'a rinƙa kaini ana ɗaukoni kamar wani ɗan primary ko kayan wonki da za'a rinƙa kaini ana ɗaukoni". Ya ƙarishe mgnar yana wuce zuwa dinning, food flask ɗin dake gefenta wanda ciki ta shiryawa Raliya abinci ta ɗauka. Koda ta fito falo, nan ta iske Ummi, da kuma Saifuddeen, da Ahmad, Hayatuddeen kuwa tuni ya baje kan dinning, inda ya turo baki gaba, wai don saboda yace suzo suci, sunce yajira Zaleehan tagama sai suci tare, sam shi gaba ɗaya yaƙosa yaji yana tauna abincin, musamman ma da ƙamshin abincin ya cika masa hanci. Zaleeha na fitowa daga kitchine ɗin ta dubi Hayatuddeen, fuskarta ɗauke da murmushi tace. "Autan Ummi sarkin ci!." Baki Hayatuddeen yaƙara turowa gaba, ashagwaɓe yace. "Eh naji, amma please kice musu suzo muci, I swear am feeling hungry fa!." yafaɗi maganar yana me shafa cikinsa, wanda hadda ganin abincin ma yaƙara masa jin yunwa. Murmushin daya bayyana zallan cute face ɗinta tayi, tare da girgiza kanta. Ummi ne tayi murmushi tare da duban Zaleehan, cikin so da ƙaunar yarinyar tace. "Sannu da aiki, Allah yasaka miki da al'khairi, ya kuma baki ƴaƴa masu al'barka, wanda zasuyi miki fiye da haka." Saɗa kai kasa Zaleeha tayi tare da ɗan sakin guntun murmushi a kunyace murya a sanyayaye tace, "Amin Ummi." Saifuddeen kuwa a fakaice ya ƙura mata idanu, yana kallon duk wani motsinta sosai yake mamakinta, har yau har yanzu ya rasa ita wace irin mutum ce mai fuska biyu da jujjuyawa tamkar hawainiya, ji yanda take ta murmushi tare da sakewa dasu, tanayin komai kamar wata wanda keson zama dasu da gaske. Shi mamakinta ma yake, tawani irin sakewa sai kace ba itace, su keta gantalin nema ba jiya. Kawar da kansa yayi daga kallonta, tare da maida hankalinsa, ga laptop ɗinsa, wanda a zahiri laptop yake kallo a baɗiri kuwa fuskata yake kallo ta cikin madubin system ɗin, rumtse ida nunshi yayi a hankali tare da sauƙe nannauyan ajiyan zuciya, "To ina take zuwa ta kwana dasu waye take kwana, me take aikatawa a inda take kwanan?." haka yaji waɗannan tambayoyin sun cika mishi zuciyarshi dake cike da azabebben kishi, gaba ɗaya ya rasa wani irin kishi Allah ya ɗora mishi a kanta ji yake tamkar zai faɗi ya mutu dan baƙin ciki. Ahmad kuwa dubanta yayi tare da sakin murmushi, cikin ransa yayi ƙwafa, ahankali yace. "Zaki sanine yarinya." Duban Ummi Zaleeha tayi tare da ɗan rusunawa, cikin nutsuwa tace. "Ummi bari na kaiwa Raliya abincinta, tunda batajin daɗi nasan ba lallaine tasamu fitowa ba." Sosai Ummi taji daɗin kulawan da Zaleehan ta nuna ga Raliya'n, amma sai tace. "A'a Zaleeha da kanki, bazaki bari Hayatuddeen yakai mata ba." Murmushi Zaleeha tayi tare da cewa. "Bakomai Ummi, kinga Hayatudeen ɗin yace bazai iya komaiba sai yaci abinci,inaga bazai iya matsawa akan dinning ɗinnan batare daya lodawa cikinsa abinci ba, kin sanshi acicine kazar birni!." Zaleehan tafaɗa tana kallon Hayatuddeen, ba iya Ummi ba harta Ahmad saida yaɗanyi murmushi sabida sunan data kira Hayatuddeen Acici kazar birni, Ummi ce tace, idan takaiwa Raliyan abincin ta dawo suci abincin, nan tace zasuci da Raliyan acan. Koda ta ƙarasa ɓangaren Raliyan, akwance ta isketa, nan ta shiga ɗan kimtsa mata ɗakin, daga nan kuma ta zuba musu abincin inda suke ta hira ita da Raliya'n sosai Raliyan ta sake da ita har taji ciwon kan nata ya saketa. A falon Ummi kuwa, tuni Ummi tayi serving ɗin kowa, nan fa Hayatuddeen yasoma kai loma, yana me jijjiga kansa. Saifuddeen kuwa ahankali yake tsakuran abincin yana kaiwa bakinsa, idanunsa kawai yake lumshewa sabida ƙuna da zuciyarshi keyi na kishi, tabbas ya yaba da iya girkinta domin sosai abincin yayi masa daɗi, sam koda wasa bai taɓa tunanin cewa Zaleeha ta iya girki har haka ba. Ummi ma sosai ta yaba da abincin, Hayatuddeen kuwa cikin santi ya ɗago kai inda ya dubi Ahmad, cikin halinsa na tsokana yace. "Wallahi Aunty Zalee ta iya abinci, mai daɗi kaman kunnena zai fita, hmmmm ai daga yau ita zatana mana girki, don sosai tafi su wance iyawa." Dariya ne ya ƙwacewa Ummi, dan tasan tabbas Hayatuddeen dan tsokana yayi maganan da Raliya yake. Harara Ahmad ya watsa masa tare da taɓe baki, cikin nuna cewa shima matarsa gwanace yace. "Oho dai, da makaho ya rasa ido sai yace da wari, wannan har wani abinci ne, an haɗamu da tarkace saikace wasu yaran larabawa, jifa wani cake na chocolate, ko ance mu yaran larabawa ne, ai dai Raliya tafita iya girki ko Ummi." Ahmad ya faɗa yana me duban Ummi. Murmushi Ummi tayi tare da gimtse dariyarta, ita dai bata da tacewa, to ma mezatace komai tace yanzu zasuce tayi sonkai. Hayatuddeen kuwa dariya yadinga yi, don yasan maganan Ahmad ɗin, a iya laɓɓan baki kawai take, ba taje zuci ba, ya faɗane kawai don ya kare matarsa, amma yasan cewa koma waye yaci girkin dole ya yaba, musamman ma spearmint tea ɗin dake ta ƙamshin kayan haɗi, uwa uba kanasha kanajin wani irin ɗan ɗanon zuma aciki. Ahaka suka kammala cin abincin, inda Ummi tasa Hayatuddeen ya kwashe kwanukan yakai kitchine. Acan gidan Baba Malam kuwa, tuni Baba Malam ya ƙira Habu, inda yace yaje gidan Zaleeha ya taho masa ita. Babu ɓata lokaci kuwa, Ya Habu yashiga cikin motarsa, kai tsaye ya nufi gidan su Saifuddeen. Aƙofar gidan yayi parking motarsa, inda yayi knocking gate ɗin gidan, maigadi ne ya leƙo tare da buɗe masa, duban maigadin Ya Habu yayi tare da basa hannu suka gaisa, dai-dai lokacin kuma Ahmad yafito daga part ɗin Ummi zaiyi nasu sashin, ganin Ya Habu yasanyashi ƙarasowa wajen daɗan sauri, nan yabawa Ya Habu hannu sukayi musabaha koda Habun ya gaya mishi saƙon Baba Malam, Ahmad ɗinne yayi masa jagora har zuwa part ɗin Ummi, amutunce suka gaisa da Ummi, bayan sun gama gaisawanne yayi musu bayanin cewa Baba Malam ne yaturosa akan cewa ya tafi da Zaleeha, aikuwa sosai zuciyar Ahmad tayi fess, Ummi ne tace da Hayatuddeen yaje yaƙirawo Zaleehan, don kuwa har yanzu tana nan a part ɗin Raliya. Koda Hayatuddeen yaje part ɗin Raliya, nan ya iskesu sunata hira, shaida mata ƙiranta da akeyi yayi, "Aunty Zaleeha Ya Habu yazo yana falon Ummi yace kije." Cikin tsoro da fargaba tace. "Ya Habu kuma! Shi da waye?." murmushi Hayatuddeen yayi tare da cewa. "Ya Habu fa nace ba dodoba, shi kaɗai mana yazo, kinga yace kiyi sauri gida zakuje tare." Ƙulullluuuu cikin Zaleeha ya bada sautin murɗa a take cikinta ya ɗuri ruwa, nan ta cika da fargaba haɗi tsoro, cikin tankwashe wuya ta kalli Hayatuddeen tare da cewa. "Pleees je kace baka ganni ba." Sosai suka cika da mamaki, Kai Raliya ta sunkuyar dan kar dariyan da ke sun kubce mata ya baiyana a fuskarta, cikin mmki tace. "Ya kuma zaije yace bakyanan bayan kuma gaki?." kwaɓe fuska tayi tare da cewa. "Eh yaje yace ina bacci to." sosai tsoronta ya baiyana a fuskarta ganin hakan yasa yakoma falon Ummi yafaɗi cewa. "Bai ganta ba." Hararan da Ahmad ya watsa masa ne, yasan yashi faɗin gaskiya inda yace. "Tace nace banganta ba, ko kuma ince tayi bacci." Nanfa Ya Habu yacika da mamaki, take kuma yaji ransa ya ɓaci, ta tabbata mara gaskiya kenan, sake tura Hayatuddeen ɗin yayi akan tazo, nan ma Hayatuddeen yaƙara dawowa, yace tace wai batanan, haka akayi juyin duniya akan Zaleeha tazo, amma ina sam taƙi zuwa, daga ƙarshema ɗakin Raliya ta gudu ta ɓuya. Rai aɓace Ya Habu yafito yabar gidan. Yana zuwa gida ya iske Ya Ameenu da Baba Malam azaune, cikin ƙunan zuciya ya kwashe duk abun da ya faru ya faɗawa Baba Malam, sosai Ya Aminu ya hatsalo gaba ɗaya jikinshi rawa ya ɗauki saboda matsanancin ɓacin rai da zafin zuciya irin nasu na sojoji da kuma fulani ji yake muddin gata gashi zai kakkarya mata ƙafafuwa yaga gobe da wanne sawun zataje yawon. Me Zaleeha takeson maidasu ne?, me take nufi dasu? Wai ko dai gani take tafi ƙarfinsu ne? miƙewa yayi tare da cewa. "Bari inje in taho da ita!." Kai Baba Malam ya gyaɗa mishi dan fitinar Zaleeha tana tafasa mishi zuciya tana gab da ƙureshi. Ahmad na zaune afalo suna mamakin halin na Zaleeha, saiga ƙiran wayar Ya Aminu yashigo wayarsa, ɗauka yayi ko gaisawa Ya Ameenu bai bari sunyi ba, yace da Ahmad ɗin yana ƙofar gida, cikin jin daɗi Ahmad ɗin yasanar dasu Ummi da Saifuddeen. Sannan yafita ya shigo da Ya Ameenu'n, gaisawa sukayi sannan Ahmad ɗin ya dubi Saifuddeen, cikin nutsuwa yayi wa Saifuddeen ɗin alama kan cewar yayi haƙuri, zasu tafi da Zaleehan, Baba Malam ne ke nemanta, cikin body language Saifuddeen yace. "Bakomai" dan shi kanshi yana cike da son sanin ina take zuwa ta kwana. Shikuwa Ya Ameenu kai tsaye cewa kawai yayi anuna masa ɗakin da Zaleehan take, a bashi izinin shiga zata fito, nan Ahmad mugu yace. "Ba komai ya Ameena ai kai ba baƙo bane, tana ɗakin Raliya muje in nuna maka ɗakin". cikin zafin jini Ya Ameenu yabi bayan Ahmad da yake ta dariyar zuci so yake adaka mishi hegiyar yarinyar nan mai ladabin kura Zaleeha na rakuɓe ajikin bango suna magana da Raliya sai gani tayi an turo ƙofar ɗakin, koda takai dubanta ga ƙofar kuwa saida numfashinta yakusan ɗaukewa ganin Ya Ameenu a bayan Ahmad sam bata tsammaci ganinsa ba, aruɗe tasoma ƙoƙarin guduwa, taku ɗaya yayi ya cafkota tare da wanka mata wani irin gigitaccen mari, wanda yasanya tasaki wata irin razanannen ƙara, take tasoma ƙoƙarin shiɗewa, aharzuƙe Ya Ameenu yace. "Wato har kinyi girman da Baba Malam zai aiko ƙiranki kiƙi zuwa ko?, wuce muje kona kakkaryaki anan wajen, mahaukaciya kawai muje yau sai kin gaya mana gidan ubanwa kike zuwa ki kwana?!!." Cikin ɗimaucewa Zaleeha ta wuce gaba, tare da fara tsalle tana yarfa hannu cikin kukan gano yau sai dai buzunta dan ta lura zargin yawo Ya Aminu da sauran ƴan uwanta suke mata. jin ya sake yarfa mata wasu tagwayen marukane tare da ce mata. "Gidan ubanwa kike zuwa ki kwana? Wato mu zaki maida sakarkaruko? Wato yawon lalata kikeson ki koyaka?." wani irin tsalle ta rinƙayi tana yarfa hannu cikin tsananin kuka da tsoro tace. "Wallahi Ya Ameenu ba yawon lalata nakeyiba, a cikin gidannan nake kwana cikin garden nake kwana wlh bana fita ko ƙofar gidan." Ummi kam dake falonta jin kukan Zaleeha ne yasata saurin juyowa ta kalli Saifuddeen dake kallonta tace. "Kai Saifuddeen dukanta fa sukeyi ,kada ka bari su tafi da ita zasu illatata,wannan sojanefa ya saba dukan garadai kar ya illatamin yarinya mai biyayya." kai ya jujjuya mata tare da haɗe hannunshi wuri ɗaya ya mata alamun dan Allah kada ta fita ta barsu su tafi da ita. Shikuwa Ya Ameenu a zafafe yace. "Maza mu tafi gida ba ni zakiyiwa bayani ba." da sauri-sauri gudu-gudu tayi hanyar fita, kana shi kuma biyo ta. Suna ƙarasawa wajen motarsa ya buɗe tare da hankaɗata ciki, ransa amatuƙar ɓace ya ja motar sukabar ƙofar gidan. Gudu yake sosai hakan yasa cikin mintuna kaɗan suka iso G.R.A yana gama dai-dai-ta fakin ɗin motar, ya fito tare da zare belt ɗin wandonsa, ƙofar da take ya buɗe tare da figota waje, nan yashiga zuba mata belt ɗin ajikinta, kuka da ihu mai firgitarwa Zaleeha keyi tare da gudu ta nufi cikin gidan, kai tsaye ɓangaren Baban nata ta nufa. Tana shiga tafaɗa bayan Mamy dake tsaye acikin falon, gefe kuma Baba Malam ne zaune, sai kuma Ya Ahmad da kuma Mama wanda tacika tayi fam, ƙiris take jira ta fashe ta tarwatsa musu buhun bala'i. A harzuƙe Ameenu yashigo cikin falon, ganin haka yasa Zaleeha yin tsalle ta faɗa jikin Ya Ahmad ɗinta, ƙan ƙamesa tayi ƙam tare da ɓoye fuskarta a ƙirjinsa, kuka take sosai kamar ranta zai fita don sosai ya tsutstsula mata bel ɗin, Ya Ameenu na ƙoƙarin ƙara mata wani dukanne, Ahmad ya girgiza masa kai, alaman yabarta hakanan, da ƙyar Ahmad ya iya lallashinta tayi shiru, nan Baba Malam ya tambayeta ina take zuwa da bata kwana agidan aurenta?. Cikin matsanancin kuka tare da tsoro murya na rawa take cewa. "A garden nake kwana, Baba Malam wallahi ko ƙofar gidan ban taɓa fitowa ba , wallahi Baba Malam babu inda nake zuwa, a cikin gidan nake kwana." Sosai sukasha mamaki, amma sanin halinta da taurin kae irin nata yasa suka yarda cewa zata aikata hakan, a hatsale Habu yace. "To meyasa bazaki kwana cikin ɗakin kiba ko dai ƙarƙashin sirran aka nuna miki akace miki nanne ɗakin kwananki?." kai ta jujjuya cikin tsananin tsoro dan a duniya dai Zaleeha bata son abinda zai taɓa mata lafiyan jikinta murya na rawa tace. "Ni tsoronshi nakeji shiyasa nake fita woje." kai kawai Baba Malam ya jujjuya dan har ga Allah shi ya yarda Zaleeha tsoron takeji dan ya santa matsoraciyace bata son abinda zai taɓa lfyarta, kana kuma duk mace budurwa akwai tsoron namiji a ranta musamman in ance mijintane tofa akwai wannan tsoron da taraddin haɗuwar forko dana biyu wasu harma na uku. Wannan tunanin yasa Baba Malam yayimata faɗa tare da Nasiha, haka tayi kuka harta godewa Allah. Mama kuwa yau saboda tsaban ɓacin ran dake cinta kasa cewa komai tayi, tuni ma tabar musu falon, don idan ta tsaya zata iya dannawa Ameenu daya dakar mata ƴa ashar babu ruwanta da surkuntaka. Nan take Baba Malam yasa Mamy tashirya inda taɗauki Zaleehan ita da Ya Ameenun suka maida ita gidan su Saifuddeen, har gaban Ummi suka kaita, nan sukaiwa Ummi bayanin cewa wai agarden take kwana, nan sukaita bawa Ummi da shi Saifuddeen ɗin haƙuri, suka sa itama ta basu haƙurin nan su Ummi suka nuna cewa bakomai ya wuce, sosai Ummi taji tausayin Zaleehan ya kama zuciyarta, don kallo ɗaya zakayi mata kasan cewa andaketa, don ga jikinta nan duk yayi wani iri, sam Ummi bataji daɗin hakan ba. Nan Su Mamy suka kai Zaleehan har ɓangarenta, sannan suka ƙarayi mata nasiha, daga haka suka barta, inda takwanta tana meda numfashi, sosai takejin wani irin tsanar Saifuddeen ya ƙara ninkuwa acikin zuciyarta, ayanzu tanajin zata iyayi masa komai don baƙanta masa, domin akansa ne aka mata irin wannan azaban. Haka ranan dai ta wuni kuka , da yamma Belkeesu tazo nan tai ta ƙara zugata, hakama Mama ta kirata tai ta zageta wai me take jira da gidan tunda dai ba gidan ubanta bane to tabar musu gidan. Kada kuma ta bari wannan nakasashen ya rabata da budurcinta, harda cewa ta kwana duk inda takeso amman dai ta kare budurcinta. Koda dare yayi kamar kullum nan ta kwana cikin garden ɗin, shiko Saifuddeen yanzu abin natama dariya yake bashi, dan in gari ya waye ta fiti kamar ba itaba, shida kanshi ya yarda tana son ƴan uwanshi da Umminshi. Yau kwana uku da faruwan abun ,wanda yayi dai-dai da cika kwanaki goma da tayi a gidan, da yamma Adda Rahma tazo, duk da Raliya ta sanar mata komai amman sai takega kamar sharri sukewa Zaleeha dan yadda take nuna muso da kulawa. ita kuwa Zaleeha harga Allah har cikin ranta take son kowa na ahlin Saifuddeen ita dai shine bata so. Bayan anyi sallan ishane Ya Ahmad da Aunty Lubna suka zo gidan don sallaman Zaleeha dan gobe zasu koma Abuja, falon Ummi suka fara zuwa suka gaidata, kana Ya Ahmad ya bawa Ummi haƙuri akan ƙuruciyar Zaleeha, cikin jin daɗi da ganin dattakun yaron Ummi tace, "In sha Allah ba komai yarin tace." daga nan Saifuddeen yayi musu jagora zuwa side ɗinsu, sai dai kafinma su iso tuni Zaleeha ta tafi makoncinta, koda suka dudduba ɓata nan, sai Saifuddeen ya sanar musu inda taken, sosai ran ya Ahmad yayi matuƙar ɓaci, Auntƴ Lubna ce taje cikin garden ɗin ta kura ta, amman tasha jinin jikinta ganin yadda Aunty Lubnanma ta haɗe mata fuska, jiki a mace ta shigo, ganin ya Ahmad ɗinta ne yasa tayi saurin ƙarasawo cikin falon gefenshi ta zauna tare da manna kanta bisa damtsen hannunshi kawai sai ta saki kuka, abin mmki saiga Ahmad ya fara rarrashinta. nan yayi ta lallaɓata da yi mata nasiha da alƙawuran abubuwa masu daraja a rayuwarta yace. "Ni dai fatana da roƙona a gareki kawai kiyiwa mahaifinmu biyayya kada ki kunya tashi, ki zauna ɗakin mijinki ni kuwa babu abida bazan miki ba, ammanfa muddin kika saɓawa umarnin Baba Malam Zaleeha ki mance da cewa na sanki kin sanni. ki dena kwana a wojenan cikin ciyawin can, Zaleeha dame na rageki me ban mikiba na kayan ɗaki, ki gaya min in akwai abinda ban miki shiba in miki? ". Cikin share hawayenta tace. "Kamin komai Ya Ahmad ngd ." Kai ya jinjina tare da cewa. "To ki zauna ɗakin mijinki kiyi mishi biyayya ki bashi duk wani haƙƙinshi dake kanki." kai ta gyaɗa mishi a ranta kuma ceqa take. "Kayi haƙuri Ya Ahmad bazan iyaba." da haka dai suka sallameta suka tafi, inda Saifuddeen yayi musu rakiya har bakin motarsu, nan Ya Ahmad ɗin ya ƙara bashi haƙuri. To ranar dai Zaleeha a falonta ma ta kwana dan yanzu tayi shirin fara tarfa mishi rashin mutunci a cewarta sai ya saketa wanima bai saniba, sai dai kafinma ya dawo daga rakiyar su Ya Ahmad ta ɓingire tayi bacci, sabida sanyin ac da ƙamshi da tsabtan falon, koda yazo wuce kanshi ya girgiza tare da taɓe baki kana ya ɗan naga kafaɗunshi alamun babu ruwanshi da ita ya wuce side ɗinshi. Koda gari ya waye sai ta maida shirinta yau. Ƙarfe sha ɗaya da kwata na dare Saifuddeen yayiwa Umminshi saida safe black coffe ɗinsa, wanda Ummi ta haɗa masa ya ɗauka, tare da fita daga ɓangaren Ummin, sam ko kaɗan baiji tausayin Zaleehan nadaga abun da akayi mata ba, don shi sam baima fahimci cewa, an daketa ba. Kaitsaye part ɗinsu ya nufa, koda ya ƙarasa cikin falon nata, direct ɗakinta ya nufa dan yau wuni zumbur bai gantaba, haƙƙinta ne kuma a kanshi yasan halin da take ciki, kuma Umminshi ma ta umarceshi da ya shiga ya duba lfyarta, dan tunda tazo gidan bata taɓa fashin fitowa gaida Ummi safe da yamma amman yau tunda tazo da safe babu wanda ya kuma ganin fitowanta, sai dai Ummi tasa Raliya tazo har ɗakinta ta tambayeta lfya kuwa bata fitoba, to nan tace kanta ke ciwo, kuma hakan baya rasa nasaba da kukanda take yawanta yine a kwanaki ukun nan kuma ga dukan Ya Ameenu. A hankali ya nufi bedroom ɗinta   Ita kuwa Zaleeha zuwa lokacin harta zage zip ɗin rigarta inda take kwance akan gado, sosai takejin jikinta nayi mata wani irin raɗaɗi na musamman akan dukan da tasha yayi tsami a jikinta. Ƙarasowa cikin ɗakin yayi, tare da ɗan tsayawa ahankali yake ƙare mata kallo. Duk da kasancewar idanunta a lumshe suke, amma ba bacci take ba dan hawaye nata kwaranya daga idanun nata, jin motsin mutum acikin ɗakin, da kuma ƙamshin turarensa daya cika mata hanci yasanyata juyowa,  idanunsu ne suka sarƙe acikin najuna, da sauri tatashi daga kwancen da take, tare da ɗanja baya da alamun tsoronshi, takurawa tayi wuri ɗaya tare da sakin kuka, cikin rawan murya tace. "Dan Allah malam meya kawoka ɗakina?,Dan Allah ka fita, Ni tsoronka nakeji." Dubansa tayi duba irin mai cike da tsantsar tashin hankali da wahala cikin takaicinsa tasa tafin hannunta ta sharce hawayenta taso ta zuba mishi fitsara da tijara, sai kuma hakan ya gagareta sabida yayi mata kwarjii da yawa, gashi ya tsareta da manyan kyawawan idanunshi da suke da kwarjin mai tarin yawa madadin tayi masifa sai kawai ta tasashi a gaba taci gaba da kuka murya na rawa tace. "Dan Allah kaji tausayi na, wallahi ina sonshi bazan iya rayuwa da wani namijiba in ba shiba". kanshi ya tankwashe yana kallon yadda laɓɓan bakinta ke motsawa yana mai jin wani irin suya da ƙuna da zuciyarsa keyi, Ita Kumahakan da yayine ya tuno mata ashefa kurmane ma, cikin zubda hawaye tace. "Ayi mutum shi burinsa kawai ya raba masoya, ni bana son ko wani ɗa namiji sai shi, nace maka bazaka samu farin ciki daga gareni ba, saboda kai ƴan uwana suka tsaneni, saboda kai yau an wayi gari Ya Ahmad ma ya nuna zai iya tsanata sabida kai aka ɗaga hannu aka dakeni da sunan dukan dole in zauna da kai, am medani kamar jaka ko ganga abu kaɗan akama jibgata!." A hankali jiki na rawa turo da ƙafafunta ƙasa tare da miƙewa tsaye, hannuwanta tasa tana share hawayenta da wasu ke korar wasu, cikin kuka tace. "Ni dai ka fitamin daga ɗaki!." Taƙare maganar tana meyi masa nuni da ƙofar fita daga cikin ɗakin. Ganin ya kafeta da mayun idanunsa ne yasanyata ƙara jan baya kaɗan tace. "Waikai kam me yasa kake abu kamar mahaukaci ne da ina maka magana kana kallona, meyasa baka babbance so da ƙiyayya? Nace maka inada wanda nakeso". da sauri ya rumtse tafin hannunshi wai a gaban shi take ce mishi tanada wanda takeso tana matsayin matarsa. Ita kuwa cikin muryar kuka tace. "Tunda bazaka fitaba ai sai kayi ta zama kai in mun zauna ɗaki ɗaya ma me zaka iya min?, da idanu kaman na....." Batare da ta tantance ƙarasowarsa gareta ba, saiji tayi ansa mata ƙafa inda aka kwasota tuni tatafi su tafaɗa kan gado, cikin matsanancin ɓacin rai haɗi da rufewar ido, yasanya hannunsa inda ya jawota jikinsa, a harzuƙe yakama duka hannayen ta biyu ya, murɗe mata hannun nata yayi da ƙarfin gaske ya maidasu bayanta, hakan ne yasa tasaki wani irin ƙaran azaba,  sosai ransa ya ɓaci dajin kalamanta na kiranshi misaltashi da aikin mahaukaci, abinda Zaleeha bata saniba mutun ɗaya ya taɓa.mishi wannan furucin Iya Bukku kuma itama ya bata haƙwarenta a hannunta, idanunsa ne suka sanja kala inda sukayi jajur dasu, take jijiyoyin jikinsa suka mimmiƙe, sam idan akwai wani abu daya tsana to baiwuce zagi ba, zai iya tolereting komai amma banda zagar masa nasabarsa, haka kuma zai iya jure kowani zagi, amma koda wasa kada kayi kuskuren ƙiransa da sunan  mahaukaci. Azafafe yasanya hannunsa inda ya kamo ƴan ƙananun laɓɓanta, da yatsunsa biyu yasanya da ƙarfi ya shiga ɗana matasu akan laɓɓan nata da ƙarfi-ƙarfi, cikin matsanancin zafi haɗi da raɗaɗin da bakin nata keyi mata, tasaki wani irin kuka haɗi da ihu,  sam kukanta ko ihunta basu tsai dashi daga horar da ita da yake ƙoƙarin yi ba, sake matse bakinta yayi, yayinda ya sanya hannunsa inda yasake matseta ƙam, cikin kuka haɗi da masifar zafin da takeji tasoma jijjiga kanta, amatuƙar wahalce tasake sakin wani gigitaccen ƙara, tare da faɗin. "Wayyo Allah na bawani a kusane, ku taimakeni dan Allah, wayyo Ummi ɓarayi ɓarawo!." ina su Ummi ba jinta zasuyiba bare ta kawo mata agaji. Sake danneta yayi tare da sanya hannunsa ya murɗe lips ɗinta, tuni tanemi bakin ihu da kuka'n ta rasa, nan fa tasoma harba ƙafafunta tare da yarfa hannuwanta, zafin da takeji yakai zafi domin tuni idanunta sun fara fitar da sabin ƙwalla,  aƙalla saida suka ɗauki kusan mintuna 5 ahaka, sosai tafita hayyacinta kuka take kamar ranta zaifita, ido take jujjuya mishi da bashi haƙuri, "Wayyo dan Allah kayi haƙuri wallahi bazan sakeba." cikin ɓacin rai ya tureta kan gadon, kana ya rufa mata baya, rumtse idonta tayi da ƙarfi jin ya konto kanta, da sauri ta kuma buɗe idanun jin ya fincike rigar tata ya cillata gefe, tuni ƙirjinta ya baiyana irin bainar nan na ziraran miraran, ido ta zazzaro da ƙarfi jin tafin hannunshi kan breast, cikin wani irin kiɗima da farga ta riƙo damatsan hannunshi tuni jikinta gaba ɗaya tsuma yakeyi murya a hargitse tace. "Wayyo Allah na,na shiga uku dan ALLAH na tuba kayi haƙuri". Sai kuma taja wani irin dogon numfashi jin yadda yake murza ƙirjinta da sarrafa shi cikin tattauanawa tafin hannunsa, Wani irin kuka ta sake tare da yunƙurawa da niyar zata ƙwace kanta daga gare shi, sai kuma ta koma ta konta jin ya sake mata nauyi shi ƙafafuwan ta fara harbawa tare da jujjuya mishi kai kana tana ta kiciniyar kwace kanta. Shi kuwa Saifuddeen hannunshi ya ɗauke daga kan ƙirjinta kana ya danne hannayenta da taketa riƙe nashi hannu, sunkuyowa yayi ya manna bakinshi kan breast ɗinta na hannun dama, kana yasa hannunshi ɗaya ya haɗe hannayenta cikin hannunshi ɗayan, wasu irin abubuwan masu wuyar fahimta da misaltawa yakeyi suna shiga jikinshi da zuciyarshi karon forko a rayuwarshi da yake cikin wannan yanayi, wani irin sassanyan tsotsan kan nipples ɗinta yakeyi tare dasa hannu shine yana murza kan ɗayan. wasu tagwayen numfarfashi yake sauƙewa tamkar zasu fita da ransa gaba ɗaya jikinshi suma da karkarwa yakeyi, haka ya sashi sarrafa ta da zafi-zafi. Zaleeha kuwa ido ya raina fata, zufane yaketa tsastsafo mata duk ta inda hudan gashin jikinta yakeyi,kuka da ihu da magiya yakeyi tamkar zata mutu, tattaro sauran ƙarfinta tayi tasa janye hannunta ɗaya cikin zafin da takeji takai hannu kan hannunshi dake murza nipples ɗinta karo na forko a tarihin rayuwarta da namiji ya taɓa mata nononta, kai ta rinƙa jujjuya mishi ganin ya zuba mata kyawawan idanunshi da suka jiye zuwa kalan bacci-bacci, murya na rawa tace. "Na tuba dan ALLAH da sonka da manzon rahma ka barni bazan sake ba, na sani zaka iya min komai". Sai kuma hawaye car-car a hankali ya zame daga kanta ya koma gefe. Da sauri ta tashi zaune can gefe ta koma,hannunta tasa ta tallabi ƙirjin nata, sai kuma wasu sabbin hawayenta suka zubo sabida jin yadda nonanta ke zafi musamman bakinsu dan sosai ya tumurmusheta. da sauri ta janye hannunta tare da yarfa hannun tana mai zubda hawaye tare da fidda sautin. "Shhhhhhh wayyo zafi wayyo ka cinye min nona". wani irin kallo mai ɗauke da tsananin gargaɗi da alamun ki kiyayeni yayi mata, can cikin ransa kuwa dariya yakeyi ganin yadda yakeyi to wannan in an ratsa budurcinta sai yaya, haɗe fuska yayi tare da watsa mata mugun kallo kana ya wurgo mata rigar ta sannan ya yunƙura ya hau kekenshi, nan ya murza wheelchair ɗinsa kai tsaye ya fice daga cikin ɗakin. Wani irin ihu tayi tare da soma buga kanta ajikin bango, kuka take sosai da sosai, yayinda bakinta ke mata wani irin azababben raɗaɗi, har takai ga tanajin kamar ma laɓɓanta basa kan fuskarta ga nononta da sukayi jazir ɗan bakunan sai wani zut-zut sukemata babban tashin hankalinta in sunyi zut-zut ɗin nan har ƙasanta takeji canma yana mata wani irin abu mai sa tsikar jikinta miƙewa. ga hsnnunta da takeji kamar ya karya mata sune Kuka tacigaba dayi inda ta laluɓo wayarta tare da cewa. "Mugu kawai azzalumai zai cinye min nonona ya wani kamani yanata sha kamar ya samu tom-tom ya lallatse min abuna ya meyar min dasu second hand". kaitsaye ta dannawa Mamanta ƙira, bugu biyu kuwa maman ta ɗaga, jin kukan Zaleeha baƙaramin tayarwa da Mama hankali yayiba, cikin matsanancin tashin hankali Mama tace. "Ke Zaleeha yi shiru gaya min meya sameki? wani ɗan abu kazan ubanne ya ta ɓaki?." Cikin matsananci kuka na raɗaɗin zafin da laɓɓanta da nononta keyi mata tace. "Wayyo Mama zai kasheni, wallahi Mama bazan zauna ba, kasheni zaiyi dukana yake tayi tun ɗazu, nikam guduwa zanyi wallahi bazan zauna ba, shi ya dakeni kuma ƴan uwana ma su dakeni, Wayyo Allah nikam nashiga uku!." Zaleeha tafaɗi maganan cikin matsanancin kuka. Wani wawan shar mai tsada mama ta lailayo inda ta bankawa Saifuddeen shida gaba ɗaya zuri'arsa, cikin bala'i tace. "Narantse babu wani wanda ya isa, ya sake dukanke, kujimin hegen nakasashshe yaro mai jajayen kunnuwa ashe dama ya aureki ne don ya tozartamin ke,  wato dama ashe ba iya nakasa bace matsalar tasa harma da ciwon mugunta wato yaga zuƙeƙƙiyar yarinya yanaso ya lallatse min ke ko, to wallahi bazaki zauna ba, bai yiwuwa su su dakeki shima ya dakeki, sam ni ban haifi musu jaka ba, saboda haka nabaki umarnin ki gudu, maza ki tattara kayanki ki gudu Numan gidan Uncle Solomon, bankuma yarje kifaɗawa kowa inda kike ba, duk sai nayi maganinsu." Jin abun da Maman nata tafaɗa yasa Zaleeha tacika da murna, cikin kuka tace da Maman nata. "To." Ko kashe wayar bata tsaya yiba tashiga zuba kayanta acikin akwati, akwatuna 4 tacika da kaya, nan taɗauki duk wani abu nata mai amfani dake cikin gidan,   key ɗin sabuwar motar da Saifuddeen ɗin yasaya mata cikin kayan aure ta ɗauka, nan tafito inda ahankali take jawo akwatunan tana fitowa dasu,   babu kowa a compound ɗin gidan hakan yasa sauri-sauri tagama loda akwatunanta acikin mota, Kana ta koma cikin gida da niyar asuban fari zata bar gombe ta nufi Numan ta jihar adamawa, nan kuma ta ƙara yin mgna da Mama inda take ce mata ta bawa Zahira system ɗinta ta kawo mata da asuba. Haka kuwa akayi ana fitowa massalaci Sallan asuba ta, fito abinta kamar ko yaushe taje ta gaida Ummi to daga side ɗin Ummune ta wuce harabar gidan, tana zuwa ta shiga cikin motan tayi mata key,  maigadi ne ya buɗe mata gate ɗin gidan, cikin yanayi naɗan mamaki ya leƙa fuskarta wanda tayi caɓa caɓa da hawaye, aɗaɗare yace. "Ranki ya daɗe fita zakiyi ne?" Batare data basa amsa ba ta cilla hancin motar tata waje, gab ƙofar gidan taga Zahira na tsaye gefen keke napep, ita kuwa Zahira ganin Zaleehan yasa tayi sauri ta ƙarasa jikin motarta, system ɗin nata ta miƙa mata, da sauri ta amsa ta ajiye bisa kujerar baya, sannan suka ɗanyi wani mgn ƙasa-ƙasa kana ta danna hancin sabuwar motar dawani irin speed ta hau kan titi, gudu take sosai kamar zata tashi sama. Kana ita kuma Zahira ta shiga napep ɗin ya juya da ita. Ahmad ne ya bi motar Zaleeha da ido wanda duk abinda sukayi a kan idonshi dan fitowarshi kenan daga massalaci yaga Zahihara ta fito cikin napep tana raɓe-raɓe shiyasa ya koma gefen wani fulawa ya zuba mata ido. Saifuddeen Yana dawowa masallaci yau sai bai wuce side ɗin Ummi ba kasan cewar a makare ya tashi baiyi wonkaba ya wuce masallacin, shiyasa yanzun ya dawo side ɗinsu yafi son sai yayi wonka kafin yaje cikin gidan. Yana shiga side ɗin nasu ya nufi ɗakin Zaleeha dan ganin ƙofar a rufe yake, ɗan ƙwanƙwasa mata ƙofar yayi saida yaji a jikinshi duk baccinta ta farka sannan ya juya ya nufi falonshi. Yana barin bakin ƙofar ɗakin nata kai tsaye bedroom ɗinsa ya nufa. Yana shiga rage kayan jikinshi yayi kana ya wuce cikin Bathroom ɗinshi. kwance yake acikin  haɗaɗɗen jakuzzien wankansa ya hango haske mai yawa alamun tashin mota, take kuma saiyaji gabansa ya faɗi. "Hasbunallahu wani'imal wakil!." Yafaɗa a ranshi, sake maida kansa cikin jakuzzie'n yayi, lokaci guda tunaninta ya shiga yawo acikin ransa, sosai yayi mamakin yanda ta jure kwanan garden mai cike da sanyi da sauro da dai sauransu, wai duk dan kada yayi mata wani abu. Can gidansu Zaleeha kuwa, a fujajan Mama tanufi falon Baba Malam, suna zaune shida Ƴa Habu, da kuma Ya Ameenu, wanda yana fitowa masallaci ya taho gaida surkin nashi bappanshi kuma kamar yadda yakeyi wasu lokutansai Mamy. Ita ko Mama a hatsale ta banko labulen, babu ko sallama cikin tsananin masifa haɗi da bala'in dake cinta tace. "Dukkan ku hankalin ku ya kwanta, shikenan ni har abada kune zaku cigaba da nakasamin rayuwar ƴaƴa na, to shikenan saiku zuba ruwa aƙasa kusha, shidai mahaukacin da kuka aurawa Zaleeha yafara aikinsa, tunda gashi taƙirani tana kuka kancewa ya yi mata dukan tsiya, ko tashi bata iyayi, to wallahi bazan taɓa lamuntan haka ba, nidai kam ban aifawa wani ƙaton namiji jaka ba, dan haka wallahi dole sai ya sakarmin ƴata,  bai yiwuwa ku ku daketa sannan wani ƙato ma daga waje ya dake ta, wallahi tagama zama dashi kenan tunda dai yakai hannunsa jikinta, ban haifawa kowa jak!." Da ƙarfi ta faɗa bisa kujerar dake bayata sabida tsananin tsoro da firgitan da tayi da jin wani irin azabebben tsawan da Baba Malam ya daka mata. kame jikinta tayi tare da rumtse ida nunta gaba ɗaya jikinta rawa yakeyi tamkar mazari, kawai jira take taji ta inda zai r...! [05/09, 10:33 am] +234 803 765 0266: *INAH ZAKI DAMU!!!* daga jin sunan labarin ba saikun tambaya ba kunsan labarine daya kunshi al'amuran da suke faruwa a cikin duniyar nan tamu wanda tunani ko zato bai taba kawowa ba, ban tausayi al'ajabi soyayya fad'akarwa da ilimantar wa duk zaku samu a cikin littafin nan da naira 200 kacal littafin marubuciyar nan da kuke nishad'antuwa da rubutun ta *SISIN MAMA* kada ku bari a baku labari dan samun mallakar littafin ku nemeta a wannan number d'in 08107499249. Aisha Aliyu Garkuwa: Sosai ta firgita da tsawan da Baba Malam ɗin ya daka mata, a zatonta zai kai mata dukane a nata banzan tunani kenan dan bashi yiwuwa namiji mai kamala da dottuku da tausayi ya daki matarsa, har sai irin dukan da shariya ta lamunce musu. Duk da Mama taci duka. Ganin yayi kwaffa ya jinjina kaine yasa ta Sake gyara tsayuwa ta, cikin rashin tunanin zuciya tace. "Tun wuri ma ku ƙira ku sanar dashi, ya sakomin ƴata, don wallahi bazan taɓa lamunta, haka nan ya dakar min ƴa ba!." Cikin matsanancin ɓacin rai da ƙunan zuciya Baba Malam ya kumadaka mata wata gigitacciyar tsawa wacce ta hautsine hanjin cikin Mama, saboda tsabar firgici  da kuma yanda tsawan yazomata abazata, saida tayi baya-baya inda ta faɗa kan kujera. Su Mamy da Ya Aminu kuwa, sosai suka shiga mamakin irin tsawan da Baba Malam ɗin yayiwa Mama wanda yake nuna zallan ɓacin ranshi,  saɗaf-saɗaf Ameenu da Mamy suka fice sukabar cikin falon. Cikin tsananin ɓacin rai Baba Malam yace da Mama.   "Ya'isa haka, kinyi min ba sau ɗaya ba, ba kuma sau biyu ba, duk ina ƙyaleki, to kisani ayanzu kin kai matakin da bai yiwuwa na ƙyaleki, sai yaushe zakiyi hankali ne? sai yaushe ne zaki samarwa kanki nutsuwa? sai yaushene ɗabi'ar musulamai da imani zai kama zuciyarki? ako yaushe idan kin tashi yin abunki bakya sa tunani acikinsa,  ashe rashin hankalinki har yakai ki tsaya akaina, gaban ɗana, ɗanki kuma surukin ki kina me ɗaga mini murya, to wallahi kisani daga yau na daina ɗaga miki ƙafa akan komai, badai zaman lafiya ne bakyaso ba, to shikenan zanbi dake aduk yanda kikeso. Sannan batun Zaleeha ki sani ƴata ce, ina da ikon da zansa ahukunta ta, aduk sanda tayi mini laifi, haka kuma  Saifuddeen mijinta ne, shima kuma yana da ikon da zai hukunta ta aduk sanda tayi masa laifi." Gyara zaman babbar rigarsa yayi tare da duban Mama cikin ɓacin rai da kuma tsanan halayenta yace. "Wallahi namiki rantsuwa Haleema aduk sanda kika sake, wata matsalar ta auku agidan auren Zaleeha, wanda har ya kasance da sa hannunki aciki, tabbas zan shayar dake mamaki,  tashi ki ficemin daga falo!!." Ya ƙare maganar murya a kausashe, kana yana meyi mata nuni da ƙofar fita daga falon. Cikin hanzari Mama ta-tashi inda ta fice daga cikin falon, duk da cewar tsawan da yayi mata ya tsorata ta sosai, amma hakan baisa ta daina cika da batsewan da takeyi ba, sosai tacika tayi fam, tana ƙarasawa part ɗinta ta saki dogon tsaki, tare da yin ƙwafa, abayyane tace. "Dani kuke wasan, ai dai nikam nawa ƙuncin kuma ya ƙare saura naku, yanzu ne aka fara buga wasan, sannan yanzu ne kuma tashin hankalinku zai fara, wallahi sai na shayar daku baƙin ciki, fiye da wanda kuka shayar dani". Tana ƙarasawa ɗaki, wayarta ta ɗauka inda ta dannawa number'n Ruda ƙira, bugu uku kuwa Ruda ta ɗaga wayar,  Mama na fitar da huci tayi mawa Ruda bayanin duk wani abu dake faruwa, shewa Ruda tayi tare da cewa. "Karki wani damu hankalinki badai kinsa ta gudu ba, shikenan ki manta dasu kawai, nan da kwana 2 zaki gansu arana karki damu kinji dai boka ya gaya mana zaisa ta daina jin tsoron ɓacin ran Babanta da son yimishi biyayya, kinji yace mana komai zai tafi yadda mukeso." Murmushin mugunta Mama tayi tare da aje wayar, kwanciya tayi akan gado, jin ranta takeyi fes, hakanan takejin kamar an rabata da ƙaya, domin kuwa tunda Zaleeha'nta ta auri gurgu, kullum kwanan duniya da baƙin ciki take kwana, yanzu kuwa Allah ya yaye musu, ya rabasu da masifa saboda haka ta gyara kwanciyarta donyin baccin safe, wanda ta ɗan kwana biyu bata yi shi ba. Can gidan su Saifuddeen kuwa, Ahmad na ganin tashin motar na Zaleeha'n, ya bita da kallo har sai da ta ɓacewa ganinsa, mamakin inda zataje awannan sanyin safiyan yake, yasan dai hakanan bazata fita da sanyin asuba ba kuma dai yasan hukunta bai ƙare ta koma wurin aikinta ba bare yace ko can ta sammakawa. Koma cikin gidan yayi, inda kai tsaye ya nufi ɓangaren Ummi, da sallama ɗauke abakinsa ya shiga cikin falon, zaune ya iske Ummi akan lallausan darduman dake shumfuɗe tsakiyar ɗakin, gefe kuwa Raliya ce, yayinda ummin ke jan carbin dake hannunta, ƙarasa shigowa cikin falon yayi, nan ya zauna abakin carpet ɗin tare, da ɗagawa Ummi gaisuwa, cikin girmamawa,  fuska ɗauke da murmushi Ummi ta amsa masa gaisuwan nasa, duban Ummin yayi tare da cewa. "Naga Zaleeha tafita yanzu, ko ta faɗa muku inda zata jene?." Ɗan jim Ummi tayi tare da cewa. "Tafita kuma, da safen nan?." Kai Ahmad yajinjina tare da cewa. "Yanzun naga fitarta." Girgiza kai Ummi tayi tare da cewa. "Ɗazun kuma tabar nan, don tazo ta gaisheni, saidai kuma sam bata faɗamin cewa zata fita ba, amma wata ƙila shi Saifuddeen yasan da fitarta." Kai Ahmad ya jinjina, tare da neman kawar da zancen ta hanyar duban Raliya, cikin kulawa yace. "Please haɗamin tea mana, yau so nake nafita da wuri." Da "To." Raliya ta amsa sannan ta tashi ta wuce kitchine, shi kuma kaitsaye ya wuce ɓangarensu don yin wanka. Can wajen Saifuddeen kuwa fitowarsa daga wanka kenan,  cikin nutsuwa ya gama goge jikinsa, inda ya sanya towel ya shiga tsane lallausan sumar kansa, wanda yaji aski irin na zamani, uwa uba yasha gyara sai ƙyalli yake, yana kammala goge jikin nasa, ya ɗauki body lotion ɗinsa mai daɗin ƙamshi, cikin nutsuwa ya shiga shafawa, yana kammala wa, ya shafe jikinsa da wani irin body oil spray mai matuƙar ƙamshi,  take gaba ɗaya ɗakin ya gauraye da ƙamshin sa,  ahankali ya tura wheellchair ɗinsa har zuwa gaban haɗaɗɗen drawer ɗinsa,  buɗe drawer'n nasa dake shaƙe da kaya yayi,  hannunsa yakai zuwa ɓangaren da ƙananan kayansa ke jere,   wani crazy combat jeans Black colour haɗi da wata D&G t-shirt mai kyaun gaske ya zaro, daga cikin tarin kayan nasa, sosai drawer'n nasa ke cike da kaya, sai kace wani kanti, wani kayan ma har mantawa yake dasu, dan ma duk bayan wani ɗan lokaci yana kyautar da kayayyakin da sosai musamman wa mutanen ƙungiyar su Jonapwd. Cikin yanayinsa na nutsuwa ya zura kayan ajikinsa, wanda suka matuƙar amsar farar fatarsa,  wani silver watch ya sanya ahannunsa, sannan ya buɗe wata ƴar glass drawer dake nan cikinsu yake aje caps ɗinsa, wata baƙar facing cap mai kyau ya zaro, inda ya ɗaura akansa, take yafito yayi wani daban dashi, ga wani irin kyau da yayi, ahankali ya tura wheelchair ɗinsa zuwa inda yake aje takalmansa, wasu flat shoe masu kyaun gaske ya zura acikin fararen ƙafafunsa, wayoyinsa da kuma laptop ɗinsa ya ɗauka, parfumed ya shafa, sannan yanufi hanyar fita daga ɗakin,  ahankali yake tafiyar da wheelchair ɗin nasa, har yasamu kansa acikin falon Zaleeha'n, ko ƙofar ɗakinta bai kalla ba haka yafice daga cikin part ɗin nasu gaba ɗaya,  direct ɓangaren Umminsa ya nufa. Kusan karo sukayi da Hayatuddeen wanda ke ƙoƙarin zuwa part ɗin nasu, ƙiransa shida Zaleeha akan cewa suzo suyi break, don su atunaninsu zuwa lokacin ta dawo. Duban Saifuddeen ɗin Hayatuddeen yayi, cikin ƙaunar Hamman nasa yace. "Wow Hammana kaga yanda kayi kyau kuwa!." Murmushi Saifuddeen yayi tare da duban Hayatuddeen, irin duban nan mai ɗauke da yanayin magana, alama yayi masa cewar. "Uhummm ." Kai Hayatuddeen yajinjina masa tare da cewa. "Fiye da kullum ma kuwa, wani lokaci Hamma nakan tambayi kaina, me yasa kai ba mace ba amma kowani kaya kasa saikayi musu kyau, saidai kuma idan na tuna da cewa Hamman nawa Namijin gaske ne, sai naji kaina ya ƙara girma, saboda samun ka amatsayin Hamma yafiyemin komai." Murmushin daya bayyana tsantsar kyawunsa yayi, cikin ƙaunar ɗan uwan nasa yasanya hannunsa inda yakamo kumatun Hayatuddeen ɗin. Dariya Hayatuddeen yayi tare da zagawa bayan hamman nasa inda ya turosa zuwa cikin falon, da shigowarsa cikin falon har falon ya ɗauki ƙamshin oud ɗin dake jikinsa. Har gaban dinning area Hayatuddeen ya tura hamman nasa,  inda Raliya da kuma Ahmad ke zaune, Raliya ne ta gaishe da yayan nata,  cikin ƙauna da kuma ganin ƙoƙarin ƴar uwar tasa na haɗa musu break fast kullum da takeyi ya amsa mata, yana tunanin gashi tasa an sallami mai akin wai duk a kanshi dan sun san yanada tsantsani.   Dai-dai lokacin Ummi ta fito daga cikin ɗaki, ganin Saifuddeen zaune yasa ta ƙara faɗaɗa fara'arta cikin kulawa tace. "Kunfito ko, ina Zaleeha'n, nace yau itama tazo cikin mu tayi break dan duk anzama ɗaya." Ummi taƙare maganar tana me jawo kujera ta zauna. Kallon Hayatuddeen Saifuddeen yayi, cikin body language yayi masa alama kan cewar yaje ya ƙirawo Zaleeha'n, kai tsaye hayatuddeen ya tafi don ƙiranta. Koda yaje part ɗin nasu, haka yayita knocking a ƙofarta, amma shiru, jin shiru ne yasashi tura ƙofar ɗakin ahankali, ɗan tsayawa yayi abakin ƙofa, da ɗan ƙarfi yace. "Aunty Zaleeha kizo muyi break, kin san dai bana iya jure yunwa." Jin shiru ba'a amsa shi bane yasanyashi ƙara kutsa kansa cikin ɗakin, nan yashiga dube dube kozai ganta amma shiru, kasa kunnensa yayi wai ko zaiji motsin ruwa a toilet, nan ma dai shiru, hakan yasashi juyawa kawai yafice daga ɓangaren nasu gaba ɗaya. Yana komawa yace musu baiganta ba, har ɗakinta ya shiga amma bakowa ciki,  fuska ɗauke da mamaki Saifuddeen ke kallonsa, to ina Zaleeha zata je kenan,  kallon Ahmad yayi wanda yake ƙoƙarin saving ɗin kanshi, yana cewa. "Maybe bata dawo daga fitan da tayi bane." Gane abun da Ahmad ɗin ya faɗa ne, yasa shi ɗan lumshe idanunsa,  Ummi ne ta dubesa, cikin kulawa tace. "Dama kasan da fitarta ne? dan Ahmad yace yaga fitanta tun da sanyin safiya koma ince asuba." Idanunsa ya rumtse tare da girgizawa Ummi'n kai, alaman "A'a."  ɗan jim Ummi tayi take kuma, wani tunani yazo mata inda ta raya aranta cewa ko gida Zaleehan taje, nan dai tace tasan cewa zuwa anjima zata dawo. Raliya ne tayi saving ɗinsu inda suka soma cin abinci cikin nutsuwa, shidai Ahmad hakanan jikinsa ya basa wani abu daban, yasan babu dalilin da zai kai Zaleeha gida awannan sanyin safiyan, idan da ace akwai dalilin ma to tabbas yasan da zuwa yanzu ansanar dasu. Haka suka kammala break fast ɗin nasu cikin nutsuwa, Ahmad ne ya miƙe dan yana so yaɗan fita, shikuwa Saifuddeen cikin falon na Umminsa ya koma, inda ya sauƙa daga kan kekensa, kwanciya yayi akan doguwar kujera tare da jawo laptop ɗinsa, ya ɗaura akan cikinsa, nan ya buɗe cikin nutsuwa yashiga yawo a internet, Hayatuddeen ma zama yayi akusa da hamman nasa inda ya jona game a tv plasma ɗin dake cikin falon, hakan yasa kowa da inda ya bada hankalinsa, Ummi kuwa ɗaki ta koma dan tanason kimtsa wasu kayyakin gudumowan biki da aka kawo mata, nan Raliya ta bita inda suka shiga aikin tare. Sosai yabada hankalinsa akan aikin da yakeyi, hakanne ma yasa har lokuta suka ja batare daya sani ba, inda Hayatuddeen kuwa tuni ya kwanta akan carpet yayinda bacci ya ɗaukesa, da dukkan alama jiya kusan kwana yayi yana chat, don abu ɗaya ne ke saka Hayatuddeen bacci da rana, shine idan bai samu enough bacci da dare ba, to dole da rana zaiyi bacci, wai abun ma yazo masa da sauƙi don yau basu da lectures sai ƙarfe 2:00 pm, shi yasama yaji gwamma yayi baccinsa, kafun time ɗin. Ummi ne tafito daga cikin ɗakinta, duban Saifuddeen tayi, ganin kaman baisan da zuwanta ba yasa ta shafi gashin kansa, ɗago da kansa yayi inda ya dubeta, ganin Umminsa ya sashi narke fuska,  akasalance yayi mata alaman sannu da fitowa, hakanan yake aduk sanda zaiga Umminsa, to fa raki da shagwaɓa kawai zai dinga yi mata, wani lokaci ko Hayatuddeen bai  kai Saifuddeen yawan shagwaɓa ba. Kansa Ummi ta shafa, cikin kulawa tace. "Inajin gabana yana ɗan faɗuwa tun ɗazu, ya kamata kaje ka duba Zaleeha kota dawo." Fuskansa yaɗan kwaɓe, tare da tashi zaune miƙa yayi inda yayiwa Ummin alaman cewa ya gaji, murmushi kawai Ummi tayi tare da ƙwala ƙiran Raliya, wanda ta shiga kitchine don ɗaura musu lunch, don a time ɗin kusan ƙarfe ɗaya ake nema. koda Raliya'n tazo, cewa da ita Ummi tayi, taje ta duba part ɗin nasu Saifuddeen ko Zaleeha ta dawo. Da "To." Kawai Raliya ta amsa, nan tafice daga cikin falon, koda taje part ɗin, haka tayi ta kwaɗa sallama amma shiru ba amsa, alaman bata dawo ba kenan,  haka ta fito daga falon, koda ta kawo compound ɗin gidan, parking space ɗinsu ta duba, nan taga babu motar Zaleeha'n, alaman kenan bata dawo ɗin ba, nan ta koma inda ta faɗawa Ummi cewa "Zaleehan bata dawo ba." Ɗan jim Ummi tayi nan tace. "To bari dai zuwa yamma, idan bata dawo ba sai muƙira gidansu mu tambaya, ko wani abunne ya faru." Shidai Saifuddeen ƙala baice ba, saboda ae Zaleehan bata maidashi miji ba, because da zata fita kanta tsaye ta fita, babu neman izini ba komai, wannan yasa shima bazai shiga cikin shirgin nemanta ba, sauƙa daga kan kujeran ma yayi, inda ya hau kan wheelchair ɗinsa, da kansa ya tashi Hayatuddeen, inda yace yaje ya ɗauro alwala yazo su wuce masallaci, don yin sallan Azahar, part ɗinsu yaje inda yayi alwala, koda yafito yasamu Hayatuddeen tsaye nan suka wuce masallacin dake kusa dasu. Ummi kam dai hakanan takejin wani abu dangane da tafiyan Zaleehan, sosai take fargaban abun da zuciyarta ke raya mata, aranta tana fatan ma Allah yasa ba hakan bane. Saifuddeen kuwa koda suka dawo masallaci, part ɗinsu ya nufa, nan ya nufi bedroom ɗinsa, inda ya kwanta ya ɗan huta. Abu kamar wasa tun ana ƙarfe ɗaya, biyu, uku, har zuwa ƙarfe huɗun yamma babu Zaleeha babu alamarta, sannan daga gidansu ba'a ƙira ance tana can ba, abun da yayi mugun ɗaga hankalin Ummi kenan, nan tatura akayi mata ƙiran Saifuddeen, zuwa yanzu yasake wanka cikin wasu tsadaddun riga da wandon jeans masu kalar navy blue, sosai sukayi masa kyau. Dubansa Ummi tayi cikin nuna damuwarta afili tace. "Gabana faɗuwa yake Saifuddeen, har yanzu fa Zaleeha bata dawo ba, kuma kace bata sanar dakai fitan ta ba." Kansa ya jinjinawa Ummin tare da kamo hannunta, cikin kulawa yayi mata alama da body language ɗinsa, kan cewar. "Kada ta damu Zaleehan zata dawo ne, wata ƙila tayi nisan zango ne." Girgiza kai Ummi tayi cikin kulawa tace. "Bari dai naƙira gidan nasu naji, ace mutum ya fita tun gari bai gama haske ba, kuma ace har yanzu kusan ƙarfe 5 ake nema amma baidawo ba." Nan Ummi ta ɗauki wayarta, inda ta danna wa number'n Mamy ƙira, don duk gidan number'n mamy kaɗai take dashi. Bugu biyu aka ɗauki ƙiran, amutunce suka gaisa da Mamyn, cikin nutsuwa Ummi tace. "Dama cewa zanyi ko Zaleeha na gidan naku ne, tun safe ta fita kuma shine har yanzu munji shiru bata dawo ba." Gaban Mamy ne ya faɗi, cikin  yanayin mamaki tace. "Tun safe kuma,  to ina take kenan don dai kam batazo gidan nan ba yau." Zuciyar Ummi ne ya tsinke cikin muryar damuwa tace. "Nima fargaba ne ya isheni shiyasa nace kawai bara naƙira na tambaya, indai ko bata gida to ina taje kenan, tunfa gari baigama haske ba ta fice." Cikin mamaki haɗi da fargaba Mamy tace. "Bakomai ku kwantar da hankalin ku, bari na shiga can ɓangaren mahaifiyarta ta saina tambaya kota zo, sannan zan faɗawa Baban nata ma, duk yanda ake ciki zaku jini." Nan Ummi tayi mata godiya, daga haka ta aje wayar,  kallon fuskar Ummi kaɗai Saifuddeen yayi, ya fuskanci cewa akwai damuwa. Mamy kuwa ko aje wayar batayi ba ta nufi ɓangaren Mama, da sallama ɗauke abakinta ta kutsa cikin falon Mama'n, Zaheera dake kwance tana kallo ne ta amsawa Mamy'n, dubanta Mamy tayi tare da cewa. "Zaheera ina maman taku." Zaheera bata kai ga cewa komai ba, saiga Mama tafito daga cikin kitchine, duban Mama Mamy tayi cikin nutsuwa tace. "Halima yanzun mahaifiyar Saifuddeen taƙirani, wai tun safe Zaleeha tabar gida kuma har yanzu bata koma ba, shine take tambaya ko nan tazo, nace da ita a'a, saidai kuma bansani ba ko tazo yau ɗin, naji ma kamar hankalinsu atashe yake, kuma gashi naga bata nan ɗin ma, ina Zaleeha tashiga kenan?." Mamy ta tambaya cikin yanayin damuwa. Tsuka Mama tayi tare da turo ɗan kwalinta gaba, cikin halin ko inkula tace. "Wani daga cikin ku yabani ajiyar Zaleeha ne da zakizo kina tambaya ta, ko kuwa idan tazo nan ɗin goyata zanyi abayana na kaita ɗaki na ɓoyeta, kwaje can kunemeta nikam banganta ba!." Mama taƙare maganar tana me yatsuna fuska. Shiru Mamy tayi tare da sauƙe ajiyar zuciya, ahankali tace. "Allah ya huci zuciyarki." Bata jirayi me maman zata ce ba, ta juya tabar falon. Ƙwafa Mama tayi tare da jijjiga kanta, cikin yanayin mugunta tace. "Gaba ɗayanku zaku sani ne, kuma ku sani, wallahi ƴata tagama zama da nakasashshe ehe." Daga ɓangaren na Mama kai tsaye Mamy wajen Baba Malam ta nufa, tana shiga kuwa ta iskesa zaune shida Habu da kuma Ameenu, cikin nutsuwa Mamyn ta sanarwa Baba Malam abun dake faruwa, nan take Baba Malam yaji zuciyarsa tayi wani irin bugawa, gyara zamansa yayi tare da fuskantar Mamy'n cikin, nuna damuwa yace. "Zaleeha bata gidan mijinta kuma, to ina tashiga?." Rumtse idanunsa yayi, tare da ambatan sunan ALLAH Acikin ransa, haƙiƙa Zaleeha kyautace daga wajen Allah, amma sosai lamuranta ke caza masa ƙwaƙwalwa, sam batajin magana ko kaɗan ta bambanta da Maryam. Ya Ameenu kuwa wani irin baƙin cikin Zaleehan ne ya turnuƙesa, shikam tun ba yauba ya gane cewa iskanci Zaleehan keji dashi, yayi rantsuwa kuma saiya sauƙe mata, guguwar dake kanta, burinta kullum shine tajawo musu abun faɗa, so take ta ɓata musu suna, ta kuma ɓatawa Baba Malam halin dattakon sa. Ya Habu ne yace. "To yanzun ina taje?." "Sai Allah!." Mamy ta faɗa asanyaye. Nan take Ya Habu ya ɗauki wayarsa, inda yasoma ƙiran ƴan uwansu na kusa ko Zaleehan taje, amma babu wanda yace tazo. Ya Ameenu ne ya ƙira Maryam awaya inda ya tambayeta ko Zaleehan tazo bayan fitowan sa daga gida, cikin tsananin tashin hankali Maryam tace masa bata zoba. Baba Malam da kansa ya ɗauki wayarsa inda ya dannawa ƙanwarsa, wato Goggo Maryama ƙira, nan ma cewa tayi sam Zaleehan bata zoba, haka Ya Habu da Ya Ameenu suka dinga ƙiran layukan ƴan uwa da kuma abokai na kusa, waƴanda suke  tsammanin cewa Zaleehan zata iya zuwa, amma babu wanda yace tazo, ko labarinta ma babu wani wanda yace yaji. Take Ya Ameenu ya danna ƙiran Lambarta, haka wayar tayita ringing har ta katse, no answer, sake dialing yayi, still har ƙiran yasake katsewa ba a ɗauka ba, saida yayi mata 4 missed calls, amma duka no answer, Ya Habu ne shima yaƙira layin nata, nan ma bata ɗauka ba, sau 5 yana ƙira amma shima bata ɗauka, Baba Malam ne dakansa ya laluɓo lambar tata, nan ya danna mata ƙira, saidai shima kamar sauran haka har ya katse no answer,  nan fa akeyinta ran Ya Ameenu idan yakai million to saida ya ɓaci, take yasoma sakin huci, yayin da yakejin wani ɗaci aransa, har wacece Zaleeha da baba Malam zaiyi mata 2 missed call amma bazata ɗaga ba, lallai idan ya kama Zaleeha, saiya rabata gida biyu. Ganin duk bata ɗauki wayansu bane, yasa Mamy ta ƙirata da layinta, duk dai abu ɗayane bata ɗagawa, nan hankalin Mamy yatashi, take tsoro ya shigeta, nan ta fara tunanin ko Zaleehan bata lafiya ne. Ya Ameenu ne ya kirata da sabon SIM ɗinsa, inda ya sake dialing number'n Zaleeha'n, shi ɗin ma dai batai picking ba, maida wayarsa cikin alj'ihu yayi, inda ransa ke ƙara tsuma yana ɓaci. Baba Malam ne ya dubi Ya Ameenu, nan yace. "Yaje gidan su Saifuddeen ɗin, don sanar dasu halin da ake ciki, idan kuma yasamu Zaleehan ta dawo, to ya basa umarni ya tattakata yayi mata duka irin wanda sai ta kasa tashi, sannan kuma ta faɗa masa gidan ubanwa taje." Nan Ya Ameenu ya miƙe, haka ya fita yana huci don cika umarnin Baba Malam ɗin. Acan gidan su Saifuddeen kuwa, sosai Ummi ta ɗaga hankalinta, tabbas tasan zuwa yanzu rashin dawowan na Zaleeha ba lafiya ba,  ita da Raliya harma da Hayatuddeen gaba ɗaya hankalinsu atashe yake, Adda Rahma wanda itama yanzu zuwanta, jin labarin rashin ganin Zaleeha'n , sosai ya tashi hankalinta. Saifuddeen kuwa yana zaune afalon, laptop ɗinsa yake ta dannawa, sam baikula da harkan neman Zaleehan ba domin duk wani motsinta afa tafin hannunshi take yasan muddin ya maida na'urarshi kanta bata da mafakar da zata shiga ya gaza ganewa.   Zuwan Ya Ameenu ne ya ƙara tada hankalin su Ummi,  nanfa abu kamar wasa ya zama gaske,  sosai aka shiga neman Zaleeha amma kamar ɓatan laya babu ita babu alamanta, Ahmad da Ya Ameenu ne suka shiga mota, inda suka soma zaga gari nemanta, har gidansu Rasheeda da Bilkeesu sunje, amma sun shaida cewa basu ganta ba, nan Ya Ameenu yasa Ahmad dake driving suka nufi family hause ɗinsu, wato gidansu Ya Ameenun kenan, nan ma dai bata nan,  gaba ɗaya ƙanne da yayyan Ya Ameenun saida yaƙirasu ko Zaleehan tazo amma haka suke cewa bata zoba, sosai hankalin familyn ya tashi, Zakariyya da Ziyada kuwa da labarin neman Zaleehan ya iskesu, haka suka shiga damuwa sosai, Hajja kuwa take tasoma kuka, abunka da tsufa, dama kuka baiwa tsofi wahala. Gaba ɗaya ran Ya Ameenu yasake ɓaci, domin sosai shida Ahmad sukayi buji-buji dasu wajen neman Zaleehan, gashi yanzu har ƙarfe goman dare kenan amma babu ita babu alamanta, still wani abun baƙin cikin kuma shine idan anƙira wayarta bata picking,  koda kuwa za'ai mata ƙira ashirin ne bazata ɗaga ba, wannan dalilin yasa ran Ya Ameenu dana Baba Malam ƙara ɓaci,  can gidan su Saifuddeen kuwa, sosai ɓatan Zaleehan ya ƙiɗima Ummi da su Raliya, Saifuddeen kuwa, ganin yanda hankalin Umminsa ya tashi sosai ne, yasan yashi barin sashin na Ummi gaba ɗaya, part ɗinsu ya koma inda ya kwanta yayi shiru, sosai al'amarin Zaleeha ke ƙona masa rai wani lokaci, sai dai yayi rantsuwa bazai taɓa bari sha'anin haukanta ya damesa ba, wani abu can daban bai damesa ba, saboda haka haukan guduwanta bazai taɓa damunsa ba, yasani koma tana inane to ita takai kanta, sannan kuma ita ta zaɓa, abinda dai ya sani yasa a ransa ta boni da aurensa dan babu saki a tsarin rayuwarsa ta gama guje-gujenta aurensu takalmin kazane mutu ka raba ya rantse wa ransa ko shekara 30 zatayi bata dawoba ba saki ta shiga ukunta dashi dan babu ita babu wanda take cewa tana son. Can gidan Baba Malam kuwa, sawa yayi aka ƙira masa Mama, cikin tsananin ɓacin rai ya dubeta, ransa nayi masa suya yace. "Zaleeha tabar gidan mijinta tun asuba, sannan har yanzu bata dawo ba, an kuma nemeta an rasa, tabbas nasan cewa kome Zaleeha ta aikata da sa hannunki, saboda haka ina kika kaita kika ɓoyeta?." Yaƙare maganar murya a kausashe. Ihu Mama tasanya tare da zamowa ƙasa ta zauna daɓas, hannu tasa aka, cikin ɗaga murya tace. "Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un! wayyo Allah na, shikenan kun cuceni kun halakarmin da ƴata, shikenan abun danake gudu shiya faru, baƙin cikinku yasa ta gudu, wayyo Allah na!!." Mama taƙare maganar tana me rushewa da kuka,  kuka sosai take tana faɗin,  "Shikenan kun cuceni, kun rabani da ƴata, wayyo Allah Zaleeha na!." Kallon takaici Baba Malam yayi mata tare da girgiza kansa kawai,  nan ya wuce zuwa ɗakinsa, don baida wadataccen lokacin da zai tsaya sauraran ihun Mama'n. Ganin Baba Malam ya wuce ɗaki, sannan Mamy da Habu sun fice daga falon ne, yasa Mama saurin tashi, cikin matsanancin farinciki tayi juyi, fes takejin zuciyarta, nan ta sake sakin kukan ƙarya, haka tafita daga falon na Baba Malam tana ta faɗin, cewa sun cuceta, tare da cewa lallai su nemo mata ƴarta duk inda ta shiga ta fita. Awannan rana kuwa har ƙarfe 2 na dare babu wanda ya rumtsa  acikin waƴannan gidaje guda biyu,  Mama kuwa da gangan tahana idanunta bacci, hakanan taketa kukan cewa ane mo mata Zaleeha'nta. Saifuddeen kuwa, damuwar dayaga Umminsa aciki ne kawai ya hanasa bacci, sosai yayi ƙoƙari wajen bawa Ummin nasa baki, amma ina Ummi har ƙwalla saida ta zubar, musamman ma idan ta tuna da cewa, basu san wani hali Zaleehan ke ciki ba, shi kuwa Saifuddeen tsab yaga text ɗin da Zaleeha ta turawa ƙawarta Bilkeesu cewa ta gudu, sabida ya haɗe kan wayar Zaleeha da tasa duk abinda zatayi zai gani kuna zaiji, to dai har yanzu baiga ko ji ga inda ta nufaba. Ɓangaren Baba Malam kuwa, baƙin ciki da ɓacin rai ne suka hanasa bacci, tabbas yaji ajikinsa cewa, ba ƴan kidnappers ko wasu mutanen bane suka kama Zaleehan ba, hakanan yaji ajikinsa cewa, guduwa kawai tayi don nuna masa cewa bai isa da ita ba, sannan tayi hakanne don ƙara masa damuwa, sannan ta kuma watsar masa da mutumcinsa a idanun jama'a. Ya Ameenu kuwa tsananin takaicin Zaleehan ne ya hanasa bacci, yayinda Maryam kuwa ke kuka wiwi, rarrashin duniya yayi mata amma takasa daina kuka. Ya Ahmad ma da ba'a gari yake bama, yanacan Abuja saida yakasa rumtsawa, wani irin babban tashin hankali yasamu kansa aciki lokacin da aka faɗa masa, haka ma Aunty Lubna, sosai hankalin Ya Ahmad ya tashi, don yasan cewa Baba Malam zaisanya damuwar acikin ransa, ko kaɗan kuma baya ƙaunar abun da zai taɓa mahaifinsu. Haka dai gaba ɗaya ahlin gidaje biyun nan sukayi kwanan zaune, dasu da kuma duk wani danginsu na kusa,  washe gari kuwa da sassafe Ya Ameenu da Ya Habu suka sake bazama neman Zaleeha. Inda Ahmad ma yashiga cikinsu,suka shiga nemanta tare. Baba Malam kuwa da sassafe ya shirya, inda ya nufi Dukku, dan zuciyarsa na raya masa cewa ko can taje. Haka su Ya Ameenu suka ƙarishe yawonsu amma babu Zaleeha babu alamarta, nan Ya Habu ya shiga motarsa, kai tsaye  ya nufi Ɓilliri, wajen dangin mahaifiyarsu, koda zai sameta acan, amma koda yaje haka yagama shan wahala, ko ina yaje, sai suce bata zoba. Baban Mama kuwa ranshi yayi masifar ɓaci duk da kasan cewarshi kafuri baiji daɗin abinda Zaleeha ta aikataba, koda yake ya zargi ƴarsane a lamarin, dan a zahiri ta nuna mishi bata son auren. Can Dukku kuwa Baba Malam babu inda baije duba Zaleeha'n ba, kama daga gidajen ƴan uwa da abokan arziki, duk yaje amma babu ita ba labarinta, sosai hankalinsa ya tashi, nan take yaji wani ciwon kai mai zafi ya rufesa, alaman cewa jininsa ne keson hawa, don dama yana da ciwon hawan jini. Ya Ahmad kuwa tuni ya biyo jirgi shida Aunty Lubna, inda suka dira acikin garin Gombe, sosai hankalinsa ya ƙara tashi ganin cewa har yanzu ba'aga Zaleehan ba, ƙira kuwa yayi mata yafi sau hamsin amma bata ɗagawa ba, wannan abun shiya ƙara jefasa acikin tashin hankali. Ɓangaren Zaleeha kuwa tun da ta ɗauki hanya bata tsaya ba harsaida tasamu kanta acikin garin Numan na Adamawa yola,  gaba ɗaya ƙiran da akeyi mata akan idanunta, amma zuciyarta tayi wani irin nauyi wanda batajin zata iya ɗaga ƙiran kowa, sannan kuma batajin cewa zata kashe wayarta. Hamdala taketayi a ranta tanaga ta tsira daga farmakin Saifuddeen, dan yayi masifar razanata da bata tsoro jiya da dare, hannu tasa ta share hawayenta wanda bata san dalilin zubowarduba a hankali tace. "Ya Allah kasa kada Babana yayi fushi sani". Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da cewa. "Hmmmm Allah na godema daka tsere tar dani daga hannun wannan mutumin, na sani tabbas da na ƙara kwana a gidan shi, haka zai ta lallatseni kamar maggoro yayi ta tsotsini kamar tom-tom daga nan zai gwada min ƙarfin yace zai farkeni, dole nema in gudu daga komarshi mugu kawai." haka dai taci gaba tuƙi. Daga cikin garin na Numan, kai tsaye anguwar bakin kogi ta nufa, don acanne uncle solomon ɗin yake, a bakin kogi nan sukeyin rayuwa,  da ƙyarma ta iya ƙarasawa wajen, don kafun ma ta isa tuni tayi laushi, amatuƙar gajiye takejin kanta,  a ƙofar ɗan madaidaicin gidan wanda gininsa yayi masifar tsufa ta dai-dai-ta parking ɗin motar, buɗe murfin motar tayi inda tafito kai tsaye tanufi cikin gidan, ko damuwa da mutanen dake kallonta batayi ba. Sanincewar su ɗin ba musulmai bane yasa, kanta tsaye ta kutsa kanta cikin gidan. Elizabet  matar Solomon dake zaune atsakar gida tana tatan markaɗen dawan burkutunsu, jin motsin shigowan mutum yasa ta ɗago kanta ta dubi ƙofar shigowa gidan, ganin Zaleeha tsaye yasanya taɗan saki fuskarta, cikin ɗaga murya Elizabet ɗin tace. "Solo oya come out ga baƙuwarka ta iso." Solomon dake cikin ɗaki jin abun da Elizabet ɗin ke faɗa yasan yashi fitowa, hannunsa riƙe da fartanya, da'alama dama gona zashi, kasancewarsa manomi kayyakin marmari na bakin kogi. Ganin Zaleeha yasashi washe haƙoransa. Cikin gurɓatacciyar hausarsa yace. "Aa Zali'a kin iso kenan, your wellcome, shigo ciki  mana." Ɗan guntun murmushi Zaleeha tayi tare da ƙarasowa cikin ɗan ƙaramin gidan,  tana wucewa Elizabet ta bita da kallo ƙasa-ƙasa ta taɓe baki. Nan Zaleeha tabi Uncle ɗin nata zuwa cikin ɗaki, inda yace da Elizabet ta kawo mawa Zaleehan ruwan sha. Abakin wata katifa wanda ta fara lashewa Zaleehan ta zauna, nan shima Uncle ɗin nata ya zauna. Dubansa tayi tare da cewa. "Good evining uncle, haw was the day?." "Am very fine my daughter, how are you, i hope are you okay, right?." Murmushi ta ɗanyi tare da jinjina masa kai, ahankali tace. "Yeah." Dai-dai lokacin Elizabet ta shigo hannunta ɗauke da kofin ruwa wanda ta tara a bakin fomfonsu dake ɗan tsakar gidan nasu, aje kofin tayi agaban Zaleeha, ɗauke kai Zaleeha tayi domin sam batason jin ƙamshi ne ko warinsu zata ce ne oho, cikin ƙasa da murya tace. "Aunty good evining." "Evining, how are you?." Elizabet tafa ɗa tana me kallon Zaleeha'n, wanda take ta faman ƙarewa ɗakin kallo. "Am fine!" Zaleeha tafaɗa tana me ƙarewa kofin da aka kawo mata ruwa aciki kallo, Allah Yasani itakam ƙyanƙyaminsu takeji, hakanan take ganin komai nasu yafita daban, komai nasu ba irin na sauran mutane ba, shiyasa ma kwata kwata bata fiye shiri da dangin mahaifiyarta ta ba, domin ita sam batason zama da su, saboda zama da waƴanda hasken addinin musulunci bai cimmusu ba, sai ahankali, zakaga kwaɓa da kuma shirme kala-kala. Duk da kasancewar tanajin ƙishin ruwa, amma kasa shan ruwan tayi, don sam bata yarda ma da tsabtan gidan ba. Hira kaɗan suka ɗan taɓa da Uncle din nata, nan yace da ita zai tafi gona, yana tafiya ta jawo akwatunanta, zanin gadon dake kan katifan da take kai ta yaye, nan taciro wani bedsheet mai ɗan taushi wanda baida nauyi ta shumfuɗa, kimtsa akwatunanta tayi agefe kana ta fito da sallayanta da komai na buƙatan musulmi ta a dana, hand bag ɗinta ta zuge, nan ta ciro wasu diary milk chocolate guda biyu, tare da wani cake, nan ta kwanta tare da jawo wayarta, power bank dinta ta ɗauko inda ta saƙala wayarta a charge, kwanciya tayi tana mecin chocolate ɗin ahankali, hakanan dai ta gwammace gwara zaman nan dana gidan SAIFUDDEEN dake cike da jin daɗin daular duniya. Acan Gombe kuwa, Haka su Ya Ameenu suka ƙare yawonsu har suka gaji, dawowa gida sukayi inda sukayi jigum jigum. Baba Malam ma haka ya dawo daga Dukku zuciyarsa duk ba daɗi. Ganin yanda gaba ɗaya dangin suka tashi hankalinsu ne yasanya wani tunani ya faɗowa Ahmad, nan yaƙira Ya Ameenu yasanar masa cewa, lokacin da Zaleeha zata tafi, tabbas yaga Zaheera tazo a napep inda ta bata wani abu a jaka, sannan ita Zaleehan tatafi, ita kuwa Zaheera ta shiga napep din daya kawota, saboda haka atambayi Zahira ko tasan inda Zaleehan taje. Habawa ae Ya Ameenu kaman kububuwa haka yaji ransa ya ɓaci, atake ya gayawa Baba Malam, nan Baba Malam yace da Zakariyya wanda tun safe yake gidan, cewa yaje ya ƙira masa Zahira, Zakariyya na zuwa ƙiranta, Mama ta buga tsalle inda ta kama hannun Zahira, tare da cewa tare zasu je, nan Mama tace da Zahiran ko kasheta zasuyi, kada ta sake tafaɗi inda Zaleeha take, dayake Zahiran ma zuciyar arna gareta, take ta kafe kan cewa bazata faɗa ba. Atare suka shiga falon ita da Mama, cikin zafin nama Ya Ameenu ya damƙo Zahira, wani lafiyayyen mari ya sauƙe mata akan fuskarta, take tafasa wani uban ƙara, tare da buga tsalle tasoma yayyarfa hannuwanta, cikin zafin zuciya yace. "Ina Zaleeeha ta tafi?." Bata iya basa amasa ba saboda marin ya matuƙar gigitata. Cikin fushi haɗi da ɓacin rai Mama tace. "Maganar banza ma kenan, wannan ai kora kunya da hauka kuke ƙoƙarin yi min, ku da kanku kuka salwantar min da rayuwar ƴata, sannan yanzu kuzo kuna tambayan Zahira, wallahi Ameenu kakiyaye ni kada kasake ka ƙara kai hannunka jikin Zahira tam!!." Mama tafaɗa ranta amatuƙar ɓace, zuciyarta kuwa cike da fargaban kada zafin mari yasa Zahira faɗin gaskiyan inda Zaleeha take. Ran Baba Malam a ɓace ya dakawa Mama tsawa, cikin faɗa yace. "Ina ki ka kai Zaleeha?." Afusace Mama tace. "Bansan inda takeba!!." Cikin ɓacin rai Baba Malam yace. "Na baki nanda kafun gari ya waye, duk inda Zaleeha tashiga ki tabbatar kin dawo da ita ɗakin mijinta, idan kuwa ba haka ba, ki tattara komai naki kibarmin gidana, kuma sannan idan kin tashi tafiya ki haɗa da Zahira karkiyi kuskuren barmin ita agidana, don bana ƙaunar zama da munafuki!, kada ki manta koki ƙira Zaleeha ta dawo ko kuma kibarmin gidana ayu basai gobe ba!!!." Yana gama faɗin haka ya wuce ɗakinsa, amatuƙar fusace. Wani irin masifeffen tsorone ya rufe Mama kadafa Baba Malam ya saketa ta koma ƙauyensu noma, wani sashin na zuciyarta kuwa zugar ruda ce ta ratsota haka yasa ta ɗan ja tsaki tare da kamo hannun Zahira, cikin ɓacin rai tace. "Mu tafi ai nima inada gidan uba, saboda haka kwana ɗaya bazamu ƙara ba, Zaleeha ne kuma bamusan inda take ba, kuma ko sama da ƙasa zasu haɗe, aurenta da nakasashshen gurgu ya ƙare kenan har gaban abadan." Littafina na kuɗine in kin gashi a wojema na satane. Turo katin Mtn na ɗari 300 kacal ta wannan number 09097853276 ko ka/koyi min transfer ta asusuna na 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa kana ki turo min shaidar biyan ki.    By *GARKUWAR FULANI* [05/09, 2:47 pm] +234 803 815 3437: Hannun Zahira Mama ta kama, cikin fushi haɗi da ƙunan zuciya ta fita daga cikin falon, tabbas ita kam ta gwammacewa tafiya, da dai ta barin Zaleeha ta cigaba da zama da Saifuddeen, cikin ranta take cewa. "Miye agidan naka banda baƙin ciki, da kuma tursasa mutum dole, dan mun bar gidanka, ae ba rayuwarmu muka bari ba." Nan tasanya Zahira ta haɗa kayanta, itama duk wani abubuwan buƙata nata ta haɗa, Zahira kuwa ganin dagaske tafiya zasuyi yasa, ta fashe da kuka, cikin fargaba haɗi da tsoro, tace. "Banason tafiya Mama, banason yin nesa da gida, bani da wani waje wanda yafimin gida, kinsan banason ƙauye, nikam wallahi zanje na bawa Baba Malam haƙuri, bazan iya tafiya nabar gida ba..." Wani wawan tsawa Mama ta daka mata, cikin takaici haɗi da ɓacin rai tace. "Zakimin shiru ne ko sai na kakkaryaki, banza wacce bata kishin mahaifiyarta da ƴan uwanta, ko anfaɗa miki nan ɗin aljannar duniya ce, da har idan muka barsa zamu tagayyara, to kiji da kyau, kamar yanda yace baya buƙatarmu, muma haka bama buƙatar kowa dake cikin gidan." Haka Mama taja hannun Zahira, suka fita, kuka sosai Zahira keyi, har cikin ranta batason barin gida da kuma ƴan uwanta. Suna fita Mama ta tara musu mai napep, nan tace. "Ya kaisu bakin tashar Gombe line". Inda ananne zasu samu motar da zata kaisu Ɓilliri. Suna zuwa kuwa suka samu mota, dama mutum biyu rak, ya rage motar ta tashi, suna shiga kuwa, aka kama hanyar Ɓilliri dasu. Can gidan su Saifuddeen kuwa, har yanzu hankalin su Ummee atashe yake, sosai ɓatan Zaleehan ya jijjiga zuƙatansu, don ɓatan mutum ba abun wasa bane,  gaba ɗaya farin ciki da walwalan gidan ya ƙaura, damuwa ne yacika zuciyoyinsu, sam Saifuddeen kuwa ya ƙi aminta wajen sanyawa zuciyarsa damuwa, gashi kuma ko kaɗan baison ganin Umminsa cikin wani hali. Haka ya Ameenu da Habu haɗi da Ahmad suka zama basu da wani aiki sai neman Zaleeha'n, duk wani waje dasuke tunanin zata iya zuwa, harma da wanda basa tunani saida sukaje. , inda yazamana kullum sai sun fita nemanta. Acan Numan kuwa, tunda Zaleeha tazo, babu abun dake fitar da ita, aɗakin sai Alwala, don dama da butar ta tazo, saboda tasan bazata taɓa samun buta awajensu ba, daga kan sallaya Qur'an sharbi,  babu abun da ta bari, wanda tasan dole zata buƙacesu,  koda dare yayi, haka Elizabet ta kawo mata, tuwo miyar shuwaka, sam bata ko kalli abincin ba, don kuwa batasa aranta cewa zata ci ba, kwanciya tayi tare da jawo jakarta, sweet ta ɓare inda ta jefa abakinta,  wayarta da ta cika da charge ta ɗauka, nan ta kunna data'nta, kai tsaye Instagram ta shiga, nan ta tarar da saƙon fans ɗinta, kala-kala, babu ɗaya da ta bawa amsa, haka tashiga duba hotuna, wanda su suka ɗebe mata kewa, gajiya da Instagram ɗinne, yasa ta faɗa Youtube, nan tayi downloading wani series film ɗin da tasaba gani kwanakin baya, wato Money Heist,  kallo ne ya taimaka inda ya rage mata kaɗaicin da take ciki, ahaka har bacci ɓarawo ya ɗauketa. Abuja Nigeria. Duk da kasancewar dare ya raba, amma duk yanda taso bacci ya ɗauketa abun ya ci tura,  sosai takejin tarin damuwa acikin zuciyarta, hawayen da suka cika idanunta ne suka samu daman gangarowa kan fuskarta, ahankali takai hannunta kan fuskarta ta inda ta share hawayen,  ganinta ta ƙara mayarwa ga screen ɗin wayar ta, wanda ke riƙe ahanunta,  hoton kyakkyawar fuskarsa ne bayyane akan fuskar wayar,  sosai yayi kyau cikin shigar ƙananan kaya dake jikinsa, wanda rigane da wando, masu kalan pink yasanya a jikinsa, sun kuwa matuƙar amsar jikin nasa,  idanunta ta lumshe tare da sauƙe ajiyar zuciya tana mai jin kishi da jin tsanar matar daya auran, har zuwa yau takasa ciresa aranta, ba tasan wani irin so ne takeyi masa ba, domin kuwa har wani zafi takeji azuciyarta, aduk sanda ta tuna da cewar yana da mata, taso zama wani ɓangare na rayuwarsa, amma burinta bai cika ba, sai dai tasa aranta cewa idan da rai to da rabo,  idan tana da rabon raɓan jikinsa, watarana zata zamo matarsa, wani ɗan guntun murmushi ne ya bayyana akan ƴar kyakkyawar fuskarta, wata zuciyarta ce tace da'ita. "Ameena ba kyaji, shin bayan Saifuddeen babu wasu mazan ne aduniya?." Sake faɗaɗa murmushin dake kan fuskarta tayi, ahankali tace. "Bayan shi akwai wasu maza masu tarin yawa, saidai shiɗin na musammanne,  irinsa guda ɗaya ne, acikin maza, bayanshi babu waninsa, wannan dalilin shiyasa nake matsanancin so da kishinsa wata can ta malliki abinda duk nake bege da so daga gareshi." a bayyane tayi maganar, domin gaba ɗaya ta faɗa cikin shauƙin ƙaunarsa, aranta ji take inama inama, da ace Saifuddeen zai zama mallakinta, to tabbas da sai tafi kowa murna da kuma farin ciki, duk da cewar tasan shiɗin ya girmewa ajinta, amma ba laifi itama ta yarda da kanta, don kuwa babu laifi, tasan  tana da nata kyau'n, domin Allah yayi mata sura, ɗan dadai haɗi da kyaun fuska, duk da kasancewar kai tsaye baza'a ƙirata da sunan kyakkyawar gaske ba, da ka nutsa da kallonta sosai kuwa, to  anan ne zaka fahimci irin nata sirrin kyaun,  domin kuwa sam ba baƙa bace, haka zalika bata kasance fara ba, saidai tana da kala mai kyau, domin  takasance tana da  brown skin mai kyau musamman dayake tana ɗan ƙara farin da mai, sannan afuskarta tana da ɗan madaidaicin hanci, mai ɗan tsawo kaɗan kuma karan hancin ba sosaiba, sai kuma ƴan saffa-saffan idanunta, masu ƴan siraran gashi a samansu, babu laifi domin tana da ɗan gashin gira iya dai-dai gwargwado,   sannan bakinta ma bashi da wani girma sosai, daga ɓangaren gashin kai kuwa, tana dashi dai-dai misali amman baida laushi, , kuma shima bashi da tsawo sosai. A taƙaice dai Ameena itama kyakkyawar mace ce, amma kuma ko kusa bata tako Zaleeha akyau ba, balle kuma aje ga uban gayyan wato Handsome guy ɗin Saifuddeen kenan. Don kuwa har yanzu da mutane sun kasa tantance tsakanin shida Zaleeha wa yafi wani kyau, sai-dai  idan za'a misalta tsananin kyawun  da Zaleeha'n, ke dashi,  koda  zata ɗarasa kyau ma ƙaɗan ne, domin kasancewarta mace, dole tsarin halittarsu ya banbanta. Gyara kwanciyarta tayi tare da jawo pillow tayi hugging ɗinsa,  cikin zuciyarta tace. "Ya Allah Ina roƙonka ka cigaba da zama gatana ako da yaushe,  Ya Allah Ka mallakamin Saifuddeen, amatsayin mijina, Ya Allah Kadubi zuciyata!." Ajiyar zuciya ta sauƙe, tare da ɗaukan wayarta ta manna a ƙirjinta, hakanan takejin wani irin nishaɗi acikin ranta. Da tarin tunaninsa a haka bacci ɓarawo ya ɗauketa. GOMBE NIGERIA Abubuwa da yawa sunata wakana acikin garin Gombe, inda gaba ɗaya yakasance a tsakanin gidan su Saifuddeen da kuma nasu Zaleeha, sam babu kwanciyar hankali, don kuwa yau kimanin kwana bakwai kenan da ɓatan Zaleeha, amma shiru har yanzu babu wani labari, wayoyinta kuwa har zuwa yau suna shiga, amma abu ɗaya ne har yau, shine bata ɗaukan ƙiran kowa, saƙonnin text message kuwa na ban tsoro da gargaɗi, akan duk inda take ta dawo gida, babu kalan wanda Ya Ameenu da kuma Ya Habu basu tura mata ba, amma Zaleeha da ta gani ko bin takansu batayi. Messages ɗin Ya Ahmad kuwa sunfi 20 wanda da ya tura mata, wanda suke cike da tsantsar lallashi haɗi da ban-baki yake bata, tare dayi mata al'ƙawarurruka da dama akan idan ta dawo zai yi mata, ba irin al'ƙawarin da baiyi mata ba, har cewa yayi da ita. "Pleess Zaleeha ki dawo gida hankali kowa ya tashi sabida rashinki, wlh idan kika amince kika dawo gida, to zan sa araba aurenki da Saifuddeen, sannan kuma zan ɗaukeki mu koma Abuja, zan sama maki aiki acan." Koda ta karanta murmushi kawai tayi, sanin cewa hakan abune mai wahala, domin tasan cewa Yayan nata bashi da wani abun da yakeso, sai wanda Baba Malam yakeso, farin cikin Baba Malam shine nasa, tasan cewa bazai taɓa iya raba auren ta da Saifuddeen ba, domin yin hakan zaisa ya faɗa cikin fushin Baba Malam, wanda tasan da Ya Ahmad ɗin  da ya faɗa cikin fushin Baba Malam, tasan zai gwammace gwara mutuwarsa. Haka koda ta karanta text ɗin, ta watsar tare da gogewa, don kuwa sun cika mata inbox da saƙonninsu, ita harma ta gaji a can ƙasan zuciyanta kuwa ji take kamar taita kuka. Ɓangaren Ya Habu kuwa, yau yagama shirinsa tsab, inda ya ƙudurta aransa cewa, yau zai je Doho, wajen Yayar mahaifiyar tasu, wato Aunty Ruda, domin ransa amatuƙar ɓace yake da ita, saboda yasan cewa, duk wani abu da maman tasu keyi, da sanya hannunta, kasancewar kowa yasan cewa, ita ɗince ke zugata  akan wasu abubuwa itace ke gurɓata komai na Mamansu. Ya Ameenu kuwa yanzu damuwar rashin lafiyar matarsa ne ya damesa, don kuwa tun randa Zaleeha ta gudu, Maryam ta kwanta zazzaɓi da ciwon kai, kasancewar bata da wani aiki kullum sai kuka, sosai ɓatan ƴar uwartata ya shiga jikinta, gefe guda kuwa ga Baba Malam daya shiga halin baƙin ciki,  kowa ya gansa yasan da cewa yana cikin damuwa,  kasancewarsu Yara masu biyayya hakan yasa basa ƙaunar ganin damuwar mahifinsu, uwa uba ga Mama da ta bar gidan, wannan abu na damun Maryam sosai, ganin lokaci ɗaya zuri'arsu naneman watsewa komai ba daɗi ga ɓatan ƴar uwa ga saɓani tsakanin iyayenta ga ɓacin ran mahaifinta damuwa dai ta taru ta cika zuciyar baiwar Allah. Ƙarfe 10 na safiyar ranan dai-dai Ya Habu ya kama hanyar zuwa Doho. Zaune yake akan wheelchair ɗinsa mai kalan silver gold,  sanye yake da wani army jeans, sai kuma wata farar long sleeve wanda ya nannaɗe hannun rigar zuwa guiwar hannunsa, aƙafansa kuwa, wasu fararen  bedroom slippers ne masu kyau,  kamar koda yaushe laptop ɗinsa ne, ɗaure akan cinyarsa, sosai ya bata hankalinsa gurin binciken da yakeyi. Gefensa Ummi ne wanda tayi jigum, duk damuwan ɓatan Zaleeha ya isheta, kusa da ita kuwa Hayatuddeen ne zaune yana ta faman latsa wayarsa, inda ya ɗan kaucewa ganin idanunsu ya matsa can gefe, chatting yake sosai, da wani sabon abokinsa da yayi acikin G.S.U, wanda yakasance department ɗinsu ɗaya, sunan abokin nasa Khamis, sosai Hayatuddeen yasoma shaƙuwa da Khamis, wanda yake kuma Khamis, yaro ne wanda bayajin magana sam, babansa mai kuɗin gaske ne, gidansu yana nan cikin New G.R.A, gaba ɗaya Khamis asangarce yake, kasancewarsa shine  ɗa namiji agidansu, hakan yasa gaba ɗaya iyayensa suka sakar masa yarda, tare da bashi daman yin duk abun da yake so,  shikuwa Khamis tun da yaga Hayatuddeen, yaji cewar yana sonsa da abota, kasancewar Hayatuddeen ba laifi yana shiga mai kyau da burgewa, sannan yana ɗan chilling ɗinsa, da sabuwar iphone ɗinsa,  makaranta kuwa kaisa ake amotar gida sannan driver ya ɗauko sa, shikuwa Khamis jibgegiyar motace ahannunsa,  hakan yasa ko zaman school ɗin bayayi, da yazo sai yawo kawai, kamar da wasa kuma suka fara abota da Hayatuddeen wanda gashi kuma zuwa ayanzun abotan nasu ya soma ƙarfi. Ajiyar zuciya mai ƙarfi ya sauƙe tare da lumshe kyawawan idanunsa, buguun zuciyarsa ne ya ɗan sassauta ahankali, hannunsa yasanya inda ya kama ƙasan haɓarsa, numfashi ya sauƙe, tare da fesar da wani irin iska mai zafi ta bakinsa,  *"NUMAN"* shine abun daya faɗa acikin zuciyarsa, sake duba inda location ɗin  ya tsaya,  kansa yajinjina tare da ɗan cije laɓɓansa, tabbas tana can Adamawa cikin Numan domin kuwa, haka sakamakon tracker ɗin da yayi ya nuna mishi. Ɗan jim yayi tare da lumshe idanunsa,  "Tabbas tana can Numan, amma kuma waye nata acan, da zata je ta zauna?." Tambayar da yayiwa kansa kenan, sanin cewa bashi da amsa yasa shi, sakin ɗan guntun murmushi,  wato da zama dashi ne ta gwammace rayuwa a wancan ƙauyen mai cike da yawan ƙabilu arnataku, hmmmm shikuwa zai zuba mata ido ya gani, bakuma zai faɗawa kowa inda take ba, sannan zaiyi duk yanda zaiyi wajen ganin, ya cire Umminsa adamuwa, dan tasanya ɓatan Zaleeha'n, sosai acikin ranta. Ta gigita mishi ƴan uwa da abokai gaba ɗaya, Ishaq Salisu Warisu Mudassir Aziz hatta Saminu Hishsm, Jabeer, da baya garin duk ta tashi hankalin kowa. Yasan ko ahaka Allah bazai bar Zaleeha ta zauna cikin farin ciki ba, saboda yasan ta ɗauki al'hakin iyayenta, sannan ga igiyar aurensa dake kanta, wanda take ta walagigi dashi. Wheelchair ɗinsa ya danna inda ya ƙarasa har gaban Umminsa, hannunsa ya ɗaura akan na Ummi'n, cikin kulawa ya karyar da kansa, tare da ɗan marairaice fuska, anutse yayi mata alama, cikin body language cewa. "Ta daina sa kanta adamuwa, Zaleehan zata dawo nan bada jimawa ba." Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe, cikin rauni ta dubeshi, murya asanyaye tace. "Banajin daɗi Saifuddeen, idan na tuna da cewar sanadiyar aurenka Zaleeha ta gwammace barin iyayenta, yayunta, ƙannenta, aikinta, mahaifanta, da duka danginta, wannan abun shine abun danake ta gudu tun farko, shiyasa naso afasa auren,  gashi yanzu an nemeta an rasa, babban tashin hankalina ma, shine bamu da tabbacin cewa ko lafiya take!." Kansa ya girgizawa Ummin nasa, tare dayi mata alaman cewa. "Zaleehan tana nan lafiya ƙalau aduk inda take." Kai kawai Ummi ta jinjina masa don bata iya cewa komai. Can Doho kuwa, Ya Habu na isa gidan Aunty Ruda yayiwa tsinke,  Aunty Ruda na ganinsa ta taɓe baki, don tasan tatsuniyar gizo bata wuce ta ƙoƙi,  first abun da Ya Habu ya fara tambayarta shine. "Ina suka kai Zaleeha?." Shewa tayi tare da cewa. "Ae baku bani ajiyan Zaleeha ba, balle kuce zaku zo nemanta, abu mafi sauƙi ku shiga uwa duniya ku nemeta kawai, tun da kune kuka salwantar da rayuwarta." Wannan abun shiya ƙara harzuƙa Ya Habu, nan take ransa ya ƙara baci, haka yayiwa Aunty Ruda'n tas, inda ya wanketa soso da sabulu, ya ɗora da cewar. "Ita ke zuga mamansu akan komai, kuma wallahi su fito da Zaleeha, duk ma inda suka kaita suka ɓoyeta, kuma ta daina zuga musu uwa tana tura mata halinsu na arna ya ƙara da cewa kada tayi zaton basu gane ita ke zuga Mamaba." Haka yabaro Doho'n ransa amatuƙar ɓace, domin yasan da cewa sunsan inda Zaleehan take faɗa ne kawai bazasuyi ba. Bayan kwana 5 da dawowan Ya Habu daga Doho, Baba Malam ya kwanta rashin lafiya, inda ciwon hawan jininsa ne ya tashi,  nanfa gaba ɗaya ahalin suka sake shiga cikin tashin hankali, ga jikin Maryam ma da yaƙi daɗi, bata da wani zance saina ƙanwarta Zaleeha. Saifuddeen dake zaune afalon Ummi ne, ya kwantar da kansa ajikin kujera,  yanzu labarin rashin lafiyar Baba Malam ya iskesa, hakanne yasa yaji babu daɗi acikin ransa, sam ada baiyi niyar faɗawa kowa inda Zaleehan take ba, yaso barinta ne idan tagaji don kanta zata dawo, amma ayanzu yazama dole ya faɗa, kodan saboda rashin lafiyar Baba Malam ɗin ma. Computer ɗinsa ya ɗauka, inda yayi rubutu mai ɗan tsawo, sannan ya nunawa Ahmad,  bai jirayi Ahmad yagama karanta saƙon ba, ya ciro wayarsa inda ya turawa Ya Ameenu saƙo,  wanda ya rubutashi ataƙaice. Ahmad nagama karanta saƙon ya ɗago ya dubi Saifuddeen, kai Saifuddeen ɗin ya jinjina masa, ajiyar zuciya Ahmad ɗin ya sauƙe, nan yakai dubansa ga Ummi, sai kuma Adda Rahama dake zaune, cikin nutsuwa Ahmad yace. "Ummi Saifuddeen ya ganno inda Zaleeha take fa." cikin mamaki Ummi tace. "Ta ina? Tana ina? ko wani abune ya sameta?." Kai Ahmad ya girgiza, cikin nutsuwa yace. "Uhmmm Ummi kenan wato dai kuna ganin kaman Zaleeha ɓata tayi ko, hmmm to wlh Zaleeha ba ɓata tayi ba, guduwa tayi da ƙafafunta, sannan yanzu haka tana can Numan, halan akwai wasu ɓoyayyun ƴan uwanta acanne, wanda tunanin su Ya Ameenu da Habu baije can ba, amma dai yanzu Saifuddeen ya faɗawa Ya Ameenu'n." Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe tare dayin hamdala acikin ranta, tabbas ta ɗanji sanyi acikin ranta,don dama ɓatan Zaleehan yayi mata tsaye acikin rai, itakuwa Adda Rahma shiru tayi tana meyin wasu nazari,  hakanan Zaleehan ta soma sanewa acikin ranta, tabbas ita duk wani wanda baison Saifuddeen, to fa itama bata ƙaunarsa ko kaɗan. Raihana kuwa da dama can bata wani sake da Zaleeha a rantaba, sai taji ta fice mata a rai haushinta kawai takeji har ita waye da zatace bata son Hammanta me ya rasa dame sauran maza suka fishi haka dai taketa ƙunƙuninta. Ƙiran Ya Ameenu ne yashigo wayan Ahmad, da sauri Ahmad ya ɗaga wayan. Daga ɓangaren Ya Ameenu, wanda ke zaune acikin falon Baba Malam, kasancewar dukaninsu suna cikin falon, hakan yasashi sanya wayar a speeker,  yanda kowa zaiji, tambayar Ahmad yayi akan saƙon dayaga Saifuddeen ya turo masa, nan take Ahmad yayi masa bayanin dukkan abun da Saifuddeen ya faɗa masa, inda yace ta hanyar yin tracker Saifuddeen ɗin ya gano inda take. Nan take gaba ɗaya suka cika da mamaki, domin koda wasa basu taɓa zaton cewa zataje Numan ɗinba, saboda su kwata-kwata ma sun manta da cewa Mama tana da ɗan uwa acan, domin kuwa ba zuwa take ba, suma kuma ba zuwa suke ba. Ya Ameenu na kashe wayan, Baba Malam dake kishingiɗe yana shan fruit salad, ɗin da Mamy ta haɗa masa ya saki ɗan guntun murmushi irin nasu na manƴan dottijai murmushi mai cike da ma'anoni da manufa masu tarin yawa,   cikin baƙin ciki Ya Ameenu ya rusuna gaban Baba Malam ɗin cikin neman izini yace. "Kayi haƙuri Baba idan kayimin izini kabarni naje ayau ɗinnan na taho da ita gida." Ahankali Baba Malam ya aje bowl ɗin dake hannunsa kai ya jujjuya mishi alaman a a,  cikin kulawa ya dubi Ya Ahmad, wanda yayi jigum, anutse yace. "Ahmad ka ɗauki matarka gobe ku koma, banason zamanka hakanan, saboda haka ka koma bakin aikin ka." Cikin salon bada umarni wa yaran nashi ya kalli Habu dake jin tamkar yayi fiffige ya fire yaje Numan cikin haiba da kamala yace. "Kai kuma Habu nabaka izinin gobe kaje can Numan ɗin, badai kasan gidan yayan Mamar taku dake can ba?." Kai Ya Habu ya jinjina tare da cewa, "Eh." Ajiyar zuciya Baba Malam ya sauƙe tare da cewa. "To nayi maka izini kaje, duk wani abu dakasan na Saifuddeen ne wanda Zaleeha tatafi dashi ka ƙwatosa ka kawomin, sannan ka ɗauko masa kayayyakin aurensa wanda ta tafi dashi, amma kuma koda wasa kada kace zaka ɗauko ta, badai ta zaɓi guduwa da zaman can ba, shikenan kubarta ta zauna acan ɗin, da sannu duniya zata koya mata hankali, kadai ji abun dana faɗa maka ko?". Da sauri Habu ya gyaɗa kanshi alamun eh, shi kuwa Baba Malam a kausashe yace. "Bana buƙatar ta saboda haka koda wasa kada kayi kuskuren ɗauko min ita, kabarta acan, amma kaya dai dayake mallakin Saifuddeen kada kabar ko abu ɗaya awajenta." Cike da gamsuwa Ya Habu ya jinjina kansa don shima, zaifison abar Zaleeha'n, ta ɗana ƙunci da baƙin ciki data ɗana musu. Duban Ya Ameenu Baba Malam yayi cikin kulawa, ya dafa kafaɗunsa, kana yace. "Matarka bata da isashshen lafiya Ameenu, saboda haka ku koma gida kaje ka kula da ita, saboda tana buƙatar kulawanka, in sha Allah Maryam ƴar aljannace, domin takasance ƴa mai biyayya ga mahaifinta, haka kuma ga mijinta, tabbas Maryam ƴa ɗayace tamkar da dubu, sannan itaɗin mafi soyuwa ce agareni, saboda haka bazanso ace kayi mata nisa, ka ɗauketa ku koma gida kaji!." Cikin yanayin gamsuwa Ya Ameenu yace. "To." Gyara zama Baba Malam yayi, cikin nutsuwa yace. "Kudukan ku idan kuka sake sanya damuwar Zaleeha a cikin ranku, to tabbas zanyi fushi daku, haka ta zaɓa haka kuma take ganin yafi mata, saboda haka mu ƙyaleta, ita da kanta wata rana zata dawo, kutashi kuje kowa yayi sabgogin gabansa, ko da ita ko babu ita zamu rayu." Haka dukansu suka miƙe, inda Ya Ahmad gaba ɗaya jikinsa yayi sanyi, har acikin ransa yaso ace Baba Malam ya bari aɗauko Zaleeha'n, baiso ace an barta acan ba, duba da cewa ba'a cikin musulmai take ba, sannan basu san ma wani irin rayuwa takeyi acan ba. Su Ya Ahmad ɗin nafita, Mamy ta gyara zama cikin kwantar da murya, haɗi da tausasa zance tace. "Amma Malam kanaga barinta acan ɗin shine mafi alfanu?, da a so nane a ɗaukota, sai ayi mata koda nasiha ce, nasan gaba zata gyara." Murmushi Baba Malam yayi tare da girgiza kansa, bowl ɗin fruit salad ɗinsa ya jawo, cikin kulawa yace da Mamy. "Ina da babban dalilin dayasa nace abarta acan, duniya zata koya mata hankali." Shiru Mamy tayi tare da ɗan jingina bayanta, ta shiga nazari. Numan. Cikin kaɗaici haka take gudanar da rayuwarta anan Numan ɗin, sosai takejin ƙyaman mutanen da take tare dasu, domin kuwa a iya arean nasu Solomon gaba ki ɗayansu christan's ne babu musulmi ko guda ɗaya, sai ita da tashigo cikinsu ayanzu, wanda kuma ba daɗin rayuwa dasu takeji ba, tana dai zaunene acikinsu bisa dole, sau da yawa Solomon baya zaman gida, kusan koda yaushe yana gona cikin lamɓunshi na shuke-shuken kayan marmari danginsu ,Ayaba, Gwaiba, Dabino, Kwakwa, Lemun zaƙi dana tsami Kankana Abarba sweet milo Aya, Gyaɗa, ɗanyar Masara, Dankalin hausa dana turawa, rogo, tumatur attaruhu albasa da dai sauransu, wanda shine sana'arsa daya dogara da ita. Hakanne yasa basosai suka cika zama dashi ba, sabida babu salla babu salati ko yaushe yana can yana yiwa ƙasa aski don inƙanta al'barkatun gonar tasa, itakuwa matarsa Elizabet baƙin halinta ma ya isheta, wanda tun Zaleehan bata fahimta ba harta fara fahimta, hakanne yasa itama take ɗauke mata kai, Sai dai can gefen unguwar su Solomon akwai rugar Fulani masu mutunci da tsabta,da riƙo da addini sosai Zaleeha ta fara sabawa dasu, wanda kullum sukan kawo mata Nono da Zuma mai kyau da inƙanci wanda hakan yake matuƙar taimaka mata ta samu abin sawa a bakin salati sai kuma ƴaƴan itatuwa da Solomon kan kawo mata. Yanzuma kwance take akan ƴar katifar da suka bata, gaba ɗaya batajin daɗin gidan, babban matsalan data fara fuskanta ma shine rashin samun ingantaccen wutan nepa, acan Gombe tasaba unguwarsu kwata kwata ba'a ɗauke musu wuta, koda kuwa ma an ɗauke tsanani bai wuce 5 minute andawo dashi, haka koda ta koma gidan su Saifuddeen ma kullum cikin wuta suke, amma tunda tazo nan saita kwana ta wuni bata ga idon wuta ba, kuma koda ma sun kawota bai wuce mintuna 50 sun ɗauketa, ita da ta saba kwana cikin sanyin AC kan makeken gado na alfarma, da tattausan blanket masu taushin gaske amma sai gashi yanzu kusan kullum dare cikin zafi take kwana, hakanne yasa gaba ɗaya takejin komai bayayi mata daɗi, gashi wayarta ayanzu bata samun wadataccen caji, wani lokaci ma tanason shiga yanar gizo don ɗebe kewa, amma rashin ƙarfin network haka yake hanata, dolenta haka zatayi jigum tayi shiru, yanzuma kwanciyar da takeyi ne ya isheta, hakan yasa ta miƙe tsaye, wani ƙaton hijabinta ta ɗauka ta zura daga kanta zuwa idon sawunta dan tasan akwai igiyar aure a kanta wani flat shoe ɗinta ta zura, sannan tafito daga cikin ɗakin. Babu kowa atsakar gidan, hakan yasa kai tsaye tanufi hanyar fita daga gidan. Tsayawa tayi daga ɗan nesa tana me hango wani wutsinyan tafkeken kogi Numan, wanda ruwan cikinsa ke gudana da ikon Allah, sosai sanyin wajen ke shiga jikinta, kasancewar da yammaci ne, ahankali ta ƙarasa kusa da kogin, zama tayi akan yashin dake shimfiɗe awajen tare da zura ƙafafunta cikin ruwan, idanunta ta lumshe tare da sauƙe ajiyar zuciya. Wani sabon shauƙin ƙaunarsa, wanda ke kwance a ƙasan zuciyarta ne ya taso mata, aduk tsawon kwanakin nan koda sau ɗaya ne soyayya da kewarsa, basu ragu acikin zuciyarta ba, kullum da soyayyarsa take kwana take kuma tashi, har yau bata fidda ran cewa watarana zai zo gareta ba, duk kwanan duniya soyayyarsa ƙara ninkuwa take acikin zuciyarta, zuwa yanzu kewa da muradinsa ya zamo wani sinadari na cikin rayuwarta, tajima awajen, ganin magriba ta gabato ne yasa, ta tashi inda ta koma cikin gida, a bakin fonfonsu ta tsaya ta buɗe ruwa mai tsabta, wanda dashi tayi alwala, ɗaki ta koma, koda tayi sallan Magriba, bata tashi akan sallayan ba, har saida ta sallame sallan isha. Haka nan take jin tausayin Baba Malam na cika mata can ƙasan zuciya, ji takeyi kamar tayi fiffige ta fire ta ganta gabanshi amman bazata iyaba ta rasa meyasa ta kasa yiwa mahaifinta biyayya. A wani yanki na zuciyarta kuwa, tana yawan tuno Ummi dasu Hayatuddeen da Raliya, musamman uban gayyan taken haɗe fuska taja tsaki duk sanda ya faɗo mata a rai. Yanzunma hakance ta kasance wani ɗan gajeren tsaki taja, tuno yadda ya rinƙa tsotse mata sweet lips ɗinta, ido ta rumtse da ƙarfi tare da cewa. "Hmmmm gwarafa dana gudu, in na tsaya wannan zalamemmen zaimin sagegeduwa, mugu duk ya lallatseni caɓɓullena,wannan in na zauna sai ya maida min nono kamar biredi ko bolon-bolon da mutumtaka ya rinƙa wani shana, mugu kawai mai idanun jaraba." a hankali ta miƙo hannunta ta jawon hand bang ɗinta wanda a ciki aka sa mata kuɗin fansan idonta da rafan sadakinta wanda Baba Malam ya damƙa mata lokacin da za'a kaita gidan wancan jarabebben. zazzage jakarta tayi gaba ɗaya kuɗin ta zubesu kan sallayar, cikin mmakin yawan kuɗin ta fara haɗe kansu, ta daɗe sosai kafin ta gama kana ta irgasu, cikin mmki tace. "Kai har dubu ɗari huɗu da talatin." Taɓe baki tayi tare da cewa. "Uhmmm kasa abokanka da ƴan uwanka zubda kuɗaɗensu a banza, ni ɗinnan dai nan gani nan bari sadakin agalawa yaseen cinye kuɗin sada kinka zanyi kuma budurcina nan gani nan bura awaran mayya ga yaji ga albasa kuma babu damar ci." Ƙasan pillow tasa ƙuɗin sabida baccin daya fara fin ƙarfinta. Daga nan kuma kwanciya tayi, domin yau ɗin da wuri taji bacci naneman ɗaukarta. Washegari. Gombe State. Tun da sanyin safiya Ya Habu ya gama kimtsawa, inda ƙarfe 7 na safiya atasha tayi masa, kasancewar a motar haya zai tafi, saboda idan yaje can ɗin, har motar da Zaleehan ta tafi dashi zai ɗauko, domin kuwa Saifuddeen ne yasaya motar, tunda ta rufe ido ta gwada cewa bata ƙaunarsa kuwa, to bazasu taɓa bar mata komai nasa awajenta, wanda yake shiya saya mata ba. Zaman ɗaki daya isheta ne yasanyata fitowa, kan wani benci dake aje a tsakar gidan ta zauna, wayarta ta ɗauka inda ta shiga latsawa, zuwa yanzu tagaji da ɗurawa cikinta kayan zaƙi, dangin su chocolate da biscuit, da ƴaƴan itatuwan kasancewar su suka zame mata abinci, duk da gidan fulanin nan suna yawan kawo mata abinci kuma Alhamdulilla ta yarda da tsabtansu kana sun iya girki sosai gata dama tana son man shanu. Ɓangaren Ya Habu kuwa, lafiya ya samu isowa cikin garin Numan, kai tsaye bakin kogi ya nufa, wato gidan Yayan Maman nasu, cikin sa'a, kuwa yana kaiwa kusa dagidan, yayi kiciɓus da Unlce ɗin nasu, fuska ɗauke da mamaki solomon ya tarbi Habu, gaisawa sukayi inda Ya habu yayi masa bayanin abun daya kawosa, sosai Solomon yasha mamakin yanda akayi suka san da cewa, Zaleehan na wajensa, don kuwa Mama tafaɗa masa cewa babu wanda yasan Zaleehan na wajensa, domin cewa dashi tayi ya ɓoye mata Zaleeha'n, ganin cewa sun gano cewar tana wajensa ne yasanya sa jin cewa bashida zaɓi, wanda ya wuce barin Habun ya gana da ita. Shine agaba yayinda habu ke binsa abaya, haka suka shiga cikin gidan. Zaleeha dake zaune atsakar gidan, jin motsin shigowar mutum cikin gidanne, yasa Zaleeha ɗago kanta, wani irin faɗuwar gaba ne da matsanaicin tsoroya ne risketa, azabure ta miƙe daga zaunen da take, tare da sanya hannu ta dafe ƙirjinta, hakan yafarune sakamakon ganin Ya Habu da tayi. Wani irin mugun harara mai cike da tsana Ya Habu ya watsa mata, tare da ɗaure fuskarsa ta mau. Ganin haka yasa ta sadda kanta ƙasa, sosai ƙirjinta ke bugawa, wani irin masifaffen tsoro haɗi da fargaba ne, suka cika zuciyarta, sosai tacika da mamakin ganin Ya Habun, don sam bata taɓa zaton cewa zasu san inda take ba, kujera Ya Habu yaja ya zauna, sake haɗe fuska yayi, tare da watsa mata harara, murya adake yace. "Ba zama nazo yi ba, maza kishiga ciki, duk wani abu da kikasan mallakin Saifuddeen ne, ki fitomin dashi, idan ba haka ba kuma na tattakaki awajen nan!." Saida cikinta ya bada wani sautin ƙuuu, domin kuwa tsawan da ya daka mata bana wasa bane. Da sauri ta juya inda tashiga cikin ɗakin, jikinta na rawa da tsuma, zamewa tayi ta zauna daɓas aƙasa, sam takasa koda kyakkyawan motsine, tsoro takeji sosai, hakanan zuciyarta ya shiga, bugun no stop, hannu tasa ta dafe dai-dai saitin ƙirjinta, dake bugawa sabida a fili ta hango tsanarta a idanun ɗan uwan nata. Shiru-shiru Ya Habu dake jiranta, yaga har yanzun bata fito ba, hakanne yasa shi fusata nan ya kutsa kansa cikin ɗakin, ganinta azaune ya sashi buga tsaki, nan ya shiga wargaza gaba ɗaya kayanta, iya abunda ya sani wanda akayi mata na gidane kawai ya barmata gaba ɗaya akwatunan da tazo dasu ya buɗe, wanda ke cike da sabin kaya, nan yaja akwatunan ya rufe, duk wani abu dayasan sabo ne wanda yake da kuɗin Saifuddeen aka saya saida ya tattare ya fiddasu tsakar gida, dubanta yayi cikin tsawa yace. "Bani makullin motar Saifuddeen wanda kika taho dashi, banza marar kunya, wanda batasan darajar kanta dana iyayen ta ba hegiya mai fuskar yahudu da nasara bakya son mutun amman kina son kayanshi." Kanta ta sadda ƙasa, lokaci ɗaya taji hawaye sun cika idanunta, tsawa ya sake buga mata tare da cewa. "Zaki bani ne ko kuma saina rabaki gida biyu!!!." Azabure tatashi inda ta ƙarasa wajen da ta aje makullin motar, da sauri ya sunkuyo ganin harda ATM ɗinta a wurin gaba ɗaya ya kwashe komai haka ya dinga jidon kayan yana sawa a motar, saida ya rabata da fiye da rabin kayan da tazo dashi gaba ɗaya, akwai sabuwar laptop ɗinta ƙiran companyn apple daya gani awajenta, shima saida ya ƙwace. Saida ya gama kwashe komai sannan ya dubeta, cikin takaicinta yace. "Kinzaɓi barin ƴan uwa da mahaifanki, akan wani banzan dalili naki wanda bashi da ƙarfi ko, good kamar yanda kika gudu da ƙafafunki, kika kuma tozarta Baba Malam, bazamu taɓa buƙatarki ba, duniya ce ae kuma gaki acikinta, saboda haka kisha zamanki ki huta cikin arnatakun, babu wani wanda zai sake nemanki, haka babu wani wanda zaizo gareki da sunan maidaki gida, in kin ga dama ki riƙe Allah da addininki in kuma kinga dama ki koma zuwa coci da cin aladu da karnuku tunda baki godewa Allah da ni'imar da ya mikiba!." Yana gama faɗan haka, ya juya yafice daga cikin gidan, motar ya shiga inda yayiwa Uncle ɗin nasu bankwana, ko mintuna 4 bai ƙaraba yayiwa motar key tare da barin ƙofar gidan. Kaitsaye ya ɗauki hanyar komawa cikin garin Gombe. Zaleeha kuwa ɗaki ta koma, inda ta faɗa kan gado, cusa kanta acikin pillow tayi tare da sakin kuka, wanda ita kanta batasan kukan na miye bane, hakanan takejin wani ƙunci acikin ranta, tabbas tanajin cewa tsanar Saifuddeen bazai taɓa gushewa acikin ranta ba, saboda duk asanadinsa tabar ƴan uwanta yayunta ƙannenta da mahaifanta, danginta aikinta har yanzu kuma tana kan bakanta na cewa bazata taɓa zama dashi ba. Kuka sosai tayi, sabida ya Habufa ya kwashe mata rabin jin daɗinta, tunowa da kuɗin data haɗa ta irga jiya da dareta ajiyesu ƙasan pillow'nta ne yasa tayi sauri tashi ta ɗaga pillow ganin suna nanne yasata jin sanyi a ranta, a fili tace. "Alhamdulilla Ya Habu mugu harda ɗaukanmin ATM to zanyi mgninka ai bari in samu caji zan yakeshe kuɗin kab in maidasu asusun Mama ko na Bilkeesu." abinda Zaleeha bata saniba tuni Habu yaje cikin numan ya yashe mata account. Dan ba wani abundan bai saniba na sirrin ƙannen nashi. Sai dare Ya Habu ya samu isowa garin na Gombe, nan ya damƙawa Baba Malam ɗan makullin motar, sannan ya nuna masa duk wani abu daya ɗauƙo, sosai Baba Malam yaji daɗin hakan, nan ya sallami Habu inda yace gobe da safe zai je har gidan su Saifuddeen ɗin. Washe gari kuwa da misalin ƙarge goma Baba Malam ya shirya tsab don zuwa gidan su Saifuddeen, bayan yasa Ya Habu yayi gaba da motar da suka amso awajen Zaleeha'n, Shida Ya Ameenu suka fita inda Ya Ameenun ne keyi musu driving, kai tsaye gidan Dirankaɗi suka nufa, wato gidansu Ishaq, kasancewar tun jiya Baba Malam ya ƙirasa sukai magana, akan hukuncin da ya yanke, koda yaje ɗaukan Dirankaɗi'n sukayi, nan suka nufo cikin federal low cost, wato unguwar su Saifuddeen, koda suka ƙaraso Ahmad ne yayi musu jagora har zuwa babban falon Ummi. Inda Ummi da Saifuddeen ke zaune. Cikin girmamawa haɗi da mutunta juna suka gaisa. gayara zama Baba Malam yayi inda yasake basu haƙuri akan abun daya faru, sosai ya basu haƙuri, hakanne yasa har Ummi saida taji kunyar haƙurin dayake ta basun. tace mishi ba komai komai ya faru yine na Allah. haka dai ya koma gida jiki a mace. Yau kusan sati uku kenan da guduwan Zaleeha, tunda aka gane inda take hankalin kowa ya konta. Amman banda Baba Malam yawanci yakan zauna yana nazarin me zaiyiwa Saifuddeen ya huce mishi baƙin cikin da ƴarsa ta cusa mishi, a cikin hakanne ya nazarto wani matakin da zai ɗauka. Saifuddeen kuwa gaba ɗaya hankalinshi na kan shige da ficen Dalla ne, dan yadda zai samu kamashi cikin laifi dumu-dumu, yayinda shima Dalla ya fahimci akwai mai bibiyarsa da bin diddiginshi, shiyasa ya sauya salo da tsarin fajircinshi dan ya sake barin gombe ma sabida ya gane ana gab da kamashi kuma binshi akeyi dan a samu kwakkwaran hujjar kamashi. Ummi kuwa tana yawan tuna Zaleeha dan ita kam har ga Allah tana son ƴarinyar, sabida ita dai bazata ce ga wani mugun abu ko raini data daɓa yi mataba cikin kwanakin da suka zauna tarenba, asalima ta fahimci yarince mai biyayya da tarbiya da iya zama da mutane. Hayatuddeen kuwa yaci gaba da zuwa makarantarshi sabonshi da Khamis yanata ƙaruwa. Amina kuwa da Asma'u har gobe suna dakon soyayyar Saifuddeen a ransu, A hankali ya gama kimtsa kanshi cikin wani tattausan yadi mai azabar kyau da taushi yadin farine ƙal-ƙal sai ɗigo-ɗigon bulu mai haske, an mishi ɗinkin mai kyau dai-dai da jikinsa an ɗan tattarfa surfanin bulu a aikin rigar, hular kanshi fara mai ratsin bulu, kana sai takalmansa sau ciki mai kalar bulu sai igiyansu daya kasance farare. Manyan idanunshi ya buɗe tare da kallon fuskarsa a madubin jikin durowar tashi, a hankali ya fidda sassanyan numfashi tare dasa tattausan tafin hannunshi ya shafa sajenshi da ya kwanta lib yayiwa fuskarsa ƙawanya, lips ɗinsa ya ɗan tsotsa tare da turosu gaba, wayarshi ya ɗauka ya da niyar zurata a aljihun gaban rigarshin sai yaga shigowar saƙo, Ganin Bappa Aline ya sashi buɗe saƙon. "Sallamu alaikum, Saifuddeen ka cewa Umminku yau ina kan hanya nida Malam Ashiru, dan surkinka yace yana buƙatarmu, to yanzuma muna tahowa, yace kuma zaizo har gidan ya samemu, to nayi ta kiran wayan Unminka bata shiga." Idanunshi ya ɗan lumshe tare da buɗesu a ranshi yace. "To wai meyasa Baba malam ya kasa kontar da hankalinshi ne a kan batun wannan fitinanniyar yariyar tasa, infa har yazo yau to zuwansa na uku kenan yana bamu haƙuri." Kai ya ɗan jujjuya kana ya rubutawa Bappa Ali amsa ya tura mishi. Daga nan ya zura wayar a al'jihunshi kana ya fice ya nufi side ɗin Ummi. Shiru falon ba kowa dan haka kai tsaye ya wuce bedroom ɗinta, kan sallaya ya sameta bisa dukkan alamu tayi walahane, shiru yayi yana kallon yadda ta ɗaga hannayenta sama tana kwaranyo musu addu'o'i shida ƙannenshi, wanda mafi yawan addu'ar a kanshi ne a hankali take cewa. "Ya Allah ga bawanka Saifuddeen cikin matsalolin rayuwar daka jarabceshi, ya Allah ina mai roƙa masa sassauci da salama da sauƙi a rayuwarshi ta duniya da lahira. Ya Allah ka yaye mishi duk wani cuta dake jikinshi ka bashi lfy ka ƙaddara mishi sake miƙewa saye da sawunshi da sake mgna da ji, Ya ubangijin talikai ka yassare masa ƙofofin samunshi gabas da yamma kudu da arewa, ya Allah ka al'barkaci kasuwancinsa ka tsare minshi daga sharrin mahassada damasharranta tsakanin mutun da al'jan, ya Allah ka tsare min imaninshi ka bashi ikon cinye jaraboɓunshi." Sai ta kuma ƙara ɗaga hannu cikin kushu'i da ƙanƙan da kai take cewa. "Ya Allah kayi mishi zaɓi mafi al'khairi tsakaninshi da matarsa Zaleeha in ita al'khairinsace Allah ka bashi haƙuri da juriyar duk wani abinda zai faru daga gareta, in kuma ita ba al'khairinshi bace, ya Allah ka musanya musu da abinda yake al'khairi a garesu baki ɗaya. Ya Allah ka karemin surkata a duk inda take." sosai Saifuddeen yake wani irin lallausan murmushi yayinda shima ya ɗaga hannayenshi sama yana mai amsa cikin ransa da . "Amin Amin. Ameen ya rabbil izzati ya Ummi." sosai ya tsura mata ido likacin da take cewa. "Ya Allahna ga ɗana Hayatuddeen cikin ganiyar ƙuriciya da tashen balaga ya Allah ka shirya minshi ka tsare minshi, da tarbiyarsa ka kare min imaninshi ka sa mishi nitsuwa da kamala kwatan-kwacin na ɗan uwanshi, ya Allah ka yaye mishi wannan rawan kan da gigin ƙuruciya". Sosai yake Murmushi Allah sarki Ummi wato rawan kan Hayatuddeen na tsoritata. numfashi ya sauƙe a hankali ganin tana cewa. "Ya Allah ka al'barkaci ahlina ka shirya minsu dama dukkan al'ummar musulmai ka azurta ɗiyata Raliya da samun haihu da ƴaƴa na gari ka basu zaman lfy da mazajensu." Haka dai tayi ta musu addu'a yana mai amsawa da amin. A tare suka shafa addu'an, kana ta juyo ta fuskanceshi da kyau cikin sakin fuska tace. "Dama kana gidane!." Kai ya jinjina mata tare da mata bayanin zuwan bappa Ali da Baba Malam, ya ƙara da cewa Bappa Ali yace sun tasoma dan haka zai jirasu kawai. kai ta gyaɗa tare da miƙewa ta cire hijabin jikinta tana mai ninkewa take cewa. "Eh lallai Faroq ya ɗauki wayar yana game to inaga ya gama da cajinta ne , dan naga yazo ya sata a cajin. jin haka ya ɗan juyo ya jawo wayar dake haɗe a caji nan kuwa ya samu a kashen take. juyawa yayi ya fito falon Ummi na biye dashi a baya tana gyara mayafin jikinta. Suna zama ba jimawa kuwa su Bappa Ali suka iso. suna cikin gaggaisawa ne Baba Malam da Malam Adam da Dirankadi suka iso bisa jagorancin Ahmad wanda yanzu ya dawo gida dan kiran bappa Ali daya samu. Falon shiru bayan duk sun gama gaggaisawa, A hankali Ummi ta miƙe da niyar basu wuri a matsayinsu na maza kuma manya su tattauna komai tsakaninsu, sai kuma ta koma ta zauna jin Baba Malam yana cewa. "Uhummm Ummin Saifuddeen zauna, akwai mgna mai mahimmancin da nake son muyi ne." shiru tayi cikin jin tausayin mutumin wato wannan shine ɗan kuka mai jawa uwarsa jifa." Duk shiru sukayi suna sauraranshi. Shi kuwa gyara zama yayi cikin nitsuwa da cikar kima yayi gyaran murya tare da cewa. "Da forko dai zan fara da baku haƙuri akan rashin ɗa'a da Zaleeha tayi mana baki ɗayanmu, wanda nake zargin kaina da cewa duk nine sila, tunda ku dai kun so'a janye batun auren tun kafin ayi auren, ni na kafe nace ayi sabida zatona itama irin Maryam ce in anyi auren zatayi biyayya ta zauna ɗakinta, amman sai gashi ta samu asarar lokaci da dukiya da mutuncina ta gudu ta watsar da auren." shiru yayi sabida yadda Bappa Ali ya fuskanceshi tare da cewa. "Dan Allah na roƙeka Malam Bashiru ka daina bamu haƙuri da ɗaurawa kanka wannan laifin, Wannan aurefa nufine na Allah, Allah ne ya ɗaura aurennan kafin mu muka ɗaurashi, kuma har gobe muna kyautata zaton zata dawo ɗakinta ta zauna." Malam Ashiru ne ya amshi zancen da cewa. "To mun isa muja da ikon Allah ne, babu laifin kowa a cikinmu, da Allah malam Bashiru ka daina tada hankalinka kam zancen yarannan." ita dai Ummi shiru kawai tayi, Saifuddeen da Ahmad shirun sukayi. Sai kuma Dirankadi da Malam Adam ne suka ƙara kwantarwa Baba Malam hankali kan dan Allah kada ya sake zuwa da batun badu haƙuri. Cikin jin sanyi a ranshi ya kallesu baki ɗaya kana ya fuskanci Saifuddeen da kyau cikin sanyi yace. "Dan Allah Saifuddeen ina neman wata al'farma a wurinka." da sauri Saifuddeen ya nuna kanshi da ƴar yatsarshi alamun. "Ni kuma al'farma kuma?." Kanshi gyaɗa mishi alamun eh kai ɗin dai. sai ya kuma gyara murya da zama kana ya kalli Ummi, Bappa Ali da kuma Malam Ashiru yace. "Ina neman al'farma a wurin ɗanku ɗalibani kuma surkina a wani sashin kuma ɗana. Dan Allah Saifuddeen kayi haƙuri akan duk wani abun da Zaleeha tayi maka daka riƙe igiyar aurenka da ita naroƙi al'farma a wurinka da iyayenka duk rintsi kada ka saki Zaleeha, lallai kam nasan saki halalne duk da ubagiji baya son shi, ina roƙonka da Allah da manzonsa kada kayiwa Zaleeha abinda take buru da son kayi mata ka riƙe igiyar aurenku duk rintsi, domin inada yaƙinnin wata rana zata dawo gareka." ya ƙarishe mgnar cikin rauni da alamun neman al'farma. Su kuwa gaba ɗaya idanu suka zubawa Saifuddeen daya fara musu bayani da yarensu na kurame wanda gaba ɗayansu suna gane hakan, A hankali ya matso gaban Baba Malam cikin tanƙwashe ƙafafu yace. "Baba Malam umarni zaka bani ba neman al'farma ba, in sha Allah bazan saki Zaleeha ba, ka daina tada hankalinka." shafa kanshi Baba Malam yayi tare da cewa. "Ngd ngd Saifuddeen Allah yayi maka al'barka ya azirtaka da yara masu biyayya." Amin Amin suka amsa baki ɗayansu, Ummi kuwa sosai taji daɗin addu'arshi ga Saifuddeen ɗinta, Shi kuwa Baba Malam kallonsu yayi baki ɗaya kana ya fuskanci Saifuddeen da kyau cikin muryar bada umarni yace. "Maganata ta gaba ba al'farma nake nema a gareka Saifuddeen umarnune nake baka a matsayina na Malaminka kuma surkinga, ina mai baka umarni da fito da wata matar auren zan aura maka ita ko ƴar wayece ni ne nan zan auro maka ita, Saifuddeen aure za ƙarayi, a cikin watannan!." Wani irin zabura da zare ido Saifuddeen yayi cikin tsananin mmki da kaɗuwa ya fara nuna kanshi da alamun tambaya. "Aure kuma? Ni kuma inyi wani auren kuma, to ita Zaleehanfa, in mata kishiya." Dirankadine yayi murmushi tare da dafa kafaɗun Saifuddeen ɗin. Jin an dafashi ne ya sashi juyowa ya kalli wanda ya dafashin kai ya runƙa jujjuyawa jin Dirankadi na cewa. "Haba Saifuddeen aurefa akace kayi ba yaƙiba, me na wannan firgitan da ɗimaucewa, to kai a zatonka barinka zamuyi ka zauna ba matane?." Kainshi ya jujjuya tare da zaro wayarshi ya fara rubutu dan yanaga kamar dai basa fahimtarsa ne. "Baba aure kuma, ko wata ɗaya banyi da yin aureba, yaza'ayi kuma inyi wani auren, ina da mata ai zata dawo, dan Allah baba ka bawa Baba Malam haƙuri, bazan fa iya zama da mata biyu ba." Murmushi Dirankadi yayi tare da cewa. "Me zai hana Saifuddeen tsab zaka iya zama da mata biyu." Wayyo Ahmad kam ji yake tamkar ya tashi ya rinƙa taka rawa dan daɗin wannan umarni na Dottijon arziƙi Baba Malam, a ranshi yake cewa. "Hegiya ifiritiya kin jazawa kanki kishiya, Aure nai dai in sha Allah za'ayishi." Ummi kam ita kanta taji daɗin wannan abu, Yes tunda ɗanta nada lfy har yanada muradin aure ainyi kuma ta gudu asheko dole a nemo mishi wata matar. Murmushi tayi lokacin da Saifuddeen ya juyo yake mata mgna da yarensa. "Wai Ummi kema naga murmushi kikeyi, nifa mijin mace ɗaya ne, ta yaya zan ƙara wani auren?." Cikin dariya tace. "A a to ni kuma ina ruwana, ka dai ji umarni ne yace ya baka ba neman al'farmaba." Tirƙashi wannan shine ana wata sai ga wata, kawai shi kam Saifuddeen ido ya zuba musu ganin da gaskefa sukeyi kuma Bappa Alima yayi na'am da hakan har cewa yake. "Ahmad kuyi ƙoƙari ku fito da matar aure dan cika umarnin surkinku, kunji dai yace nanda mako biyu yakeso ayi auren,." Wani mugun harara Saifuddeen ya dannawa Ahmad ganin yadda yaketa dariyar jin daɗi harda cewa. "In sha Allah kuwa, Kawu Ali zumu fito da matar, ayi komai kamar yadda malam yake so." Shi kuwa Baba Malam cikin son kontarda hankalin Saifuddeen yace. "Ka nemo matar da take sonka, Ni zanyi maka komai na auren ko sisinka bana buƙata." Shifa yanzu ganinsu yake kamar al'mara, su kuwa nan suka gama tattauna komai. Ganin azahar tayine yasa suka yi addu'a suka tashi a taron kana suka sallami Ummi suka fita baki ɗayansu su. Anan matsallacin jikin gidan nasu sukayi salla kana su Baba Malam da Dirankadi da Malam Adam suka tafi. Su bappa Ali kuwa suka dawo cikin gida sukaci abinci sannan suka ƙara jaddawa Saifuddeen batun auren sannan suka tafi. Su Babba Ali na fita Ahmad ya kwashe da dariya harda dukan cinya cikin jin daɗi ya kalli Saifuddeen daya haɗe fuska girarshi ɗaya ya ɗaga mishi tare da cewa. "Ya akayi ne angon mata biyu a wata ɗaya, kai Alhamdulillah lallai wannan dattijon ya cika adali mutun, kaga nanda mako biyu kana tare da sabuwar amaryarka dal a leda." Wani irin bugu ya ya kaiwa Ahmad, da sauri ya kauce tare da cewa. "Sai fa an maka auren na." Dariya Ummi tayi ganin yadda Saifuddeen ɗin ya haɗe fuska cikin dariyar tace. "To wai duk wannan haɗ...! [04/09, 2:52 pm] اسماء بشير: Cikin bedroom ɗin ta da nufin zataje ta sanarwa Ahmad, ko meye ta tuna kuma, oho sai ta koma ta zauna tana nazari. Sosai abun yayiwa Raliya ciwo, koda Ahmad ya fito ganin meya tsareta,  kamar zata faɗa masa saikuma tayi shiru, shi kuwa da bai san meke faruwaba sai janta yayi suka koma bedroom ɗinta dan yana tare da begenta. Ɓangaren Saifuddeen kuwa kwata-kwata ma bai nemi Zaleehan ba, yana fitowa daga wanka kwanciya kawai yayi,  sam bayaso yaje gareta, harma yaga abun da zai rabasa da nutsuwarsa, dan shikaɗai yasan irin azaban dayasha jiya, saboda haka baya sake fatan shan wani azaban kalan wannan, kasancewar agajiye yake hakan yasa yana kwanciya bacci ya ɗaukesa. Zaleeha kuwa gaba ɗaya tatakura akan kujeran da take kwance, sam kujeran bata da daɗin kwanciya bare daɗin bacci, cikin mintuna ƙalilan har jikinta yasomayi mata ciwo, gawani irin masifaffen sanyi dake busawa acikin garden ɗin, mutsutstsuka jikinta kawai takeyi, sosai takejin wuyanta ya ƙage amma kuma bata da wani zaɓi, wanda ya wuce yin haƙurin kwana awajen. Atakure haka bacci ɓarawo yasamu nasarar ɗaukarta. Ƙiran sallan asuban fari da akeyine ya ratsa jikinshi ya bashi lokacin salla yayi, ahankali ya buɗe idanunsa,  ɗan miƙa yayi tare da haɗawa da salati a zuciyarsa, nan yatashi zaune, kekensa ya jawo tare da hawa kanta, cikin nutsuwa da ɗan sauran kasalan bacci yakai kansa banɗaki, wanka yayi tare da ɗauro alwala, kaitsaye yafice daga ɓangaren nasa. Har yaƙarasa jikin ƙofar na Zaleehan saikuma wani tunani yazo masa, take yafasa shiga tada'ita da yayi niyya, sai ya ƙonƙasa mata ƙofar, kana ya juya ya tafi, kai tsaye yawuce masallaci. Zaleeha kuwa dama gaba ɗaya batayi wani ishashshen bacci ba, dan sanyine awajen sosai, jin motsi alaman cewa yatafi masallaci yasata tashi zaune, cikin sauri ta ɗau bargon haɗi da pillow'n ta, ahanzarce tanufi ƙofar falon nata, dai-dai lokacin Ahmad yafito daga ɓangarensu dan zuwa masallaci, idanunsa ne suka gane masa Zaleeha, fuskarsa ɗauke da ɗan mamaki yabita da kallo, ganin fitowarta daga cikin garden gashi hannunta riƙe da bargo da kuma pillow alamun nan ta kwana kenan yasanyashi girgiza kansa, cikin ransa yace. "Allah Ya shirya ki, ae dama mai hali baya taɓa fasa halinsa, saidai in ba'a zauna ba kuma dai duk tsaurin wayon amarya to wlh sai ansha manta anci sadaki an suɗe ki dai gama ɓoye-ɓoyenki." Nan yawuce masallaci. Itakuwa Zaleeha sam-sam ma bataga Ahmad ɗin ba, kaitsaye ɗakinta ta wuce, cikin hanzari tasoma rage kayan jikinta, ruwan ɗumi ta haɗa inda tayi wanka, tana fitowa daga wankan ta zura wata farar jallabiya mai kyau,  hijab tasanya tare da ta da sallah, koda ta idar da sallan bata tashi akan sallayan ba saida tayi azkar, nan ta ɗauko ɗan ƙaramin Qur'aninta tasoma karatu,  ba'ita ta rufe Qur'anin ba saida taga gari yaɗan somayin haske, wasu bedroom slippers masu kyau ta zura aƙafafunta, inda tasake feshe jikinta da turare me daɗin ƙamshi. Koda tafito daga ɓangaren nasu kai tsaye part ɗin Ummi ta  nufa, bakinta ɗauke da sallama haka ta kutsa cikin falon, wanda ke cike da jama'a, Raihana ne da Saminu waƴanda zasu koma Kaduna asafiyar ta yau, saikuma Goggo Dada da Aunty Meena wanda zasu koma Dukku, Aunty Rahama ma yau zata koma, don tunjiya Dr.Adnan keyi mata waya, kan cewar yayi kewarta gashi weekend  yana gida shiyasa yace zaizo da safen ya ɗauketa. Cikin yin ƙasa da kai haɗi da nuna tsantsar ladabi taƙaraso cikin falon,  har ƙasa ta durƙusa inda ta gaishe da Ummi, cikin fara'a haɗi da sakin fuska Ummi ta amsa mata gaisuwan nata, tare da miƙo mata hannu ta kamo nata, cikin kulawa Ummi tace. "Taso kizonan kusa da Umminki yarinyar kirki, kema ai ɗiyatace, tunda kika shigo cikin mu kuwa kinzama jininmu." Tasowa tayi daga inda take tare da ƙarasowa kusa da Ummi, Ummi ne tajawota inda ta zaunar da ita agefenta, sadda kai ƙasa Zaleeha tayi tana murmushi, hakanan itakam Allah ya samata son matan aranta, sosai take ganin ƙima da kuma darajan Ummi'n,  su Raihana ne suka gaishe da Zaleehan, amatsayinsu na ƙannen Saifuddeen,  haka ta amsa musu fuska asake, ɗan zamowa ƙasa tayi inda tagaishe da Goggo Dada dakuma Aunty Meena, sai kuma babbar yaya wato Adda Rahama, da kuma Saminu wanda ke zaune gefen Saifuddeen, da fara'a akan fuskarsu duka suka amsa gaisuwar nata,  komawa gefen Ummi tayi ta zauna a ƙasan carpet dan tana matuƙar ji da ganin darajar Ummi, shiru tayi yayinda ko kallon inda Saifuddeen yake batayi ba, shikuwa har acikin ransa mamakin irin tsantsar ladabinta ga ƴan uwansa yake, tanason kowa acikin ahalinsa tana mutuntasu da girmamasu, amma wato shine marainin wayonta sam bata ganinsa da gashin ido, murmushi yayi wanda  shi kaɗaine yasan ma'anonin murmushin ransa yace.   tabbas kuwa zanyi maganinta ne, very soon zankashe bakin tsiwan, badai ni ta raina ba?." hmmm yasha alwashin duk randa ya kamata kuwa zataji ajikinta. Saminu ne yace da Raihana su hanzarta sutafi, bayason tafiyar da bata safiya ba, saboda alokacinne yakejin karsashi ajikinsa, nan kowa yatashi don yi musu rakiya zuwa compound ɗin gidan, ciki kuwa harda Zaleeha wanda ta kamo hannun Daddy yaron Bappa Ali wato Junior mai sunan Abbandu Saifuddeen kenan,  kasancewar yaron kyakkyawane yasanya sosai yashiga ranta, gashi nan da wayonsa irin yaran nanne masu shiga zuciya, haka suka fito compound ɗin gidan inda yaketa zuba mata surutu, itakuwa murmushi kawai take tayi masa, har bakin mota suka rako su Raihanan, nan sukayi sallama da juna, cikin yanayi na tsokana Raihana ta dubeta, tare da cewa. "Kikulamin da Hammana da kyau da kyau, dan ko ƙuda bama son ya taɓa manashi." Dariya sukayi gaba ɗayansu, itakuwa Zaleeha ɗan guntun murmushi tayi, yayinda taji wani malolon abu ya tokare maƙoshinta, cikin zuciyarta tace. "Lallai kuwa zai mutu, indai nice zan kula dashi!. Yo ni me haɗina dashi kunamai ma su sauƙa ajikinsa mana ba ƙuda ba ni me yadameni." Motar su Raihana baigama fita daga gidan ba saiga Dr.Adnan nan shima yazo ɗaukar matarsa, nanfa suka gaisa, inda Zaleeha tagaishesa cikin mutuntawa,  Farouq da Adam kuwa sai tsalle suke dan sunga babansu, duk girmansu baigani ba haka yasasu ajikinsa,  babu yanda basuyi ba akan cewa Daddy yazo su tafi ba amma yaƙi,  waishi ala dole yasamu sabuwar Aunty yace shi Dukkunma bazai komaba, kusan saida yabawa kowa dariya haka suka tafi anata raha. Daddy kuwa da ƙyar  suka iyayi masa wayo yabi iyayen nasa da karatunshi,  Ahmad ne yazo da motarsa wanda dama shine zai mayar dasu Goggo Dada gida, lokaci ɗaya fa gaba ɗaya jama'an baƙin biki  suka watse gida yayi shiru. Ummi Raliya da kuma Zaleehan kawai aka bari, dama Saifuddeen yana part ɗin Ummi, kasancewar shi baifito rakiyan ba, shikuwa Hayatudden sarkin bacci, yanacan tun dawowansa daga sallan asuba daya koma bacci shine haryanzun baitashi ba. Direct Zaleeha part ɗinta ta koma, inda su Ummi da Raliya suka koma wajen Saifuddeen. Tana shiga cikin ɗakin nata ta cire hijabin dake jikinta, kan gado ta faɗa tare da ɗan lumshe idanunta, sosai takejin wani sabon bacci naƙoƙarin ɗaukarta. Can ɓangaren Ummi kuwa, Saifuddeen naganin dawowansu, ya sakawa Ummin nasa shagwaɓa, sanin halinsa na sakalci kaman wani ƙaramin yaro yasanya Ummi da kanta tashiga kitchine inda ta haɗa masa coffee, sosai yaji daɗin haɗin coffee ɗin da Ummin tayi masa, ɗaukan mug ɗin yayi tare da bar musu falon, kai tsaye yanufi sashinsu. Saifuddeen nafita, Ummi tayi murmushi cikin jin daɗi tace. "Allah kenan maiyin yadda yaso a lokacin da yaso, kafun auren nan kowa yasan cewa yarinyar nan bason auren nan take ba, amma yanzu cikin ƙuduran Allah gashi suna zaune lafiya, kinga ta saki ranta." Murmushin gefen baki Raliya tayi tare daɗan muskutowa, cikin jimamin abun dake damun zuciyarta tun daren jiya tace. "Hmmmm hakane kam Ummi, amma nikuwa jiya naga abun daya ɗauremin kai ya bani mmki, dan nima da fari da naga ta saki ranta naji daɗi." Dubanta Ummi tayi tare da cewa. "Mene kuma yafaru?." Gyara zama Raliya tayi tare da cewa. "Ummi kinsan kuwa cewa jiya awaje cikin garden ta kwana? wallahi Ummi abun yabani mamaki sosai, inata tunanin dalilin da zaisa ta kwana cikin garden, idan har zatana gudunsa haka, meyasa ta amince da aurensa?." Cikin matsananci mamakin jin maganan da Raliyan ta faɗa Ummi ta sauƙe wani irin ajiyar zuciya, jiki amace tace. "Raliya kin tabbatar da abun da kike faɗa kuwa?." Kai Raliya tajinjina tare da cewa. "Wallahi Ummi da idanuna naganta jiya a garden ta kwana, kuma koda natashi sallan asuba dana leƙa naganta, alokacin tana ƙoƙarin barin wajen, kuma tabbas nasan babu makawa itace dan Abban Farida ma ya ganta dayazo tafiya masallaci." Ɗan jim Ummi tayi tare dajinjina kanta, take taji zuciyarta tayi mata wani irin ba daɗi, hankali ya tashi fargaba ya cika mata zuciya wato har ƙiyayyar ta kai haka, jiki a mace tace. "To Allah dai ya kyauta." Amin Amin Raliya ta amsa jiki a mace. Haka dai zaman yaci gaba da gudana har tsawon kwanaki, Kullum  in gari ya waye Zaleeha na idar da salla zataje ta gaida Ummi a mutunce, lokuta da dam takan samu Saifuddeen a wurin Ummi, amman tsakaninta dashi sai harara da murguɗa baki, tana son kowa na gidan yayinda suma duk suke matuƙar sonta musamman Raliya da takanje har ɗakin Zaleeha su ɗanyi hira, dan itacema ta tayata shirya tarin akwatunan kayan aurenta da kimtsa mata duk abinda zata buƙata a durowa, sauran akwatunan suka kaisu ɗaya ɗakin, Hayatuddeen kuwa dama akwai sabo a tsakaninta haushinta da yaji kan cewa da tayi bata son Hammanshi yanzu babushi tunda yanaga har ta yarda da auren ta zauna lafiya dashi. tana matuƙar girmama Ummi wanda hakan yasama mata soyayya a idanunsu, tana mutunta Ahmad a cewanta mai sunan yayanta ne dan Yaya ma take kiranshi tun tana gaidashi yana amsawa a yatsine har dai ya fara ɗan sasaautawa. Har yau kuma a woje take kwana cikin gardin, wannan abun shine yasa Ahmad yake matuƙar jin baƙin cikinta, shi kuwa Saifuddeen  da fari baisan bata kwana a ɗakintaba dan baya shiga kuma da safe yana ganinta a wurin Umminshi, To tun shekaran jiya daya dare ya ankara da bata ɗakin, ya dudduba ko ina na cikin part ɗin nata babu ita ba dalilinta, falonshi ya koma wayarshi ya ɗauka tare da yin mgnar zuciya, "To ina take zuwa ta kwana yau kwana biyu kenan bata kwana a nan." Kanshi ya ɗan jingina da jikin kujerarsa tare daci gaba da mgnar zuci. "To waya sanima ko ta daɗe da barin kwana a nan." sai kuma yayi ajiyan zuciya tare da cewa. "ko dai part ɗin Ummi take kwana? kai Anya kuwa Ummi zata barta ta kwana a side ɗinta, to ko dai part ɗin Raliya take kwana." Text ya rubutawa Ahmad, "Kayi bacci ne?." Ahmad da ke zaune a falo shida Raliyya suna mgnar Zaleeha dan hango wucewarta da sukayi, murya a sanyaye Raliya tace. "To wai ko dai Hamma Saifuddeen bai san bata kwana a ɗakinba?." Ajiyan zuciya Ahmad ya sauƙe tare da cewa, "Ina zaton bai saniba, kinfa san shi da miskilanci, in kuwa yasan bata kwana a cikin to yasan inda take kwanan shiyasa bai kulataba ai jiki magayi." da sauri ya ɗago wayarshi ganin saƙon Saifuddeen ne ya sashi cewa. "To ina ga dai bai san bata kwana cikiba sai yanzu dan ga text ɗinshi wai nayi bacci ne." ido Raliya ta zuba fuskar wayarshi tana ganin amsar da yake rubuta mishi. "A a banyi bacci ba, lfy dai ko?." jim kaɗan sai ga wani saƙon. "To lafiya dai zance,amman Zaleeha na wurinku ne?." murmushi Ahmad yayi tare da cewa Raliya, "Hmmm zanyi mgnin yarinyar nan." sai kuma ya rubuta mishi amsa. "A a Zaleeha kuwa, bata nan." a take sai ga wani saƙon. "Kasa Raliya ta dudduba nan wurinku, taje Side ɗin Ummi ma ta duba ko tana can." yana gama karan tawa yace. "Lafiya dai kam ko?." tsaki Saifuddeen ya ɗan ja kana ya rubuta mishi, "Nima ban saniba lafiya ko ba lfy ba, ina dai zargin yarinyar bata kwana a gidan nan, dan tun shekaran jiya na lura babu motsinta, sannan yanzu na dudduba ko ina bata ciki side ɗin." cikin nuna fargaba Ahmad yace. "Innalillahi, to ina take zuwa ta kwana, gani nan fitowa." sai ya kuma miƙe ya kalli Raliya tare da cewa, "Maza kije side ɗin Ummi ki gaya mata, ana neman Zaleeha ki kuma ce karta nuna tasan inda take kwana zanyi mgninta." to tace tare da juyawa ta nufi side ɗin Ummi, kana shi kuma Ahmad ya nufi ƙofar falon Zaleehan nan yayi kicibis da Saifuddeen daya fito, "To wai ina ta shigane, mufa mun dudduba wurinmu babu ita." kai ya jujjuya mishi alamun shimafa ya dudduba wurinsu babu ita. dai-dai lokacin kuma Ummi da Raliya suka iso, nan fa suka haɗu suka nuna basu san inda takeba. ita kuwa Zaleeha tun fitowan su Ahmad ta buɗe ido, jin ita ake nema yasa ta zame a hankali ta konta a ƙasan kujerar fulawi ke zagaye da ita. Ahmad kuwa yana hangota hakan ya sashi cewa. "Hmmmm zaki gane kurenki." wayarshi ya zaro lallatsata yayi ya nemo number Ya Aminu, ya kirashi kana ya kara wayar a kunnenshi. Can cikin bacci Ya Ameenu yaji wayarshi nata suwa, a hankali ya ɗan zare Maryam daga jikinshi, hannu yasa ya ɗauki wayar time ya duba ƙarfe ɗaya na dare. "Ahmad kuma a daren nan lfy kuwa?." sosai yaji fargaba ,kar dai Zaleeha nacan na tarfa musu rashin ɗa'a, jiki na rawa ya amsa kiran cikin sauri yace. "Salamu alaikum ,Ahmad lfy kuwa?." cikin nuna tashin hankali yace. "Ya Ameenu Zaleeha ce bamu ganiba mun nemata ko ina a gidan babu ita ba dalilinta, kuma Saifuddeen yace tun shekaran jiya bata kwana a side ɗinsu, to sai yayi tunanin wai ko side ɗinmu take shigowa ta ɓuya ko na Ummi, to shine yanzu ya sanarmana zatonsho tana wurinmu,mun duba kab gidan bata, nan shine nace bari in kiraka ko ta dawo gidane?." cikin kaɗuwa Ya Ameenu ya miƙe tare da cewa. "Zaleehan to ina take zuwa?." a taƙaice Ahmad yace. "To ko tana gida ne?." rai a ɓace Ameenu yace. "Kai anya kuwa sam bata gida, to ina take zuwa ta kwana, yi haƙuri bari in kira Baba malam." to Ahmad yace kana ya katse kiran sannan ya gaya.musu yadda sukayi da Yayanta Ameenu, kana yace su shiga ciki kafin Ameenun ya kirashi. Shi kuwa Ya Ameenu wani irin tashin hankali ne da ɓacin raine mai tsanani ya rufeshi to ina Zaleeha take zuwa ta kwana ina take tafiya ta bar ɗakin mijinta me haka yake nufi? kiran Baba Malam yayi bawan Allah yana zaune bisa sallaya yana karatun qur'an kiran Ameenu ya shigo wayarshi, har wayar ta katse bai ɗaukaba duk da yaga Aminune so yake yaje ƙarshen surar Arrahaman da yake karantawa, yayinda wani fargaba ya rufeshi lfy kuwa kira da tsakiyar daren nan. Yana zuwa ƙarshen surar kira na uku na shiga wayar, da hamzari ya amsa kiran, "Barka da dare Baba Malam kayi haƙuri na tada kai daga bacci." Ameenu ya faɗa a ladabce, murya a ɗan harɗe Baba Malam yace. "Ameenu lfy kuwa meke faruwa?." cikin sanyi Ya Ameenu yayi mishi bayanin da Ahmaɗ yayi mishi, ya ƙara da cewa. "Ko dai ta taho gida ne?." lumshe ido Baba Malam yayi yana jin wani irin suya da zuciyarshi keyi me Zaleeha ke nufi zubda mishi mutunci da kima  a idanun mutane ko? a hankali ya cewa Ameenu. "Ameenu bana zaton tana cikin gidana ,bazata zo nanba, amman dai bari in bincika." to Aminun yace kana y katse kiran. shi kuwa Baba Malam fitowa yayi da kanshi yayi tabin luggu da saƙo na gidan ya duba ko ina kab babu ita, koda ya titse Mama da tambayar ina Zaleeha ke zuwa ta kwana, rantse-rantse tayi ta mishi akan ita bata san ina Zaleeha ke zuwa ta kwanaba. a daren Ameenu ya kira goggonsu Maryama da duk inda suke zaton zataje ko ina sai ace musu bata zoba. Wannan abu yayi matuƙar tada hankalin Baba Malam ya Ameenu kuwa ji yake in yaga Zaleeha zai kusan karta, dole ya kira Ahmad yace, wlh bata wurinsu amman tunda da safe tana dawowa zai zo ya sameta, har ɗakinta. Da  wannan kowa ya koma ɗakinshi, Ahmad kuwa ranshi ƙal yasan Zaleeha zata gane kurenta. Washe gari kamar yadda ta saba, suna tafiya masallaci ta koma ɗakinta wonka tayi da ruwan ɗumi wai ko tsamin cizon sauro da  jikinta keyi zai ragu, wanka da al'wala tayi, kana ta fito tazo tayi salla koda ta idar  azkar tayi sanan ta miƙe ta kimtsa jikinta cikin wata doguwar rigar mai ɗan karen.kyau wanda duk na kayan aurene, da mayafinshi ta yane kanta ,kana ta nufi sashin Ummi. a falo ta samesu, dukansu, cikin nitsuwa ta isa gaban Ummi dake mata murmushi tare da cewa. "Gari ya waye ko ɗiyata?." murmushi tayi tare da rusunawa gaban Ummi cikin ladabi da sanyin lafazi tace. "Ummi Ina kwana?." cikin kula Ummi tace. "Lafiya lau ya  baƙunta?." kai a sunkuye tace, "Alhamdulillahi." "Masha Allah." cewar Ummi kenan Hayatuddeen ne ya gaidata ta amsa fuska a sake, kana ta kalli, Ahmad dake zaune kusa da Saifuddeen bisa alamu lissafi sukeyi, cikin sanyin sauti tace. "Yaya ina kwana?." a taƙaice yace. "Lafiya lau." daga nan kuma sai ta miƙe tare da cewa Ummi . "Raliya na kitchen  ko?." cikin jin daɗi Ummi tace. "A a tana sashinta yau wai kanta ke ciwo." a hankali tace, "Ayyah ban saniba Allah ya bata lfy." Amin Amin Ummi tace, Kana sai ta ɗan rusuno tare da cewa, "To Ummi bari in shiga kitchen, me zan  haɗa  mana breakfast?." sosai Ummi take jin daɗin yadda take sakewa da Raliya su shiga kitchen tare, gashi yanzu har tana shiga ita ɗaya ma tayi musu girki. cikin kula Ummi tace. "Bari inzo mushiga tare to." da sauri tace . "A a Ummi ki bari zan iya ki huta." sai kuma ta kalli Hayatuddeen daketa murmushi tace, "Zo muje kitchen ka tayani hira." da sauri ya miƙe yabi bayanta, yana cewa. "Yauwa muje ki min dege-dege." da ido Ummi ta bisu har suka shiga kitchen ɗin. koda suka ƙarasa cikin kitchine ɗin, hayewa kan wata kujera Hayatuddeen yayi ya zauna, wayarsa ya fiddo daga aljihunsa tare da soma latsawa, ita kuwa Zaleeha, direct wajen fridge ta nufa, buɗe cikin firjin dake shaƙe da kayayyakin abinci tayi, nan ta zaɓo manya manyan kaji guda biyu,  sake wankesu tayi sannan ta ɗaura akan wuta tare dasa kayayyakin ƙamshi dana danɗano. nan ta ɗibo irish patatoe tasoma ƙoƙarin ferewa,  Hayatuddeen ne ya taso tare da soma taya ta,  haka suka cigaba da firan, yana ta zuba mata surutu,    mayafin dake jikinta ta ajiye, tare da soma yin aikinta cikin nutsuwa, yayinda Hayatuddeen gaba ɗaya ya sakota gaba da surutunsa,  cikin abun da bai wuce awa ɗaya da rabi ba, ta kammala haɗa barbecued chicken da kuma patotoe balls,  sai kuma bread Pizza, wanda gaba ɗaya ƙamshinsa ya cika kitchine ɗin, Hayatuddeen dake zaune agefe sai haɗiye miyau yake, dan har ya tsara irin cin da zaiyiwa bread pizza ɗin, da ƙamshinsa ya cika masa hanci, spearmint tea ta haɗa, sannan ta juyesa acikin flask, nan ta kimtsa gaba ɗaya kayan akan wani babban tray, duban Hayatuddeen tayi tare dayi masa alama akan yazo ya tayata ɗauka, aikuwa shi ya kwashe komai inda ya jere musu break fast ɗin akan dinning table, ita kuwa Zaleeha har yanzu tana kitchine, fruit salad ta haɗa, inda ta zubashi cikin wani babban glass bowl, tunanin haɗa chocolate fudge cake ne yazo mata, nan ta duba taga akwai komai na buƙata, kanta ta jinjina, sannan tashiga ƙoƙarin haɗawa, cikin mintuna ƙalilan kuwa ta kammala, ita kanta saida tayaba da ƙamshin chocolate fudge cake ɗin, Hayatuddeen dake falo kuwa koda ƙamshin yaje masa, saida yakasa haƙuri ya biyota zuwa kitchine ɗin, ganin, fudge cake ɗin yasan yashi cewa. "Wow fantastic, Aunty Zalee dama wai kin iga girki har haka ne?, na ɗauka a faɗa da masifa chart da zuwa wurin aiki kawai kika iya." Hannu tasa takai masa bugu, da sauri ya kauce yanayi mata dariya, hararan wasa ta watsa mai, tare da cewa. "Kaɗauka yanda kuke sakarkaru kaida Zakariyya haka kowa ma yake ne baku da aikin sai yawo a gari dama tsokana da ci." Taƙare maganar tana me miƙo masa, wani haɗaɗɗen tray wanda ciki tashirya chocolate fudge cake ɗin, amsa yayi yana wani malau malau da baki, tare da cewa. "Hmmm ai yanzune ma zakuga tashen jami'a zakusha mmki bari dai in gama sabawa da jami'ar kin san banfi sati ɗaya da fara zuwa ba." Dariya ta ɗanyi tare da cewa. "Yo ai da an ganka ansan kanka na fizga da igiyar iskar sabin shiga jami'a ka dai yi a hankali yaro dan ita jami'a gidan ban kashine." Murmushi ya ɗanyi tare da cewa. "Gobe zan kawo miki sabon abo kina Khamis ku gaisa. kiga irin salon takun mu, yaseen ki kuma cewa mijinki ya saya min mota. Dan ni ba yaro bane da za'a rinƙa kaini ana ɗaukoni kamar wani ɗan primary ko kayan wonki da za'a rinƙa kaini ana ɗaukoni". Ya ƙarishe mgnar yana wuce zuwa dinning, food flask ɗin dake gefenta wanda ciki ta shiryawa Raliya abinci ta ɗauka. Koda ta fito falo, nan ta iske Ummi, da kuma Saifuddeen, da Ahmad, Hayatuddeen kuwa tuni ya baje kan dinning, inda ya turo baki gaba, wai don saboda yace suzo suci, sunce yajira Zaleehan tagama sai suci tare, sam shi gaba ɗaya yaƙosa yaji yana tauna abincin, musamman ma da ƙamshin abincin ya cika masa hanci. Zaleeha na fitowa daga kitchine ɗin ta dubi Hayatuddeen, fuskarta ɗauke da murmushi tace. "Autan Ummi sarkin ci!." Baki Hayatuddeen yaƙara turowa gaba, ashagwaɓe yace. "Eh naji, amma please kice musu suzo muci, I swear am feeling hungry fa!." yafaɗi maganar yana me shafa cikinsa, wanda hadda ganin abincin ma yaƙara masa jin yunwa. Murmushin daya bayyana zallan cute face ɗinta tayi, tare da girgiza kanta. Ummi ne tayi murmushi tare da duban Zaleehan, cikin so da ƙaunar yarinyar tace. "Sannu da aiki, Allah yasaka miki da al'khairi, ya kuma baki ƴaƴa masu al'barka, wanda zasuyi miki fiye da haka." Saɗa kai kasa Zaleeha tayi tare da ɗan sakin guntun murmushi a kunyace murya a sanyayaye tace, "Amin Ummi." Saifuddeen kuwa a fakaice ya ƙura mata idanu, yana kallon duk wani motsinta sosai yake mamakinta, har yau har yanzu ya rasa ita wace irin mutum ce mai fuska biyu da jujjuyawa tamkar hawainiya, ji yanda take ta murmushi tare da sakewa dasu, tanayin komai kamar wata wanda keson zama dasu da gaske. Shi mamakinta ma yake, tawani irin sakewa sai kace ba itace, su keta gantalin nema ba jiya. Kawar da kansa yayi daga kallonta, tare da maida hankalinsa, ga laptop ɗinsa, wanda a zahiri laptop yake kallo a baɗiri kuwa fuskata yake kallo ta cikin madubin system ɗin, rumtse ida nunshi yayi a hankali tare da sauƙe nannauyan ajiyan zuciya, "To ina take zuwa ta kwana dasu waye take kwana, me take aikatawa a inda take kwanan?." haka yaji waɗannan tambayoyin sun cika mishi zuciyarshi dake cike da azabebben kishi, gaba ɗaya ya rasa wani irin kishi Allah ya ɗora mishi a kanta ji yake tamkar zai faɗi ya mutu dan baƙin ciki. Ahmad kuwa dubanta yayi tare da sakin murmushi, cikin ransa yayi ƙwafa, ahankali yace. "Zaki sanine yarinya." Duban Ummi Zaleeha tayi tare da ɗan rusunawa, cikin nutsuwa tace. "Ummi bari na kaiwa Raliya abincinta, tunda batajin daɗi nasan ba lallaine tasamu fitowa ba." Sosai Ummi taji daɗin kulawan da Zaleehan ta nuna ga Raliya'n, amma sai tace. "A'a Zaleeha da kanki, bazaki bari Hayatuddeen yakai mata ba." Murmushi Zaleeha tayi tare da cewa. "Bakomai Ummi, kinga Hayatudeen ɗin yace bazai iya komaiba sai yaci abinci,inaga bazai iya matsawa akan dinning ɗinnan batare daya lodawa cikinsa abinci ba, kin sanshi acicine kazar birni!." Zaleehan tafaɗa tana kallon Hayatuddeen, ba iya Ummi ba harta Ahmad saida yaɗanyi murmushi sabida sunan data kira Hayatuddeen Acici kazar birni, Ummi ce tace, idan takaiwa Raliyan abincin ta dawo suci abincin, nan tace zasuci da Raliyan acan. Koda ta ƙarasa ɓangaren Raliyan, akwance ta isketa, nan ta shiga ɗan kimtsa mata ɗakin, daga nan kuma ta zuba musu abincin inda suke ta hira ita da Raliya'n sosai Raliyan ta sake da ita har taji ciwon kan nata ya saketa. A falon Ummi kuwa, tuni Ummi tayi serving ɗin kowa, nan fa Hayatuddeen yasoma kai loma, yana me jijjiga kansa. Saifuddeen kuwa ahankali yake tsakuran abincin yana kaiwa bakinsa, idanunsa kawai yake lumshewa sabida ƙuna da zuciyarshi keyi na kishi, tabbas ya yaba da iya girkinta domin sosai abincin yayi masa daɗi, sam koda wasa bai taɓa tunanin cewa Zaleeha ta iya girki har haka ba. Ummi ma sosai ta yaba da abincin, Hayatuddeen kuwa cikin santi ya ɗago kai inda ya dubi Ahmad, cikin halinsa na tsokana yace. "Wallahi Aunty Zalee ta iya abinci, mai daɗi kaman kunnena zai fita, hmmmm ai daga yau ita zatana mana girki, don sosai tafi su wance iyawa." Dariya ne ya ƙwacewa Ummi, dan tasan tabbas Hayatuddeen dan tsokana yayi maganan da Raliya yake. Harara Ahmad ya watsa masa tare da taɓe baki, cikin nuna cewa shima matarsa gwanace yace. "Oho dai, da makaho ya rasa ido sai yace da wari, wannan har wani abinci ne, an haɗamu da tarkace saikace wasu yaran larabawa, jifa wani cake na chocolate, ko ance mu yaran larabawa ne, ai dai Raliya tafita iya girki ko Ummi." Ahmad ya faɗa yana me duban Ummi. Murmushi Ummi tayi tare da gimtse dariyarta, ita dai bata da tacewa, to ma mezatace komai tace yanzu zasuce tayi sonkai. Hayatuddeen kuwa dariya yadinga yi, don yasan maganan Ahmad ɗin, a iya laɓɓan baki kawai take, ba taje zuci ba, ya faɗane kawai don ya kare matarsa, amma yasan cewa koma waye yaci girkin dole ya yaba, musamman ma spearmint tea ɗin dake ta ƙamshin kayan haɗi, uwa uba kanasha kanajin wani irin ɗan ɗanon zuma aciki. Ahaka suka kammala cin abincin, inda Ummi tasa Hayatuddeen ya kwashe kwanukan yakai kitchine. Acan gidan Baba Malam kuwa, tuni Baba Malam ya ƙira Habu, inda yace yaje gidan Zaleeha ya taho masa ita. Babu ɓata lokaci kuwa, Ya Habu yashiga cikin motarsa, kai tsaye ya nufi gidan su Saifuddeen. Aƙofar gidan yayi parking motarsa, inda yayi knocking gate ɗin gidan, maigadi ne ya leƙo tare da buɗe masa, duban maigadin Ya Habu yayi tare da basa hannu suka gaisa, dai-dai lokacin kuma Ahmad yafito daga part ɗin Ummi zaiyi nasu sashin, ganin Ya Habu yasanyashi ƙarasowa wajen daɗan sauri, nan yabawa Ya Habu hannu sukayi musabaha koda Habun ya gaya mishi saƙon Baba Malam, Ahmad ɗinne yayi masa jagora har zuwa part ɗin Ummi, amutunce suka gaisa da Ummi, bayan sun gama gaisawanne yayi musu bayanin cewa Baba Malam ne yaturosa akan cewa ya tafi da Zaleeha, aikuwa sosai zuciyar Ahmad tayi fess, Ummi ne tace da Hayatuddeen yaje yaƙirawo Zaleehan, don kuwa har yanzu tana nan a part ɗin Raliya. Koda Hayatuddeen yaje part ɗin Raliya, nan ya iskesu sunata hira, shaida mata ƙiranta da akeyi yayi, "Aunty Zaleeha Ya Habu yazo yana falon Ummi yace kije." Cikin tsoro da fargaba tace. "Ya Habu kuma! Shi da waye?." murmushi Hayatuddeen yayi tare da cewa. "Ya Habu fa nace ba dodoba, shi kaɗai mana yazo, kinga yace kiyi sauri gida zakuje tare." Ƙulullluuuu cikin Zaleeha ya bada sautin murɗa a take cikinta ya ɗuri ruwa, nan ta cika da fargaba haɗi tsoro, cikin tankwashe wuya ta kalli Hayatuddeen tare da cewa. "Pleees je kace baka ganni ba." Sosai suka cika da mamaki, Kai Raliya ta sunkuyar dan kar dariyan da ke sun kubce mata ya baiyana a fuskarta, cikin mmki tace. "Ya kuma zaije yace bakyanan bayan kuma gaki?." kwaɓe fuska tayi tare da cewa. "Eh yaje yace ina bacci to." sosai tsoronta ya baiyana a fuskarta ganin hakan yasa yakoma falon Ummi yafaɗi cewa. "Bai ganta ba." Hararan da Ahmad ya watsa masa ne, yasan yashi faɗin gaskiya inda yace. "Tace nace banganta ba, ko kuma ince tayi bacci." Nanfa Ya Habu yacika da mamaki, take kuma yaji ransa ya ɓaci, ta tabbata mara gaskiya kenan, sake tura Hayatuddeen ɗin yayi akan tazo, nan ma Hayatuddeen yaƙara dawowa, yace tace wai batanan, haka akayi juyin duniya akan Zaleeha tazo, amma ina sam taƙi zuwa, daga ƙarshema ɗakin Raliya ta gudu ta ɓuya. Rai aɓace Ya Habu yafito yabar gidan. Yana zuwa gida ya iske Ya Ameenu da Baba Malam azaune, cikin ƙunan zuciya ya kwashe duk abun da ya faru ya faɗawa Baba Malam, sosai Ya Aminu ya hatsalo gaba ɗaya jikinshi rawa ya ɗauki saboda matsanancin ɓacin rai da zafin zuciya irin nasu na sojoji da kuma fulani ji yake muddin gata gashi zai kakkarya mata ƙafafuwa yaga gobe da wanne sawun zataje yawon. Me Zaleeha takeson maidasu ne?, me take nufi dasu? Wai ko dai gani take tafi ƙarfinsu ne? miƙewa yayi tare da cewa. "Bari inje in taho da ita!." Kai Baba Malam ya gyaɗa mishi dan fitinar Zaleeha tana tafasa mishi zuciya tana gab da ƙureshi. Ahmad na zaune afalo suna mamakin halin na Zaleeha, saiga ƙiran wayar Ya Aminu yashigo wayarsa, ɗauka yayi ko gaisawa Ya Ameenu bai bari sunyi ba, yace da Ahmad ɗin yana ƙofar gida, cikin jin daɗi Ahmad ɗin yasanar dasu Ummi da Saifuddeen. Sannan yafita ya shigo da Ya Ameenu'n, gaisawa sukayi sannan Ahmad ɗin ya dubi Saifuddeen, cikin nutsuwa yayi wa Saifuddeen ɗin alama kan cewar yayi haƙuri, zasu tafi da Zaleehan, Baba Malam ne ke nemanta, cikin body language Saifuddeen yace. "Bakomai" dan shi kanshi yana cike da son sanin ina take zuwa ta kwana. Shikuwa Ya Ameenu kai tsaye cewa kawai yayi anuna masa ɗakin da Zaleehan take, a bashi izinin shiga zata fito, nan Ahmad mugu yace. "Ba komai ya Ameena ai kai ba baƙo bane, tana ɗakin Raliya muje in nuna maka ɗakin". cikin zafin jini Ya Ameenu yabi bayan Ahmad da yake ta dariyar zuci so yake adaka mishi hegiyar yarinyar nan mai ladabin kura Zaleeha na rakuɓe ajikin bango suna magana da Raliya sai gani tayi an turo ƙofar ɗakin, koda takai dubanta ga ƙofar kuwa saida numfashinta yakusan ɗaukewa ganin Ya Ameenu a bayan Ahmad sam bata tsammaci ganinsa ba, aruɗe tasoma ƙoƙarin guduwa, taku ɗaya yayi ya cafkota tare da wanka mata wani irin gigitaccen mari, wanda yasanya tasaki wata irin razanannen ƙara, take tasoma ƙoƙarin shiɗewa, aharzuƙe Ya Ameenu yace. "Wato har kinyi girman da Baba Malam zai aiko ƙiranki kiƙi zuwa ko?, wuce muje kona kakkaryaki anan wajen, mahaukaciya kawai muje yau sai kin gaya mana gidan ubanwa kike zuwa ki kwana?!!." Cikin ɗimaucewa Zaleeha ta wuce gaba, tare da fara tsalle tana yarfa hannu cikin kukan gano yau sai dai buzunta dan ta lura zargin yawo Ya Aminu da sauran ƴan uwanta suke mata. jin ya sake yarfa mata wasu tagwayen marukane tare da ce mata. "Gidan ubanwa kike zuwa ki kwana? Wato mu zaki maida sakarkaruko? Wato yawon lalata kikeson ki koyaka?." wani irin tsalle ta rinƙayi tana yarfa hannu cikin tsananin kuka da tsoro tace. "Wallahi Ya Ameenu ba yawon lalata nakeyiba, a cikin gidannan nake kwana cikin garden nake kwana wlh bana fita ko ƙofar gidan." Ummi kam dake falonta jin kukan Zaleeha ne yasata saurin juyowa ta kalli Saifuddeen dake kallonta tace. "Kai Saifuddeen dukanta fa sukeyi ,kada ka bari su tafi da ita zasu illatata,wannan sojanefa ya saba dukan garadai kar ya illatamin yarinya mai biyayya." kai ya jujjuya mata tare da haɗe hannunshi wuri ɗaya ya mata alamun dan Allah kada ta fita ta barsu su tafi da ita. Shikuwa Ya Ameenu a zafafe yace. "Maza mu tafi gida ba ni zakiyiwa bayani ba." da sauri-sauri gudu-gudu tayi hanyar fita, kana shi kuma biyo ta. Suna ƙarasawa wajen motarsa ya buɗe tare da hankaɗata ciki, ransa amatuƙar ɓace ya ja motar sukabar ƙofar gidan. Gudu yake sosai hakan yasa cikin mintuna kaɗan suka iso G.R.A yana gama dai-dai-ta fakin ɗin motar, ya fito tare da zare belt ɗin wandonsa, ƙofar da take ya buɗe tare da figota waje, nan yashiga zuba mata belt ɗin ajikinta, kuka da ihu mai firgitarwa Zaleeha keyi tare da gudu ta nufi cikin gidan, kai tsaye ɓangaren Baban nata ta nufa. Tana shiga tafaɗa bayan Mamy dake tsaye acikin falon, gefe kuma Baba Malam ne zaune, sai kuma Ya Ahmad da kuma Mama wanda tacika tayi fam, ƙiris take jira ta fashe ta tarwatsa musu buhun bala'i. A harzuƙe Ameenu yashigo cikin falon, ganin haka yasa Zaleeha yin tsalle ta faɗa jikin Ya Ahmad ɗinta, ƙan ƙamesa tayi ƙam tare da ɓoye fuskarta a ƙirjinsa, kuka take sosai kamar ranta zai fita don sosai ya tsutstsula mata bel ɗin, Ya Ameenu na ƙoƙarin ƙara mata wani dukanne, Ahmad ya girgiza masa kai, alaman yabarta hakanan, da ƙyar Ahmad ya iya lallashinta tayi shiru, nan Baba Malam ya tambayeta ina take zuwa da bata kwana agidan aurenta?. Cikin matsanancin kuka tare da tsoro murya na rawa take cewa. "A garden nake kwana, Baba Malam wallahi ko ƙofar gidan ban taɓa fitowa ba , wallahi Baba Malam babu inda nake zuwa, a cikin gidan nake kwana." Sosai sukasha mamaki, amma sanin halinta da taurin kae irin nata yasa suka yarda cewa zata aikata hakan, a hatsale Habu yace. "To meyasa bazaki kwana cikin ɗakin kiba ko dai ƙarƙashin sirran aka nuna miki akace miki nanne ɗakin kwananki?." kai ta jujjuya cikin tsananin tsoro dan a duniya dai Zaleeha bata son abinda zai taɓa mata lafiyan jikinta murya na rawa tace. "Ni tsoronshi nakeji shiyasa nake fita woje." kai kawai Baba Malam ya jujjuya dan har ga Allah shi ya yarda Zaleeha tsoron takeji dan ya santa matsoraciyace bata son abinda zai taɓa lfyarta, kana kuma duk mace budurwa akwai tsoron namiji a ranta musamman in ance mijintane tofa akwai wannan tsoron da taraddin haɗuwar forko dana biyu wasu harma na uku. Wannan tunanin yasa Baba Malam yayimata faɗa tare da Nasiha, haka tayi kuka harta godewa Allah. Mama kuwa yau saboda tsaban ɓacin ran dake cinta kasa cewa komai tayi, tuni ma tabar musu falon, don idan ta tsaya zata iya dannawa Ameenu daya dakar mata ƴa ashar babu ruwanta da surkuntaka. Nan take Baba Malam yasa Mamy tashirya inda taɗauki Zaleehan ita da Ya Ameenun suka maida ita gidan su Saifuddeen, har gaban Ummi suka kaita, nan sukaiwa Ummi bayanin cewa wai agarden take kwana, nan sukaita bawa Ummi da shi Saifuddeen ɗin haƙuri, suka sa itama ta basu haƙurin nan su Ummi suka nuna cewa bakomai ya wuce, sosai Ummi taji tausayin Zaleehan ya kama zuciyarta, don kallo ɗaya zakayi mata kasan cewa andaketa, don ga jikinta nan duk yayi wani iri, sam Ummi bataji daɗin hakan ba. Nan Su Mamy suka kai Zaleehan har ɓangarenta, sannan suka ƙarayi mata nasiha, daga haka suka barta, inda takwanta tana meda numfashi, sosai takejin wani irin tsanar Saifuddeen ya ƙara ninkuwa acikin zuciyarta, ayanzu tanajin zata iyayi masa komai don baƙanta masa, domin akansa ne aka mata irin wannan azaban. Haka ranan dai ta wuni kuka , da yamma Belkeesu tazo nan tai ta ƙara zugata, hakama Mama ta kirata tai ta zageta wai me take jira da gidan tunda dai ba gidan ubanta bane to tabar musu gidan. Kada kuma ta bari wannan nakasashen ya rabata da budurcinta, harda cewa ta kwana duk inda takeso amman dai ta kare budurcinta. Koda dare yayi kamar kullum nan ta kwana cikin garden ɗin, shiko Saifuddeen yanzu abin natama dariya yake bashi, dan in gari ya waye ta fiti kamar ba itaba, shida kanshi ya yarda tana son ƴan uwanshi da Umminshi. Yau kwana uku da faruwan abun ,wanda yayi dai-dai da cika kwanaki goma da tayi a gidan, da yamma Adda Rahma tazo, duk da Raliya ta sanar mata komai amman sai takega kamar sharri sukewa Zaleeha dan yadda take nuna muso da kulawa. ita kuwa Zaleeha harga Allah har cikin ranta take son kowa na ahlin Saifuddeen ita dai shine bata so. Bayan anyi sallan ishane Ya Ahmad da Aunty Lubna suka zo gidan don sallaman Zaleeha dan gobe zasu koma Abuja, falon Ummi suka fara zuwa suka gaidata, kana Ya Ahmad ya bawa Ummi haƙuri akan ƙuruciyar Zaleeha, cikin jin daɗi da ganin dattakun yaron Ummi tace, "In sha Allah ba komai yarin tace." daga nan Saifuddeen yayi musu jagora zuwa side ɗinsu, sai dai kafinma su iso tuni Zaleeha ta tafi makoncinta, koda suka dudduba ɓata nan, sai Saifuddeen ya sanar musu inda taken, sosai ran ya Ahmad yayi matuƙar ɓaci, Auntƴ Lubna ce taje cikin garden ɗin ta kura ta, amman tasha jinin jikinta ganin yadda Aunty Lubnanma ta haɗe mata fuska, jiki a mace ta shigo, ganin ya Ahmad ɗinta ne yasa tayi saurin ƙarasawo cikin falon gefenshi ta zauna tare da manna kanta bisa damtsen hannunshi kawai sai ta saki kuka, abin mmki saiga Ahmad ya fara rarrashinta. nan yayi ta lallaɓata da yi mata nasiha da alƙawuran abubuwa masu daraja a rayuwarta yace. "Ni dai fatana da roƙona a gareki kawai kiyiwa mahaifinmu biyayya kada ki kunya tashi, ki zauna ɗakin mijinki ni kuwa babu abida bazan miki ba, ammanfa muddin kika saɓawa umarnin Baba Malam Zaleeha ki mance da cewa na sanki kin sanni. ki dena kwana a wojenan cikin ciyawin can, Zaleeha dame na rageki me ban mikiba na kayan ɗaki, ki gaya min in akwai abinda ban miki shiba in miki? ". Cikin share hawayenta tace. "Kamin komai Ya Ahmad ngd ." Kai ya jinjina tare da cewa. "To ki zauna ɗakin mijinki kiyi mishi biyayya ki bashi duk wani haƙƙinshi dake kanki." kai ta gyaɗa mishi a ranta kuma ceqa take. "Kayi haƙuri Ya Ahmad bazan iyaba." da haka dai suka sallameta suka tafi, inda Saifuddeen yayi musu rakiya har bakin motarsu, nan Ya Ahmad ɗin ya ƙara bashi haƙuri. To ranar dai Zaleeha a falonta ma ta kwana dan yanzu tayi shirin fara tarfa mishi rashin mutunci a cewarta sai ya saketa wanima bai saniba, sai dai kafinma ya dawo daga rakiyar su Ya Ahmad ta ɓingire tayi bacci, sabida sanyin ac da ƙamshi da tsabtan falon, koda yazo wuce kanshi ya girgiza tare da taɓe baki kana ya ɗan naga kafaɗunshi alamun babu ruwanshi da ita ya wuce side ɗinshi. Koda gari ya waye sai ta maida shirinta yau. Ƙarfe sha ɗaya da kwata na dare Saifuddeen yayiwa Umminshi saida safe black coffe ɗinsa, wanda Ummi ta haɗa masa ya ɗauka, tare da fita daga ɓangaren Ummin, sam ko kaɗan baiji tausayin Zaleehan nadaga abun da akayi mata ba, don shi sam baima fahimci cewa, an daketa ba. Kaitsaye part ɗinsu ya nufa, koda ya ƙarasa cikin falon nata, direct ɗakinta ya nufa dan yau wuni zumbur bai gantaba, haƙƙinta ne kuma a kanshi yasan halin da take ciki, kuma Umminshi ma ta umarceshi da ya shiga ya duba lfyarta, dan tunda tazo gidan bata taɓa fashin fitowa gaida Ummi safe da yamma amman yau tunda tazo da safe babu wanda ya kuma ganin fitowanta, sai dai Ummi tasa Raliya tazo har ɗakinta ta tambayeta lfya kuwa bata fitoba, to nan tace kanta ke ciwo, kuma hakan baya rasa nasaba da kukanda take yawanta yine a kwanaki ukun nan kuma ga dukan Ya Ameenu. A hankali ya nufi bedroom ɗinta   Ita kuwa Zaleeha zuwa lokacin harta zage zip ɗin rigarta inda take kwance akan gado, sosai takejin jikinta nayi mata wani irin raɗaɗi na musamman akan dukan da tasha yayi tsami a jikinta. Ƙarasowa cikin ɗakin yayi, tare da ɗan tsayawa ahankali yake ƙare mata kallo. Duk da kasancewar idanunta a lumshe suke, amma ba bacci take ba dan hawaye nata kwaranya daga idanun nata, jin motsin mutum acikin ɗakin, da kuma ƙamshin turarensa daya cika mata hanci yasanyata juyowa,  idanunsu ne suka sarƙe acikin najuna, da sauri tatashi daga kwancen da take, tare da ɗanja baya da alamun tsoronshi, takurawa tayi wuri ɗaya tare da sakin kuka, cikin rawan murya tace. "Dan Allah malam meya kawoka ɗakina?,Dan Allah ka fita, Ni tsoronka nakeji." Dubansa tayi duba irin mai cike da tsantsar tashin hankali da wahala cikin takaicinsa tasa tafin hannunta ta sharce hawayenta taso ta zuba mishi fitsara da tijara, sai kuma hakan ya gagareta sabida yayi mata kwarjii da yawa, gashi ya tsareta da manyan kyawawan idanunshi da suke da kwarjin mai tarin yawa madadin tayi masifa sai kawai ta tasashi a gaba taci gaba da kuka murya na rawa tace. "Dan Allah kaji tausayi na, wallahi ina sonshi bazan iya rayuwa da wani namijiba in ba shiba". kanshi ya tankwashe yana kallon yadda laɓɓan bakinta ke motsawa yana mai jin wani irin suya da ƙuna da zuciyarsa keyi, Ita Kumahakan da yayine ya tuno mata ashefa kurmane ma, cikin zubda hawaye tace. "Ayi mutum shi burinsa kawai ya raba masoya, ni bana son ko wani ɗa namiji sai shi, nace maka bazaka samu farin ciki daga gareni ba, saboda kai ƴan uwana suka tsaneni, saboda kai yau an wayi gari Ya Ahmad ma ya nuna zai iya tsanata sabida kai aka ɗaga hannu aka dakeni da sunan dukan dole in zauna da kai, am medani kamar jaka ko ganga abu kaɗan akama jibgata!." A hankali jiki na rawa turo da ƙafafunta ƙasa tare da miƙewa tsaye, hannuwanta tasa tana share hawayenta da wasu ke korar wasu, cikin kuka tace. "Ni dai ka fitamin daga ɗaki!." Taƙare maganar tana meyi masa nuni da ƙofar fita daga cikin ɗakin. Ganin ya kafeta da mayun idanunsa ne yasanyata ƙara jan baya kaɗan tace. "Waikai kam me yasa kake abu kamar mahaukaci ne da ina maka magana kana kallona, meyasa baka babbance so da ƙiyayya? Nace maka inada wanda nakeso". da sauri ya rumtse tafin hannunshi wai a gaban shi take ce mishi tanada wanda takeso tana matsayin matarsa. Ita kuwa cikin muryar kuka tace. "Tunda bazaka fitaba ai sai kayi ta zama kai in mun zauna ɗaki ɗaya ma me zaka iya min?, da idanu kaman na....." Batare da ta tantance ƙarasowarsa gareta ba, saiji tayi ansa mata ƙafa inda aka kwasota tuni tatafi su tafaɗa kan gado, cikin matsanancin ɓacin rai haɗi da rufewar ido, yasanya hannunsa inda ya jawota jikinsa, a harzuƙe yakama duka hannayen ta biyu ya, murɗe mata hannun nata yayi da ƙarfin gaske ya maidasu bayanta, hakan ne yasa tasaki wani irin ƙaran azaba,  sosai ransa ya ɓaci dajin kalamanta na kiranshi misaltashi da aikin mahaukaci, abinda Zaleeha bata saniba mutun ɗaya ya taɓa.mishi wannan furucin Iya Bukku kuma itama ya bata haƙwarenta a hannunta, idanunsa ne suka sanja kala inda sukayi jajur dasu, take jijiyoyin jikinsa suka mimmiƙe, sam idan akwai wani abu daya tsana to baiwuce zagi ba, zai iya tolereting komai amma banda zagar masa nasabarsa, haka kuma zai iya jure kowani zagi, amma koda wasa kada kayi kuskuren ƙiransa da sunan  mahaukaci. Azafafe yasanya hannunsa inda ya kamo ƴan ƙananun laɓɓanta, da yatsunsa biyu yasanya da ƙarfi ya shiga ɗana matasu akan laɓɓan nata da ƙarfi-ƙarfi, cikin matsanancin zafi haɗi da raɗaɗin da bakin nata keyi mata, tasaki wani irin kuka haɗi da ihu,  sam kukanta ko ihunta basu tsai dashi daga horar da ita da yake ƙoƙarin yi ba, sake matse bakinta yayi, yayinda ya sanya hannunsa inda yasake matseta ƙam, cikin kuka haɗi da masifar zafin da takeji tasoma jijjiga kanta, amatuƙar wahalce tasake sakin wani gigitaccen ƙara, tare da faɗin. "Wayyo Allah na bawani a kusane, ku taimakeni dan Allah, wayyo Ummi ɓarayi ɓarawo!." ina su Ummi ba jinta zasuyiba bare ta kawo mata agaji. Sake danneta yayi tare da sanya hannunsa ya murɗe lips ɗinta, tuni tanemi bakin ihu da kuka'n ta rasa, nan fa tasoma harba ƙafafunta tare da yarfa hannuwanta, zafin da takeji yakai zafi domin tuni idanunta sun fara fitar da sabin ƙwalla,  aƙalla saida suka ɗauki kusan mintuna 5 ahaka, sosai tafita hayyacinta kuka take kamar ranta zaifita, ido take jujjuya mishi da bashi haƙuri, "Wayyo dan Allah kayi haƙuri wallahi bazan sakeba." cikin ɓacin rai ya tureta kan gadon, kana ya rufa mata baya, rumtse idonta tayi da ƙarfi jin ya konto kanta, da sauri ta kuma buɗe idanun jin ya fincike rigar tata ya cillata gefe, tuni ƙirjinta ya baiyana irin bainar nan na ziraran miraran, ido ta zazzaro da ƙarfi jin tafin hannunshi kan breast, cikin wani irin kiɗima da farga ta riƙo damatsan hannunshi tuni jikinta gaba ɗaya tsuma yakeyi murya a hargitse tace. "Wayyo Allah na,na shiga uku dan ALLAH na tuba kayi haƙuri". Sai kuma taja wani irin dogon numfashi jin yadda yake murza ƙirjinta da sarrafa shi cikin tattauanawa tafin hannunsa, Wani irin kuka ta sake tare da yunƙurawa da niyar zata ƙwace kanta daga gare shi, sai kuma ta koma ta konta jin ya sake mata nauyi shi ƙafafuwan ta fara harbawa tare da jujjuya mishi kai kana tana ta kiciniyar kwace kanta. Shi kuwa Saifuddeen hannunshi ya ɗauke daga kan ƙirjinta kana ya danne hannayenta da taketa riƙe nashi hannu, sunkuyowa yayi ya manna bakinshi kan breast ɗinta na hannun dama, kana yasa hannunshi ɗaya ya haɗe hannayenta cikin hannunshi ɗayan, wasu irin abubuwan masu wuyar fahimta da misaltawa yakeyi suna shiga jikinshi da zuciyarshi karon forko a rayuwarshi da yake cikin wannan yanayi, wani irin sassanyan tsotsan kan nipples ɗinta yakeyi tare dasa hannu shine yana murza kan ɗayan. wasu tagwayen numfarfashi yake sauƙewa tamkar zasu fita da ransa gaba ɗaya jikinshi suma da karkarwa yakeyi, haka ya sashi sarrafa ta da zafi-zafi. Zaleeha kuwa ido ya raina fata, zufane yaketa tsastsafo mata duk ta inda hudan gashin jikinta yakeyi,kuka da ihu da magiya yakeyi tamkar zata mutu, tattaro sauran ƙarfinta tayi tasa janye hannunta ɗaya cikin zafin da takeji takai hannu kan hannunshi dake murza nipples ɗinta karo na forko a tarihin rayuwarta da namiji ya taɓa mata nononta, kai ta rinƙa jujjuya mishi ganin ya zuba mata kyawawan idanunshi da suka jiye zuwa kalan bacci-bacci, murya na rawa tace. "Na tuba dan ALLAH da sonka da manzon rahma ka barni bazan sake ba, na sani zaka iya min komai". Sai kuma hawaye car-car a hankali ya zame daga kanta ya koma gefe. Da sauri ta tashi zaune can gefe ta koma,hannunta tasa ta tallabi ƙirjin nata, sai kuma wasu sabbin hawayenta suka zubo sabida jin yadda nonanta ke zafi musamman bakinsu dan sosai ya tumurmusheta. da sauri ta janye hannunta tare da yarfa hannun tana mai zubda hawaye tare da fidda sautin. "Shhhhhhh wayyo zafi wayyo ka cinye min nona". wani irin kallo mai ɗauke da tsananin gargaɗi da alamun ki kiyayeni yayi mata, can cikin ransa kuwa dariya yakeyi ganin yadda yakeyi to wannan in an ratsa budurcinta sai yaya, haɗe fuska yayi tare da watsa mata mugun kallo kana ya wurgo mata rigar ta sannan ya yunƙura ya hau kekenshi, nan ya murza wheelchair ɗinsa kai tsaye ya fice daga cikin ɗakin. Wani irin ihu tayi tare da soma buga kanta ajikin bango, kuka take sosai da sosai, yayinda bakinta ke mata wani irin azababben raɗaɗi, har takai ga tanajin kamar ma laɓɓanta basa kan fuskarta ga nononta da sukayi jazir ɗan bakunan sai wani zut-zut sukemata babban tashin hankalinta in sunyi zut-zut ɗin nan har ƙasanta takeji canma yana mata wani irin abu mai sa tsikar jikinta miƙewa. ga hsnnunta da takeji kamar ya karya mata sune Kuka tacigaba dayi inda ta laluɓo wayarta tare da cewa. "Mugu kawai azzalumai zai cinye min nonona ya wani kamani yanata sha kamar ya samu tom-tom ya lallatse min abuna ya meyar min dasu second hand". kaitsaye ta dannawa Mamanta ƙira, bugu biyu kuwa maman ta ɗaga, jin kukan Zaleeha baƙaramin tayarwa da Mama hankali yayiba, cikin matsanancin tashin hankali Mama tace. "Ke Zaleeha yi shiru gaya min meya sameki? wani ɗan abu kazan ubanne ya ta ɓaki?." Cikin matsananci kuka na raɗaɗin zafin da laɓɓanta da nononta keyi mata tace. "Wayyo Mama zai kasheni, wallahi Mama bazan zauna ba, kasheni zaiyi dukana yake tayi tun ɗazu, nikam guduwa zanyi wallahi bazan zauna ba, shi ya dakeni kuma ƴan uwana ma su dakeni, Wayyo Allah nikam nashiga uku!." Zaleeha tafaɗi maganan cikin matsanancin kuka. Wani wawan shar mai tsada mama ta lailayo inda ta bankawa Saifuddeen shida gaba ɗaya zuri'arsa, cikin bala'i tace. "Narantse babu wani wanda ya isa, ya sake dukanke, kujimin hegen nakasashshe yaro mai jajayen kunnuwa ashe dama ya aureki ne don ya tozartamin ke,  wato dama ashe ba iya nakasa bace matsalar tasa harma da ciwon mugunta wato yaga zuƙeƙƙiyar yarinya yanaso ya lallatse min ke ko, to wallahi bazaki zauna ba, bai yiwuwa su su dakeki shima ya dakeki, sam ni ban haifi musu jaka ba, saboda haka nabaki umarnin ki gudu, maza ki tattara kayanki ki gudu Numan gidan Uncle Solomon, bankuma yarje kifaɗawa kowa inda kike ba, duk sai nayi maganinsu." Jin abun da Maman nata tafaɗa yasa Zaleeha tacika da murna, cikin kuka tace da Maman nata. "To." Ko kashe wayar bata tsaya yiba tashiga zuba kayanta acikin akwati, akwatuna 4 tacika da kaya, nan taɗauki duk wani abu nata mai amfani dake cikin gidan,   key ɗin sabuwar motar da Saifuddeen ɗin yasaya mata cikin kayan aure ta ɗauka, nan tafito inda ahankali take jawo akwatunan tana fitowa dasu,   babu kowa a compound ɗin gidan hakan yasa sauri-sauri tagama loda akwatunanta acikin mota, Kana ta koma cikin gida da niyar asuban fari zata bar gombe ta nufi Numan ta jihar adamawa, nan kuma ta ƙara yin mgna da Mama inda take ce mata ta bawa Zahira system ɗinta ta kawo mata da asuba. Haka kuwa akayi ana fitowa massalaci Sallan asuba ta, fito abinta kamar ko yaushe taje ta gaida Ummi to daga side ɗin Ummune ta wuce harabar gidan, tana zuwa ta shiga cikin motan tayi mata key,  maigadi ne ya buɗe mata gate ɗin gidan, cikin yanayi naɗan mamaki ya leƙa fuskarta wanda tayi caɓa caɓa da hawaye, aɗaɗare yace. "Ranki ya daɗe fita zakiyi ne?" Batare data basa amsa ba ta cilla hancin motar tata waje, gab ƙofar gidan taga Zahira na tsaye gefen keke napep, ita kuwa Zahira ganin Zaleehan yasa tayi sauri ta ƙarasa jikin motarta, system ɗin nata ta miƙa mata, da sauri ta amsa ta ajiye bisa kujerar baya, sannan suka ɗanyi wani mgn ƙasa-ƙasa kana ta danna hancin sabuwar motar dawani irin speed ta hau kan titi, gudu take sosai kamar zata tashi sama. Kana ita kuma Zahira ta shiga napep ɗin ya juya da ita. Ahmad ne ya bi motar Zaleeha da ido wanda duk abinda sukayi a kan idonshi dan fitowarshi kenan daga massalaci yaga Zahihara ta fito cikin napep tana raɓe-raɓe shiyasa ya koma gefen wani fulawa ya zuba mata ido. Saifuddeen Yana dawowa masallaci yau sai bai wuce side ɗin Ummi ba kasan cewar a makare ya tashi baiyi wonkaba ya wuce masallacin, shiyasa yanzun ya dawo side ɗinsu yafi son sai yayi wonka kafin yaje cikin gidan. Yana shiga side ɗin nasu ya nufi ɗakin Zaleeha dan ganin ƙofar a rufe yake, ɗan ƙwanƙwasa mata ƙofar yayi saida yaji a jikinshi duk baccinta ta farka sannan ya juya ya nufi falonshi. Yana barin bakin ƙofar ɗakin nata kai tsaye bedroom ɗinsa ya nufa. Yana shiga rage kayan jikinshi yayi kana ya wuce cikin Bathroom ɗinshi. kwance yake acikin  haɗaɗɗen jakuzzien wankansa ya hango haske mai yawa alamun tashin mota, take kuma saiyaji gabansa ya faɗi. "Hasbunallahu wani'imal wakil!." Yafaɗa a ranshi, sake maida kansa cikin jakuzzie'n yayi, lokaci guda tunaninta ya shiga yawo acikin ransa, sosai yayi mamakin yanda ta jure kwanan garden mai cike da sanyi da sauro da dai sauransu, wai duk dan kada yayi mata wani abu. Can gidansu Zaleeha kuwa, a fujajan Mama tanufi falon Baba Malam, suna zaune shida Ƴa Habu, da kuma Ya Ameenu, wanda yana fitowa masallaci ya taho gaida surkin nashi bappanshi kuma kamar yadda yakeyi wasu lokutansai Mamy. Ita ko Mama a hatsale ta banko labulen, babu ko sallama cikin tsananin masifa haɗi da bala'in dake cinta tace. "Dukkan ku hankalin ku ya kwanta, shikenan ni har abada kune zaku cigaba da nakasamin rayuwar ƴaƴa na, to shikenan saiku zuba ruwa aƙasa kusha, shidai mahaukacin da kuka aurawa Zaleeha yafara aikinsa, tunda gashi taƙirani tana kuka kancewa ya yi mata dukan tsiya, ko tashi bata iyayi, to wallahi bazan taɓa lamuntan haka ba, nidai kam ban aifawa wani ƙaton namiji jaka ba, dan haka wallahi dole sai ya sakarmin ƴata,  bai yiwuwa ku ku daketa sannan wani ƙato ma daga waje ya dake ta, wallahi tagama zama dashi kenan tunda dai yakai hannunsa jikinta, ban haifawa kowa jak!." Da ƙarfi ta faɗa bisa kujerar dake bayata sabida tsananin tsoro da firgitan da tayi da jin wani irin azabebben tsawan da Baba Malam ya daka mata. kame jikinta tayi tare da rumtse ida nunta gaba ɗaya jikinta rawa yakeyi tamkar mazari, kawai jira take taji ta inda zai r...! Littafina na kuɗine in kina buƙata turo katin mtn na 300 ta wannan number 09097853276 ko kimin transfer ta asusuna na 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. By *GARKUWA'N FULANI* [05/09, 10:46 am] اسماء بشير: *INAH ZAKI DAMU!!!* daga jin sunan labarin ba saikun tambaya ba kunsan labarine daya kunshi al'amuran da suke faruwa a cikin duniyar nan tamu wanda tunani ko zato bai taba kawowa ba, ban tausayi al'ajabi soyayya fad'akarwa da ilimantar wa duk zaku samu a cikin littafin nan da naira 200 kacal littafin marubuciyar nan da kuke nishad'antuwa da rubutun ta *SISIN MAMA* kada ku bari a baku labari dan samun mallakar littafin ku nemeta a wannan number d'in 08107499249. Aisha Aliyu Garkuwa: Sosai ta firgita da tsawan da Baba Malam ɗin ya daka mata, a zatonta zai kai mata dukane a nata banzan tunani kenan dan bashi yiwuwa namiji mai kamala da dottuku da tausayi ya daki matarsa, har sai irin dukan da shariya ta lamunce musu. Duk da Mama taci duka. Ganin yayi kwaffa ya jinjina kaine yasa ta Sake gyara tsayuwa ta, cikin rashin tunanin zuciya tace. "Tun wuri ma ku ƙira ku sanar dashi, ya sakomin ƴata, don wallahi bazan taɓa lamunta, haka nan ya dakar min ƴa ba!." Cikin matsanancin ɓacin rai da ƙunan zuciya Baba Malam ya kumadaka mata wata gigitacciyar tsawa wacce ta hautsine hanjin cikin Mama, saboda tsabar firgici  da kuma yanda tsawan yazomata abazata, saida tayi baya-baya inda ta faɗa kan kujera. Su Mamy da Ya Aminu kuwa, sosai suka shiga mamakin irin tsawan da Baba Malam ɗin yayiwa Mama wanda yake nuna zallan ɓacin ranshi,  saɗaf-saɗaf Ameenu da Mamy suka fice sukabar cikin falon. Cikin tsananin ɓacin rai Baba Malam yace da Mama.   "Ya'isa haka, kinyi min ba sau ɗaya ba, ba kuma sau biyu ba, duk ina ƙyaleki, to kisani ayanzu kin kai matakin da bai yiwuwa na ƙyaleki, sai yaushe zakiyi hankali ne? sai yaushe ne zaki samarwa kanki nutsuwa? sai yaushene ɗabi'ar musulamai da imani zai kama zuciyarki? ako yaushe idan kin tashi yin abunki bakya sa tunani acikinsa,  ashe rashin hankalinki har yakai ki tsaya akaina, gaban ɗana, ɗanki kuma surukin ki kina me ɗaga mini murya, to wallahi kisani daga yau na daina ɗaga miki ƙafa akan komai, badai zaman lafiya ne bakyaso ba, to shikenan zanbi dake aduk yanda kikeso. Sannan batun Zaleeha ki sani ƴata ce, ina da ikon da zansa ahukunta ta, aduk sanda tayi mini laifi, haka kuma  Saifuddeen mijinta ne, shima kuma yana da ikon da zai hukunta ta aduk sanda tayi masa laifi." Gyara zaman babbar rigarsa yayi tare da duban Mama cikin ɓacin rai da kuma tsanan halayenta yace. "Wallahi namiki rantsuwa Haleema aduk sanda kika sake, wata matsalar ta auku agidan auren Zaleeha, wanda har ya kasance da sa hannunki aciki, tabbas zan shayar dake mamaki,  tashi ki ficemin daga falo!!." Ya ƙare maganar murya a kausashe, kana yana meyi mata nuni da ƙofar fita daga falon. Cikin hanzari Mama ta-tashi inda ta fice daga cikin falon, duk da cewar tsawan da yayi mata ya tsorata ta sosai, amma hakan baisa ta daina cika da batsewan da takeyi ba, sosai tacika tayi fam, tana ƙarasawa part ɗinta ta saki dogon tsaki, tare da yin ƙwafa, abayyane tace. "Dani kuke wasan, ai dai nikam nawa ƙuncin kuma ya ƙare saura naku, yanzu ne aka fara buga wasan, sannan yanzu ne kuma tashin hankalinku zai fara, wallahi sai na shayar daku baƙin ciki, fiye da wanda kuka shayar dani". Tana ƙarasawa ɗaki, wayarta ta ɗauka inda ta dannawa number'n Ruda ƙira, bugu uku kuwa Ruda ta ɗaga wayar,  Mama na fitar da huci tayi mawa Ruda bayanin duk wani abu dake faruwa, shewa Ruda tayi tare da cewa. "Karki wani damu hankalinki badai kinsa ta gudu ba, shikenan ki manta dasu kawai, nan da kwana 2 zaki gansu arana karki damu kinji dai boka ya gaya mana zaisa ta daina jin tsoron ɓacin ran Babanta da son yimishi biyayya, kinji yace mana komai zai tafi yadda mukeso." Murmushin mugunta Mama tayi tare da aje wayar, kwanciya tayi akan gado, jin ranta takeyi fes, hakanan takejin kamar an rabata da ƙaya, domin kuwa tunda Zaleeha'nta ta auri gurgu, kullum kwanan duniya da baƙin ciki take kwana, yanzu kuwa Allah ya yaye musu, ya rabasu da masifa saboda haka ta gyara kwanciyarta donyin baccin safe, wanda ta ɗan kwana biyu bata yi shi ba. Can gidan su Saifuddeen kuwa, Ahmad na ganin tashin motar na Zaleeha'n, ya bita da kallo har sai da ta ɓacewa ganinsa, mamakin inda zataje awannan sanyin safiyan yake, yasan dai hakanan bazata fita da sanyin asuba ba kuma dai yasan hukunta bai ƙare ta koma wurin aikinta ba bare yace ko can ta sammakawa. Koma cikin gidan yayi, inda kai tsaye ya nufi ɓangaren Ummi, da sallama ɗauke abakinsa ya shiga cikin falon, zaune ya iske Ummi akan lallausan darduman dake shumfuɗe tsakiyar ɗakin, gefe kuwa Raliya ce, yayinda ummin ke jan carbin dake hannunta, ƙarasa shigowa cikin falon yayi, nan ya zauna abakin carpet ɗin tare, da ɗagawa Ummi gaisuwa, cikin girmamawa,  fuska ɗauke da murmushi Ummi ta amsa masa gaisuwan nasa, duban Ummin yayi tare da cewa. "Naga Zaleeha tafita yanzu, ko ta faɗa muku inda zata jene?." Ɗan jim Ummi tayi tare da cewa. "Tafita kuma, da safen nan?." Kai Ahmad yajinjina tare da cewa. "Yanzun naga fitarta." Girgiza kai Ummi tayi tare da cewa. "Ɗazun kuma tabar nan, don tazo ta gaisheni, saidai kuma sam bata faɗamin cewa zata fita ba, amma wata ƙila shi Saifuddeen yasan da fitarta." Kai Ahmad ya jinjina, tare da neman kawar da zancen ta hanyar duban Raliya, cikin kulawa yace. "Please haɗamin tea mana, yau so nake nafita da wuri." Da "To." Raliya ta amsa sannan ta tashi ta wuce kitchine, shi kuma kaitsaye ya wuce ɓangarensu don yin wanka. Can wajen Saifuddeen kuwa fitowarsa daga wanka kenan,  cikin nutsuwa ya gama goge jikinsa, inda ya sanya towel ya shiga tsane lallausan sumar kansa, wanda yaji aski irin na zamani, uwa uba yasha gyara sai ƙyalli yake, yana kammala goge jikin nasa, ya ɗauki body lotion ɗinsa mai daɗin ƙamshi, cikin nutsuwa ya shiga shafawa, yana kammala wa, ya shafe jikinsa da wani irin body oil spray mai matuƙar ƙamshi,  take gaba ɗaya ɗakin ya gauraye da ƙamshin sa,  ahankali ya tura wheellchair ɗinsa har zuwa gaban haɗaɗɗen drawer ɗinsa,  buɗe drawer'n nasa dake shaƙe da kaya yayi,  hannunsa yakai zuwa ɓangaren da ƙananan kayansa ke jere,   wani crazy combat jeans Black colour haɗi da wata D&G t-shirt mai kyaun gaske ya zaro, daga cikin tarin kayan nasa, sosai drawer'n nasa ke cike da kaya, sai kace wani kanti, wani kayan ma har mantawa yake dasu, dan ma duk bayan wani ɗan lokaci yana kyautar da kayayyakin da sosai musamman wa mutanen ƙungiyar su Jonapwd. Cikin yanayinsa na nutsuwa ya zura kayan ajikinsa, wanda suka matuƙar amsar farar fatarsa,  wani silver watch ya sanya ahannunsa, sannan ya buɗe wata ƴar glass drawer dake nan cikinsu yake aje caps ɗinsa, wata baƙar facing cap mai kyau ya zaro, inda ya ɗaura akansa, take yafito yayi wani daban dashi, ga wani irin kyau da yayi, ahankali ya tura wheelchair ɗinsa zuwa inda yake aje takalmansa, wasu flat shoe masu kyaun gaske ya zura acikin fararen ƙafafunsa, wayoyinsa da kuma laptop ɗinsa ya ɗauka, parfumed ya shafa, sannan yanufi hanyar fita daga ɗakin,  ahankali yake tafiyar da wheelchair ɗin nasa, har yasamu kansa acikin falon Zaleeha'n, ko ƙofar ɗakinta bai kalla ba haka yafice daga cikin part ɗin nasu gaba ɗaya,  direct ɓangaren Umminsa ya nufa. Kusan karo sukayi da Hayatuddeen wanda ke ƙoƙarin zuwa part ɗin nasu, ƙiransa shida Zaleeha akan cewa suzo suyi break, don su atunaninsu zuwa lokacin ta dawo. Duban Saifuddeen ɗin Hayatuddeen yayi, cikin ƙaunar Hamman nasa yace. "Wow Hammana kaga yanda kayi kyau kuwa!." Murmushi Saifuddeen yayi tare da duban Hayatuddeen, irin duban nan mai ɗauke da yanayin magana, alama yayi masa cewar. "Uhummm ." Kai Hayatuddeen yajinjina masa tare da cewa. "Fiye da kullum ma kuwa, wani lokaci Hamma nakan tambayi kaina, me yasa kai ba mace ba amma kowani kaya kasa saikayi musu kyau, saidai kuma idan na tuna da cewa Hamman nawa Namijin gaske ne, sai naji kaina ya ƙara girma, saboda samun ka amatsayin Hamma yafiyemin komai." Murmushin daya bayyana tsantsar kyawunsa yayi, cikin ƙaunar ɗan uwan nasa yasanya hannunsa inda yakamo kumatun Hayatuddeen ɗin. Dariya Hayatuddeen yayi tare da zagawa bayan hamman nasa inda ya turosa zuwa cikin falon, da shigowarsa cikin falon har falon ya ɗauki ƙamshin oud ɗin dake jikinsa. Har gaban dinning area Hayatuddeen ya tura hamman nasa,  inda Raliya da kuma Ahmad ke zaune, Raliya ne ta gaishe da yayan nata,  cikin ƙauna da kuma ganin ƙoƙarin ƴar uwar tasa na haɗa musu break fast kullum da takeyi ya amsa mata, yana tunanin gashi tasa an sallami mai akin wai duk a kanshi dan sun san yanada tsantsani.   Dai-dai lokacin Ummi ta fito daga cikin ɗaki, ganin Saifuddeen zaune yasa ta ƙara faɗaɗa fara'arta cikin kulawa tace. "Kunfito ko, ina Zaleeha'n, nace yau itama tazo cikin mu tayi break dan duk anzama ɗaya." Ummi taƙare maganar tana me jawo kujera ta zauna. Kallon Hayatuddeen Saifuddeen yayi, cikin body language yayi masa alama kan cewar yaje ya ƙirawo Zaleeha'n, kai tsaye hayatuddeen ya tafi don ƙiranta. Koda yaje part ɗin nasu, haka yayita knocking a ƙofarta, amma shiru, jin shiru ne yasashi tura ƙofar ɗakin ahankali, ɗan tsayawa yayi abakin ƙofa, da ɗan ƙarfi yace. "Aunty Zaleeha kizo muyi break, kin san dai bana iya jure yunwa." Jin shiru ba'a amsa shi bane yasanyashi ƙara kutsa kansa cikin ɗakin, nan yashiga dube dube kozai ganta amma shiru, kasa kunnensa yayi wai ko zaiji motsin ruwa a toilet, nan ma dai shiru, hakan yasashi juyawa kawai yafice daga ɓangaren nasu gaba ɗaya. Yana komawa yace musu baiganta ba, har ɗakinta ya shiga amma bakowa ciki,  fuska ɗauke da mamaki Saifuddeen ke kallonsa, to ina Zaleeha zata je kenan,  kallon Ahmad yayi wanda yake ƙoƙarin saving ɗin kanshi, yana cewa. "Maybe bata dawo daga fitan da tayi bane." Gane abun da Ahmad ɗin ya faɗa ne, yasa shi ɗan lumshe idanunsa,  Ummi ne ta dubesa, cikin kulawa tace. "Dama kasan da fitarta ne? dan Ahmad yace yaga fitanta tun da sanyin safiya koma ince asuba." Idanunsa ya rumtse tare da girgizawa Ummi'n kai, alaman "A'a."  ɗan jim Ummi tayi take kuma, wani tunani yazo mata inda ta raya aranta cewa ko gida Zaleehan taje, nan dai tace tasan cewa zuwa anjima zata dawo. Raliya ne tayi saving ɗinsu inda suka soma cin abinci cikin nutsuwa, shidai Ahmad hakanan jikinsa ya basa wani abu daban, yasan babu dalilin da zai kai Zaleeha gida awannan sanyin safiyan, idan da ace akwai dalilin ma to tabbas yasan da zuwa yanzu ansanar dasu. Haka suka kammala break fast ɗin nasu cikin nutsuwa, Ahmad ne ya miƙe dan yana so yaɗan fita, shikuwa Saifuddeen cikin falon na Umminsa ya koma, inda ya sauƙa daga kan kekensa, kwanciya yayi akan doguwar kujera tare da jawo laptop ɗinsa, ya ɗaura akan cikinsa, nan ya buɗe cikin nutsuwa yashiga yawo a internet, Hayatuddeen ma zama yayi akusa da hamman nasa inda ya jona game a tv plasma ɗin dake cikin falon, hakan yasa kowa da inda ya bada hankalinsa, Ummi kuwa ɗaki ta koma dan tanason kimtsa wasu kayyakin gudumowan biki da aka kawo mata, nan Raliya ta bita inda suka shiga aikin tare. Sosai yabada hankalinsa akan aikin da yakeyi, hakanne ma yasa har lokuta suka ja batare daya sani ba, inda Hayatuddeen kuwa tuni ya kwanta akan carpet yayinda bacci ya ɗaukesa, da dukkan alama jiya kusan kwana yayi yana chat, don abu ɗaya ne ke saka Hayatuddeen bacci da rana, shine idan bai samu enough bacci da dare ba, to dole da rana zaiyi bacci, wai abun ma yazo masa da sauƙi don yau basu da lectures sai ƙarfe 2:00 pm, shi yasama yaji gwamma yayi baccinsa, kafun time ɗin. Ummi ne tafito daga cikin ɗakinta, duban Saifuddeen tayi, ganin kaman baisan da zuwanta ba yasa ta shafi gashin kansa, ɗago da kansa yayi inda ya dubeta, ganin Umminsa ya sashi narke fuska,  akasalance yayi mata alaman sannu da fitowa, hakanan yake aduk sanda zaiga Umminsa, to fa raki da shagwaɓa kawai zai dinga yi mata, wani lokaci ko Hayatuddeen bai  kai Saifuddeen yawan shagwaɓa ba. Kansa Ummi ta shafa, cikin kulawa tace. "Inajin gabana yana ɗan faɗuwa tun ɗazu, ya kamata kaje ka duba Zaleeha kota dawo." Fuskansa yaɗan kwaɓe, tare da tashi zaune miƙa yayi inda yayiwa Ummin alaman cewa ya gaji, murmushi kawai Ummi tayi tare da ƙwala ƙiran Raliya, wanda ta shiga kitchine don ɗaura musu lunch, don a time ɗin kusan ƙarfe ɗaya ake nema. koda Raliya'n tazo, cewa da ita Ummi tayi, taje ta duba part ɗin nasu Saifuddeen ko Zaleeha ta dawo. Da "To." Kawai Raliya ta amsa, nan tafice daga cikin falon, koda taje part ɗin, haka tayi ta kwaɗa sallama amma shiru ba amsa, alaman bata dawo ba kenan,  haka ta fito daga falon, koda ta kawo compound ɗin gidan, parking space ɗinsu ta duba, nan taga babu motar Zaleeha'n, alaman kenan bata dawo ɗin ba, nan ta koma inda ta faɗawa Ummi cewa "Zaleehan bata dawo ba." Ɗan jim Ummi tayi nan tace. "To bari dai zuwa yamma, idan bata dawo ba sai muƙira gidansu mu tambaya, ko wani abunne ya faru." Shidai Saifuddeen ƙala baice ba, saboda ae Zaleehan bata maidashi miji ba, because da zata fita kanta tsaye ta fita, babu neman izini ba komai, wannan yasa shima bazai shiga cikin shirgin nemanta ba, sauƙa daga kan kujeran ma yayi, inda ya hau kan wheelchair ɗinsa, da kansa ya tashi Hayatuddeen, inda yace yaje ya ɗauro alwala yazo su wuce masallaci, don yin sallan Azahar, part ɗinsu yaje inda yayi alwala, koda yafito yasamu Hayatuddeen tsaye nan suka wuce masallacin dake kusa dasu. Ummi kam dai hakanan takejin wani abu dangane da tafiyan Zaleehan, sosai take fargaban abun da zuciyarta ke raya mata, aranta tana fatan ma Allah yasa ba hakan bane. Saifuddeen kuwa koda suka dawo masallaci, part ɗinsu ya nufa, nan ya nufi bedroom ɗinsa, inda ya kwanta ya ɗan huta. Abu kamar wasa tun ana ƙarfe ɗaya, biyu, uku, har zuwa ƙarfe huɗun yamma babu Zaleeha babu alamarta, sannan daga gidansu ba'a ƙira ance tana can ba, abun da yayi mugun ɗaga hankalin Ummi kenan, nan tatura akayi mata ƙiran Saifuddeen, zuwa yanzu yasake wanka cikin wasu tsadaddun riga da wandon jeans masu kalar navy blue, sosai sukayi masa kyau. Dubansa Ummi tayi cikin nuna damuwarta afili tace. "Gabana faɗuwa yake Saifuddeen, har yanzu fa Zaleeha bata dawo ba, kuma kace bata sanar dakai fitan ta ba." Kansa ya jinjinawa Ummin tare da kamo hannunta, cikin kulawa yayi mata alama da body language ɗinsa, kan cewar. "Kada ta damu Zaleehan zata dawo ne, wata ƙila tayi nisan zango ne." Girgiza kai Ummi tayi cikin kulawa tace. "Bari dai naƙira gidan nasu naji, ace mutum ya fita tun gari bai gama haske ba, kuma ace har yanzu kusan ƙarfe 5 ake nema amma baidawo ba." Nan Ummi ta ɗauki wayarta, inda ta danna wa number'n Mamy ƙira, don duk gidan number'n mamy kaɗai take dashi. Bugu biyu aka ɗauki ƙiran, amutunce suka gaisa da Mamyn, cikin nutsuwa Ummi tace. "Dama cewa zanyi ko Zaleeha na gidan naku ne, tun safe ta fita kuma shine har yanzu munji shiru bata dawo ba." Gaban Mamy ne ya faɗi, cikin  yanayin mamaki tace. "Tun safe kuma,  to ina take kenan don dai kam batazo gidan nan ba yau." Zuciyar Ummi ne ya tsinke cikin muryar damuwa tace. "Nima fargaba ne ya isheni shiyasa nace kawai bara naƙira na tambaya, indai ko bata gida to ina taje kenan, tunfa gari baigama haske ba ta fice." Cikin mamaki haɗi da fargaba Mamy tace. "Bakomai ku kwantar da hankalin ku, bari na shiga can ɓangaren mahaifiyarta ta saina tambaya kota zo, sannan zan faɗawa Baban nata ma, duk yanda ake ciki zaku jini." Nan Ummi tayi mata godiya, daga haka ta aje wayar,  kallon fuskar Ummi kaɗai Saifuddeen yayi, ya fuskanci cewa akwai damuwa. Mamy kuwa ko aje wayar batayi ba ta nufi ɓangaren Mama, da sallama ɗauke abakinta ta kutsa cikin falon Mama'n, Zaheera dake kwance tana kallo ne ta amsawa Mamy'n, dubanta Mamy tayi tare da cewa. "Zaheera ina maman taku." Zaheera bata kai ga cewa komai ba, saiga Mama tafito daga cikin kitchine, duban Mama Mamy tayi cikin nutsuwa tace. "Halima yanzun mahaifiyar Saifuddeen taƙirani, wai tun safe Zaleeha tabar gida kuma har yanzu bata koma ba, shine take tambaya ko nan tazo, nace da ita a'a, saidai kuma bansani ba ko tazo yau ɗin, naji ma kamar hankalinsu atashe yake, kuma gashi naga bata nan ɗin ma, ina Zaleeha tashiga kenan?." Mamy ta tambaya cikin yanayin damuwa. Tsuka Mama tayi tare da turo ɗan kwalinta gaba, cikin halin ko inkula tace. "Wani daga cikin ku yabani ajiyar Zaleeha ne da zakizo kina tambaya ta, ko kuwa idan tazo nan ɗin goyata zanyi abayana na kaita ɗaki na ɓoyeta, kwaje can kunemeta nikam banganta ba!." Mama taƙare maganar tana me yatsuna fuska. Shiru Mamy tayi tare da sauƙe ajiyar zuciya, ahankali tace. "Allah ya huci zuciyarki." Bata jirayi me maman zata ce ba, ta juya tabar falon. Ƙwafa Mama tayi tare da jijjiga kanta, cikin yanayin mugunta tace. "Gaba ɗayanku zaku sani ne, kuma ku sani, wallahi ƴata tagama zama da nakasashshe ehe." Daga ɓangaren na Mama kai tsaye Mamy wajen Baba Malam ta nufa, tana shiga kuwa ta iskesa zaune shida Habu da kuma Ameenu, cikin nutsuwa Mamyn ta sanarwa Baba Malam abun dake faruwa, nan take Baba Malam yaji zuciyarsa tayi wani irin bugawa, gyara zamansa yayi tare da fuskantar Mamy'n cikin, nuna damuwa yace. "Zaleeha bata gidan mijinta kuma, to ina tashiga?." Rumtse idanunsa yayi, tare da ambatan sunan ALLAH Acikin ransa, haƙiƙa Zaleeha kyautace daga wajen Allah, amma sosai lamuranta ke caza masa ƙwaƙwalwa, sam batajin magana ko kaɗan ta bambanta da Maryam. Ya Ameenu kuwa wani irin baƙin cikin Zaleehan ne ya turnuƙesa, shikam tun ba yauba ya gane cewa iskanci Zaleehan keji dashi, yayi rantsuwa kuma saiya sauƙe mata, guguwar dake kanta, burinta kullum shine tajawo musu abun faɗa, so take ta ɓata musu suna, ta kuma ɓatawa Baba Malam halin dattakon sa. Ya Habu ne yace. "To yanzun ina taje?." "Sai Allah!." Mamy ta faɗa asanyaye. Nan take Ya Habu ya ɗauki wayarsa, inda yasoma ƙiran ƴan uwansu na kusa ko Zaleehan taje, amma babu wanda yace tazo. Ya Ameenu ne ya ƙira Maryam awaya inda ya tambayeta ko Zaleehan tazo bayan fitowan sa daga gida, cikin tsananin tashin hankali Maryam tace masa bata zoba. Baba Malam da kansa ya ɗauki wayarsa inda ya dannawa ƙanwarsa, wato Goggo Maryama ƙira, nan ma cewa tayi sam Zaleehan bata zoba, haka Ya Habu da Ya Ameenu suka dinga ƙiran layukan ƴan uwa da kuma abokai na kusa, waƴanda suke  tsammanin cewa Zaleehan zata iya zuwa, amma babu wanda yace tazo, ko labarinta ma babu wani wanda yace yaji. Take Ya Ameenu ya danna ƙiran Lambarta, haka wayar tayita ringing har ta katse, no answer, sake dialing yayi, still har ƙiran yasake katsewa ba a ɗauka ba, saida yayi mata 4 missed calls, amma duka no answer, Ya Habu ne shima yaƙira layin nata, nan ma bata ɗauka ba, sau 5 yana ƙira amma shima bata ɗauka, Baba Malam ne dakansa ya laluɓo lambar tata, nan ya danna mata ƙira, saidai shima kamar sauran haka har ya katse no answer,  nan fa akeyinta ran Ya Ameenu idan yakai million to saida ya ɓaci, take yasoma sakin huci, yayin da yakejin wani ɗaci aransa, har wacece Zaleeha da baba Malam zaiyi mata 2 missed call amma bazata ɗaga ba, lallai idan ya kama Zaleeha, saiya rabata gida biyu. Ganin duk bata ɗauki wayansu bane, yasa Mamy ta ƙirata da layinta, duk dai abu ɗayane bata ɗagawa, nan hankalin Mamy yatashi, take tsoro ya shigeta, nan ta fara tunanin ko Zaleehan bata lafiya ne. Ya Ameenu ne ya kirata da sabon SIM ɗinsa, inda ya sake dialing number'n Zaleeha'n, shi ɗin ma dai batai picking ba, maida wayarsa cikin alj'ihu yayi, inda ransa ke ƙara tsuma yana ɓaci. Baba Malam ne ya dubi Ya Ameenu, nan yace. "Yaje gidan su Saifuddeen ɗin, don sanar dasu halin da ake ciki, idan kuma yasamu Zaleehan ta dawo, to ya basa umarni ya tattakata yayi mata duka irin wanda sai ta kasa tashi, sannan kuma ta faɗa masa gidan ubanwa taje." Nan Ya Ameenu ya miƙe, haka ya fita yana huci don cika umarnin Baba Malam ɗin. Acan gidan su Saifuddeen kuwa, sosai Ummi ta ɗaga hankalinta, tabbas tasan zuwa yanzu rashin dawowan na Zaleeha ba lafiya ba,  ita da Raliya harma da Hayatuddeen gaba ɗaya hankalinsu atashe yake, Adda Rahma wanda itama yanzu zuwanta, jin labarin rashin ganin Zaleeha'n , sosai ya tashi hankalinta. Saifuddeen kuwa yana zaune afalon, laptop ɗinsa yake ta dannawa, sam baikula da harkan neman Zaleehan ba domin duk wani motsinta afa tafin hannunshi take yasan muddin ya maida na'urarshi kanta bata da mafakar da zata shiga ya gaza ganewa.   Zuwan Ya Ameenu ne ya ƙara tada hankalin su Ummi,  nanfa abu kamar wasa ya zama gaske,  sosai aka shiga neman Zaleeha amma kamar ɓatan laya babu ita babu alamanta, Ahmad da Ya Ameenu ne suka shiga mota, inda suka soma zaga gari nemanta, har gidansu Rasheeda da Bilkeesu sunje, amma sun shaida cewa basu ganta ba, nan Ya Ameenu yasa Ahmad dake driving suka nufi family hause ɗinsu, wato gidansu Ya Ameenun kenan, nan ma dai bata nan,  gaba ɗaya ƙanne da yayyan Ya Ameenun saida yaƙirasu ko Zaleehan tazo amma haka suke cewa bata zoba, sosai hankalin familyn ya tashi, Zakariyya da Ziyada kuwa da labarin neman Zaleehan ya iskesu, haka suka shiga damuwa sosai, Hajja kuwa take tasoma kuka, abunka da tsufa, dama kuka baiwa tsofi wahala. Gaba ɗaya ran Ya Ameenu yasake ɓaci, domin sosai shida Ahmad sukayi buji-buji dasu wajen neman Zaleehan, gashi yanzu har ƙarfe goman dare kenan amma babu ita babu alamanta, still wani abun baƙin cikin kuma shine idan anƙira wayarta bata picking,  koda kuwa za'ai mata ƙira ashirin ne bazata ɗaga ba, wannan dalilin yasa ran Ya Ameenu dana Baba Malam ƙara ɓaci,  can gidan su Saifuddeen kuwa, sosai ɓatan Zaleehan ya ƙiɗima Ummi da su Raliya, Saifuddeen kuwa, ganin yanda hankalin Umminsa ya tashi sosai ne, yasan yashi barin sashin na Ummi gaba ɗaya, part ɗinsu ya koma inda ya kwanta yayi shiru, sosai al'amarin Zaleeha ke ƙona masa rai wani lokaci, sai dai yayi rantsuwa bazai taɓa bari sha'anin haukanta ya damesa ba, wani abu can daban bai damesa ba, saboda haka haukan guduwanta bazai taɓa damunsa ba, yasani koma tana inane to ita takai kanta, sannan kuma ita ta zaɓa, abinda dai ya sani yasa a ransa ta boni da aurensa dan babu saki a tsarin rayuwarsa ta gama guje-gujenta aurensu takalmin kazane mutu ka raba ya rantse wa ransa ko shekara 30 zatayi bata dawoba ba saki ta shiga ukunta dashi dan babu ita babu wanda take cewa tana son. Can gidan Baba Malam kuwa, sawa yayi aka ƙira masa Mama, cikin tsananin ɓacin rai ya dubeta, ransa nayi masa suya yace. "Zaleeha tabar gidan mijinta tun asuba, sannan har yanzu bata dawo ba, an kuma nemeta an rasa, tabbas nasan cewa kome Zaleeha ta aikata da sa hannunki, saboda haka ina kika kaita kika ɓoyeta?." Yaƙare maganar murya a kausashe. Ihu Mama tasanya tare da zamowa ƙasa ta zauna daɓas, hannu tasa aka, cikin ɗaga murya tace. "Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un! wayyo Allah na, shikenan kun cuceni kun halakarmin da ƴata, shikenan abun danake gudu shiya faru, baƙin cikinku yasa ta gudu, wayyo Allah na!!." Mama taƙare maganar tana me rushewa da kuka,  kuka sosai take tana faɗin,  "Shikenan kun cuceni, kun rabani da ƴata, wayyo Allah Zaleeha na!." Kallon takaici Baba Malam yayi mata tare da girgiza kansa kawai,  nan ya wuce zuwa ɗakinsa, don baida wadataccen lokacin da zai tsaya sauraran ihun Mama'n. Ganin Baba Malam ya wuce ɗaki, sannan Mamy da Habu sun fice daga falon ne, yasa Mama saurin tashi, cikin matsanancin farinciki tayi juyi, fes takejin zuciyarta, nan ta sake sakin kukan ƙarya, haka tafita daga falon na Baba Malam tana ta faɗin, cewa sun cuceta, tare da cewa lallai su nemo mata ƴarta duk inda ta shiga ta fita. Awannan rana kuwa har ƙarfe 2 na dare babu wanda ya rumtsa  acikin waƴannan gidaje guda biyu,  Mama kuwa da gangan tahana idanunta bacci, hakanan taketa kukan cewa ane mo mata Zaleeha'nta. Saifuddeen kuwa, damuwar dayaga Umminsa aciki ne kawai ya hanasa bacci, sosai yayi ƙoƙari wajen bawa Ummin nasa baki, amma ina Ummi har ƙwalla saida ta zubar, musamman ma idan ta tuna da cewa, basu san wani hali Zaleehan ke ciki ba, shi kuwa Saifuddeen tsab yaga text ɗin da Zaleeha ta turawa ƙawarta Bilkeesu cewa ta gudu, sabida ya haɗe kan wayar Zaleeha da tasa duk abinda zatayi zai gani kuna zaiji, to dai har yanzu baiga ko ji ga inda ta nufaba. Ɓangaren Baba Malam kuwa, baƙin ciki da ɓacin rai ne suka hanasa bacci, tabbas yaji ajikinsa cewa, ba ƴan kidnappers ko wasu mutanen bane suka kama Zaleehan ba, hakanan yaji ajikinsa cewa, guduwa kawai tayi don nuna masa cewa bai isa da ita ba, sannan tayi hakanne don ƙara masa damuwa, sannan ta kuma watsar masa da mutumcinsa a idanun jama'a. Ya Ameenu kuwa tsananin takaicin Zaleehan ne ya hanasa bacci, yayinda Maryam kuwa ke kuka wiwi, rarrashin duniya yayi mata amma takasa daina kuka. Ya Ahmad ma da ba'a gari yake bama, yanacan Abuja saida yakasa rumtsawa, wani irin babban tashin hankali yasamu kansa aciki lokacin da aka faɗa masa, haka ma Aunty Lubna, sosai hankalin Ya Ahmad ya tashi, don yasan cewa Baba Malam zaisanya damuwar acikin ransa, ko kaɗan kuma baya ƙaunar abun da zai taɓa mahaifinsu. Haka dai gaba ɗaya ahlin gidaje biyun nan sukayi kwanan zaune, dasu da kuma duk wani danginsu na kusa,  washe gari kuwa da sassafe Ya Ameenu da Ya Habu suka sake bazama neman Zaleeha. Inda Ahmad ma yashiga cikinsu,suka shiga nemanta tare. Baba Malam kuwa da sassafe ya shirya, inda ya nufi Dukku, dan zuciyarsa na raya masa cewa ko can taje. Haka su Ya Ameenu suka ƙarishe yawonsu amma babu Zaleeha babu alamarta, nan Ya Habu ya shiga motarsa, kai tsaye  ya nufi Ɓilliri, wajen dangin mahaifiyarsu, koda zai sameta acan, amma koda yaje haka yagama shan wahala, ko ina yaje, sai suce bata zoba. Baban Mama kuwa ranshi yayi masifar ɓaci duk da kasan cewarshi kafuri baiji daɗin abinda Zaleeha ta aikataba, koda yake ya zargi ƴarsane a lamarin, dan a zahiri ta nuna mishi bata son auren. Can Dukku kuwa Baba Malam babu inda baije duba Zaleeha'n ba, kama daga gidajen ƴan uwa da abokan arziki, duk yaje amma babu ita ba labarinta, sosai hankalinsa ya tashi, nan take yaji wani ciwon kai mai zafi ya rufesa, alaman cewa jininsa ne keson hawa, don dama yana da ciwon hawan jini. Ya Ahmad kuwa tuni ya biyo jirgi shida Aunty Lubna, inda suka dira acikin garin Gombe, sosai hankalinsa ya ƙara tashi ganin cewa har yanzu ba'aga Zaleehan ba, ƙira kuwa yayi mata yafi sau hamsin amma bata ɗagawa ba, wannan abun shiya ƙara jefasa acikin tashin hankali. Ɓangaren Zaleeha kuwa tun da ta ɗauki hanya bata tsaya ba harsaida tasamu kanta acikin garin Numan na Adamawa yola,  gaba ɗaya ƙiran da akeyi mata akan idanunta, amma zuciyarta tayi wani irin nauyi wanda batajin zata iya ɗaga ƙiran kowa, sannan kuma batajin cewa zata kashe wayarta. Hamdala taketayi a ranta tanaga ta tsira daga farmakin Saifuddeen, dan yayi masifar razanata da bata tsoro jiya da dare, hannu tasa ta share hawayenta wanda bata san dalilin zubowarduba a hankali tace. "Ya Allah kasa kada Babana yayi fushi sani". Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da cewa. "Hmmmm Allah na godema daka tsere tar dani daga hannun wannan mutumin, na sani tabbas da na ƙara kwana a gidan shi, haka zai ta lallatseni kamar maggoro yayi ta tsotsini kamar tom-tom daga nan zai gwada min ƙarfin yace zai farkeni, dole nema in gudu daga komarshi mugu kawai." haka dai taci gaba tuƙi. Daga cikin garin na Numan, kai tsaye anguwar bakin kogi ta nufa, don acanne uncle solomon ɗin yake, a bakin kogi nan sukeyin rayuwa,  da ƙyarma ta iya ƙarasawa wajen, don kafun ma ta isa tuni tayi laushi, amatuƙar gajiye takejin kanta,  a ƙofar ɗan madaidaicin gidan wanda gininsa yayi masifar tsufa ta dai-dai-ta parking ɗin motar, buɗe murfin motar tayi inda tafito kai tsaye tanufi cikin gidan, ko damuwa da mutanen dake kallonta batayi ba. Sanincewar su ɗin ba musulmai bane yasa, kanta tsaye ta kutsa kanta cikin gidan. Elizabet  matar Solomon dake zaune atsakar gida tana tatan markaɗen dawan burkutunsu, jin motsin shigowan mutum yasa ta ɗago kanta ta dubi ƙofar shigowa gidan, ganin Zaleeha tsaye yasanya taɗan saki fuskarta, cikin ɗaga murya Elizabet ɗin tace. "Solo oya come out ga baƙuwarka ta iso." Solomon dake cikin ɗaki jin abun da Elizabet ɗin ke faɗa yasan yashi fitowa, hannunsa riƙe da fartanya, da'alama dama gona zashi, kasancewarsa manomi kayyakin marmari na bakin kogi. Ganin Zaleeha yasashi washe haƙoransa. Cikin gurɓatacciyar hausarsa yace. "Aa Zali'a kin iso kenan, your wellcome, shigo ciki  mana." Ɗan guntun murmushi Zaleeha tayi tare da ƙarasowa cikin ɗan ƙaramin gidan,  tana wucewa Elizabet ta bita da kallo ƙasa-ƙasa ta taɓe baki. Nan Zaleeha tabi Uncle ɗin nata zuwa cikin ɗaki, inda yace da Elizabet ta kawo mawa Zaleehan ruwan sha. Abakin wata katifa wanda ta fara lashewa Zaleehan ta zauna, nan shima Uncle ɗin nata ya zauna. Dubansa tayi tare da cewa. "Good evining uncle, haw was the day?." "Am very fine my daughter, how are you, i hope are you okay, right?." Murmushi ta ɗanyi tare da jinjina masa kai, ahankali tace. "Yeah." Dai-dai lokacin Elizabet ta shigo hannunta ɗauke da kofin ruwa wanda ta tara a bakin fomfonsu dake ɗan tsakar gidan nasu, aje kofin tayi agaban Zaleeha, ɗauke kai Zaleeha tayi domin sam batason jin ƙamshi ne ko warinsu zata ce ne oho, cikin ƙasa da murya tace. "Aunty good evining." "Evining, how are you?." Elizabet tafa ɗa tana me kallon Zaleeha'n, wanda take ta faman ƙarewa ɗakin kallo. "Am fine!" Zaleeha tafaɗa tana me ƙarewa kofin da aka kawo mata ruwa aciki kallo, Allah Yasani itakam ƙyanƙyaminsu takeji, hakanan take ganin komai nasu yafita daban, komai nasu ba irin na sauran mutane ba, shiyasa ma kwata kwata bata fiye shiri da dangin mahaifiyarta ta ba, domin ita sam batason zama da su, saboda zama da waƴanda hasken addinin musulunci bai cimmusu ba, sai ahankali, zakaga kwaɓa da kuma shirme kala-kala. Duk da kasancewar tanajin ƙishin ruwa, amma kasa shan ruwan tayi, don sam bata yarda ma da tsabtan gidan ba. Hira kaɗan suka ɗan taɓa da Uncle din nata, nan yace da ita zai tafi gona, yana tafiya ta jawo akwatunanta, zanin gadon dake kan katifan da take kai ta yaye, nan taciro wani bedsheet mai ɗan taushi wanda baida nauyi ta shumfuɗa, kimtsa akwatunanta tayi agefe kana ta fito da sallayanta da komai na buƙatan musulmi ta a dana, hand bag ɗinta ta zuge, nan ta ciro wasu diary milk chocolate guda biyu, tare da wani cake, nan ta kwanta tare da jawo wayarta, power bank dinta ta ɗauko inda ta saƙala wayarta a charge, kwanciya tayi tana mecin chocolate ɗin ahankali, hakanan dai ta gwammace gwara zaman nan dana gidan SAIFUDDEEN dake cike da jin daɗin daular duniya. Acan Gombe kuwa, Haka su Ya Ameenu suka ƙare yawonsu har suka gaji, dawowa gida sukayi inda sukayi jigum jigum. Baba Malam ma haka ya dawo daga Dukku zuciyarsa duk ba daɗi. Ganin yanda gaba ɗaya dangin suka tashi hankalinsu ne yasanya wani tunani ya faɗowa Ahmad, nan yaƙira Ya Ameenu yasanar masa cewa, lokacin da Zaleeha zata tafi, tabbas yaga Zaheera tazo a napep inda ta bata wani abu a jaka, sannan ita Zaleehan tatafi, ita kuwa Zaheera ta shiga napep din daya kawota, saboda haka atambayi Zahira ko tasan inda Zaleehan taje. Habawa ae Ya Ameenu kaman kububuwa haka yaji ransa ya ɓaci, atake ya gayawa Baba Malam, nan Baba Malam yace da Zakariyya wanda tun safe yake gidan, cewa yaje ya ƙira masa Zahira, Zakariyya na zuwa ƙiranta, Mama ta buga tsalle inda ta kama hannun Zahira, tare da cewa tare zasu je, nan Mama tace da Zahiran ko kasheta zasuyi, kada ta sake tafaɗi inda Zaleeha take, dayake Zahiran ma zuciyar arna gareta, take ta kafe kan cewa bazata faɗa ba. Atare suka shiga falon ita da Mama, cikin zafin nama Ya Ameenu ya damƙo Zahira, wani lafiyayyen mari ya sauƙe mata akan fuskarta, take tafasa wani uban ƙara, tare da buga tsalle tasoma yayyarfa hannuwanta, cikin zafin zuciya yace. "Ina Zaleeeha ta tafi?." Bata iya basa amasa ba saboda marin ya matuƙar gigitata. Cikin fushi haɗi da ɓacin rai Mama tace. "Maganar banza ma kenan, wannan ai kora kunya da hauka kuke ƙoƙarin yi min, ku da kanku kuka salwantar min da rayuwar ƴata, sannan yanzu kuzo kuna tambayan Zahira, wallahi Ameenu kakiyaye ni kada kasake ka ƙara kai hannunka jikin Zahira tam!!." Mama tafaɗa ranta amatuƙar ɓace, zuciyarta kuwa cike da fargaban kada zafin mari yasa Zahira faɗin gaskiyan inda Zaleeha take. Ran Baba Malam a ɓace ya dakawa Mama tsawa, cikin faɗa yace. "Ina ki ka kai Zaleeha?." Afusace Mama tace. "Bansan inda takeba!!." Cikin ɓacin rai Baba Malam yace. "Na baki nanda kafun gari ya waye, duk inda Zaleeha tashiga ki tabbatar kin dawo da ita ɗakin mijinta, idan kuwa ba haka ba, ki tattara komai naki kibarmin gidana, kuma sannan idan kin tashi tafiya ki haɗa da Zahira karkiyi kuskuren barmin ita agidana, don bana ƙaunar zama da munafuki!, kada ki manta koki ƙira Zaleeha ta dawo ko kuma kibarmin gidana ayu basai gobe ba!!!." Yana gama faɗin haka ya wuce ɗakinsa, amatuƙar fusace. Wani irin masifeffen tsorone ya rufe Mama kadafa Baba Malam ya saketa ta koma ƙauyensu noma, wani sashin na zuciyarta kuwa zugar ruda ce ta ratsota haka yasa ta ɗan ja tsaki tare da kamo hannun Zahira, cikin ɓacin rai tace. "Mu tafi ai nima inada gidan uba, saboda haka kwana ɗaya bazamu ƙara ba, Zaleeha ne kuma bamusan inda take ba, kuma ko sama da ƙasa zasu haɗe, aurenta da nakasashshen gurgu ya ƙare kenan har gaban abadan." Littafina na kuɗine in kin gashi a wojema na satane. Turo katin Mtn na ɗari 300 kacal ta wannan number 09097853276 ko ka/koyi min transfer ta asusuna na 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa kana ki turo min shaidar biyan ki.    By *GARKUWAR FULANI* [05/09, 7:46 pm] اسماء بشير: Hannun Zahira Mama ta kama, cikin fushi haɗi da ƙunan zuciya ta fita daga cikin falon, tabbas ita kam ta gwammacewa tafiya, da dai ta barin Zaleeha ta cigaba da zama da Saifuddeen, cikin ranta take cewa. "Miye agidan naka banda baƙin ciki, da kuma tursasa mutum dole, dan mun bar gidanka, ae ba rayuwarmu muka bari ba." Nan tasanya Zahira ta haɗa kayanta, itama duk wani abubuwan buƙata nata ta haɗa, Zahira kuwa ganin dagaske tafiya zasuyi yasa, ta fashe da kuka, cikin fargaba haɗi da tsoro, tace. "Banason tafiya Mama, banason yin nesa da gida, bani da wani waje wanda yafimin gida, kinsan banason ƙauye, nikam wallahi zanje na bawa Baba Malam haƙuri, bazan iya tafiya nabar gida ba..." Wani wawan tsawa Mama ta daka mata, cikin takaici haɗi da ɓacin rai tace. "Zakimin shiru ne ko sai na kakkaryaki, banza wacce bata kishin mahaifiyarta da ƴan uwanta, ko anfaɗa miki nan ɗin aljannar duniya ce, da har idan muka barsa zamu tagayyara, to kiji da kyau, kamar yanda yace baya buƙatarmu, muma haka bama buƙatar kowa dake cikin gidan." Haka Mama taja hannun Zahira, suka fita, kuka sosai Zahira keyi, har cikin ranta batason barin gida da kuma ƴan uwanta. Suna fita Mama ta tara musu mai napep, nan tace. "Ya kaisu bakin tashar Gombe line". Inda ananne zasu samu motar da zata kaisu Ɓilliri. Suna zuwa kuwa suka samu mota, dama mutum biyu rak, ya rage motar ta tashi, suna shiga kuwa, aka kama hanyar Ɓilliri dasu. Can gidan su Saifuddeen kuwa, har yanzu hankalin su Ummee atashe yake, sosai ɓatan Zaleehan ya jijjiga zuƙatansu, don ɓatan mutum ba abun wasa bane,  gaba ɗaya farin ciki da walwalan gidan ya ƙaura, damuwa ne yacika zuciyoyinsu, sam Saifuddeen kuwa ya ƙi aminta wajen sanyawa zuciyarsa damuwa, gashi kuma ko kaɗan baison ganin Umminsa cikin wani hali. Haka ya Ameenu da Habu haɗi da Ahmad suka zama basu da wani aiki sai neman Zaleeha'n, duk wani waje dasuke tunanin zata iya zuwa, harma da wanda basa tunani saida sukaje. , inda yazamana kullum sai sun fita nemanta. Acan Numan kuwa, tunda Zaleeha tazo, babu abun dake fitar da ita, aɗakin sai Alwala, don dama da butar ta tazo, saboda tasan bazata taɓa samun buta awajensu ba, daga kan sallaya Qur'an sharbi,  babu abun da ta bari, wanda tasan dole zata buƙacesu,  koda dare yayi, haka Elizabet ta kawo mata, tuwo miyar shuwaka, sam bata ko kalli abincin ba, don kuwa batasa aranta cewa zata ci ba, kwanciya tayi tare da jawo jakarta, sweet ta ɓare inda ta jefa abakinta,  wayarta da ta cika da charge ta ɗauka, nan ta kunna data'nta, kai tsaye Instagram ta shiga, nan ta tarar da saƙon fans ɗinta, kala-kala, babu ɗaya da ta bawa amsa, haka tashiga duba hotuna, wanda su suka ɗebe mata kewa, gajiya da Instagram ɗinne, yasa ta faɗa Youtube, nan tayi downloading wani series film ɗin da tasaba gani kwanakin baya, wato Money Heist,  kallo ne ya taimaka inda ya rage mata kaɗaicin da take ciki, ahaka har bacci ɓarawo ya ɗauketa. Abuja Nigeria. Duk da kasancewar dare ya raba, amma duk yanda taso bacci ya ɗauketa abun ya ci tura,  sosai takejin tarin damuwa acikin zuciyarta, hawayen da suka cika idanunta ne suka samu daman gangarowa kan fuskarta, ahankali takai hannunta kan fuskarta ta inda ta share hawayen,  ganinta ta ƙara mayarwa ga screen ɗin wayar ta, wanda ke riƙe ahanunta,  hoton kyakkyawar fuskarsa ne bayyane akan fuskar wayar,  sosai yayi kyau cikin shigar ƙananan kaya dake jikinsa, wanda rigane da wando, masu kalan pink yasanya a jikinsa, sun kuwa matuƙar amsar jikin nasa,  idanunta ta lumshe tare da sauƙe ajiyar zuciya tana mai jin kishi da jin tsanar matar daya auran, har zuwa yau takasa ciresa aranta, ba tasan wani irin so ne takeyi masa ba, domin kuwa har wani zafi takeji azuciyarta, aduk sanda ta tuna da cewar yana da mata, taso zama wani ɓangare na rayuwarsa, amma burinta bai cika ba, sai dai tasa aranta cewa idan da rai to da rabo,  idan tana da rabon raɓan jikinsa, watarana zata zamo matarsa, wani ɗan guntun murmushi ne ya bayyana akan ƴar kyakkyawar fuskarta, wata zuciyarta ce tace da'ita. "Ameena ba kyaji, shin bayan Saifuddeen babu wasu mazan ne aduniya?." Sake faɗaɗa murmushin dake kan fuskarta tayi, ahankali tace. "Bayan shi akwai wasu maza masu tarin yawa, saidai shiɗin na musammanne,  irinsa guda ɗaya ne, acikin maza, bayanshi babu waninsa, wannan dalilin shiyasa nake matsanancin so da kishinsa wata can ta malliki abinda duk nake bege da so daga gareshi." a bayyane tayi maganar, domin gaba ɗaya ta faɗa cikin shauƙin ƙaunarsa, aranta ji take inama inama, da ace Saifuddeen zai zama mallakinta, to tabbas da sai tafi kowa murna da kuma farin ciki, duk da cewar tasan shiɗin ya girmewa ajinta, amma ba laifi itama ta yarda da kanta, don kuwa babu laifi, tasan  tana da nata kyau'n, domin Allah yayi mata sura, ɗan dadai haɗi da kyaun fuska, duk da kasancewar kai tsaye baza'a ƙirata da sunan kyakkyawar gaske ba, da ka nutsa da kallonta sosai kuwa, to  anan ne zaka fahimci irin nata sirrin kyaun,  domin kuwa sam ba baƙa bace, haka zalika bata kasance fara ba, saidai tana da kala mai kyau, domin  takasance tana da  brown skin mai kyau musamman dayake tana ɗan ƙara farin da mai, sannan afuskarta tana da ɗan madaidaicin hanci, mai ɗan tsawo kaɗan kuma karan hancin ba sosaiba, sai kuma ƴan saffa-saffan idanunta, masu ƴan siraran gashi a samansu, babu laifi domin tana da ɗan gashin gira iya dai-dai gwargwado,   sannan bakinta ma bashi da wani girma sosai, daga ɓangaren gashin kai kuwa, tana dashi dai-dai misali amman baida laushi, , kuma shima bashi da tsawo sosai. A taƙaice dai Ameena itama kyakkyawar mace ce, amma kuma ko kusa bata tako Zaleeha akyau ba, balle kuma aje ga uban gayyan wato Handsome guy ɗin Saifuddeen kenan. Don kuwa har yanzu da mutane sun kasa tantance tsakanin shida Zaleeha wa yafi wani kyau, sai-dai  idan za'a misalta tsananin kyawun  da Zaleeha'n, ke dashi,  koda  zata ɗarasa kyau ma ƙaɗan ne, domin kasancewarta mace, dole tsarin halittarsu ya banbanta. Gyara kwanciyarta tayi tare da jawo pillow tayi hugging ɗinsa,  cikin zuciyarta tace. "Ya Allah Ina roƙonka ka cigaba da zama gatana ako da yaushe,  Ya Allah Ka mallakamin Saifuddeen, amatsayin mijina, Ya Allah Kadubi zuciyata!." Ajiyar zuciya ta sauƙe, tare da ɗaukan wayarta ta manna a ƙirjinta, hakanan takejin wani irin nishaɗi acikin ranta. Da tarin tunaninsa a haka bacci ɓarawo ya ɗauketa. GOMBE NIGERIA Abubuwa da yawa sunata wakana acikin garin Gombe, inda gaba ɗaya yakasance a tsakanin gidan su Saifuddeen da kuma nasu Zaleeha, sam babu kwanciyar hankali, don kuwa yau kimanin kwana bakwai kenan da ɓatan Zaleeha, amma shiru har yanzu babu wani labari, wayoyinta kuwa har zuwa yau suna shiga, amma abu ɗaya ne har yau, shine bata ɗaukan ƙiran kowa, saƙonnin text message kuwa na ban tsoro da gargaɗi, akan duk inda take ta dawo gida, babu kalan wanda Ya Ameenu da kuma Ya Habu basu tura mata ba, amma Zaleeha da ta gani ko bin takansu batayi. Messages ɗin Ya Ahmad kuwa sunfi 20 wanda da ya tura mata, wanda suke cike da tsantsar lallashi haɗi da ban-baki yake bata, tare dayi mata al'ƙawarurruka da dama akan idan ta dawo zai yi mata, ba irin al'ƙawarin da baiyi mata ba, har cewa yayi da ita. "Pleess Zaleeha ki dawo gida hankali kowa ya tashi sabida rashinki, wlh idan kika amince kika dawo gida, to zan sa araba aurenki da Saifuddeen, sannan kuma zan ɗaukeki mu koma Abuja, zan sama maki aiki acan." Koda ta karanta murmushi kawai tayi, sanin cewa hakan abune mai wahala, domin tasan cewa Yayan nata bashi da wani abun da yakeso, sai wanda Baba Malam yakeso, farin cikin Baba Malam shine nasa, tasan cewa bazai taɓa iya raba auren ta da Saifuddeen ba, domin yin hakan zaisa ya faɗa cikin fushin Baba Malam, wanda tasan da Ya Ahmad ɗin  da ya faɗa cikin fushin Baba Malam, tasan zai gwammace gwara mutuwarsa. Haka koda ta karanta text ɗin, ta watsar tare da gogewa, don kuwa sun cika mata inbox da saƙonninsu, ita harma ta gaji a can ƙasan zuciyanta kuwa ji take kamar taita kuka. Ɓangaren Ya Habu kuwa, yau yagama shirinsa tsab, inda ya ƙudurta aransa cewa, yau zai je Doho, wajen Yayar mahaifiyar tasu, wato Aunty Ruda, domin ransa amatuƙar ɓace yake da ita, saboda yasan cewa, duk wani abu da maman tasu keyi, da sanya hannunta, kasancewar kowa yasan cewa, ita ɗince ke zugata  akan wasu abubuwa itace ke gurɓata komai na Mamansu. Ya Ameenu kuwa yanzu damuwar rashin lafiyar matarsa ne ya damesa, don kuwa tun randa Zaleeha ta gudu, Maryam ta kwanta zazzaɓi da ciwon kai, kasancewar bata da wani aiki kullum sai kuka, sosai ɓatan ƴar uwartata ya shiga jikinta, gefe guda kuwa ga Baba Malam daya shiga halin baƙin ciki,  kowa ya gansa yasan da cewa yana cikin damuwa,  kasancewarsu Yara masu biyayya hakan yasa basa ƙaunar ganin damuwar mahifinsu, uwa uba ga Mama da ta bar gidan, wannan abu na damun Maryam sosai, ganin lokaci ɗaya zuri'arsu naneman watsewa komai ba daɗi ga ɓatan ƴar uwa ga saɓani tsakanin iyayenta ga ɓacin ran mahaifinta damuwa dai ta taru ta cika zuciyar baiwar Allah. Ƙarfe 10 na safiyar ranan dai-dai Ya Habu ya kama hanyar zuwa Doho. Zaune yake akan wheelchair ɗinsa mai kalan silver gold,  sanye yake da wani army jeans, sai kuma wata farar long sleeve wanda ya nannaɗe hannun rigar zuwa guiwar hannunsa, aƙafansa kuwa, wasu fararen  bedroom slippers ne masu kyau,  kamar koda yaushe laptop ɗinsa ne, ɗaure akan cinyarsa, sosai ya bata hankalinsa gurin binciken da yakeyi. Gefensa Ummi ne wanda tayi jigum, duk damuwan ɓatan Zaleeha ya isheta, kusa da ita kuwa Hayatuddeen ne zaune yana ta faman latsa wayarsa, inda ya ɗan kaucewa ganin idanunsu ya matsa can gefe, chatting yake sosai, da wani sabon abokinsa da yayi acikin G.S.U, wanda yakasance department ɗinsu ɗaya, sunan abokin nasa Khamis, sosai Hayatuddeen yasoma shaƙuwa da Khamis, wanda yake kuma Khamis, yaro ne wanda bayajin magana sam, babansa mai kuɗin gaske ne, gidansu yana nan cikin New G.R.A, gaba ɗaya Khamis asangarce yake, kasancewarsa shine  ɗa namiji agidansu, hakan yasa gaba ɗaya iyayensa suka sakar masa yarda, tare da bashi daman yin duk abun da yake so,  shikuwa Khamis tun da yaga Hayatuddeen, yaji cewar yana sonsa da abota, kasancewar Hayatuddeen ba laifi yana shiga mai kyau da burgewa, sannan yana ɗan chilling ɗinsa, da sabuwar iphone ɗinsa,  makaranta kuwa kaisa ake amotar gida sannan driver ya ɗauko sa, shikuwa Khamis jibgegiyar motace ahannunsa,  hakan yasa ko zaman school ɗin bayayi, da yazo sai yawo kawai, kamar da wasa kuma suka fara abota da Hayatuddeen wanda gashi kuma zuwa ayanzun abotan nasu ya soma ƙarfi. Ajiyar zuciya mai ƙarfi ya sauƙe tare da lumshe kyawawan idanunsa, buguun zuciyarsa ne ya ɗan sassauta ahankali, hannunsa yasanya inda ya kama ƙasan haɓarsa, numfashi ya sauƙe, tare da fesar da wani irin iska mai zafi ta bakinsa,  *"NUMAN"* shine abun daya faɗa acikin zuciyarsa, sake duba inda location ɗin  ya tsaya,  kansa yajinjina tare da ɗan cije laɓɓansa, tabbas tana can Adamawa cikin Numan domin kuwa, haka sakamakon tracker ɗin da yayi ya nuna mishi. Ɗan jim yayi tare da lumshe idanunsa,  "Tabbas tana can Numan, amma kuma waye nata acan, da zata je ta zauna?." Tambayar da yayiwa kansa kenan, sanin cewa bashi da amsa yasa shi, sakin ɗan guntun murmushi,  wato da zama dashi ne ta gwammace rayuwa a wancan ƙauyen mai cike da yawan ƙabilu arnataku, hmmmm shikuwa zai zuba mata ido ya gani, bakuma zai faɗawa kowa inda take ba, sannan zaiyi duk yanda zaiyi wajen ganin, ya cire Umminsa adamuwa, dan tasanya ɓatan Zaleeha'n, sosai acikin ranta. Ta gigita mishi ƴan uwa da abokai gaba ɗaya, Ishaq Salisu Warisu Mudassir Aziz hatta Saminu Hishsm, Jabeer, da baya garin duk ta tashi hankalin kowa. Yasan ko ahaka Allah bazai bar Zaleeha ta zauna cikin farin ciki ba, saboda yasan ta ɗauki al'hakin iyayenta, sannan ga igiyar aurensa dake kanta, wanda take ta walagigi dashi. Wheelchair ɗinsa ya danna inda ya ƙarasa har gaban Umminsa, hannunsa ya ɗaura akan na Ummi'n, cikin kulawa ya karyar da kansa, tare da ɗan marairaice fuska, anutse yayi mata alama, cikin body language cewa. "Ta daina sa kanta adamuwa, Zaleehan zata dawo nan bada jimawa ba." Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe, cikin rauni ta dubeshi, murya asanyaye tace. "Banajin daɗi Saifuddeen, idan na tuna da cewar sanadiyar aurenka Zaleeha ta gwammace barin iyayenta, yayunta, ƙannenta, aikinta, mahaifanta, da duka danginta, wannan abun shine abun danake ta gudu tun farko, shiyasa naso afasa auren,  gashi yanzu an nemeta an rasa, babban tashin hankalina ma, shine bamu da tabbacin cewa ko lafiya take!." Kansa ya girgizawa Ummin nasa, tare dayi mata alaman cewa. "Zaleehan tana nan lafiya ƙalau aduk inda take." Kai kawai Ummi ta jinjina masa don bata iya cewa komai. Can Doho kuwa, Ya Habu na isa gidan Aunty Ruda yayiwa tsinke,  Aunty Ruda na ganinsa ta taɓe baki, don tasan tatsuniyar gizo bata wuce ta ƙoƙi,  first abun da Ya Habu ya fara tambayarta shine. "Ina suka kai Zaleeha?." Shewa tayi tare da cewa. "Ae baku bani ajiyan Zaleeha ba, balle kuce zaku zo nemanta, abu mafi sauƙi ku shiga uwa duniya ku nemeta kawai, tun da kune kuka salwantar da rayuwarta." Wannan abun shiya ƙara harzuƙa Ya Habu, nan take ransa ya ƙara baci, haka yayiwa Aunty Ruda'n tas, inda ya wanketa soso da sabulu, ya ɗora da cewar. "Ita ke zuga mamansu akan komai, kuma wallahi su fito da Zaleeha, duk ma inda suka kaita suka ɓoyeta, kuma ta daina zuga musu uwa tana tura mata halinsu na arna ya ƙara da cewa kada tayi zaton basu gane ita ke zuga Mamaba." Haka yabaro Doho'n ransa amatuƙar ɓace, domin yasan da cewa sunsan inda Zaleehan take faɗa ne kawai bazasuyi ba. Bayan kwana 5 da dawowan Ya Habu daga Doho, Baba Malam ya kwanta rashin lafiya, inda ciwon hawan jininsa ne ya tashi,  nanfa gaba ɗaya ahalin suka sake shiga cikin tashin hankali, ga jikin Maryam ma da yaƙi daɗi, bata da wani zance saina ƙanwarta Zaleeha. Saifuddeen dake zaune afalon Ummi ne, ya kwantar da kansa ajikin kujera,  yanzu labarin rashin lafiyar Baba Malam ya iskesa, hakanne yasa yaji babu daɗi acikin ransa, sam ada baiyi niyar faɗawa kowa inda Zaleehan take ba, yaso barinta ne idan tagaji don kanta zata dawo, amma ayanzu yazama dole ya faɗa, kodan saboda rashin lafiyar Baba Malam ɗin ma. Computer ɗinsa ya ɗauka, inda yayi rubutu mai ɗan tsawo, sannan ya nunawa Ahmad,  bai jirayi Ahmad yagama karanta saƙon ba, ya ciro wayarsa inda ya turawa Ya Ameenu saƙo,  wanda ya rubutashi ataƙaice. Ahmad nagama karanta saƙon ya ɗago ya dubi Saifuddeen, kai Saifuddeen ɗin ya jinjina masa, ajiyar zuciya Ahmad ɗin ya sauƙe, nan yakai dubansa ga Ummi, sai kuma Adda Rahama dake zaune, cikin nutsuwa Ahmad yace. "Ummi Saifuddeen ya ganno inda Zaleeha take fa." cikin mamaki Ummi tace. "Ta ina? Tana ina? ko wani abune ya sameta?." Kai Ahmad ya girgiza, cikin nutsuwa yace. "Uhmmm Ummi kenan wato dai kuna ganin kaman Zaleeha ɓata tayi ko, hmmm to wlh Zaleeha ba ɓata tayi ba, guduwa tayi da ƙafafunta, sannan yanzu haka tana can Numan, halan akwai wasu ɓoyayyun ƴan uwanta acanne, wanda tunanin su Ya Ameenu da Habu baije can ba, amma dai yanzu Saifuddeen ya faɗawa Ya Ameenu'n." Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe tare dayin hamdala acikin ranta, tabbas ta ɗanji sanyi acikin ranta,don dama ɓatan Zaleehan yayi mata tsaye acikin rai, itakuwa Adda Rahma shiru tayi tana meyin wasu nazari,  hakanan Zaleehan ta soma sanewa acikin ranta, tabbas ita duk wani wanda baison Saifuddeen, to fa itama bata ƙaunarsa ko kaɗan. Raihana kuwa da dama can bata wani sake da Zaleeha a rantaba, sai taji ta fice mata a rai haushinta kawai takeji har ita waye da zatace bata son Hammanta me ya rasa dame sauran maza suka fishi haka dai taketa ƙunƙuninta. Ƙiran Ya Ameenu ne yashigo wayan Ahmad, da sauri Ahmad ya ɗaga wayan. Daga ɓangaren Ya Ameenu, wanda ke zaune acikin falon Baba Malam, kasancewar dukaninsu suna cikin falon, hakan yasashi sanya wayar a speeker,  yanda kowa zaiji, tambayar Ahmad yayi akan saƙon dayaga Saifuddeen ya turo masa, nan take Ahmad yayi masa bayanin dukkan abun da Saifuddeen ya faɗa masa, inda yace ta hanyar yin tracker Saifuddeen ɗin ya gano inda take. Nan take gaba ɗaya suka cika da mamaki, domin koda wasa basu taɓa zaton cewa zataje Numan ɗinba, saboda su kwata-kwata ma sun manta da cewa Mama tana da ɗan uwa acan, domin kuwa ba zuwa take ba, suma kuma ba zuwa suke ba. Ya Ameenu na kashe wayan, Baba Malam dake kishingiɗe yana shan fruit salad, ɗin da Mamy ta haɗa masa ya saki ɗan guntun murmushi irin nasu na manƴan dottijai murmushi mai cike da ma'anoni da manufa masu tarin yawa,   cikin baƙin ciki Ya Ameenu ya rusuna gaban Baba Malam ɗin cikin neman izini yace. "Kayi haƙuri Baba idan kayimin izini kabarni naje ayau ɗinnan na taho da ita gida." Ahankali Baba Malam ya aje bowl ɗin dake hannunsa kai ya jujjuya mishi alaman a a,  cikin kulawa ya dubi Ya Ahmad, wanda yayi jigum, anutse yace. "Ahmad ka ɗauki matarka gobe ku koma, banason zamanka hakanan, saboda haka ka koma bakin aikin ka." Cikin salon bada umarni wa yaran nashi ya kalli Habu dake jin tamkar yayi fiffige ya fire yaje Numan cikin haiba da kamala yace. "Kai kuma Habu nabaka izinin gobe kaje can Numan ɗin, badai kasan gidan yayan Mamar taku dake can ba?." Kai Ya Habu ya jinjina tare da cewa, "Eh." Ajiyar zuciya Baba Malam ya sauƙe tare da cewa. "To nayi maka izini kaje, duk wani abu dakasan na Saifuddeen ne wanda Zaleeha tatafi dashi ka ƙwatosa ka kawomin, sannan ka ɗauko masa kayayyakin aurensa wanda ta tafi dashi, amma kuma koda wasa kada kace zaka ɗauko ta, badai ta zaɓi guduwa da zaman can ba, shikenan kubarta ta zauna acan ɗin, da sannu duniya zata koya mata hankali, kadai ji abun dana faɗa maka ko?". Da sauri Habu ya gyaɗa kanshi alamun eh, shi kuwa Baba Malam a kausashe yace. "Bana buƙatar ta saboda haka koda wasa kada kayi kuskuren ɗauko min ita, kabarta acan, amma kaya dai dayake mallakin Saifuddeen kada kabar ko abu ɗaya awajenta." Cike da gamsuwa Ya Habu ya jinjina kansa don shima, zaifison abar Zaleeha'n, ta ɗana ƙunci da baƙin ciki data ɗana musu. Duban Ya Ameenu Baba Malam yayi cikin kulawa, ya dafa kafaɗunsa, kana yace. "Matarka bata da isashshen lafiya Ameenu, saboda haka ku koma gida kaje ka kula da ita, saboda tana buƙatar kulawanka, in sha Allah Maryam ƴar aljannace, domin takasance ƴa mai biyayya ga mahaifinta, haka kuma ga mijinta, tabbas Maryam ƴa ɗayace tamkar da dubu, sannan itaɗin mafi soyuwa ce agareni, saboda haka bazanso ace kayi mata nisa, ka ɗauketa ku koma gida kaji!." Cikin yanayin gamsuwa Ya Ameenu yace. "To." Gyara zama Baba Malam yayi, cikin nutsuwa yace. "Kudukan ku idan kuka sake sanya damuwar Zaleeha a cikin ranku, to tabbas zanyi fushi daku, haka ta zaɓa haka kuma take ganin yafi mata, saboda haka mu ƙyaleta, ita da kanta wata rana zata dawo, kutashi kuje kowa yayi sabgogin gabansa, ko da ita ko babu ita zamu rayu." Haka dukansu suka miƙe, inda Ya Ahmad gaba ɗaya jikinsa yayi sanyi, har acikin ransa yaso ace Baba Malam ya bari aɗauko Zaleeha'n, baiso ace an barta acan ba, duba da cewa ba'a cikin musulmai take ba, sannan basu san ma wani irin rayuwa takeyi acan ba. Su Ya Ahmad ɗin nafita, Mamy ta gyara zama cikin kwantar da murya, haɗi da tausasa zance tace. "Amma Malam kanaga barinta acan ɗin shine mafi alfanu?, da a so nane a ɗaukota, sai ayi mata koda nasiha ce, nasan gaba zata gyara." Murmushi Baba Malam yayi tare da girgiza kansa, bowl ɗin fruit salad ɗinsa ya jawo, cikin kulawa yace da Mamy. "Ina da babban dalilin dayasa nace abarta acan, duniya zata koya mata hankali." Shiru Mamy tayi tare da ɗan jingina bayanta, ta shiga nazari. Numan. Cikin kaɗaici haka take gudanar da rayuwarta anan Numan ɗin, sosai takejin ƙyaman mutanen da take tare dasu, domin kuwa a iya arean nasu Solomon gaba ki ɗayansu christan's ne babu musulmi ko guda ɗaya, sai ita da tashigo cikinsu ayanzu, wanda kuma ba daɗin rayuwa dasu takeji ba, tana dai zaunene acikinsu bisa dole, sau da yawa Solomon baya zaman gida, kusan koda yaushe yana gona cikin lamɓunshi na shuke-shuken kayan marmari danginsu ,Ayaba, Gwaiba, Dabino, Kwakwa, Lemun zaƙi dana tsami Kankana Abarba sweet milo Aya, Gyaɗa, ɗanyar Masara, Dankalin hausa dana turawa, rogo, tumatur attaruhu albasa da dai sauransu, wanda shine sana'arsa daya dogara da ita. Hakanne yasa basosai suka cika zama dashi ba, sabida babu salla babu salati ko yaushe yana can yana yiwa ƙasa aski don inƙanta al'barkatun gonar tasa, itakuwa matarsa Elizabet baƙin halinta ma ya isheta, wanda tun Zaleehan bata fahimta ba harta fara fahimta, hakanne yasa itama take ɗauke mata kai, Sai dai can gefen unguwar su Solomon akwai rugar Fulani masu mutunci da tsabta,da riƙo da addini sosai Zaleeha ta fara sabawa dasu, wanda kullum sukan kawo mata Nono da Zuma mai kyau da inƙanci wanda hakan yake matuƙar taimaka mata ta samu abin sawa a bakin salati sai kuma ƴaƴan itatuwa da Solomon kan kawo mata. Yanzuma kwance take akan ƴar katifar da suka bata, gaba ɗaya batajin daɗin gidan, babban matsalan data fara fuskanta ma shine rashin samun ingantaccen wutan nepa, acan Gombe tasaba unguwarsu kwata kwata ba'a ɗauke musu wuta, koda kuwa ma an ɗauke tsanani bai wuce 5 minute andawo dashi, haka koda ta koma gidan su Saifuddeen ma kullum cikin wuta suke, amma tunda tazo nan saita kwana ta wuni bata ga idon wuta ba, kuma koda ma sun kawota bai wuce mintuna 50 sun ɗauketa, ita da ta saba kwana cikin sanyin AC kan makeken gado na alfarma, da tattausan blanket masu taushin gaske amma sai gashi yanzu kusan kullum dare cikin zafi take kwana, hakanne yasa gaba ɗaya takejin komai bayayi mata daɗi, gashi wayarta ayanzu bata samun wadataccen caji, wani lokaci ma tanason shiga yanar gizo don ɗebe kewa, amma rashin ƙarfin network haka yake hanata, dolenta haka zatayi jigum tayi shiru, yanzuma kwanciyar da takeyi ne ya isheta, hakan yasa ta miƙe tsaye, wani ƙaton hijabinta ta ɗauka ta zura daga kanta zuwa idon sawunta dan tasan akwai igiyar aure a kanta wani flat shoe ɗinta ta zura, sannan tafito daga cikin ɗakin. Babu kowa atsakar gidan, hakan yasa kai tsaye tanufi hanyar fita daga gidan. Tsayawa tayi daga ɗan nesa tana me hango wani wutsinyan tafkeken kogi Numan, wanda ruwan cikinsa ke gudana da ikon Allah, sosai sanyin wajen ke shiga jikinta, kasancewar da yammaci ne, ahankali ta ƙarasa kusa da kogin, zama tayi akan yashin dake shimfiɗe awajen tare da zura ƙafafunta cikin ruwan, idanunta ta lumshe tare da sauƙe ajiyar zuciya. Wani sabon shauƙin ƙaunarsa, wanda ke kwance a ƙasan zuciyarta ne ya taso mata, aduk tsawon kwanakin nan koda sau ɗaya ne soyayya da kewarsa, basu ragu acikin zuciyarta ba, kullum da soyayyarsa take kwana take kuma tashi, har yau bata fidda ran cewa watarana zai zo gareta ba, duk kwanan duniya soyayyarsa ƙara ninkuwa take acikin zuciyarta, zuwa yanzu kewa da muradinsa ya zamo wani sinadari na cikin rayuwarta, tajima awajen, ganin magriba ta gabato ne yasa, ta tashi inda ta koma cikin gida, a bakin fonfonsu ta tsaya ta buɗe ruwa mai tsabta, wanda dashi tayi alwala, ɗaki ta koma, koda tayi sallan Magriba, bata tashi akan sallayan ba, har saida ta sallame sallan isha. Haka nan take jin tausayin Baba Malam na cika mata can ƙasan zuciya, ji takeyi kamar tayi fiffige ta fire ta ganta gabanshi amman bazata iyaba ta rasa meyasa ta kasa yiwa mahaifinta biyayya. A wani yanki na zuciyarta kuwa, tana yawan tuno Ummi dasu Hayatuddeen da Raliya, musamman uban gayyan taken haɗe fuska taja tsaki duk sanda ya faɗo mata a rai. Yanzunma hakance ta kasance wani ɗan gajeren tsaki taja, tuno yadda ya rinƙa tsotse mata sweet lips ɗinta, ido ta rumtse da ƙarfi tare da cewa. "Hmmmm gwarafa dana gudu, in na tsaya wannan zalamemmen zaimin sagegeduwa, mugu duk ya lallatseni caɓɓullena,wannan in na zauna sai ya maida min nono kamar biredi ko bolon-bolon da mutumtaka ya rinƙa wani shana, mugu kawai mai idanun jaraba." a hankali ta miƙo hannunta ta jawon hand bang ɗinta wanda a ciki aka sa mata kuɗin fansan idonta da rafan sadakinta wanda Baba Malam ya damƙa mata lokacin da za'a kaita gidan wancan jarabebben. zazzage jakarta tayi gaba ɗaya kuɗin ta zubesu kan sallayar, cikin mmakin yawan kuɗin ta fara haɗe kansu, ta daɗe sosai kafin ta gama kana ta irgasu, cikin mmki tace. "Kai har dubu ɗari huɗu da talatin." Taɓe baki tayi tare da cewa. "Uhmmm kasa abokanka da ƴan uwanka zubda kuɗaɗensu a banza, ni ɗinnan dai nan gani nan bari sadakin agalawa yaseen cinye kuɗin sada kinka zanyi kuma budurcina nan gani nan bura awaran mayya ga yaji ga albasa kuma babu damar ci." Ƙasan pillow tasa ƙuɗin sabida baccin daya fara fin ƙarfinta. Daga nan kuma kwanciya tayi, domin yau ɗin da wuri taji bacci naneman ɗaukarta. Washegari. Gombe State. Tun da sanyin safiya Ya Habu ya gama kimtsawa, inda ƙarfe 7 na safiya atasha tayi masa, kasancewar a motar haya zai tafi, saboda idan yaje can ɗin, har motar da Zaleehan ta tafi dashi zai ɗauko, domin kuwa Saifuddeen ne yasaya motar, tunda ta rufe ido ta gwada cewa bata ƙaunarsa kuwa, to bazasu taɓa bar mata komai nasa awajenta, wanda yake shiya saya mata ba. Zaman ɗaki daya isheta ne yasanyata fitowa, kan wani benci dake aje a tsakar gidan ta zauna, wayarta ta ɗauka inda ta shiga latsawa, zuwa yanzu tagaji da ɗurawa cikinta kayan zaƙi, dangin su chocolate da biscuit, da ƴaƴan itatuwan kasancewar su suka zame mata abinci, duk da gidan fulanin nan suna yawan kawo mata abinci kuma Alhamdulilla ta yarda da tsabtansu kana sun iya girki sosai gata dama tana son man shanu. Ɓangaren Ya Habu kuwa, lafiya ya samu isowa cikin garin Numan, kai tsaye bakin kogi ya nufa, wato gidan Yayan Maman nasu, cikin sa'a, kuwa yana kaiwa kusa dagidan, yayi kiciɓus da Unlce ɗin nasu, fuska ɗauke da mamaki solomon ya tarbi Habu, gaisawa sukayi inda Ya habu yayi masa bayanin abun daya kawosa, sosai Solomon yasha mamakin yanda akayi suka san da cewa, Zaleehan na wajensa, don kuwa Mama tafaɗa masa cewa babu wanda yasan Zaleehan na wajensa, domin cewa dashi tayi ya ɓoye mata Zaleeha'n, ganin cewa sun gano cewar tana wajensa ne yasanya sa jin cewa bashida zaɓi, wanda ya wuce barin Habun ya gana da ita. Shine agaba yayinda habu ke binsa abaya, haka suka shiga cikin gidan. Zaleeha dake zaune atsakar gidan, jin motsin shigowar mutum cikin gidanne, yasa Zaleeha ɗago kanta, wani irin faɗuwar gaba ne da matsanaicin tsoroya ne risketa, azabure ta miƙe daga zaunen da take, tare da sanya hannu ta dafe ƙirjinta, hakan yafarune sakamakon ganin Ya Habu da tayi. Wani irin mugun harara mai cike da tsana Ya Habu ya watsa mata, tare da ɗaure fuskarsa ta mau. Ganin haka yasa ta sadda kanta ƙasa, sosai ƙirjinta ke bugawa, wani irin masifaffen tsoro haɗi da fargaba ne, suka cika zuciyarta, sosai tacika da mamakin ganin Ya Habun, don sam bata taɓa zaton cewa zasu san inda take ba, kujera Ya Habu yaja ya zauna, sake haɗe fuska yayi, tare da watsa mata harara, murya adake yace. "Ba zama nazo yi ba, maza kishiga ciki, duk wani abu da kikasan mallakin Saifuddeen ne, ki fitomin dashi, idan ba haka ba kuma na tattakaki awajen nan!." Saida cikinta ya bada wani sautin ƙuuu, domin kuwa tsawan da ya daka mata bana wasa bane. Da sauri ta juya inda tashiga cikin ɗakin, jikinta na rawa da tsuma, zamewa tayi ta zauna daɓas aƙasa, sam takasa koda kyakkyawan motsine, tsoro takeji sosai, hakanan zuciyarta ya shiga, bugun no stop, hannu tasa ta dafe dai-dai saitin ƙirjinta, dake bugawa sabida a fili ta hango tsanarta a idanun ɗan uwan nata. Shiru-shiru Ya Habu dake jiranta, yaga har yanzun bata fito ba, hakanne yasa shi fusata nan ya kutsa kansa cikin ɗakin, ganinta azaune ya sashi buga tsaki, nan ya shiga wargaza gaba ɗaya kayanta, iya abunda ya sani wanda akayi mata na gidane kawai ya barmata gaba ɗaya akwatunan da tazo dasu ya buɗe, wanda ke cike da sabin kaya, nan yaja akwatunan ya rufe, duk wani abu dayasan sabo ne wanda yake da kuɗin Saifuddeen aka saya saida ya tattare ya fiddasu tsakar gida, dubanta yayi cikin tsawa yace. "Bani makullin motar Saifuddeen wanda kika taho dashi, banza marar kunya, wanda batasan darajar kanta dana iyayen ta ba hegiya mai fuskar yahudu da nasara bakya son mutun amman kina son kayanshi." Kanta ta sadda ƙasa, lokaci ɗaya taji hawaye sun cika idanunta, tsawa ya sake buga mata tare da cewa. "Zaki bani ne ko kuma saina rabaki gida biyu!!!." Azabure tatashi inda ta ƙarasa wajen da ta aje makullin motar, da sauri ya sunkuyo ganin harda ATM ɗinta a wurin gaba ɗaya ya kwashe komai haka ya dinga jidon kayan yana sawa a motar, saida ya rabata da fiye da rabin kayan da tazo dashi gaba ɗaya, akwai sabuwar laptop ɗinta ƙiran companyn apple daya gani awajenta, shima saida ya ƙwace. Saida ya gama kwashe komai sannan ya dubeta, cikin takaicinta yace. "Kinzaɓi barin ƴan uwa da mahaifanki, akan wani banzan dalili naki wanda bashi da ƙarfi ko, good kamar yanda kika gudu da ƙafafunki, kika kuma tozarta Baba Malam, bazamu taɓa buƙatarki ba, duniya ce ae kuma gaki acikinta, saboda haka kisha zamanki ki huta cikin arnatakun, babu wani wanda zai sake nemanki, haka babu wani wanda zaizo gareki da sunan maidaki gida, in kin ga dama ki riƙe Allah da addininki in kuma kinga dama ki koma zuwa coci da cin aladu da karnuku tunda baki godewa Allah da ni'imar da ya mikiba!." Yana gama faɗan haka, ya juya yafice daga cikin gidan, motar ya shiga inda yayiwa Uncle ɗin nasu bankwana, ko mintuna 4 bai ƙaraba yayiwa motar key tare da barin ƙofar gidan. Kaitsaye ya ɗauki hanyar komawa cikin garin Gombe. Zaleeha kuwa ɗaki ta koma, inda ta faɗa kan gado, cusa kanta acikin pillow tayi tare da sakin kuka, wanda ita kanta batasan kukan na miye bane, hakanan takejin wani ƙunci acikin ranta, tabbas tanajin cewa tsanar Saifuddeen bazai taɓa gushewa acikin ranta ba, saboda duk asanadinsa tabar ƴan uwanta yayunta ƙannenta da mahaifanta, danginta aikinta har yanzu kuma tana kan bakanta na cewa bazata taɓa zama dashi ba. Kuka sosai tayi, sabida ya Habufa ya kwashe mata rabin jin daɗinta, tunowa da kuɗin data haɗa ta irga jiya da dareta ajiyesu ƙasan pillow'nta ne yasa tayi sauri tashi ta ɗaga pillow ganin suna nanne yasata jin sanyi a ranta, a fili tace. "Alhamdulilla Ya Habu mugu harda ɗaukanmin ATM to zanyi mgninka ai bari in samu caji zan yakeshe kuɗin kab in maidasu asusun Mama ko na Bilkeesu." abinda Zaleeha bata saniba tuni Habu yaje cikin numan ya yashe mata account. Dan ba wani abundan bai saniba na sirrin ƙannen nashi. Sai dare Ya Habu ya samu isowa garin na Gombe, nan ya damƙawa Baba Malam ɗan makullin motar, sannan ya nuna masa duk wani abu daya ɗauƙo, sosai Baba Malam yaji daɗin hakan, nan ya sallami Habu inda yace gobe da safe zai je har gidan su Saifuddeen ɗin. Washe gari kuwa da misalin ƙarge goma Baba Malam ya shirya tsab don zuwa gidan su Saifuddeen, bayan yasa Ya Habu yayi gaba da motar da suka amso awajen Zaleeha'n, Shida Ya Ameenu suka fita inda Ya Ameenun ne keyi musu driving, kai tsaye gidan Dirankaɗi suka nufa, wato gidansu Ishaq, kasancewar tun jiya Baba Malam ya ƙirasa sukai magana, akan hukuncin da ya yanke, koda yaje ɗaukan Dirankaɗi'n sukayi, nan suka nufo cikin federal low cost, wato unguwar su Saifuddeen, koda suka ƙaraso Ahmad ne yayi musu jagora har zuwa babban falon Ummi. Inda Ummi da Saifuddeen ke zaune. Cikin girmamawa haɗi da mutunta juna suka gaisa. gayara zama Baba Malam yayi inda yasake basu haƙuri akan abun daya faru, sosai ya basu haƙuri, hakanne yasa har Ummi saida taji kunyar haƙurin dayake ta basun. tace mishi ba komai komai ya faru yine na Allah. haka dai ya koma gida jiki a mace. Yau kusan sati uku kenan da guduwan Zaleeha, tunda aka gane inda take hankalin kowa ya konta. Amman banda Baba Malam yawanci yakan zauna yana nazarin me zaiyiwa Saifuddeen ya huce mishi baƙin cikin da ƴarsa ta cusa mishi, a cikin hakanne ya nazarto wani matakin da zai ɗauka. Saifuddeen kuwa gaba ɗaya hankalinshi na kan shige da ficen Dalla ne, dan yadda zai samu kamashi cikin laifi dumu-dumu, yayinda shima Dalla ya fahimci akwai mai bibiyarsa da bin diddiginshi, shiyasa ya sauya salo da tsarin fajircinshi dan ya sake barin gombe ma sabida ya gane ana gab da kamashi kuma binshi akeyi dan a samu kwakkwaran hujjar kamashi. Ummi kuwa tana yawan tuna Zaleeha dan ita kam har ga Allah tana son ƴarinyar, sabida ita dai bazata ce ga wani mugun abu ko raini data daɓa yi mataba cikin kwanakin da suka zauna tarenba, asalima ta fahimci yarince mai biyayya da tarbiya da iya zama da mutane. Hayatuddeen kuwa yaci gaba da zuwa makarantarshi sabonshi da Khamis yanata ƙaruwa. Amina kuwa da Asma'u har gobe suna dakon soyayyar Saifuddeen a ransu, A hankali ya gama kimtsa kanshi cikin wani tattausan yadi mai azabar kyau da taushi yadin farine ƙal-ƙal sai ɗigo-ɗigon bulu mai haske, an mishi ɗinkin mai kyau dai-dai da jikinsa an ɗan tattarfa surfanin bulu a aikin rigar, hular kanshi fara mai ratsin bulu, kana sai takalmansa sau ciki mai kalar bulu sai igiyansu daya kasance farare. Manyan idanunshi ya buɗe tare da kallon fuskarsa a madubin jikin durowar tashi, a hankali ya fidda sassanyan numfashi tare dasa tattausan tafin hannunshi ya shafa sajenshi da ya kwanta lib yayiwa fuskarsa ƙawanya, lips ɗinsa ya ɗan tsotsa tare da turosu gaba, wayarshi ya ɗauka ya da niyar zurata a aljihun gaban rigarshin sai yaga shigowar saƙo, Ganin Bappa Aline ya sashi buɗe saƙon. "Sallamu alaikum, Saifuddeen ka cewa Umminku yau ina kan hanya nida Malam Ashiru, dan surkinka yace yana buƙatarmu, to yanzuma muna tahowa, yace kuma zaizo har gidan ya samemu, to nayi ta kiran wayan Unminka bata shiga." Idanunshi ya ɗan lumshe tare da buɗesu a ranshi yace. "To wai meyasa Baba malam ya kasa kontar da hankalinshi ne a kan batun wannan fitinanniyar yariyar tasa, infa har yazo yau to zuwansa na uku kenan yana bamu haƙuri." Kai ya ɗan jujjuya kana ya rubutawa Bappa Ali amsa ya tura mishi. Daga nan ya zura wayar a al'jihunshi kana ya fice ya nufi side ɗin Ummi. Shiru falon ba kowa dan haka kai tsaye ya wuce bedroom ɗinta, kan sallaya ya sameta bisa dukkan alamu tayi walahane, shiru yayi yana kallon yadda ta ɗaga hannayenta sama tana kwaranyo musu addu'o'i shida ƙannenshi, wanda mafi yawan addu'ar a kanshi ne a hankali take cewa. "Ya Allah ga bawanka Saifuddeen cikin matsalolin rayuwar daka jarabceshi, ya Allah ina mai roƙa masa sassauci da salama da sauƙi a rayuwarshi ta duniya da lahira. Ya Allah ka yaye mishi duk wani cuta dake jikinshi ka bashi lfy ka ƙaddara mishi sake miƙewa saye da sawunshi da sake mgna da ji, Ya ubangijin talikai ka yassare masa ƙofofin samunshi gabas da yamma kudu da arewa, ya Allah ka al'barkaci kasuwancinsa ka tsare minshi daga sharrin mahassada damasharranta tsakanin mutun da al'jan, ya Allah ka tsare min imaninshi ka bashi ikon cinye jaraboɓunshi." Sai ta kuma ƙara ɗaga hannu cikin kushu'i da ƙanƙan da kai take cewa. "Ya Allah kayi mishi zaɓi mafi al'khairi tsakaninshi da matarsa Zaleeha in ita al'khairinsace Allah ka bashi haƙuri da juriyar duk wani abinda zai faru daga gareta, in kuma ita ba al'khairinshi bace, ya Allah ka musanya musu da abinda yake al'khairi a garesu baki ɗaya. Ya Allah ka karemin surkata a duk inda take." sosai Saifuddeen yake wani irin lallausan murmushi yayinda shima ya ɗaga hannayenshi sama yana mai amsa cikin ransa da . "Amin Amin. Ameen ya rabbil izzati ya Ummi." sosai ya tsura mata ido likacin da take cewa. "Ya Allahna ga ɗana Hayatuddeen cikin ganiyar ƙuriciya da tashen balaga ya Allah ka shirya minshi ka tsare minshi, da tarbiyarsa ka kare min imaninshi ka sa mishi nitsuwa da kamala kwatan-kwacin na ɗan uwanshi, ya Allah ka yaye mishi wannan rawan kan da gigin ƙuruciya". Sosai yake Murmushi Allah sarki Ummi wato rawan kan Hayatuddeen na tsoritata. numfashi ya sauƙe a hankali ganin tana cewa. "Ya Allah ka al'barkaci ahlina ka shirya minsu dama dukkan al'ummar musulmai ka azurta ɗiyata Raliya da samun haihu da ƴaƴa na gari ka basu zaman lfy da mazajensu." Haka dai tayi ta musu addu'a yana mai amsawa da amin. A tare suka shafa addu'an, kana ta juyo ta fuskanceshi da kyau cikin sakin fuska tace. "Dama kana gidane!." Kai ya jinjina mata tare da mata bayanin zuwan bappa Ali da Baba Malam, ya ƙara da cewa Bappa Ali yace sun tasoma dan haka zai jirasu kawai. kai ta gyaɗa tare da miƙewa ta cire hijabin jikinta tana mai ninkewa take cewa. "Eh lallai Faroq ya ɗauki wayar yana game to inaga ya gama da cajinta ne , dan naga yazo ya sata a cajin. jin haka ya ɗan juyo ya jawo wayar dake haɗe a caji nan kuwa ya samu a kashen take. juyawa yayi ya fito falon Ummi na biye dashi a baya tana gyara mayafin jikinta. Suna zama ba jimawa kuwa su Bappa Ali suka iso. suna cikin gaggaisawa ne Baba Malam da Malam Adam da Dirankadi suka iso bisa jagorancin Ahmad wanda yanzu ya dawo gida dan kiran bappa Ali daya samu. Falon shiru bayan duk sun gama gaggaisawa, A hankali Ummi ta miƙe da niyar basu wuri a matsayinsu na maza kuma manya su tattauna komai tsakaninsu, sai kuma ta koma ta zauna jin Baba Malam yana cewa. "Uhummm Ummin Saifuddeen zauna, akwai mgna mai mahimmancin da nake son muyi ne." shiru tayi cikin jin tausayin mutumin wato wannan shine ɗan kuka mai jawa uwarsa jifa." Duk shiru sukayi suna sauraranshi. Shi kuwa gyara zama yayi cikin nitsuwa da cikar kima yayi gyaran murya tare da cewa. "Da forko dai zan fara da baku haƙuri akan rashin ɗa'a da Zaleeha tayi mana baki ɗayanmu, wanda nake zargin kaina da cewa duk nine sila, tunda ku dai kun so'a janye batun auren tun kafin ayi auren, ni na kafe nace ayi sabida zatona itama irin Maryam ce in anyi auren zatayi biyayya ta zauna ɗakinta, amman sai gashi ta samu asarar lokaci da dukiya da mutuncina ta gudu ta watsar da auren." shiru yayi sabida yadda Bappa Ali ya fuskanceshi tare da cewa. "Dan Allah na roƙeka Malam Bashiru ka daina bamu haƙuri da ɗaurawa kanka wannan laifin, Wannan aurefa nufine na Allah, Allah ne ya ɗaura aurennan kafin mu muka ɗaurashi, kuma har gobe muna kyautata zaton zata dawo ɗakinta ta zauna." Malam Ashiru ne ya amshi zancen da cewa. "To mun isa muja da ikon Allah ne, babu laifin kowa a cikinmu, da Allah malam Bashiru ka daina tada hankalinka kam zancen yarannan." ita dai Ummi shiru kawai tayi, Saifuddeen da Ahmad shirun sukayi. Sai kuma Dirankadi da Malam Adam ne suka ƙara kwantarwa Baba Malam hankali kan dan Allah kada ya sake zuwa da batun badu haƙuri. Cikin jin sanyi a ranshi ya kallesu baki ɗaya kana ya fuskanci Saifuddeen da kyau cikin sanyi yace. "Dan Allah Saifuddeen ina neman wata al'farma a wurinka." da sauri Saifuddeen ya nuna kanshi da ƴar yatsarshi alamun. "Ni kuma al'farma kuma?." Kanshi gyaɗa mishi alamun eh kai ɗin dai. sai ya kuma gyara murya da zama kana ya kalli Ummi, Bappa Ali da kuma Malam Ashiru yace. "Ina neman al'farma a wurin ɗanku ɗalibani kuma surkina a wani sashin kuma ɗana. Dan Allah Saifuddeen kayi haƙuri akan duk wani abun da Zaleeha tayi maka daka riƙe igiyar aurenka da ita naroƙi al'farma a wurinka da iyayenka duk rintsi kada ka saki Zaleeha, lallai kam nasan saki halalne duk da ubagiji baya son shi, ina roƙonka da Allah da manzonsa kada kayiwa Zaleeha abinda take buru da son kayi mata ka riƙe igiyar aurenku duk rintsi, domin inada yaƙinnin wata rana zata dawo gareka." ya ƙarishe mgnar cikin rauni da alamun neman al'farma. Su kuwa gaba ɗaya idanu suka zubawa Saifuddeen daya fara musu bayani da yarensu na kurame wanda gaba ɗayansu suna gane hakan, A hankali ya matso gaban Baba Malam cikin tanƙwashe ƙafafu yace. "Baba Malam umarni zaka bani ba neman al'farma ba, in sha Allah bazan saki Zaleeha ba, ka daina tada hankalinka." shafa kanshi Baba Malam yayi tare da cewa. "Ngd ngd Saifuddeen Allah yayi maka al'barka ya azirtaka da yara masu biyayya." Amin Amin suka amsa baki ɗayansu, Ummi kuwa sosai taji daɗin addu'arshi ga Saifuddeen ɗinta, Shi kuwa Baba Malam kallonsu yayi baki ɗaya kana ya fuskanci Saifuddeen da kyau cikin muryar bada umarni yace. "Maganata ta gaba ba al'farma nake nema a gareka Saifuddeen umarnune nake baka a matsayina na Malaminka kuma surkinga, ina mai baka umarni da fito da wata matar auren zan aura maka ita ko ƴar wayece ni ne nan zan auro maka ita, Saifuddeen aure za ƙarayi, a cikin watannan!." Wani irin zabura da zare ido Saifuddeen yayi cikin tsananin mmki da kaɗuwa ya fara nuna kanshi da alamun tambaya. "Aure kuma? Ni kuma inyi wani auren kuma, to ita Zaleehanfa, in mata kishiya." Dirankadine yayi murmushi tare da dafa kafaɗun Saifuddeen ɗin. Jin an dafashi ne ya sashi juyowa ya kalli wanda ya dafashin kai ya runƙa jujjuyawa jin Dirankadi na cewa. "Haba Saifuddeen aurefa akace kayi ba yaƙiba, me na wannan firgitan da ɗimaucewa, to kai a zatonka barinka zamuyi ka zauna ba matane?." Kainshi ya jujjuya tare da zaro wayarshi ya fara rubutu dan yanaga kamar dai basa fahimtarsa ne. "Baba aure kuma, ko wata ɗaya banyi da yin aureba, yaza'ayi kuma inyi wani auren, ina da mata ai zata dawo, dan Allah baba ka bawa Baba Malam haƙuri, bazan fa iya zama da mata biyu ba." Murmushi Dirankadi yayi tare da cewa. "Me zai hana Saifuddeen tsab zaka iya zama da mata biyu." Wayyo Ahmad kam ji yake tamkar ya tashi ya rinƙa taka rawa dan daɗin wannan umarni na Dottijon arziƙi Baba Malam, a ranshi yake cewa. "Hegiya ifiritiya kin jazawa kanki kishiya, Aure nai dai in sha Allah za'ayishi." Ummi kam ita kanta taji daɗin wannan abu, Yes tunda ɗanta nada lfy har yanada muradin aure ainyi kuma ta gudu asheko dole a nemo mishi wata matar. Murmushi tayi lokacin da Saifuddeen ya juyo yake mata mgna da yarensa. "Wai Ummi kema naga murmushi kikeyi, nifa mijin mace ɗaya ne, ta yaya zan ƙara wani auren?." Cikin dariya tace. "A a to ni kuma ina ruwana, ka dai ji umarni ne yace ya baka ba neman al'farmaba." Tirƙashi wannan shine ana wata sai ga wata, kawai shi kam Saifuddeen ido ya zuba musu ganin da gaskefa sukeyi kuma Bappa Alima yayi na'am da hakan har cewa yake. "Ahmad kuyi ƙoƙari ku fito da matar aure dan cika umarnin surkinku, kunji dai yace nanda mako biyu yakeso ayi auren,." Wani mugun harara Saifuddeen ya dannawa Ahmad ganin yadda yaketa dariyar jin daɗi harda cewa. "In sha Allah kuwa, Kawu Ali zumu fito da matar, ayi komai kamar yadda malam yake so." Shi kuwa Baba Malam cikin son kontarda hankalin Saifuddeen yace. "Ka nemo matar da take sonka, Ni zanyi maka komai na auren ko sisinka bana buƙata." Shifa yanzu ganinsu yake kamar al'mara, su kuwa nan suka gama tattauna komai. Ganin azahar tayine yasa suka yi addu'a suka tashi a taron kana suka sallami Ummi suka fita baki ɗayansu su. Anan matsallacin jikin gidan nasu sukayi salla kana su Baba Malam da Dirankadi da Malam Adam suka tafi. Su bappa Ali kuwa suka dawo cikin gida sukaci abinci sannan suka ƙara jaddawa Saifuddeen batun auren sannan suka tafi. Su Babba Ali na fita Ahmad ya kwashe da dariya harda dukan cinya cikin jin daɗi ya kalli Saifuddeen daya haɗe fuska girarshi ɗaya ya ɗaga mishi tare da cewa. "Ya akayi ne angon mata biyu a wata ɗaya, kai Alhamdulillah lallai wannan dattijon ya cika adali mutun, kaga nanda mako biyu kana tare da sabuwar amaryarka dal a leda." Wani irin bugu ya ya kaiwa Ahmad, da sauri ya kauce tare da cewa. "Sai fa an maka auren na." Dariya Ummi tayi ganin yadda Saifuddeen ɗin ya haɗe fuska cikin dariyar tace. "To wai duk wannan haɗ...! Littafina na kuɗine turo katin mtn na 300 ta wannan numbers 09097853276 ko ta asusuna na 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Masu iya magana dai sunce kyauta da kayan wani mugunta dan haka masu fitarmin da littafi ku bari, By *GARKUWAR FULANI* [06/09, 3:30 pm] اسماء بشير:                              "Wai Duk wannan haɗe fuskan na memene wai? dan ance za'a ƙara maka aure?." kanshi ya sunkuyar ba tare da yace komaiba. Ahmad ne ya gyara zama tare da duban Saifuddeen ɗin, cikin zolaya yace. "Manya kenan angon mata biyu, gaskiya bakowani namiji bane zai taki sa'a irin wanda ka taka, auren mata biyu awata ɗaya kacal, lallai Saifuddeen kai ɗan gata ne." Harara Saifuddeen ya watsa Ahmad ɗin tare da haɗe fusks, wani irin abu yakeji a maƙoshinsa, sam shi atsarinsa babu auren mace wanda ta wuce sama da ɗaya a rayuwarsa. Ummi ne ta ɗan saki murmushi tare da duban Ahmad, cikin kulawa tace. "Ni kaina naji na gamsu da batun ƙarin auren Saifuddeen, amma kuma sai-dai bansan wace kalar matar kuma zai ƙara samowa ba, musamman ma yanzu da yace babu wata wacce ya keso." Murmushi Ahmad yayi cikin nutsuwa yace. "Saifuddeen ai mai farin jini ne, muna nan zaune zamuga wata santaleliyar budurwa ta bayyana, don neman aurensa! In wata ta gudu wata zata zo. Ita kuwa ɗiyar taki Zaleeha in taga dama tafi ruwa gudu." ya ƙare maganar yana  gimtse dariyarsa, don sosai yakejin wani irin farin ciki yau ɗin, don yasan ta hanyar ƙarin auren Saifuddeen ɗinne kaɗai Zaleeha zata shiga cikin sense ɗinta kuma tanannne Saifuddeen zai samu nitsuwa. Cin ƙufula Saifuddeen ya ɗauki ɗaya daga cikin pillow kujerun falon, nan ya wurgawa Ahmad ɗin, da sauri Ahmad ya kauce yana dariya,   duban Raliya dake zaune Ahmad yayi, cikin son ƙara tsokar Saifuddeen ɗin yace. "Nikam zan fita, idan na fita kuwa sai inda mai na ya ƙare, saboda zan zaga gari, ko Allah ma zai sa na samawa ɗan bazawarin abokina mata ta biyu!." Yanzun kam harta Ummi saida tayi dariya, shikuwa Saifuddeen sake kwaɓe fuska yayi nan yasake wurgawa Ahmad ɗin pillow, da sauri Ahmad ya kauce kana ya fice daga cikin falon yana murmushi. Ahankali ya danna madannin wheelchair ɗinsa, inda ya ƙaraso har gaban Ummi dake zaune,  Raliya kuwa miƙewa tayi inda tabi bayan mijinta. Hannun Ummin Saifuddeen ya kamo, karyar da wuyansa yayi, tare da shagwaɓe fuska, narai-narai yayi da idanunsa, tare da ɗan yaɓe lips ɗinsa, hakan yasa yanayinsa ya koma kamar na ƙaramin yaro,  ganin yanda yayi da fuskar ne yasa Ummi fuskantar me yake nufi, cikin yanayin lallashi ta kama hannunsa, tausasa murya tayi tare da cewa. "Nasan bakaso amma haƙuri zakayi ka ƙara auren nan Saifuddeen, tun da dai kaga shi baban Zaleehan da kansa ya faɗa, kuma ai dai nasan kafahimci me yace, tun da dai yace akan maganar ƙarin auren,  ba shawara yake ba ka ba, umarni ne." Kai Saifuddeen ya ɗan girgiza, tare da ɗan lumshe idanunsa, kana ya buɗe su alokaci guda, duban Ummin nasa yayi, cikin body language ɗinsa yake yi mata alaman cewa. "Bashi da ra'ayin ƙarin aure, sam babu auren mata biyu atsarinsa, idan ma ya ƙara auren ya zaiyi da matar?." Kanshi ta shafa cikin bashi ƙarfin guiwa tace. "Je kasha maganinka, daga gobe zamuyi mgnar, kana Kayita Addu'ar Allah ya tabbatar maka da al'khairi a cikin lamarin." Kanshi ya gyaɗa mata cikin bin umarninta ya juya ya nufi side ɗinshi. Ita kuwa ta koma cikin ɗakinta zuciyarta fal farin ciki, Adda Rahama ta kira ta sanarwa abinda ke faruwa, abinda yayi matuƙar faran ta mata rai, nan tace. "In sha Allah zanzo in ya Adnan ya barni." "Allah ya kaimu." cewar Amin Amin ta amsa kana sukayi sallama. Washe gari da yamma, Saifuddeen na zaune gaban Umminshi cikin nitsuwa yake mata tambayar meyasa zata bari aƙara mishi aure bayan tasan shi mai raunine. Wani irin yalwataccen murmushi Ummin tayi tare kamo hannunshi, bata kai ga basa amsa ba. Adda Rahama wanda tun ɗazun ta shiga kitchine haɗo wa kanta abun da zata ci, ta dawo cikin falon, zama tayi tare da duban su Ummi'n. Nan Ummi ta sauƙe ajiyar zuciya tare da duban Adda Rahama'n, cikin kulawa tace. "Kinjisa wai shi bayason wani ƙarin aure, waishi mai raunine." Dubansa Adda Rahama tayi cikin kula tare da ɗan nutsuwa, cikin son fahimtar dashi tace. "Akan maganar ƙarin auren nan, ba wai zaɓinka aka nema bafa, zaɓin da aka baka dai kawai shine ka fito da wata, wanda kake ganin ta kwanta maka arai, amma ƙarin aure kasa aranka cewa in sha Allah babu fashi, ita wanda kake mutuwar so ɗin ba guduwa tayi daga gareka ba, saboda haka nidai ina goyon bayan da kasakeyin wani auren, don gaskiya bazamu barka kaci gaba da zama ahaka ba." Fuskarsa ya haɗe tare da dubansu su duka biyun, cikin body language ɗinsa, yayi musu alaman cewa. "Ahakanne zai ƙara aure bayan ko yaushe bisa keke yake, kodai sun manta cewa shi ba cikakken lafiyayye bane, ko kuwa sun manta da cewar shiɗin mai rauni ne, ayanda yake ma gaskiya baijin zai iya zama da mata biyu." Murmushi Adda Rahama tayi tare da tasowa, ta ƙaraso inda yake, hannunta ta sanya inda ta dafa kafaɗunsa, cikin ƙauna haɗi da tausayinsa tace. "Ni na tabbatar kai ba rago bane, nasan zaka iya rayuwa da mata huɗu ma ba biyu ba,  kai jajirtaccen Namiji ne Saifuddeen, saboda haka kada kabari rauni ya ziyarci tunanin ka, tun ada kai jarumi ne, haka ayanzu ma kai ɗin, you are the super hero, sannan kafi kowa sanin nakasa bata taɓa zama kasawa, sai-dai ga wanda ya bari zuciya da kuma tunaninsa suka mace, saboda haka ako yaushe kasa azuciyarka cewa, kai ɗin jarumi ne!! Sai dai kuma in salon tirjiyarka ce hakan". Taƙare maganar tana me ɗan bubbuga kafaɗunsa tana murmshin zanca wai shi mai raunine kaji yaro da wayo wato ace bazai iya jure mu'amala da mata biyu ba. Shiru yayi tare da lumshe idanunsa,  hakan na nufin cewa kenan bashida wani zaɓi? ko kuwa dai ƙaddaransa ne take ƙoƙarin canzawa? Ganin yayi shiru ne yasa Adda Rahama komawa kan kujera ta zauna, nan ta shiga cin abincinta hankali kwance. Da sallama Hayatuddeen ya shigo cikin falon Ummi, ganin su azaune ga kuma Hammansa daya haɗe fuska, yasan yashi ƙarasowa cikin falon, jakar makaranta da kuma littatafan dake hannunsa ya watsa akan kujera, zama yayi daɓas akan sofa, tare da miƙe ƙafafunsa, cikin shagwaɓa haɗi da kasala ya ɗago indo ya dubi Ummi, asangarce yace. "Ummi am so tired, ƙafana bayana kaina idona kunennena ɗuwawuna kai ko'ina ɗina ma ciwo suke min!." Murmushi Ummi tayi, tare da cewa. "To sannu auta na, ae dai ku kam gaba ɗayan ku haka kuke, abu kaɗan ke gajiyar daku, sai kace ba gwaraza ba." Sake shagwaɓe fuska yayi, cikin salon sakalci yace. "Wallahi Ummi makaranta ba daɗi, duk acika ku da lectures, yau fa ko ɗan hutu bamu samu ba." Ƙare maganar yayi yana me ɗago kansa, inda ya kalli Saifuddeen, wanda ya haɗe fuska, inda ya kawar da kansa gefe, da'alamu cewa ba ya cikin yanayi me daɗi, cikin kulawa haɗi da faɗuwar gaba, asanyaye Hayatuddeen ɗin yace. "Hamma!." Kasancewar Saifuddeen ɗin ya juyar da fuskarsa, zuwa wani ɓangare na daban hakan yasa baiji ƙiran da Hayatuddeen ɗin yayi masa ba, don dama sai yana kallon ka ne, sannan yake karantar abun da kake faɗa, ta hanyar kallon yanayin motsin bakinka shiyasa yake da yawan kallon ammanfa ga wanda yake son ya gane abinda zai faɗa. Ganin Hamman nasa baisan da cewa yanayi ba, hakan yasa ya taso da sauri ya, ƙarasowa gaban Hamman shi hannunshi ya ɗaura a akan kafaɗan Hamman nasa, ahankali Saifuddeen ya ɗago da kansa, duban Hayatuddeen ɗin yayi, sai kuma ya kau da kansa gefe. Hakanne yasa jikin Hayatuddeen yayi sanyi sosai. A take kuma yaji gabansa ya faɗi, ƙirjinsa ne ya shiga duka, cikin zuciyarsa yace. "Nashiga uku badai Hamma na yasamu labarin cewa, yau na fita amakaranta, na bi Khamis muntafi yawo ba?." Cikin ɗari-ɗari da fargaba ya kalli Ummi, wanda ke ƙoƙarin tashi, don komawa ɗaki, da sauri ya rufa mata baya, jin mutum abayanta yasata juyowa, kafe Hayatuddeen ɗin tayi da ido, tare da cewa. "Lafiyanka ƙalau kuwa kake biye dani, sai kace wani ƙaramin jariri, kodai ka aikata wani rashin gaskiya ne?." Ummi tafaɗa tana me ƙare masa kallo, don tsab tasan yaranta, da zaran sunyi wani abun da ba dai-dai ba, takan saurin ganewa, ko daga halin rashin nutsuwa da zata gansu aciki, kamar dai yadda ta fara zargin yanayin canji nitsuwar Hayatuddeen. Ƙifi-ƙifi Hayatuddeen ɗin yayi da idanunshi tare da cewa. "A'a babu abun danayi, kawai dai naga ran Hamma Saifuddeen ne kamar aɓace yake." Ajiyar zuciya Ummi tayi tare da cewa. "Hmm rabu da Hammanku, gata ake son a mishi shi kuma wai baya so." Da sauri yace. "Ummi wanne irin gatane?." murmushi tayi tare da cewa. "Wai fushi yake don ance masa ya ƙara aure, shine yake ta faman haɗa rai sai kace wanda akace yayi wani abun, wanda ba dai-dai ba." Cikin zaro ido Hayatuddeen yace. "Haaah Ummi to kuce ni inyi auren mana, tunda shi baya son gatan ni kuyi mini." Cikin mamaki da al'ajabi da zazzaro ido Ummi tayi kana tayi kasake tana kallonshi da nazartanshi. Shi kuwa da sauri ya dawo nitsuwarsa gudun karta ramfoshi. Ajiyar zuciya mai ƙarfi Hayatuddeen ya sauƙe, ya godewa Allah da yasa, ba asirinsa bane ya tonu, domin yasan tabbas idan Hamman nasa, ya gane irin abubuwan da yake yi, to fa kashinsa ya bushe, yasan sai anrabasa da duk wani abu nasa najin daɗi. Gyara tsayuwarsa yayi tare da cewa. "To Ummi me yasa zai ƙara aure, yaushe ma yayi auren?." Harara Ummi ta watsa masa, tare da cewa. "To kai mekasani acikin aure da kake tsoma baki cikin abun  da babu ruwanka?." Kanshi ya jujjuya tare da cewa. "Wallahi ba abinda na sani, kawai a auro mishi mai sonshi tunda hegiyar nan taƙi zama." haɗe fuska Ummi tayi tare da cewa. "Hayatu baka da kunya fa ba yayarka bace kake ce mata hegiya, to a kul wlh kada in sake jin ka zagarmin ƴata dan mu dai Zaleeha bata ƙi muba bata mana wani laifiba ita dai auren ne da bata so." Murmushi yayi tare da ɗan shafa kansa yace. "Afwan ya Ummi bazan sakeba, nima nasan Zaleeha na sonmu amman dai ina jin haushinta in na tuno wai bata son Hamma nane yasa ta gudu." ya ƙarishe mgnar tare da, juyawa ya inda ya fice daga cikin ɗaki, a falo ya samu Adda Rahama, har yanzun Saifuddeen na zaune afalon,   komawa kan sofa yayi ya zauna, inda ya matso kusa da Adda Rahama wanda kecin abinci,  dubansa Adda Rahama tayi tare da cewa. "Bafa zanci dakai ahaka ba, jeka wanko hannunka." Ɗan shagwaɓe fuska yayi tare da cewa. "Dan Allah Adda Rahama, muyi karɓe-karɓe, don nagaji, dama kafun na zauna ne kikace na wanko hannun nawa." Kai Adda Rahama ta girgiza tare da cewa. "Allah ya shiryeka, sarkin lalaci kawai, da ace kai mace ne, tabbas da anyi uwar son jiki." Murmushi kawai yayi tare da amsan spoon ɗin dake hannunta, haka suka shigayin karɓe-karɓe, idan tayi loma guda, ta bashi spoon ɗin shima yayi, duk wai saboda tsananin ganda, ɗauko spoon kaɗai ya gagaresa. Ummi ce tafito ɗaga cikin ɗaki, hannunta ɗauke da wayarta, duban Saifuddeen tayi tare da cewa. "Bappa Ali ne ya ƙira." Ɗago kai Adda Rahama tayi tare da cewa. "Akan maganan auren ne ko?." Kai Ummi ta jinjina tare da cewa. "Ƙwarai kuwa, koda na faɗa masa cewa, babu wacce ayanzu Saifuddeen ɗin keso, cewa yayi wannan ba uzuri bane, za'a ne mamasa ko acikin dangi." Idanu Saifuddeen yaɗan zaro waje, kasancewar yana kallon Ummin nasa, hakanne yasa ya fahimci me take faɗa. Murmushi Adda Rahama tayi, ɗan satan kallon Saifuddeen ɗin tayi, cikin kulawa tace. "Hakan ma yayi, tun da dai shi yace bashida zaɓi." Hayatuddeen ne ya ɗago kai tare da duban Ummi, cikin nutsuwa yace. "Acikin dangi kuma tab, nikam dai banso Hamma ya yi auren dangi, to idan ma hakane ae ga nan Amina da Asma'u, duk suna sonshi, musamman  ma Ameena, dake bala'in sonsa ae sai ya zaɓi ɗaya acikin su ko?." Ɗan jim Ummi tayi, nan kuma tasaki murmushi, cikin gamsuwa da kalaman Hayatuddeen tace. "Tabbas, ka ga kuwa ni na manta ma da batun Ameena, gaskiya yarinyar akwai hankali, sannan kuma tana da kirki sosai, don ko lokacin da yake jinya a Hospiatal ɗin Abuja, ta kula dashi sosai, gaskiya na yaba da hankalinta sosai tana son Babana." Duban Ummi Adda Rahama tayi tare da cewa. "Okay wannan nurse ɗin ba, gaskiya nima yarinyar ta kwanta min arai, sai-dai kuma wacece Asma'u, don ban shaida ta ba." Carab Hayatuddeen yayi inda yace. "Wata jarumar film ne, kinma santa ae, wannan Asma'u Ahmad Matawalle wanda take rawa da waƙa, tauraronta yana haskawa sosai." Idanu Adda Rahama ta ɗan zaro tare da cewa. "Mai rawa da waƙa kuma? chab awani gidan? gaskiya a'a, Ameenan dai tayi, don ƴar gidan mutumci ce da dukkan alama, kuma Saifuddeen da yawan kishi ai bazai iya aurenta ba." Cikin gamsuwa Ummi tace. "Tabbas nima Ameenan tafi kwanciya min arai, don dai ita Asma'un kam sam batayi ba, don idan ma muka zaɓeta bamusan da wanne ita kuma zata zo ba, duba da irin lalurar da yake fama da ita ma, sam baidace ya auri wata ƴar nanaye ba, wanda suka saba cuɗanya da maza, ko yaushe suna cakuɗe da maza awaje guda ga Saifudden da ɗan karen kishi, balallai ma yasamu ingantacciyar kulawa daga gareta ba, Ameena ɗin dai ita muka zaɓa." Nan Adda Rahama ta jinjina kai cikin gamsuwa. Shikuwa Saifuddeen daya duƙar da kanshi kasa, sai alokacin ya ɗago, kasancewar bai kallesu ba, hakan yasa baiji mai suka tattauna ba. Madanannin wheellchair ɗinsa ya danna, kai tsaye yanufi hanyar barin falon, don yagaji so yake yaɗan je ya kwanta ya huta. Yana fita Ummi ta dubi Hayatuddeen wanda keta aikin zubawa cikinsa abinci, cikin kulawa Ummi tace. "Hayatuddeen bani wayarka." Adaburce ya ɗago kansa, kasancewar yakai loman abinci bakinsa, hakanne ya sakashi ƙwarewa, take tari ya sarƙesa, da mamaki Ummi ke kallonsa, yayinda Adda Rahama kuma keyi masa sannu, botle water ta miƙo masa, nan ya amsa haɗe da kafa bakin goran abakinsa, saida yasha sosai kafun yaji ya samu relief,   cikin kulawa Ummi tace. "Sannu, haba kaima sai cikawa cikin ka abinci kake babu ko tsayawa, tayaya bazaka ƙware ba, bacin abincin ba guduwa zaiyi ba, kana abu kamar mara gsky." Shiru yayi tare da ƙoƙarin neman hanyar barin falon. Dubansa Ummi tayi tare da cewa. "Ina kuma zakaje? bacewa nayi kabani wayarka na ɗau number'n Ameena ba." Jin haka yasashi sauƙe gagarumar ajiyar zuciya,  zaro wayar daga cikin al'jihun wandonsa yayi, nan yashiga contact ɗinsa, inda ya laluɓo number'n Ameena'n, nan ya miƙawa Ummin nasa. Tsab Ummi ta kwafe number'n Ameena'n, inda ta sanya awayanta, kana ta miƙa masa wayarsa, haka ya wuce sama sumu-sumu, daganinsa kasan bashida wadataccen gaskiya. Nan Adda Rahama da Ummi suka ci gaba da tattaunawa akan sabon auren da za'a ƙarawa Saifuddeen ɗin, sai ayanzu ne suma suke ganin cancantar yin hakan, saboda Zaleeha ta gujesa, tana ganin cewar shi nakasashshe ne, yayinda su gani sukeyi dan shi nakasasshene yasa ta gujeshi sannan babu wata mace wanda zata iya zama dashi, hakan yasa dole ne ma su Aura masa Ameena, tun da dai ita tana son shi, sun tabbatar da cewa kuma zata kula dashi. Sun ɗan taɓa hira kafun Adda Rahama ta tafi, Ummi kuma ta nufi ɗaki ta kwanta, bayan taƙira Bappa Ali ta sanar masa zaɓin da tayiwa Saifuddeen ɗin, sosai shima Baffa Ali'n yayi na'am da batun, nan take yaƙirayi Baba Malam ya sanar masa, da batun,  sosai Baba Malam yaji daɗi, don kuwa ko ba komai hakan da sukayi sun karramasa. Saifuddeen kuwa yana shiga ɗakinsa, ya soma rage kayan jikinsa,  ƙarasawa gaban tankamemen bed ɗinsa yayi, nan ya sauƙa akan wheellchair ɗinsa, inda ya hau gadon. Lumshe idanunsa yayi tare da jawo blanket ya rufe jikinsa,   maganar ƙarin auren nasa daya dawo cikin kunnensa ne, ya sashi jin wani ɗaci a maƙoshinsa, sam shi baima ɗauki abun agaske ba, yasan suna faɗa ne kawai, amma shi ina yaga ta wani ƙara aure, shiru zaiyi ya ƙyalesu, yasan nan da kwana biyu suma zasu daina batun. Yana nan kwance, yaji vibration na wayarsa, don dama akusa dashi take. Kasancewarsa wanda bayajin magana, ko kuma wani sauti, hakan yasa koda yaushe wayarsa a vibrate take,  domin ta hakanne kaɗai zai gane cewar an turo masa saƙo, domin idan kunnensa baya ji, to ai jikinsa naji, don aduk sanda wayan ke kusa dashi, ko kuma take jikinsa, to zai jita tana rawa, hakan kuwa alamane na cewar an turo masa saƙo, ɗaukan wayar yayi tare da dubawa, ganin  saƙon na Ummin sane ya sashi buɗewa. Number'n wayane arubuce da kuma rubutu aƙasan sa kamar haka. "Wannan number'n itace number'n matar da na zaɓa maka amatsayin wacce zaka aura, saboda haka kayi saving ɗinta." Yana gama karanta saƙon ya tashi zaune cikin hanzari, jiyayi gabansa ya faɗi, cikin sauri ya jawo rigarsa wanda ya cire, nan ya sanya tare da hawa kan wheellchair ɗinsa, ahanzarce ya nufi part ɗin Ummi'n dan yafa lura su da gask suke nufin ƙara mishi auren. Koda yaƙarasa falon ta bai ganta ba, kai tsaye yanufi bedroom ɗinta. Tsayawa ajikin ƙofar yayi, tare dayi mata knocking,  Ummi dake kwance jin ana knocking yasa ta tashi ta zauna, murmushi tayi don tasan cikin biyu za'ai ɗaya, ko Saifuddeen ko kuwa Raleeya. "Shigo." Ta faɗa ataƙaice. Da sauri ya tura ƙofar ya shiga, Ummi na ganinsa taɗan tsume, tare da dubansa. Ƙarasowa yayi har gabanta, inda ya kamo duka hannayenta, kansa ya shiga girgiza mata, alaman "a'a." murmushi tayi tare da cewa. "A 'a me? bazakayi auren ba ko kuwa me? ko bakason zaɓin danayi maka, ba kuma zaka iya karɓanta matsayin zaɓina ba?." Shiru yayi tare da ɗan lumshe idanunsa, kansa ne ke sarawa, cikin body language ɗinsa, yace. "Bawai zaɓinki bane banaso Ummi, ni auren ne banaso, ki dubeni ki gani fa, tayaya zan iya rayuwa da mata biyu, ko kun manta abun da Dr. ya faɗa ne, ina ɗauke da nakasa banjin cewa, zan iya bawa mata biyu kulawan daya dace dasu ba." Dariya Ummi tasanya, tare da dubansa, saida tayi dariya sosai sannan taɗan soma tsagaitawa, shikuwa Saifuddeen kafeta yayi da idanunsa, tare da sanya mata fuskan tausayi. Ɗan tsagaitawa da dariyan Ummi tayi tare da cewa. "Ikon Allah, Yau kuma Saifuddeen kaida kanka kake ƙiran kanka da Nakasashshe? duk saboda ance ka ƙara aure shine har ka aminta cewar kai nakasashshe ne, har kuma ma kake ƙiran kanka da hakan, tsawon lokaci ban taɓa ji kaƙira kanka da wannan sunan ba, amma yau sai gashi da bakinka ka faɗa, ka kuma nanata.  hmmm lallai ma kuwa to wallahi in sha Allah auren nan babu fashi, sai anyi shi, na kuma gama yi maka zaɓi, umarni ne idan kuma kace a'a, shikenan saika ƙira surukin naka wanda ya yanke hukuncin, kace masa kai bazaka bi umarninsa ba." Idanunsa ya lumshe, jin zuciyarsa yake tayi masa nauyi, a kasalance, cikin yanayi marar daɗi yace da Ummi, ta sanar dashi, "Wacece zaɓin nata?." Nan Ummi tace. "Idan yana buƙatar sani, zai iya zuwa ya tambayi Adda Rahama, zata sanar dashi koma wacece." Jin haka yajuya yafita jiki a mace, yana mai saƙawa ransa to wacece ina take ina suka samota da zasu liƙa mishi ita, tuno babu in da zai samu amsoshin duk waɗanan-nan tambayoyin sai wurin Adda Rahma. Ae kuwa kaman jira yake cikin sauri ya juya ya fice daga cikin ɗakin. Kai tsaye ɓangarensa ya nufa, inda ya kimtsa kansa,  koda ya fito text message ya turawa Ahmad kan cewar yana son ganinsa. Kasancewar Ahmad ɗin na cikin gida, hakan yasa mintuna kaɗan sai gashi ya fito. Cikin body language Saifuddeen ɗin yace da Ahmad. "Ya kaishi gidan Adda Rahama." Sanin kwanan zancen yasa babu musu, Ahmad ya ɗauko musu mota, nan suka shiga, inda ya jasu zuwa gidan Adda Rahaman bayan sun biya jonapwd sun ɗauƙi ishaq wanda a zaton Saifuddeen ishaq zaibi bayanshi. Koda Adda Rahama ta gansu batayi mamaki ba, don tun kafun zuwansu Ummi ta ƙirata ta yi mata bayanin komai. Tray ɗin drinks masu sanyi ta dire agabansu, Ahmad ne ya ɗauki kwalin exotic ya miƙawa ishaq kana shima ya ɗauka inda yasoma kwankwaɗa, don shi fes yakejin ransa bashi da wata damuwa. Hakama ishaq da shi yafi kowa jin haushin Zaleeha, kuma Babanshi ya mishi bayanin son ƙarawa Saifuddeen aure da Baban Zaleeya ya shiryawa. Saifuddeen kuwa fuska ya marairaice, duban Adda Rahama yayi, tare da ɗaukan wayansa, cikin message ɗin Ummi ya shiga, nan ya nuna mata fuskar wayar, tare da yi mata alaman tambaya, kan cewa. "Wacece? Ina take?". Murmushi Adda Rahama tayi masa tare da cewa. "Miye abun tada hankalinka haka ne Saifuddeen? da ka nutsu ma don amaryar taka ba ɓoyayya bace awajenka kasanta." Cikin son ƙarin bayani ya zubawa Adda Rahama'n fararen idanunsa. Duban tsab Adda Rahama tayi masa, kana cikin nutsuwa tace. "Nasan kasan Ameena ae, wannan nurse ɗin da ta baka kulawa, lokacin da kake jinya a Abuja, kafun ku wuce India, to ita ce dai Ummi ta zaɓa maka, nima kuma nayi na'am don yarinyar akwai hankali, Masha Allah. Ka tuna har gida tazo itada Mamanta suka dubaka da jiki." Idanunsa ya zazzaro waje tare da jujjuya kai da ƙarfi sosai yashiga mamaki, lokaci ɗaya yaji kaman an watsa masa ruwan zafi, amamakance ya ɗan ƙanƙance idanunsa, cikin yanayin maganarsa wanda ya saba, wato body language yace. "Allah ya sauwaƙe ni dai na auri wannan Ameenan, mezanyi da ita bazawara ce fa!." Cikin tsananin mamaki Adda Rahama ta dubeshi,  kallonsa tayi da kyau tare da faɗin. "Kai Saifuddeen banda sharri bazawara kuma? wa ya faɗa maka cewar bazawara ce?". Murmushin gefen baki yayi, tare da jijjiga kansa, in a body language ɗinsa yace. "Impossible!, nine zan auri bazawara? chab hmmm Allah ma ya sauwaƙe, sam banason sauran wani wlh Allah ya kiyasheni suɗe ƙashin da wani ya rigani tsotsa." Baki Adda Rahama ta buɗe fuska cike da tarin mamaki sauƙe a jiyan zuciya tayi tare da cewa. "Wai nikam wayace dakai itaɗin bazawara ce?." A shagwaɓe ya rubutawa Addan nasa. "Ae basai an faɗa min ba, duk ckekken Namiji in dai ya nitsu idan mace bazawara ce zai gane ta ido, kuma nayi imani cewa Ameena bazawara ce, saboda haka ni dai bana sonta wlh bazan iyaba, ba kuma zan aure ta ba." Ahmad da Ishaq kam dariya sukeyi sosai fahimtar abinda yake faɗin. Baki Adda Rahama ta taɓe, inda ta gyara zamanta, dubansa tayi da kyau,ido cikin ido tace. "Naji koma dai bazawara ce, ita Ummi ta zaɓa maka a matsayin mata, sannan da kake ta maganar cewa, ita bazawara ce, kai ɗin dakake magana saurayi ne kai? inace kaima bazawarinne tunda dai kayi aure." Bakinsa ya turo gaba, a shagwaɓe ya narke fuska, cikin body language yace. "Wallahi ni banason Ameena, yarinyar da idanunta abuɗe suke, ta fa riga da tasan Namiji, sannan kuma har yanzu ni matashin saurayi ne, tayaya ma zan yarda na auri Ameena." Duban Adda Rahaman yayi tare da kamo hannunta, cikin yanayin daya saba musu alaman magana yace. "Kin sanni tun ina ƙaramin yarona ma ko ta yaya bana amfani da tsohon abu, hatta kaya idan ya kasance gwanjo ne bana sawa, sannan idan yakasance wani ya taɓa amfani da abu, bana kuma amfani da abun, a iyaka tsawon rayuwata nafison komai sabo, koda wajen zama ne nafison sabo, banason wanda wani ya taɓa amfani dashi, harta mota ko wayar hannu, ban taɓa sayan second ba, komai na nafison yakasance sabo, ko lokacin da nake makaranta, ko yaushe ni nake zuwa first a acikin aji, bana taɓa yarda nazo second akomai na, to me yasa yanzu zan yarda na auri mace second hand? sauran wani, wanda wani ya cakalkala ya bari, ragowar wani fa Adda tunda nake gidannane kawai nataɓa sayan abu second hand kuma kin san shima saida na sabunta mana shi, bazan iya auren sauran waniba kinfa san inada kishi." Kansa ya girgiza tare da cije laɓɓansa. Baki buɗe Adda Rahama ke kallonsa, sosai take mamakin ƙarfin hali irin na Saifuddeen ɗin. Shikuwa Ahmad da shaq dake gefe sai ƙyalƙyala dariya suke tayi, don sosai show ɗin na Saifuddeen keyi musu daɗi. Ajiyar zuciya Adda Rahama ta sauƙe tare da cewa. "Koma menene dai Ummi ta gama magana, kuma ta yanke hukunci, wanda mu dukan mu mun gamsu, ta kuma ce zata sanar wa Bappa Ali, don asamu ayi bikin cikin gajeren lokaci, kaman yanda Baba Malam ya buƙata, kai da za'ayi maka auren gata ma, miye na damun kanka, sadaki, kayan aure, komai da komai, duk fa Baban Zaleeha yace ya ɗauke ma, wannan kaɗai bai isa saka farinciki ba, auren huce haushi fa zaiyi maka." Jan kujeransa baya yayi, inda ya kwaɓe fuska, nan ya dubi Ahmad yace dashi. "Su tafi." kana ya ja hannun ishaq Shidai Ahmad dariya kawai yake, har hakan yaso ƙular da Saifuddeen. Haka dai suka dawo gida, bayan sun sauƙe ishaq ko amota Saifuddeen fuskar nan tasa aɗaure take tamau. Suna isowa gida, kai tsaye part ɗin Ummi ya sake komawa. Ganinsa yasa Ummi kafesa da ido, cikin sanya fuskar tausayi, yayiwa Ummi alaman cewa. "Shi bayason Ameena, saboda bazawara ce, sannan kuma shi tsoronta ma ya keji, gata da kallon tsiya, sai kace mayya, gaba ɗaya idanunta abuɗe suke." Dubansa Ummi tayi, tare dayin dariyar zuci batayi mamakin jin cewa Ameenan bazawara bace, saboda kafun isowarsu Adda Rahama ta kirata tasanar mata. gyara tsayuwa tayi tare da cewa. "Allah mai iko, yau kuma Saifuddeen  kai ne me tsoron mace? uhmm saboda bakason auren ta  shiyasa kake tsoronta ko?" Sake shagwaɓe fuska yayi, duk yanda yaso Ummi ta fahimce sa, ƙiyawa tayi, daga ƙarshe ma juyawa tayi ta koma cikin ɗaki. Ganin haka yasashi komawa part ɗinsa, ransa duk ba daɗi, wani haushin Ameenan nema duk ya cika masa zuciya, wannan rana haka dai yayi bacci zuciyarsa duk ba dadi. Washegari. Yana gamayin break fast ya shirya kansa, inda ya ɗauki Sule driver suka nufi gidan su Ishaq, don tun adaren jiya ya tsara cewa zai je yasamu Dirankaɗi da maganar, wato Baban Ishaq kenan." Koda yaje Ishaq ne yayi masa jagora zuwa falon mahaifin nasa,  bayan sun gaisane Saifuddeen yayi masa bayanin duk wani abun daya kawosa, ta hanyar yi masa rubutu a laptop ɗinsa. Koda Dirankaɗi ya karanta murmushi yayi tare da duban Saifuddeen ɗin. Cikin son basa ƙarfin guiwa yace. "Tayaya kake tunanin cewa, bazaka iya auran mata biyu ba? Kai jarumi ne Saifuddeen, saboda haka kada kasa wani damuwa aranka zaka iya." Nan fa Saifuddeen ya tubure masa kan cewar lallai shi bazai iya ba, ganin haka yasa Dirankaɗi ɗaukar wayarsa, inda ya ƙira Bappa Ali, shi kuma Ishaq dariyan Saifuddeen ɗin kawai yake. Gaba ɗaya abun da Saifuddeen ɗin ya faɗa, shi Dirankaɗi ya maidawa Bappa Ali, nan Bappa Ali yace da Dirankaɗi, ya faɗawa Saifuddeen ɗin, aure babu fashi, tunda Baba Malam da kansa ya yanke hukunci. Koda Dirankaɗi ya faɗawa Saifuddeen ɗin, take yace. "To Baba nifa banida kuɗin auren ma in da ba sadakanta iyayenta zasuyi ba". Nan Dirankaɗi da Ishaq suka saka dariya, dubansa Dirankaɗi yayi tare da cewa. "Ae dama ba kaine zaka sayi komai na auren ba, auren gata za'ayi maka ae." Haka duk yanda Saifuddeen yaso ya kaucewa auren, Dirankaɗi da Bappa Ali sunƙi basa dama, dama shi Baba Malam baisan wainar da ake toyawa ba. Dole haka Saifuddeen ya dawo gida, zuciyarsa cike da tunani kala-kala. Haka akayi ta kai ruwa rana da Saifuddeen inda yaketa cemusu wai aifa Dr yace bazai iya zama da mata biyuba, Ya Adnan kuma yace a a ba wani Dr daya faɗi hakan. Ɓangaren Baba Malam kuwa, tuni ya turawa Yaya Ahmad kuɗi, kan cewar ya bawa Aunty Lubna ta shiga cikin shoprite na Abuja, tayi musu sayayyan kayan lefe,  wanda za'aiwa Saifuddeen sabon aure dashi. Yaya Ahmad  ne yace da Baba Malam ya amshi kuɗinsa,  shi zai haɗa lefen da kansa,  nan Baba Malam yace "a'a so yake komai na auren yayi da guminsa, da kuma haƙƙinsa, don ya ƙudurta aransa cewa, auren huce haushi da kuma gata zai yiwa Saifuddeen ɗin." Can ɓangaren Zaleeha kuwa, rayuwarta mai sauƙi take gudanarwa acan garin na Numan, zuwa yanzu bata da wani abinci sai kayan fruits,  dangin su apples da kuma ayaba, goiba dabina sai su water meloon, acikin ƴan kwanki kaɗan ɗin, tuni abubuwa da yawa sun sau ya mata, zuwa yanzu abu biyu ne ke damunta, wato tana jin can ƙasan zuciyarta bata son gudowan da tayi tana kewan kowa hatta su Ummi tana kewansu, ji take kamar ta koma amman da zaran ta tuna ta koma ɗin sai taji kanta yana juyawa sai taji ta gigice lokaci ɗaya taji kamar an ɗaure mata zuciyarta. Sai kuma nata soyayyar mutumin da har yanzu takasa sake sanyashi acikin idanunta, sosai soyayyarsa ke ƙara ninkuwa acikin zuciyarta, dashi take kwana kana dashi kuma take tashi, yayi mata tsaye acikin rai. Yanzu ma zaune take akan katifarta, laptop ɗinta ne agabanta, inda ta saka earpiece akunnenta, wani series film take kallo acikin laptop ɗin nata, don tahakane take samun rage kewa, wayarta dake gefe ne ta soma ƙara alamar shigowar ƙira, sunan Balkeesu ne ke yawo akan screen ɗin wayar, saida ta kusa katsewa ta ɗauka tare da kara wayar akan kunnenta. Daga can ɓangaren Balkeesu tace. "Mutanen ƙauye." Baki Zaleeha ta taɓe tare da faɗin. "Ya akayi ne." Balkeesu kuwa dariyar dake cinta arai ta danne tare da faɗin. "Lafiya lau, ya kike kwana biyu ina ƙiran number ki baya tafiya." Ajiyar zuciya Zaleeha ta sauƙe, cikin halin rashin kulawa tace. "Maybe matsalan network ne." Dariya Balkeesu tayi inda cikin zuciyarta tace. "Ko kuma matsalan wuta ba." Afili kuwa cewa tayi. "Dama Rabeel ne yace nayi miki magana, yana ta ƙiran wayarki amma bakya ɗauka, sannan yayi miki text duk babu reply, meyasa bazaki ɗauki wayarsa ba, ko kin manta cewar abokin aikin ki ne?." Baki Zaleeha ta taɓe tare da cewa. "Tayaya kike tunanin zan ɗaga ƙiransa, halan ya manta cewar ina da aure ne? igiyoyin auren wani ne fa akaina, to me yasa zan ɓata lokacina nakuma ɗaukarwa kaina zunubi wajen magan, da Rabeel wanda kuma bai zama lalle dole sai munyi magana ba." Hararan wayar Balkeesu tayi, kamar Zaleehan na ganinta, taɓe baki tayi tare da faɗin. "Uhummm su aure manya, dama naƙira ne kawai don naji ykk, da kuma dalilin ƙin ɗaga wayar Rabeel da kikayi." Ɗan jim Zaleeha tayi tare da cewa. "Bani da wani dalili naƙin ɗaga wayarsa sai na darajar auren dake kaina, kuma ma koda zai ƙira sau 100 bazan ɗaga wayarsa ba, saboda ina da aure, kuma shi ba muharrami na bane babu yadda za'ayi nayi magana dashi ina matar aure." "Okay." Balkeesu ta faɗa ataƙaice tare da kashe ƙiran, ita so take taga rayuwar Zaleeha tazama lalatacciya ta yadda zata samu damar maye gurbinta a ma'aikarsu da kuma gidan Saifuddeen, amman ta kaicinta ɗaya Zaleeha nada riƙo da mutuncinta na ɗiyamace musulma tana kare budurcinta da lallaɓashi tamkar ranta ga ibada. Ita kuwa Zaleeha aje wayar tayi tare da maida hankalinta akan laptop ɗinta. Itan kuwa Balkeesu tana kashe wayan, ta saki dariyan mugunta, inda a fili tace. "Ko ahaka aka tsaya awasan nasamu kaɗan daga cikin abun danakeso tunda ko yanzu shirinki na mushaƙata ya dawo hannuna." Can ɓangaren su Baba Malam kuwa, gaba ɗaya sun fita daga sha'anin Zaleeha, ko zancenta ma Baba Malam baiso ayi masa. Maryam kuwa sosai take cikin damuwa, domin kullum da tunanin ƴan uwa da kuma mahaifiyarta take wuni, ganin yanda ta damu sosai ne, yasa Ya Ameenu ɗaukan ta ya kaita wajen Baba Malam, nan Baba Malam yayi mata kalamai irin na mahaifa masu kwantar da zuciya, tare da sa mata al'barka, hakan kuwa yasa zuciyarta ta saki, kaɗan daga cikin damuwarta ya kau. Rayuwar Mama a Ɓilliri kuwa abun yazo mata cikin wani irin yanayi, komai ba yayi mata daɗi, zaman takura kawai takeyi agarin nasu, yayinda Zahira kuwa kullum bata da wani aiki, sai ƙworafi da mita, kan cewar ita lallai saida Maman ta maida ita gida, ita kuwa Mama har yanzu gani take kamar Baba Malam ɗin zai sauƙo yace su dawo gidan, don tasawa kanta aƙidar cewa bazata taɓa ƙiransa ta basa haƙuri ba, har sai shida kansa ya gaji yace su dawo. To gatanan dai rayuwar batayi mata daɗi, abinci ma bata samun wanda takeso, gaba ɗaya komai yayi mata duhu, badon komai ba kuwa saidan tana rayuwa acikin mutanen da gabansu da kuma bayansu duk duhu ne, basa ɗauke da haske ko kaɗan, zaman Ɓillirin sam baya yi mata daɗi Babanta kuwa duk da kafurine yaga rashin kyauta warta, shiyasa ya tsananta mata yace gata ga ƙauyen ta zauna kuma damuna na dawowa noma zatayi, Zahiri kuwa ji take kamar a rami take gida ba wuta bare fanka ko AC ba Radio bare tv babu firij bare kayan more rayuwa babu gado bare lafiyayyan katifa babu ƙamshin komai sai warin burkutu, rayuwa dai ta masu tsamari gashi ita Zahira an katse mata karatu ta. Ruda kuwa Addan Mama daɗi hakan taji dan ko yanzu ta samu sun zama dai-dai da ƙanwar tata, itama ta wahalan dai. Bayan Kwana Uku, da turawa Ya Ahmad kuɗin lefe, Baba Malam da kansa ya kimtsa, inda ya tsara tafiyarsu Abuja, shi da Dirankaɗi, da kuma Bappa Ali, yayinda za suje nemawa Saifuddeen auren Ameena, Alhaji Naseer Maichanji shine mariƙi ga Ameena, wanda yake ɗan kasuwa ne sosai, hakan yasa mafi yawancin mutane sun sanshi, koda zasuyi tafiyar tasu ta yanzun da expriance ɗinsu zasu tafi, kasancewar Dirankaɗi yasan Alhaji Naseer wanda a binciken da Dr Adnan yayi akan Amina a wurin Dr Aliyu ne sukaji komai na Amina. ananne Dirankadi ya gane ɗiyar tsohon abokin kasuwancishi shiɗin, har ma number'n wayarsa yana dashi, domin sun sha haɗa busineess dashi Alhaji Naseer ɗin tun shekarun baya. To kuma bisa jagorancin Dirankadin zasuyi tafiyar da tuni sun sanarwa Alhaji Nasir Daddy kenan zuwan nasu. Ɓangaren Saifuddeen kuwa shi har yanzu ganin abun yake, kamar almara, musamman idan ya tuna da cewar. "Ameena ɗin bazawara ce." Sai yaji sam shi bazai iya mu'amala da ita ba. Ƙarfe 10 na safiya dai-dai jirgin da zai ɗaga zuwa Abuja, ya kwashi su Baba Malam da Bappa Ali. Inda suka tafi da niyar cewa bazasu dawo nan Gombe ba sai an tsaida lokaci da kuma ranan aure, don suna sa ran cewa. "Insha Allah Alhaji Naseer ɗin bazai hanasu ɗiyarsa ba." Sun isa garin Abuja lafiya, inda Ya Ahmad da kansa yaje ɗauko su a airport, nan fa dukansu suka shiga motar, kaitsaye unguwar Asokoro suka nufa, wanda anan gidan su Ameena yake. Yayinda duk abinda akeyi Amina bata da labari. Maigadi ne ya wangale musu gate ɗin gidan, nan cikin parking space ɗin gidan Ya Ahmad yayi parking, dai-dai lokacin wani ɗan Dattijon mutumi me cike da kamala, wanda yasha adonsa cikin manyan kaya, yafito daga cikin wata ƙofa, ganinsu da yayi yasa ya nufosu cikin sauri, fuskarsa ɗauke da fara'a ya miƙa musu hannu, nan suka shiga gaisawa cikin mutunta juna, kai tsaye yayi musu jagora zuwa ɓangarensa, wani babban falo ne mai kyau, inda anan yake tarban baƙinsa masu mahimmanci. Zama sukayi, tare da sake sabon gaisuwa. Duban Dirankaɗi Alhaji Naseer yayi tare da cewa. "Alhaji Ma'aruf ashe rai kan ga rai?." Murmushin manya Dirankaɗi yayi tare da cewa. "Ƙwarai kuwa Alhaji Naseer, gashi bayan lokaci mai tsawo da muka ɗauka gashi kuma mun sake haɗuwa." Shima Alhaji Naseer ɗin murmishi yayi tare da cewa. "Allah Mai iko, gashi kuwa harda Malam Bashir Sulaiman Dukku kuka zo, a gaskiya yau gidana yana ɗauke da manya manyan baƙi, masha Allah sannunku da zuwa." ya ƙarishe maganar yana miƙawa Baffa Ali hannu Dai dai lokacin masu aiki suka shigo, nan suka cika musu gaba da kayan ciye ciye harma da dangin su snacks. Drinks ɗin kaɗai suka ɗan taɓa, nan Baba Malam da kansa ya gyara zama, duban Alhaji Naseer yayi tare da cewa. "Nasan zakayi mamakin ganinmu, to amma ance wanda yake da buƙata shi yake zuwa, ko ba haka ba?." Nan dukansu suka jinjina kai, inda Alhaji Naseer yace. "Ƙwarai haka ne." Ajiyar zuciya Baba Malam ya sauƙe tare da cewa. "To kamar dai yanda ka ganmu dukan mu nan al'khairi ne ya kawo mu, dan kuwa munzo newa ɗan mu auren ɗiyar ka Ameena, muna fatan Allah yasa ba ai mata miji ba." Ajiyar zuciya Alhaji Naseer ya sauƙe, tare da ɗan numfasawa, cikin murna haɗi da farin cikin ganin manyan malamai sunzo neman haɗa zuriya dashi a hankali yace. "Masha Allah, Haƙiƙa naji daɗin wannan zancen naku ƙwarai, sannan kuma ba aiwa Ameena miji ba, saidai kuma bazan ɓoye muku ba, magana ta gaskiya banine mahaifin Ameena ba, nine dai mariƙinta, dani da mahaifinta kuwa uwa ɗaya uba ɗaya muke, sannan kuma magana ta biyu dai ita ce, Ameena ba budurwa bace, bazawara ce, don kuwa ta taɓa aure, ta auri ɗan wajena Amir, sai-dai kuma da yake Allah bai tsara zamansu tare ba, sati ɗaya kacal auren yayi Allah ya kawo ƙarshensa, sannan ahalin yanzu dai babu wani wanda ta tsayar mazaunin wanda zata aura." Ajiyar zuciya suka sauƙe su dukansu, cikin gamsuwa Baba Malam ya gyara zama, inda ya fuskanci Alhaji Naseer, cikin yanayin dattako yace. "Alhamdulillah, duk da kafun muzo bamusan da wannan magana ba, koda muka jita yanzu kuwa bazaisa mu fasa niya da kuma ƙudurin dake ranmu ba, saidai kuma muma zamu faɗa muku cewar ɗan mu na ɗauke da laluri, wanda idan akayi dubida ƙaddara ce wanda zata iya hawa kan kowa, sannan kuma duk cikinmun nan babu wanda baisan cewa, Lafiya da rashinta duk na Allah bane, sannan shike sawa bawa cuta, kuma shike yaye masa, sannan lalurar da ɗan mu kedashi, bai tauyesa daga zama cikakken ɗa namiji ba, domin yana da lafiyar da zai iya kusantar mace, sannan yana da wadatar da zai iya zama da mace, saboda haka muna fatan hakan bazaisa ku hanamu ƴarku ba, saboda shi aure nufi ne na Allah, matar mutum kuma ance kabarinsa." Bappa Ali ne ya gyara zama tare da soma yiwa Alhaji Naseer ƙarin bayani, dan gane da larurar Saifuddeen ɗin, bai ɓoye masa komai ba, ya fayyace masa komai yanda zai fahimta. Jinjina kai Alhaji Naseer yayi tare da cewa. "Nafahimce ku, ƙwarai kuma ai nakasa ba kasawa bace, kana nakasashshe zai iyayin abun da wani mai lafiyan ma bai iyawa, tabbas kuma idan na fahimta kune iyayen Saifuddeen ko?." Cikin Mamaki suka kalli juna, Dirankaɗi ne yace. "Ƙwarai kuwa, amma dama kasan Saifuddeen ɗinne?" Murmushi Alhaji Naseer yayi inda yace. "Ƙwarai kuwa, ai sanadiyar ita Ameenan nasanshi, don ita ta kula dashi lokacin da yayi jinya anan, sannan kuma koda suka koma india, danaje wani business ɗina naje har New Delhi na dubasa, gaskiya ni kaina na yarda da ƙwazon sa, don dagani matashi ne mai tsayayyar zuciya, tabbas wannan nakasa tasa bazata sa mu hanaku auren Ameena ba, sai-dai kuma kunsan cewa itaɗin bazawara ce, ba budurwa bace daza'ayi mata dole, saboda haka idan kunbani dama zan shiga ciki don na tambayo ra'ayi da kuma zaɓinta, sannan zan ƙira ɗan uwana awaya zan sanar dashi nasan bazaiƙi amincewa ba." Nan su Baba Malam sukaji daɗin hakan sosai, har saida murnarsu takasa ɓoyuwa, Nan dai Alhaji Naseer ya miƙe ya wuce cikin gida, inda yace su bashi mintina kaɗan. Acan cikin gida kuwa, koda yasamu Momma da maganar sosai tashiga mamaki, sai-dai kuma wani tunani daya faɗo ranta, hakan yasata sakin murmushi tare da cewa. "Masha Allah, ae kuwa nasan Ameena ba zata ƙi ba, bana ƙirawo maka ita yanzun nan saikaji ta bakinta." Nan Momma tawuce ɗakin Ameena, koda Momma ta shaidawa Ameena ƙiran da Daddyn nasu keyi mata, hakan taji gabanta yaɗan faɗi, hijab ta zura ajikinta sannan ta nufi falon. Durƙusawa tayi agaban Daddy'n nasu, cikin rusunawa tace. "Daddy gani." Dubanta Alhaji Naseer yayi cikin kulawa, yayi mata bayanin komai. Mamaki, haɗi da zallan farin ciki ne suka cika zuciyar Ameena, wannan shi ake ƙira da ƙarfin ikon Allah, haɗi da kuma falalar addu'a, tabbas ko kaɗan bata taɓa kawowa aranta cewa zata samu Saifuddeen anan kusa ba, tabbas takai kukanta wajen ubangiji gashi kuma ya amsa addu'arta, inda ya share hawayenta, alokacin da bata zata ba. "Ameena kinyi shiru." Maganan Daddyn ya katseta. Murmushi tayi, cikin sassanyar murya tace. "Idan dai har ka aminta da auren Daddy nima na amince, bani da wani zaɓi sai naka." Farin ciki da jin daɗi ne suka lulluɓe zuciyar Daddy, nan yashiga sanya mata al'barka, inda yace tatashi taje. Wayarsa ya zaro, inda ya ƙira Alhaji Sadam, wato Baban Ameena, koda Baban Ameenan ya ɗauka, nan Alhaji Naseer ya labarta masa komai, hakanan Alhaji Sadam yaji zuciyarsa ta aminta da batun, nan take yace ya amince, inda yace da ƙanin nasa yayi komai, ai Ameena ƴarsa ce. Nan fa Alhaji Naseer ya koma falon tarban baƙinsa, nan yasanar dasu Baba Malam Amincewar Ameena, da kuma mahaifinta, take suka cika da tsananin farinciki, sosai sukaji daɗi, ƙwarai kuma sun yaba da karamcin mutanen. Nan take suka tsaida magana, inda anan wurin a take Baba Malam yabada sadaki Naira dubu Hamsin, sannan ya kuma ce nan da kwana uku za a kawo kayan lefe, ananne Alhaji Naseer ya yanke musu lokacin biki, wato nan da sati biyu masu zuwa, domin kuwa dukansu ajiƙe suke da naira saboda haka babu wani amfanin jan bikin yayi nesa. Haka suka rabu cikin mutunta juna, kowa zuciyarsa fes. Ɓangaren Ameena kuwa tana shiga ɗaki, tsalle ta buga cikin matsanancin mamaki tace. "Ya Allah idan mafarki nake ka tasheni na farka ka kuma tabbatarmin dashi a zahiri. Wayyo Allah na wai dagaske Saifuddeen zai aureni? zan zama mata agaresa, wayyo Allah na!! Alhamdulillah." Sulalewa ƙasa tayi inda tayi sujjadan godiya ga Allah, cikin matsanancin jin daɗi tace. "Tabbas Allah Shi kaɗaine bashida wani abokin tarayya, sannan shike isar mana da komai namu." faɗawa kan gado tayi cikin matsanancin murma tayi hugging pillow. Nan fa tashiga birgima akan gado tana dariya, mai ɗauke da tsananin farinciki. Sbp egwl Ɓangaren su  Baba Malam kuwa, kai tsaye gidan Ya Ahmad suka koma, inda anan suka ɗan huce gajiyansu, zama sukayi suna maida batun karamci da kuma halin dattako irin na iyayen Ameena'n, tabbas sun shaida cewa suna da mutumci, kana kowani mutum zai so haɗa zuri'a dasu.                                       Da misalin ƙarfe 6 na yammaci jirgin da zai maidasu Gombe zai tashi, hakan yasa 5::40  pm  ababban filin airport na Nnamdi Azikwe International Airport Abuja.    Ƙarfe shida dai-dai kuwa jirginsu ya tashi, bayan Baba Malam ya ƙara jaddadawa Ya Ahmad, maganan haɗo lefe da wuri, nan Ya Ahmad yace. "Insha Allah zaisa Aunty Lubna ta haɗo lefen, nan bada jimawa ba."                                       Bakwai dai-dai jirgin da ya ɗaukosu daga Abuja zuwa Gombe, ya sauƙa acikin Gombe International Airport.              Ya Ameenu  da kuma Ahmad ne sukazo ɗaukarsu anan airport ɗin.                                          Motar Ya Ameenu Baba Malam ya shiga, inda Bappa Ali da Dirankadi kuwa suka shiga motar Ahmad, don sune zasu je suiwa Ummi bayanin duk abun da ya wakana.                            Haka suka rabu da juna cikin aminci da salama.            Tun daga yanayin yanda Ahmad yaga fuskokinsu ɗauke da annuri, hakan yasa shi fahimtar cewa lallai anyi nasara tafiya tayi kyau, sosai kuwa yaji sanyi azuciyarsa.                           Koda suka ƙarasa gidan, a falon na Ummi suka zauna, cikin nutsuwa kuwa Bappa Ali da Dirankadi sukaiwa Ummi bayanin komai, sosai Ummi ta cika da farin ciki haɗi da jin daɗi,  haka kuma lokacin da aka sanya auren yayi mata daɗi sosai, dama ba ta son aja lokacin, nan dai  tasa aka kawowa su Bappa Alin kayan ciye ciye,  nan suka ɗan taɓa, daga haka Dirankadi ya ƙirayi driver'nsa,  nan ya zo ya maidasa gida, shikuwa Bappa Ali anan zai kwana, kasancewar qdare yayi, idan yaso gobe da safe, Ahmad ko sule driver ɗaya daga cikinsu zai maidashi.                           Can ɓangaren Saifuddeen kuwa, ganin sun dage da gaske suke maganar auren yasa, wunin yau duk bai fito waje ba, anan ɓangarensa ya zauna, yayinda ya maida hankalinsa kan Laptop ɗinsa yana aiwatar da sabon aikin da shugaban DSS suka bashi. Koda ya dawo sallan Isha, kai tsaye part ɗinsa ya koma,  kasancewar yau din ana yanayin sanyi hakan yasa  shi kwanciya da wuri, luf yayi acikin lallausan bargonsa, inda ya ɓoye kansa acikin bargon, ajiyar zuciya ya sauƙe tare da lumshe idanunsa, tunaninta ne kwance acikin zuciyarsa, sau da yawa idan ya tuna da ƙiriniya da kuma rashin ji irinta na yarintarta dama yanzun da takega ta girma, yakan samu kansa da sakin murmushi.  Da haka bacci ya ɗaukesa. Washegari. Tun da ya dawo daga sallan asuba ya koma bacci, bashine  kuwa ya farka ba sai wajen ƙarfe 10:30 am.    Ahankali yazuro da ƙafafunsa ƙasa, tare da jawo wheellchair ɗinsa, wanda akullum take kusa dashi, sam baya bari tayi masa nisa, hawa samanta yayi, kai tsaye ya nufi toilet, koda ya shiga ruwan wanka mai ɗam ɗumi ya haɗawa kansa, cikin haɗaɗɗen jakuzzie, nan ya zuba turaren wanka mai daɗin ƙamshi acikin ruwan,  Luf ya kwanta acikin jakuzzien tare da ɗan lumshe idanunsa. Sama da mintuna 10 ya ɗauka ahaka, yayinda yakejin daɗin ruwan, kasancewar ruwan nada ɗan ɗumi, shiyasa yakejin daɗi yanayin, domin kuwa yanzu ana weather ne na sanyi hunturu.   Wanka yayi kana ya ya rufe jikinsa da wani fari ƙal ɗin towel,  haka ya nufi ƙofar fita daga cikin toilet ɗin, jikinsa ɗauke da danshin ruwa, yayinda kwantaccen sajen dake kan fuskarsa ya ƙara lafewa, saman kumatunsa. Kaitsaye gaban drawer ɗinsa ya nufa, inda ya zaro kayan da zaisa, wani ƙaramin towel ya ɗauka sannan ya shiga goge ruwan dake jikinsa, yana kammalawa, ya ɗauki handryer wanda  dashi yayi amfani wajen busar da tarin sumar dake kansa, cumb yasa inda yaƙara gyara lallausan sajensa, yayi kyau matuƙa, wani body lotion mai sauƙin ƙamshi ya shafa ajikinsa,  dogon wandon pencil jeans ya sanya, kana ya zura wata haɗaɗɗiyar riga, wanda take kaman na sanyi domin harda hulanta, kasancewar rigar nada kalan grey hakan yasa sosai tayi masa kyau, yayinda agaban rigar aka rubuta NIKE da manyan baƙaƙe,  wasu combat shoe wanda suma na company'n NIKE ɗin ne ya sanya aƙafafunsa, sosai shigar tayi masa kyau, saiya fito kaman irin shahararren jarumin ƙwallon ƙafa,  wani simple watch ya ɗaura akan tsintsiyar hannunsa,  kana ya feshe gaba ɗaya jikinsa da turare, take ɗakin ya gauraya da daddaɗan ƙamshin turarensa.      Wayoyinsa ƙiran iPhone da kuma Samsung ya ɗauka, kana ya zura su cikin ajihun dake jikin haɗaɗɗiyar rigar tasa. Daga part ɗinnasa kai tsaye barayin Ummi ya nufa. Tun kafun isowarsa falon nata, ƙamshin turarensa ya rigayesa isowa. Cikin nutsuwa ya ƙarasa shigowa cikin falon,   Hayatuddeen ne zaune akan dinning area, yayinda ya saka pepper meat soup agaba sai sha yake.  Ƙarasowa dinning area ɗin yayi, dubansa Hayatuddeen yayi cikin kulawa yace. "Barka da fitowa Hammana." Kai ya jinjinawa Hayatuddeen din bayan yasaki taƙaitaccen murmushi, dai-dai lokacin Ummi tafito daga ɗakinta, ganin Saifuddeen ɗin yasa ta sakin murmushi cikin kulawa tace. "Masha Allah ka fito kenan, yanzu fa nake cewa Hayatuddeen ya gama ya ƙiraka, kazo kayi break fast."  Ummi taƙare maganar tana mejan kujera wanda take facing na Saifuddeen ta zauna, duk dama shi always akan wheellchair ɗinsa yake zama.    Raliya ce tafito daga cikin kitchine, hannunta ɗauke da plate.  Ganin Hamman nata yasata sakin murmushi, cikin nutsuwa tace. "G/N Hamma."   Kansa ya jinjina mata alaman ya amsa, zagayowa ɓangaren da yake tayi, nan ta aje masa plate ɗin da ta fito dashi daga kitchine ɗin, wanda saman sa ke ɗauke da roasted fish, wanda yaji kayan haɗi, hadda lemon tsami.   murmushi Saifuddeen yayi tare da dubanta, hannu ya jinjina mata alaman "Thanks."  Itama murmushin tayi, don dama tayi hakanne don ta faranta masa, kasancewar tasan yanason roasted fish. Nan ta zauna, inda suka shiga cin breakfast ɗin cikin nutsuwa,  Ya lura dukaninsu suna cikin farinciki, musamman ma Umminsa, wanda duk bayan ƴan mintuna kaɗan take sakin murmushi, haka dai suka kammala break ɗin nasu, nan ya dawo cikin falon Ummin ya kwanta,  Hayatuddeen kuwa ɗaki ya koma, inda shima yayi shiga shigen irin ta hamman nasa, nan yafito riƙe da jakarsa ta makaranta, duban Ummi dake zaune afalon yayi, cikin sangarta haɗi da zallan shagwaɓa yace. "Ummi zan tafi school, 11:30 muke da lecture." Batare da Ummi ta ɗago kanta ba tace. "To Autana adawo lafiya." Jin haka yasashi ɓata fuska ashagwaɓe yace. "Ummi kuɗin hannuna fa ya ƙare." Murmushi Ummi tayi, don dama tasan kwanan zancen. Dubansa tayi tare da cewa. "Kullum sai an baka kuɗi Hayatuddeen sai kace ƙaramin yaro." Cikin tura baki yace. "Ni ban san ammafin buɗe min ac da Hamma Saifuddeen yayiba, ya tarkata komai ya riƙe ko Atm ɗin ban taɓa riƙewa koda na wuni ɗayaba, sai dai inyi ta ganin Arlet yanata shiga ba sauƙi, ina ganin miliyoyi amman bani da damar taɓasu." Dariya Ummi tayi hakama Saifuddeen, dan zancen autan nasu ya nuna burinshi na a bashi kuɗi ya fara lalata. Shi kuwa auta sake shagwaɓe mata yayi, wai adole sai ta bashi kuɗi, saikace ƙaramin yaro, nan Ahmad yashigo ya iske suna maganan, Ahmad ne ya ciro 5k daga cikin aljihunsa, inda ya bawa Hayatuddeen ɗin, nan Hayatuddeen yasaki murmushi sannan yasakai yafice daga cikin falon. Nan Ahmad ya zauna acikin falon suka shiga ɗan taɓa hira da Ummi, Saifuddeen kuwa, luf yayi tare da lumshe idanunsa, kamar wanda ke bacci. Abuja Nigeria. Kwana biyu kenan da zuwan su Baba Malam Abujan, yayinda yau Tsab Aunty Lubna da kuma wata ƙawarta, mai suna Samira suka shiga cikin shoprite, don haɗo kayan auren, ba laifi kaya masu kyau da kuma tsada suka sayo, duk da cewa ran Aunty Lubna baiso ƙara auren na Saifuddeen ba tanajin taya Zaleeha kishi, tana kuma tausayawa Zaleeha a gaba, to amma tasan cewa koma menene hakan shine dai-dai, don itama guduwan da Zaleehan tayi ya sosa mata zuciya. Akwatuna goma sha biyu suka saya, kana kuma suka cikasu da kaya, sannan kuma suka saya wasu uku daban wanda ciki aka sanya kayan uwa da na uba. Haka dai suka dawo gida bayan motarsu cike da kaya. Aranan kuwa Ya Ahmad ya ƙira Baba Malam, inda yasanar dashi cewa, anagama haɗa kayan auren. Kasancewar da dare ne Ya Ahmad da Baba Malam ɗin sukai waya, hakan yasa washe gari da safe, Baba Malam yaƙirayi Bappa Ali ya sanar masa, nan Bappa Ali yace. "Zai sanar da Ummin, sai susa ranan da za'a kai kayan." Hakan kuwa akayi don bayan sallan Azahar Ummi na zaune akan sallaya, sallame sallan ta kenan, wayarta tasoma ruri, ɗaga ƙiran tayi, bayan sun gaisa da Bappa Ali'n ne kuma, yake shaida mata cewar. "An kammala haɗa kayan auren, yanzun ita zata sanya ranan da za akai kayan." Cikin jindaɗi da gamsuwa Ummi tace. "Masha Allah, amma ni sai nake ga kamar ku ya kamata kutsai da ranan kai lefen, tunda dai auren bawani lokaci mai tsawo aka ɗauka masa ba, yanzu gashi kamar wasa har anci kwana uku acikin ranakun." Cike da gamsuwa Bappa Ali yace. "Tunda yau takasance asabar ne, to ranan litinin da safe, sai waƴanda zasu kai lefen su shirya." Nan Ummi take sanar dashi cewa. "Goggo dada, Adda Rahama, da kuma Ahmad, sai kuma Hayatuddeen, sune wanda zasuje, amma bawai kai tsaye abujan zasu nufa ba, a Kaduna gidan Raihana zasu sauƙa tukun." Nan dai tace ya kawo shawaransa. Cikin gamsuwa Bappa Ali yace mata. "Hakan ma yayi." Nan akayanke cewa, ranan litinin zasu kai lefen. Ummi na gama waya da Bappa Ali'n, numbern Adda Rahama ta ƙira, nan take shaida mata duk yanda sukayi da Bappan nasu, sosai itama Adda Rahama tayi na'am da hakan. Nan dai sukayi sallama. Numan. Zaman Zaleeha a numan ya miƙa sosai, duk da cewa bawai tanajin daɗin rayuwa acikin ƙauyen bane, amma babu laifi tana ɗan samun abun da take ɗan so, tunda da kuɗi a hannunta, rayuwa take cike da kaɗaici, saidai wani lokaci wayarta da kuma tsohuwar laptop ɗinta suke ɗebe mata kewa. Sai kuma wata sabuwar ƙawa wacce take ƴar fulani da tayi, inda sun haɗu ne, abakin kogi, don wani lokaci Zaleeha kan zuwa bakin kogin ta zauna, itakuwa sabuwar ƙawar Zaleehan mai suna Aisha, anan cikin wani ɗan ƙaramin rugar fulani dake kusa da Numan ɗin take, wanda yake rugace na zallan fulani sannan kuma dukansu musulmai ne, babu christan ko ɗaya acikinsu, tun Zaleeha bata sake da Aishan ba, har dai zuwa yanzu suka sama, domin kuwa taji daɗin haɗuwa da Aishan, kasancewar sosai Aishan ke ɗebe mata kewa, ta wani ɓangare kuwa mamaki take, kasancewar ansan cewa fulani suna aurar da ƴaƴansu da wuri, sai gashi ita kuma Aishan karatu ma take acikin birni, inda take aji biyu a university, wato level two, duka duka Aishan bazata ɗarawa Zaleehan ba, domin kusan ma kansu ɗaya, haka ma dai shekarunsu, sai-dai Zaleehan tafi Aishan cika dama duk wani abu na gogewa. Yanzu ma dai tsab ta gama shirinta, cikin wani riga da sket na material masu kyaun gaske, wani babban mayafi ta yafa ajikinta, wanda yazo har ƙasa ya ɓoye duk wani kyawun surarta, waya da kuma power bank ɗinta ta ɗauka, duban Aishan dake zaune tayi. Aishan ma dubanta tayi, ganin Zaleehan ta kammala shirinta yasa tace. "Masha Allah, kinga yanda kikayi kyau kuwa, sau dayawa ina mamakin ki, duk da cewa aƙauye kike zaune, amma kuma kullum ƙara kyau kike, yanayin shigarki ta kame kai tana matuƙar yi miki kyau." Murmushi Zaleeha tayi tare da cewa. "Uhumm kedai Aisha bakya gajiyawa da surutu, kullum ganin kyauna kike ke bakya ganin naki, dan Allah tashi muje, yau kam naƙosa muje gidanku, kodan ma na huta, da gorin da kikemin, kan cewa da kike, wai kullum ni bana zuwa gidanku, saidai ke kizo." Miƙewa Aisha tayi tana dariya, nan suka fito daga ɗakin. Babu kowa atsakar gidan, domin kuwa tun safe Elizabet, da kuma Solomon suka tafi church, kasancewar yau Lahadi. Suna fita Zaleeha ta jawo ƙofar gidan ta rufe, nan suka ɗauki hanya zuwa cikin rugar su Aisha, wanda yake nan kusa bashi da nisa, Koda suka shiga cikin rugar sosai Zaleeha taji zuciyarta tayi sanyi, sakamakon ganin yanda jama'ar rugar keta hada hadansu, wanda dukansu musulmai ne kana kuma fulani masu mutunci waɗanda hasken addini ya ratsasu, don da ka kallesu zakaga hasken musulunci agoshinsu, idanu ta lumshe, tare da sauƙe ajiyar zuciya, tabbas akullum tana ƙara godewa Allah daya yita musulma, domin kuwa tabbas duk wani addini da ba na musulunci ba, babu komai acikinsa sai ɓata, musulunci shi kaɗaine haske. Koda suka ƙarasa gidan nasu Aisha, cikin girmamawa ta gaishe da Innar na Aisha, haka dai suka ɗan gaggaisa da ɗan sauran jama'ar gidan. Nan suka zauna da Aisha'n, suka shiga ɗan taɓa hira. Sun ɗan jima suna hira ganin cewa la'asar ta kusa ne, yasa Zaleehan miƙewa, nan tace zata tafi, batason yammaci ya mata awaje, Inna Maman Aishan ne, ta bata pure nono cikin wani babban gora, wanda aka zuba zuma acikinsa, Aisha kuwa da kanta ta gasawa Zaleehan naman ƙatuwar Zabuwa, duk yanda Zaleeha taso kin amsa, saida suka sata ta amsa, nan tayi musu godiya sosai, sannan Aisha ta rakota, har kusan wajen rugar, daga haka sukai sallama, inda Aishan tace da Zaleeha sai tazo. Batayi wani tafiya mai nisa ba ta iso gida, nan ta iske har zuwa wannan lokacin su kawun nata basu dawo ba, ɗakinta ta shiga inda ta aje nama da kuma nonon da suka bata. Fitowa tayi donyin alwalan sallan la'asar, dai-dai nan Elizabet ta shigo cikin gidan, kamar an jefota ba sallama duk tayi wujiga-wujiga da ita, ƙafarnan tata tayi futu-futu, idanunta kuwa sunyi tsuru tsuru, alamun gajiya da wahala ya bayyana ƙarara ajikinta. Dubanta Zaleeha tayi, kana ta kau da kanta gefe, da taso yi mata sannu da dawowa, amma tunowa cewa Elizabet ɗin daga church take, hakan yasa ta fasa, zama tayi akan dakali, tare da jawo ƴar butar ta, ta soma al'wala. Elizabet kuwa kan wani benci dake tsakar gidan ta baje, nan tashiga maida numfashi akai-akai, saikace wacce tayi wasan tsere, amatuƙar gajiye ta ɗago kai ta dubi Zaleeha, wanda ke gudanar da al'wala cikin nutsuwa, ƙura mata idanu Elizabet ɗin tayi, tana me kallon yanda take alwala'n, cikin ranta tace. "Oo ni Elizabet kalli yanda suke gudanar da ibadansu cikin nutsuwa da kwanciyar hankali da jin daɗi, batare da wani hayaniya ba da ife-ife da raye-rayeba." Ajiyan zuciya ta sauƙe tare da ɗan gantsarewa dan azabar ciwon da ƙugunta yakeyi sabida wuni rawan da suka wuni tiƙawa a majami'ar bautar tasu. Duban ƙafanta wanda sukayi suntum tayi, hakan kuma ya farune sakamakon tiƙar rawa da tayi a church, don kuwa tun safe suke rawan bahutu, gaba ɗaya ta gaji. Idon dai ta zubawa Zaleeha tana ganin yadda take gudanar da harkar ibadarta a mutunce. Ita kuwa Zaleeha, tana alwalanne amma gaba ɗaya kewar da begen gida da danginta da Baba Malam ne ya cika zuciyarta, sosai takejin kewar mahaifin nata, tana matuƙar son Baban nata ƙwarai da gaske, tabbas ta wani ɓangare tanajin son komawa gida, tana so da ƙaunar taga tayiwa mahaifinta biyayya tana son farin cikin shi dana Ya Ahmad koda irin al'ƙawarurrukan da ya mata, tana jin ciwo a ranta ace da aure a kanta a kuma bata gidanta ɗakinta damahaifinta ya umarceta data zauna lokuta da dama tamkar tayi zama tsuntsuwa tayi fiffige ta koma cikin iyayenta tayiwa mahaifinta biyayya, koda ko sanadin rasa masoyin nata zaisa ta rasa ranta. To amma hakanan takeji kaman anɗaure ta da jijiyoyin jikinta, wanda takejin kamar dole akai mata zama anan Numan ɗin tanaji a ranta tana son ta koma amman duk sanda ta aiyana haka sai taji kamar a ɗaureta ne, a garin, haka dai ta kammala al'walanta kai tsaye ta wuce ɗakinta, a nan tabar Elizabet zaune tana ta faman maida ajiyar zuciya. Sallah tayi sannan ta jawo goran nonon, nan taɗansha kaɗan sosai kuwa taji daɗinsa, kasancewar bata wani jin yunwa yasa ta ajiye, kan cewar sai zuwa dare taci zabuwan da kuma nono'n.... Gombe State. Kasancewar yau ya kasance litinin, kuma yaune su Adda Rahama zasu wuce Kaduna, daga nan kuwa Abuja zasu inda zasu ɗau lefen agidan Ya Ahmad, sukai zuwa gidansu Ameena. Ƙarfe 9 dai-dai dukansu suka hallara afalon na Ummi, Adda Rahama, Goggo Dada, Ahmad da kuma Hayatuddeen, sune wanda zasu tafi, tun ƙarfe 8 Raliya ta gama musu break fast, inda sukaci suka ƙoshi, ƙarfe goma dai-dai jirgin dazai kwashesu zuwa Kaduna zai tashi, hakan yasa tuni suka kammala duk wani shirye-shiryensu, ɓangaren Saifuddeen kuwa, yana can part ɗinsa, baimasan wainar da suke toyawa ba. Kasan cewar lokacin ana tsaka da gyara Airport ɗin Abuja shine ya basu damar samun jirgin kaduna kai tsaye. Raliya da kuma Ummi sune sukai musu rakiya, har zuwa airport, kamar yanda yake arubuce kuwa ƙarfe 10 dai-dai jirgin nasu ya tashi. Kwata kwata tafiyar mintuna 46 jirgin nasu yayi, ya iso cikin airport ɗin garin Kaduna, koda suka sauƙo daga cikin jirgin nan suka iske Saminu najiransu, wanda shi da kansa yazo ɗaukarsu, sunyi farin ciki sosai da ganin juna, nan ya kwashesu cikin motarsa, suka nufi gidansa. Adda Rahama na shiga cikin gidan, Raihana ta rungumeta cikin tsananin farin ciki, itama Adda Rahaman rungume Raihanan tayi, don kuwa tayi kewarta, Hayatuddeen ne ya zumɓura baki tare da cewa. "Wayyo Adda Raihana ni bazaki rungumeni bane, kodai bakiyi kewata bane?." Dariya Raihana tayi tare dajan kumatunsa, cikin tsokana tace. "Ƙato dakai ne zan rungume ka, kaikam ai saidai ma nasa maka duka, kancewa ka shigomin gida, ƙato dakai, ai da katsaya daga waje." Dariya suka sanya su duka, Hayatuddeen kuwa, sake tunzura baki yayi, tare da faɗin. "Ae dama batun yauba nasan Raliya tafiki sona." Jin haka yasa Adda Raihana'n jawo hannunsa, cikin ƙaunar autan nasu, ta rungumesa, cikin son sanyaya masa zuciya tace. "Inasonka mana autan Ummi, ai kowa ya soka bayana ne, saboda kai fa yasa na shirya lafiyayyen girki, harma fa ferfesu nayi maka naka kai kaɗai na musamman." Jin haka yasa Hayatuddeen sakin murmushi mai ɗauke da tsananin farinciki. Cikin jin dadi yace. "Yesss shiyasa nake ƙara sonki Adda na, saboda koba komai kinfi su matar o'o kirki." Yaƙare maganar yana me satan kallon Ahmad. Dariya suka sanya don sarai sun gane dawa yake. Ahmad kuwa ƙwafa yayi inda yace. "Zamu koma ne yaro zakayi bayani agabanta." Nan dai suka zazzauna inda Raihana ta cika musu gabansu da kayan ciye ciye, haɗi dasu drinks. Saida sukaci abincin suka ƙoshi sannan, suka kimtsa don kama hanyar Abuja. Inda Ahmad ya ɗauki ɗayar motar Saminu, wanda ya ɗauki Goggo Dada da kuma Adda Rahama acikinsa, sai kuma Saminu wanda ya ɗauki, Hayatuddeen da kuma Matarsa Raihana. Kasancewar tsakanin Abuja da kuma Kaduna babu wani nisa, hakan yasa suka isa dai-dai an idar da sallan Azahar. Kaitsaye unguwar Wuse zone 2 suka nufa, wanda anan gidan Ya Ahmad yake. Koda suka ƙarasa gidan sun samu tarba me kyau daga wajen Aunty Lubna, sunkuwa ji daɗi ƙwarai, nan tafito musu da kayan auren suka gani, sosai suka yaba, don ƙwarai kayan sunyi kyau. Kimtsawa itama Aunty Lubna'n tayi, inda cikin motarta su Hayatuddeen suka loda akwatunan. Kaitsaye suka nufi Asokoro wato gidansu Ameena. Horn sukayi inda maigadi ya wangale musu gate ɗin gidan, suka shigar da motocinsu ciki. Tabbas gidan yayi kyau ba laifi, sannan suma masu kuɗi ne. Wata matashiyar Mata itace ta fito zuwa compound ɗin gidan, nan tayiwa su Adda Rahama jagora zuwa cikin gidan, yayinda driver da kuma mai bawa flowers ruwa sune suka shiga jidon akwatunan suna shigarwa zuwa falon gidan. Koda su Adda Rahama suka ƙarasa zuwa cikin gidan, sun samu tarba mai kyau, cikin karramawa matan da suka samu acikin falon suka tarbesu. Nan dai suka zauna inda suka gaggaisa. Take kuwa aka cika musu gaba da kayan shaye shaye. Bayan sun ɗan nutsane. Adda Rahama ta gabatar musu da kayan, nan suma suka yaba sosai, haka dai suka ɗan taɓa hira cikin mutunta juna. Koda suka tashi tafiya haka aka cika musu bayan motarsu da kayan ciye ciye. Nan dai suka rabu cike da ganin mutumcin juna. Duk wannan wainar da ake toyawa Ameena na kwance aɗaki tayi ƙumus, zuciyarta cike take da ɗanyar farinciki, ji take kaman tafi kowa sa'a aduniya, bazata iya misalta daɗin da takeji ba, tabbas babbar nasarace samun Saifuddeen amatsayin miji. Su Adda Rahama kuwa, gidan Aunty Lubna suka koma, nan dai suka ɗiba mata kayan ciye ciye dana shaye shayen da aka haɗosu dashi. Basuwani jima agidannata ba suka kamo hanyar Kaduna. Can gidan su Ameena kusa, ƙwarai sun yaba da kayan, kasancewar sanin Ameena ba budurwa bace, hakan yasa basui tunanin dangin Saifuddeen din zasuyi mata wannan karamcin ba. Koda Momma taƙirawo ta akan cewar tazo taga kayan, koda tagani taji daɗi ƙwarai, don harta farincikinta saida ya kasa ɓoyuwa, Allah kawai take ta godewa acikin ranta. Can Kaduna kuwa, gaba ɗayansu zaune suke afalon Raihanan, inda suke ta hiransu, Hayatuddeen ne yasaka bowl ɗin snacks agaba yanaci kana yana yagan cinyar kaza, sai wani jijjiga kansa yake, yana lashe red lips ɗinsa, wanda suke shige dana Hamma Saifuddeen ɗinsa. Dubansa Adda Rahama tayi, cikin zolaya tace. "Aikin ka kenan autan Ummi ci, acici kazar birni, niko da ace halittarka mai ƙiba ne, sannan ci nasa ƙiba, tabbas Hayatuddeen da yanzu girman jikinka ya cika falon nan." Idanunsa ya zazzaro waje. Cikin shagwaɓa yace. "Haba Adda saikace Yaya Saminu." Dundu Raihana takai masa tare da cewa. "Mijin nawa?." Dukansu suka sa dariya. Ahmad kuwa cewa yayi "Kaɗan ma kika gani indai Hayatuddeen ne." Shima dariyar yayi kana yace. "Ya Wareesu fa nake nufi." Haka dai sukaci gaba da hiransu, har aka ƙirayi sallan magriba. Saida sukayi sallan Isha kafun suka zauna inda suka sake kafa sabon hira. Haka dai sukaita hira har kusan goman dare, dagananne kowa ya nemi makwanci, Inda Ahmad da Hayatuddeen suka shiga cikin wani extra ɗakin dake cikin falon, Su Adda Rahama, da goggo Dada ma ɗaki guda aka basu. Domin kuwa gidan na Saminu akwai yalwatattun ɗakuna. Washegari da safe kuwa, Raihana lafiyayyen break fast ta shirya musu, inda suka cika cikinsu, nan kuma suka soma shirye-shiryen tafiya, don yau ɗinma jirgin ƙarfe 10 zasu bi zuwa Gombe. Saminu ne ya kaisu airport wanan karon hadda Raihana tayi musu rakiya. Basu bar airport ɗin ba kuwa saida suka ga tashin jirginsu, sannan suka dawo gida. Ƙarfe sha ɗayan rana acikin garin Gombe tayi musu, inda Sule driver yazo da babbar motar Saifuddeen har airport ya kwashesu zuwa gida. Afalon Ummi suka baje, wanda nan suka samu Saifuddeen zaune akan wheellchair dinsa, yana shan yogo fruit wanda Ummi ta haɗa masa, yayinda tasashi agaba sai tarairayarsa takeyi kamar wani ƙaramin yaro, shikuwa dama aikinsa ne shagwaɓa hakan yasa ya narke mata. Sam abun baya bawa su Adda Rahama mamaki, saboda sun san ƙaunar dake tsakanin Ummi da kuma Saifuddeen mai ƙarfi ce. Nan dai suka shiga labartawa Ummi, irin tarban mutumcin da suka samu daga wajen dangin Amina. Jin suna ta yaba kirkin dangin su Ameenan yasanya Saifuddeen kauda fuska, nan yamaida hankalinsa ga tv, don bama yason fahimtar mai suke faɗa. Anan dai Adda Rahama tayi sallan La'asar kafun Dr Adnan yazo ya ɗauketa. Goggo Dada ma ɗakin Ummi ta wuce don hutawa, shi kuwa Hayatuddeen sama ya haura, yana shiga ɗakinsa ya jawo wayarsa, data ya kunna sannan yashiga cikin Whatsapp ɗinsa. Nan ya iske saƙon Ameena. Inda tace. "Hey ƙanina." Ganin tana online yasashi sakin murmushi, nan yayi mata reply da cewa. "Sannu me wayo, wato kinma fara ƙirana da ƙaninki ko, saboda kinsan kinyi nasara, zaki auri handsome ɗin Hammana." Ameena dake kwance ganin saƙon Hayatuddeen din yasa ta saki murmushi, harda dariya. Cikin kulawa tace. "Dama na faɗa maka ae watarana insha Allah zan zama auntynka saboda haka biyayya dole." Koda Hayatuddeen yagama karanta saƙon dariya sosai yayi, nan dai ya tsaya suka ɗan taɓa hira da Ameenan, daga ƙarshe ganin ta sauƙa online, yasashi maida hankalinsa wajen chatting da abokansa. Yau kwana Uku kenan dakai lefen Ameena, har zuwa yau kuwa ko da sau ɗaya ne Saifuddeen bai taɓa tura mata saƙo ba, harkokin gabansa ma yake, yayinda ya watsar da batun auren acikin ransa. Inda yanzu auren ya kama saura kwana takwas kacal, domin dasa lokacin auren zuwa yanzu anci kwana shida acikin kwanakin bikin. Adda Rahama da kanta taƙirayi Ummi inda tace ta tambayi Saifuddeen, ko yayi mgna da Ameena'n, sai alokacinne ma Ummi ta farga. Aikuwa tana aje wayan, ta dubi Hayatuddeen dake kwance akan doguwar kujera yana chat. Cikin kulawa tace. "Hayatuddeen ƙiramin Hamma'n ka." Take kuwa ya miƙe, inda ya nufi part ɗin Hamman nashi. Koda yaje afalo ya iskesa, zaune akan wheellchair, inda yake sanye da dogon wando da kuma wata farar t shirt, laptop ɗinsa ne agabansa yana ta faman dannawa yana ta murmushin ganin amsar saƙon da ya kai kwana goma da turawa Zaleeha shi da numbarsa ta sirri in da ya nuna mata shi saurayine kuma yana sonta, to bata duba saƙonba sai shekaran jiya, bata kulashiba kuma sai yanzu da ya sake ce mata. "Hello my love". Koda ta buɗe saƙon sai yaga ta turo mishi amsa. "Wa iyazubillahi, kai wanne irin mutunne da zaka rasa wanda zaka so da bibiya sai matar aure, nayi block naka tun randa naga saƙonka sai kuma naga ka kuma min mgna ban san kai waye bane dake iya sarrafa na'urar da ba tasaba, na haɗaka da Allah da Manzonsa kada ka sake yimin mgna ni matar aurece, kaji tsoron Allah ka rabu dani!". Murmushi yaketayi yana mai-maita karanta saƙonta, yasan dole tayi mmkin cewar tayi blocking nashi kuma taga ya sake mata mgna. A ranshi yake cewa. "Baki san cewa nike sarrafa wayarki ba." Saƙon Ummin Hayatuddeen yasanar masa, sannan ya juya ya fita. Bai wani ɓata lokaci ba, ya nufi ɓangaren Ummin nasa bayan ya rufe system ɗin nashi. Tana nan zaune akan kujera, tana ganinsa taɗan sanja yanayin fuskarta, sarai tasanshi dayaga murmushi akan fuskartata, to tabbas tasan zai ɗauki maganar da zata faɗa masa amazaunin wasa kuma zai samu damar shigar da ƙorafinshi. Dubansa Ummin tayi bayan ya ƙaraso gabanta. Cikin kulawa tace. "Daga ranan dana baka number'n Ameena kawo yau sau nawa katura mata saƙo?." Gane abun da ta faɗa yasashi kwaɓe fuska, tabbas yasan dama watarana za'ayi haka. Ganin yanda ya kwaɓe fuska yasa Ummi cewa. "Au baka tura mata saƙon ba kenan?." Kansa ya jinjina alaman "Eh." danshi dama kwata-kwata bai iya ƙarya ba, sannan kuma koda wasa baya yiwa Umminsa ƙarya. Duban sa Ummi tayi tare da cewa. "To lallai katabbatar da yau katura mata saƙo, ko ka manta cewa aurenta zakayi ne?." Fuska ya sake kwaɓewa, tare da ɗan ciza kyawawan laɓɓansa, shikam yaga takansa da wannan liƙaƙƙen auren, hakanan an tilastashi auren wata mayyar yarinya, gashi tun ma bata shigo cikin gidan nasu ba, Umminsa ta fara takura masa akanta. "Kajini dae kam ko?." Ummi ta katse masa tunanin da yake. Kansa ya jinjina mata alaman yaji. Daga haka Ummi batace dashi komai ba, ta juya inda ta wuce ɗakinta, idanunsa yaɗan lumshe tare da buɗesu alokaci guda, kallonsa ya mayar ga Hayatuddeen wanda gaba ɗaya hankalinsa nakan wayarsa, sai murmushi yake yi, da'alama wani abun yake. Ƙura masa idanu yna ƴan wasu mintuna Saifuddeen yayi, kana ya girgiza kansa, cikin nutsuwa ya tura kekensa inda yabar falon. Bayan yadawo Sallan Isha ne, yaje part ɗin Ummin coffee ya amso tare da dawowa part ɗinsa, wayarsa ya ɗauka inda ya shiga cikin Whatsapp chat ɗinsa. Contact ɗinsa yabi inda ya laluɓo numbern Ameenan, da yayi seven ɗinta da sunan *Ta'annabi* a cewarsa wai sadaka za'a kawo misho ita shiyasa ya raɗa mata sunan Ta'annabi. ido ya ɗan zuwa no tata wanda hoton ta nema akan profile picture ɗinta. View ɗin hoton yayi, inda ya ƙurawa hoton ido. Sosai tayi kyau a hoton don tasha adone cikin wani jan lace, sannan fuskartan nan tayi fayau, don tana murmushi ne aka ɗauketa hoton, taɓe baki yayi tare da maganar zuci, mayya ko me ya tuno kuma sai yayi murmushi sannan ya rubuta mata saƙo kamar haka. "Slm". Ameena wanda kusan always tana online, kwance take akan gado, kamar da wasa kuwa taga numbern Saifuddeen ɗin yayi mata magana, azabure tatashi ta zauna, cikin zumuɗi tace. "Wayyo Allah ni daɗi kasheni, nakarɓi numbern ka wajen Hayatuddeen inason yi maka magana, sai gashi kai ka rigani." Cikin sauri ta amsa masa da. "Wslm". harma da ƙarin tambayarsa. "Ya gida." Yana karanta saƙon nata, yaƙara taɓe laɓɓansa, cikin zuciyarsa yace. "Su mazari, daga magana sai amsa babu ɗan jan aji kamar ba maceba." Ɗan jim yayi, cikin rashin sabo ya rubuta. "Ykk." Sannan ya tura mata. Lumshe idanu Ameena tayi tsabar daɗi, cikin mamaki tace. "Wai yau ni Ameena Saifuddeen ke tambaya ya nake?." Cikin sauri tayi typing.... "Lafiya ƙalau ya aiki, yasu Ummi?." Saida yayi kusan 3 minute bai buɗe saƙon ba, kafun daga bisani ya buɗe. Koda ya karanta ataƙaice yace. "Lfy." Ya amsa ataƙaice. Sanan ya kuma rubuta. "Meyasa kika amincewa Aurena, bayan kinsan da cewa, ni kurma ne, sannan kuma bana iya tafiya?." Ganin tambayar tasa yasa Ameena sakin murmushi, abayyane tace. "Kaiɗin nakeso Saifudeen ina matuƙar sonka, inasonka fiye ma da yanda nakeson komai." Arubuce kuwa cewa tayi. "Nakasa Ba Kasawa Bace, inasonka aduk yanda kake, sannan kuma zan zauna dakai ahaka, aurenka kuma ba kasawa bace." Koda ya karanta saƙon idanunsa ya lumshe tare dayin shiru, kamar zaice wani abu kuma, ataƙaice ya rubuta. "Okay saida safe jekiyi bacci." Daga haka ya kashe data'n sa, tare da aje wayan gaba ɗaya. Inda ya haurawa saman gado ya kwanta. A ranshi yake cewa. "Hmmmm kina dai da abin da kikeso a jikina, fitinanniya kawai mai idon cin maza." Ameena kuwa ganin ya sauƙa online yasa ta lumshe idanunta, daɗi da farin ciki su suka cika zuciyarta, haka tayita juyi akan gadon, wani irin shauƙinsa ne ke damunta, da haka tayi bacci. Tabbas akullum kwanaki ƙarewa suke, haka kuma lokaci na shuɗewa, akwana atashi asaran me rai, yau dai ya kama saura kwana uku kacal bikin Ameena da Saifuddeen. Inda daga ɓangare biyu na gidajen duk shirye shiryen bikin suke. Babu ma kamar gidansu Ameena, inda Ameena'n ke karɓan gyara na musamman, sosai ake mata gyaran jiki, hakan yasa fatarta tayi fresh. Ɓangaren gidansu Saifuddeen kuwa, su Ummi ne kaɗai ke kiɗa da rawansu, Saifuddeen iyakacinsa ido, tunkuwa ranan da yayiwa Ameenan magana ta Whatsapp baisake bi ta kanta ba. Zaune suke su dukansu Afalon Ummi, nan Ahmad ya shigo inda yake ƙara sanar dasu batun tashinsu don dama ya kammala gidansa tuntuni, Nan fa Saifuddeen ya kafe kan cewar Ahmad ɗin babu inda zaije, ae tunda ya saka baki ake ƙoƙarin yi masa auren dole dolensa kuwa ya zauna agidan. Duk kuwa yanda Ahmad yaso Saifuddeen da Ummi su barshi ya koma gidansa sun ƙiya. Nandai Saifuddeen yace Hayatuddeen ya dawo ƙasa, su kuma Ahmad ɗin su koma sama. Hakan kuwa akayi, inda aka gyara duka ɓangare biyun, Raliya ta tattaro kayanta suka dawo sama. Hayatuddeen kuwa ƙasa ya dawo. Can ɓangaren su Ahmad ɗin kuwa aka gyarawa Amarya Ameena. Sannu-sannu bata hana zuwa saide adaɗe ba'a je ba. Rana kuwa bata ƙarya. Yau yakasance Alhamis, inda gobe Jumma'a ɗaurin auren Saifuddeen da Ameena. Acan Abuja yau Ameena ta gudanar da walima, inda aka yi wa'azi mai ratsa jiki, sosai kuwa waliman ya ƙawatar, don Ahmad dakansa ya tura mata kuɗi a account ɗinta, inda yace tayi duk wani hidima da takeso. Kana kuma yaune akaiwa Amarya jere, domin kuwa Babanta da kansa yayiwa kamfanin masu saida furnitures magana, ta online suka sai kayan, wanda Ameenan da kanta ta zaɓi kalan da takeso. Ma'aikatan kamfanin kuwa suda kansu suka zo har gidan su Saifuddeen ɗin suka jera mata kayanta, sosai kuma yayi kyau. Washegari. Jumma'a. Ranan yau takasance jumma'a, wanda kuma ayau ɗinne za'a ɗaura Auren Saifuddeen da kuma Ameena. Tun safe kuwa Saifuddeen yaƙi fitowa, inda ya ce bashi da lafiya, sanin cewa Ameenan ba budurwa bace, kana kuma ba agari za'ai ɗaurin auren ba, yasa sam su Bappa Ali basu matsa masa ba. Ƙarfe tara dai-dai jirginsu zai tashi. Baba Malam, Bappa Ali, Dirankadi, Malam Adam, Baba Bello, Ishaq, Ahmad, Wareesu, Saleesu, Hayatuddeen, sune waƴanda zasuje ɗaurin auren, sai kuma Adda Rahama da Aunty Meena, wanda sune zasu ɗauko amarya. Ƙarfe tara acikin jirgi tayi musu, inda suka ɗaga zuwa garin na Abuja. Sun isa Abuja ƙarfe goma dai-dai, inda kuma za'a ɗaura auren ƙarfe 11 na rana dai-dai. Ya Ahmad ne yazo ɗaukansu kai tsaye Asokoro gidansu Amarya suka nufa. Nan suka tarar da ƙofar gidan ɗinke da jama'a, ƴan ɗaurin aure. Alhaji Naseer da kuma mahaifin Ameena Alhaji Sadam su suka tarbesu cikin mutum tawa, inda su Adda Rahama kuwa suka wuce cikin gidan. Kamar yanda aka sanya lokaci, ƙarfe sha ɗaya dai-dai jama'an dake wajen suka shaida ɗaurin auren Saifuddeen da Ameena, akan sadaki naira dubu hamsin. Nan fa jama'a suka dinga sanya alkahiri, da nema musu zaman lafiya. Acan cikin gida kuwa, amarya Ameena tayi kyau don an tsantsara mata meckup dai-dai misali, inda ta suturce jikinta da shiga ta al'farma, balaifi tayi kyau don kuwa sam bata da muni, saidai kuma bata da azababben kyau. Jirgin ƙarfe ɗaya zasu biyo don dawowa Gombe, hakan yasa Dady wato Alhaji Naseer da kuma mahaifinta suka jata gefe inda sukayi mata nasiha sosai mai ratsa jiki. Harma da ɗan guntun ƙwallanta. Daga haka su Adda Rahama suka kamata, inda aka sanyata a mota, ƴan uwanta biyu ne zasuyi mata rakiya. Akwai auntynta wanda ake ƙira da Aunty Zubaida, sai kuma ƙanwar mamanta, Aunty Zainab, nan dai suka ɗunguma dukansu zuwa airport. Ƙarfe ɗaya kuwa dai-dai jirginsu ya tashi, zuciyar Ameena cike da kewar gida. Sun iso cikin garin Gombe lafiya, inda lafiyayyun motoci har guda shida suka zo ɗaukarsu, Baba Malam dai kaitsaye gidansa aka wuce dashi shida Malam Adam, sai kuma Dirankadi da Ishaq, wanda suma kaitsaye gida suka wuce. Koda suka ƙaraso, sosai ƴan uwan Ameenan suka yaba da kyaun gidan nasu Saifuddeen, nan dai kaitsaye part ɗin Ummi aka wuce da ita. Tarba mai kyau Ummi tayi musu, tare da nuna musu ƙauna, haka ta jawo Ameenan jikinta cikin kulawa tayi musu addu'an samun zaman lafiya, da kuma zuri'a ta gari. Daga nan kuma Adda Rahama tayi musu jagora zuwa ɓangaren Ameenan. Nan ma sun yaba da tsaruwan part ɗin nata. Kasancewar waƴanda sukai mata rakiyan ba kwana zasuyi ba, ƙarfe 5 na yammaci dai-dai sukabi jirgi inda suka koma Abuja. Nan fa akabar Amarya Ameena ita kaɗai aɗakinta. Yayinda ƴan tsirarun mutanen da sukazo bikin, tuni suma sun koma, domin dama Ummi batayi wani gayya ba, Aunty Mina ma tabi Bappa Ali sun koma dukku. Haka gidan ya rage, daga Ummi, Adda Rahama, sai Raliya da kuma Hayatuddeen. Shikuwa Saifuddeen tuni dama yana ƙule acikin ɗakinsa. Koda akayi sallan Isha kuwa, saiga su Ahmad da Ishaq wai sunzo yi masa rakiya zuwa ɗakin amarya, abun ma dariya ya basa, nan dai ya haɗe gabar da yamma, inda yace. "Baya buƙatar rakiyan nasu." Duk yanda sukaso rakasa wajen Amaryar ƙiyawa yayi. Haka suka tafi suna masa dariya. Part ɗin Ummi ya nufa inda yasamesu zaune su dukansu afalo. Cikin salon shagwaɓansa, ya dubi Ummin, gane abun dayake nufi yasa tace da Raliya ta ɗauko masa flask ɗin coffe ɗinsa, don dama tuni ta haɗa masa. Yana amsa kuwa ya juya inda ya nufi part ɗinsa. Ta ɓangaren Zaleeha yabi inda yashiga falonsa, kai tsaye ɗaki ya wuce, kayan jikinsa yaɗan rage sannan yasha coffee ɗin, kan gadonsa ya haye tare da rufawa kansa blanket, sam babuma maganar zuwa wajen Ameena acikin ransa, don kuwa ko Zaleeha dayake mutuwar so, ranan farko baije ɗakinta ba balle wata Ameena da yasan jira take ta ganshi ta mishi fyaɗe dan ya dai san abinda take so. Can ɓangare Ameena kuwa koda tayi sallan isha, komawa tayi ta zauna jigum, kaɗaici ne ya dameta, tun tana zaune harta gaji ta kwanta, take kuwa bacci ya ɗauketa. Washegari. Tunda ya fita sallan asuba bai dawo gidan ba, can ya zauna amasallaci inda ya shiga rera karatun alƙur'ani. Ameena kuwa tana idar da sallah, ɗakinta ta kimtsa, sannan ta zura doguwar hijabinta ta fito. Nanne ta shiga ƙarewa ɓangaren nata kallo. Ganin wata ƙofa acikin falon nata yasata buɗewa, nan ta tsinci kanta cikin wani haɗaɗɗen falo wanda haɗuwarsa ya zarce misali, ƙamshinsa kaɗai da taji yasa ta fahimci cewa ɗakinsa ne. Ƙarewa falon kallo tayi sosai, sannan aɗaɗare ta nufi wata ƙofa dake cikin falon, wanda tana kyautata zaton cewa bedroom ne. Aɗan ɗaɗare tayo knocking, amma shiru ba'a amsa mata ba, tunowa da tayi cewar bazai jita ba koda yana ciki hakan yasa tatura ƙofar ahankali tare da tura kanta ciki, ni'imtaccen ƙamshin daya daki hancinta ne yasata lumshe ido, ƙara kutsawa cikin ɗakin tayi, baki ta buɗe tana ƙarewa aljannar duniyar ɗakinnasa kallo, komai dake cikin ɗakin ya haɗu, ganin baya cikin ɗakinne yasa taɗan sauƙe ajiyar zuciya. Komai dake cikin ɗakin nead, kan gadonne kawai dayake aɗan hargitse, cikin nutsuwa ta shiga kimtsa masa gadon nasa, sabon bedsheet ta shumfuɗa masa, kana ta sake share ɗakin. Nan ta fesa air freshner'n da ta gani asaman mirror'n ɗakin. Take ɗakin yasake ɗaukan ƙamshi. Fita tayi daga ɗakin inda kaitsaye ta wuce ɓangaren Ummi don ta gaida ita. Tana shiga kuwa ta samu Ummin afalo. Cikin ladabi ta rusuna har ƙasa tagaishe da Ummin, cikin jindaɗi haɗi da ƙaunarta Ummi ta amsa mata, tare da tambayanta ya kwanan baƙunta. Cikin al'kunya tace. "Alhamdulillah." Dai-dai lokacin kuwa saiga Saifuddeen din yashigo wanda dawowansa daga masallaci kenan. Afakaice Ameena tasaci kallonsa, shikuwa bai kalli inda take bama saima gaishe da Ummi da yayi. Fuska ɗauke da murmushi Ummin ta amsa. Cikin matsanancin nuna girmamawa Ameena. Tayi ƙasa da murya aladafce tace dashi. "Ina, kwana!." Muskarshi ya ɗan yamutsa tare da taɓe fuska, a hankali ya ɗan ɗago ida nunshi ya kalli fuskarta, kauda kanshi yayi dasauri kana ya...! By *GARKUWAR FULANI* [8/25, 1:58 PM] A: Speɗɗbl Ya buɗe lips ɗinshi a hankali tare da haɗesu alamar lfy. Lumshe idanunta tayi ganin yadda ya motsa jajayen laɓɓansa tabbas tasan zuciyarta tayi kewar ganinsa, sosai taga ya ƙara kyau da kuma cikar haiba, kwarjininsa ya sake bayyana acikin idanunta, don kuwa ga sajen dake kwance akan fuskarsa ya kwanta lub-lub, gwanin ban sha'awa. Aladaf ce ta miƙe daga durƙuson da take, cikin nutsuwa ta nemi hanyar fita daga cikin falon. Har zuwa yanzu ko inda take bai kuma kalla ba, Ummi kuwa tana kula dashi sarai. Ameenan na fita Ummi ta dubeshi da kyau, cikin kulawa da nazartan shi da kyau tace. "Bazan dai gaji da tuna maka cewar Ameena amana ce agare ka, saboda duk wata matar mutum amanarsa ce, saboda haka kada kace wai don itaɗin ba zaɓinka bace zaka wuƙalanta-ta." Ɗan ɓata fuska yayi tare da shagwaɓewa, kana ya gyaɗa kanshi alamu to ƙoƙarin ƙarasawa dinning area ya somayi, duban tsab Ummi tayi masa, cikin kulawa tace. "Ina kuma zaka? ai dai mungama yin break fast da kai, kana da mata saboda haka nasa Raliya ta sa muku abincinku daban a food flask ta kai maka kaje can kaci abincin da matarka." Kasancewar yana kallon fuskar Ummin tasa, hakan yasa shi fahimtar me take cewa. Shagwaɓe fuska yayi, tare da ɗan waro idanunsa waje. Sam bai tsammaci haka ba, haƙiƙa yafara tunanin cewa. Aurensa da Ameena zaisa su Ummi su ɗauke duk wani tallafin da suke basa. Kamar wani ƙaramin yaro haka ya ɗan tura baki. Dai-dai lokacin Raliya tafito daga cikin kitchine hannunta ɗauke da babban food flask ɗin da abincin nasu ke ciki. Dubanta Ummi tayi tare da ƙwalawa Hayatuddeen ƙira, cikin mintuna kaɗan Hayatuddeen ya fito daga cikin ɗakinsa. Kulan Ummi tace da Raliya ta basa, yakai can ɓangaren Ameena'n. Hakan kuwa akayi inda Hayatuddeen ya karɓi kulan ya fita. Ganin da gaske suke, yasa Saifuddeen ɓata fuska, ganin yanda Ummin nasa ta tsaresa da ido ya sa shi tura kekensa, kai tsaye ya nufi hanyar barin falon. Ameena kuwa tana barin part ɗin Ummi kai tsaye part ɗinsu ta dawo, anan cikin falonta ta zauna, inda ta kunna babban tv plasma ɗin dake cikin falon, ɗan lumshe idanunta tayi, tare da sauƙe ajiyar zuciya, har zuwa yanzu tana mamaki, wai ita Ameena ce ke zaune cikin gidan su Saifuddeen kuma take amsa sunan matarsa tabbas wanda ya mance Allah ya wahala. Hayatuddeen ne ya shigo cikin falon bakinsa ɗauke da sallama. Fuska cike da murmushi Ameeena'n ta amsa masa. Ƙarasowa cikin falon yayi, tare da aje mata haɗaɗɗiyar kulan dake hannunsa agabanta. Cikin kulawa yace. "Matar Hamma na ina kwana." Hararan wasa ta watsa masa, tare da cewa. "Yau kuma da wani salon ka ɓullo." Ɗan dariya yayi tare da kama waist ɗinsa, cikin salon tsokana irin nasa yace. "Eh mana, nasan ae yanzu haka daɗi kikeji kin auri min Hammana ko, shiyasa ae na faɗa miki hakan, don ki ƙara jin daɗi da kyau." Murmushi tayi tare da cewa. "Nidai zan so ganin ranar da zaka zamo very gentle man Hayatu." Idanu Hayatuddeen ya ɗan zaro, cikin sangarta yace. "Hayatu? nine ma Hayatu, gaskiya banson Hayatu, ae da Hamma ne bazaki ce masa Saifu ba." Dariya sosai Ameena tayi, don dama ta faɗi hakanne don kawai taga rigiman Hayatuddeen ɗin, sosai sakalci da kuma sangartansa na auta ke burgute. Cikin zunɓura baki Hayatuddeen yace. "Dama hira nazo tayaki tunda kuwa kika ƙirani da Hayatu na fasa." Cikin dariya tace. "To menene sunanka idan ba Hayatu ba? dan ma banƙiraka da Hayatutu ba." Jin haka yasa Hayatuddeen ƙulewa, bakinsa ya turo gaba, cikin halayensa na auta, yace. "Keda Hamma na." Daga haka yafice daga cikin falon. Murmushi Ameena tayi tare da girgiza kanta, sosai takejin dadin hira da Hayatuddeen din. Duban kulan daya kawo tayi, tare da buɗewa. Kasancewar kula ce irin me hawa huɗun nan, hakan yasa ko wanni ɓangare da kalan abincin dake cikinsa. Ganin abincin nada yawa ne hakan yasa ta tabbatar da cewa, bana ta ita kaɗai bane, jitayi zuciyarta tayi mata sanyi domin koba komai zasu keɓe waje guda dashi. Komawa tayi ta zauna tana me jiran shigowansa. Saifuddeen kuwa yana barin falon Ummin nasa, ta ɓangaren Zaleeha yabi inda ya wuce part ɗinsa. Afalonsa ya zauna, bayan ya ƙarasa gaban fridge ya ɗauki goran fresh milk, ahankali yake shan fresh milk ɗin, kana yana ɗan lumlumshe idanunsa, yana kammalawa ya ɗauki laptop ɗinsa, nan ya maida hankalinsa sosai wajen bin diddigin layukan da ƴan kinnafin ɗin da suka sace babbar jikar Matawallen gombe, wanda shine sabon aiki da DSS suka bashi kuma al'ahamadulilla ya gano komai ya kuma miƙashi hannun SS. sam baiji cewa zai je wajen Ameenan cin abinci ba, fresh milk ɗin daya sha ma ya ishesa. Dan yana sane da ita kallon kura da akuya take mishi, ya lura ji take kamar ta cinyeshi ɗanye. Can ɓangaren Ameena kuwa, tun tana zaune har ta gaji ta kwanta, duk kuwa zaman jiran zuwansa take. Abu kamar wasa, sai gashi ana neman share kusan awa ɗaya babu ƙyallinsa, jikinta ne yayi sanyi, hakan yasa taɗan tsakuri abincin kaɗan taci. Tana kammala wa kuwa ta wuce ɗaki. Kwanciya tayi zuciya tasan ta cike da saƙe-saƙe kala kala, so take tasan ina matarsa da ya aura wata daya baya, dam taji zuciyarta ta buga sabida tuno da kyau da tsari da haibar Zaleeha da ta gani a status ɗin Hayatuddeen, to ina taje? Wa zata tamɓaya taji ina take dan ranta na raya mata wani abun akan matar da take tsananin jin kishinta. Ahaka bacci ɓarawo ya ɗauketa. Ba itace ta farka ba kuwa saida aka soma ƙiraye ƙirayen sallan Azahar sannan ta-tashi tayi sallah. Wanka tayi inda ta tsantsara adonta cikin atamfarta me kyau, mayafi ta yafa ajikinta, kana ta nufi ɓangaren Ummi. Nan ta iske Ummi zaune a falo, Raliya kuwa na kitchine tana ta faman hada-hadan abincin rana. Cikin jin dadin sake ganinta Ummi ta tarbeta, hira kaɗan suka ɗan taɓa, sannan ta bi Raliya zuwa kitchine, inda ta shiga tayata suka haɗa abincin rana me rai da lafiya, koda suka kammala ɗakinta ta sake komawa. Ahaka dai Ameena ta ƙare wunin wannan ranan, inda tana idar da sallan isha ta kwanta. Ɓangaren Saifuddeen kuwa gaba ɗaya wunin yau ɗin aɗakinsa ya ƙaresa, saboda ko kaɗan bama yason yaje ɓangaren Ummi, tayi masa maganar Ameena. Washe gari da safe kuwa, kamar yanda tayi jiya haka tayi yau ɗin, domin kuwa tana idar da sallan Asuba, karatu taɗan taɓa, sannan kai tsaye ta wuce ɓangaren nasa. Tana shiga kuwa ta samu baya nan, yauma kimtsa masa ɗakin nasa tayi, inda ta gyara komai yayi nead. Turaren wuta me ƙamshin gaske yau tasanya masa aɗakin nasa. Nan ta wuce ɓangaren Ummi don miƙa gaisuwa. Tana shiga cikin falon Ummi, idanunta suka sauƙa akanshi, wani irin kifiyar ƙaunarsa ce taji ta cake ta aƙirji, saurin sadda kanta ƙasa tayi. Haka ta durƙusa har ƙasa ta gaishe da Ummi, kana shima ta gaidashi. Saboda ganin fuskar Ummi yasashi amsa mata, bisa dole yaɗan kalleta. Miƙewa tayi inda yau dakanta tace da Ummi zata shiga kitchine. To, Ummi tace don bata hanata ba, nan dai ta haɗa musu break mai rai da lafiya, don babu laifi wajen girki kam bata da makusa, ta iya abinci kala-kala. Saifuddeen kuwa ganin cewa yau ita kaɗai tayi girkin, ya sashi guduwa part dinsa, inda ya ƙule cikin ɗaki, bama yaso aƙirasa cin abinci. Taɗan jim a ɓangaren Ummi kafun ta koma sashinta. Koda dare yayi kuwa, zaman kaɗaici gaba ɗaya ya isheta, sosai ta takura da zaman ɗakin, idanuwanta kuwa sun zaƙu dason ganinsa, saidai kuma sam taga alaman babu daman hakan. Saifuddeen kuwa dawowansa daga sallan isha kenan. Kaitsaye ɓangaren Ummi ya nufa. Kamar koda yaushe tana zaune tana lazumi ya sameta. Ganinsa kaɗai yasa ta gane cewar me yazo ɗauka. Dubansa tayi tare da cewa. "Kaje can ɓangaren ku za'a kawo ma Coffee ɗin." Idanunsa yaɗan zaro alaman mamaki, kasancewar ya saba, koda yaushe ko wani dare ita ke haɗa masa coffee ɗin, kana ya amsa ya tafi dashi. Sake cewa da tayi yaje za a kawo masa coffee ɗinne yasa shi juyawa ya koma ɓangarensa. Ummi kuwa kaitsaye wayar Ameena taƙira, bugu ɗaya kuwa Ameenan ta ɗauka, nan Ummi tace da ita. "Tazo ta ɗauki kayan haɗin coffee din, idan yaso taje can ta haɗa masa." Jin cewar zata samu ganinsa, yasa taji sanyi acikin ranta, nan ta zura takalmin ta ta fito. Koda ta isa ɓangaren Ummin tasamu tuni an haɗa kayan haɗin coffee ɗin nasa, cikin wani tray na glass me kyaun gaske. Ɗauka tayi inda ta koma ɓangaren nasu. Kasancewar ta falonta ta bi, hakan yasa saida ta tsaya taɗan fesa turare ajikinta sannan ta nufi ɗakin nasa. A hankali ta kutsa kanta cikin side ɗin nasa falon nasa shiru , babu motsin komai sai sautin Ac dake tashi, ko ina tsab tsab, sai ƙamshin air freshner ke tashi. Cikin nutsuwa ta ɗaura hannunta akan handle ɗin ƙofar tare da buɗewa, taɗan tura kanta kaɗan, hangosa tayi zaune akan wheellchair ya bawa ƙofar baya. Hakanne yasa sauƙe akiyan zuciya kana ta ƙarasa shigowa cikin ɗakin. Ƙarasowa tayi kusan shi, hakanne ya sashi ɗan waigawa, nan fa ya sauƙe idanunsa akanta, dama kuwa tun kan taƙaraso sa hancinsa ya jiye masa baƙon ƙamshi, hakan yasa ya gane cewa, anshigo ɗakin nasa ne. Haɗuwar idanunsu waje ɗaya yasa tayi ƙasa da kanta. Ajiye tray tayi bisa stoll ɗin dake gabanshi. Cikin nutsuwa ta ɗan sunkuyo a hankali ta fara haɗa masa coffee ɗin. Shi kuwa Saifuddeen hannunta ya tsurawa ido zuciyarsa na raya masa abubuwa da yawa, wani irin abu yakeji, wanda shi kansa baisan dame zai ƙirasa ba, kishi ne koko haushi yakasa tantancewa. Musamman ma da yake tuna cewa, kafun shiɗin ta taɓa haɗawa wani abu da hannunta, sannan kuma kafun shiɗin wani ya taɓa mallakarta a matsayin mata duk abinda zatayi mishi ta taɓa yiwa wani ƙaton, Allah ya sani shi dai yanada zafin kishi, shiyasa har kishi yake taya Zaleeha na aure mata shi da Amina tayi. Ɗan taɓe lips ɗinsa yayi kana ya ɗan kawar da kansa gefe. Anutse ta ɗago kofin tea ɗin, ɗan rusunawa tayi tare da miƙa masa. Hannunsa yasa ya amsa. Ɗan dubansa tayi tare da yin ƙasa da kai cikin sanyin murya tace. "Bayan wannan akwai wani abun da kake buƙata ne?." ta ƙare mgnar da mishi misali da hannu. Kansa ya girgiza mata alaman, "A'a" Dubansa tayi inda asanyaye tace dashi. "Saida safe." Still kansa ya jinjina mata. Haka ta juya ta fice daga cikin ɗakin. Ɗakinta ta koma ta kwanta cike da matsanancin begensa, kullum ta ganshi sai taji ƙarin sonsa da kishinsa acikin ranta. Shikuwa baiwani sha coffee ɗin sosai ba, yana kammalawa kuwa ya kwanta. Yau kwana uku kenan da zuwan Ameena cikin gidan amma kuma, ko ka ɗan bata wani samun sakin fuska daga garesa, hasalima sosai zaman kaɗaici ke damunta, donma wani lokaci Hayatuddeen na ƙoƙarin ɗebe mata kewa, daga ɓangaren Ummi dasu Raliya kuwa, suna nuna mata ƙauna dai-dai gwargwado. Yau kuwa gidan nasu ya karɓi baƙoncin Adda Rahama, wacce tazo duba Ummi da zazzaɓin mura ke damunta jin labarin zuwan Adda Rahma a bakin Raliya ne yasa Ameenan tatafi takanas har zuwa part ɗin Ummi inda suka ɗan taɓa hira da Adda Rahaman. Ameenan na fita dan ta koma ɓangarensu ne Adda Rahama ta gyara zama tare da fuskantan Ummi cikin kulawa tace. "Nikuwa Ummi anya Saifuddeen yana kulawa da yarinyar nan?, ki duba fa shigowarsa ɗazun yasame mu dukan mu, amma ko kallonta baiyi ba anya zaman nasu da daɗi." Ɗan jim Ummi tayi tare da cewa. "Nima ina tunanin haka, domin kuwa kullum idan tazo gaisheni ta iskesa, anan part ɗin nawa take gaishesa, hakan kuwa kinga alama ne dake nuna cewa ba'a ɗaki ɗaya ma suke kwana ba." Gyara zama Adda Rahama tayi tare da cewa. "Ae kuwa bai isa ba, hakanan bazai kunyata mu idon mutane ba, wanda yake haukan so da ƙulafashinta ɗin ba ita ke gudunshi ba, yasamu wacce zata zauna dashi kuma shi sai yafara gudunta. Ina a nan Zaleehan ke kwanan garden duk dan kada ta haɗa makwanci dashi, hmm bari zanyi maganinsa ne ɗan nema." Nan ta zaro wayarta, inda ta tura Saifuddeen ɗin text, kan cewar tana son ganinsa afalon Ummi, sannan kuma ya taho mata da key ɗin part ɗin Zaleeha. Ganin saƙonta yasa Saifuddeen ya shiga mamaki me zatayi da key ɗin side'n Zaleeha, haka dai ya ɗauko key ɗin ya nufo ɓangaren na Ummi. Yana zuwa kuwa Adda Rahama ta amshi key ɗin, dubansa tayi tare da cewa. "Daga yau zan kulle part ɗin Zaleeha tunda dai bata nan, sannan kuma zan tafi da key ɗin na ajiye, daga yau kuma idan zaka shiga side ɗinka, sai ka nabi ta ɓangaren Ameena tunda duk nan ma hanya ne." Idanunsa yaɗan zaro waje, cikin yanayin mamaki, tabbas abun nasu yanason shallakewa tunaninsa. Fuska ya ɓata cikin body language yace. "Haba Adda Rahama, wai me yasa kukemin haka ne, hanya ma sai an zaɓamin wanda zanbi, kamar wani ƙaramin yaro." Hararansa Adda Rahama tayi tare da cewa. "Ƙwarai kuwa dole in zaɓa maka inda zakabi." Ummi dai ido ta zuba musu. Ita kuwa Adda Rahama miƙewa tayi ta fice daga cikin falon, ta nufi part ɗin Saifuddeen da matan nashi. Shikuwa Saifuddeen duban Ummi yayi tare da marairaice fuska, kau da kai Ummi tayi, don sam bazata ɗauki excuse ɗinsa ba. Ganin haka ya gane abin nasu haɗin bakine, a ranshi yace. "Sai ta cinye muku ni ai kun huta." Adda Rahama kuwa jawo ƙofar part ɗin Zaleeha tayi ta kullesa. Nan ta wuce ɓangaren Ameena. Afalo ta sameta, tayi jigum ganin Adda Rahaman yasa Ameena sakin murmushi tare da cewa. "Sannu da zuwa. ɗanmurmushi tayi cikin sakin fuska ta zauna kusa da Aminan, A hankali tace. "Ke kaɗai ne ma?." Da sauri ta gyaɗa mata kai tare da cewa. "Eh ni kadai gidan shiru." Ɗan gyara zama tayi kana tace. "Gsky kam gashi kin saba zuwa aikin nan kuma shiru, Amman dama Ya Adnan yace in sanar miki shida da Dr Aliyu sun sa an miki transfer zuwa nan F,M,C Gombe, in kin gama hutun bikin dai zakici gaba da zuwa aikinki a nan." Cikin tsananin jin daɗi tace. "Kai naji daɗi ngd matuƙa Allah ya saka da al'khairi." Amin Amin Adda Rahma tace kana ta fuskanceta da kyau cikin kulawa ta ƙira sunanta. "Ameena." jin yadda ta kiratanne yasa ta ɗago kai a hankali ta dube ta. Gyara zama Adda Rahama tayi tare da sanya hannu ta dafa kafaɗan Ameenan. Cikin kulawa tace. "Ban san irin zaman da kukeyi da ɗan uwana ba kuma basai namiki dogon tambaya ko bindiddiba, ko ko nace ki faɗamin sirrinku ba." Shiru ta ɗanyi ta zubawa Amina ido, Ita kuwa Amina shiru tayi a ranta kuwa cewa take ina na ganshi mutumin da guduna yakeyi. Ganin tayi shirunne yasa Adda Rahma taci gaba da cewa. "Amma tabbas nasan dacewa, har zuwa yau babu wani abu da ya shiga tsakaninki da Saifuddeen, kiyi haƙuri wani zubin hakanan yake, bai fiye son shiga rayuwar kowa ba, bai shiga harkan mutun kai tsaye, kuma baida saurin sabo, amma kuma kema ya zama dole kitashi tsaye, ke dai ba ƙaramar yarinya bace Ameena, saboda haka ke zaki zage ki jawosa jikin ki, kada kuma kijira cewa sai yazo, ko ko sai ya miki magana kafun ki amsa masa, a'a koda bai gayyaceki ba kije garesa, sabida ke halaliyanshi ne. Haka yake duk yadda yake son abu baya nuna kulafashinsa, tunda yake a tsawon rayuwarsa kan abu ɗaya, abu ɗaya tai ya taɓa nuna mana kulafashinsa a kanta. Tun yana yaro koda wani abin cine duk yadda yake son abin in dai ba an bashi bane bazai taɓa roƙaba ko ya nuna yana so. Dan haka na roƙeki da Allah kada ki bari kinesanta kanki dashi idan dare yayi, kinsan hanyar da zaki bi wajen jawo hankalinsa, saboda haka wuƙa da nama duka suna hannunki, mu dai kwanciyar hankalinsa da farin cikinsa shine namu, kada ki bari kuna raba makwanci na roƙeki da Allah." Ta ƙarishe maganar tana mai haɗe hannayenta wuri ɗaya alamun roƙo da neman al'farma. Kai Ameena ta jinjina cike da gamsuwa sabida itama tana fatan samun kusanci dashi, nan tayiwa Adda Rahaman godiya, sannan suka ɗan taɓa hira, daga haka Adda Rahama ta tafi. Haka dai Ameena ta wuni yau ɗin cike da son dare yayi. Ƙarfe 9 na dare dai-dai ta gama kimtsa kanta, cikin nutsuwa ta nufi ɓangaren nasa. Zaune yake akan wheelchair ɗinsa, dagashi sai wani 3 guater jeans da kuma wata fara ƙal ɗin singlet. Yau ɗin agajiye yakejin kansa hakan yasa shi yunƙurin kwanciya da wuri. Turo ƙofar ɗakin tayi wanda kuma dama idanunsa na kan ƙofan. Ganinsa yasanya taji zuciyarta na bugawa da sauri, sannan kwarjinin sa ya cika mata ido, haka dai ta ƙaraso cikin ɗakin, ƙarasowa gabansa tayi inda ta tsaya gefenshi kaɗan. Dubanta yayi cikin yanayin mamaki, don dai baice yana da buƙatar wani abu ba bare yayi zaton wani abun ta kawo masa. Hannu ya ɗaga mata alaman "Lafiya dai." Ɗan shagwaɓe fuska tayi tare da yin ƙasa da murya, a shagwaɓe tace. "Ni dai tsoro nakeji, dana kwanta sai naga kaman abun tsoro zai zo ya kamani." Idanunsa ya ƙura mata, cike da tsananin mamakin maganar nata, mintuna 3 ya ɗauka yana kallonta, kafun ya sauƙe ajiyar zuciya a ranshi yace anzo wurin tazo zata cinyeni ai na sani wannan harijar ƴarinyar bazata barni in samu salamaba. cikin body language ɗinsa yace. "To yanzu da kikazo nan, nine zan kare miki tsoron ko kuma me?." Gane abun da yake nufi yasa tasake saka muryar shagwaɓa. Dubansa tayi tare da cewa. "Nidai gaskiya anan zan kwana, dan tsoron ɗakin can nakeyi." Duk mgnar da zatayi mishi takan haɗa da misalta mishi da yarensu na kurame, dan har yau bata san yana iya fahimtar mgnar mutunba. Shikam dama ya jima da harbo jirginta, ace duk tsawon kwanaki ukun da tayi bata taɓa jin tsoro ba, sai yau, hmmm. Taɓe laɓɓansa yayi tare da nuna mata kan gadon, alaman gata ga gadon ae saita kwanta. Wani irin sanyi taji acikin ranta, saboda ko ba komai zata kwana tana jin sassanyan ƙamshinsa kuma bai koreta kamar yadda ta zataba ko ya nuna mata kyara. Shi kuwa Saifuddeen sauƙa yayi daga kan wheellchair din inda ya hau kan gadon, abaki bakin gadon ya kwanta, tare da jan bargo yaɗan rufa rabin jikinsa, hannunsa yakai inda ya kashe hasken wutan dake ɗakin, bedsite lamp ya kunna. Ta daɗe a tsaye jin shiru ya kuma kashe wutan ɗakin ne yasa Ameena ƙarasowa ta hau gadon, can bayansa ta kwanta, inda ta aje kanta bisa lallausan pillown dake ta fitar da ƙamshi. Lumshe idanunta tayi sakamakon jin yanda ta nutse cikin lallausan katifan, ga kuma wani fitinannen ƙamshi da sanyi me dadi da wani irin azabebben sanyin ɗakin. Ƙura masa ido tayi tana mejin matsanancin shauƙi na fusgarta, ji take kaman tayi hugging ɗinsa, amma kwarjini da nauyi bazai iya barinta ba. Shikuwa Saifuddeen baya ya bata, tare da lumshe idanunsa, bacci yakeji sosai, hakan yasa batare da yayi tunanin komai ba bacci ya ɗaukesa. Ameena kam tajima batayi bacci ba, saboda tuni ta faɗa wata duniyar ta daban, sosai ta shiga tunani. Sai wajen 10 na dare kafun bacci ya ɗauketa. Washegari kuwa koda ta tashi bata iskesa cikin ɗakin ba, toilet ɗinsa ta shiga tayi al'wala, sannan tayi sallah, tana idarwa ta kimtsa masa ɗakin, sannan ta je ta gaishe da Ummi, kamar kullum ita da Raliya suka haɗa kayan break, sannan ta koma sashinta. Wunin yau ɗin kusan kab ɗinsa da Hayatuddeen suka ƙaresa, kasancewar yau ɗin ba school, sosai kuwa ya ɗebe mata kewa. A nanne ta gane ashe Saifuddeen na iya gane mgnar da mutun keyi muddun yana gani motsin bakin mutun, jin wannan abu yasa wata iriyar kuya ta rufeta,kenan duk abubuwan data faɗa mishi a asibitinsu yana jinta, wannan shine shuka a idon makorwa. Taso ta ƙoƙƙefe Hayatuddeen taji labarin Zaleeha amman sai ta gane cewa Haytuddeen ɗin wayone dashi kamar dila, wato duk surutunshi yasan abinda yakeyi, sam yama ƙi bata fuskar suyi mgnar, Dan da tace mishi. "Ni kam ina uwar gidan take ne?." Sai ce mata yayi. "Nine mijinku?." yayi mata halin ɗan Nigeria amsa tambaya da tambaya, haka yasa tayi murmushi tare da cewa "A a." daga nan sai ya meda hankalinshi kan wayarshi. Ita kuwa a ranta take cewa. "Kaji yaro da iya zaro zance, ashe haka yakeda wayo kamar dila, wato in ina son ji in tamɓayi mijinmu kenan." Uhm ta nisa tare da maida hankalinta kan tv. Yau ma dai da misalin ƙarfe 9 dai-dai, ta kuma kaiwa ɗakinsa ziyara, shidai baice da ita komai ba. Hasalima yauɗin tarigasa bacci, don shi ya jima yana amfani da laptop inda yake aikinsa na sirri, ya daɗe yana aikin kafun ya kwanta nan baki bakin gadon. Yau dai kusan kwana uku kenan da Ameena ke kwana a ɓangaren nasa, sai-dai kuma har kawo yau banda gaisuwa babu wani abun dake haɗasu, haka ma duk da cewa agado ɗaya suke kwana, amma ko ƴar yatsarta bai taɓa taɓawa ba, haka itama... Kwanci tashi yau dai kwanan Ameena 13 agidan, sosai kuwa tashaƙu dasu Raliya, sannan idan suka haɗu a falon Ummi, sosai suke shan hira da Ahmad, Ishaq da Salisu kuwa suna yiwa ango tsiyar wai ya samu mace kusa dashi yayi bulum buƙui ya dena leƙa kasuwa ko kaɗan. ɓangaren Saifuddeen kuwa har yanzu ba wani sabo atsakaninsu, idan tashiga ɗakinsa kuwa iya kanta bacci, da gari ya waye kuwa tatashi ta fita.... Yau tun da safe taketa kiran Dr Batulu da suke cewa Mommy ta kirata a kalla sau uku dan tana buƙatar ƙarin bayanin yadda masu irin larurar Saifuddeen ke iya mu'amala da mace. Amman sai ta kasa yiwa Dr batulu tambayar a ƙarshe dai text ta rubuta mata tambayarta, aiko tana ganin tambayar Amina ta kirata da kanta ta bata duk wani ƙarin bayani. Fitowarta daga wanka kenan, body lotion ta shafa ajikinta, tare da ɗan murzawa fuskarta powder, wata nighty gown me fitar da shape ɗin jiki ta sanya, babu laifi kuma dama tana da sura me ɗan kyau, nan rigar ta lafe ajikinta, inda tayi mata kyau, ɗan madaidaicin gashinta ta ɗaure sannan tayiwa jikinta wankan turare. Koda ta kalli kanta amadubi tasan cewar tayi kyau. Cikin nutsuwa tafice daga ɓangarenta batare da ta sanya mayafi ko wani abu ta rufe jikinta ba, yau dai kam ta ƙudurta aranta cewa, zata bawa kanta nutsuwa daga garesa koda ƴar kaɗance. Ahankali ta tura ƙofar ɗakin nasa ta shiga. Yana zaune a tsakiyar gado yasa system ɗinshi a gaba wayarsa na riƙe ahannunsa yana dannawa. Jin ƙamshinta ya cika masa hanci ya sashi ɗago da kansa, inda ya sauƙe idanunsa akanta. Dai-dai lokacin ta maida ƙofar ɗakin ta rufe. Ƙura mata idanu yayi yana me bin ko ina na jikinta da kallo, sosai shape ɗinta ya bayyana har takai ga yana iya hango komai na ƙirjinta. Cikin salon jan hankali tashiga takowa zuwa garesa, inda ta kafesa da idanunta wanda suke cike da mayen soyayyarsa, shiɗin ma yau dai kasa ɗauke idanunsa daga gareta yayi. Ahaka taci gaba da ta kowa zuwa garesa, tana isowa kusa dashi ta lumshe idanunta tare da haurawa kan gadon, kanshi ya ɗan kauda ya maida ida nunshi kan wayarshi, shiru yayi ya bar daddanna wayar tashi jin ta matso kusa dashi gab da gab, juyowa yayi ya ɗan kalleta kwaɓe fuska tayi tare da cewa. "Zan kwanta bacci nakeji." Da idonshi ya nuna mata wurin kwanciya, Madadin ta kwanta inda ya nuna matan sai kawai tasa hannu ta ture system ɗin na shi, da sauri ya sunkuyo dan tare system ɗin daga faɗawa ƙasa, sunkuyowan da yayine ya bawa jikinsu daman haɗewa, fuska ya haɗe tare da yi mata kallon zaki min ta'adi. A hankali tace. "Sorry." Daga nan ta koma ta kwanta, shi kuwa ya ɗan jima a zaune yana chat da Ishaq, in da yake ce mishi yanzu dai saura shida Mudassir suyi aure, tunda shi dai sun nace sun liƙa mishi mata. Jin hakane ishaq yace. ina amaryar. ɗan juyowa yayi ya kalleta, da sauri ya kauda kanshi ganin har yanzu batayi bacciba kuma shi ta zubawa ido. Taɓe fuska yayi tare da rubutawa ishaq. "Gata nan a gefena ta zuba min ido kamar mayya ina ga dai yau kam cinyeni zatayi." Ishaq na karanta saƙonshi ya turo mishi amsa. "In ta cinyeka ma ai halal ɗinta taci, Pleess Saifuddeen mu bar wasa, kayi ƙoƙarin yiwa yariyar nan adalci." Da sauri ya maidawa ishaq amsa cewa. "To naji me nayi mata na rashin adalci, me ta nema ta rasa ban zagetaba ban doketaba, Da tace ɗakina take son kwana ma ban hanataba, kuma gadona na bata ba'a ƙasa nace ta kwanta. Me ya rage zan mata?." Da sauri ishaq yace. "Haƙƙin aurenta mana wanda yake kanka, waji bine bayan ciyarwa da shayarwa ka biya mata buƙayar ta na ƴa mace ka kawar mata da buƙatan Namiji." Uhum Saifuddeen yace lokacin daya karanta batun ishaq cikin sanyi yace. "To ai batace tana soba. Ni kuma banji inada buƙata ba, amman in tace tana so ai gani gata ba sai tayiba tunda ai tasan komai, kuma a ɓurme take tunda ta taɓa aure wani gardin ya taɓa ɓurmata, ni ba rami kawai aka kawo min ba." Sosai ishaq yayi dariyar daga bisani yace, "Tana mace ya za'ayi tace tana so." Cikin ƙosawa da zancen yace. "Uhum baka santa bane wannan da idanu a tsakar ka, ai fyaɗe ma zata min. Kuma na gaji sai da safe." Yana faɗin haka ya rufe data sannan ya ajiyo woyar da laptop ɗin bisa bed side kana a hankali ya kwanta tare da yin miƙa, a hankali yake sauƙe nufamshi dan ya daɗe a zaune gugunshi ya gaji. Shiru sukayi baki ɗayansu a tunaninshi Amina tayi bacci. Ita kuwa idonta biyu, jin motsin ya kwanta ne yasa, ta ɗan buɗe idonta a hankali ta mirgono ta matso kusa dashi. ƙara matsoshi tayi cikin tsananin ƙaunarsa ta manna ƙirjinta da bayanshi, yana jin hakan a jikinshi yace. "Uhummm ta nan kikafi ƙarfi." A zahiri kuwa juyowa yayi da niyar yaga fuskarta sai kuma yayi lub bisa gadon jin ta ruggumeshi da kyau, wani irin yam tsikar jikinshi ta bada, ita kuwa Amina kanta ta ɗan nago ta kalli fuskarsa cikin sanyi ta mirgino jikinta kanshi gaba ɗaya tayi mishi rumfa, hannunta tasa tana shafar sajenshi, har zuwa haɓarshi a hankali ta lumshe ida nunta kana ta manna bakinta kan nashi, da ƙarfi ya sauƙi numfashi lokacin da yaji ta lome tattausan lips ɗinshi tanayi musu wani irin zazzafan tsotso wanda yasan hucewa takeyi a kansu. Shiru yayi mata kamar baisan me takeyi ba ya dai bata jikinshi tayi yadda takeso dan bashi da hurim hanata, ita kuwa lallatseshi tayi son ranta sannan ta sahirta mishi ta koma ta konta, tana sauƙe numfashi. shi kuwa gaba ɗaya yama rasa meke gudana a jiki da zuciyarshi. A haka duk sukayi bacci. Washe gari da safe, koda suka haɗu a falon Ummi ƙin yarda yayi su haɗa ido ya lura so take ta titse mishi idanu. Ganin ta dameshi da kallone ya sallamesu ya fita. Kasan cewar yau jumma'a kai tsaye shirin zuwa masallaci yayi. Wata ɗanyar shadda mai kalan sararin samaniya ya sanya, sosai shaddan tayi masifar yi mishi kyau, hulan zanna bukar ya kafa akansa, inda ya ɗaura tsadadden agogon apple watch a hannunsa, yayi kyau ƙwarai, sai tashin ƙamshi yake, ƙwarai Saifuddeen ya iya tsantsara gaye sosai. Direct wajen Ishaq ya nufa. Daga wajen ishaq ɗin kuwa gidan Baba malam suka wuce, dan kai mishi gaisuwar jumma'a kamar yadda suka saba. Nan suka samu Ya Aminu da Ya Habu kana da Malam Adam, cikin mutunci suka gaisa, kana suka ɗan taɓa hira, a nan Ya Aminu ke cewa zai kawo Maryam taga amaryarshi, sosai kuma yaji daɗin nasihar da Baba Malam da Malam sukayi mishi suma dai sun jaddada yayi mata adalci a cikin zaman nasu. Daga ƙarshe duk suka tafi masallaci kofar sarki a tare kasan cewar Baba malam ne limamin masallacin. Daga masallacin gidansu Ishaq ɗin suka wuce wanda a nanne ya samu Hayatuddeen Zakariyyah da isma'il da Sulaiman Da Khamis sabon abokin Hayatuddden, daga ganin yaron Saifuddden ya karan ceshi ɗan banzan yarone da fuska kamar faskaren wawa ya ƙudurta yana gama aikin da yakeyi, zai maida akalan ƙoƙƙofinshi kan autan Ummi da wannan abokin nashi dan sam bai konta mishiba. Zaleeha kuwa sosai ta saba da Aisha wanda zuwa yanzu mahaifin Aisha Man liman da kanshi yace a ajiyewa Zaleeha kwaryan abinci daga gidanshi wanda kullum yara ke kai mata. Wannan abin yayi matuƙar yiwa Zaleeha nauyi inda taso taƙi amman fir dottijon ya hana, To yau kusan a nan ta wuni ita da Aisha sai yamma ta tafi. Bayan tafiyarta ne, Inna ta kalleshi cikin son fahimtar wani abu tace. "Meyasa ka sawa lamarin yarinyar nan ido ne?." Kanshi ya jujjuya tare da cewa. "Lamarin yariyar akwai abin tausayi, ta gefe biyu ake jefanta da sihiri, Asali zuwanta garin nanma ture akayi mata, kana kuma an kafata anan ɗin bazata iya komawa inda ta fitoba in ba an karya abinda ke jikinta ba, kuma aikine mai wuya dan matsafine yayi aikin, Sannan akwai wani sashin da ake binta da sihirin lalata rayuwarta, wanda badon tana da ƙarfin imani da riƙo da ibadaba da karuwa aka a maidata, ina son ku jata a jiki kuji meya kawota nan, yarinƴar abar tausace dan akwai fushi a kanta." Wani nannauyan ajiyan zuciya Inna ta sauƙe tare da cewa. "In sha Allah za'ayi haka, zan sanarwa Aisha manufarka." Kanshi ya rausayar tare da cewa. "Ƴar birni kamrta mai cikar gata da jin daɗi da wayewa musulma mai ibada me zai sa ta baro inda take cikin jin daɗi tazo ƙauye tsakiyar kafurai ta zauna ai dole da walakin goro a miya." Cikin gamsuwa inna tace. "Gsky kam baza'a rasa ba." daga nan Man liman yaci gaba dayi mata bayanin abubuwan da yake gani a jikinta, wanda duk sihirin Mamane da Ruda sai Bilkeesu dake yi mata dan ta lalace. A haka kwanaki suka ɗan miƙa. Saifuddeen kuwa ya gama tsinkewa da lamarin Amina don yanzu kullum dere da salon da take zuwar mishi, ta kai matakin da tana iya kama kamoi na jikinshi ta tsotsa ko ta kamo hannunshi ta kai inda bai zataba a jikinta. Yau kuwa tun da Yamma Amina keta shirya kanta dan yau dai tayi niyar malaka mishi kanta, ya isheta zamansu a haka zata mori ƙuruciyarta da santalelen mijin da Allah ya azirta-ta dashi. Wani tsumi wanda yaji haɗi sosai ta kafa kai tasha har kusan rabin gora, sannan ta ajiye, ɗan madaidaicin maƴafinta ta yafa inda kai tsaye ta wuce ɓangaren Ummi. Nan falon ta iske Hayatuddeen da kuma Raliya zaune acikin falon, inda suke buga wasan game, wanda sukai connecting da tv, Hayatuddeen sai buga rinto yake, yayinda ko ya faɗi sai yace. "Sam shi bafaɗuwa yayi ba, ko kuwa yace ai bayagani da kyau ne." Raliya kuwa masifa kawai take ta zazzaga masa, don tasani sarai abun nasa zallan rinto ne. Zama tayi agefensu, inda tashiga tayasu game ɗin. Haka dai sunayi suna kuma ɗan taɓa hira, har Ummi ta fito ta iske su, zama Ummin tayi suka ɗan taɓa hira. Ganin magriba ta gabato ne yasa Ameenan komawa part ɗinta. Wanka tayi tare da ɗauro al'walan sallan magriba. Koda ta fito wata simple jallabia irin ta mata ta sanya. Darduma ta shumfuɗa tare da ta da sallah. Koda ta idar kuwa bata tashi akan sallayan ba, saida ta gabatar da sallan isha. Tana sallamewa kuwa tashafa addu'an da tayi, ƙarasawa gaban mirror tayi bayan ta cire jallabiyan dake jikinta. Wani body lotion mai ƙamshi ta shafa ajikinta, sannan tabi jikinta da wani oil ɗin turare irin me kama jikinnan. light meckup tayi akan fuskarta, babu laifi kuma tayi kyau, wani lip gloss me zaƙi ta shafa akan laɓɓanta, wardrobe ɗinta ta buɗe inda ta zaro wani fitinanniyar rigar bacci, wanda take kama da rariyan tata, sam bata ɓoye komai na jiki. Sanya rigar tayi wanda ta tsaya iyaka guiwanta, nan ta sake feshe jikinta da turaruka, wanda musamman anyisu ne don jan hankalin namiji, kasancewar anzuba wasu irin sinadari acikinsu. Zama tayi abakin gadonta, inda ta ɗauki wayarta, ganin lokacin ƙarfe 8:40 na dare ne yasa ta kunna data'n ta, don tasan ba lallaine zuwa yanzu idan taje tasa mesa ba, wata ƙila ma yana ɓangaren Ummi. Shikuwa Saifuddeen kasancewar yau ɗin bai wuni agida ba, hakan yasa yakejinsa agajiye, saboda haka yana idar da sallan isha, bai wani jima a waje ba ya dawo gida, haka kuma kaitsaye ɓangarensa ya wuce baije part ɗin Ummin nasa ba. Yana shiga cikin ɗakinsa, ya soma rage kayan jikinsa, saida ya rage dagashi dai dogon wandon jeans, wata farar riga irin me aninayen nan ya sanya, laptop ɗinsa ya jawo, dan kuwa akwai wani aiki me mahimmanci da yakeson yi, duk dama dai bayajin ƙarfi ajikinsa. Sama-sama yaɗan danna laptop ɗin, jin idanunsa na lumshewa, yasa ya aje komai, hawa kan gado yayi, tare da kashe ƙwan wutan dake ɗakin, blanket ya rufawa jikinsa, kwanciya yayi tare da lumshe idanunsa, cikin ransa yace. "Ya Allah kasa bacci ya ɗaukeni kafun wannan natacciyar tazo, saboda yau bansan da wani salo zata zo ba, ayi mace kamar mayya, shegen kallo, bayaga haka ma, yanzu tagano salon lashe-lashe sai tayi ta lasheni, kullum bata da aiki sai tsotse-tsotsen jikin mutum." sake gyara kwanciyarsa yayi tare da lumshe idanunsa. Ameena kuwa chat ta ɗan taɓa ita da ƴan uwa, da kuma abokanta na can wajen aikinsu, ganin tara da kusan rabi, yasa ta kashe datan nata, nan tasake fesawa jikinta turare, kashe duk wani hasken wutan ɗakin nata tayi, sannan tafice daga cikin ɗakin. Koda tashiga falon nasa, ganin babu wadataccen haske yasa ta gane cewa, yadawo, don aɗan zaman da sukayi ta fahimci cewa, bai cika son haske ya yi yawa awaje ba. Ahankali ta murɗa handle ɗin ƙofar ta shiga, duhun da tagani ne yasa, taƙarasa jikin makunnin wutan ɗakin ta kunna, take haske ya gauraye ko ina. Saifuddeen kuwa da har yanzu bacci bai ɗaukesa ba, ganin hasken wuta ya sashi ɗago kansa, nan suka haɗa idanu da ita, kallonta yayi, inda ta sakar masa murmushi, haɗi da ɗan sunkuyar da kanta, don masifar kwarjini yake mata, aduk sanda ta kalleshi. Cikin wasu ƴan sakanni ya gama ƙare mata kallo, maida idanunsa yayi ya rufe, tare da fesar da numfashi, cikin ransa yace. "Tofa yau kuma da salon da akazo kenan, ni Saifuddeen naga takaina." Ƙarasowa cikin ɗakin Ameena tayi, bayan ta kashe ƙwan wutan, bedside lamp ta kunna, wanda shi ya ɗan haska ɗakin. Cikin nutsuwa haɗi da sanyi ta haura saman gadon, amaimakon ta kwanta, saita ɗan zauna tare da tanƙwashe ƙafafunta, tayi irin zaman nan na sallah, hannunta tasanya inda ta kamo hannunsa ta riƙe acikin nata. Jin haka yasashi juyowa ya dubeta, kallon tsab yayi mata, sai kuma ya tuna da cewa, tabbas akwai haƙƙinta akansa, bacin haka da shareta zaiyi, don agajiye yake. Cikin body language ɗinsa, wanda taɗan fara ganewa, yace da ita. "Wani abu na damunki ne?." Kanta ta jinjina masa, tare da ƙara matse hannunsa dake cikin nata. Ɗan yunƙurawa yayi inda ya tashi zaune, saidai rabin jikinsa akwance suke. Asanyaye Ameena ta sake matsosa, nan take ta shige jikinsa, tare da ɗaura kanta adai-dai wuyansa, ƙamshin turarensa ta shaƙa, tare da sauƙe ajiyar zuciya, sake shigewa jikinsa tayi, inda ta matso da fuskarta kusa da nashi, ahankali ta kawo bakinta dai-dai saitin laɓɓansa, zaro harshenta tayi inda tashiga laso kyawawan laɓɓansa, masu matuƙar kyau. Idanunsa ya lumshe yayinda yaji zuciyarsa na bugawa, can cikin ransa kuwa cewa yayi. "The first wannan itace matsalan auren macen da tasan namiji, gaba ɗaya bazata barka ka huta ba, ta dinga lashe ka kenan kamar sabuwar mayya." Hannunta ta ɗaura akan chest dinsa, ahankali ta shiga wasa da aninayen gaban rigar tasa, cikin sanyi take lasan laɓɓansa, kana tana kusanto da lips ɗinsa kusa da nashi. cikin yanayin sha'awa wanda ƙamshin jikinsa ya sake jefata, ta zame gaba ɗaya aninayen rigar tasa, ahankali tayi ƙasa da rigan nasa, rigar baccin dake jikinta ta zame, sake shigewa cikin jikinsa tayi, take ta sauƙe wani irin ajiyar zuciya me ƙarfi, dan kuwa haɗuwar fatar jikinsu waje ɗaya, yaso zautar da ita. Cikin matsanancin feeling ta jefa bakinta cikin nasa, aɗimauce takamo harshensa tana tsotsa, inda ahankali take goga masa ƙirjinta ajikinsa. Sam yakasa tantance wani irin yanayi yake ciki, sai-dai kuma yasa aransa cewa kome zatayi masa zai daure bazai hanata ba dan haƙƙinta ne. Haryanzu mamakin ta yake, musamman yanda takasa haƙuri, kullum nuna masa zalamarta afili take, shikam dama ae tun ganinta yasan dacewa itaɗin ba ƙaramar jarababbiya bace, kuma shine don munafurci, lokacin da za ai masa aiki, da aka sata cire masa kaya, daganin abunsa ya tashi shine harda wani tsorata, ashe duk tsoron munafurci ne. Ita kuwa ɗan zamewa tayi inda ta ƙarasa cire komai najikinta, inda ta zama naked, ƙara shigewa jikinsa tayi, yayinda ta kuma sauƙe wata irin wawiyar ajiyar zuciya, musamman alokacin da zallan fatan ƙirjinta suka haɗe da nasa, cikin wani irin yanayi ta sake kamo harshensa tana tsotsa, numfashi kawai take ta faman sauƙewa akai akai, ahankali ta zare bakinta daga nasa, cikin nutsuwa ta shiga kissing ɗinsa, akowani ɓangare na jikinsa, harshenta ta ɗaura akan nipples ɗinsa tana jujjuyawa, har cikin jikinsa yaji hakan, amma sai-dai baisan ta yaya zai iya nuna mata cewa, yana enjoying mood ɗin. Cikin salonta, tazage belt din wandon dake jikinsa, anutse ta rabasa da komai nasa. Jin yanda ta maidashi naked yasa shi ɗan buɗe idanunsa, ya saci kallonta. Tabbas ya gamsu cewa, idan ya hanata ƙudurinta, to tabbas zata iya danneshi, abu me sauƙi ne kuma awajenta tayi rape ɗinsa. Ameena kuwa bazata iya tantance awani yanayi take ciki ba, abu ɗaya ta sani shine yauɗin tana matsanancin buƙatarsa fiye da ko yaushe, sannan rashin samun abun da takeso kan iya haifar mata da matsala, musamman ma yanda magungunan da tasha suka soma yi mata aiki. Harshenta ta sanya inda take lashe stomach skin ɗinsa, har wani yaarr haka ya keji ajikinsa. Ahankali tayi ƙasa da hannunta inda tashiga shafa saman mararsa ahankali, harshenta ta ɗaura asaman marar nasa insa tasoma yawo dashi, har ta iso dai-dai kan babban manhood ɗinshi, wanda take ganin ya kai biyun na Ya Amir ahankali ta ɗaura bakinta akai, kana ta sa harshenta tana juyawa abakinta. Wani irin abu Saifuddeen yaji acikin kai zuwa tafin ƙafansa, take tsikar jikinsa suka soma zubawa, yaso daurewa, amma ta iso inda bazai iya daurewa ba, hakan yasa shi sakin wani irin nannauyan numfashi mai zafi. Idanunsa ya lumshe, tabbas yanajin daɗin abun da takeyi masa sosai. Ganin yanda gashin jikinsa suka mimmiƙe kana ga manhood ɗinsa da ta ta cika mata baki, yasan ya taɗan janye bakinta, kana ta haurawa saman jikinsa tayi inda ta jawo blanket ta rufesu, ahankali Saifuddeen yaɗan ja jikinsa, inda ya jingina bayansa da jikin gadon, hakanne ya taimakawa Ameena, sake shigewa jikinsa tayi, ɗan lumshe idanunta tayi bayan ta dai-dai-ta manhood ɗinsa ta yanda zai shige jikinta, ahankali take turasa ajikinta, duk da cewa tasha magunguna da yawa, babu wani wadataccen ƙofa ko dan hakan ya faru ne sanadin haɗe-haɗen da tayi kana kuma tayi katari da inƙarman namiji, amma hakan bazai hana komai wakana ba, wani irin ƙara ta saki alokacin da ta game jikinsu waje ɗaya, lokacin da abun nasa ya gama shigewa cikin jikinta, cikin wani irin pleasure tasamu kanta, irin wanda bata taɓa jiba arayuwarta, bakinsu ta haɗe waje ɗaya. Bisa mamakinta sai taji shima ya cabke lips dinta, yana ɗan tsotsa ahankali. Hakan shiya ƙara taimaka wa wajen mantar da ita, duniyar da take, nan take tashiga sarrafa jikinta ta yanda zasu amfana su duka biyun. Harzuwa yanzu bakinsu na haɗe waje guda. Idan yace baijin daɗi a yanayin da yake cikiba tabbas yayi ƙarya, saidai kuma yanajin cewa kaman akwai wani abu guda wanda bai kammala ba, hakanan yakejin wani abu na daban, a maimakon tunanin Ameena yataho zuwa mine ɗinsa, sai gashi tunanin Zaleeha haɗi da tsantsar soyayyarta sune suka bijiro masa, adadin yadda yake tuno Zaleeha adadin haka Saif ɗinshi ke harbawa yana zautar da Ameena. Ameena macece saboda haka dole take da rauni, sannan ba zata taɓa iya jure yin abun da cikakken namiji mai lafiya zaiyi ba, hakan yasa cikin 30 minute kacal gaba ɗaya tayi weak, nan ta mirgina gefensa tare da kwanciya tayi luf kana tasa hannu ta mirginoshi kanta sabida bin shawaran likitoci, ajiyar zuciya kawai take ta sauƙewa akai akai, wani irin mugun gajiya takejin tayi. Shikuwa Saifuddeen a hankali ya zame daga kanta bayan yazazaga ruwan fitinarshi a jikinta. Juya mata baya yayi tare da lumshe idanunsa, ajiyar zuciya ya sauƙe, yayinda yakejin wani irin sanyi, da'alama zazzaɓi ke son shiga jikinsa, abuku da wanda bai taɓa ba, bai kuma saba ba kuma ga raunin nakasarsa, kusan duk yanda Ameena takai ga jin gajiya, zai iya cewa ya fita bashi yayi aikin ba, amma shiyake jin gajiya, hakanan yakejin jikinsa duk ba daɗi. Cikin ransa yace. "Wayyo Allah na shikenan nikam ta tsotseni, ta kwashe duk wani ɗan kuzari da nake dashi, indai kuwa naci gaba da biye mata, nan gaba kaɗan baza'a sameni da ruwa ajikina ba." Ɗan tashi yayi tare da ɗaukan dogon wandonsa ya sanya, wheelchair ɗinsa ya jawo inda ya hau kai, kai tsaye ya nufi bathroom, kasancewar yasan cewa kwana da najasa ba kyau, sannan kuma dole yayi wanka da ruwan ɗumi ko zaiji ɗan dama, dazaran ya fito a wankan kuwa, dole ya sha maltina da fruit salad don kuwa yana zaton cewa, Ameena ta tsotse masa gaba ɗaya ruwan jikinsa.         Sbpett Lumshe idanunta tayi tana mejin wani irin sanyi na shiga jikinta, cikin wani irin tsantsar farin ciki ta samu kanta, hakanan takejin zuciyarta fes, gaba ɗaya duk wani damuwarta ta kau,  sake shigewa cikin blanket tayi,  cikin zuciyarta tace.   "Tabbas shiɗin na dabanne, duk da cewa namiji ɗaya na taɓa sani kafun shi, amma  nasan cewa, samun irinsa abune me matuƙar wahala."   murmushi tayi tare da ɗan cije laɓɓanta, cikin zuciyarta ta kuma cewa. "Wai ahakan ma don bashi da lafiya, duk lokacin da yasamu lafiya yaya kenan, tabbas ranar zai zautar dani zai sani duniya gajumare."  hannu tasa ta ɗan rufe fuskarta, sakamakon wani irin kunya da taji ya rufeta.     Can  cikin toilet kuwa Saifuddeen ne kwance cikin bathtube ɗin wanka,  yayinda kansa ne kaɗai ke waje,  ya lumshe kyawawan idanunsa, masu matuƙar kyau, ahankali yake fitar da numfashi,  wani irin sanyi haɗi da zazzaɓi zazzaɓi yakeji,  cikin yanayin dauriya haka yayi wanka, wheelchair dinsa ya jawo, kana ya hau kai, ƙarasawa gaban wani ɗan glass, dake kamar sip yayi, nan ya zaro ɗaya daga cikin bathrobe's ɗin dake cikin glass ɗin, sanyawa yayi ajikinsa, yayinda ya riƙe towel ɗaya ahannunsa yana goge jiƙaƙƙen gashin kansa, madannin wheelchair ɗinsa ya danna, tare da nufan hanyar fita daga bathroom ɗin. Ahankali ya buɗe ƙofar ya fito.        Cikin nutsuwa ya tura kekansa zuwa  gaban mirror, handryer ya jona tare da busar da gashin kansa,  turarensa mai sanyin ƙamshi ya fesa, nan ya ƙarasa gaban drawer'nsa, dogon wando da t shirt ya zaro, tare da sanyawa ajikinsa.   Nan ya nufi gadon nasa. Wanda har yanzu Ameena ke kananna ɗe akai.    Hannunsa yakai inda yaɗan janye bargon da take rufa dashi, kasancewar duk abun dayakeyi tana jinsa ba bacci take ba, hakan yasa   ta ɗago da kanta ta kalleshi.     Ganin cewa ba bacci take ba, yasashi jan kekensa baya,  yasake komawa gaban dressing mirror.        Ganin ya juya mata baya, yasa ta tashi daga kwancen da take.  Rigarta dake yashe bisa kan gadon ta ɗauka, nan ta sanya, ahankali ta sauƙo daga kan gadon, cikin yanayin sanyi ta wuce bathroom.          Dukkan abun da take yana lure da ita, dan yana ganinta ta gefen idonsa.      Ganin ta shige bathroom ne yasa shi, ƙarasawa jikin gadon, hannunsa yakai inda ya yaye bedsheet ɗin dake shumfuɗe akan gadon, cikin wani durtsbin wanda yake aje, ƴan kayayyakin da ba a wanke ba,  ya jefasa, sannan ya ciro wani sabo acikin drawer ya shumfuɗa, kasancewar sa mutum me tsananin son tsabta,  shiyasa baijin zai iya kwana akan  wannan bedsheet ɗin, domin idanunsa sun gane  masa sperm ya zuba kaɗan ajikin zanin gadon.              Yana gama shumfuɗa zanin gadon, ya sauƙa daga kan wheelchair ɗinsa, hawa kan gadon yayi  tare da jawo sabon blanket ya rufa ajikinsa.                    Kwanciya yayi tare dayin lub, sannu ahankali  yakejin zazzaɓin jikinsa na ƙaruwa.              Can cikin toilet kuwa  wanka Ameena tayi, sannan ta ɗauro alwala,  itama ɗaya daga cikin bathrobe ɗin nasa ta sanya,  nan ta fito daga toilet ɗin tana me goge kanta.         Handryer'n da yayi amfani wajen busar da gashin kansa, itama dashi tayi amfani, wajen busar da gashin kanta, daba yawane dashi ba, saidai yana da ɗan cika, amma baida wani tsawo. Dubanta takai garesa, ganin ya naɗe akan gado  tare da ɓoye jikinsa cikin blanket, yasa tayi tunanin cewa ko bacci ne ya ɗaukesa.     Ganin cewa bata da kaya anan ɗakin nasa, yasa cikin nutsuwa ta buɗe kofar ɗakin  ta fice.    Kaitsaye ɗakinta ta wuce. Nan ta sanya wata ƴar doguwar riga marar nauyi ajikinta,  turare ta fesa sannan  ta koma zuwa ɗakin sa, don ayanzu batajin zata iya kwana awani ɗakin bayan nasa, koda ta kwana anata ɗakin ma, tasan cewa bazata ji daɗin kwanciyar ba, kasancewar ta fahimci cewa, bacci yafi mata daɗi idan tana shaƙan daddaɗan ƙamshinsa. Koda ta koma ɗakin nasa, hayewa saman faffaɗan gadon tayi  tare da jawo sabon blanket ɗin ta rufe jikinta, kanta ta ɗaura akan pillow tare da lumshe idanunta.                 Jin alaman kwanciyarta ya sashi buɗe idanunsa, don dama ba bacci yake ba.                 Ɗan mirginowa yayi tare da juyowa, ya zama  suna fuskantar juna,  matso da jikinsa yayi kaɗan,  tare da sa hannunsa ya tallafi fuskarta,  hakanne yasa  ta buɗe idanunta.         Bakinsa ya ɗaura a dai-dai goshinta, inda ya ɗan manna mata sasanyan kiss.     Sosai taji abun ajikinta hakan yasa ta lumshe idanunta. A hankali yasa tafin hannunshi ya shafi fuskata, Jawota yayi ya mannata da jikinshi, cikin yanayin zazzaɓi da yakeji ya ruggimeta. sannan yasake rufasu da blanket,  shigawa cikin jikinshi tayi da kyau tare da lafewa tana sauƙe ajiyan zuciya, shi kuwa Saifuddeen bisa goshinta ya kuma sumbata kana ya rufesu da kyau saboda wani irin sanyi da yake ji.                 Itakuwa Ameena sosai ɗan kiss ɗin da ruggumar   da yayi mata ya jefata cikin shock, taji daɗi ƙwarai, dan kuwa koda wasa bata tsammaci kulawa daga garesa ba,  rungumeshi tayi tana murmushi.                 Shikuwa Saifuddeen yayi  hakanne, saboda yaga dacewar abun, bai kyautuwa ace yana shareta, sannan  kuma ya hanata kulawarsa, tabbas akwai haƙƙinta akansa, wanda kuwa idan bai sauƙe ba, Allah zai iya kamashi,  saboda haka dole zaiyi ƙoƙari sauƙe duk haƙƙinta daya rataya kanshi, amma badon wai yana jin sonta aransa ba sam babu ko ɗaya, ƙauna dai guda ɗaya ce, kuma tun a haɗuwar farko ya mallakawa Zaleeha gaba ɗaya ƙauna da zuciyarsa, saboda haka baijin cewa Ameena zata taɓa samun gurbi cikin zuciyarsa, saidai yayi mata kara da kawaici kawai dan darajar sonshi da takeyi tafi ƙarfin wulaƙantawa, amma bawai don yana sonta ba. Tana rungume dashi haka bacci ya ɗauketa,  shikuwa yajima sosai kafun bacci ya ɗaukesa,  saboda zazzaɓin jikin nasa yaƙi sauƙa.                           Ƙiran sallan asuban fari da akayi yayi dai-dai da lokacin dayi juyi, saboda gaba ɗaya zazzaɓi ya hanashi samun isashshen bacci,   ahankali ya tashi zaune,  hannunsa ya ɗaura akan wuyansa, sosai jikin nasa yayi zafi jau.   Cikin ɗan dauriya ya jawo wheelchair ɗinsa,   hawa yayi tare da shagwaɓe fuska, sam shi hakanan yake baida dauriyan ciwo, musamman ga  irin waƴannan ƙananun ciwukan, yafiso idan baida lafiya yayita zuba sakalci, haɗi da shagwaɓa tamkar ƙaramin yaro kuma ma dai halittarsa ce raki in yaji ciwo kaɗan zaitawa Ummyn shi da Adda Rahma Raki.       Bathroom yashiga inda ya ɗauro alwala, koda ya fito sallaya ya shumfuɗa, sauƙa yayi daga kan wheelchair ɗin, inda ya zauna akan sallayan.              Nafila raka'a biyu yayi,  yana idarwa ya jingina jikinsa da jikin wheelchair ɗinsa, wanda ke bayansa,  ganin alamun anshiga sallan asuba ne, yasa shi ta da nasa sallan a gida, dan sam baijin cewa zai iya zuwa masallaci, bama yajin ƙarfi ajikinsa.     Yana cikin gabatar da sallan Ameena tatashi, tasha mamakin ganinsa, dan kuwa tasan baya sallah agida,  nan dai ta wuce toilet ta ɗauro alwala, can gefe ta shumfuɗa sallayanta sannan ta tada nata sallan.              Saifuddeen kuwa yana idarwa, addu'a kawai ya shafa,  ataƙaice yayi azkar tare da ɗan jan jikinsa ya sake hayewa saman gado,  dan zazzaɓin ƙara hawa jikinsa yake, ko ina na jikinsa ya ɗau zafi jau, kamar wanda ake hura masa wuta, sake  duƙunƙunewa yayi acikin blanket, lokaci ɗaya ya fara masassara.               Koda Ameena ta idar da salla, cikin sanyi ta dubeshi,   tashi daga kan sallayan tayi nan taƙaraso zuwa jikin gadon.       Cikin kulawa tasanya hannu inda taɗan taɓa forehead ɗinsa, jin jikinsa da zafi yasa taɗan waro idanunta waje.     Cikin yanayin tausayinsa tace.    "Sannu baka da lafiya ne?"                        Idanunsa ya lumshe batare daya amsa mata ba, saboda sam baya son damuwa, cikin zuciyarsa kuwa cewa yayi. "Kuji shegen iyayi, koma mene bake kika jawomin ba, ina zaman zamana kinzo kin tsotseni, jarababbiya kawai, saboda kin zuƙeni ne ae yasa duk zazzaɓin ya hau jikina,  hakanan ina matsayin saurayi, kinzo cikin mintuna kaɗan kin maidani ɗan ƙaramin bazawari."                  Ganin yayi shiru ne yasa Ameena cikin tausayawa  ta gyara masa blanket ɗin, nan ta kashe AC'n da sanyinsa keta busawa,   asanyaye tace.    "Allah ya ƙara sauƙi."      Nan tashiga kimtsa ɗakin nasa, tana kammalawa kuwa ta kunna burner, inda ta zuba turaren wuta mai daɗin ƙamshi, take kuwa ɗakin ko ina ya cika da ƙamshi.      Fita tayi daga ɗakin nasa, kai tsaye ta koma nata ɗakin, wanka tayi  tare da kimtsa kanta cikin riga da sket na atamfa, kana ta yane jikinta da mayafi, flat shoe tasanya, kai tsaye ta nufi ɓangaren Ummi dan zuwa gaisheta, kamar yanda ta saba akowacce rana. Saifuddeen kuwa, bacci ne ya ɗaukesa, don dama daren jiya baiwani samu isashshen bacci ba.               Itakuwa Ameena koda ta ƙarasa ɓangaren Ummi, yau bata iske Ummin a falo ba, saidai ta taradda Raliya wanda ke ƙoƙarin kimtsa falon, kasancewar daren jiya anan Hayatuddeen ya ƙare hirarsa da ciye ciyensa, gaba ɗaya yayi fatali da filullukan kujerun falon, ya watsar su aƙasa, sannan ga ledodin sweet wanda yasha ya zubar acikin falon.      Gaisawa sukayi da Raliyan sannan ta nufi ɗakin Ummi.  Tsayawa tayi ajikin ƙofar tare dayin knocking,  Ummi dake zaune akan gado, jin ana buga ƙofar, yasa ta bada izinin shigowa,  ahankali Ameenan ta tura ƙofar ɗakin ta shiga.   Ganin Ameena yasa Ummi sakin murmushi.  Ƙarasowa cikin ɗakin Ameena tayi, anutse ta durƙusa, cikin ladabi ta gaishe da Ummi'n, nan Ummi ta amsa mata fuska asake, tana murmushi kamar kullum.    Ganin kaya akan gadon Ummi'n, wanda da dukkan alama kayan gugane, yasa Ameenan tashi, cikin nutsuwa ta shiga jerawa Ummi kayan acikin drawer, sosai Ummi kuwa taji daɗin hakan, dan dama tana ƙoƙarin jera kayan kenan Ameenan ta shigo.   Haka Ameena ta gama jera  kayan tsab, inda suke ɗan taɓa hira kaɗan kaɗan da Ummi'n, tana kammalawa kuwa ta sharewa Ummi ɗakin nata, duk da cewa ma ɗakin fes yake, bai wani buƙatan shara, don kuwa Ummi sam batason ƙazanta, kusan awajenta ma Saifuddeen ya gaji ƙamshi da kuma yawan tsabta da ƙyanƙyami.      Koda ta gama  falo ta dawo, bayan tasamu sanya al'barka daga bakin  Ummi'n,  ganin Raliya  a kitchine yasa tayi  kitchine ɗin itama, nan  tashiga tayata aikin breakfast ɗin da takeyi, inda suke hira sosai.           Koda suka kammala kuwa akan dinning suka jere komai, lokacin kusan ƙarfe 8 na safiya kenan, Ahmad ne ya shigo cikin falon, dai-dai lokacin kuma Ummi ta fito daga ɗakinta.     Cikin girmamawa Ahmad ya gaidata,  cikin kulawa, da kuma nuna ƙauna ta amsa masa. Sosai tayi mamakin rashin ganin Saifuddeen a falon, dan kuwa tasan dayaje sallan asuba ya dawo, ita yake fara zuwa ya gaisar, amma saigashi yau bashi babu alamansa, abun dayaso ɗaga mata hankali kenan, dan tasan cewa idan Saifuddeen nada lafiya bazai taɓa kai warhaka baizo ya gaisheta ba, kuma kullum, koda yaushe, a irin wannan lokacin zaka sameshi cikin falon nata zaune. Duban Ameena tayi cikin kulawa tace. "Ameena waini kuwa yau ina Saifuddeen, anya kuwa yana lafiya?." Kai Ameena ta sadda ƙasa, cikin sanyi tace. "Yana ɗakinsa, tun safe yake kwance, zazzaɓi ke damunsa." Cikin matsanancin damuwa Ummi tace. "Subahanallah, zazzaɓi kuma, to yasha magani ne?." Kai Ameena ta girgiza alaman. "A'a" Ahmad dake zaune ne yace. "Nima nayi mamaki dan yau banganshi cikin masallaci ba, kenan ko sallan asuba bai samu yaje ba." Kai Ameena ta jinjina alaman.  "Eh." Cikin yanayin sanyi haɗi da tausayawa Ummi tace. "Nidai nasan cewa hakanan Saifuddeen bazai taɓa kaiwa har iwar haka, batare da yazo ya ganni ba, rashin lafiya ce kaɗai zata ɓoyeshi, muje yanzu ki kaini sashin naku na duba shi." Nan Ahmad da Raliya sukace suma zasu, Hayatuddeen da fitowarsa kenan, jin cewa zazzaɓi na damun hammansa yasa yaji gaba ɗaya hankalinsa ya tashi. Nan suka bi Ameena zuwa part ɗin nasu. Haryanzu kwance yake acikin blanket, dan kuwa zazzaɓin nasa bai ragu ba, saidai kuma ya farka daga ɗan baccin daya ɗaukesa. Ahankali Ameena ta tura ƙofar ɗakin, kasancewar itace agaba. Nan su Ummi suka rufa mata baya. Ganinsa nannaɗe cikin bargo yasa Ummi ƙarasowa cikin sauri, hannu tasa taɗan ɗage blanket ɗin, hannunta takai ta taɓa goshinsa, jin an taɓa goshinsa ya sashi ɗan buɗe idanunsa kaɗan, dan duk atunaninsa mayyarsan ce Ameena.  Ganin Ummi yasa shi ware idanunsa, tare daɗan yunƙurawa ya tashi ya zauna. Cikin kulawa Ummi tace. "Sannu Saifuddeen." Kansa ya jinjina mata amatuƙar shagwaɓe, yana me kallon su Ahmad dake tsaye. Kafaɗansa Ummi taɗan kama, cikin kulawa haɗe da tausayinsa tace. "Sannu meke damunka ne?." Sake shagwaɓe mata fuska yayi, cikin zuciyarsa yace. "Bakune kuka matsa sai na auri wannan Ameenan ba, gashinan jiya duk ta tsotseni, ta rabani da samartaka na, ji yanda take wani wuƙi-wuƙi da ido, ko kunyana ma bataji."    a bayyane kuwa hannun Ummin nasa ya kamo, ya ɗaura akan wuyansa. Nan Ummi taji jikin nasa zafi jau, cikin tausayawa ta dubesa, murya asanyaye tace. "Zazzaɓine ke damunka ko, sannu, yanzu me kakeson ci, idan kaci sai kuwuce asibiti da Ahmad, dan nasan bakasha magani ba." Kwaɓe fuska yayi tare da kamo hannun Ummin nasa ya sanya acikin nasa, idanunsa yaɗan lumshe, gane abun da yake nufi yasa Ummin riƙe hannunsa ɗaya cikin kulawa tace. "Bayan zazzaɓin kuma saime ke damunka!." haka take lallaɓasa kamar wani ɗan yaro. Shikuwa kansa ya ɗaura akan kafaɗanta, inda yasa hannunsa ɗaya ya nuna mata waist ɗinsa ta baya, alaman bayan zazzaɓin nan ke masa ciwo, sannan kuma ya nuna mata jikinsa, alamun cewa gaba ɗaya jikin nasa ma ciwo yake masa. Ɗan jim Ummi tayi tare da ƙuresa da ido, hakanan zuciyarta ta bata wani abu, ɓoyayyen murmushi ta sake, take wani irin daɗi ya cika zuciyarta, hannunta tasanya cikin gashin kansa, cikin yanayin kulawa tace.   "Fine boy ɗina sannu ko, zakaji sauƙi insha Allah, sannan ciwon jikinma zai daina, yanzu faɗamin mekakeson ci, zan dafa ma da kaina." Baki Ameena ta buɗe tana kallon Ummi da Saifuddeen ɗin, tunda take aduniya bata taɓa ganin ƙauna irin tasu ba, wannan salon ƙaunar tasu daban take, musamman idan akayi dubi da irin yanda Ummi ke shagwaɓa Saifuddeen, shikuwa indai yana gaban Umminsa jinsa yake kamar yaro ɗan shekara 3, saboda haka duk wata irin shagwaɓa ta duniya da taɓara ya iyata. Ahmad  da Raliya kuwa murmushi kawai sukayi, dan sunsaba da ganin zallan shagwaɓan Saifuddeen da kuma yanda Ummi ke biye masa, Hayatuddeen kam waje yanema ya zauna. Sake narkewa Ummin nasa yayi, asakalce ya kuma ƙara ɗaura kansa akan kafaɗanta, sai wani ɗan yamutsa fuska yakeyi, saikace wanda shi yayi aikin. Kansa Ummi ke shafawa, duban Raliya tayi kana tace. "Raliya haɗo masa tea, da kuma chips, idan yaci sai su wuce asibiti" Hannun Ummin nasa ya kamo tare da girgiza kansa, cikin body language ɗinsa, yace. "Fruit salad da maltina kawai yake da buƙata." Dubansa Ummi tayi tare da sakin murmushi, nan tace da Raliya takawo masa maltina'n, idan yaso saita koma ta haɗo masa fruit salad ɗin. Hakan kuwa akayi, maltina meɗan sanyi Raliya ta kawo masa,  Ummi dakanta ta ɓalle masa murfin maltina'n, ahankali yakai bakinsa tare daɗan lumshe idanunsa,  cikin ransa yace. "Idan kuwa nasha naji ƙarfi ajikina, ya tabbata cewa wannan Ameenan ba sperm kaɗai ta zuga ajikina ba harda jinina." Ɗago idon da zaiyi kuwa karab sukai ido huɗu da Ameena wanda ta ƙura masa ido, itakam sosai duk wani acting ɗin da zaiyi yake burgeta, yanzu ma haka ji take inama da ace ita yakeyiwa shagwaɓan nan ba Ummyn shiba aima itace matarsa itace ta dace da irin wannan abin da yakeyi. Ɗauke idanunsa daga kallonta yayi, cikin ransa yace. "Wallahi gudunki zannayi, hakanan da ƙuruciyata  bazan amince ki maidani tsoho ba, daga zuwa ɗaya har kinsani rashin lafiya, next kuwa inaga ko tashi bazan iya ba, da wani idanunki awajen ai kin san dai bani da lfy." Yaƙare zancen zucin yana ɗan hararan gefenta. Ahmad kuwa duk abun da Saifuddeen din keyi yana lure dashi, hakanan yasaki wani irin dariya, wanda yasa Saifuddeen ɗin watsa masa harara, cikin ransa yace. "Ehem dole kayi dariya ae, tunda kafahimci cewa mayyar da kuka haɗani da ita, tun ba'ayi nisa ba tafara tsotseni."    Idanu Ahmad ya kashe masa alaman, yane?  laɓɓa SAIFUDDEEN ɗin ya ciza, tare da jinjina kai, alaman zasu haɗu ne. Ummi kuwa murmushi take, dan tagama fahimtan komai, tabbas tasan cewa Saifuddeen baison wahala ko kaɗan, wannan dalilin shiyasa ma wata ƙila zazzaɓi ya sauƙar masa. Yana gama shan maltina'n Raliya ta kawo masa, haɗaɗɗen fruit salad wanda yaji madara. Balaifi ya ɗan sha, ya kuma ji daɗin bakinsa. Dubansa Ummi tayi cikin kulawa tace. "Kasamu kayi wanka, kuje asibiti likita ya dubaka, ko kuma ma zan ƙira Dr Adnan kawai yazo ya dubamin kai agida." Tana gama faɗan haka ta miƙe tsaye, nan ta fice daga cikin ɗakin,  kana Raliya ma ta rufa mata baya. Ahmad ma binsu yayi, Hayatuddeen kuwa hannun Hamman nasa ya kamo, cikin kulawa yace. "Sannu My lovely Hamma Allah yabaka lafiya." Kai Saifuddeen ya jinjina masa alaman "Ameen." Nan Hayatuddeen ɗin ya miƙe yafice daga cikin ɗakin. Ajiyar zuciya Ameena ta sauƙe, tare da takowa taƙaraso kusa dashi, zama tayi agab dashi, cikin kulawa ta kamo hannunsa,  fuskarsa ta shafa tare da cewa. "Ya jikin naka?" Kansa yaɗan jinjina mata, alaman. "Dasauƙi"  tare da ɗan mako hannunta yayi kissing bayan hannun, sannan ya janye fuskarsa  baya. Jawo wheelchair ɗinsa yayi ya hau, ahankali ya tura kansa zuwa toilet. Ajiyar zuciya Ameena ta sauƙe, hartayi tunanin binsa cikin toilet ɗin kuma saita fasa,   nan dai tayi kwance akan gadon, lumshe idanunta tayi, tana me tuno moment dinsu na daren jiya, hannunta takai kan mararta, asanyaye tace. "Ya Allah kasa adaren jiya nasamu rabo daga Saifuddeen, tabbas kuwa da sainafi kowa farinciki, domin samun iri daga Saifuddeen babban abun al'fahari ne,  sannan kuma zan zama kamar zara acikin taurari, dan haihuwa da Saifuddeen babban nasara ce, ya Allah kabani ɗa ko ƴa me kama dashi." Cikin farin ciki ta amsawa kanta da "Ameen." Saifuddeen kuwa balaifi yaɗanji dama, sake wanka yayi tare dayin brush, nan yafito jikinsa duk danshin ruwa, harzuwa lokacin Ameena na kwance, kasancewar wani ɗan bacci-bacci ne ke fusgarta. Tsane jikinsa yayi, inda ya shirya kansa cikin wasu lafiyayyun riga da wando ƴan kanti masu tsadar gaske, sosai yayi kyau cikin kayan,  wankan turare yayiwa jikinsa,  wasu baƙaƙen toms yasanya aƙafansa, masu kamar combat, gashin kansa sai ƙyalli yake, wayansa ya ɗauka, nan yaƙaraso jikin gadon, ahankali yaɗan leƙa fuskar Ameena, gani yayi ma baccinta take cikin kwanciyar hankali. Kansa ya jinjina tare da yin ɗan murmushi cikin zuciyarsa yace. "Badole kiyi bacci ba, tun da dai daren jiya kinsamu ɗan bawan Allah kin gurza."   tura kekensa yayi inda ya fice daga cikin ɗakin. Cikin nutsuwa ya nufi part ɗin Ummin nasa, koda Ummi tagansa taji daɗi sosai, duk da cewa zazzaɓin baisakesa duka ba amma dai yaɗanji sauƙi, kwanciya yayi afalon, Ahmad dake zaune afalon ne ya matso kusa dashi. Duban Saifuddeen ɗin yayi cikin ƙasa da murya yace. "Ango kasha mai, to yaya yakaji auren da daɗi ko?" Cikin takaici Saifuddeen ya ɗauki pillow'n kujera ya gwaɗawa Ahmad ɗin, dariya Ahmad yayi, tare da cewa. "Daga faɗan gaskiya kawai, ai kuwa dai wannan amarya taka jaruma ce, saboda haka ka ƙara riƙeta da kyau, kaikuma saika tsaya adubaka,  saboda dai yanzu kam kafita sahun saurayi kadawo bazawari!." Cikin tsokana Ahmad ya ƙare maganar, sanin cewa ya hasala Saifuddeen ɗinne yasashi matsawa gefen cikin sauri, dan yasan yanzu Saifuddeen ɗin zaikai masa duka. Saifuddeen kuwa sosai ya ƙulu, hakan yasa yadinga cije laɓɓansa, yana hararan Ahmad, Ahmad kuwa mezaiyi inba dariya ba. Suna haka Dr Adnan ya iso, dan Ummi taƙirasa, inda tasanar dashi matsalan Saifuddeen ɗin. Sosai Dr Adnan din yayi checking dinsa, ganin komai lafiya yasashi, rubutawa Saifuddeen ɗin magunguna, nan ya miƙawa Ahmad yace "Yaje pharmacy ya sayo."   bakomai yasa masa zazzaɓin ba kuwa face, yanayin daya samu kansa aciki wanda bai taɓa ba, hasali kuma hakan yafarune bawai don bashida lafiya ba,  ko wasu masu lafiyan sukan samu kansu cikin irin condition ɗin da Saifuddeen yasamu kansa,  musamman idan hakan yazama shine farkon fara sex ɗinsu, sannan hakan na faruwa idan Namiji yaɗauki tsawon lokaci yanajin sha'awa, sannan kuma bai samu yayi sex ba, to aduk lokacin da yayi sex da mace, yana zubar da sperm zazzaɓi  me zafi zai iya rufesa, wanda kuma zai iya sauƙa akowani lokaci. Nan dai Dr Adnan yayi masa fatan sauƙi daga, haka yayiwa Ummi sallama ya tafi. Cikin mintuna kaɗan kuwa Ahmad ya kawo maganin, shida kansa ya bawa Saifuddeen din magungunan yasha. Haka dai Saifuddeen ya ƙare, gaba ɗaya wunin yau  a part ɗin  Ummin sa, ba laifi kuma yaji sauƙin jikinnasa sosai.            Can cikin Gombe State University kuwa Hayatuddeen ne ke zaune acikin class, inda gaba ɗaya fiye da rabin ɗaliban ajin nasu ke waje, kasancewar sun ƙarƙare lecture ɗinsu na wannan ranan,   can ƙarshen benci yaje ya takure kansa, wayarsa ƙirar iphone 8+ ne ahanunsa, yayinda ya saƙala earpiece akunnensa,  gaba ɗaya yaba da hankali haɗi da nutsuwarsa ga wayarsa, da dukkan alama wani abu yake kallo wanda ya ɗauke masa hankali.            Khamis dake tsaye akansa tun ɗazu batare da, Hayatuddeen din  yasan da zuwansa ba ne yasaki dariya, azabure Hayatuddeen ya ɗago kansa, ganin Khamis yasashi, sakin wata irin ajiyar zuciya me ƙarfi, aɗan hasale yace.  "Mcheeww wallahi Khamis kai banza ne ji ka tsoratani."      Murmushi Khamis yayi tare da zama agefen Hayatuddeen ɗin, hannu yasa ya dafa kafaɗan sa, dubansa yayi tare da cewa.    "Kai wallahi tsoronka yayi yawa, menene to acikin BF da har ma sai ka ɓuya kake kallonsa, hmmm yaro inzakasha giya kasha ta dubu, kaine har yanzu kanka bai gama wayewa ba, har yanzu fa baka iya ko riƙe hannun mace, iya iskancinka ya ƙare a waya, daga anyi magana kace kai bazaka iya ba, mufa yanzu mune manyan gobe, yanzu ne ya kamata ace munci ƙuruciyar mu, mun shana, sannan muyi abun da mukeso."            Iska Hayatuddeen ya fesar ta bakinsa,  girgiza kansa yayi tare da   cewa.                   "Bazan iyaba Khamis, ni sam bazan taɓa iya aikata haka ba, insha Allah har duniya ta tashi bazan taɓa yarda nakusanci zina ba, kasan girman zunubin wanda ya aikata zina kuwa Khamis?  hmmm nikam dai ba ruwana, iskancina a iyaka waya ya tsaya kamar yanda ka faɗa da farko, amma taɓa jikin wata mace, wanda ba muharamma ta ba gaskiya bazan iya ba."      Hararansa Khamis yayi tare da cewa.  "Shiyasa nace bazaka taɓa wayewa ba, yanzu mene amfanin kallon BF matuƙar bazakanemi inda zaka gusar da sha'awan ka ba? hmmm nidai wallahi shanawa ma yanzu na fara ehe."      Murmushi kawai Hayatuddeen yayi tare da playing vedio'n sa ya cigaba da kallo, yana mejin wani irin abu acikin jikinsa, sau dayawa yakanji kamar ya daina kallo, amma kuma zama da Khamis yasa kallon BF ya zame masa tamkar wani kallon film, yayi sabo da ganin BF sosai, saboda haka koda yace zai daina sai yaji ya kasa, duk da cewa yasan kallon BF din ba kyau, amma sosai idan yana kallo yakejin kansa cikin wani irin shauƙi, saboda  yanajin cewa shima yanzu yazama saurayi shekara 20 da yake dasu, sunsa yanajin kansa kaman ɗan 30 years. Shida kansa yasan da taraiyar sa da su Imran tafi mishi daɗi da al'khairi to abin ta kaicin Imran F.C.E yake Sulaiman kuma da Isma'il Kashere University suke. Zakariyya kuma da yake nan cikin G.S.U ɗin sai kuma ya kasance Department ɗinsu ba ɗayaba, tofa wannan dalilin ne ya rabashi da tsoffin abokansa a makaranta ya haɗashi da wannan ɗan banzan khamis ɗin mai ƙafafu kamar faskaren wawa. Wannan yana ɗaya daga cikin illar abokai, dole iyaye mu lura da abokan yaranmu muddin sun fara tasawa. Zakiyi shekara 14 kina bawa ɗanki/ƴarki tarbiya mai inƙanci to. Tofa daga shekara 15 zuwa 18 akai ashirin zaki fara yaƙi da gasa da abokanshi da zasu fara bashi tasu tarbiyar da in kinyi sakaci da addu'a dasa ido cikin awa ɗaya zasu kore taki tarbiyar nan su ɗaura tasu, shike nan sunyi nasara a kanki sun cuci rayuwar yaronki damake kanki, hattara garemu iyaye mu kula...! Tashi tsaye Khamis yayi tare da cewa.    "Saika tayi ae, kazauna nan a haka kada ka nemi ƙarin wayewa akan wanda kake dashi, ni kaga ma tafiyata, saboda yau ƙarfe 7 dai-dai muna da wani show me zafi a night club, nasan ma idan nace kazo ba zuwa zakayi ba."                   Kai Hayatuddeen ya jinjina tare da cewa.        "Saimun haɗe gobe, danni ma nasan driver ya kusa zuwa ɗauka na,  aje night club lafiya amman banda ni kam, bazanci amanar hamma da Ummynmu ba."        Dukan wasa Khamis ya kai masa, sannan ya juya ya fice daga cikin class ɗin.                  Bawani jimawa shima Hayatuddeen ɗin, sule driver yazo ya ɗaukeshi.                            Ƙarfe takwas na dare dai-dai  yadawo daga masallaci, kaitsaye part ɗinsa ya wuce, kasancewar akwai wani aikin sirri wanda zai gabatar, domin ansashi binciken wani riƙaƙƙen ɗan fashi, wanda ya addabi mutane, sannan kuma har zuwa yau ankasa gano inda yake, saboda hakane ma aka danƙawa Saifuddeen ɗin ragamar case ɗin ahanunnsa, kasancewar sun san ya ƙware wajen iya computer, da computer kaɗai zai iya gano musu inda mutumin yake.           Yana  shiga ɗaki kayan jikinsa ya soma ragewa, inda ya zauna daga shi sai 3 guater da kuma farar singlet, laptop ɗinsa ya jawo tare da sanyata  gaba, nan ya maida gaba ɗaya hankalinsa ga aikin da yakeyi.              Da misalin ƙarfe 9 kuwa Ameena tashigo cikin ɗakin.    ganin cewa yana gudanar da aiki me mahimmanci,  yasa batayi ƙoƙarin damunsa ba, kan gado kawai ta ɗale tare da kwanciya, sama-sama taɗan latsa wayarta daga haka bacci ya ɗauketa, ko data'n ta dake akunne bata kashe ba.     Shikuwa Saifuddeen har wajen 12 na dare yakai yana aikin bincike, cikin sa'a kuwa yagama haɗa duk wani information da yake so, dan kuwa ya gano inda mutumin yake, saida ya turawa ogansu komai kafun yake rufe laptop  ɗinsa, nan ya ɗauro alwala sannan yazo ya kwanta, ganinta haka bata rufe jikinta ba, yasashi rufa mata blanket, tare da gyara mata konciyarta, cikin mintuna kaɗan bacci ya ɗauke sa.       Washegari kuwa ya tashi da ayyuka masu yawa akansa,  hakan yasa tunda ya fita daga gidan bai dawo ba sai wajajen 3pm,  nan ma dai part ɗin Ummi ya zauna.   Koda dare yayi ya tafi zuwa ɓangaren su, nan yasamu Ameena har tayi bacci, yaji daɗin hakan kuwa, don dama baiso ya isketa idanunta biyu, gudun kada ta ce zata ƙara neman wani abu daga garesa.               Aikinsa ya ɗan taɓa kafun bacci ya ɗaukesa.        Yauɗin ma dai baitashi da niyan zaman gidan ba, dan yanzu aikin nasa yaɗau zafi wani abun dole sai ya fita da kansa yaje ofishin sirri na DSS.   Cikin nutsuwa yagama kimtsa wa, cikin wani lallausan yadi me kyau da tsada, yayi kyau matuƙa, Ameena dake tsaye tana kallonsa ne tasaki murmushi, tare da ƙarasowa kusa dashi,ido ya ɗan zuba mata ganin ta sunkuyo kanshi a hankali ta dai-daita fuskarsa da nata, batare da yayi  aune ba sai kawai jin bakinta yayi, acikin nasa tanayi masa tsosan sweet,  sam bai hanata ba saboda haƙƙin tane, saidai kuma baiwani biye mata ba, cikin mayen soyayyarsa ta ɗago idanunta ta kallesa, kallo ɗaya yayi mata yaɗan ɗauke kansa, murmushin yasakar mata tare da shafa gefen fuskarta, cikin body language ɗinsa yayi mata alama kan cewa. "Saiya dawo." Fatan al'khairi tayi masa, yana fita tafaɗa kan gado, tare da sakin ajiyar zuciya.        Shikuwa  Saifuddeen saida ya biya ta wajen Umminsa kafun ya fito, inda sule driver yayi driving ɗinsa suka fice daga cikin gidan. Ameena kuwa yau a ɓangaren Ummi ta wuni, ba ita ta koma sashinsu ba sai da magrib ta gabato.       Tanayin sallah kuwa ta ɗauki tsumin ta ta sha, tare da turara jikinta da turaren ƙamshi. Nan dai ta kimtsa kanta tsab, dan tana matuƙar begen mijinta, kwana uku kacal amma tayi mugun missing lallausan jikinsa.      Duk da cewa ya jima da dawowa amma bai shigo gidan ba saida  yayi sallan Isha, ɓangaren Ummi yaje suka ɗan taɓa hira, kafun ya komawa part ɗin nasu.         Yana shiga ɗakinsa ya iske Ameena zaune akan gado, tasha ado cikin sleeping dress masu kalar pink.                 Yau ita da kanta ta haɗa masa ruwan wanka.  Koda ya fito daga wankan, amsan towel ɗin hannunsa tayi, nan tashiga goge masa ɗan danshin ruwan dake jikinsa, haka dai yaɗan kimtsa inda ya hau kan gado ya kwanta. Itama Ameenan kwanciya tayi akan gadon, tare da  zagayowa ya zama suna fuskantar juna,     ɗan ranƙwafowa tayi tare da kamo hannunsa ta ɗaura akan waist ɗinta,   bakinta ta ɗaura akan nasa,  inda ta kamo laɓɓansa tana sucking,  lumshe idanunsa yayi cikin ransa yace.   "Oh ni Saifuddeen naga takaina, nadawo kaman wani alawa, ko yaushe tana cikin tsostsotseni ita ko gajiya ma batayi ne."      Ameena kuwa gaba ɗaya ta fara manta inda take, sosai take romancing ɗinsa,  gane abun da take nufi yasashi, kasa hanata abun da takeso, saboda haƙƙinta ne, idan ya hanata sai Allah ya tambayesa.                     Kamar dai wancan daren haka awannan daren ma Ameena ta more Saifuddeen, Ido ya lumshe dai-dai lokacin data zauna kan cinyoyinshi suna fuskantar juna, Zaleeha yake jida gani a cikin jikinshi da zuciyarshi, shiyasa a take lafiyarshi ta harba ya miƙe ƙam yana ta harbawa da cika, Ajiyan zuciya ya sauƙe da ƙarfi jin ta haɗe kanta dashi, yana mai mmkin duk abinda fa  Ameena zata mishi baya tashi har sai dai in ya tuno Zaleeha ya kawota cikin ransa, Haka nan yake jin tausayin Zaleeha dan wallahi Allah yasan karonta dashi bazai mata ta daɗiba, ya guturta kashe bakin tsiwar nan a dare ɗaya, yanaji a jikinsa tabbas Zaleeha matarsace zata dawo da ƙafafunta zai kuma yi maganinta yana dai-dai ƙugunta, a haka dai yana cikin tunanin Ameena tayi ta bidirinta a jikinshi, ido ya ɗan lumshe sai da aka ɗan zo bakin boda ne, sai ya jawota jikinshi ya ruggumeta da ƙarfi tare da sauƙe tagwayen numfarfashi. Dan gane da gajiyar jiki kuwa, sai ma abun daya ƙaru, don kusan yau zaice yamafi ranan jin gajiya, sam bayason wahala, bazaice Ameena bata gamsar dashi ba, sannan bazaice bayajin daɗin kasancewa da ita ba, saidai ajikinsa yanajin tabbas akwai wani  babban gurbi wanda bata iya cikewa, hakanan yakeji kamar akwai wani abun da ta rasa baijin irin gamsuwar da yake buƙata ba, hakan kuma baya rasa nasaba da bata iya jure tsawon lokacin da yake buƙata, yana buƙatar gamsuwa ta sosai da sosai ita kuwa Amina macece dole tanada rauni.          Wanka yayi sannan ya dawo ya kwanta, ajiyar zuciya yaketa sauƙewa dan yagaji sosai, itama Ameenan kwanciya tayi bayan tayi wanka, haka takejin ranta ƙal, bata da wani sauran damuwa. Hannunshi ya ɗan sa a hankali ya s....! sbpeny. Shafa gefen fuskarta, yayi har zuwa wuyanta, ido ta zubawa jajayen laɓɓansa da bata gajiya da tsotsansu. Shi kuwa janye hannunshi yayi a hankali kana gyara kwanciyarsa. Washegari kuwa gidan nasu ya karɓi baƙoncin Adda Maryam da kuma Ya Ameenu, dan dama Ya Ameenun turawa Saifuddeen ɗin saƙo dakansa yasanar masa da zuwansu. Aɓangaren Ummi Maryam ɗin ta sauƙa, cikin girmamawa kuwa suka gaisa da Ummi, nan taƙara basu haƙuri akan abun daya faru, tare da yi wa Ummin murnar ƙarin auren Saifuddeen. Hayatuddeen dakansa ya je ɓangaren Ameena inda yace tazo su gaisa da Adda'n Zaleeha, wato Adda Maryam ɗin, jin haka yasa Ameena tasanya hija binta, nan ta nufo ɓangaren Ummi'n. Cikin girmamawa suka gaisa da Ameena', sosai Adda Maryam tasaki jikinta suka sha hira da Ameena'n, hakan kuwa yasa Ameena taji daɗi sosai, take taji ƙaunar Adda Maryam ɗin ya cika zuciyarta. Hira sosai suka sha, sai wajajen Sallan la'asar Ya Ameenu yazo ya ɗauki Adda Maryam ɗin suka koma gida, turarukan wuta masu ƙamshi Ummi ta haɗawa Adda Maryam ɗin, nan tayi ta mata godiya, saboda Maryam macece da bata rena kyauta, komin ƙanƙantan abu idan kabata zata nuna maka farin ciki kana kuma zatayi maka godiya sosai. Bayan zuwan Adda Maryam da kwana huɗu ne. Saifuddeen ya turawa Ameena saƙo kan cewar tashirya yanaso zasu fita. Koda Ameena taga text message ɗin sosai zuciyarta yayi fari, wani irin daɗi taji, karon farko kenan da zata fita tare dashi. Wanka tayi inda ta kimtsa kanta cikin wani haɗaɗɗen lace mai laushi, babu laifi kuma tayi kyau. Koda zasu fita saida tabiya ɓangaren Ummi tayi mata sallama. Nan ta fito dan Saifuddeen ɗin yace tasameshi amota, tana ƙarasawa jikin motar tasa ta buɗe, nan tashiga ta zauna agidan baya, inda shima anan yake zaune, sosai yayi kyau cikin shigar shadda dake jikinsa, inda ya kafa hula mai kalan coffee akansa. Yayi kyau ƙwarai, hakanne yasa ta kasa ɗauke idanunta akansa, shikuwa kallo ɗaya ya mata tare da ɗan gutun murmushi kana ya kauda kanshi dan ya lura in yabar lips ɗinshi kusa da ita zata cafesu yanzu tayi sabon nata. Sule driver ne ke driving ɗin motar. Kaitsaye G.R.A gidan Baba Malam suka nufa. Agaban tanfatsetsen gate ɗin gidan sule driver ya tsaya tare da danna horn, cikin mintuna kaɗan aka wangale masa gate ɗin ya tura hancin motar ciki. Yana gama dai-dai-ta parking ɗin motar kuwa ya buɗe motar ya fito, zagayowa yayi inda ya buɗewa Saifuddeen ɗin murfin motar, tare da fito masa da kekensa. Cikin nutsuwa Saifuddeen ɗin ya hau kan keken, Ameena kuwa da kanta ta buɗe murfin motar ta fito, sosai tashiga ƙarewa yanayin gidan kallo, tabbas gidan yayi kyau, cikin ranta tace. "Zanso ganin wannan Zaleeha, idanuna sun zaƙu dason ganinta sosai, inason ganinta sosai a zahiri ido da ido kodan naga me take dashi wanda ya ɗauke hankalin Saifuddeen da dangishi ji wai an kwasota tazo ta gaida iyayen kishiyarta, wannan abu yayi masifar ci mata rai badan ma Ummy ta gaya mata gidansu Zaleeha zasuje ba ai ita a zatonda ko ɗan wani garding zasu je to koma meye haɗina da gidan". sosai tsarin gidan ya tabbatar mata da nagarta da darajar masu gidan. Zakariyya wanda ya fito daga ɓangaren Mamy ne ya hangosu, cikin sauri ya ƙaraso garesu, fuska ɗauke da tsananin farin ciki yace. "Oyoyo Hamma Saifuddeen, yau kaine agidan namu." murmushi Saifuddeen yayi tare da miƙawa Zakariyyan hannu, suka yi musabaha, cikin girmamawa Zakariyya ya dubi Ameena, fuska ɗauke da murmushi yace. "Sannu da zuwa Aunty Ameena." Murmushi Ameena tayi tare da cewa. "Yauwa Zakariyya ya makaranta?". tasan sunan Zakariyyan ne saboda, yawanci tana ganinsa wajen Hayatuddeen. Zakariyyan ne yayi musu jagora zuwa sashin Baba Malam, Suna tafene tana mai maganar zuciya. "Uhum kalli ƙaninta shi da yake na mijima yanada kyau irin kyan da ba'a gajiya da kallon fuskarsa inaga ita mace." sosai taji kishin Zaleeha ya daki ranta tana masifar son Saifuddeen shiyasa kuma take masifar kishinsa, ya zatayi da ranta randa zataga Saifuddeen yashiga ɗaki ɗaya da wata mace sun rufe ƙofa ina zata sa ranta?." A haka tana zancen zuci suka isa cikin gidan kasancewar Mamyn ma bata sashinta tana nan wajen Baba Malam ɗin. Koda suka shiga da matuƙar farin ciki Baba Malam ya tarbesu, cikin girmamawa haɗi da mutuntawa suka gaisa, yaji daɗin ganinsu ƙwarai, nan Mamy ta cika musu gabansu da kayan ciye ciye, itama taji daɗin ganinsu hakanan, saidai kuma ganinsu haka yasa taji sha'awan inama ace da Zaleeha ce, tabbas tasan da zuciyar Baba Malam sai yafi haka sanyi. Cikin body language Saifuddeen suka sha hira shida Baba Malam, sosai Baba Malam yayi musu nasiha mai shiga jiki, Mamy kuwa kayayyakin humra ta haɗawa Ameenan ta bata, sosai kuwa Ameenta taji daɗi, tabbas taga kirkin mutanen hakan nema yasa ta ɗanji zafin kishinta ya ɗan ragu akan ƴarsu dan ita a zatonta Mamy ce maman Zaleeha. Nan dai sukayi musu sallama, inda har bakin motarsu Mamy da Baba Malam ɗin suka rakasu. Kaitsaye gida suka dawo, inda Saifuddeen yayi masauƙi a falon Ummi. Washegari yau ya kamana monday sannan kuma yaune Ameena zata fara zuwa aiki nan Federal Medical Center wato (F.M.C) Dan angama yi mata komai, inda kuwa suka amsheta batare da wani matsala ba, saboda takardunta masu kyaune. Kamar kullum yau ma saida taje ta gaishe da Ummi, kasancewar babu wadataccen time yasa sama-sama taɗan taya Raliya aiki, dan kuwa ƙarfe 7:30 ne dai-dai lokacin zuwa wajen aikin nata, suna kammalawa ta koma ɗakinta, nan ta kimtsa kanta cikin kayansu na nurse, wato riga da wando farare da kuma ɗan madaidaicin hijab, kayan suna mata kyau ba laifi, sannan kuma basa fidda tsiraicin ta, don basu kama jikinta ba ko kaɗan. Tana gama kammala shirin nata, taɗauki ƴar handbag ɗinta, kai tsaye ɗakin Saifuddeen ta nufa, nan ta iskesa yana aiki ya saka laptop ɗinsa gaba, zama tayi anan kusa dashi, ɗago kansa yayi ya kalleta, murmushi ta sakarmasa, kana ta miƙe, ƙarasowa gabansa tayi, ɗan ranƙwafowa tayi tare da manna masa kiss akan laɓɓansa, cikin soyayya tace. "Kakulamin da kanka saina dawo." tana faɗin haka ta juya tana me ɗaga masa hannu, murmushi yasakar mata tare da ɗaga mata hannu, tana ficewa kuwa ya sauƙe ajiyar zuciya, cikin ransa yace. "Alhamdulillah, aini naji daɗin fara zuwa aikin naki ma, nasan ko bakomai zakina dawowa agajiye, daganan kuma zan huta da jarabanki, da kuma wannan tsotse tsotsen naki Allah kiyaye hanya hajia rabo tawo." Murmushi yayi tuno wasu abubuwan da Ameena ke mishi shida kanshi yasan Ameena ta sonshi irin zazzafan so ɗin nan shiyasa yake ƙoƙarin ganin ta samu nitsuwa dashi. Kansa ya maida ga laptop ɗinsa inda yaci gaba da aikinsa cikin kwanciyar hankali. Sai dai can cikin ransa yana jin ɓaƙin cikin duk fa abin take mishi ta taɓa yiwa wani ƙaton, A saman lips ɗinsa yace. "Waya sanima iya sau dubu nawa ya kusanceta wata ƙil shinema ya maida jarabebbiya yana ɗaya daga abinda yake sashi kasa sakin jiki da ita. Ameena kuwa Sule driver ne yakaita wajen aikin nasu, cikin ɗaya daga cikin motar Saifuddeen wanda baiwani cika hawanta sosai ba. *** *** Alhamduillahi akwana atashi asaran me rai, rayuwa tana ta tafiya kwanaki sun shuɗe i zuwa makonni makkonni su juya i zuwa watanni. Yau Ameena da Saifuddeen suke cika wata biyu da sati biyu cif-cif da aure, harzuwa yau kuwa Saifuddeen bai taɓa jin son Ameena acikin zuciyarsa ba, sai-dai kuma yana iyaka ƙoƙarinsa wajen ganin ya sauƙe haƙƙinta dake kansa, sannan kuma yanajin daɗin aikin da yakeyi, ga kasuwancinsa na tafiya. ɓangaren Ameena kuwa sosai rayuwa ta miƙa mata, domin Saifuddeen bai rageta da komaiba duk abinda takeso zai mata in ta buƙaci nitsuwa dashi kuwa yana iya ƙoƙarin shi, kana tana zuwa aikinta cikin kwanciyar hankali, idan ta dawo daga wajen aiki kuwa haka Ummi takesa Hayatuddeen yakawo mata abinci har sashinta, sosai takejin daɗin zama da Ummi da kuma su Raliya, wanda ayanzu takejin cewa sun zame mata ƴan uwa, haka kuma aduk lokacin da take da buƙatar Saifuddeen baya hanata sannan kuma aduk ƙarshen sati yakan tambayanta ko tana da wani buƙata na kuɗi? koda tace batada shi kuwa, yakan bata wasu kuɗi yace ta riƙe watarana ko zatayi amfani dashi. Sai dai a cikin ƴan kwanakin da suka wuce gaba ɗaya takan kasa ganewa kanta, hakanan take fama da matsanancin ciwon kai, sannan kuma bata wani jin daɗi, sai-dai kuma abun baishiga jikinta ba, dan tanayin komanta batare da gajiyawa ba. Yaudai tunda ta fito wajen aiki takejin yanayin jiri naɗan ɗibanta, haka dai ta share, har zuwa kusan la'asar, jin abun na tsanantawa ne yasa tayi tunanin cewa kodai yunwa ne takeji, hakan yasa, batare da lokacin tashinsu yayi ba, ta ɗauki excuse, kaitsaye Napep ta tara ta nufo gida. Koda tashigo cikin gidan ɓangaren Ummi ta nufa, dan har wani ji take cikinta na murɗawa, hakan yasa ta al'laƙanta abun da cewa, yunwa ne kawai keson takurata. Afalo ta iske Ummi da Hayatuddeen wanda dawowansa daga makaranta kenan, jakarta ta ajiye, zama tayi akan sofa tare daɗan ƙaƙalo murmushi, cikin son daurewa yanayin da takejin kanta aciki tace. "Ummi sannu da gida." Cikin kulawa Ummi tace. "Yauwa Ameena har kuntaso daga wajen aikin?." Girgiza kai tayi tare da cewa. "A'a wallahi, kawai dai naɗanji yunwa na damuna ne shine nace bari na gudo gida." Murmushi Ummi tayi tare da faɗin. "Ayya sannu to, Raliya na kitchine bara nace ta zubo miki abinci kici ko". Ummi taƙare maganar cikin kulawa. Akunyace Ameenan ta miƙe tare da cewa. "Bari naje na zubo da kaina kawai Ummi kada asata wahala." Nan tamiƙe ta wuce kitchine ɗin. Ummy kuwa cewa tayi. "To inaga fa gwara Sule ya rinƙa kai miki abinci bana son wuni da yunwa da kikeyin nan." Tana ƙoƙarin shiga kitchin ɗinne tace. "Ba komai fa Ummy in naji yunwa ina sayan abu inci kinga wani Lokacin kuma inama tafiya da abinda zan ci." Kai kawai Ummy ta jinjina, ita kuwa Ameena. Raliya ta iske tsaye tana ta ƙoƙarin haɗawa Saifuddeen pepper chicken soup. Cikin kulawa Ameena tace. "Sannu agogo sarkin aiki." Murmushi Raliya tayi tare da faɗin. "Ke kuma likita bokan turai ba." Dariya sukayi su dukansu, nan Ameena ta buɗe food flask ɗin da aka zuba haɗaɗɗiyar fried rice aciki, plate ta ɗauka inda ta ɗebi kaɗan, coslow ta zuba asaman shinkafan sannan ta buɗe wata ƴar kula wanda ke ɗauke da liver sauce, kaɗan ta zuba akan abincin, sannan ta sanya spoon tundaga cikin kitchine ɗin tasoma ci. Dubanta Raliya tayi tare da sakin murmushi, har acikin ranta tana ƙaunar Ameenan badan komai ba kuwa saidan ƙaunar Saifuddeen da Ameenan keyi. Saifuddeen kuwa shigowarsa cikin falon kenan, yana riƙe da kwalin holandia milk inda yake sipping da kaɗan kaɗan. Dai-dai lokacin Ameena ta fito daga cikin kitchine ɗin, hannunta riƙe da plate ɗin abinci. Ɗan jim tayi tare da lumshe idanunta, lokaci guda taga wani duhu naneman mamaye ganinta, taku ɗaya zuwa biyu tayi, taji gaba ɗaya jikinta ya saki wani irin jiri mai ƙarfi ya kwasheta, nan tatafi luuuuu tafaɗa kan kujera, take kuwa plate ɗin hannunta ya faɗi, abincin ya tarwatse acikin falon. Arazane su Ummi da Hayatuddeen sukayo kanta, cikin tsananin damuwa Ummi tace. "Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un, Ameena! Ameena lafiya kuwa?." aruɗe Ummi tayi maganan tana me jijjiga Ameena'n, Saifuddeen ne ya tuƙa wheelchair ɗinsa inda ya ƙaraso cikin sauri, hannunsa yakai yaɗan taɓa fuskar Ameena'n, tare da ɗan bubbuga kumatunta. Ahankali taɗan buɗe idanunta wanda sukayi luhu-luhu dasu, dishi-dishi haka take ganinsu. Hannunta ya kamo ya riƙe acikin nasa, cikin kulawa ya ɗaura hannunsa akan goshinta, jin zafi ajikinta yasa shi ɗago kansa ya kalli Ummi. Jin jina kai Ummi tayi tare da cewa. "Hayatuddeen miƙomin wayata naƙira Dr Adnan." Cikin sauri kuwa Hayaruddeen yamiƙo mata wayan nata. Dialing numbern Dr Adnan ɗin Ummi tayi, bugu biyu ya ɗauka, nan ta shaida masa abun dake faruwa, cikin sauri kuwa yace. "To Ummy ganinan zuwa." Anutse Saifuddeen ya gyarawa Ameenan kwanciyarta akan kujera, inda har yanzu yana riƙe da hannunta acikin nasa. Hakanne yasa Ummi taji wani irin sanyi acikin ranta, saboda dama burinta ne taga Saifuddeen ɗin na kulawa da Ameena. Cikin mintuna ƙalilan Dr Adnan da ya iso, har zuwa lokacin kuwa Ameena dishi-dishin take gani a idanunta. Jininta Dr Adnan ya ɗiba, sannan yace zaije yayi checking ɗin jinin nata, yana dawowa, amma kafunnan asama mata wani abu taci. Ummi da kanta tahaɗawa Ameenan maltina da madara, nan ta ɗan ɗagota cikin kulawa ta bata tasha, tana gama sha kuwa ta koma ta kwanta, gefenta Saifuddeen ya koma, nan dai sukayi jigum suna jiran dawowan Dr Adnan. Inda duk bayan minti ɗaya sai Ummi tayiwa Ameenan sannu. Turo ƙofar falon Dr Adnan yayi ya shigo, fuskarsa ƙunshe take da zallan farinciki marar misaltuwa. Zama yayi akan kujera tare da duban Ummi, murmushi yayi inda ya kuma duban Saifuddeen, cikin farin ciki ya tashi ya rungume Saifuddeen ɗin, abun daya basu mamaki kenan. Ɗan janye jikinsa yayi tare da kamo hannun Saifuddeen ɗin ya riƙe, cikin yanayin farin ciki yace. "Congratulation My brother, tabbas ƙarfin ikon Allah ya wuce misali Alhamdulillah yau dai ɗaya daga cikin tabbacin da Dr Acash ya bamu ya tabbata saura na biyu, domin da yardan Allah ka kusa zama Baba, dan kuwa Ameena na ɗauke da ciki har na tsawon wata biyu!!" Cikin tsananin mamaki Saifuddeen dasu Ummi ke kallon Dr Adnan. Kai ya gyaɗawa Ummy tare da ce mata, "Eh Ummy matar Saifuddeen nada shigar ciki har na tsawon wata biyu." Cikin wani irin matsanancin farin ciki Ummi tace. "Alhamdulillah Allah abun godiya, Alhamdulillah, tsarki ya tabbata ga Allah maɗaukakin sarki, tabbas kaine me kowa me komai, me kumayi alokacin da yaso, sannan ya hana alokacin da yaso!". Tuni har ƙwallan farin ciki sun cika idanun Ummi. Shikuwa Saifuddeen lumshe idanunsa yayi yana murmushi mai ɗauke da zallan farin ciki. Hayatuddeen kuwa wani irin tsalle ya buga, tare da faɗawa jikin Raliya cikim matsanancin farin ciki yace. "Wayyo Allah na daɗi kasheni zanga ɗan Hammana nima." Raliyanma da matsanancin farin ciki yasa hawaye suka gangaro daga cikin idanunta, ta rungume Hayatuddeen ɗin, duk da cewa ɗazu suka gama faɗa dashi, amma yanzu farin cikin da suke ciki ya goge wannna faɗan. Ameena kuwa jin abun da Dr Adnan yafaɗa yasa ta ɓoye kanta cikin hijabi, dan wani irin kunyan Ummi ne ya kamata, cikin zuciyarta kuwa wani irin farin ciki ne wanda bata taɓajin irinsa ba ashe zatonta gsky ne cikine da ita. Tashi Ummi tayi inda tazo ta rungume Ameena'n, cikin matsanancin farin ciki tace. "Tabbas aurenki da Saifuddeen yazame mana al'khairi agremu Ameena, Allah yayi miki al'barka ya kuma sauƙeki lafiya." Akunyace Ameena taɗanyi murmushi tare da sadda kanta ƙasa. Raliya kuwa sakin Hayatuddeen tayi, tare da zagayowa ta rungume Ameena'n, cikin farin ciki tace. "Allah ya sauƙeki lafiya Auntyna." Asanyaye Ameena ta rungumeta tare da faɗin "Ameen." Murmushi Dr Adnan ketayi, yayinda Ummi kuwa bakinta ya kasa rufuwa. Ashe zataga jinin Saifuddeen ɗinta aduniya? Ta godewa Allah da cewar nakasan sa bata shafi lafiyarsa ba. Saifuddeen ma murmushi yake ta saki, sosai yaji wani irin farin ciki aransa, ashe shima zai zamanto uba, cikin ransa yake ta yiwa Allah godiya, da wannan kyautar daya basa. Nan Ahmad ya shigo ya iske labari me matuƙar daɗi, cikin farin ciki kuwa ya rungume Saifuddeen yana me tayasa murna. Ummi ce tace da Raliya ta taimakawa Ameena'n ta yi wanka sannan ta kwanta ta huta. Hakan kuwa akayi Raliya ne ta riƙeta suka je har part ɗinsu, sannan ita ta haɗa mata ruwan wanka, tananan har Ameenan ta fito daga wanka, nan ta kimtsa kanta, inda ta haye gado ta kwanta, sai alokacin Ameena tafita don bata waje ta huta. Can ɓangaren Ummi kuwa Dr Adnan ne ya haɗa kayan aikinsa inda ya musu sallama ya koma office. Nan Saifuddeen ma ya fice daga falon. Ummi kuwa waya ta ciro inda ta dannawa numbern Adda Rahama ƙira, koda ta sanar da Adda Rahama maganan cikin Ameena'n, baƙaramin farin ciki tayi ba, har hawaye saida ta zubar. Nan tace tananan zuwa da yamma. Ummi na gama waya da Adda Rahama taƙirayi Bappa Ali ta faɗa masa, baƙaramin farin ciki kuwa Bappa Ali yayi ba, sosai yaji daɗin maganan. Ahankali ya tura ƙofar ɗakinta ya shiga ɗakinda tun da tazo gidan bai taɓa shigaba sai yau kuma yanzu, kwance take akan gado, inda ta lumshe idanunta, dan bacci ne keson ɗaukarta. Ƙarasowa cikin ɗakin yayi, inda ya nufo inda take. Jin motsinsa yasa ahankali ta ɗan buɗe idanunta, ganinsa yasa ta sakin murmushi, kusa da ita ya ƙaraso, ahankali yakai hannunta inda ya shafi kanta, cikin kulawa fuska ɗauke da murmushi ya jinjina mata kai tare da buɗe mata hannunshi, alamun tazo yaji ɗumin Baby'nshi murmushi ta kuma sakar masa tare da tashi zaune ta faɗa jikinsa, yau yana cikin farin ciki hakan ne yasa yayi hugging ɗinta, haɗe fuskarsu waje ɗaya tayi nan ta haɗe bakinsu, yau kam biye mata yayi, inda ya soma sucking lips ɗinta tare dasa hannunshi yana ɗan shafa cikinta. Daga nan kuma ta shiga gwada masa salon romance ɗinta. Sosai yau ya biye mata, hakanne yasa daɗin da taji yau dabanne, sannan aɓangarensa shima babu laifi. Da Yamma kuwa saiga Adda Rahama tazo, rungume Saifuddeen ɗin tayi tana mejin matsanamcin farin ciki, haka dai ta zauna har kusan magriba sannan ta-tafi. Acikin dangi kuwa kowa yaji labarin samun cikin Ameena sai yayi murna sosai ƴan uwa da abokanshi kabsun cika da farin ciki. Haka dai Ameena keta renon cikin jikinta kulawa take samu sosai da sosai daga wajen gaba ɗaya mutanen gidan, aɓangaren Saifuddeen ma yanzu kulawa na musamman yake bata, duk da cewa bawai yana wani damuwa da ita bane, amma yana kulawa da ita yanda ya kamata, sannan kuma cikin nata ma ba irin me laulayi ɗinnan bane, tana zuwa wajen aikinta, sannan kuma bata yarda ta gaza wa Saifuddeen takowani ɓangare ba, naci da jaraba kuwa sai abunda ya ƙaru, wani lokaci Saifuddeen idan yaga abun nata yayi yawa, guduwa yake sashin Ummi, bazai dawo ba kuwa sai ya tabbatar da cewa tayi bacci in gari ya waye taita fushinta yaita mata dariya yace zata lalata shi daga nan ta huce. Daga can gidansu Zaleeha kuwa suma murnan samun cikin Adda Maryam wanda yakeda wata ɗaya amman sabida yawan laulayinshi duk dangi sun gane, inda Ya Ameenu ke cike da farin ciki yana kulada matarsa sanyin idanunshi tamkar ransa . A hankali rayuwa ke juyawa watanni na tafiya tuni lokaci ya tafi. Numan. To zuwa yanzu dai Zaleeha tana jin zazamanta cikin garin Numan ɗin tamkar zama cikin kurku ne, domin hankalinta da nitsuwar kab basa jikinta, Kullum da begen iyayenta da ƴan uwanta take kwana, musaman Adda Maryam da suna magana da ita. Tana son komawa cikin ƴan uwanta tayiwa mahaifinta biyayya amman sai taji bazata iyaba. Sauƙin ta ɗaya tana ɗan samun nitsuwa cikin musulmai ƴan uwanta na rugar fulanin nan, do kuwa sosai sukayi sabo da Aisha, sannan kuma tana ɗebe mata kewa, Damuwar da take ciki ya baiyana a jikinta domin ta rame fuskarsa tayi fiyau sai dai daga ɓangaren kyawunta kuwa sai abun da yaci gaba, dan wani irin fresh skin ɗinta yayi, komai nata yayi normal, fatarta takara haske da sheƙi sakamakon kayan fruits da take ci da kuma yanayin ni'imar wurin, ita kanta tanajin sauyi ajikinta sosai ramar da tayi sai yasa hancinta ya ƙara baiyana, daga gefe kuwa kullum Aisha saita kawo mata abinci daga gidansu, Man Liman kuwa sosai yake janta a jiki in tazo ta sameshi a gida har sun ɗan saba. Yauma tana gidan su Aishan kasan cewar yau jumma'a ne bayan an sauƙo daga sallan jumma'an ne Man Liman ya iske su a tsakar gida ƙarƙashin bishiyar ceɗiya bisa dukkan alamu suma sallan sukayi. Cikin girmamawa suka haɗa baki wurin ce mishi. "Baffa sannu da dawowa." Murmushi yayi tare da miƙa musu ledan cefen da ke hannunshi tare da ce musu. "Yauwa sannunku tagwayen Baffa, kunyi sallanko?." Murmushi sukayi tare da gyaɗa mishi kai alamun eh. Man Liman dattijone me karamcin gaske, Har ya wuce sai kuma ya juyo ya kalli Zaleeha cikin fullanci yace. "Zaleehatu taho ki ɗan rubuta min wani abu, ke kuma Aisha wonke allon ƙarfen can ki miƙo min." Da sauri sukace to tare da miƙewa. A hankali Zaleeha ta shiga sashin baffa, kan taburma ta sameshi bisa farin buzunshi, gefenshi ya nuna mata tare da cewa. "Zauna nan wasiƙa zaki rubuta min zuwa ga sarkin numan, dan arnan garin sun samu a gaba." Cikin ganin girman dottijon tace to. Kana ya gaya mata duk abinda zata rubuta, ta rubuta mishi sannan ya kira wani ɗanshi ya kaiwa ɗan aikensu takardar. Har ta yunƙura zata tashi sai kuma ta koma ta zauna jin yace. "A a zauna Zaleehatu ban gama da keba." Murmushi tayi tare da cewa. "To". Gyara zamanshi yayi da kyau ya fuskanceta kana a hankali yace. "Zaleeha." jin yadda ya kirata yasa ta amsa a nitse, cikin kulawa yace. "In na tambayeki wani abu zaki gaya min gaskiya, kuma. Sannan ban miki shisshigi bako?." Da sauri ta jujjuya kanta tare da cewa. "In sha Allah zan gaya maka iya gskyar da na sani. Kuma ka tambayeni duk abin da kakeso dan ka isa katambayenin." Gyaran murya yayi tare da cewa. "Ke ƴar wanne garine?." Cikin nitsuwa tace. "Baffa ni bagombiyace." Kai ya gyaɗa cikin gamsuwa kana yace. "Me sunan mahaifinki?." a take idanunta suka cika da hawaye, murya na rawa tace. "Sunan babana Malam Bashir Sulaiman Dukku." Fuska cike da al'ajabi Man Liman yace. "ikon Allah Malam Bashiru ne mahaifinki?". cin mmki tace. "Baffa ka sanshi ne?". Kai ya jujjuya mata tare da cewa. "Eh to ba a zahiri na sanshiba ina dai jin azuzzukan shi, a radio, shiyasa bai zama ɓoyeyyen mutunba". Sai kuma ya gyara zama tare da zuba mata ido cikin kula yace. "To amman meyasaki daga tambayar sunashi kika fara zubda hawaye?, kuma meya kawoki nan cikin arna kika zauna Zaleehatu gaya min meyasa?." Hannunta tasa ta share hawayenta dake zuba tanajisa kamar matsayin Babanta mahaifi, cikin rawar murya ta bashi labarin duk abinda ya faru na sanadin gudowanta har kwana a gardin da takeyi bata ɓoye mishiba, ta ƙara da cewa. "Ina so in koma in je in bawa Baba malam haƙuri inyi mishi biyayya kan zaɓin dayamin amman ji nake bazan iyaba gani nake kamar in na koma zan mutu, nasan babana da ƴan uwana duk sunyi fushi dani". Nisawa yayi tare da gyara zama cikin kula yace. "Ae bazaki komaba Zaleehatu sabida kafa akayi anan matuƙar ba'a karya sihirin dake jikinki ba, haka bazaki iya yiwa mahaifinki biyayya, kuma dolene yasa kikayi ta gudun ɗakinki kina kwana cikin ciyawayi, domin an miki turen sihiri a ƙarƙashin gadonki, muddin ba'a karya sihirinba ɗakin zaike miki duhu zaina baki tsoro, kuma sihirin da akayi miki kin maganshi a mafarki sai in kin manta ne koda yake an rufe bakinma bazaki iya faɗiwa ko abinda kikeji ba, nima kaina yau tsawon wata uku kenan ina miki tofi cikin abincin da ake mishi shiyasa kika samu damar min bayani da izinin Allah." Shiru tayi cikin sanyi tace. "Baffa bana son mijin da aka haɗani dashi wanda nacema ya taimakenin nan shine nakeso." Murmushi yayi tare da cewa. "Kada ki damu, dukkan wani farin cikinki yana ƙarƙashin inuwar mijin da aka aura miki, na nemi al'farma kada ki sake cewa bakya son mijinki, kuma kada ki sake cewa akwai wanda kikeso bayanshi kisa a ranki shine ya taimakeki kuma dashi aka haɗaki, sai kici gaba da yiwa shi wancan ɗin addu'ar Allah ya azirtashi da mafificiyar al'janna Allah ya taimakeshi fiye da yadda ya taimakeki, Allah yasa soyayyarshi a zuciyar maƙiyanshi soyayya ta rinjaƴi ƙiyayyarsa a zuƙatan makusan tansa wlh in kin masa haka kin gama mishi komai sannan in kin yiwa mahaifinki biyayya zaki samu dukkan salama. Kiyi min wannan al'ƙawarin ni kuwa daga yawau zan fara baki addu'oi insha Allah zaki rabu da duk wani sihiri kuma zaki koma ɗakinki." Cikin jin sanyin da tunda ta gudo bataji ba tace. "To baffa in sha Allah zanyi ta mishi addu'a, ngd da taimako." Murmushi yayi kana a hankali yace. "Akwai wacce ke zuga mahaifiyarki, kuma ta asirce mahaifiyarki ne, da bata isa ta mata musuba,duk abinda tasata ko bata so sai tayi, amman ina karya abin jikinki itama abinda ke jikinta zai karye domin sunan ALLAH a duk inda take zaije ya sameta". Ganin tayi shiru ne ya sashi ɗan sahir tawa tare da cewa. "Ko Mamanki bata da yar uwa da suke tare". A hankali ta gyaɗa mishi kai tare da. "Tana dasu ɗaya musul mace ɗaya kuwa arniya ce". Murmushi yayi tare da cewa. "Ba Shatuba ai ita hasken addini na jikinta da zuciyarta, ita ɗayar dai domin ita burinta Mamanku daku yaranta duk kuyi ridda ku koma addininsu, to kuma ya rigada Allah ya tsareku kana mahaifinku a tsaye yake a kanku kun kuma samu cikakkiyar tarbiya." Ajiyan zuciya ya sauƙe tare da cewa. "Akwai kuma ƙawayenki cikinsu wacca kikafi so ɗin ita ke cin dunduniyarki, amman da zaran kin samu waraka da abinda akayi miki, keda kanki zakiji bakya son mu'amala da ita". Cikin mutuwan jiki tace. "Baffa ina son komawa gida". Murmushi yayi tare da cewa. "Zaki koma in sha Allah, yanzu zamu fara addu'oi tsawon sati biyu, daga randa zamu fara miki rubutu kina sha kuma duk mafarkin da kikayi ki sanarmin". Kai ta gyaɗa alamar to. Hahira sukayi sosai da Baffa'n, nan ta ƙara faiyace mishi irin yanayin da takejin kanta aciki, wanda sau da yawa tanajin son komawa gida aranta, amma saita najin kaman kafata agarin akayi, cikin son kwantar mata da hankali Baffa'n yace. "Insha Allah zai taimaka mata da wasu addu'o'i wanda zatana sha, da kuma wanda zata nayi." Nan dai tayi masa godiya sosai, dan ita kanta tanajin son komawa gida acikin ranta. Bayan wasu ƴan kwanaki ne kuma Baffan yasa, Aisha tayi ƙiranta, nan yabata wani ruwan addu'a yace tana sha tana shafawa jikinta. Sai kuma haɗin ayatushshifa da ganyen magarya guda bakwai, da kuma zam-zam, yace tana amfani dasu, ƙara jaddada mata yawan yin azkar da kuma zama da al'wala yayi, nan dai tayi masa godiya sosai. Cikin ikon Allah kuwa yau kwananta biyu da fara amfani da maganin, sannan kuma tanajin sauƙin wasu abubuwan. Gashi daren jiya ne Adda Maryam taƙirata awaya, sosai kuma tayi mata nasiha, mai ratsa jiki, wanda kalamanta suka ƙara sanyawa taji gaba ɗaya jikinta yayi sanyi. A gefen Solomon da matarsa kuwa zaman Zaleeha a gidansu yasa hasken addinin musulunci yana ratsa zuƙatansu, suna ganin daraja da kimar addinin musulunci fiye da nasu addinin har an kai matin da yanzu sun fara watsi da addininsu dan sai ayi lahadi uku basuje majami'arsuba, zuwa yanzu Zaleeha kuwa tana tallata musu addinin dayi musu tayi su shiga domin shine hanyar tsira, kana tana ƙyautata musu sosai da kuɗin dake hannunta irin kyautatawar da musulunci ya umarci musulmi yayiwa ahlul kitab dan da kyautata zasu ƙaunaci addinin su san addinine mai sauƙi da tausayawa, to zuwa yanzu dai Zaleeha na zaton musuluntar su Solomon da elizabet a ko wanne lokoci. Kwanci tashi babu wuya, inda yanzu cikin Ameena yakai wata bakwai, sosai kuma yayi girma, dan kuwa zuwa yanzu daƙyar ma take iya taka ƙafafunta, dan sun kumbura sosai, saikace me haihuwa yau ko gobe, wannan daliline yasa ta ɗauki hutu awajen aikinsu, Ummi ne ke bata kulawa sosai. Ɓangaren Adda Maryam ma kuwa yanzu cikinta nada wata shida itama, saidai girman cikin nata baikai na Ameena ba. Yau tunsafe da ta tashi takejin wani irin matsanancin ciwon mara, haka takejin bayanta ya riƙe ƙam, gashi ƙafarta ta sake kumburi, da ƙyar dai take iya takawa, haka ta lallaɓa ta nufi ɓangaren Ummi tana zuwa kuwa ta iskesu zaune afalo, zama tayi itama tana cije laɓɓanta, ganin haka yasa Ummi da kanta ta haɗa mata emptyn shayi me zafi ta bata tace tasha. Tana sha kuwa tariƙe bayanta da takejinsa kaman zai ɓalle, Ummi da Raliya ne sukayo kanta, abu kaman wasa fa saiga naƙuda ya tashiwa Ameena gadan gadan, nan Ummi ta ka mata, inda ita da Raliya suka sanyata amota, hankalinsa Saifuddeen a tashe ya shiga motar yana tsoron abinda zai sami ɗanshi tunda yasan cikin bai kai haihuwa ba. Ahmad ne yayi driving ɗinsu zuwa Medical center, suna zuwa kuwa abokan aikinta suka karɓeta hannu bibbiyu nan aka wuce da ita labour room. Jigum-jigum haka su Ummi sukayi suna mejiran sakamako, hankalin Ummi atashe yake sosai, musamman da likitotin suka tabbatar musu da cewa haihuwace Ameenan zatayi, ma'ana ɗan abakwaini zaizo. Da shigar da Ameena labour room ko 40 minute ba a rufa ba, wata nurse ta fito inda take sanar musu da cewa. "Ameenan ta haihu ta haifi ɗa namiji, kuma daga ita har yaron dukansu suna cikin ƙoshin lafiya." Wannan magana ita tasanya dariya ya wanzu akan fuskokin su Ummi, Saifuddeen kuwa hamdala yayi tare da ɗaga hannunsa sama ya godewa Allah. Nan Ummi tashiga ƙiran ƴan uwa da abokan arziki tana sanar musu, ana fito da Ameena zuwa ɗakin hutu kuwa, nurse ɗin tace zasu iya shiga. Suna shiga ɗakin wata nurse ta miƙowa Ummi yaron, hawayene suka cika idanun Ummi abayyane tace. "Alhamdulillah, masha Allah." Saboda tsananin kaman Saifuddeen ɗinta da ta hango akan fuskar yaron, gashi yaron kamar ba bakwaini ba, dan yana da girmansa, tsabar fari kuwa har saida yayi wani jaja-jaja. Miƙawa Saifuddeen tayi ya amshi yaron yana mejin tarin ƙaunarsa acikin ransa, rumgume yaron yayi aƙirjinsa yana murmushi, bayan yayi wa yaron huɗuba da ƙiran sallah acikin kunnensa. Nan dai Su Adda Rahama da Raliya suka amshi yaron suma suna yabawa da irin kyautar da Allah yayi musu. Kasancewar Ameena bata wani jigata ba, hakan yasa bayan ankimtsata aka basu sallama da ƙara bata shawarwarin yadda zata kula da ɗanta tunda ɗan bakwainine sun sallamesune sabida sanin ita ɗin sashin Doctors take, nan dai suka tattaro suka dawo gida. Kusan kullum ƴan barka sai sunzo, Mamy da Adda Maryam ma sunzo barka, Inna matar Baba Bello ma tazo yi musu barka. Ana sauran kwana uku suna Raihana ta diro garin na Gombe, da Aliyun ta takwaran bappa Alinsu (Affan) ɗinta kenan sosai itama tayi murna da ganin ɗan Hamma'nta. Ranan washe garin suna ne dangin Ameena suka zo, Aunty's ɗinta dama Sister's ɗinta duk sunzo daga Abuja wasu daga Jada. Ranan suna kuwa yaro yaci sunan MUHAMMAD BASHEER. wato takwaran Baba Malam kenan, inda za'ana ƙiran yaron sa sunan. (Adeel) wannan karamci da Saifuddeen yayiwa Baba Malam yasashi matuƙar jin daɗi, bama iya shi ba, harta ga ƴaƴansa sunji matuƙar daɗi, haka Baba Malam da Mamy suka cika akwati guda da kayan yaro masu kyau'n gaske. Nan dai akasha shagalin suna wanda yasamu hallaran mutane da yawa, dan dayawan danginsu na Dukku ma sunzo, ga kuma dangin Ameena. Adda Maryam ma tazo, duk da cewa cikinta na sata laulayi gashi dai yanzu har ya kai wata shida amman har yanzu yana sata laulayi. amma hakan baihanata zuwa ba. Sosai Saifuddeen yayi ɓarin naira ranan sunan, dan anci ansha, sannan an rarraba kyautuka gaduk wanda yazo. Aranan kuwa ya damƙawa Ameena makullin sabuwar motar daya saya mata, saboda tsabar daɗi Ameena har ƙwalla saida tayi. Shikuwa Saifuddeen yayi hakanne saboda sauƙe haƙƙinta, dan bai kyautuwa ace yasawa Zaleeha mota da kuɗinsa, amma ita Ameenan bai saya mata ba, duk da cewa Zaleehan tariga zuwa kafun ita, sannan kuma ma motar Amina tafi ta Zaleeha kyau da kuma tsada. Anyi taron suna an watse, inda Ummi dasu Adda Rahama suka nunawa Ameena gata sosai, dan kaya suka mata baɗan kaɗan ba, Hayatuddeen ma ba a barsa abaya ba, dan rigunan yaro har kala 6 ya saya masu kyaun gaske, Ameenan kuwa turamen vlisco ya saya mata guda biyu masu tsada, asusun da yakeyi musamman ya fasa dan yin shagalin sunan. Hatta Zakariyya ma saida ya sayawa ɗan Hamma Saifuddeen ɗin riguna masu kyau. Hakama Ya Ahmad da yaji labarin Baba malam akayiwa mai suna sosai ya goggojesu Babu wani ɗaya daga cikin abokan Saifuddeen kuwa dabai kawo nasa kayan ba, sosai sukayi bajinta. Abun saidai ace masha Allah. Haka rayuwa tatafi har Ameena tayi wata biyu da haihuwa, wanda yanzu ta gama wanka, sannan tana bawa ɗanta kulawa sosai yanda ya dace, idan kaga yaron kuwa bazaka taɓa cewa bakwaini bane, saidai in anfaɗa maka, dan yana da girman jiki. Sannan yarone me shiga rai sosai. Kasancewar ta cika wata biyu da haihuwa hakan yasa ta shirya tsab inda su Ummi da Saifuddeen suka cikata da abubuwan al'khairi, nan ta tafi Abuja, kwananta uku acan ta dawo, tana dawowa kuwa ta koma bakin aikinta, don dama hutun 2 month kawai suka bata. Acan Numan kuwa Abubuwa sunyiwa Zaleeha sauƙi sosai, inda ta kama addu'a sosai, ruwan addu'a kuwa kullum shi take sha, Alhamdulillah taji sauƙin abubuwa da yawa, dan yanzu begen gidane gaba ɗaya ya cika zuciyarta. Yau tun da safe ta shirya tatafi gidan su Aisha nan ta samu Baffa agida dan bai fita gona ba bayan sun gaisa ya bata rubutun da ya mata tasha, nanne yake tambayanta ko daga fara maganin nata zuwa yanzu ko taji sauyi ajikinta? Sosai kuwa tagaya masa irin sauyin da taji, Gyaran murya yayi tare da cewa. "Tunda kika fara shan rubutun nan nece miki duk mafarkin da kikayi ki gaya min shin har yau bakiyi mafarkin komai ba?." Da sauri ta kalleshi cikin al'ajabi tace. "Baffa jiya nayi mafarkin daya bani mmki dan na taɓa yin makamancinsa". Gyara zama yayi tare da fuskantarta da kyau yace. "Mafarkin me kikayi?". Gyara maya fita tayi tare cewa. "Nayi mafarkin, da'a cikin mafarkin naga wani ƙaton maciji baƙiƙƙirin ya fito daga ƙarƙashin gadona na gidan Saifuddeen, wanda acikin mafarkin ne kuma naga Baba Malam yana cikin ɗakin ni kuma ina ta waje bakin ƙofar shiga ɗakin ta gefe, naji Baba Malam na cemin, in dawo gida in dawo ɗakinna in zauna, yanzu babu komai babu wani abu wanda zai cutar da ni a ɗakin. Har yana ce min in matsa a baƙin ƙogar kada macicijin ya taɓa ni." Cikin sauri da fargaba Baffa yace. "Macijin yataɓaki?." kai ta jujjuya tare da cewa. "A a bai taɓani." ajiyan zuciya ya sauƙe tare da gyara zama. Ita kuwa Zaleeha cikin sanyi tace. "Na dai ga Macijin kuma na taɓa yin mafarkinshi, tun randa akaje akayi jeren kayana a gidan Saifuddeen nayi mafarkin wai ina kan gado sai macijin ya shigo ina ganinshi ƙato ya lume ƙarƙashi gadona. To randa aka kaini gidanma na sake yin mafarkin." Jinjina kai Baffa yayi bayan yagama jin kalaman nata cikin jin daɗi yace. "Alhamdulillah. babu komai sai al'khairi kuma Insha Allah duk wani asirin dake jikinki yanzu ya karye, babushi a jikinki sannan yadda kikaga macijin nan ya shiga ƙasan gadonki haka sihiri yayi ta ratsaki, kuma yanzu yadda kikaga macin ya fita daga ƙasan gadonki to sihirin ya bar jikinki da ɗakinki, kuma zan baki maganin tsarin jiki tayanda insha Allah Allah zaikareki da dukkan wani sharri zakiyi amfani dashi sau uku." Cikin wani irin begen gida da son komawa cikin ahlinta tace. "Baffa ina son komawa yau in dai zan samu mota". Cikin jin daɗi da gamsuwa da cewa ta samu waraka yace. "Kiyi haƙuri sai gobe, tabbas kam tafiyar ta karato, dan haka kiyi haƙuri yanzu zan baki mgnin tsari kiyi wonka dashi sau uku yanzu in kin koma sai kuma da yamma, sai kuma gobe da asuba ki ƙarashi." Don dole da kimar dottijon ta haƙura dan ji take tamkar ta zama tsunstsuwa tayi fiffige ta fire ta koma gida,ji yakeyi kamar ta rumtse idonta ta buɗe su ta ganta gaban Baba Malam ya mata duk hukuncin daya dace da ita ta nemi yafiyarshi da sanya al'barkanshi. Ae kuwa bata bar gidan ba saida ya haɗa mata magungunan tsari, wanda duk addu'o'i ne, nan yake ce mata. "Insha Allah takusa komawa gida." Tajima agidan nasu Aisha kafun take komawa gida. A ranar ne kuma Solomon da matarsa sukayi mata tambayar da ta bata mmki, suna tambayarta in mutun zai musulunta me da me zaiyi kuɗi kamar nawa zai kashe, wannan abu ya sata jin karsashi ta zauna tayi musu bayanin komai na sauƙin musulunci, sai suke ce mata to suna son musulunta to amman sai sun gayawa sarkin majami'arsu. Tace su gaya mata da dole sai sun gaya mishi , sai sukace ta bari nanda sati ɗaya zasu gaya mata. A safiyar ranar dai kuma A Gombe. Saifuddeen ne zaune akan wheelchair ɗinsa, yana riƙe da Adeel ɗan wata uku ya shiga na uɗu wanda ya ƙara girma yakuma yi wayo yayi kuɓul-kuɓul, wasa yakeyiwa yaron yana me shafa lallausan gashin kansa, wanda yayi shige da nasa, sosai yakejin ƙauna da son yaron acikin ransa. Ƙurawa yaron idanu yayi aransa.yana me cewa. "Badan ƙaddara ta kawo Hajia Ameena rabo ba, da yanzu wannan yaron ajikinki zai fito Zaleeha, amman ba damuwa in sha Allah kema naki yana jikina in Allah ya yarda ni dake sai mun samar da abu ɗaya ina ji a jikina kin kusa dawowa gareni, kin gama naki zaki dawo ki tadda nawa. Wai toms in kin dawo me zakice? Ina kikaje? Meyasaki tafiya?". Yayiwa kansa tambayar tare daɗan lumshe idanunsa, tabbas yayi kewar Zaleeha sosai musamman cikin kwanakin nan tana yawa faɗo mishi cikin rai, ya rasa dalili gashi yanzu sam ta daina hawa online kuma duk sabida yana mata mgna da number sa ta siirin nan dama tace mishi zata goge whatsapp gaba ɗaya kuma ta goge ɗin acewarta ita matar aurece. Ameena ne tafito daga cikin ɗaki cikin shirinta na zuwa wajen aiki, ƙarasowa wajen su tayi cike da ƙaunarsu, ranƙwafowa tayi inda ta mannawa Saifuddeen din kiss akan laɓɓansa, sannan ta ɗaga yaron zuwa kafaɗanta, cikin kulawa ta ce da Saifuddeen ɗin. "Saimun dawo" hannu ta ɗaga masa sannan ta fice, dan tayi late. Shikuwa Saifuddeen laptop dinsa ya ɗauka, inda ya shiga cikin file ɗin da yake aje hotunan Zaleeha, view ɗin wani hoton Zaleehan yayi yana kallo, sosai tayi kyau acikin hoton dimple ɗinta ya zubawa ido, dan tana sanye ne da doguwar rigar da ta amshi jikinta, yajima yana kallon hoton kafun ya rufe laptop ɗin ya nufi ɗaki. Ameena kuwa saida tabiya ta wajen Ummi tayi mata sallama kafun take wucewa wajen aikin. Federal medical center. Baba Malam ne da Ya Ameenu haɗe da Mamy, da kuma Ya Habu ke tsaye, sunyi jigum, matsanancin damuwane kwance biss fuskokinsu, sakamakon kawo Maryam haihuwa da sukayi, gashi kuma ance dole saidai ayi mata theatre. Wasu nurses biyu ne suka turo wani ɗan dogon gado da Maryam ɗin ke kwance akai, ansanya mata kayan theatre, dai-dai sunzo wucewa ta wajen su Baba Malam ɗinne, Maryam ta sanya hannunta ta kamo na Baba Malam, tare da cewa. "Baba Malam kazo mana kayi min addu'a kafin a shiga dani." da sauri Baba Malam ya dubeta cikin tausayawa yace. "To Maryam zan miki addu'a kinjiko ƴata mai sunan ƴar uwata insha Allah zaki haihu lafiya da yardan Allah." ganin nos ɗin zasu shiga da itane yasa ta kallesu cikin sanyin murya tace. "Dan Allah in mun shiga ku kirawo min Babana da mijina suzo akwa abinda zan ce musu kafin ayi aikin." yanayin nitsuwarta ne yasa sukace. "To". Suna shigar da ita ɗan falon da za'a ratsa a shiga ainhin ɗakin tiyatan. Nan suka tsaida gadon kana ɗaya nos ɗin ta fito ta kira su Baba Malam da Ya Ameenu. Suna shiga ta yunƙura ta tashi zaune cikin sanyi tasa hannunta da yayi sanyi ƙalau tamkar ƙanƙara ta riƙo hannun mahaifinta. Kai ta girgiza take kuma saiga hawaye sun silalo daga cikin idanunta, cikin muryarta dake fita da sanyi tace. "Baba Malam ka yafe mi ninaji ajikina cewa bazan tashi ba Baba, dan Allah kayafemin in akwai laifin da nayi maka." Da sauri Baba malam ya riƙe hannunta tare da cewa. "Ni kam bakiyi komai ba Maryam, koda ko kinyi min na yafe miki duniya da lahira, bare ni baki min komai ba face biyayya, ubangiji ya yassare miki rayuwar duniya data lahira." Hannu tasa ta share hawayenta murya na rawa tace. "Nagode Babana." Da ƙarfi zuciyar Baba Malam ta buga jin yadda ta kirashi, kama hannunta yayi da kyau jin tana cewa. "Sannan kuma ina neman wata al'farma a wurinka Babana". Zuciya a tsinke yace. "Wacce al'farmace Maryam gaya min". Lumshe idanunta tayi wasu zafafan hawaye suka kwaranyo mota, cikin sanyin murya tace. "Dan Allah ina son ka dawo da Mama dan Allah, ka kuma yafewa ƴar uwata Zaleeha, dan Allah Baba kayafe mana baki ɗayanmu Baba Malam ka yafewa Zaleeha dan kada rayuwa tayi mata muni bance kada kayi fushi ka nuna mata illar abinda tayiba, amman kada kuyi dogon fushi da ita, sannan in Mamana tazo kace mats na nemi yafiyarta, ta gafarta min". Sai kuma ta fara kuka murya na rawa taci gaba da cewa. "Baba malam Nasan duk inda Zaleeha take. Duk inda take a faɗin wannan duniyar in dai tana raye in taji rasuwata zata zo, dan Allah idan tazo kace mata na ajiye mata saƙo a cikin durowar gadona, kuma kada taje ita kaɗai in zata ɗauka taje ita da Mijinta Saifuddeen sannan kacewa. Ya Ahmad da Zakariyya kada suyi dogon fushi da Zaleeha su zame mata madadina." taƙare maganar tana dhessheƙan kuka, kai Baba Malam ya jijjiga lokaci ɗaya hawaye suka cika idanunsa, hannunta ya kama ƙam cikin matsanancin ƙaunar ƴartasa yace. "Insha Allah zaki tashi Maryam, za ayi miki aiki lafiya, kidaina faɗin irin waƴannan maganganun." Murmushi tayi tare da kamo hannun Ya Ameenu wanda tuni hawaye sun wanke masa fuska, cikin matsanancin ƙaunar mijin nata tace. "Inaji ajikina cewa zan barka Yayana, zantafi inda bazaka sake ganinka ba, kakulamin da Ayman ɗinmu kaji, sannan kayafemin duk wani abu danayi maka." Kuka Ya Ameenu ya fashe dashi tare da durƙushewa awajen, don bayajin zai iya cewa komai. Mamy ma kuka take, nan ita da Ya Habu suka kama hannun Maryam ɗin, murya asanyaye Mamy tace. "Ki daina faɗin haka Maryam zaki tashi da yardan Allah." Hannun Mamyn Maryam tasake riƙewa sosai, cikin muryan kuka tace. "Ku yafemin Mamy, idan Zaleeha ta dawo kice mata nace tabi mijinta sauda ƙafa tayi masa biyayya, danni kam bazan samu daman faɗa mata hakan da bakina ba. Ya Habu kaima kayafemin, sannan kada kuyi dogon fushi da Zaleeha." Kukane ya ƙwace wa Mamy, da Ya Habu, Baba malam ma hawaye yake sosai. Ganin haka yasa nurses ɗin suka tura keken sukayi ciki da Maryam ɗin, tana kallon Ya Ameenu shima yana kallonta haka aka shiga da ita ɗakin theatre'n, kuka sosai Ya Ameenu yasa kaman ƙaramin yaro, Baba Malam ne ya riƙesa yana rarrashinsa. Ameena kuwa koda taje asibitin aje Adeel tayi awajen wata ƙawarta mesuna Umaima, nan ta nufi theatre room dan ansanar da ita cewa, babban Dr ɗinsu na nemanta acan ɗin. Takusan kaiwa theatre room ɗinne tahango Baba Malam, Ya Ameenu, da kuma Ya Habu, sai Mamy suna tsaitsaye, cikin sauri taƙarasa garesu, ganin fuskokinsu ɗauke da matsanancin damuwa yasa jikinta yin sanyi asanyaye ta gaidasu, tare dayi musu tambayan halan ko wani suka kawo bashi da lafiya, dan taga idanunsu gaba ɗaya sunyi jajur. Hankalim Mamy amatuƙar tashe yake faɗa mata cewa. "Maryam ne suka kawota haihuwa, ankuma ce dole sai theatre za'ayi mata, yanzu haka ma anshiga da ita ɗakin theatre'n." Hankalin Ameena ne ya tashi sosai, take cikin sauri ta nufi ɗakin theatre'n. *(heart touching)* Sbpejy Su Baba Malam kuwa tsayuwa sukayi, gaba ɗaya jikinsu asanyaye y'ake, babu wanda yayi yunƙurin zama acikinsu, Mamy kuwa hawaye take ta sharewa, zuciyarta cike take da tausayin Maryam. Can cikin theater room kuwa, alluran nan dake gusar da hankali, likitotin sukayiwa Adda Maryam, Doctors kusan guda huɗu ne suka duƙufa akanta, cikin ƙwarewa kuwa suka soma yi mata aiki. Shiru ɗakin theater'n yayi bakajin motsin komai, sai na kayayyakin aikin da likitotin ke amfani dasu. Sosai aikin nasu ya ɗauko nisa, gefe kuwa Ameena ne da wata nurse wanda sune ke taimakawa wajen miƙawa doctors ɗin kayan aiki. Ahankali ƙwayar idanunta ke tsiyayar da wasu sassanyan hawaye, sosai kuma hawaye suka rinƙa kwaranyowa daga cikin idanunta, Ameena wanda gaba ɗaya hankalinta naga Maryam din ne, ganin idanun Maryam ɗin na zubda hawaye, yasa amatuƙar firgice ta matso kusa da ɗaya daga cikin doctors ɗin dake yi mata aiki'n, ɗan taɓasa tayi yana juyowa kuwa tayi masa nuni da fuskar Maryam, cikin yanayin tsoro haɗi da mamakin ikon Allah likitan yayiwa ƴan uwansa nuni da Maryam ɗin, wanda idanunta suke ta zubda hawaye, koda suma suka ga yanda Maryam ɗin take , sosai suka shiga shock, saboda sunsan sunyi mata alluran gusar da hankali masu ƙarfi, wanda baiyiwuwa ma ta farfaɗo koda nan da awa 2 ne, sai gashi abun mamaki ko mintuna 30 ba acika ba idanunta na zubda hawaye kamar dai kuka takeyi mamakin hakanne yakamasu ƙwarai, saboda koda jinin mutum nada ƙarfi, idan akayi masa wannan alluran yana tasiri sosai ajikinsa, ɗaya daga cikin doctors ɗinne ya sake haɗa wani alluran yayi mata, bayan ya mata alluran da kamar mintuna uku ne, suka ga idanunta sunyi lib sun dena ɗan motsawan da sukeyi saidai kuma har yanzu hawaye na fita daga cikin idanunta, yana bi ta cikin kunnenta, kana yana sauƙa akan matashin kanta. Sosai abun ya ɗaure musu kai, dan kuwa basu taɓa samun irin haka a cikin aikin su ba, nan dai suka maida hankalinsu wajen ciro yaron dake cikin nata. Cikin ikon Allah kuwa suka fito da santalelen yaro, saidai kuma yariga daya rasu, tun jiya shiyasa ma haihuwar ta gagara, ya zama sai an mata tiyata, ɗayar nurse ɗin da suke aiki tare da Ameena suka miƙawa yaron, sannan suka duƙufa wajen ɗinke ta, cikin mintuna kaɗan suka gama yi mata duk wani abun daya dace cikin iya da kwarewa da sanin makaman aikinsu. Ɗaya daga cikin doctors ɗinne yayiwa su Ameena alama kan cewa su fita da ita, zuwa ɗakin hutu. Hakan kuwa akayi, inda Ameena da wannan nurse din suka turo gadon da Adda Maryan ɗin ke kai. Gaba ɗaya jikin Ameena yayi sanyi, tausayin maryam ɗinne ya cika zuciyarta, tana tausayin halin da Maryam din zata shiga, idan ta tashi, taji cewa yaron nata baizo da rai ba, tasan tabbas zata shiga damuwa. Haka dai suka turo gadon, inda suka fito daga theater room ɗin, direct ɗakin da zasu kaita dan hutuwa suka nufa, wanda yazama kuma dole sai sun wuce ta gaban su Baba Malam, kasancewar su Baba Malam ɗin sunyi kusa da ɗakin theater'n. Dab da sun kusa ƙarasowa wajen su Baba Malam ɗinne, Maryam ta bude idanunta a hankali lokaci guda kuwa hankalinta ya dawo jikinta, ahankali ta buɗe idanunta, cikin wata irin murya me sanyi, da kuma yanayin mayen jinya taƙira sunan. "Baba Malam!!." Al'amarin daya sanya su Baba Malam ɗago kansu kenan, dan dukansu kansu aƙasa yake, basu ma lura da fitowar su daga ɗakin theater'n ba, cikin hanzari su Baba Malam suka nufo ta, da sauri ɗayar nurse ɗin ta dakatar dasu, cikin sauri tashiga tura gadon, don ba aso kowa yaje kan wanda akaiwa theater sai bayan mutum ya huta tukun, Ameena kuwa cikin sauri haɗi da tashin hankali tanufi office ɗin babban doctor ɗinsu, hankalinta amatuƙar tashe yake, domin farfaɗowan Adda Maryam ɗin akaro na biyu, zai iya zama hatsari. Maryam kuwa a hankali ta samu ta ɗaga ƴan yatsunta cikin wata dashashshiyar murya tace. "Yaya Ameenu kazo, kazo kada su hanaka zuwa Yaya Ameenu mutuwa zanyi." Dai-dai lokacin kuma nurse ɗin ta shige da ita wani ɗaki, cikin matsanancin sauri Ya Ameenu yazo dan bin bayan matarsa, wata nurse ce ta taresa dan ba'a shiga kai tsaye, sai an baka izini, cikin wani irin gigita Ya Ameenu ya daka mata tsawa, ransa amatuƙar ɓace hankali a tashe yace. "Matatace fa, tana ƙirana kuma kuce bazan je ba." Hannu yasa ya ture nurse ɗin gefe, nan ya faɗa cikin ɗakin su Baba Malam suka rufa masa baya. Yana shiga cikin sauri ya ƙarasa jikin gadon, Adda Maryam kuwa da hawaye ke zuba daga cikin idanunta hannunsa ta kama, dai-dai lokacin su Baba Malam suka iso, ɗayan hannunta tasa ta kamo hannun Baba Malam ɗin. Ƙam ta riƙe hannun Baba Malam, cikin wata irin murya me ɗauke da tsananin sanyi tace. "Tun kwanaki nake ta ji ajikina cewa, mutuwa zanyi Baba, rayuwata tazo ƙarshe, Dan Allah Baba Malam kayafemin, sannan kaya fewa Zaleeha, nasan duk inda take tana cike da kewa, da kuma nadamar abun da ta aikata, natabbata kuma idan ta dawo zatayi maka biyayya fiye da wanda ni nayi ma, dan Allah Baba Malam ka yafewa Mama, ka barta ta dawo ɗakinta ta zauna, dan nasan itama tayi nadama, nikam nasan bazan sake zama acikin ku ba, nasan daga nan bazan koma gida da numfashi ba, lokaci na yazo, zan tafi na barku badan naso ba, zan yi nesa daku, zan tafi inda bazaku sake gani, ko jina ba." Hannu ya Ameenu yakai ya rufe bakinta, tuni wani irin kuka ya taso masa, kansa ya shiga girgiza wa, murya na rawa yace. "Bazaki mutuba Maryam, bazaki mutu kibarni ba Insha Allah zaki samu lfy. Rayuwata bazata taɓayin inganci ba, matuƙar babu ke acikinta, dan Allah kidaina faɗin cewa zaki tafi ki barmu, muna tsananin buƙatarki agaremu." Hawaye ne suka tsananta zuba daga cikin idanunta, wani irin murmushi me ciwo tayi tare da girgiza kanta cikin sanyi tace. "Dan Allah ya Ameenu idan na cika, ku maidani gidan Baba Malam kuyi mini wanka acan, sannan kusamin sutura, idan kun sallaceni, inaso kusani cikin kabarina da hannuwanku." Shiru tayi sakamakon shaƙuwan daya taso mata, kuka Ya Ameenu ya fashe dashi, tare da soma girgiza kansa, sake damƙe hannun Yaa Ameenu da kuma Baba Malam tayi, cikin wani irin yanayi da muryarta wanda bata fita sosai tace. "Kuyafewa Zaleeha, kada kuyi mummunan kuma dogon fushi da ita, Mamy ke da Ya Habu ku yafe mata, nikam zantafi na barku nasan da cewa zakuyimin addu'a aduk lokacin da kuka tuna dani, sannan Baba Malam zan tafi, ina me al'faharin kasancewar ka mahaifi agareni." Hawayen da suka cika idanun Baba Malam ne suka samu daman gangarowa, take wani irin kuka ya taso masa, sake damƙe hannun Maryam ɗin yayi, Mamy kuwa tuni ta koma gefe tana kuka, Ya Habu ma kukan yake sosai. Idanunta wanda sukayi farare fat ta ɗago ta zubawa Ya Ameenu dake kuka, yana ta faman girgiza mata kai, murmushi tayi masa, kana kuma tamaida dubanta ga Baban Malam, lokaci guda ta soma wani irin shaƙuwa, ganin haka yasa Baba Malam fashewa da wani irin kuka, mai tsuma zuciya, sosai ya kama hannunta yana ji yana gani ƙudirin Allah na wakana bashida iko ko da, da ace duk duniya gatan Maryam ne da masoyanta bazasu tseratar da ita koda na second ɗaya ba, cikin muryar kukan yake. faɗin kalmar. "La'ila ha'illallah, muhammadur rasulullah, sallallahu alaihi wasallam!!!." Haka yake faɗan kalman ararrabe saboda matsanancin kukan dayaci ƙarfinsa. Cikin muryarta, dake ɗauke da shaƙuwa itama tasoma bin bakinsa, tana faɗan kalman shahada'n, duk abun daya faɗa itama sai ta faɗa, atare suka kai ƙarshen salati'n shida ita, nan take yaji jikinta yayi sanyi, komai nata ya sake, idanunta sun kafe suna kallon sama, yayinda baƙin cikin ƙwayar idanun nata ya ɓace ɓat, sai farin kawai kake gani. Ya Ameenu kuwa dama tuni ya daina gane komai, hakanne ma yasa bai lura da cewar ta daina motsi ba, cikin wani irin yanayi Baba Malam yaja da baya tare da fashewa da wani irin kuka mai tsuma zuciya, kuka irin wanda bai taɓayi ba arayuwarsa, wannan kukan nasa shine abun dayasa Mamy da kuma Ya Ameenu da Habu, suka kai dubansu garesa, ganin irin kukan da yake, yasa Mamy da Ya Habu suka tabbatar da cewa, Maryam ɗin tarasu, kuka Mamy tasa sosai, shima Ya Habu haka, Ya Ameenu kuwa hannunta dake cikin nasa yaɗan murza, idanunsa sun cika tab da ƙwalla, hakan yasa baya ganin yanda idanunta suka juye, cikin muryar kuka yace. "Bazaki mutu ba Maryam, in sha Allah bazaki mutu yanzu ba, saboda muna da buƙatarki acikin rayuwarmu, kidaina faɗin cewa zaki mutu, mutuwa bazata ɗaukeki yanzu ba, idan kika mutu kuma ya kikeso ni nayi da rayuwata? bazan iya zama babu ke ba, ki tashi kinji!." ya ƙare maganar yana meɗan jijjigata, jin hannunta dake cikin nasa, jin yayi nauyi ne, yasashi matse hawayen da suka cika idanunsa, har suka hanasa gani da kyau, duban fuskarta yayi, nan yaga idanunta sunkafe, take yaji wani irin abu ya bugi kansa, dai-dai lokacin kuma, Doctor'n da Ameena ta ƙira ya shigo cikin ɗakin da sauri, ganin yanda su Baba Malam ke kuka, ya sa shi ƙarasowa jikin gadon, idanunta daya gani akakkafe yasashi girgiza kansa, nan yaja wani ɗan mayafin dake jikinta ya rufe fuskarta bayan yasa hannu ya shafe idanunta. Girgiza kai Ya Ameenu yashiga yi, cikin kiɗima yace. "Miye haka? meyasa ka rufe mata fuska?" Cikin tsananin tausayawa Dr. ɗin yace. "Am sorry to say Allah yayi mata rasuwa." Tamkar sauƙan guduma haka Ya Ameenu yaji maganan doctor'n acikin kai da kunnuwansa, lokaci guda yaji gaba ɗaya lakar jikinsa ta tsinke, ƙafafunsa ne suka gaza ɗaukan nauyinsa, take yazube akan guiwowinsa, kifa kansa da jikin gadon Maryam ɗin yayi, yasaki wani irin kuka mai tada hankali, wani irin kukane, me matuƙar jijjiga zuciya, wanda hakanne yasa Ameena dake waje shigowa cikin ɗakin. kuka Ya Ameenu keyi me tsanani, irin wanda duk wanda yaji sa, dole ya tausaya masa, lokaci ɗaya jikinsa ya soma rawa, numfashinsa ne yayi wani irin fusga, take ya faɗi awajen sumamme. Cikin sauri Ya Habu da Dr. ɗin sukayo kansa, dan Baba Malam kam kuka yake sosai da sosai. Hawaye ne suka silalo daga cikin idanun Ameena, wanda ke tsaye agefe, sosai jikinta yayi sanyi da rasuwan Adda Maryam ɗin, Da taimakon Ya Habu doctor ɗin ya ɗan yayyafawa Ya Ameenu dake sume ruwa akan fuskarsa, cikin abun da baiwuce minti ɗaya ba kuwa Ya Ameenu'n ya farfaɗo da wani irin gigitaccen kuka, dukansu kuka suke anrasa wanda zai rarrashi wani acikinsu, da ƙyar Baba Malam ya iya tsaida kukansa, ganin cewa magriba ta kawo kai, tasowa yayi inda ya ƙaraso har wajen da Ya Ameenu'n ke zaune, har yanzu kuka yake me tsuma zuciya, yayinda ya jingina kansa da jikin gadon da gawar Maryam ɗin take, dafa kafaɗansa Baba Malam yayi, cikin da shashshiyar muryarsa yace. "Kayi haƙuri Ameenu, ayanzu Maryam bata buƙatar kukan mu, tafi buƙatar addu'ar mu fiye da komai." kai Ya Ameenu ya shiga jijjigawa cikin matsanancin kuka, yace. "Yazanyi na daina kuka Baba, bazan iya ba, bazan iya daina kuka ba, bazan iya jure rashin Maryam ba Baba, mutuwa ta ɗauki Maryam ta barni, mutuwa ta nisanta ni da Matata, mace mafi soyuwa agareni, tayaya zan iya jure rashin Maryam, wanda koda sau ɗaya ne bata taɓa ɗaga min murya, ko ƙin abun da nakeso ba, komai nakeso shi take so, idan nace kada tayi, har abada bata taɓa yi, idan na umurceta bata taɓa tsallakewa, farinciki na shine nata, ta amince da aure na batare da tana sona ba, hakan kuma baisa taƙi min biyayya ba, Dama mutuwa ta sani da ta barmin Maryam saboda ina da buƙatarta acikin rayuwata!." sake rushewa da wani sabon kuka mai tsuma zuciya yayi, idanu Baba Malam ya lumshe take wasu hawaye masu zafi suka gangaro daga cikin idanunsa, matuwar Maryam tayi matukar girgizasa ƙwarai, yanaji yana gani mutuwa ta ɗauki ƴarsa agaban idanunsa, mutuwa ta ɗauki ƴarsa mafi soyuwa agaresa, ina ma da ace mutuwa tana neman zaɓi, tabbas daya bata zaɓi ta ɗauke Zaleeha tabar masa Maryam, saboda Maryam takasance tamkar haske ne awajensa, takasance meyi masa biyayya, ita da Ahmad sun kasance suɗin daban suke acikin ƴaƴansa, masu tsananin biyayyya ne suɗin. Sanin cewa kuka bazai bawa Maryam ɗin komai ba, yasa can cikin zuciyarsa ya soma ambaton sunan Allah, yana meyi mata addu'a, cikin ransa kuwa, yanajin cewa Insha Allah, Maryam ɗin zata dace da rahamar Allah. Duban Mamy dake kuka sosai yayi, kana ya kalli Ya Habu wanda shima kukan yake kaman ƙaramin yaro, dai-dai nan Dr Adnan ya shigo cikin ɗakin, gaba ɗaya jikinsa amace yake, dan kuwa labarin rasuwar Maryam ɗin yaje kunnensa, ganin yanda Ya Ameenu dasu Ya Habu ke kuka, yasa yaji idanunsa sun cika da ƙwalla, haƙiƙa mutuwa wata abace dake ruguza duk wani farincikin iyali, sannan kuma bata barin wani dan wani yaji daɗi. Cikin matsanancin tausayawa Dr Adnan yayiwa Baba Malam ɗin ta'aziyyan rasuwar, Ya Habu ne ya miƙe ya fita daga cikin ɗakin, nan cikin kuka ya laluɓo wayarsa daga aljihun rigarsa, number'n Yaa Ahmad ya fara dannawa ƙira. Ya Ahmad dake zaune afalo shida Aunty Lubna, hakanan yana ganin ƙiran Ya Habu'n yaji zuciyarsa ta tsinke, gabansa ya faɗi, Yana ɗaga wayan kuwa zuciyarsa ta soma bugawa da ƙarfi, sakamakon yanda yaji Ya Habu'n na kuka wiwi. Cikin matsanancin tashin hankali Ya Ahmad yamiƙe tsaye akiɗime yace. "Habu lafiya meke faruwa ina Baba Malam?". cikin muryan kuka Ya Habu yace. "Ya Ahmad, Allah yayiwa Maryam rasuwa!." Ɗaɓas haka Ya Ahmad ya sulale ya zauna aƙasa, cikin matsanancin tashin hankali da kuma mugun kaɗuwa, take jikinsa ya soma ɓari, inda yaji kunnensa sunyi masa wani irin luuuuuu, sake wayar tasa yayi lokaci guda kuma sai ya fashe da wani irin kuka me sauti, wanda har Ya Habu da bai katse ƙiran ba yana jiyo sautin kukan. Cikin matsanancin tashin hankali Aunty Lubna tace. "Lafiya kuwa wani abune ya faru agida? dan Allah meke faruwa?". Tayi masa tambayar aruɗe. Cikin matsanancin kukan da yakeyi, ya ɗago kansa, ya dubeta, yana kuka sosai yace. " Lubna Allah yayiwa Maryam rasuwa." Wani irin hajijiyane taji naneman ɗaukanta, domin maganar tazo mata abazata, durƙushewa tayi kan ƙafafunta, take wasu irin hawaye suka silalo daga cikin idanunta, sai kawai itama ta fashe da kuka, Ya Habu kuwa yana katse ƙiran, Goggo Maryama yaƙira inda ya sanar mata maganan rasuwan, amatuƙar rikice Goggo Maryama tasa masa kuka, jin tana kuka itama yasashi katse wayan, Nan ya dannawa lambar Malam Adam ƙira, bugu biyu kuwa ya ɗauka, jin abun da Ya Habun ke faɗi, yasa Malam Adam, sanya salati, hankalinsa amatuƙar tashe, yace zaizo nan asibitin ya samesu. Lambar Hajja Inna ya kuma laluɓa, saida wayar ta kusa tsinkewa kafun ta ɗaga, tana shirin masifance sa kan cewa ya dameta da ƙira, jinsa yana kuka yasa cikin matsanancin tashin hankali tace. "Kai Habu lafiyanka kuwa? me yake faruwa naji kana kuka?" Cikin matsanancin kuka yace. "Maryam ne." Cikin sauri Hajja Inna da ƙirjinta ke bugu tace. "Maryam ne me? Meya sameta." Zakariyya da Ziyada dake zaune nan falon, tun da Hajja Inna ta fara wayan suka tsura mata ido. Cikin kukan da yaci ƙarfinsa yace. "Allah yayi mata rasuwa." Sa ke wayan Hajja Inna tayi, tare da sulalewa ƙasa. Cikin sauri Zakariyya ya ɗauki wayar ya kara akan kunnensa, jin muryan Ya Habu na kuka, yasa aruɗe yace. "Ya Habu, meya samu Adda Maryam ɗin." Jin muryan Zakariyya yasa, Yaya Habu cewa. "Maryam ta rasu Zakariyya, Allah ya karɓi rayuwarta." azabure Zakariyya yasoma girgiza kai, lokaci guda kuma wani irin kuka ya ƙwace masa, nan ya durƙushe gaban Hajja Inna dake kuka, shima kukan yasa me tsuma zuciya, fahimtar abun daya faru yasa Ziyada faɗawa jikin Zakariyyan ta rungumesa tana kuka. Hajja Inna, Zakariyya, Ziyada, duka kuka suke, an rasa mai rarrashin wani acikinsu. Ya Habu kuwa haka ya dinga ƙiran ƴan uwa yana sanar musu da rasuwan, kowa yaji saiya girgiza, saboda Maryam macece abun soyuwa ga kowa, bata banbance kowa natane. Nan take labarin rasuwar ya kewaya gaba ɗaya cikin danginsu yan uwa da maƙoto, lokaci ɗaya kuwa iyalan familyn suka ruɗe da koke koke. Saida Ya Habu yagama sanarwa kowa, kafun yake dannawa number'n Mama ƙira, wayar bata wani jima tana ringing ba Mama ta ɗaga, Kukan da taji Habun nayi ne yasa hankalin ta matuƙar tashi, cikin ruɗewa tace. "Tun safe nakejin gabana na faɗuwa, Habu faɗamin wani abune ya samu Zaleeha ko?". Jin abun da ta faɗa yasa Ya Habu sake fashewa da kuka, cikin matsanancin kuka yace. "Mama Maryam ne, Maryam tatafi ta barmu, Maryam tayi nesa damu ta yanda har abada bazamu sake ganinta ba, Mama Allah ya karɓi rayuwar Maryam ɗazun nan, shikenan Mama Maryam tatafi inda bazamu sake ganinta ba...." Tunda Mama taji yace Maryam ta rasu, shikenan ta daina fahimtan sauran maganganun da yake faɗi, har wayar hannunta ta faɗi kasa batare da ta sani ba, akiɗime ta shiga jujjuya kanta, maganan rasuwan ƴarta ta Maryam ne ke yawo acikin kunnuwanta, ƙafafunta ne sukai mata nauyi, hannu ta ɗaura aka ta saki wani irin fitinannen kuka, wanda yasa Zahira fitowa daga cikin ɗaki da sauri, ganin Maman zaune daɓas aƙasa tana kuka, yasa Zahiran ƙarasowa cikin tashin hankali tace. "Mama meya faru?." Cikin kuka Mama tace. "Tarasu Zahira, Maryam ta rasu, tabar mana duniyar." Wani irin ƙara Zahira tayi take kuma ta faɗi awajen tana kuka. Can cikin asibiti kuwa Dr. Adnan ne ya nemo ambulance inda aka sanya gawar Maryam aciki. Da ƙyar Baba Malam ya iya rarrashin Ya Ameenu, sai-dai kuma har yanzu bai-daina kuka ba, Cikin minti kaɗan saiga Malam Adam yazo, zuwan Malam Adam ɗin shiya taimaka wajen rarrashin Baba Malam da kuma su Ya Habu da Mamy, suka bar kuka, amma Ya Ameenu kam hawaye sun kasa daina zuba, daga cikin idanunsa. Malam Adam ne yayi duk wani abun da ya dace, shine ma yasanya Ya Ameenu amota, sannan dukansu suka nufo gida. Nan gidan nasu kuwa tunkan isowan su tuni ya cika da ƴan uwansu na kusa, nan fa kuka ya dawo sabo, kaitsaye falon Baba Malam aka wuce da gawan, nan kan tiles ɗin falon aka kwantar da ita kudu da arewa tana fuskantar gabas Ya Ameenu ne ya zauna inda yasa gawan agaba ya fashe da wani irin kuka, wanda saida yasa kowa kuka awajen, ganin kukan yayi yawane yasa, Malam Adam ya tara gaba ɗaya jama'an gidan, nan ya bawa kowa alƙur'ani, yace sufara karatu, sannan ayanzu Maryam addu'a take buƙata, bawai kuka ba, nan aka fara karanta mata al'ƙur'ani, Baba Malam ne yasa gawan agaba, yana mata karatun al'ƙur'ani hawaye na tsiyaya daga idanunsa, Ya Ameenu kuwa muryarsa kwata kwata ta daina fita saboda tsabar kuka. Ɓangaren Ameena kuwa, koda taga tafiyan su Baba Malam gida tare da gawan Adda Maryam ɗin, excuse ta ɗauka, dan batajin zata iya zama, mutuwar Adda Maryam ɗin yasa gaba ɗaya jikinta yayi sanyi, koda ta fito daga asibitin, adai-dai-ta sahu ta hau, dan bawani iya mota tayi ba, shiyasa bata fitowa da motar da Saifuddeen ɗin ya saya mata wajen aiki, sannan kuma tasani sarai, duk wani abu na ƙarfe ba karɓanta yake yi ba, da ta fara amfani dashi zai lalace, shiyasa ma kawai ta ajiye motar, gudun kada Motar ta mutu da wuri. Zaune suke dukansu afalon Ummi suna hira, lokacin dawowar su Saifuddeen da Ahmad kenan daga sallan magriba. Bakinta ɗauke da sallama ta shigo ɗakin, jikinta amatuƙar sanyaye. Da mamaki Ummi ke kallonta, dan kuwa tasan bayanzu ne lokacin dawowanta ba, kasancewar duty'n dare takeyi sai nanda kwana uku zata koma na rana, cikin kulawa Ummi tace. "Ameena lafiya kuwa naganki haka asanyaye." Hawaye ne suka zubo daga cikin idanunta, hakanne yasa hankalin su Ummi tashi, hannu Raliya tasa ta amshi Adeel dake riƙe ahannunta, cikin sanyin murya tace. "Ummi ɗazu fi ta na aiki nasamu ankai Adda Maryam ɗin su Zakariyya haihuwa, kuma bazata iya haihuwa da kanta ba, sabida yaron ya rasu a cikinta sai anyi mata theater, kuma anyi mata theater'n, an ciro ɗan ba rai, bayan anfito da ita daga ɗakin theater'n ne kuma Allah yayi mata rasuwa, Ummi Adda Maryam ɗin su Zakariyya ta rasu." Ta ƙare maganan tana kuka, don dama ita akwaita da tsoron mutuwa, kona wanda bata sani ba ma kuwa. Salati su Ummi suka sa, cikin matsanancin tashin hankali Ummi tace. "Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un, Maryam ta rasu? Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un!." taƙare maganar hawaye nabin kan fuskarta, Raliya ma salatin tayi take kuma sai idanunta suka kawo ƙwalla, Kuka Ummi ta fashe dashi, tare da sanya hannu ta rufe fuskarta, haka nan rasuwar maryam ya daki zuciyarta, yatuno mata rasuwar Abbansu Saifuddeen da Ya Nuruddeen ɗinsu sosai kuka yaci ƙarfinta. Saifuddeen kuwa hankalinsa ne ya tashi matuƙa, sakamakon jin rasuwar Adda Maryam ɗin, Ahmad ma dake gefe shi da kansa saida yaji ƙwalla a idanunsa, saboda alokacin bikin Zaleeha da Saifuddeen sosai suka ɗan saba da Adda Maryam ɗin, kasancewar itace ta tsaya akan duk wani abu da ya shafi bikin, macece me sauƙin kai, da sakin fuska. Hayatuddeen ne ya shigo falon afujajan fuskarsa gaba ɗaya tayi caɓa caɓa da hawaye, dan yanzun Zakariyya ke sanar dashi, rasuwar Adda Maryam ɗin, yazo faɗawa su Ummi kenan ya iske su ahaka, faɗawa jikin Ummi yayi tare da sakin kuka, cikin kukan yace. "Ummi dagaske Adda Maryam ta rasu, yanzu Zakariyya ke faɗamin, Ummi Zakariyya kuka yake sosai har kaman zai shiɗe." ɗan shafa bayansa tayi, tare da ciresa ajikinta, dan kukan nasa, ƙara mata nata kukan zaiyi. Duban Saifuddeen wanda yayi ƙasa da kansa tayi, kana ta kai duban ta ga Ahmad, cikin sanyin murya tace. "Ahmad kuje can gidan Baba Malam ɗin da Saifuddeen" Jin jina kai Ahmad yayi, nan ya miƙe tsaye, zunbur Hayatuddeen yayi tare da cewa zai bisu, basu hanashi ba, haka suka shiga mota, kai tsaye suka nufi gidan Baba Malam, zuciyoyinsu cike da alhinin abun da ya faru. Ummi kuwa miƙewa tayi ta shige ɗaki, dan taji mutuwar Maryam din sosai, tabbas Maryam yarinyace me hankali, da kuma daɗin zama, uwa uba mutunta na gaba da ita, Ameena ma asanyaye ta koma ɓangarenta, Raliya kuwa bayan Ummi ta bi, ɗauke da Adeel akan kafaɗanta. Koda su Saifuddeen suka isa gidan, Ya Habu wanda idanunsa suka kumbura shi yayi musu jagora zuwa falon Baba Malam, domin anan gaba ɗaya mazan familyn suke tare, sun saka gawan agaba suna tayi mata karatun alƙur'ani, bayan sunyiwa Baba Malam ɗin ta'aziyya da kuma Ya Ameenu wanda har yanzu idanunsa ke tsiyayar da hawaye, nan dai sukayiwa sauran jama'an dake cikin falon gaisuwa, alƙur'anin suma suka ɗauka suka soma karantawa, muryan kowa na tashi amma banda na Saifuddeen, danshi koda yaushe saidai yayi karatunsa azuciyarsa. Can Abuja kuwa, Ya Ahmad hankalinsa amatuƙar tashe yake, yayi kuka harsaida yaji numfashinsa na ƙoƙarin ƙwacewa, haka Aunty Lubna ma tsakaninsu babu me rarrashin wani, sam baiduba cewa dare yayi ba, haka ya haɗa kayansa, inda yasa Aunty lubna ma tahaɗo nata kayan dana yaransu, duk da ƙaramin yaronsu data ƙara haihuwa, nan suka zuba yaransu amota suma suka shiga, kaitsaye suka kama hanyar Gombe, dan bayajin zai iya bari har gobe kafun ya taho, gaba ɗaya ma ya manta da wani batun hawa jirgi, ya ƙudurta aransa cewa bazai taɓa tsayawa ba harsai ya gansa acikin garin Gombe, haka yake tuƙin mota yana hawaye, tsananin tausayin mahaifinsu yakeji, dan yasan Baba Malam ɗin saiya fisu jin mutuwan Maryam ɗin, saboda kowa yasan Baba Malam, to yasan akwai ƙauna me zafi tsakanin sa da Maryam, daga gefe guda kuwa idan ya tuna da ɗan uwansa Ameenu, sai yaji kukan nasa ya tsananta, saboda yasan mutuwar Maryam ɗin zata wujijjiga Ameenu, domin kuwa yasan Ya Ameenu'n nayiwa Maryam wani irin ninkekken so. Zakariyya kuwa wanda yasha kuka har dana fitar hayyaci ne, ya jawo wayarsa, number'n Zaleeha ya nema tare da danna mata ƙira. Dai-dai lokacin kuwa Zaleeha na kwance akan ƴar katifarta, gaba ɗaya yau ɗin tun safe tarasa mekeyi mata daɗi, hakanan take yawanjin faɗuwar gaba, da kuma tsinkewar zuciya, wanda bata san dalili ba, saidai addu'a kawai take ta yi abakinta, kasancewar kwana biyun Balkeesu na yawan matsa mata da ƙira, hakan yasa, yau ta sanya wayarta a silent, dan kwata-kwata bata son damuwa, wannan dalilin yasa, sam bataga ƙiran da Zakariyyan keyi mata ba. Zakariyya kuwa saida yayi mata 10 missed calls, ganin bata ɗaga ba yasashi fashewa da wani sabon kuka, da ƙyar Hayatuddeen ke iya tausansa. Su Saifuddeen basu bar gidan Baba Malam ba, sai wajen ƙarfe shaɗayan dare. Dan bayau ne za a kai Maryam din makwancinta ba, dole sai tayi kwanan keso, gobe kuwa da ƙarfe goma insha Allah za ayi sallan jana'izar ta, koda suka koma gida direct ɗakinsa ya wuce, inda ya murzawa ƙofarsa key, sam yau baison Ameena ta dameshi, dan ƙwarai rasuwar Adda Maryam ta daki jiki da zuciyarshi. Ɓangaren Mama kuwa taso tahowa yau ɗin, amma babu abun hawan da zata hau tazo, haka taci kuka har idanunta suka kumbura, Zahira ma kukan take sosai, bata iya rarrashin Mama, haka Maman ma bata iya rarrashinta Maman Mama da Babantama sosai mutuwar Maryam ta shigesu. Agidan Baba Malam kuwa kwana akayi anawa gawan Maryam karatun alƙur'ani, yanda suka ga safiya haka suka ga dare, kab gidan babu wanda ya iya runtsawa, Mamy tayi kuka harta godewa Allah, idanunta sunyi luhu luhu dasu, sam bata banbance su Maryam da ɗanta na cikinta, har gaban abada kallonsu take mazaunin ƴaƴanta na cikinta, haka suma sun ɗauketa uwace, basa taɓa banbantata da mahaifiyarsu, wannan dalilin yasa shaƙuwa me ƙarfi ta shiga tsakaninsu, sau da yawa Maryam saitayi shawara da Mamy, batayi da Mama mahaifiyarta ba, haka ma Zakariyya duk wata damuwarsa koda ta kuɗi ce, Mamyn yake faɗawa, dan gaba ɗaya uwa suka ɗauketa. Washegari ana idar da sallan asuba kuwa Ya Ahmad wanda suka kwana ahanya suka samu isowa gidan, nanne fa wani sabon kuka ya tashi, dan ganin gawan Maryam da kuma yanda ƴan uwansa ke kuka yasa gaba ɗaya hankalinsa yayi masifar tashi, haka yazauna yana kuka kaman ƙaramin yaro. Zakariyya kuwa koda ya sallame sallan asuba, wayarsa ya ɗauka still ƙiran Zaleeha yayi amma no answer, nan ya shiga rubuta mata saƙo kamar haka. _"Adda Zaleeha Ina ta ƙiranki bakya ɗagawa ko, kowa yaƙira wayanki bazaki ɗaga bako?, saboda kinsawa kanki zuciyar kafurci aranki, kin bijirewa Baba Malam, kin bijirewa kowa, kin gujewa gaba ɗaya danginki, kinƙi bin umarnin mahaifin mu, kin tafi can wata uwa duniya cikin kafurai kinje kin zauna, wataƙila ke kam bazaki dawo ba harsai gaba ɗayanmu mun ƙare, har sai kin rasa kowa naki na a faɗin duniya sannan zaki dawo, shikenan kici gaba da zama Adda Zaleeha, Adda Maryam kam tatafi ta barmu, tabar mana duniya'n, tayi nesa damu inda bazamu ƙara ji da ganinta ba yadda kika gujewa dangi duk suma sun guje miki gashi babu wanda ya tunaki,sannan nidana tunakin na kiraki baki amsaba."_ Yana rubuta saƙon yana kuka sosai, yana gamawa kuwa ya tura mata, inda ya kifa kansa ya cigaba da kuka." Da duru-durun Asuba Mama da Zahira da wasu ƴan uwanta suka samu isowa gidan, ganin gidan nasu acike shiya ƙara ɗaga musu hankali, Nan Mama ta buɗe ɓangarenta ta shiga, anan falonta ta zauna tana wani irin kuka me cike da ban tausayi da tsantsar nadama. Zaleeha kuwa yau makara tasoyi, tana tashi tayi alwala tayi salla, tana nan zaune akan sallaya tajiyo sallaman Aisha, cike da ɗan mamaki ta amsa mata tare da bata izinin shigowa. Aishan ne ta shigo ta zauna hannunta ɗauke daɗan kula, agaban Zaleehan ta aje kulan tare da cewa. "Kinganni da sassafe ko, wallahi kinsan yau ƙarfe 6 dai-dai muke da lecture shiyasa da zan fito nace Inna tabani abun karin kumallonki na kawo miki." Murmushi Zaleehan tayi, tana ƙoƙarin cewa wani abune taga screen ɗin wayarta ya kawo haske, hakanan taji ƙirjinta ya buga, zuciyarta ta tsinke, jawo wayartata tayi tare da dubawa, text message ta gani da sunan Zakariyya, nan ta cire wayan a key, tare da shiga cikin message ɗin. Hannunta na ɓari jikinta na rawa, haka tashiga karanta message ɗin, maganansa na kusa da na ƙarshe shine abun dayasa taji gaba ɗaya duniyar ta tsaya mata kanta yayi wani irin mugun sarawa duhu ya wulgawa ganinta, azabure ta miƙe tsaye, cikin wani irin gigita haɗi da kiɗima da tsananin tashin hankali ta dannawa numbern Zakariyyan ƙira, bugu biyu kuwa ya ɗauka, yana kara wayar akan kunnensa ya saki kuka, abun dayasa hankalin Zaleeha tashi kenan, lokaci guda bakinta ya soma ɓari, murya asarƙafe tace. "Zak....kar iya, ina Adda Maryam, meya sameta, mekakeson faɗamin Zakariyya?" Cikin matsanancin kuka Zakariyya, yace. "Adda Maryam tarasu Zaleeha, Adda Maryam ta rasu tun daren jiya, tatafi inda bazata ƙara dawowa ba, tayi nisa nisa irin na har abada....." Kuka ne ya ci ƙarfinsa hakan yasa ya kasa ƙarasa maganan. Tun afaɗan maganganunsa na farko, ta dainajin komai, duk wani abu najikinta tsayawa yayi, wayar hannunta ne ta sulale inda ta faɗi ƙasa, wani irin ƙara ta saki take kuma ta faɗi awajen sumammiya, cikin matsanancin tashin hankali, Aisha tayi kanta tana jijjigata, haɗi da ƙiran sunanta, ihunta da su Elizabet sukaji ne yasasu shigowa aguje, ganin Zaleehan asume yasa Elizabet dafe ƙirji cikin ɗaga murya tace. "Innalillahi, a madadin tace Oh jesus meya ke faruwa?" Uncle solomon ne ya fita da gudu, bajimawa ya shigo hannunsa riƙe da kofin ruwa, ƙarasowa yayi inda ya ɗan yayyafawa Zaleehan ruwa afuskarta. Azabure tatashi, cikin wani irin tashin hankali, damƙo Aisha tayi tana me jujjuya kanta, take kuma sai ta fashe da wani irin kuka mai matuƙar tada hankali, cikin kukan take ja da baya, tana me sake girgiza kanta, hankalinta amatuƙar tashe tace. "Aisha Adda Maryam, Adda Maryam ɗina ta rasu, Adda Maryam tabar duniya batare da na sake sanyata a idanuna ba, wayyo Allah na wayyo ni, kaicon rayuwata, kaicona !!!" Wani irin azababben kuka ta saka kukane mai cushe zuciya da numfashi, lokaci ɗaya ta miƙe tsaye wayarta kawai ta ɗauka tare da buɗe jakanta, kuɗi ta ɗauko wanda batamasan ko nawa bane, takalmi ta zura aƙafafunta, ƙoƙarin fita daga cikin ɗakin take Elizabet ta riƙota cikin kulawa tace. "Zaleeha ina zakije, dan Allah kitsaya ki nutsu tukun" Faɗawa jikin Aishan tayi tana wani irin kuka, kanta ta girgiza cikin kuka tace. "Adda Maryam ɗina Uncle Solomo Addana, Adda Maryam ɗina ta rasu" Hawayen tausayin Zaleehan ne suka kwaranyo daga cikin idanun baki ɗayansu cikin sanyin murya Aisha tace. "Muje to na rakaki ki hau mota, amma kafun nan ki kimtsa tukunna." Kai Zaleeha ta girgiza cikin matsanancin kukan dake neman shiɗar da ita ya tafi da rants. Hannunta Aisha ta kama suka nufi ƙofar fita daga gidan Solo da martasa na biye dasu a baya. Gaba ɗaya Zaleeha bata cikin hayyacinta, hakanne yasa Aisha mannata da jikinta, domin kukan da Zaleehan keyi yasa bata ko iya ganin gabanta. Suna kawo bakin titi kuwa sukai sa'a nan suka samu wata mota, wanda kaitsaye Gombe zata taho, da kwai ma mutane cike acikinta, Aisha ce tayi mata komai, tasata acikin motar, hannun Zaleehan dake kuka ta kamo, nan ta ɗan ɗaga mata hannu, itama hawayene ke zuba akan fuskarta, murya asanyaye tace. "Allah yajiƙanta yasa al'janna tazamo makoma agareta, kiyi haƙuri kinji Zaleeha, dukkan me rai dama mamaci ne, kowa lokacinsa yake jira, dayazo kuma babu jinkiri." Kai Zaleeha ta jinjina, tare da sakin sabon kuka, nandai Me motar yaja suka tafi, kowa dake cikin motar kallon yanda Zaleeha ke kuka suke, wasu kukan nata ya damesu, wasu kuwa matsanancin tausayinta ne ya kamasu, domin kukan da take irin kukan nanne me karƴar da zuciya, kukan da take, kukane me fitar da irin tsananin tashin hankalin da take ciki, kukane da duk me imani dole zaiji tausayinta. Sbpejg Acan gidan Baba Malam kuwa, kamar yadda Maryam ta buƙata kafun rasuwarta, Ya Ameenu da kuma Baba Malam ne sukayi mata wanka, wanda da ƙƴar suka iya daure zuciyarsu, nan ma Ya Ameenu saida ya durƙushe awajen yayi kuka sosai, har saida yaji numfashinsa na ƙoƙarin cushewa a ƙirjinsa, Baba Malam ma hawaye ne keta tsiyaya daga cikin idanunsa, haka dai suka kammala yi mata wanka, Ya Ameenu ne ya zura mata likkafani, sannan yayi mata duk wani abun daya dace, sosai jikinsa yake rawa, sakamakon kukan da yakeyi, ga wani irin jiri dake neman kadashi. Bayan sun kimtsa ta ne suka koma gefe suka zauna, dan kuwa da sauran lokaci, ƙarfe goma ne za a sallaceta, yanzu kuwa ƙarfe 9 ne dai-dai. Can ɓangaren Zaleeha kuwa, tunda ta shiga cikin motar, ta tura kanta tsakankanun cinyoyinta har zuwa yanzu bata ɗago ba, kuka take sosai harsaida numfashinta ya soma ƙoƙarin ɗaukewa, sosai motar tasu ke tsula gudu akan titi, hakanne yasa cikin abun dabai wuce awa uku ba suka iso cikin garin Gombe, nan cikin tashan gombe line aka sauƙe su, zuwa lokacin idanunta sun kunbura sunyi luhu-luhu dasu, kaitsaye bakin titi ta nufa, wani mai adai-dai ta sahu wato keke napep ne, ya tsaya agabanta tare da ɗan leƙo kansa, cikin kulawa yace. "Ranki ya daɗe tafiya ne?". Bata iya cewa dashi komai ba, kawai faɗawa cikin keke napep ɗin tayi, nan ta jingina kanta da jikin keken, kana ta rumtse idanunta, wasu hawaye masu ɗumi ne suka silalo daga cikin idanunta, dubanta me adai-dai-ta sahun yayi, cikin yanayi naɗan mamakin ganin hawaye akan fuskarta, yace. "Hajiya ina zamu ne?". Kasa amsa masa tayi domi , bakinta yayi mata nauyi sosai, batajin bayan kuka zata iya motsa laɓɓanta dan tace wani abu, wayarta dake hannunta ta kunna, cikin text message ta shiga, ataƙaice ta rubuta masa. "New G.R.A, da kuma layin da zai sauƙe ta." miƙa masa wayar tayi, amsa yayi ya karanta, yana gama karantawa ya miƙa mata wayar, cikin ransa yace. "Masha Allah wannan gata kyakkyawa amma kuma da dukkan alama kurmace bata magana, amma dai Allah yayi baiwar kyau anan, ko me yasata kuka kuma oho?" Ganin zancen zucin bazai kaisa ko ina ba, ya sashi tuƙa keken nasa yaja sukai gaba. Kamar yanda ta rubuta masa arubuce kai tsaye cikin G.R.A ɗin ya nufa da ita, har kuwa cikin layin da tayi masa kwatancen ya kawo ta, gaba ɗaya bata cikin hayyacinta saboda haka batasan da cewa sun iso ba, dawani idanu zata kalli ƴan gidansu? da wani bakin zata basu haƙuri? mezata ce dasu? da wani idanun zata kalli gawan Adda Maryam ɗinta? Da wanne ƙafar zata shiga gidansu da wanne ido zata kalli Baba malam me zata ce mishi?. waƴannan tambayoyin sune abun da suka cika zuciyarta, juyowa me adai-dai-ta sahun yayi, cikin kulawa yace. "Ranki ya daɗe mun iso fa." Sai alokacin ta buɗe idanunta da suke alumshe, gaba ɗaya kuɗin dake hannunta ta damƙa masa, wanda ita kanta bata masan ko dubu nawa bane, idanunsa ya waro waje, cike da mamaki, dai-dai lokacin ita kuma tafice daga cikin napep ɗin, ƙofar gidan nasu cike yake da jama'a wanda suka fara taruwa danyin sallan jana'iza, tsaye tayi tana kallon tankamemen gidan nasu, lokaci guda kuma wasu hawaye masu tsananin zafi suka fito daga cikin idanunta, da ƙyar take iya jan ƙafanta haka ta nufi cikin gidan, bataji bakuma ta ganin kowa agabanta, hakan yasa tafiya kawai take, sai faman cin tuntuɓe take tayi, amma bata ko kulawa, da wani dutse ta buge har saida babban ƴar yatsar ƙafarta ta fashe, amma koda kaɗanne bata ji zafi ajikinta ba, domin kuwa zafin dake cikin zuciyarta, ya zarce na wannan ciwon, wannanne yasa wasu daga cikin mutanen da suka zo jana'izan suka tsura mata idanu, saboda yanayinta ya gama nuna cewa bata cikin hayyacinta. Tana jefa ƙafanta acikin gidan taji wani irin abu ya daki zuciyarta, kaitsaye sashin Baba Malam ta nufa, sai faman gauraya hanya take, tana zuwa dai-dai bakin ƙofar shiga falon Zakariyya yazo zai fito sukayi karo da juna, amatuƙar mamakance Zakariyya yasoma ja da baya yana komawa cikin falon, dai-dai lokacin kuwa nan cikin falon Baba Malam ne zaune yana kuka mai tsananin taɓa zuciya, kuka yake sosai wanda hakan yasa gaba ɗaya mutanen falon suma suka fara zubda ƙwalla, cikin kuka murya na rawa Baba Malam ke cewa. "Ya Allah ka jiƙan Maryam kayi mata rahama,ya Allah ka ƙara mana haƙurin rashinta. Tabbas mutuwa ta yanke mana ƙauna, mutuwa ta nesantani da ƴata me tsananin biyayya agareni." Sai ya kuma saki shessheƙan kuka mai cike da ciwo a zuciya murya a disashe yace. "Inama ina ma da ace mutuwa tana bada zaɓi. To wallahi dana bata zaɓi ta ɗauki min Zaleeha a doron duniya tabarmin Maryam, dana bata zaɓi ta nesantamin Zaleeha daga wannan duniyar ta barmin Maryam! Da ta ɗauke Zaleeha dana huta da baƙin cikin da take ƙunsamin." Ya ƙare maganar yana kuka sosai. Waɗannan maganganun sune suka dira acikin kunnuwan Zaleeha, Zakariyya kuwa bakinsa na rawa, cikin ɗan ɗaga murya yace. "Adda Zaleeha!." Ƙiran sunan Zaleehan da yayi, shiya sanya gaba ɗaya mutanen falon suka kai dubansu ga ƙofan shigowa, ae kuwa tabbas suka ga Zaleehan ce tsaye, hawaye na shatata akan fuskarta kaman an buɗe famfo, dai-dai lokacin kuwa aka fito da gawar Adda Maryam daga ɗakin Baba Malam, angama kimtsata tsaf saura ai mata sallah kawai akaita makwancinta na gaskiya. Cikin wani irin gigita Zaleeha ta ɗaga ƙafanta da niyar ƙarasowa cikin falon, Baba Malam ne ya ɗaga mata hannu, alaman dakatarwa, kanta ta shiga jujjuyawa tana kallon gawar Adda Maryam ɗin, take ta saki wani irin firgitaccen kuka mai tsananin ƙarfi, tare da sulalewa anan jikin ƙofan falon, tana wani irin kuka mai tada hankali. Daga Ya Ahmad zuwa kan sauran ƴan uwanta kuwa babu wanda ya dubeta, dai-dai za afita da gawan Adda Maryam ɗinne, Ya Ameenu yasake sakin wani irin kuka mai tsuma zuciya, take kuma sai wani irin jiri ya ɗebesa haka yatafi luuu, ya faɗi ƙasa sumamme, abun daya ƙara ɗaga hankalin su Baba Malam kenan, Cikin kuka Baba Malam yace amiƙo masa ruwa, Zakariyya wanda ke kuka sosai ne ya miƙowa Baba Malam ɗin ruwa, nan Baba Malam ya ɗan yayyafa ruwan akan fuskar Ya Ameenu'n, saida ya ɗauki kusan mintuna 7 bai farfaɗo ba koda ya farfaɗo kuwa da wani irin kuka mai tsanani ya tashi, kuka yake sosai tare da rirriƙe Baba Malam yana nuna masa gawar Adda Maryam, Wannan abun shiya ƙara sanya gaba ɗaya mutanen falon kuka, cikin kuka Baba Malam yasanya hannu ya dafa kafaɗan Ya Ameenu'n, cikin matsanancin tausayawa yace. "Muyi haƙuri Ameenu, kada rasuwar Maryam yasa imaninmu gushewa, tabbas duk wani me rai mamaci ne, mutuwa bata barin wani dan wani, da ace tana bari kuwa da ta barmana Maryam, kayi haƙuri ka tuna da wasiyan da ta barmaka, kacika mata wasiyarta, katashi muje asallace ta, kasata acikin kabarinta kamar yanda ta buƙata." Zaleeha dake durƙushe tana kuka, duk abun dake faruwa akan idanunta, hakanne yasa ta ƙara gigicewa, kuka take jikinta na tsuma, ko ina na jikinta rawa yake. Ya Ahmad dake kuka sosai idanunsa gaba ɗaya sun kunbura sunyi suntum, shi ya riƙo Ya Ameenu, Haka duk jama'an dake cikin falon suka mimmiƙe, Zaleeha dake durƙushe bakin ƙofa ganin za a fita da gawan Adda Maryam ɗin yasa,ta sakin wani irin gigitaccen ƙara me ɗauke da kuka, zubewa tayi awajen takama ƙafan Yaya Fahad, da kuma na Yaya Sudais, wato ƙannen Ya Ameenu kenan, wanda suke ɗauke da gawan, sai kuma wasu abokan Baba Malam na kusa, cikin fusata Ya Fahad da Sudais suka ƙwace ƙafafunsu, dan kuwa gaba ɗaya family'n cike suke da baƙin cikin ta, haka tanaji tana gani suka fita da gawan Adda Maryam, Wani kukan kuma ta sake wanda yafi kowanne zafi, haka Baba Malam da kuma sauran jama'an dake cikin falon suka tsallake Zaleeha suka wuce, Ya Ahmad ne yayi fitan ƙarshe, cikin matsanancin kuka Zaleeha ta kama ƙafan Ya Ahmad ɗin tana wani irin kuka, cikin matsanancin kukan da yake cinsa ya ƙwace ƙafarsa, tare da wucewa ko waiwayenta baiyi ba. Wannan dalilin yasa ta soma buga kanta ajikin bango tana kuka, mai ɗauke da fitar hayyaci. Acan waje kuwa ana fita da gawan nata, jama'a suka soma kimtsawa, Baba Malam shikansa ya shiga mamakin irin yawan mutanen da sukazo sallan jana'izar Maryam ɗin, saboda mutanene da yawa kamar ƙasa, ga wanda baisani ba ma zai iya cewa wani babban malami ko kuwa babban ɗan siyasa ne ya rasu, dan jama'an sun zarce tunaninsa, daga gidan su Saifuddeen kuwa babu wanda baizo ba, kama daga kan Saifudeeen, Ahmad, Dr Adnan, Bappa Ali Malam Ashiru Hayatuddeen, Harma dasu Wareesu abokan Saifudeen gaba ɗaya sunzo, ga Ishaq ma da Babansa Dirankadi da ƙananinsa Imran duk sunzo. Haka akayiwa Maryam Sallah, nan aka ɗauketa aka sata acikin motan gawa, Dayawansu kuka suke me tsuma zuciya, haka dai waƴanda zasu rakata zuwa maƙabarta suka shiga cikin motocin da zasu tafi, ciki kuwa harda Ahmad da Dr Adnan da kuma Hayatuddeen, Saifuddeen kuwa anan ƙofar gidan suka zauna, saboda shi bazai samu zuwa maƙabartan ba, saboda larurarsa. Acan cikin gida kuwa, Zaleeha har yanzu na zaune anan bakin ƙofar falon na Baba Malam, tana wani irin kuka, tariga da ta zauce, gaba ɗaya ta shiɗe bata wani cikin hayyacinta, wani irin kuka take wanda duk wani wanda ke cikin hayyacinsa dole ya tausaya mata, tun muryarta na fita har ya zamana kukan kawai takeyi, idanunta sunyi wani irin kumbura, fuskarta tayi jajur, cikin haka numfashinta ya soma ƙoƙarin ɗaukewa, duhu ne ya soma rufe ganinta, take kuwa ta sulele ƙasa daga durƙushen da take, lokaci guda numfashinta ya ɗauke, haka dai takejin kanta kamar ba aduniya take ba. Sama da mintuna 20 ta ɗauka batare datasan inda hankalinta yake ba, harzuwa wannan lokacin kuwa babu wanda yazo yabi ta kanta, zafin ranan dake dukan jikinta shine abunda yasanya taɗan buɗe idanunta wanda suka wani irin ƙanƙancewa, hawayene suka kwaranyo daga cikin idanun nata, ahankali ta tashi inda ta jingina bayanta da jikin ƙofan falon, kuka ta fashe dashi tare da dafe saitin ƙirjinta wanda keyi mata zafi. Aunty Lubna da tazo wucewa ne taga Zaleehan ahaka, ɗan tsayawa tayi tana meyi mata kallon mamaki, ganin Aunty Lubna yasa tasoma yunƙurin tashi dan zuwa ga Aunty Lubna'n, cikin sauri Aunty Lubna taja baya, hawayen dake cikin idanunta ta share, ɗauke kanta tayi daga kallon Zaleehan taci gaba da tafiyanta. Abun daya ƙara sautin kukan Zaleehan kenan, nan ta zube akan guiwowinta tana kuka, gaba ɗaya aduniya babu inda zata shiga taji sanyi, kowa fushi yake da ita, gaba ɗaya danginta sun ƙita, harma da wanda take tunanin zasuji tausayinta, sun nuna mata fushi alokacin da take tsananin buƙatarsu. Acan maƙabarta kuwa, Baba Malam da Ya Ameenu ne suka sanya Adda Maryam cikin ramin ƙabarinta, shikuwa Ya Ameenu zuwa yanzu gaba ɗaya hawayensa sun kafe, idan kuwa ya maka kallo ɗaya bazaka so ya ƙara ba, saboda gaba ɗaya idanunsa sun rune, sun zama jajur kamar wanda aka watsa masa garin barkono, zuwa yanzu yadaina tunanin komai, haka ya zama kaman mutum mutumi wato, statue, hatta da buɗe bakinsa baya iyawa, lokaci ɗaya yazama wani iri dashi, cikin rana ɗaya yayi wani irin muguwar rama, suna gama bunneta suka soma ƙoƙarin barin maƙabartan, amma me Ya Ameenu zama yayi anan bakin kabarin nata, da ƙyar su Malam Adam da Dirankadi suka lallashesa, Ya Ahmad dake wani irin kuka ne ya kama hannun Ya Ameenun suka fito daga maƙabarta'n, dan kuwa Ameenun yazama kamar wani ƙaramin yaro, ba ya um baya um um saidai shiru kawai, harkuwa suka shiga cikin mota bai daina kallon kabarin Maryam ɗin ba. Dahaka suka nufo gida. Suna ƙarasowa ƙofar gida kuwa suka samu ankakkafa manyan runfuna, nan suka zauna ko cikin gida basu shiga ba, dan amsar gaisuwa, Baba Malam wanda da taimakon addu'o'in da yakeyi, yaji zuciyarsa ta ɗan samu salama, duban Zakariyya, dake zaune abayansa yayi, cikin muryarsa dake nuna tsananin ɓacin rai yace. "Zakariyya kaje kacewa Zaleeha ta fice min daga gida, bana buƙatarta, kome kama da da ita bana buƙata, matuƙar bata fitamin daga gida, nan da mintuna goma ba, Allah Ya isa bazan taɓa yafe mata ba." Hankalin Zakariyya ne ya tashi, take yaji wani kuka ya taso masa, shikenan zai rasa ƴan uwansa har guda biyu alokaci ɗaya, amma ya sani kome ya faru da Zaleeha ita ta jama kanta. Nan ya miƙe cikin sanyin jiki, ya nufi cikin gidan. Haryanzu tana nan adurƙushe kaman yanda suka fita suka barta tun da farko, kuka take harda majina, kaman ranta zai fita, fuskarta gaba ɗaya tayi jawur. Ƙarasowa inda take Zakariyya yayi, muryarsa asanyaye ya ƙira sunanta. Ɗago kanta tayi ta kalleshi, da idanunta wanda ko gani sosai basayi, kai Zakariyya ya girgiza tare da kawar da kansa gefe, cikin shanye kukansa yace. "Baba Malam yace kifita masa daga gidansa, idan kika kara wasu mintuna sama da mintuna 10 acikin gidannan yace. Allah Ya isa baiyafe ba." Cikin matsanancin tashin hankali Zaleehan ta riƙo hannun Zakariyya, cikin muryarta wanda ta dashe saboda kuka tace. "Nashiga Uku, Zakariyya ya zanyi, ina zanje? nima Zakariyya mutuwa zanyi, bazan iya jure wannan baƙin cikin ba, kowa guduna yake kowa baya sona, waƴanda nake tunanin zasuji ƙaina, sunyi watsi dani, Adda Maryam ta rasu ta barni, Zakariyya bansan inda zanje ba, bani da kowa sama daku aduniya!.." Taƙare maganar tana tsananta kukanta, kai Zakariyya ya girgiza mata hawaye na fita daga idanunsa yace. "Kina dasu mana Adda Zaleeha, kina da wasu bayan mu mana, dan da ace kinsa azuciyarki cewa baki da wasu bayan mu, da baki gudu kin bar Mahaifinmu da mu kanmu acikin baƙinciki ba, ki koma inda kika fito, ki koma cikin arna'n da kika zaɓesu sama damu." kanta ta shiga girgizawa, cikin kuka tace. "Bazan iya jurewa ba Zakariyya, inama mutuwa tazo ta ɗaukeni, inama da ace mutuwa ni ta ɗauka ba Adda Maryam ba, kamar yanda Baba Malam ya faɗa, wayyo Allah na, ya Allah ka ka kawo min ɗauki a rayuwa ta!!!." tafaɗi maganar tana wani irin kuka, Zakariyya ma fashewa da kuka yayi, dan kuwa yana matuƙar jin tausayin Yayartasa, saidai kuma laifin da ta aikata kowa ya sani me girma ne. Dai-dai lokacin Malam Adam ya shigo cikin gidan, bayansa wasu baƙine, wanda zai sauƙesu anan falon na Baba Malam, ganin Malam Adam yasa ta rarrafa, ta faɗi agabansa, cikin kuka tace. "Dan Allah Daddy kataimakeni, (Daddy shine sunan da suke ƙiran Malam Adam ɗin dashi.) Baba Malam yayi fushi dani ya koreni, dan Allah kabashi haƙuri!!." Fuska Malam Adam ya haɗe, cikin cushewar murya yace. "Babu abun da zan iya miki, ba haƙurin kuma da zan bashi, abun da kika shuka shikike girba." Daga haka yasa kai ya wuce cikin falon, baƙin nasa suka rufa masa baya. Cikin kuka Zaleeha ta miƙe tsaye, duban Zakariyya tayi, sai kawai ta faɗa jikinsa ta saki wani irin fitinannen kuka, shima Zakariyyan kuka ya saka, tare da rungume ta, jin tausayinta yake kamar zai fasa masa zuciya. Saida tayi kuka sosai kafun Zakariyya ya janyeta daga jikinsa, cikin sheshsheƙan kuka yace. "Lokaci yana daɗa ƙurewa ki tafi kawai." Juyawa yayi cikin sauri yana kuka ya nufi boys guater. Cikin kuka haka ta nufi ƙofar fita daga gidan, kasancewar wajen gidan cike yake da jama'a, hakan yasa tabi ta ƙofar baya, tana cire ƙafanta daga cikin gidan tasaki wani irin kuka, haka ta miƙi titi, ta fiya take tana gauraya hanya, hawaye kuwa wani na koran wani akan fuskarta, gaba ɗaya ta fita hayyacinta, tayi wani wujiga-wujiga da ita, batasan inda zataje ba, bata da kowa aduniya bayansu da Adda Maryam na raye nema tasan ko duk zasu tsaneta ita bazata tsaneta ba, kuma tasan ko Ya Ameenu baya so zata bata mafaka kuma da Adda Maryam ta roƙa mata gafara wurin mahaifinsu, sukaɗaine gatan ta, gefe guda kuwa ga ƙafanta wanda taji ciwo har ta ɗan kumbura, ga wani busashshen jini da ya zauna akan fatarta. Tafiya kawai take batare da ta san inda ta dosa ba, Jin an riƙe hijabinta ta baya yasanyata juyowa, Zakariyya ta gani hakan yasa ta fashe masa da wani sabon kuka, hannunta Zakariyya'n ya kama, suka ci gaba da tafiya, kasancewar unguwar tasu ta masu kuɗi ce, hakan yasa ko masu abun hawa irin na hayan nan basu cika shigowa sosai ba, sun ɗanyi tafiya, kafun Zakariyya ya hango wani mai adai-dai-ta sahu, wanda ya kawo wata mata, hannu Zakariyya yasa ya tare mai adai-dai-ta sahun, mai adai-dai-ta sahun na ƙarasowa gabansu, Zakariyya ya shiga cikin napep ɗin, tare da jawota itama ta shigo, har zuwa lokacin kuka take, sannan kuma yana riƙe da hannunta, duban me napep ɗin Zakariyya yayi asanyaye yace. "Malam Shango estate zaka kaimu." Kai me napep ɗin ya jinjina, sannan ya tada keken suka tafi. Ɗaura kanta akan kafaɗan Zakariyyan tayi, tare da sanya hannu ta dafe ƙirjinta dake mata zafi, nunfashinta nata ƙoƙarin yankewa saboda kukan da tayi har ta godewa Allah. Koda suka ƙarasa Shango Estate ɗin anan ƙofar haɗaɗɗen sabon gidan Hajja Inna aka sauƙesu, Zakariyya ne ya ciro kuɗi ya bawa me napep ɗin, yana riƙe da hannun Zaleeha ya tura ƙofar gate ɗin gidan ya shiga, jin motsin buɗe ƙofa yasa me gadi dake kishingiɗe ya taso da sauri, ganin Zakariyya ne yasashi sakin numfashi ya koma ya zauna, Zakariyya kuwa yana riƙe da hannun Zaleehan har zuwa jikin bakin ƙofar da zata sadasu da babban falon gidan, key yaciro daga cikin aljihunsa ya buɗe ƙofar, sannan yaja Zaleehan suka shiga ciki. Akan kujera ya zaunar da ita, tare da ƙarasawa gaban fridge, goran ruwa me sanyi ya ɗauko sannan yazo ya aje mata agabanta, dubanta yayi cikin sanyi yace. "Ki zauna anan, tunda Hajja Inna batanan tana can gida, wata ƙila gobe idan kika koma Baba Malam zaiyi haƙuri ya yafe miki". Kuka ta fashe dashi tare da faɗawa jikin Zakariyya'n, cikin kuka tace. "Na cuci kaina Zakariyya, nadasawa ƴan uwana baƙin ciki da ɓacin rai, nayi nesa da ku gashi har Adda Maryam tarasu batare da mun sake ganawa ba, lokacin dana tafi taƙira wayana, yafi sau 20 amma ban taɓa ɗagawa ba, kowa yaƙini sai bayan nayi wata biyu a can na fara amsa kiranta Zakariyya kai kaɗaine kaji tausayina, ya zanyi Zakariyya idan Baba Malam be yafemin ba, ya zanyi?". Kukane yaci ƙarfinta sosai. Zakariyya ma kukan yake. Zamewa yayi ya zauna tare da ɗaura kanta akan cinyarsa, ganin haka yasa ta takure jikinta waje ɗaya, nan tashiga rera sabon kuka, ita tanayi Zakariyya nayi, an rasa me rarrashin wani acikinsu, tayi kuka kam bana wasa ba, ita kanta bazata iya faɗin yaushe ne kuma tayaya ne, bacci ya ɗauketa ba, haka tayi bacci kanta nakan cinyan Zakariyya, yin baccin nata kuwa bairasa nasaba da irin kukan da tasha ta ƙoshiba, saboda yawan kuka nasanya mutum bacci, batare daya shiryawa hakan ba. Ganin tayi bacci yasa Zakariyya zame jikinsa, pillown kujera ya ɗauka ya ɗora mata kanta akai, dubanta yayi, bacci take amma kuma sheshsheƙan kuka take tayi, hawayen da suka zubo daga cikin idanunsa ya goge, sannan ya tashi ya fita daga falon, kaitsaye ya koma gida. Ita kuwa Zaleeha ko mintuna 20 batayi tana baccin ba, azabure tatashi, ganin bataga Zakariyyan ba, yasata dasa wani sabon kukan. Tayi kukan tayi kukan harsaida taji kamar ma ba aduniya ta ke ba, ciwon kai kuwa ba'a magana, domin saboda tsabar ciwon da kanta keyi mata, har wani dishi dishi take gani Haka dai ta zauna agidan idan tayi shiru yanzu anjima kuwa tayi kuka, da ƙyar ma ta iya tashi tayi sallah. Tana nan tana kuka har dare ya rufa, yanda taga rana kuwa haka taga dare, ko lumshewa idanunta batayi ba, balle bacci ya ɗauketa, batun ciwon kai kuwa sai abun da yayi gaba, dan kuwa zuwa yanzu harwani ji take kaman kannata ya kumbura, saboda tsabar ciwo da yakeyi mata. Haka ta kwana azaune tana karatu qur'an da kuka har gari yayi haske. Nan dai daga falon babu inda ta gusa, banda toilet da ta shiga ta ɗauro alwala, tana nan zaune Zakariyya ya buɗe kofar falon ya shigo, ganin yanda idanunta suka kumbura kana sukai jajur yasa shi ɗan zaro idanunsa, cikin sauri ya ƙaraso cikin falon, agabanta ya zauna tare da aje ƴar ƙaramar kulan dake hannunsa, hankalinsa amatuƙar tashe yace. "Kwana kikayi kina kuka ko?." Yafaɗa yana me sanya hannunsa ya share mata hawayen dake kan fuskarta, kulan da ya shigo dashi ya buɗe, soyayyen dankali da ƙwai ne, sai sauce ɗin egg, turo mata kulan gabanta yayi, cikin tausayawa yace. "Waima rabonki da abinci tun yaushe ne Adda Zaleeha? kici wannan abincin kinji." Kanta ta girgiza masa, cikin da shashshiyar muryarta tace. "Banajin zan iyacin wani abu Zakariyya, bana buƙatar komai yanzu a duniya sai yafiyan Baba Malam, tayaya kake tunanin zan iya sakawa cikina abinci a airin wannan halin da nake ciki? bazan iya ba, ka kaini kawai naje nasake bawa Baba Malam haƙuri, hakanne kaɗai zaisa naji sanyi araina." Hawayen tausayinta ya share, sannan ya kamo hannunta, cikin sanyin murya yace. "Taso muje." Nan ta miƙe yana riƙe da hannunta yazama kaman shine yayanta ita kuma ƙanwarsa, haka suka fita daga gidan, tafiya kaɗan sukayi suka samu napep. Aƙofar gidan ta baya Zakariyya yace da me napep ɗin ya sauƙesu, duban Zaleehan Zakariyya yayi, cikin sanyi yace. "Kije Baba Malam shida su Mamy suna falonsa, nikam zan shiga ta babban ƙofa kar agane tare muke dake, nasan fushin da Baba Malam keyi dake zai iya shafana." Kanta ta jinjina tana me share hawayenta, nan ta nufi cikin gidan, shikuwa Zakariyya ya sallami me napep ɗin ya tafi. Jikinta amatuƙar sanyaye haka ta shiga cikin gidan nasu, dayawan familynsu na cikin gida, na zaune a compund ɗin gidan, ganinta yasa gaba ɗaya duk suka tsaya kallonta, kanta aƙasa tana me zubar da ƙwalla haka ta nufi sashin Baba Malam, jikinta asanyaye ta kai hannunta jikin ƙofar falon ta buɗe, Baba Malam, Malam Adam, Ya Ameenu, Ya Habu, Mamy, Ya Ahmad, da kuma Mama sai Goggo Maryama, sune zaune afalon, sunyi jigum, gefe kuwa wani babban abokin Baba Malam ne wanda yazo tundaga Kaduna, dan yi musu ta'aziyya, Ganin Zaleehan yasa Baba Malam rumtse idanunsa, Itakuwa Zaleeha ƙarasowa tsakiyar falon tayi, nan ta zube akan guiwowinta, tare da sakin wani irin fitinannen kuka, cikin kukan ta soma rarrafawa, dan ƙarasawa wajen Baban nata, cikin sauri Baba Malam ya ɗaga mata hannu, ransa amatuƙar ɓace yace. "Idan kika sake kika taɓani banyafe miki ba, banason ganinki kifitamin daga gida!" Yafaɗi maganar yana me yi mata nuni da ƙofar fita. Hankalinta ne yasake tashi, take taji komai ya dawo mata sabo, cikin wani irin matsanancin kuka, ta rarrafa zuwa gaban su Mamy, azauce take matuƙa, cikin matsanancin kuka ta kamo hannun Mamy dana Goggo Maryama, amatuƙar gigice cikin tsananin kuka murya na rawa tace. "Dan Allah Mamy Goggo Maryama ku bawa Baba Malam haƙuri, wallahi aduniya bani da kowa sama daku, Mamy dan Allah kibasa haƙuri na tuba ku yafe min." Hawayene suka zubo daga idanun Mamy na tausayin Zaleehan to amma itama, bata da ikon buɗan baki tace da Baba Malam ɗin yayi haƙuri, Goggo Maryama kuwa ma ɗauke kanta tayi gaba ɗaya, ganin haka yasa Zaleeha rarrafawa ta nufi wajen Ya Ahmad, cikin sauri Ya Ahmad ɗin natama ya miƙe batare daya bari ta iso wajen ba, ya nufi can cikin ɗakin Baba Malam ɗin, Allah yasani shi zuciyarsa me rauni ce akan Zaleeha, ko a jiya kukanta daya ganine yaƙara masa nasa kukan, sannan kuma awannan karan shi kansa baida wani hurumin bawa Baba Malam haƙuri akan ya yafe mata, ganin Ya Ahmad ɗin ya tashi, yasa Zaleeha sakin firgitaccen kuka, Mama ma kukan take sosai, wanda gaba ɗaya zuciyarta nadama da dana sanine ne ya cinye, dan har kunyan haɗa idanu dasu Baba Malam ɗin takeyi. Kallon Ya Habu Baba Malam yayi, cikin ɓacin rai yace. "Habu fitarmin da ita daga falo na da gida na baki ɗaya." Tsam kuwa Ya Habu ya miƙe, hannunsa yakai ya damƙi hannun Zaleeha'n, haka ya jata yana ƙoƙarin fitar da ita daga falon, kuka take sosai har numfashinta na sarƙewa, sam Ya Habu baiji tausayinta acikin ransa ba, saboda har yanzu bai manta da irin baƙincikin da ta shayar dasu ba, asanadin ɓacin ranta, har Baba Malam saida ya kwanta jinya, shine yanzu zata zo da wani kuka tace a yafe mata. Zakariyya kuwa ganin an fito da Zaleeha'n, kamar wata wanda ba ƴar gidan ba, yasashi fashewa da kuka, nan ya lallaɓa ya fita, dan zuwa ya sameta, Ya Habu kuwa ƙofa ya buɗe, ya turata waje, sannan ya jawo ƙofar gidan ya rufe, sulalewa tayi ajikin ƙofar tare da sakin wani irin marayan kuka, dai-dai lokacin Zakariyya ya ƙaraso, hannunta ya kamo, tare da jawota jikinsa ya rungumeta, ahankali yake ɗan bubbuga bayanta, shiɗin ma kuka yake sosai. Cikin sheshsheƙan kuka tace. "Bani da inda zanje Zakariyya, Baba Malam ya tsaneni, yasa Ya Habu ya koreni kamar karya, ko ganina bayason yi, wayyo Allah ni Zaleeha ina zansakana kai da rayuwata! Wa zan samu ya tayani bawa Baba Malam haƙuri,tunda kowa yaƙi ya saurareni" Cikin kuka Zakariyya yace. "Mafita ɗayace Adda Zaleeha,." Cikin tsananin kuka murya a disashe tace. "Menene mafitan me zanyi in samu Baba Malam ya yafe min ne Zakariyya?". Hawayenshi ya share tare da cewa. "Mafitar kuwa itace baki da wajen zuwa wanda ya wuce gidan su Hayatuddeen, wallahi na tabbata mutum ɗayane zai roƙi Baba Malam akan ya yafe miki, kuma ya aminta ya yafe miki ɗin a sauƙaƙe." Cikin disashewar murya tace. "Waye ne?." Gyara tsayuwanshi yayi tare da cewa. "Bakowa bane kuwa wannan mutumin face HAMMA SAIFUDDEEN, na tabbata idan kikazo da Hamma SAIFUDDEEN to Baba Malam zai yarda ya yafe miki." Cikin kukan ta shiga jinjina kanta. Murya na rawa tace. "Nayarda zanje koma inane, matuƙar Baba Malam zai yafemin, zanje shima in bashi haƙuri dan Allah Zakariyya ka kaini gidan su Hamma Saif ɗin kaji." Kai Zakariyya ya girgiza, cikin tausayinta yace. "Bazan iya zuwa ba. Sam bazan iya kaikiba Adda Zaleeha, saboda bansan da wani idon zan kallesu nace nadawo musu dake ba, ke kikayi amanki saboda haka ke zaki lashe abunki ke ɗayanki, ke kaɗanki kika gudu kuma ke kaɗanki zaki koma da ƙafarki zakije ki shiga gidan dai da kika gujewan ki kwashi kayan kunyanki". Yana gama faɗin haka ya tara mata wani mai adai-dai-ta sahu, sam bata fahimci ma me yake cewa ba, ita dai burinta kawai shine ta samu me baiwa Baba Malam haƙuri. Zakariyya ne ya faɗawa mai napep ɗin inda zai kaita, tare da zaro kuɗinsa ya basa. Ko acikin napep ɗin kuka take sosai, batasan cewa girman fushin da ƴan uwan nata sukayi da ita har yakai haka ba. Koda mai napep ɗin ya sauƙeta a bakin gate ɗin gidan Saifuddeen, ido ta zubawa gidan da data gujewa kusan shekara ɗaya kenan. Toma me matsayinta a gidan? Me sunanta? Matar gidan ko baƙuwar gidan? Da waɗanne idanun zata kallesu? Me zata cewa Ummi dottijiyar mata mai tarin mutunci da kima a idonta, me zata ce mata meyasa ta gudu? tace mata bata son ɗanta na cikinta ne ko meye? Ina zata ce musu taje? Da izinin wa ta fita? Zasu saurareta ma kuwa? Gaba ɗaya tsoro da fargaba da kunya da ƙuncin zuciya da rayuwa da nadama da danasani sun rufeta, fuskar nan tayi tib-tib tayi jazir idanun duk sun ƙanƙance, a hankali take jan ƙafarta har ta isa baki ƙofa, hannu tasa ta ƙonƙosa, Da sauri mai gadinsu yazo ya buɗe mata ƙofar, ganin matar mai gidan ne dan bai mancetaba, da sauri ya bata hanya tare da cewa. "Hajia barka da hanya. An dawo lfy?". Kai kawai ta iya gyaɗa mishi a wani sashin na zuciyarta kuwa ta ɗanji sauƙin tsoronta na kada su Ummi su koreta, taku takeyi a hankali yayinda hawayenta ke kwaranya, jin muryar mai gadin nasu na cewa. "Ya mukaji da haƙuri Allah ya jiƙanta da rahma". a hankali tace. "Amin Amin." kana ta ci gaba da nufar sashin Ummi. Acan cikin gidan Hamma Saifuddeen kuwa Gabaki ɗayansu suna tare a falon Ummi, banda Ameena wanda tun da sassafe data dawo ta ɗan huta so ta koma dan zasuyi wani taro da manyansu shiyasa tatafi wajen aiki, Saifuddeen, Ummi, Ahmad, Raliya, Hayatuddeen, sai kuma Adda Rahama, wanda dawowanta kenan daga gidan su Zaleehan, inda taje tayi musu ta'aziyya, yanzu ma zaune suke suna ƙara jajanta rasuwan Maryam ɗin, duban Ummi Adda Rahama tayi kana tace. "Wallahi Ummi na tausayawa Ya Ameenun su Zaleeha ƙwarai, domin tabbas yayi rashin mace ta gari, kinga fa ko ranan nan nakaiwa Abban su Akih abinci, kasancewar yana sauri, hakan yasa ya fita batare da yayi break fast ba, nan asibitin nasu na haɗu da ita taje awu, ashe haɗuwan mu na ƙarshe kenan, Allah sarki Maryam, wallahi mace ce me hankali da nutsuwa, babu ruwanta, ta iya zama da mutane, kowa nata ne, gata da fara'a da kuma kyautata wa, insha Allah halinta na gari zai bita, Allah Ubangiji kuma ya jiƙanta da rahama." Nan suka amsa da Ameen su dukansu, Hayatuddeen kuwa, miƙewa yayi daga zaunen da yake, kaitsaye yafice daga falon, so yake yaɗanje shagon nan dake ƙarshen titin gidan nasu ya sayo rechard card. Dai-dai ya kawo ƙofar fita daga falon, ita kuma Zaleeha ta kawo kai, hakan yasa sukayi karo da juna, da sauri yaja baya, idanunsa ya waro cike da mamakin ganin Zaleehan agidansu. Ita Zaleeha kuwa idanu ta ƙura masa, hawaye na bin fuskarta, lokaci guda kuwa Hayatuddeen ya sanja fuska, tare da ɗauke kansa, yi yayi ma kamar baisanta ba, kana ya raɓa ta gefenta ya wuce, batare da yace da ita ƙala ba, hakan ne yasa jikin Zaleehan yayi wani irin mugun sanyi, take kuma hawayenta suka ƙaru fargaba da tsoro ya ƙara rufeta, haka dai da ƙyar take iya ɗaga ƙafafunta ta nufi cikin falon Ummi zuciyarta na duka tara-tara, koda ta ƙarasa bakin ƙofar shiga falon, hakanan taji ƙirjinta na wani irin bugu, kuka ne me ƙarfi keson ƙwace mata, cikin wata irin dashashshiyar murya wanda bata fita sosai tayi sallama, tare da shigowa cikin falon!. Cikin mamaki su duka suka ɗago kansu suna kallonta kusan a tare sukace, "Laaaaa." Saifuddeen ne ya fara ganinta, kasancewar dama shi yana facing ɗin ƙofar shigowan falon ne shiyasa ya rigasu ganinta. Taku ɗaya tayi tana ƙoƙarin shigowa cikin falon Saifuddeen yayi wani irin tsuke fuska cikin yanayin zafi ya ɗaga mata hannu, alaman dakatarwa. Hawayen dake cikin idanunta ne suka kuma gangarowa har zuwa kan ƙirjinta kai ta fara jujjuyawa cikin kiɗima ganin ya ɗago, Hannunsa ya yana me yi mata alama akan cewa kada tayi kuskuren shigowa cikin falon, ta koma inda ta fito. Wani marayan kuka ta saki tare yayyarfa hannu alamun bata cikin haiyacintama bisa alamu duk a gigice take. Dubansa Ummi tayi tare da cewa. "Lafiyanka kuwa Saifuddeen, akan me zaka koreta?" Rumtse idanunsa yayi tare da girgizawa Ummin nasa kai, alaman cewa bayason ganin Zaleehan. Kukan daya zo mata ne takasa dannewa, hakan yasa ta sakeshi da tsananin ƙarfi a hankali jiki na rawa ta shiga takowa, tana ƙarasowa gaban Ummi. Ganin halin da take cikine yasa Ummi miƙo mata hannu alamun tazo. ai kuwa ganin haka yasa da sassarfa ta ƙaraso gaban Ummi cikin kuka ta zube akan guiwowinta, tare da ɗaura kanta akan cinyar Ummin, nan ta saki wani irin gigitaccen kuka, mai ratsa zuciya, da kuma ban tausayi, Shiru sukayi gaba ɗayansu falon sai sautin kukan Zaleeha'n ne kawai ke tashi, wanda hakanne ya sanya gaba ɗaya jikin su Adda Rahama Ahmad Raliya yayi sanyi, Kuka take kamar ranta zai fita, cikin kukan tare da sarƙaƙƙiyar muryarta wanda bata fita sosai tace. "Na shiga uku Ummi Baba Malam yayi fushi dani, naje gidansa ya koreni, yace baya ko son ganina, Ummi kowa baya sona, kowa guduna yake, Ummi ya zanyi, yazanyi da rayuwata, Ƴar uwata tatafi ta barni, Babana kuma yana fushi dani, duka ƴan uwana suna fushi dani, ina zansa rayuwata, Ina ma da ace mutuwa ni ta ɗauka ba Adda Maryam ba, ina ma ace mutuwa zata ɗaukeni!!!." ta ƙare maganar tana sakin wani irin gigitaccen kuka, harda shiɗewa. Jin abun da Zaleeha'n ke faɗa ne yasa Ummi taji idanunta sun kawo ƙwalla, wani irin tausayin Zaleehan ne ya kamata, Cikin wani irin yanayi Numfashin Zaleehan ya sarƙe aƙirjinta, Ummi ne tasanya hannu ta ɗan ɗagota, hakan kuwa yayi dai-dai da ɗaukewar numfashinta, take ta tafi luuuu ta faɗi ƙasa summamiya. Hankalin Ummi da su Adda Rahama ne yayi wani irin masifaffen tashi, da sauri sukayo kanta. Ganin Haka yasa Saifuddeen rumtse idanunsa, wanda lokaci guda sukayi ja, bayajin zai iya cigaba da zama acikin falon baya jin zuciyarshi nada ƙarfi da taurin da zata juri ganin halin da Zaleeha ke cikiba, hakan yasa ya danna madannin kekensa, batare dasu Ummi sun farga ba ya fice daga cikin falon. Littafin nan na ƙuɗine By *GARKUWAN FULANI* [14/09, 11:38 am] +234 706 370 3964: Sbpejtt Kai kawai Ummi ta girgiza tare da tashi kaitsaye ta wuce ɗakinta, Hayatuddeen ma dake zaune ji yayi gaba ɗaya jikinsa yayi sanyi, sam baiso hakan ba, yaso ace Hamman nasa ya amince, saboda shima ya gamsu cewa, da taimakon Hamman nashi ne kaɗai Baba Malam zai iya haƙura ya yafewa Adda Zaleeha'n. Haka dai suka kammala cin abincin nasu duk jikinsu asanyaye, acan ɓangaren Saifuddeen kuwa yana barin falon nasa, kaitsaye ɓangarensa ya nufa, sauƙa daga kan wheelchair ɗinsa yayi, tare da haurawa saman ɗaya daga cikin haɗaɗɗun kujerun falon ya kwanta, idanunsa ya lumshe yana jin zuciyarsa nayi masa wani iri, maganganun Ummin ne ya dawo cikin tunaninsa, ahankali ya girgiza kansa, cikin zuciyarsa yace. "Ada ni ba komai bane awajenta, bata ɗaukeni matsayin komai ba, kullum idan akwai wata magana da zai fito abakinta, wanda ta shafeni to baiwuce kalmar ƙiyayya ba, matsalar da ta faɗa ayanzu, shiyasa ta ɗaukeni wani me mahimmanci agareta, ta gudu ne saboda batason aurena, yanzu kuma gashi ta dawo tana zaune aƙarƙashin inuwata, ahaka kuwa shine har da wani neman alfarmarta." wani murmushi me ciwo yayi tare da girgiza kansa, shiba sakarai bane, ita tayi amanta saboda haka ita kaɗai zata lashe. Yana gama tunanin ya gyara kwanciyarsa, tare da sake lumshe idanunsa, yana sakin ajiyar zuciya. Acan ɓangaren Part ɗin Ummi kuwa baccin Zaleeha baiyi wani nisa sosai ba ta farka, Hayatuddeen ne ya kawo mata abinci, haka ya sakata gaba dolen ta saida taci, tana kammalawa kuwa ya miƙo mata ruwa da magungunanta tasha, nan ƙasan carpet ya zauna, ita kuwa tana kwance akan gado, ganin cewa akwai damuwa atattare da itane yasa shi, soma bata labarai wanda yasan dole zasu ɗebe mata kewa, suna zaune ahaka Raleeya ta shigo, akusa da Zaleehan ta zauna, cikin kulawa tace "Aunty Zaleeha ya jikin naki?". ɗan jinjina kanta tayi, asanyaye tace. "Da sauƙi." Murmushi Raleeya tayi, tare da faɗin. "Masha Allah, Allah Ya ƙarasa sauƙi." Da "Ameen" Zaleehan ta amsa, haka dai suka ci gaba da hiransu, Ita dai Zaleeha idanu kawai ta zuba musu, sau dayawa dramer'n Hayatuddeen da Raleeyan na burgeta. Duk dama har yanzu akwai damuwa kwance aƙasan zuciyarta. Suna ahaka Ummi tashigo cikin ɗakin, ganinsu atare ne yasata sakin murmushi, sake gaisheta Zaleehan tayi, ta amsa mata fuska asake, har cikin ranta kuwa taji daɗin ganin Zaleehan cikin ɗan yanayi me kyau, kallon kayan dake jikin Zaleehan tayi, take wani tunani yazo mata hakan yasa tace da Hayatuddeen yazo zata aikeshi. Babu musu ko ya tashi yabi bayanta. Kaitsaye ɗakinta suka wuce, nan kan gado ta zauna, tare da jawo jakarta ta zage zip ɗin, duban Hayatuddeen tayi, cikin kulawa tace. "Makay zan aike ka ne, ko San Hussain Super Market?". ta tambayesa da yanayi na ɗan tunani, zama yayi akusa da ita, tare da cewa. "Wani abu za a sayo miki ne?". "Kaya nakeson kasayowa Zaleeha, kaga dai bata zo da kayanta ba, part ɗin ta kuma akulle yake, na kuma ce Hammanku ya bada key yayimin biris, dama daya ba da key ɗin sai nasa ko Raleeya ne ta ɗebo mata sauran kayanta." cikin zumuɗi Hayatuddeen yace. "Ummi Makay zanje, wallahi dama ina kwaɗayin strowberry cake, kinga kawai sai na shiga Makay shawarma na saya, nasan itama Adda Zaleehan idan na sayo mata zataci." Hararansa Ummi tayi tare da cewa. "To sarkin kwaɗayi, an faɗa maka cewa dama kowa irinka ne, koko ance maka kowa kwaɗayi kawai yasa agaba?." Murmushi yayi, cikin zaƙuwa yace. "Hmm Ummi bakisan wacece Adda Zaleeha ba kenan, ai shan zaƙinta ko shazumami sai haka, yanzu kawo kuɗin naje na sayo mata kayan." Kai kawai Ummi ta girgiza tare da zaro Kuɗin da aƙalla zasu kai 70k, acikin jakanta ta miƙa masa, cikin kulawa tace. "Kanutsu dan Allah Hayatuddeen, dogayen riguna nakeson kasayo mata masu kyau, ni hankalina ma kwata kwata bai kwanta da aikanka ka ba, dan tunda ka iya mota kuma shikenan ka zama ayawo, dan ma ana zaman makokin nan ne da da Zakariyya zakuje, saboda hankalina zaifi kwanciya, saboda ya fika nutsuwa wani lokaci'n." Ɗan bakinsa ya turo gaba, cikin halin sakalcinsa yace. "Yanzu Ummi dan Allah Zakariyya'n ne ya fini nutsuwa." Murmushi Ummi tayi, tana me zuge zip ɗin jakarta tace. "Ni maza yi sauri ka kawomin aikana, sannan kuma katabbatar kayi driving cikin nutsuwa." Haka yafita daga ɗakin yanata wani shagwaɓa, da turo baki gaba, tuno da cewa zaije ya saya strowberry cake yasan yashi sakin murmushi, haka ya fice daga cikin falon, yana karkaɗa ɗan makullin motar dake hannunsa. Zaleeha da Raleeya kuwa har yanzu suna tare, hira Raleeya ke tayiwa Zaleeha'n, ahaka har wani sabon bacci ya ɗauketa, ganin tayi bacci ne yasa Raleeya sakin murmushi, nan tatashi ta fice daga ɗakin dan zuwa kitchine ɗaura lunch. Ummi kuwa ganin fitan Hayautuddeen yasa, ta ɗauki wayarta, text ta turawa Saifuddeen akan cewa tana son ganinsa, tana nan zaune kuwa ko mintuna 7 ba acika ba, sai gashi ya shigo cikin ɗakin. Har gaban Ummin ya ƙaraso da kekensa, sai wani shagwaɓe fuska yake, saboda yasan bai wuce maganan Zaleeha Ummin zatayi masa. Ummi kuwa ɗago kai tayi ta dubesa, cikin nutsuwa tace. "Wai Saifuddeen me kake nufi da Zaleeha ne? tunfa jiya nake binka da ka bani key ɗin ɗakinta amma kaƙi, ko anan kakeso ta zauna mana bayan gacan ɗakinta?" Ɗan kwaɓe fuska yayi, cikin body language ɗinsa yace. "Nifa Ummi bansan inda key ɗin ɗakinta yake ba." gane abunda yake nufi yasa Ummi ɗan buɗe baki, da mamaki tace. "Bakasan inda key ɗin yake ba kuma.?" Kansa ya jinjina alamar "Eh" kuma har ga Allah ya mance inda ya ake key ɗin. Kai Ummi ta jinjina tare da cewa. "Sannu uban maƙaryata, Saifuddeen yaushe ka fara yimin ƙarya? wato ma sokake kace key ɗin ya ɓata ko? hmmm inace nan da Addarku Rahama ta amshi key ɗin tatafi dashi, ko wata ɗaya baicika ba kaje har gidan ta ka amso, ko kana tunanin banida labari ne? kaga tunkan raina ya ɓaci Saifuddeen ka buɗewa yarinyar nan ɗakinta ta koma tayi zamanta." bakinsa ya turo gaba, sam shi baisoma Ummi tanayi masa maganan Zaleeha'n, ai koma me yafaru itace ta jawo, hakanan saboda ta ɗaukesu sakarkaru saita gudu ta kuma dawo alokacin da take so. Kuma zancen gaskiya harga Allah ya mance in da ya ɓoye key ɗin side ɗinta, amman gashi Ummi gani take ƙarya yayimata abinda bai taɓata kwatanta yimataba. Hararansa Ummi tayi tare da ɗanyin ƙwafa tace. "Ayi mutum da taurin kai da riƙo sai kace mutanen farko, wallahi ka tabbatar ka kawomin key ɗinnan tunkan raina ya ɓaci, idan kaƙi kuwa zansa a ɓalla ƙofan da ƙarfi, ta koma ɗaƙinta ta zauna." Idanunsa yaɗan zaro waje, jin cewa za'a ɓalla ƙofar, tuna cewa ma ƙofar bazata taɓa ɓalluwa bane ya sashi ɗan sakin ajiyar zuciya, hannuwansa ya haɗe waje ɗaya, alaman Ummin tayi haƙuri, kuma shi ya mance inda key ɗin yake ne. Haranshi tayi sannan tace. "To batun rakata gidansu ta bawa Babanta haƙurifa ko shima ka mance hanyar gidan ne?". A hankali ya jujjuya mata kai alamun bai mance ba, sai kuma yayi ƙasa da kanshi. Ganin cewa bazai biyu ta sauƙi ba yasa Ummi'n, cewa ya tashi yaje kawai. Yana fita kuwa Ummi tayi ƙwafa tare da cewa. "Ɗan nema zan yi maganinka ne." Daga haka ta-tashi ta wuce toilet dan ɗauro al'walan sallan azahar. Can ɓangaren Hayatuddeen kuwa saboda tsabar kwaɗayi yaci ransa saida ya fara zuwa makay shawarma ya sayi strowberry cake ɗinsa, ya kuma haɗa da roasted fish, saboda yasan Adda Zaleehan naso kuma idan ya kai mata zata ci. Saida ya gama ƙwalamarsa kafun yafito daga Makay Shawarma ɗin, kaitsaye ya nufi cikin Makay Super Market, ɓangaren da dogayen rigunan mata suke ya nufa, sosai ya darje wajen zaɓawa Adda Zaleehan nasa dogin riguna masu kyau, bai tsaya anan ba kuwa harda wasu riga da sket ƴan kanti masu kyau kusan kala uku ya zaɓa mata, haka dai ya gama sayayyyan cikin nutsuwa, sannan ya ƙarasa wajen biyan kuɗi, koda akayi lissafin kayan kuɗin sun haura wanda Ummi ta basa, dan 70k Ummi ta basa, kayan da ya saya kuwa sun haurawa haka, dan kuɗinsu 77k ne, baiwani damu ba, haka ya zaro ATM card ɗinsa dake cikin aljihunsa ya basu, kasancewar dama yana aje ƴan kuɗaɗensa anan cikin asusun banki, dan sau dayawa kuɗin da Hammansa ke basa ba kashewa yake ba, yakan tarasu ne idan sun ɗanyi yawa sai yakai ƙaramin account ɗinsa na bank ba asalin babba da ake sa mishi kason dukiyarsa ba a ƙaramin yake ɗan gutun ajiyarsa, haka dai suka zare 7k ɗinsu suka basa ATM card ɗinsa, daganan kuma suka zuba masa kayan acikin leda. Har mota kuwa sukasa aka kai masa kayan, haka ya ɗauki hanyar gida, sai ciye ciye yake acikin motar. Koda ya ƙarasa gida kuwa, Ummi ya bawa kayan, dan har zuwa lokacin Zaleeha bata tashi abacci ba, babu laifi kuma Ummi ta yaba da rigunan dan sunyi kyau sosai. Saifuddeen kuwa tunda yabar part ɗin Ummi ɓangarensa ya koma, al'wala yayi sannan ya nufi masallaci, tunda yayi sallan azahar kuwa bai dawo gidan ba, Sule driver yaƙira suka ɗan fita, saboda wani aikin daya taso masa, dole saida yaje office ɗinsu, saida aka kusa sallan la'asar sannan ya dawo, anan masallacin ƙofar gidansu yayi sallan la'asar, sannan ya shigo cikin gidan, ɓangaren Ummin nasa ya sake nufa, dan kuwa ɗazu koda yana zaune a office saida yaga text message ɗinta, kancewa "Lallai ya kawo mata key ɗin ɗakin Zaleeha, sannan kuma ya tabbatar yazo yakai Zaleehan gida ta bawa Baba Malam haƙuri." Shidai kam yama rasa yanda zaiyi. Yana shiga falon kuwa ya iske Ummi da Ahmad, sai kuma Hayatuddeen dake zaune ƙasan turkish carpet yana ta faman lodawa cikinsa abinci. Ganin yanda fuskar Ummi take babu wani walwala asamanta yasa yaji jikinsa yayi sanyi, ƙarasowa cikin falon yayi tare da bawa Ahmad hannu suka gaisa, saboda yau duk basu haɗuba. duban Ummin nasa yayi, asanyaye cikin body language ɗinsa yayi mata sannu da gida. Kai kawai ta jinjina masa, ko kallonsa batayi ba, hakanne yasa jikinsa ƙarayin sanyi, sam baisom fushin Ummin nasa. Ummi kuwa da gangan ta nuna cewar tana fushi dashi, saboda tasan idan ba haka tayi masa ba bazai taɓa yin abun da ta sakashi ba. Raleeya wanda shigowarta falon kenan, ganin Hamman nata yasa ta wuce kitchine, abinci da drinks ta zubo masa, saboda yau ɗin favorite food ɗinsa ta dafa. nan gabansa ta ƙaraso tare da ɗan durƙusawa, ƙoƙarin aje plate ɗin abincin agabansa take, cikin sauri yaɗan riƙe hannunta tare da girgiza mata kai, alaman ya ƙoshi, kallon sa tayi fuskarta ɗauke da ɗan damuwa, kansa ya jinjina mata alaman cewa. "Tayi haƙuri bayajin yunwa." Asanyaye ta ɗaga kanta ta kalli Ummi, gani tayi fuskar Ummin atsuke, hakanne yasa ta juyawa ta maida abincin kitchine. Cikin sanyin jiki ya danna madannin wheelchair ɗinsa tare da ƙarasawa gaban Ummin nasa, hannunta ya kamo tare da ɗan shagwaɓe fuska, ɗago kai tayi ta dubesa. Rau-rau yayi da idanunsa, tare da yi mata alama kancewar "Tayi haƙuri karta ce zatayi fushi da shi." gane hakanne yasa Ummi ta sake haɗe fuska, tare da ɗan kau da kanta gefe, cikin haɗe fuska tace. "Idan ma nayi fushi dakai ae kai ka nema, meyasa zanta maimaita maka magana ɗaya, amma ka kasa aiwatarwa, tunjiya naketa binka, akan maganan key ɗin ɗakin Zaleeha, sannan ga kuma maganar rakata ta bawa Babanta haƙuri, amma gaba ɗaya ka share maganta, bansan yaushe kazama haka ba Saifuddeen, bansan kuma meke damunka da har yasa ka kasa jin tausayin Zaleeha acikin ranka ba, To Wallahi matuƙar ba ɓacin raina kakeson gani ƙiri-ƙiri ba, tun wuri kaɗauki yarinyarnan kuje ku bawa Baba Malam haƙuri, tun da dai idan har dakai taje, baban nata zai iya yafe mata." Idanunsa ya rumtse, lokaci guda yaji zuciyarsa na bugawa da ƙarfi, ɗanjan kekensa baya yayi, tare da zamewa ya durƙusa akan guiwowinsa, sake kamo hannun Ummin nasa yayi, lokaci guda ya shiga girgiza mata kai, sosai rauni ya bayyana akan fuskarsa, cikin body language ɗinsa yace. "Dan Allah Ummi kiyi haƙuri, ki bani ko wani irin umarni ne zan bi, sannan kuma bazan taɓa bijiremiki ba, amma dan Allah kada ki tursasani kan cewa na raka Zaleeha ta bawa Baba Malam haƙuri, idan nayi hakan Ummi zan cutu, tunda batasan ina da ƙima ba sai yanzu da matsala ta taso mata? kuma ma Ummi lokacin da tayi lefinta tare dani tayi ne? ai ita kaɗai tayi lefinta, da tazo guduwa kuma bata shawarceni ba, tanajin cewa ta isa shiyasa ta gudu alokacin da takeso, ta kuma dawo alokacin da takeso, ni nasan sam bata shirya yin nadama ba, kawai dan rasuwar Adda Maryam ne, amma bacin haka ai bazata dawo ba." Dubansa Ummi tayi tare da ɗan girgiza kai, sam bata taɓa tunanin cewa wai Saifuddeen zaiyi fushi akan maganar Zaleeha ba, amma babu komai tayi masa uzuri, saboda tasan ba har zuciyarsa maganar da yake faɗi take fitowa ba, gyara zamanta tayi, cikin son nusar dashi da kuma yanda zai fahimta tace. "Koma me Zaleeha ta maka, bai kamata kayi irin wannan fushin da ita ba, sannan kuma kaima shaida ne akan irin damuwar da take ciki, ca nake jiya anan gabanka ta suma, ko so kake mu barta haka, mu zuba mata idanu ciwon zuciya ya kamata? ko kuwa so kake mubar rayuwarta cikin garari?, kakuwa san halin da take ciki? bata da wani abunyi sai kuka dare da rana, bata da wani sauran farinciki, da wanne zataji, mutuwar ƴar uwarta ko kuwa ƙunci da baƙin cikin rayuwa? ko Allah ma muna masa laifi me girma, amma damunyi kyakkyawan tuba yake yafe mana, saboda meyasa to mu bazamu yafe mata ba?." Rumtse idanunsa yayi da ƙarfi tare da tattauna lips ɗinsa, sosai yakejin wani abu azuciyarsa, wanda shikansa bazai iya fassara sa kaitsaye ba. Raleeya wanda tuni idanunta sun ciko da ƙwalla ne ta ɗan matsa kusa da Ahmad, cikin sanyi tayi masa alamar cewa. "Ya taimaka yasa baki, Hamma Saifuddeen ɗin ya raka Zaleeha ta bawa Baba Malam ɗin haƙuri, saboda rashin agaza mata zai iya sawa ta kamu da wani ciwon, musamman ma idan akayi la'akari da yanda take wuni kuka." Jinjina mata kai Ahmad ɗin yayi alaman "Yaji kuma zaiyi wa Saifuddeen ɗin magana. Hayatuddeen dake zaune shikansa saida yaji hawaye sun cika masa ido. Ummi kuwa gaba ɗaya ranta ya gama ɓaci, domin shirun da Saifuddeen ɗin yayi, alamace dake nuna cewa, har yanzu yana kan bakansa, hakan ne yasa cikin fushi ta tashi ta nufi ɗakinta. Cikin sauri Zaleeha dake tsaye jikin ƙofa ta koma ɗakinta, dan batason wani daga cikinsu ya ganta, saboda tunda suka fara magana'n harzuwa yanzu tana jinsu, duk da cewa Saifuddeen ɗin baya magana, amma ayanayin yanda yake gudanar da body language ɗin nasa, yasa ta fahimci komai dake zuciyarsa, ga kuma alaman fushin da yakeyi da ita da ya bayyana ƙarara, zamewa tayi anan jikin ƙofar ɗakin ta saki wani irin kuka mai taɓa zuciya, dama shi kaɗaine hope ɗinta, kuma shima gashi yaƙi amincewa, shikenan bata da wani me taimakonta ayanzu ta tabbata fushin uba dana mijinta yana kanta, kuka ta shigayi sosai, sanin cewa yanzu bata da wani madafa, ya zatayi mijinda a ƙarƙashin shi aljannarta yake yana fushi da abinda ta aikata a baya,kana babanta mahaifi yana fushi da ita ya zatayi, ta ina zata fara neman tafiyar mijinta. Saifuddeen kuwa ganin Ummi ta tafi cikin fushi, yasa yaji gaba ɗaya jikinsa yayi masa sanyi, sosai zuciyarsa ta karye, damuwa me tarin yawa ya ɗarsu acikin ransa, sam bai saba da fushin Ummi ba, asanyaye ya hau saman wheelchair dinsa, ahankali yake tura keken har ya fice daga cikin ɗakin, part ɗinsa ya nufa, yana shiga kuwa ya laluɓo wayarsa dake cikin aljihu, numbern Ummin nasa ya laluɓo, asanyaye ya shiga rubuta mata text message, sai ya faɗi maganar acikin zuciyarsa, kafun yake rubutawa, kalamaine naban haƙuri, ya turawa Ummin nasa inda yace _"Kiyi hakuri Ummina, akullum bana fatan na zamo me ɓata miki,ko yanzu ma ba'a son raina bane nakasa bin umarninki, kawai dai naga abun da Zaleehan tayi ne bai dace ace an roƙa mata yafiya ba, ta gujemu tayi tafiyarta, sai yanzu da duniya da kuma ƴan uwanta suka juya mata baya shine ta dawo garemu, wato mu gidanmu ya zama gidan ƴan iska kenan, da zata tafi ta kuma dawo alokacin da take so, nayi hakanne bawai dan na ɓata miki ba, kiyi haƙuri Ummi ki yafemin"_ Yana gama rubutun yayi sending message ɗin, tare da ɗan kifa kansa ajikin keken nasa, kana ya lumshe idanunsa. Ummi na zaune akan gado, saƙon ya shigo, koda ta gama karanta saƙon nasa murmushi tayi, dama ita ba fushi tayi dashi ba, tayi hakanne kawai saboda yayi mata abun da takeso. amsa ta shiga rubuta masa, tare da jaddada masa cewar _"Yayi abun da takeso kawai, idan kuma baso yake, damuwa yayi sanadiyar taɓa zuciyar Zaleehan ba, dan jiya kwana tayi kuka, bakin cikin rayuwa sunyi wa Zaleehan yawa, da wanne zataji mutuwar ƴar uwarta ko kuwa fushin da Babanta keyi da ita? sannan gefe guda kuma ga fushin ƴan uwanta, ga kuma shima da ya kamata ace yazame mata garkuwa fushi yakeyi da ita, meyasa bazaiji tausayin Zaleeha'n ba, wanda har yanzu yasan cewa, ita yarinyace, sannan kuma tayi nadama har acikin zuciyarta."_ tura masa saƙon Ummi tayi tare da aje wayarta. Shi kuwa Saifuddeen yana gama karanta saƙon Ummin sake lumshe idanunsa yayi, zuciyarsa duk ba daɗi. Cikin sanyi ya rubuta cewa. _"Kiyi haƙuri Ummi banso na ɓata ranki ba, shikenan naji na amince zan rakata, amma dan Allah Ummi kiyi haƙuri zuwa gobe idan anyi sadakan uku saina kaita kafin nan mutane sun ɗan ragu a gidan nasu"_ Murmishin farinciki da samun nasara Ummi tayi, bayan ta gama karanta text message ɗin daya turo mata, nan tace dashi. "Allah ya kaimu goben." Sai alokacin ya ɗanji sanyi acikin ransa, saboda yasan zuwa yanzu, zuciyar Ummin nasa zata ɗanyi sanyi. Can ɓangaren Zaleeha kuwa kuka tasha sosai har taji babu daɗi, dan kanta haka ta share hawayenta saboda koma menene tasan ita ta jawa kanta, ko ahaka suka barta ma, tasan sunyi mata gata tunda suka bata muhallin zama, abun da ƴan uwa da mahaifinta suka kasa yi mata kenan saboda fushin da sukeyi da ita. Ganin kukan bazai kaita ba yasa ta tashi ta wuce toilet tare da wanko fuskarta wanda tayi ja sosai saboda kukan da tayi, fitowarta daga toilet ɗin kuwa yayi dai-dai da shigowar Ummi cikin ɗakin, ganin fuskar Zaleehan da kuma idanunta sunyi luhu luhu, yasa Ummi kamo hannunta suka zauna anan bakin gado. Cikin kulawa Ummi tace. "Kuka kikayi ko?" Sadda kanta ƙasa tayi, saboda bazata iya musawa Ummi'n ba, kanta Ummi ta shafa, tare da cewa. "Ki kwantar da hankalinki kinji, Insha Allah gobe Hammanku zai kaiki kuje ku bawa Baba Malam haƙuri, kuma Insha Allah Baba Malam zai yafe miki, ki daina kukan nan kinji!." Ummi tafaɗi maganar cikin lallashi, jin cewa Hamma Saifuddeen ɗin ya yarda zai kaita yasa taji wani irin farinciki ya lulluɓe Zuciyarta, hakanne yasa ta faɗa jikin Ummi ta saki kuka. Rarrashinta Ummin ta somayi tare da sanya hannu tana shafa bayan Zaleeha'n, cikin kukan tace. "Nagode sosai Ummi, haƙiƙa kin zame min uwa, nagode sosai..." saurin rufe mata baki Ummi tayi, cikin kulawa tace. "Kamar ƴa haka na ɗaukeki Zaleeha, saboda haka bama saikin min godiya ba, duk wani burina bai wuce farincikin ku, Allah Ubangiji ya muku al'barka, ungo wannan kayan ɗazun Hayatuddeen ya sayo miki su." Ummi ta faɗi maganar tana me miƙawa Zaleehan ƙatuwar ledan dake hannunta. Amsar ledan tayi cikin farinciki tace. "Nagode sosai Ummi." har cikin ranta taji daɗin kayan, saboda itama kayan jikin nata sun isheta, yau kwanansu biyu kenan ajikinta, abunda tunda take aduniyarta bata taɓayi ba kenan, dama haka rayuwa take tana juyawa da abubuwa kala-kala, wai ita Zaleeha me yawan ado da kwalliya uwa uba ƙwalisa, itace ke sanye da kaya ɗaya ajikinta har tsawon kwanaki biyu, bacin da arana ɗaya saita sanja kaya kusan kala uku, amma yau gashi komai ya juya mata, damuwa ya mata yawa, wani lokacin har takan manta wasu abubuwan da suka shafeta. Ummi kuwa tashi tayi inda da kanta ta shiga toilet ta haɗawa Zaleehan ruwan wanka me ɗumi, cikin kulawa Ummi tace da Zaleehan ta shiga tayi wanka, babu musu kuwa ta shiga rage kayan jikinta, ganin haka yasa Ummi fita daga cikin ɗakin, tare da jawo mata ƙofa. Jikinta aɗan sanyaye haka tayi wankan, ba laifi kuwa taɗanji damuwarta ta ragu, nan cikin kayan da Ummin ta kawo mata ta zaɓo wata doguwar abaya gown me kyau ta sanya, sam damuwar da take ciki kuwa bai hana zallan kyawunta fitowa ba, gashi rigar ta amshi jikinta tayi mata ɗas, mayafin doguwar rigar ta yafa, sannan cikin yanayin sanyi ta fito zuwa falo. Nan ta iske Raleeya da Hayatuddeen zaune, Raleeya karatun littafin hausa take, shikuwa Hayatuddeen game ya haɗa yakeyi. Yana ganinta ya ɗan waro idanunsa, tare da cewa. "Wow Adda Zaleehan mu kinyi kyau, yeah ashe dai niɗin gwanine wajen iya zaɓen kaya." Murmushi tayi masa, tare da zama anan kusa da Raleeya. Duban Raleeya tayi cikin kulawa tace. "Sister sannu da gida." cikin sakin fuska Raleeya tace. "Yauwa sannu my kyakkyawar Auntyn mu, halan wannan kwalliyan duk na hamma ne" Raleeya ta ƙare maganar cikin yanayi naɗan tsokana, murmushi Zaleehan tayi wanda har saida fararen haƙwaranta suka bayyana, nan ta sadda kanta ƙasa tana tunanin. Uhum Hammanku kam ko kallo ban isheshiba ba ai. Hayatuddeen kuwa tashi yayi ya wuce ɗakinsa, mintuna kaɗan sai gashi ya dawo da leda ahannunsa, nan kan cinyarta ya ajiye mata, cikin kulawa yace. "Aunty roasted fish ne da cake, please kici kinji, nasan kinaso." murmushi tayi tare da cewa. "Nagode auta." Dukansu murmushi sukayi sannan suka shiga ɗan taɓa hira, ita dai haryanzu akwai damuwa kwance aƙasan zuciyarta, hakanne ma yasa maganarta bai wuce. "Eh, ko A'a ba". Suna nan azaune Ummi ta fito ta samesu, zama tayi acikinsu, itane ma take ƙoƙarin jan Zaleehan da hira. Saifuddeen ne ke tura wheelchair ɗinsa, yana son ƙarasawa part ɗin Ummi, dai-dai lokaci Ameena wanda dawowarta daga aiki kenan ta shigo cikin gidan, ganin Saifuddeen ɗin yasa ta ƙaraso da sauri tana sakar masa murmushi, shiɗinma murmushin ya sakar mata, tare da miƙa hannu ya karɓi Adeel dake rungume akafaɗanta. Ɗan ranƙwafowa tayi tayi mishi kiss a forehead ɗinsa, cikin kulawa tace. "Nayi kewarka Mijina." murmushinsa me kyau yayi mata, tare dayi mata alaman cewa shima haka, nan ta riƙe saman wheelchair ɗin nasa, tana turasa shikuwa yana riƙe da Adeel haka suka nufi part ɗin Ummi. Ahankali suka tura ƙofar falon suka shiga bakin Ameena ɗauke da sallama, hakanne yasa gaba ɗayansu suka ɗago kai suka kallesu, Ummi ne ta fara amsa sallaman, kafun suma suka amsa, kallo ɗaya Zaleeha tayi musu ta duƙar da kanta ƙasa, cikin kulawa Ummi tace. "Mutanen asibiti kun dawo." Murmushi Ameena tayi, wanda ganin Zaleeha cikin shiga me kyau yasa duk taji zuciyarta ba daɗi, ɗan durƙusawa tayi tare da cewa. "Ummi barka da gida." Murmushi Ummi tayi tare da cewa. "Yauwa Ameena ya wajen aikin naki?" tana murmushi ta amsa da lafiya lau, Raleeya da Hayatuddeen ne sukayi mata sannu da dawowa, baki awashe haka ta amsa musu, duk dama dai aranta sam bataji dadin ganin Zaleeha ba, gashi kuma Zaleehan tayi kyau sosai, Ɗago kai Zaleeha tayi tare da ɗan kallon Ameena'n, cikin sanyin murya tace. "Ummu Adeel barka da dawowa." Cakwai haka Ameena taji muryan Zaleehan acikin kunnuwanta, take kuwa taji kaman an watsa mata ruwan zafi ajikinta, wani irin haushin Zaleehan ne ya cika mata zuciya, amma ganin idon su Ummi yasa ta ɗanyi yaƙe tare da cewa. "Yauwa Sannu." Ɗan ɗago kai Zaleeha tayi ta saci kallon Adeel dake kan cinyar Saifuddeen, Gani tayi Adeel ɗin na kallonta, hakan yasa ta sakar masa murmushi wanda har saida dimples ɗinta suka lotsa, shima yaron murmushi yake ta mata yana wangale mata haƙora tare da mutsu-mutsu har yana zamowa tare da miƙo mata hannu alamun ta ɗaya shi. Cikin dariya Hayatuddeen yace. "Aunty Zaleeha ke yakeyiwa hakafa". murmushi Ummi tayi tare da cewa. "Ae wannan ɗan naku saiku yaron ba dai ƙirniya ba abinda ya iya". Murmushi sukayi baki ɗaya su. Ita kuwa tashi tayi daga zaunen da take, gaba ɗaya ta gama mantawa cewar ma yaron akan cinyar Saifuddeen ɗin yaƙe, ƙarasawa tayi tare da ɗan ranƙwafawa tasa hannu zata ɗauki Adeel ɗin, daddaɗan ƙamshin turarensa ne ya daki hancinta, cikin tsautsayi kuwa hannunta ya gogi nasa, wani irin shock sukaji su duka biyun, ahankali ta ɗauki Adeel ɗin, sannan ta ɗagashi sama tana sakar masa murmushi, baki ya wangale mata harda tsalle shi, Allah ya sani tana son Adeel har cikin ranta kuma shima yaro yana sonta. Baki buɗe Ameena ke kallonsu, kishi kuwa haka takeji kaman zai fasa ƙirjinta, ƙwarai tazo iya wuya, dan kasantuwar Zaleeha akusa da Saifuddeen ɗin baƙaramin dacewarsu ta gani ba. Ummi kuwa jin wayarta dake cikin ɗaki na ƙara yasa tatashi ta bar musu falon, Raleeya ma miƙewa tayi ta haura sama. Nan falon ya rage daga Hayatuddeen, Zaleeha, sai su Saifuddeen ɗin, Zaleeha kuwa rungume Adeel ɗin tayi tana yi masa wasa, Saifuddeen kuwa ahankali yake ɗan satan kallon Zaleeha'n, saboda tayi masa kyau sosai, duk da kasancewar ma ya lura cewa idanunta aɗan kumbure suke kuma gaba ɗaya yanayin rayuwarta ta sauya ta zama mai sanyi, hakan yasa shi jin wani abu na tausayi acikin ransa. Ameena kuwa ganin cewa Saifuddeen ɗin na ɗan satan kallon Zaleehan ƙasa-ƙasa ne, yasa taji gaba ɗaya ranta ya ɓaci, wani irin matsanancin kishi ne ya taso mata, amma saita dake, cikin kirsa ta tashi ta dawo kusa da Saifuddeen ɗin, ɗan durƙusawa tayi tare da tallafo haɓarsa cikin son nunawa Zaleeha matsayinta tace. "Mijina Mekakeso na kawo maka kasha?" Shikuwa sanin cewa Zaleeha na falon, yasashi jawo hannun Ameenan kusa dashi, kissing ɗinta yayi, tare da nunata da hannunsa, alaman ita yake so, wani irin daɗi haɗi da farinciki ne suka cika zuciyar Ameena, wani irin fari tayi da idanunta, da ɗan ƙarfi yanda ta tabbatar cewa Zaleehan zataji tace. "Indai nice kasameni." Saman Wheelchair ɗinsa ta kama, tare da juya akalan keken suka fice daga cikin falon, sai sakin wani shu'umin murmushi takeyi. Duk da cewa duk abun da sukeyi tana jinsu, amma gaba ɗaya hankalinta ba akansu yake ba, sam kuma bataji wani abu na ɓacin rai dangane da hakan ba, gaba ɗaya ma ita hankalinta naga wajen yiwa Adeel wasa, sai dai tana jin zuciyarta na riƙe da abinda sukayi. Hayatuddeen kuwa sosai hakan da Ameenan tayi yasa yaji ba daɗi, saboda ya fahimci cewa, Ameenan so take ta ƙuntatawa Zaleeha, amma ganin cewa Zaleehan bata damu ba, yasashi girgiza kansa kawai ya ci gaba da game ɗinsa. Ameena kuwa suna isa part ɗinsu, cikin mazari tasoma ƙoƙarin rage musu kayan jikinsu, jin ranta take fari ƙal, saboda hakane ma zata gwadawa Saifuddeen ɗin soyayya kala-kala, tayanda sai tasa ya manta da wata Zaleeha. Afalon Ummi kuwa saida aka ƙira sallan Magriba, kafun Ummi ta karɓi Adeel, inda tace da Zaleeha taje tayi sallah. Koda ta idar da sallan kuwa bata tashi akan sallayan ba sai da aka idar da sallan isha, daganan bata ƙara leƙa waje ba, kifi da kuma cake ɗin da Hayatuddeen ya bata shi taɗan ci, sannan ta kwanta, take kuwa bacci ya ɗauketa. Saifuddden da Ameena kuwa, yau zagewa tayi ta nuna masa soyayya kala kala, babu laifi kuma shima ya biye mata, hakanne kuma yasa kasantuwarsu tayi mata armashi, dan bakaɗan ba takejin daɗin Saifuddeen. Haka ko da suka kwanta bacci tawani rungemesa, ranta kuwa fari ƙal, bata da wani damuwa, saboda kasantuwarsu na yau yasa tanajin kanta kamar wata sarauniya. Washegari Yau ya kama Lahadi, inda gobe Monday Amina zata fara zuwa aikin rana. kuma yaune ake sadakan Uku na rasuwar Adda Maryam, Inda sukejin mutuwar ta dawo musu sabuwa, sosai suka sha kuka har suka godewa Allah, yayinda mafi yawancin mutanen da suka zo musu ta'aziyya duk kowa ya kama gabansa. Haka gidan ya rage daga, su Yaya Ahmad sai kuma Hajja Inna da Goggo maryama, sai kuma su Ziyada da kuma wasu mata guda biyu, wanda suke ƙannen. Yaya Ameenu ne, wato Zainab da kuma Ubaida, sai wanda suma dukansu matan aure ne, sai Hajja Ma'u mahaifiyarta Ya Ameenu kenan rasuwar ne ya sasu zama anan gidan na Baba Malam, wanda suɗin ma yau zasu tafi, zuwa yanzu babu wani baƙo ko ɗaya da ya rage acikin gidan, iya su yasu ne, haka suka sha kukansu suka ƙoshi, daga ƙarshe sukayiwa Adda Maryam ɗin addu'a da fatan Allah ya raya ɗanta Ayman. Can gidan su Saifuddeen kuwa, Yau Zaleeha da wuri ta tashi, tana idar da sallah kuwa tawuce ɗakin Ummi ta gaisheta, anan ta iske Saifuddeen ɗin, koda ta gaishesa, saida ya ɗauki kusan second 30 kafun ya jinjina mata kai alaman ya amsa, haka tatashi ta koma ɗakinta jikinta duk asanyaye, shikuwa falon Ummi ya koma ya zauna. Wanka tayi sannan tasaka ɗaya daga cikin riga da sket ɗin da aka sayo mata, ganin kayan ya kamata yasa ta ɗaura hijab akai, murɗa handle ɗin ƙofar tayi tafita, dan tanason fara taya Raleeya aikace aikacen gidan. Tana fitowa falon kuwa anan zaune ta iskesa, sadda kanta ƙasa tayi sannan ta wuce kitchine, Sarai ya ganta amma saiyayi kaman bai ganta ba, saida ta wuce yabi bayanta da kallo, harda wani ɗan lumshe idanunsa. Tana shiga kitchine ɗin kuwa tasamu Raleeya na firan dankali, amsa tayi ta soma tayata suna ɗan taɓa hiransu. Ameena ce tashigo cikin falon, ɗauke da Adeel akan kafaɗunta, ganin Saifuddeen zaune afalon Ummin yasa ta sakin murmushi, shima murmushin ya sakar mata, har acikin ransa yaji daɗin ganinta yanzun, dan da itane zaina buga Game ɗinsa, wanda ya tabbata wata rana kuwa zaiyi winning, ƙarasowa cikin falon tayi, tare da ajiye masa Adeel akan cinyarsa, nan ta wuce ɗakin Ummi, koda taje ɗakin na Ummi kuwa cikin ladabi ta gaisheta, fuska asake Ummi ta amsa mata, tare da tambayanta Adeel, murmushi tayi tare da cewa. "Ummi yana falo suna tare da Abban shi." Itama Ummin murmushi tayi tare da jinjina kanta, dan tana lazumi ne, batason magana. Miƙewa Ameena tayi ta fice daga ɗakin, Tana fitowa falo Saifuddeen ya miƙo mata hannunsa, cikin jin daɗi ta ɗauke Adeel dake kan cinyarsa tayi, ta ɗaurasa akan kujera, raɓawa kan cinyar Saifuddeen ɗin ta ɗanyi dan taga falon ba kowa kuma tasan Ummi na lazumi ba yanzu zata fitoba, ahankali ya sanya hannuwansa, ya saƙalo waist ɗinta, harshensa yasa inda ya ɗan laso lips ɗinta, idanunta ta ƙura masa bata ko ƙiftawa, ganin haka yasashi ɗan ɗaga mata gira, murmushi tayi tare da sake shigewa jikinsa, fuskarta ya ɗago ya haɗe bakinsu waje ɗaya, jin haka yasa ta kamo laɓɓansa tana tsotsa sosai. Gaba ɗaya sun shagala, musamman ma Ameena, wanda idan tana shan laɓɓansa takejin kamar tana shan sweeet. Adeel kuwa sai wutsil wutsil yake, yanason jawo flowern dake gefen kujera, hakanne yasa har yazo bakin kujeran batare da sun ankara ba, Zaleeha ce ta fito daga cikin kitchine ɗin hannunta riƙe da flask, da sauri taja baya sakamakon abun da idanunta suka gane mata, ƙoƙarin komawa cikin kitchine ɗin take, idanunta suka sauƙa akan Adeel wanda saura ƙiris ya faɗo daga kan kujeran, cikin sauri ta ajiye flask ɗin hannunta, da gudu ta ƙarasa inda yake, dai-dai lokacin kuma har ya faɗo daga kan kujeran, saidai kuma bata bari yakai ƙasa ba, tayi saurin zubewa akan guiwowinta ta taro sa, yafaɗa jikinta, wani irin firgitaccen ihu ya saki har kamar zai shiɗe dan yayi masifar tsorita ruggumeshi tayi a jikinta da kyau, hakan yasa ya ƙanƙameta tare da kuma cilla ihu, wanda hakanne ya fargar dasu Saifuddeen, azabure suka juyo suna kallonsu, ɗagosa Zaleeha tayi tare da mannasa aƙirjinta, tana jijjigasa, Idanu Saifuddeen ya zuba mata, ita kuwa Ameena hakanan taji wani iri aranta, kukan Adeel ɗinne yafito da Ummi, daga ɗaki, harta Raleeya ma saida tafito, cikin kulawa da tsananin son yaron Ummi tace. "Lafiya kuwa me ya sameshi." ta ƙarasa maganar tana shafa kanshi tare da kallon Zaleeha Cikin damuwa murya a tausashe Zaleeha kamar zatayi kuka tace. "Faɗowa ya kusayi daga kan ƙujera, inaga shiyasa ya tsorata, gashi yana ta kuka." ta faɗi maganar tana me ci gaba da jijjigasa, saboda sam batason kukan Adeel ɗin, tanajin yaron sosai aranta, ganin baiyi shiru bane yasa ta sanya bakinta akunnenshi tana ɗan hurawa masa isaka tare da ɗan bubbuga bayanshi kana tana jijjigashi, wanda hakanne ya bawa jikinta damar rausaya wa, take kuwa yayi shiru, tare dayin lub ajikinta, jin yayi shiru yasa ta wuce ɗakinta dashi. Har zuwa lokacin kuwa idanun Saifuddeen akanta suke, Ameena kuwa gaba ɗaya ma takasa tantance meke damunta, tausayin ɗanta ne ko baƙin ciki da kishi takasa tantance wanne ne ɗaya, ganin lokaci na ƙurewa yasa ta juya ta fice daga falon dan batason tayi lattin zuwa wajen aiki dan yau ɗin mitin zasuyi da manyan likitoci. Zaleeha kuwa tana shiga ɗaki, ruwa me ɗan ɗumi ta haɗa, tayiwa Adeel ɗin wanka, Hayatuddeen ne ya shigo cikin ɗakin, hakan yasa tace dashi yaje ya karɓo mata kayan Adeel tasa mai. Part ɗin Ameenan yaje, ya amso kayan sannan ya kawo mata, tsab ta shirya Adeel ɗin cikin kayansa me kyau, sosai kuwa yaron yayi kyau, haka ta rungumesa aƙirjinta tana ta yi masa wasa. Ganin alamun bacci yakeji yasa ta ɗauki towel ta goyeshi ai tuni yayi bacci. Saida Ameena ta zo tafiya aiki sannan ta amshe sa, still agaban Zaleehan Saifuddeen ya sake jawo Ameenan yayi mata kiss abayan hannunta kafun ta tafi, Zaleeha kam idan ta kallesu sau ɗaya bata yarda ta sake kallonsu, zuwa yanzu ma mamaki suke bata dan ta lura basa gajiya da tsotse, saidai kuma idan ta tuna cewar rashin damuwa ne ke sasu hakan, sai taji matsanancin tausayin kanta. Tace su kam sunji daɗi da basu da damuwar duniya. Koda tayi break ɗaki ta komawa tayi ta kwanta, cikin zuciyarta kuwa fargaba ne, me tarin yawa, saboda batasan ta yaya zata fuskanci Baba Malam ba. Saifuddeen kuwa sanin cewa yau ne zaikai Zaleehan ta bawa Baba Malam haƙuri, yasa shi barin gidan ma gaba ɗaya, bashi ya dawo ba kuwa sai wajajen sallan azahar. Kaitsaye ɓangaren sa ya wuce, wanka yayi sannan ya shirya kansa cikin wata ɗanyar getzner me masifar kyau da tsada, kasancewar getzner ɗin na sa nada kalan coffee, shi yasa ya matuƙar amsar farar fatar jikinsa, yayinda akayiwa getzner ɗin dinkin half jumper da kuma wandon pencil, wata murzazziyar hula mai kalan light coffee ya ɗaura akansa, hatta takalmin dake ƙafansa me kalan dark coffee ya sanya, yayi kyau matuƙa ga kuma apple touch watch ɗinsa dake ta faman ɗauke ido, tabbas Saifuddeen yayi kyau ƙwarai, dan bazaka kallesa sau ɗaya ka ɗauke idanunka ba, haɗaɗɗiyar sajen dake kwance akan fuskarsa kuwa ta kwanta tayi lub lub, jajayen laɓɓansa kuwa sai sheƙi suke, ga wanda baisansa ba zaice wani abun ya shafa musu, amma ko ɗaya haka yake, sirrin kyau ajininsa yake. Wayoyinsa ya zura acikin aljihun rigarsa, sannan kai tsaye ya danna madannin wheelchair ɗinsa ya fita daga cikin ɗakin, sai baza ƙamshi yake. Anan compound ɗin gidan kuwa, sanin cewa zasu fita yasa Sule driver tuni ya gama tsabtace motar da zasu fita da ita ɗin, wata haɗaɗɗiyar mercedes benz ce me kyau, sabuwa dal sai sheƙi take tana ɗauke ido, fitowarsa compound ɗin gidan ne, ya hango Sule driver, hakanne ya sashi ƙarasawa wajen Sule driver'n, cikin kulawa Sule driver'n, yayi masa barka da fitowa, da kai ya amsa masa kamar koda yaushe. Buɗe murfin motar yayi, nan ɓangaren gidan baya ya shiga, dan dama shi baicika zama agaba ba, akomansa yafison sirri, musamman ma yanzu da yake mazaunin jami'in sirri, yana shiga ya jawo murfin motar ya rufe, wayarsa ya laluɓo daga cikin aljihunsa, cikin text message ya shiga, ataƙaice ya rubuta cewa. _"Ummi kice mata tayi sauri, dan tana ɓatamin lokaci."_ yana gama rubutun yayi sending, tare da maida wayan ya ajiye, laptop ɗinsa ya ɗauko yana dannawa. Ummin kuwa dama tuntuni tasa Zaleehan ta shirya, tsab cikin ɗaya daga cikin sabin rigunan da tasa aka sayo mata, duk da cewa akwai yanayin damuwa mai yawa akan fuskarta, amma hakan baihana kayan yi mata kyau ba, saboda doguwar rigace irin abaya ɗinnan ta larabawa me kyau, yayinda ta yane kanta da ɗan kwalin kayan, wanda ya sauƙo har zuwa ƙirjinta. Tunda ta gama shiryawan take zaune abakin gado, gaba ɗaya ta rasa mekeyi mata daɗi, tsoro da fargaba ne suka cika zuciyarta, ga kuma yawan faɗuwar gaba da takeji, ƙirjinta ne ke wani irin duka, gaba ɗaya atsorace take, koda tayi ƙoƙarin bawa kanta ƙarfin guiwa kuwa hakan baya yiwuwa, saboda fargaban daya cika zuciyarta. "Me zata tarar agidan Baba Malam? wata ƙila ma yaƙi yafe mata ya kuma sake koranta." Wannan abun shine abun daya tsaya mata arai, duk yanda taso jin sauƙi azuciyarta abun yaci tura, hakanne yasa kawai ta fashe da kuka, dai-dai lokacin Ummi ta turo ƙofar ɗakin ta shigo, ganin Zaleehan na kuka yasa ta ɗan dafe kanta, sam batason yawan kukan na Zaleeha, jin an shigo ɗakin ne yasata ɗago kanta, ganin Ummi yasa cikin hanzari ta tashi tare da ƙarasa gareta, cikin muryarta dake rawa tace. "Wallahi Ummi tsoro nakeji , idan mukaje Baba Malam ya koreni sannan yaƙi yafemin ya zanyi? shikenan nikam rayuwata tana cikin garari." taƙare maganar hawaye na silalowa daga cikin idanunta, Ɗan bubbuga bayanta Ummi tayi, cikin son kwantar mata da hankali tace. "Kada ki faɗi haka Zaleeha, share hawayenki, insha Allah Baba Malam zai yafe miki, nasan nanda ƴan wasu awanni zaki kasance cikin farincikin yafiyar Baba Malam, yanzu taho muje Hammanku nacan mota yana jiranki." Idanunta ta ɗan lumshe, ahankali taɗan gƴaɗa kanta kamar wata ƙaramar yarinya, haka hawaye ke tsiyaya daga cikin cikin idanunta, hannunta Ummi ta kama suka fice daga cikin ɗakin, anan falo suka samu Raleeya tsaye. Ummi na riƙe da hannunta, yayinda Raleeya ka biye dasu abaya, haka suka fito zuwa compound ɗin gidan, har jikin motar tasa suka ƙarasa, still hawaye Zaleeha take, Ummi kuwa na riƙe da hannunta, murfin motar Ummi ta buɗe tare da sanya Zaleehan aciki, ganin ankawo masa ita kusa dashi ne, ya sashi ɗago kansa ya dubi Ummi, amatuƙar shagwaɓe ya ɓata fuska, cikin body language ɗinsa yace wa Ummi da ke kallonsa, "Ni Ummi me yasa zaki kawomin ita kusa dani, baganan gidan gaba ba, dan Allah Ummi kisata agaba, ni banason ta zauna akusa dani." Daƙuwa Ummi tayi masa, tare da kama haɓanta, sosai take mamakinsa itakam, musamman ma yanzu da ya ari halin da ba nasa ba ya yafa. Sake ƙara shagwaɓe fuska yayi, cikin ransa yake ta ƙunƙuni, wanda ko bakin zuciyarsa bai je ba, dan duk abun da yakeyi pretending ne kawai, sam baisa azuciyar sa ba. Allah ya kiyaye Ummi tayi musu sannan Sule driver yaja motar suka fita daga gidan. Saida su Ummi suka ga, fitansu kafun suke komawa cikin gida. Koda tafiyan nasu tayi nisa, ƙanƙame jikinta waje ɗaya tayi, saboda sanyin AC'n dake tashi acikin motar yaso ya yiwa jikinta yawa, gaba ɗaya bata wani cikin nutsuwarta, domin suna fita daga cikin gidan na Ummi taji gaba ɗaya zuciyarta ya karye, haka hawaye keta fita daga cikin idanunta, yana sauƙa akan fuskarta, daga gefe guda kuwa daddaɗan ƙamshin turarensa ne ya gauraye numfashinta, haka take ta sakin sheshsheƙan kuka ahankali. Saifuddeen kuwa, duk da kasancewar bai ɗago kai ya kalleta ba, amma duk wani abu da takeyi, yana lure da ita, amma azahirance yi yayi kamar baisan da wata halitta agefensa ba, itakuwa gaba ɗaya damuwa ya cika mata zuciya, hakanan taji tana son kallonsa, amma wani irin abu me kama da tsoro ya hanata kallon sa, wanda kuma tunda take dashi bata taɓa jin irin hakan a dangane dashi ba. Cusa kanta atsakankanun cinyoyinta tayi, tana me sake sakin sheshsheƙa, can cikin zuciyarta kuwa sunan Allah. take ta faman ambato. Shikuwa Saifuddeen text message ya turawa Dirankadi kan cewa. "Yana neman al'farma idan yana gida, yanaso yazo ya ɗaukesa, akan maganan Zaleeha, dan suje su bawa Baba Malam haƙuri, saboda yana fushi da'ita sosai, sannan kuma idan yaje shi kaɗai baisan mezai faɗawa Baba Malam ɗin ba, wataƙila ma balallai Baba Malam ɗin ya sauraresu ba." Cikin fahimta kuwa Dirankadi yace masa. "Babu damuwa Sai sunzo ɗin, dama fita zaiyi, amma zaijirayi zuwansu.." Sosai kuwa Saifuddeen yaji daɗi, hakan yasa ya ɗan taɓa Sule driver, Juyowa Sule driver'n yayi yana fuskantar sa, miƙawa Sule driver'n wayarsa wanda yayi rubutu akan screen ɗin Yayi, koda Sule driver ya karanta saƙon jinjina kansa yayi, cikin kulawa yace. "Angama ranka ya daɗe." Nan take kuwa ya karkata akalar motar suka nufi gidansu Ishaq. Koda suka ƙarasa gidan nasu Ishaq kuwa, nan suka samu harma Dirankadi'n ya shirya, su kawai yake jira, koda Saifuddeen ɗin ya buƙaci da Dirankadi'n ya shiga motarsa, cewa yayi dashi. "A'a zaije da tasa motar, saboda daga gidan su Zaleehan zai wuce wajen aiki, saboda haka amotarsa zai tafi." Saifuddeen ne yayiwa Sule driver, alamar cewa ya yiwa Zaleehan magana tazo ta gaida Dirankadi ɗin, haka kuwa akayi Sule driver da kansa ya buɗe mata murfin motar ta fito, har ƙasa kuwa ta durƙusa ta gaishe da Dirankadi'n. Fuska asake ya amsa mata, tare dayi mata ta'aziyyan rasuwar Adda Maryam, haka ta amsa masa cikin yanayin sanyi, dan aɗan kukan nan da tayi, har muryarta ta dashe. Haka dai Dirankadi ya shiga motarsa, itakuma Zaleehan ta koma motar su ta zauna tare dayin jigum, saboda zuciyarta dake ƙara tsinkewa, Nan dai suka kama hanyar gidansu Zaleehan, inda motar Dirankadi ce agaba. Basuyi wani tafiya me nisaba suka iso gidan, jin motar ta tsaya ne yasata ɗago kanta amasifar tsorace, aikuwa ganinta acikin compound ɗin gidansu yasa gaba ɗaya duk wani kuzarinta ya kau, yanayin yanda zuciyarta ke bugawa kuwa, idan kaji zakai tunanin cewa faso ƙirjinta zatayi ta fito waje, sosai jikinta ya ɗauki rawa, tsoro ne yagama lulluɓeta, makomarta kawai take tunawa. Dirankadi ne yafara fitowa daga cikin motarsa, ƙarasowa jikin motar Saifuddeen ɗin yayi, cikin kulawa yace. "Saifuddeen ku zauna kada ku fito, duk yanda ake ciki zan maka text sai ku shigo." Kai Saifuddeen ya jinjina masa alamar gamsuwa, Nan Dirankadi ya nufi cikin gidan, kaitsaye ɓangaren Baba Malam ya nufa. Acikin falon Baba Malam kuwa, shi da Ya Ahmad, da kuma Malam Adam ne zaune, gefe dasu kuwa Ya Ameenu ne wanda ayanzu ya zama kamar wani mutum mutumi, komai nasa ya sanja, ya zama wani mutum me sanyi, magana kuwa inbanda "Eh, da kuma A'a." ba bu abun da yake iya fitawo daga bakinsa, sosai mutuwar Adda Maryam ɗin ya maidashi wani silently, hakanne ma yasa gaba ɗaya dangim suke masifar jin tausayinsa. Dirankadi ne ya shigo cikin falon bakinsa ɗauke da sallama, amutunce su Baba Malam da kuma Malam Adam suka amsa masa, cikin mutum tawa Baba Malam ya taso ya tarosa, tare da basa hannu sukayi musabaha, kujera Baba Malam ya nuna masa, zama yayi tare da bawa su Yaya Ameenu hannu suka gaisa, sake musu sabon gaisuwa yayi, tare da sake bawa Baba Malam hannu suka gaisa amutunce, hira kaɗan sukayi, kafun Dirankadi ya gyara zamansa, cikin nutsuwa ya dubi Baba Malam, a mutumce yace. "Kayi haƙuri Malam Bashir, domin ba haka kawai nake tafe ba, alfarma muka zo nema awajenka, wanda kuma nake saka ran cewa Insha Allah, zaka mana ita." Ɗan jim Baba Malam yayi tare da sauƙe ajiyar zuciya, tabbas Dirankadi nada kima da kuma mutumci a idanunsa, saboda haka zai iya yimasa alfarma kuwa kowacce iri ce, saidai kuma ayanzu baisan yaya girman alfarmar take ba, cikin halin dattako da nutsuwa irin nasa yace. "Ai Dirankadi kafi ƙarfin al'farma awajena, saidai kuma bazanyi hanzari ba, ina jinka wace al'farma ce wannan, dahar yasa ka taso da kanka kazo, ai da ko awaya kaƙira ka sanar dani zan iya yi maka ita." Kai Dirankadi ya jinjina cikin jin daɗi yace, "Nagode ƙwarai da wannan karramawar Malam Basheer, yanzu kuwa zanyiwa abokan tafiyana magana dan su samu shigowa." Nan ya ciro wayarsa ya turawa Saifuddeen text akan cewa. "Su shigo." Koda Saifuddeen ya karanta text ɗin na Dirankadi, buɗe murfin motar yayi ya fita, dan dama tuni Sule ya fito masa da wheelchair ɗinsa, ganin haka yasa Sule zagayawa ɓangaren da Zaleehan take ya buɗe mata murfin motar, asanyaye kuwa ta fito daga cikin motar, gaba ɗaya jikinta rawa yake saboda fargaba da kuma tsoro. Haka suka nufi ɓangaren Baba Malam ɗin, Saifuddeen na gaba, ita kuma tana biye dashi abaya, da ƙyar take iya taka ƙafafunta da suka mata nauyi, ga kuma wani masifaffen tsoro haɗi da faɗuwar gaba da takeji. Dai-dai sun kawo ƙofar shiga falon ne, tayi saurin kamo hannun sa, ɗan tsayawa yayi tare da juyowa ya kalleta, wasu irin hawaye masu zafi ne suka silalo daga cikin idanunta, sosai jikinta ke rawa, harta laɓɓan bakinta ma rawa suke, idanunsa ya ɗan lumshe jin yadda ta rumtse tafin hannunshi cikin nata tana mammatse mishi hannun da jan yatsunshi cikin yanayin tsoro, ajiyan zuciya ya sauƙe tare da girgiza mata kansa, hannunta yaɗan murza sannan suka nufi cikin falon Baba Malam ɗin. Jin an taɓa ƙofar falon yasa dukansu suka zubawa ƙofar idanu, dan ganin me shigowa, Ganin Saifuddeen Yasa Baba Malam ɗan sakin murmushi, take kuma saiga Zaleeha ta biyo baya, dan dama har yanzu Saifuddeen ɗin na riƙe da hannunta, da sauri Baba Malam ya ɗauke kansa daga kallonta, take yanayin annurin fuskarsa ya sauya, jiyayi kwata kwata ma bayason ganinta hakan yasa ya kawar da kansa gefe. Saifuddeen na riƙe da hannunta suka ƙaraso cikin falon, har gaban Baba Malam ɗin ya ƙaraso, ita kuwa Zaleeha kanta na ƙasa, hawayene kawai keta tsiyaya daga cikin idanunta, sake hannunta Saifuddeen yayi tare da sauƙa akan wheelchair din nasa, ya yasa guiwowinsa aƙasa, itama Zaleehan zubewa tayi aƙasa, wanda hakan yasa kusan rabin jikinta ya shiga jikin Saifuddeen, gaba ɗaya idanunta sun rufe, ƙwalla ne kawai acikinsu, hawaye wani na koran wani kaman an kunna sabon famfo. Kifa kanta tayi akan ƙafafun Baba Malam dake zaune, lokaci guda ta saki wani irin kuka mai taɓa zuciya, cikin kukan tace. "Dan Allah Baba Malam kayi haƙuri ka yafemin, kar in mutu da fushinka na tuba ka yafemin ko zan samu kekyawan rayuwa, Idan baka yafemin ba nima mutuwa zanyi, wallahi nayi nadamar abun da na aikata, na tuba Ka jiƙaina ka yafemin!!." Taƙare maganar tana Kuka sosai kamar ranta zai fita. Cikin fushi Baba Malam ya janye ƙafansa baya, hakanne yasa ta ɗago da kanta, tana kuka sosai haɗe hannuwanta waje ɗaya tayi alaman roƙo, cikin matsanancin kukan ta ɗaga idanu ta kalli Malam Adam, da kuma Ya Ahmad gani tayi sun kauda kansu daga kallonta, alaman har yanzu suna fushi da ita, duƙar da kanta tayi tana wani irin kuka mai taɓa zuciya, hakanne yasa Saifuddeen ɗaura hannunsa akan nata ya riƙe ƙam, jin haka yasa ta sake mannewa a jikinsa, tare da kama hannunsa tana jijjigawa kuka take sosai, wanda hakan yasa yakejin wani abu na taɓa zuciyarsa, kowani ɗigan hawayenta ɗaya tamkar ɗigan narkakken dalma ne, akan zuciyarsa haka yakeji. Dirankadi ne ya gyara zama zuciyar sa cike da tausayin Zaleehan, saboda yanda take kuka, wanda dagani kasan daga cikin ƙarƙashin zuciyarta da kuma ranta yake fitowa. Asanyaye yace. "Yafiya ga Zaleeha itace al'farmar da nake nema awajenka Malam Basheer, haƙiƙa Zaleeha ta aikata ba dai-dai ba, wanda alokacin ni kaina saida naji babu daɗi, amma ayanzu tabbas ta gane kuskurenta kuma tayi na dama, shikansa wanda ta gudawa ɗin na tabbatar da cewa ya yafe mata, tunda gashi shida kansa ya ɗaukota dan su zo su baka haƙuri, dan Allah Malam Basheer ku yafe mata, kada ku manta fa cewa ita macece me raunin zuciya, rashin yafe mata zai iya haifar da wata sabuwar matsalan, abun zaiyi mata yawa, har yanzu Zaleeha yarinyace ƙara ma, damuwa kaɗan zai iya haifar mata da matsala, da wanne ɗaya zataji? da rashin ƴar uwarta ko kuwa da fushin da kukeyi da ita, ayanzu Al'barkarku take nema, bawai ɓacin rai da fushi ba, nidai ina roƙa mata al'farma dan Allah ayafe mata." Kai Baba Malam ya girgiza, tare da miƙewa tsaye, sam bayajin zai yafewa Zaleeha'n, saboda har yanzu akwai ƙunci da baƙin cikin da ta shayar dashi kwance acikin zuciyarsa, kuma ma baisan niyartaba dole yayi wani abu dan gano meke cikin ranta. Juyawa yayi da niyar barin falon, cikin bazata yaji an riƙe hannunsa, ɗan juyowa yayi afusace dan yasan cewa Zaleehan ce kawai zatayi mishi haka, amma ga mamakinsa sai yaga Saifuddeen ne, wanda idanunsa gaba ɗaya sun ciko da ƙwalla, sannan sunyi jajir, sakin hannu Baba Malam ɗin yayi, tare da haɗe hannuwansa waje ɗaya alaman roƙo, kansa ya rinƙa jujjuya wa yayinda wayenshi ke gab da zubowa. Zaleeha kuwa sake shigewa jikin Saifuddeen ɗin tayi, tare da ɗaura kanta akan kafaɗansa, tana wani irin kuka me matuƙar tsuma zuciya, kukanta kuwa shikesa Saifuddeen yaji kansa kamar zai fashe, haka kuma har cikin ransa yakejin kukan nata, ci gaba yayi da jijjigawa Baba Malam kai, alaman yayi haƙuri yayi musu afuwa. Jikin Baba Malam ne yayi matuƙar sanyi, ganin hawaye acikin idanun Saifuddeen yasa yaji gaba ɗaya tunaninsa ya tsaya, idanunsa yaɗan lumshe tare da komawa ya zauna akan kujera inda ya yi ƙasa da kansa tare dayin shiru. Ya Ahmad kuwa duk yanda yaso shanye kukansa abun yaci tura, dole haka ya saki kuka kaman ƙaramin yaro, dama shi tun farko zuciyarsa me raunice akan Zaleeha, tausayinta ne ke maye ko ina najikinsa, ga kuma jimamin rasuwar Adda Maryam wanda yakejin ta dawo masa sabuwa, kansa ya kifa da jikin kujera yana kuka. Ya Ameenu dake zaune acan gefe kaman mutum mutumi kuwa idanunsa kawai ya zuba musu, shikam aduniya yanajin cewa tunda matarsa ta rasu ta barsa, shikenan duk wani jin daɗi da farinciki sun ƙare masa. Ɗago kai Baba Malam yayi da idanunsa wanda sukai jajur, cikin sanyin murya yace. "Tabbas kin shayar dani baƙinciki marar misaltuwa, kinyimin abun da duk acikin ƴaƴana babu wanda ya ta ɓamin, kin ƙi zaɓina sannan kika gudu kikabar gidan mijinki ɗanki aurenki ba tare da izinin mijinki ba." farin handkerchief ɗin dake hannunsa yasa, inda ya share ƙwallan dake ƙoƙarin fitowa daga cikin idanunsa. Ajiyar zuciya ya sauƙe, sannan yace. "Bani zaki bawa haƙuriba, shi kika saɓa kika wulaƙanta aureshi, shine al'jannarki take ƙarƙashin diga-diginsa dan haka shi zaki bawa haƙuri ba niba yafiyarsa zaki nema da kika fita bada izininshi ba, sai ya yafe miki kafin ni in yafe miki". Da sauri ta juyo ta fuskanci Saifuddeen murya na rawa kana murya a disashe tace. "Kayi hakuri Hamma Saif ka yafe min in sha ALLAH har iya raina da mutuwata bazan sake fita ba saida izininka ko bakin gate bazan sake zuwaba saida izininka". Haɗe hannayenta tayi alamu roƙo kana hawaye na kwaranya a fuskarsa, kanshi ya rinƙa jujjuya mata yana mai jin zazzafan tausayi ya, murya na rawa ta kuma cewa. "Dan Allah Hamma Saif ka yafe min". Kanshi ya kuma jujjuya tare da mata alamun ya yafe mata duniya da ƙiyama, sai kuma ta juyo da sauri ta kalli Baba Malam murya a harde tace. "Baba Malam ka yafe min shi yace ya yafe min". Gyara zama Baba Malam yayi kana yace. "To in na yafe miki me kuma shirinki na gaba zaki sake, gudawa ne? Ko dai kinyi tuba na gaskiya ne zaki zauna ɗakinki, ko bazaki zauna ba?." A hankali ta sunkuyar da kanta zazzafan hawaye na zuba murya na rawa tace. "Har Abadan bazan sake guduba, zan zauna iya raina da mutuwata har sai dai in na mutune zan bar gidanshi babu inda zanje duk rintsi koda ko ba daɗi zan zauna Baba malam zanyi biyayya kwatankwacin wanda Adda Maryam tayi maka, koda daɗi ko ba daɗi zan zauna." Gaba ɗaya jikinsu yayi sanyi hatta shi kanshi Baba malam tausayi ta ya rufeshi, cikin sanyi yace. "Kin san yayi aure bayan guduwanki?". Cikin kuka tace. "Ban saniba saida naje gidanshi naga matar da ɗanshi." Kai ya jinjina tare da cewa. "To ki koma gidanki ɗakinki, ban kuma yarje miki fitina da abokiyar zama kina ki zauna lafiya da ita da ƙanneshi da yayunshi, kada inji wani abu tsakanin ki da abokiyar zamanki, kada ki tsokaneta ko kaɗan in kuma itace ta tsokaneta ki mata uzuri ki yafe mata kada kice zaki rama duk abinda tayi miki". Cikin wani masifeffen kuka tace. "To Baba Malam in sha Allah zaka sameni mai bin umarni ka". Kanshi ya gyaɗa cikin tausayinta a ranshi sabida kukanta na ƙunshi da abubuwa da dama, cikin sanyi yace. "Koda ki tauye haƙƙin mijinki a kanki Zaleeha kada ki haneshi abinda duk Allah ya halattamishi a kanki". Cikin rawan murya tace. "To in sha Allah zan zauna dashi sai kuma in shine yace baya sona." Wani irin tausayinta ne ya rufesu baki ɗaya cikin taushin lafazi Baba Malam yace. "Tabbas kinci al'barkacin Dirankadi da kuma Saifudddeen, saboda haka kije na yafemiki duniya da ƙiyama, ina roƙon Allah Ubangiji kuma ya shiryeki, Ya sa miki imani azuciyarki ya baki zaman lfy da mijinki da abokiyar zamanki, haƙiƙa kin ƙuntatawa zuciyata, kin shayar da ahalinki baƙin ciki, Maryam harta koma ga ubangijinta bata taɓa saɓawa maganata ba koda kuwa sau ɗaya ne, na aurar da ita ga zaɓina, kuma ta amince duk da cewa bataso amma tayi Mini biyayya, haka kuma bata taɓa saɓawa mijinta ba, gashi Allah ya ɗauketa adai-dai lokacin da kowa yake da buƙatanta, Ya Allah kajiƙan Maryam kasa al'janna tazamo makoma agareta...". Kukane ya ƙwacewa Baba Malam ɗin, wanda hakan kuwa yayi matuƙar taɓa zuciyoyinsu, hakanne kuma yasa hawayen dake cikin idanun Saifuddeen samun daman gangarowa, zuwa kan ƙuncinsa, Zaleeha kuwa kuka take sosai kaman ranta zai fita, haka ma Ya Ahmad, wannan karon harta Malam Adam da Dirankadi saida sukayi hawayen, tausayin ahalin. Ya Ameenu kam, bai iyayin kuka ba, saboda ayanzu kukan zuci yake, wanda yafi na fili ciwo, adai-dai wannan lokacin kuwa shi kaɗai yasan me yakeji. Cikin matsanancin kukan, ta rarrafa inda ta ƙarasa gaban Ya Ahmad wanda ke kuka sosai, tana zuwa ta kifa kanta akan cinyansa, tana kuka sosai har kaman zata shiɗe, hannu Ya Ahmad ɗin yasa ya dafa kanta, lokaci guda kuwa ƙarfin kukansa ya ƙaru, gaba ɗaya falon haka ya ɗauki shiru babu abun dake tashi sai sautin kuka anrasa me rarrashin wani, hatta Malam Adam da Dirankadi gaba ɗaya jikinsu amace yake, gaba ɗaya zuciyoyinsu sunyi rauni. Da ƙyar Baba Malam ya iya share hawayensa, cikin muryarsa da ta ɗan dashe yace. "Nayafe miki Allah ya yafe mana baki ɗaya, ki tashi ki koma ɗakin mijinki, Sannan in mijinki ya amince miki duk sanda kuka samu lokaci kuje gidan Maryam ta barmin wasiyar tayi miki ajiya cikin durowar ta ta jikin gado." Hannu yasa ya share hawayenshi kana yaci gaba da cewa. "Kuma matuƙar kika sake mugun saɓawa Saifuddeen ba irin wanda dole akwaishi tsakanin ma'aurataba wallahi! bazan taɓa yafe miki ba Zaleeha, kuma daga wannan lokacin kiceri kanki daga mazaunin ƴata!!!." Jin furucin Baba Malam ɗinne yasanya cikin kuka ta ɗago daga jikin Ya Ahmad, dawowa gaban Baba Malam ɗin tayi tare da durƙusa guiwowinta a ƙasa, kanta ta ɗaura ajikin Baba Malam ɗin tana wani irin kuka me ɗaga hankali, gaɓa ɗaya jikinta rawa yake, ga kuma wani sheshsheƙa da take saki wanda yasa numfashinta keyi kaman zai ɗauke. Cikin kukan da kuma muryarta wanda bata fita sosai tace. "Nagode Baba Malam! Nagode sosai da ka yafemin, kuma insha Allah zaka sameni me biyayya agareka dashi Hamma Saif..." Kuka take sosai harda majina, Ahankali Saifuddeen ya haɗe hannuwansa, tare da ɗan lumshe idanunsa, alaman godiya, still kuma hawayene kwance akan fuskarsa. Murmushi Baba Malam yayi tare da sanya hannu ya shafi kan Saifuddeen ɗin, tabbas Saifuddeen mutunne me nagarta, da kuma zuciyar imani, sai yanzu yake ƙara aminta cewa bazai taɓa danasanin bawa Saifuddeen auren ƴarsa ba, haƙiƙa Saifuddeen yacika me kyakkyawar zuciya, tabbas irinsu aduniya basu da yawa. Malam Adam ne ya rarrashi Ya Ahmad wanda yake ta kuka, Dirankadi ne yayiwa Baba Malam ɗin godiya, ganin irin kukan da take, yasa Baba Malam yiwa Saifuddeen alama cewa ya ɗauki Zaleehan suje. Wheelchair ɗinsa ya hau, sannan ya sanya hannu ya ɗago ta, kuka take sosai, haka ya riƙe hannunta suka fice daga cikin falon. Anan cikin ɗan corridor ɗin ƙofar falon ya tsaya, tare da zaro handkerchief a al'jihunsa idanunsa wanda suka ɗan lumshe ya zuba mata, sannan ya miƙa mata handkerchief ɗin, Cikin wani irin zazzafan kuka ta faɗa jikinshi tare da kife kanta bisa cinyoyinshi ta saki kuka mai cike da rauni, wani irin tausayinta yakeji na ratsashi a hankali ya ɗan magoya kana ya kuma miƙa mata handkerchief din hannunta na rawa haka ta amshi handkerchief ɗin, ahankali take goge hawayen fuskarta tana sakin sheshsheƙa. Littafina na kuɗine in kina buƙata ga no 09097853276 Wannan shafin nakune NAKASA BA KASAWA BACE fans 3&4 inayi muku fatan al'khairi By *GARKUWAR FULANI* [14/09, 4:05 pm] +234 803 620 1562: Sbpejtt Kai kawai Ummi ta girgiza tare da tashi kaitsaye ta wuce ɗakinta, Hayatuddeen ma dake zaune ji yayi gaba ɗaya jikinsa yayi sanyi, sam baiso hakan ba, yaso ace Hamman nasa ya amince, saboda shima ya gamsu cewa, da taimakon Hamman nashi ne kaɗai Baba Malam zai iya haƙura ya yafewa Adda Zaleeha'n. Haka dai suka kammala cin abincin nasu duk jikinsu asanyaye, acan ɓangaren Saifuddeen kuwa yana barin falon nasa, kaitsaye ɓangarensa ya nufa, sauƙa daga kan wheelchair ɗinsa yayi, tare da haurawa saman ɗaya daga cikin haɗaɗɗun kujerun falon ya kwanta, idanunsa ya lumshe yana jin zuciyarsa nayi masa wani iri, maganganun Ummin ne ya dawo cikin tunaninsa, ahankali ya girgiza kansa, cikin zuciyarsa yace. "Ada ni ba komai bane awajenta, bata ɗaukeni matsayin komai ba, kullum idan akwai wata magana da zai fito abakinta, wanda ta shafeni to baiwuce kalmar ƙiyayya ba, matsalar da ta faɗa ayanzu, shiyasa ta ɗaukeni wani me mahimmanci agareta, ta gudu ne saboda batason aurena, yanzu kuma gashi ta dawo tana zaune aƙarƙashin inuwata, ahaka kuwa shine har da wani neman alfarmarta." wani murmushi me ciwo yayi tare da girgiza kansa, shiba sakarai bane, ita tayi amanta saboda haka ita kaɗai zata lashe. Yana gama tunanin ya gyara kwanciyarsa, tare da sake lumshe idanunsa, yana sakin ajiyar zuciya. Acan ɓangaren Part ɗin Ummi kuwa baccin Zaleeha baiyi wani nisa sosai ba ta farka, Hayatuddeen ne ya kawo mata abinci, haka ya sakata gaba dolen ta saida taci, tana kammalawa kuwa ya miƙo mata ruwa da magungunanta tasha, nan ƙasan carpet ya zauna, ita kuwa tana kwance akan gado, ganin cewa akwai damuwa atattare da itane yasa shi, soma bata labarai wanda yasan dole zasu ɗebe mata kewa, suna zaune ahaka Raleeya ta shigo, akusa da Zaleehan ta zauna, cikin kulawa tace "Aunty Zaleeha ya jikin naki?". ɗan jinjina kanta tayi, asanyaye tace. "Da sauƙi." Murmushi Raleeya tayi, tare da faɗin. "Masha Allah, Allah Ya ƙarasa sauƙi." Da "Ameen" Zaleehan ta amsa, haka dai suka ci gaba da hiransu, Ita dai Zaleeha idanu kawai ta zuba musu, sau dayawa dramer'n Hayatuddeen da Raleeyan na burgeta. Duk dama har yanzu akwai damuwa kwance aƙasan zuciyarta. Suna ahaka Ummi tashigo cikin ɗakin, ganinsu atare ne yasata sakin murmushi, sake gaisheta Zaleehan tayi, ta amsa mata fuska asake, har cikin ranta kuwa taji daɗin ganin Zaleehan cikin ɗan yanayi me kyau, kallon kayan dake jikin Zaleehan tayi, take wani tunani yazo mata hakan yasa tace da Hayatuddeen yazo zata aikeshi. Babu musu ko ya tashi yabi bayanta. Kaitsaye ɗakinta suka wuce, nan kan gado ta zauna, tare da jawo jakarta ta zage zip ɗin, duban Hayatuddeen tayi, cikin kulawa tace. "Makay zan aike ka ne, ko San Hussain Super Market?". ta tambayesa da yanayi na ɗan tunani, zama yayi akusa da ita, tare da cewa. "Wani abu za a sayo miki ne?". "Kaya nakeson kasayowa Zaleeha, kaga dai bata zo da kayanta ba, part ɗin ta kuma akulle yake, na kuma ce Hammanku ya bada key yayimin biris, dama daya ba da key ɗin sai nasa ko Raleeya ne ta ɗebo mata sauran kayanta." cikin zumuɗi Hayatuddeen yace. "Ummi Makay zanje, wallahi dama ina kwaɗayin strowberry cake, kinga kawai sai na shiga Makay shawarma na saya, nasan itama Adda Zaleehan idan na sayo mata zataci." Hararansa Ummi tayi tare da cewa. "To sarkin kwaɗayi, an faɗa maka cewa dama kowa irinka ne, koko ance maka kowa kwaɗayi kawai yasa agaba?." Murmushi yayi, cikin zaƙuwa yace. "Hmm Ummi bakisan wacece Adda Zaleeha ba kenan, ai shan zaƙinta ko shazumami sai haka, yanzu kawo kuɗin naje na sayo mata kayan." Kai kawai Ummi ta girgiza tare da zaro Kuɗin da aƙalla zasu kai 70k, acikin jakanta ta miƙa masa, cikin kulawa tace. "Kanutsu dan Allah Hayatuddeen, dogayen riguna nakeson kasayo mata masu kyau, ni hankalina ma kwata kwata bai kwanta da aikanka ka ba, dan tunda ka iya mota kuma shikenan ka zama ayawo, dan ma ana zaman makokin nan ne da da Zakariyya zakuje, saboda hankalina zaifi kwanciya, saboda ya fika nutsuwa wani lokaci'n." Ɗan bakinsa ya turo gaba, cikin halin sakalcinsa yace. "Yanzu Ummi dan Allah Zakariyya'n ne ya fini nutsuwa." Murmushi Ummi tayi, tana me zuge zip ɗin jakarta tace. "Ni maza yi sauri ka kawomin aikana, sannan kuma katabbatar kayi driving cikin nutsuwa." Haka yafita daga ɗakin yanata wani shagwaɓa, da turo baki gaba, tuno da cewa zaije ya saya strowberry cake yasan yashi sakin murmushi, haka ya fice daga cikin falon, yana karkaɗa ɗan makullin motar dake hannunsa. Zaleeha da Raleeya kuwa har yanzu suna tare, hira Raleeya ke tayiwa Zaleeha'n, ahaka har wani sabon bacci ya ɗauketa, ganin tayi bacci ne yasa Raleeya sakin murmushi, nan tatashi ta fice daga ɗakin dan zuwa kitchine ɗaura lunch. Ummi kuwa ganin fitan Hayautuddeen yasa, ta ɗauki wayarta, text ta turawa Saifuddeen akan cewa tana son ganinsa, tana nan zaune kuwa ko mintuna 7 ba acika ba, sai gashi ya shigo cikin ɗakin. Har gaban Ummin ya ƙaraso da kekensa, sai wani shagwaɓe fuska yake, saboda yasan bai wuce maganan Zaleeha Ummin zatayi masa. Ummi kuwa ɗago kai tayi ta dubesa, cikin nutsuwa tace. "Wai Saifuddeen me kake nufi da Zaleeha ne? tunfa jiya nake binka da ka bani key ɗin ɗakinta amma kaƙi, ko anan kakeso ta zauna mana bayan gacan ɗakinta?" Ɗan kwaɓe fuska yayi, cikin body language ɗinsa yace. "Nifa Ummi bansan inda key ɗin ɗakinta yake ba." gane abunda yake nufi yasa Ummi ɗan buɗe baki, da mamaki tace. "Bakasan inda key ɗin yake ba kuma.?" Kansa ya jinjina alamar "Eh" kuma har ga Allah ya mance inda ya ake key ɗin. Kai Ummi ta jinjina tare da cewa. "Sannu uban maƙaryata, Saifuddeen yaushe ka fara yimin ƙarya? wato ma sokake kace key ɗin ya ɓata ko? hmmm inace nan da Addarku Rahama ta amshi key ɗin tatafi dashi, ko wata ɗaya baicika ba kaje har gidan ta ka amso, ko kana tunanin banida labari ne? kaga tunkan raina ya ɓaci Saifuddeen ka buɗewa yarinyar nan ɗakinta ta koma tayi zamanta." bakinsa ya turo gaba, sam shi baisoma Ummi tanayi masa maganan Zaleeha'n, ai koma me yafaru itace ta jawo, hakanan saboda ta ɗaukesu sakarkaru saita gudu ta kuma dawo alokacin da take so. Kuma zancen gaskiya harga Allah ya mance in da ya ɓoye key ɗin side ɗinta, amman gashi Ummi gani take ƙarya yayimata abinda bai taɓata kwatanta yimataba. Hararansa Ummi tayi tare da ɗanyin ƙwafa tace. "Ayi mutum da taurin kai da riƙo sai kace mutanen farko, wallahi ka tabbatar ka kawomin key ɗinnan tunkan raina ya ɓaci, idan kaƙi kuwa zansa a ɓalla ƙofan da ƙarfi, ta koma ɗaƙinta ta zauna." Idanunsa yaɗan zaro waje, jin cewa za'a ɓalla ƙofar, tuna cewa ma ƙofar bazata taɓa ɓalluwa bane ya sashi ɗan sakin ajiyar zuciya, hannuwansa ya haɗe waje ɗaya, alaman Ummin tayi haƙuri, kuma shi ya mance inda key ɗin yake ne. Haranshi tayi sannan tace. "To batun rakata gidansu ta bawa Babanta haƙurifa ko shima ka mance hanyar gidan ne?". A hankali ya jujjuya mata kai alamun bai mance ba, sai kuma yayi ƙasa da kanshi. Ganin cewa bazai biyu ta sauƙi ba yasa Ummi'n, cewa ya tashi yaje kawai. Yana fita kuwa Ummi tayi ƙwafa tare da cewa. "Ɗan nema zan yi maganinka ne." Daga haka ta-tashi ta wuce toilet dan ɗauro al'walan sallan azahar. Can ɓangaren Hayatuddeen kuwa saboda tsabar kwaɗayi yaci ransa saida ya fara zuwa makay shawarma ya sayi strowberry cake ɗinsa, ya kuma haɗa da roasted fish, saboda yasan Adda Zaleehan naso kuma idan ya kai mata zata ci. Saida ya gama ƙwalamarsa kafun yafito daga Makay Shawarma ɗin, kaitsaye ya nufi cikin Makay Super Market, ɓangaren da dogayen rigunan mata suke ya nufa, sosai ya darje wajen zaɓawa Adda Zaleehan nasa dogin riguna masu kyau, bai tsaya anan ba kuwa harda wasu riga da sket ƴan kanti masu kyau kusan kala uku ya zaɓa mata, haka dai ya gama sayayyyan cikin nutsuwa, sannan ya ƙarasa wajen biyan kuɗi, koda akayi lissafin kayan kuɗin sun haura wanda Ummi ta basa, dan 70k Ummi ta basa, kayan da ya saya kuwa sun haurawa haka, dan kuɗinsu 77k ne, baiwani damu ba, haka ya zaro ATM card ɗinsa dake cikin aljihunsa ya basu, kasancewar dama yana aje ƴan kuɗaɗensa anan cikin asusun banki, dan sau dayawa kuɗin da Hammansa ke basa ba kashewa yake ba, yakan tarasu ne idan sun ɗanyi yawa sai yakai ƙaramin account ɗinsa na bank ba asalin babba da ake sa mishi kason dukiyarsa ba a ƙaramin yake ɗan gutun ajiyarsa, haka dai suka zare 7k ɗinsu suka basa ATM card ɗinsa, daganan kuma suka zuba masa kayan acikin leda. Har mota kuwa sukasa aka kai masa kayan, haka ya ɗauki hanyar gida, sai ciye ciye yake acikin motar. Koda ya ƙarasa gida kuwa, Ummi ya bawa kayan, dan har zuwa lokacin Zaleeha bata tashi abacci ba, babu laifi kuma Ummi ta yaba da rigunan dan sunyi kyau sosai. Saifuddeen kuwa tunda yabar part ɗin Ummi ɓangarensa ya koma, al'wala yayi sannan ya nufi masallaci, tunda yayi sallan azahar kuwa bai dawo gidan ba, Sule driver yaƙira suka ɗan fita, saboda wani aikin daya taso masa, dole saida yaje office ɗinsu, saida aka kusa sallan la'asar sannan ya dawo, anan masallacin ƙofar gidansu yayi sallan la'asar, sannan ya shigo cikin gidan, ɓangaren Ummin nasa ya sake nufa, dan kuwa ɗazu koda yana zaune a office saida yaga text message ɗinta, kancewa "Lallai ya kawo mata key ɗin ɗakin Zaleeha, sannan kuma ya tabbatar yazo yakai Zaleehan gida ta bawa Baba Malam haƙuri." Shidai kam yama rasa yanda zaiyi. Yana shiga falon kuwa ya iske Ummi da Ahmad, sai kuma Hayatuddeen dake zaune ƙasan turkish carpet yana ta faman lodawa cikinsa abinci. Ganin yanda fuskar Ummi take babu wani walwala asamanta yasa yaji jikinsa yayi sanyi, ƙarasowa cikin falon yayi tare da bawa Ahmad hannu suka gaisa, saboda yau duk basu haɗuba. duban Ummin nasa yayi, asanyaye cikin body language ɗinsa yayi mata sannu da gida. Kai kawai ta jinjina masa, ko kallonsa batayi ba, hakanne yasa jikinsa ƙarayin sanyi, sam baisom fushin Ummin nasa. Ummi kuwa da gangan ta nuna cewar tana fushi dashi, saboda tasan idan ba haka tayi masa ba bazai taɓa yin abun da ta sakashi ba. Raleeya wanda shigowarta falon kenan, ganin Hamman nata yasa ta wuce kitchine, abinci da drinks ta zubo masa, saboda yau ɗin favorite food ɗinsa ta dafa. nan gabansa ta ƙaraso tare da ɗan durƙusawa, ƙoƙarin aje plate ɗin abincin agabansa take, cikin sauri yaɗan riƙe hannunta tare da girgiza mata kai, alaman ya ƙoshi, kallon sa tayi fuskarta ɗauke da ɗan damuwa, kansa ya jinjina mata alaman cewa. "Tayi haƙuri bayajin yunwa." Asanyaye ta ɗaga kanta ta kalli Ummi, gani tayi fuskar Ummin atsuke, hakanne yasa ta juyawa ta maida abincin kitchine. Cikin sanyin jiki ya danna madannin wheelchair ɗinsa tare da ƙarasawa gaban Ummin nasa, hannunta ya kamo tare da ɗan shagwaɓe fuska, ɗago kai tayi ta dubesa. Rau-rau yayi da idanunsa, tare da yi mata alama kancewar "Tayi haƙuri karta ce zatayi fushi da shi." gane hakanne yasa Ummi ta sake haɗe fuska, tare da ɗan kau da kanta gefe, cikin haɗe fuska tace. "Idan ma nayi fushi dakai ae kai ka nema, meyasa zanta maimaita maka magana ɗaya, amma ka kasa aiwatarwa, tunjiya naketa binka, akan maganan key ɗin ɗakin Zaleeha, sannan ga kuma maganar rakata ta bawa Babanta haƙuri, amma gaba ɗaya ka share maganta, bansan yaushe kazama haka ba Saifuddeen, bansan kuma meke damunka da har yasa ka kasa jin tausayin Zaleeha acikin ranka ba, To Wallahi matuƙar ba ɓacin raina kakeson gani ƙiri-ƙiri ba, tun wuri kaɗauki yarinyarnan kuje ku bawa Baba Malam haƙuri, tun da dai idan har dakai taje, baban nata zai iya yafe mata." Idanunsa ya rumtse, lokaci guda yaji zuciyarsa na bugawa da ƙarfi, ɗanjan kekensa baya yayi, tare da zamewa ya durƙusa akan guiwowinsa, sake kamo hannun Ummin nasa yayi, lokaci guda ya shiga girgiza mata kai, sosai rauni ya bayyana akan fuskarsa, cikin body language ɗinsa yace. "Dan Allah Ummi kiyi haƙuri, ki bani ko wani irin umarni ne zan bi, sannan kuma bazan taɓa bijiremiki ba, amma dan Allah kada ki tursasani kan cewa na raka Zaleeha ta bawa Baba Malam haƙuri, idan nayi hakan Ummi zan cutu, tunda batasan ina da ƙima ba sai yanzu da matsala ta taso mata? kuma ma Ummi lokacin da tayi lefinta tare dani tayi ne? ai ita kaɗai tayi lefinta, da tazo guduwa kuma bata shawarceni ba, tanajin cewa ta isa shiyasa ta gudu alokacin da takeso, ta kuma dawo alokacin da takeso, ni nasan sam bata shirya yin nadama ba, kawai dan rasuwar Adda Maryam ne, amma bacin haka ai bazata dawo ba." Dubansa Ummi tayi tare da ɗan girgiza kai, sam bata taɓa tunanin cewa wai Saifuddeen zaiyi fushi akan maganar Zaleeha ba, amma babu komai tayi masa uzuri, saboda tasan ba har zuciyarsa maganar da yake faɗi take fitowa ba, gyara zamanta tayi, cikin son nusar dashi da kuma yanda zai fahimta tace. "Koma me Zaleeha ta maka, bai kamata kayi irin wannan fushin da ita ba, sannan kuma kaima shaida ne akan irin damuwar da take ciki, ca nake jiya anan gabanka ta suma, ko so kake mu barta haka, mu zuba mata idanu ciwon zuciya ya kamata? ko kuwa so kake mubar rayuwarta cikin garari?, kakuwa san halin da take ciki? bata da wani abunyi sai kuka dare da rana, bata da wani sauran farinciki, da wanne zataji, mutuwar ƴar uwarta ko kuwa ƙunci da baƙin cikin rayuwa? ko Allah ma muna masa laifi me girma, amma damunyi kyakkyawan tuba yake yafe mana, saboda meyasa to mu bazamu yafe mata ba?." Rumtse idanunsa yayi da ƙarfi tare da tattauna lips ɗinsa, sosai yakejin wani abu azuciyarsa, wanda shikansa bazai iya fassara sa kaitsaye ba. Raleeya wanda tuni idanunta sun ciko da ƙwalla ne ta ɗan matsa kusa da Ahmad, cikin sanyi tayi masa alamar cewa. "Ya taimaka yasa baki, Hamma Saifuddeen ɗin ya raka Zaleeha ta bawa Baba Malam ɗin haƙuri, saboda rashin agaza mata zai iya sawa ta kamu da wani ciwon, musamman ma idan akayi la'akari da yanda take wuni kuka." Jinjina mata kai Ahmad ɗin yayi alaman "Yaji kuma zaiyi wa Saifuddeen ɗin magana. Hayatuddeen dake zaune shikansa saida yaji hawaye sun cika masa ido. Ummi kuwa gaba ɗaya ranta ya gama ɓaci, domin shirun da Saifuddeen ɗin yayi, alamace dake nuna cewa, har yanzu yana kan bakansa, hakan ne yasa cikin fushi ta tashi ta nufi ɗakinta. Cikin sauri Zaleeha dake tsaye jikin ƙofa ta koma ɗakinta, dan batason wani daga cikinsu ya ganta, saboda tunda suka fara magana'n harzuwa yanzu tana jinsu, duk da cewa Saifuddeen ɗin baya magana, amma ayanayin yanda yake gudanar da body language ɗin nasa, yasa ta fahimci komai dake zuciyarsa, ga kuma alaman fushin da yakeyi da ita da ya bayyana ƙarara, zamewa tayi anan jikin ƙofar ɗakin ta saki wani irin kuka mai taɓa zuciya, dama shi kaɗaine hope ɗinta, kuma shima gashi yaƙi amincewa, shikenan bata da wani me taimakonta ayanzu ta tabbata fushin uba dana mijinta yana kanta, kuka ta shigayi sosai, sanin cewa yanzu bata da wani madafa, ya zatayi mijinda a ƙarƙashin shi aljannarta yake yana fushi da abinda ta aikata a baya,kana babanta mahaifi yana fushi da ita ya zatayi, ta ina zata fara neman tafiyar mijinta. Saifuddeen kuwa ganin Ummi ta tafi cikin fushi, yasa yaji gaba ɗaya jikinsa yayi masa sanyi, sosai zuciyarsa ta karye, damuwa me tarin yawa ya ɗarsu acikin ransa, sam bai saba da fushin Ummi ba, asanyaye ya hau saman wheelchair dinsa, ahankali yake tura keken har ya fice daga cikin ɗakin, part ɗinsa ya nufa, yana shiga kuwa ya laluɓo wayarsa dake cikin aljihu, numbern Ummin nasa ya laluɓo, asanyaye ya shiga rubuta mata text message, sai ya faɗi maganar acikin zuciyarsa, kafun yake rubutawa, kalamaine naban haƙuri, ya turawa Ummin nasa inda yace _"Kiyi hakuri Ummina, akullum bana fatan na zamo me ɓata miki,ko yanzu ma ba'a son raina bane nakasa bin umarninki, kawai dai naga abun da Zaleehan tayi ne bai dace ace an roƙa mata yafiya ba, ta gujemu tayi tafiyarta, sai yanzu da duniya da kuma ƴan uwanta suka juya mata baya shine ta dawo garemu, wato mu gidanmu ya zama gidan ƴan iska kenan, da zata tafi ta kuma dawo alokacin da take so, nayi hakanne bawai dan na ɓata miki ba, kiyi haƙuri Ummi ki yafemin"_ Yana gama rubutun yayi sending message ɗin, tare da ɗan kifa kansa ajikin keken nasa, kana ya lumshe idanunsa. Ummi na zaune akan gado, saƙon ya shigo, koda ta gama karanta saƙon nasa murmushi tayi, dama ita ba fushi tayi dashi ba, tayi hakanne kawai saboda yayi mata abun da takeso. amsa ta shiga rubuta masa, tare da jaddada masa cewar _"Yayi abun da takeso kawai, idan kuma baso yake, damuwa yayi sanadiyar taɓa zuciyar Zaleehan ba, dan jiya kwana tayi kuka, bakin cikin rayuwa sunyi wa Zaleehan yawa, da wanne zataji mutuwar ƴar uwarta ko kuwa fushin da Babanta keyi da ita? sannan gefe guda kuma ga fushin ƴan uwanta, ga kuma shima da ya kamata ace yazame mata garkuwa fushi yakeyi da ita, meyasa bazaiji tausayin Zaleeha'n ba, wanda har yanzu yasan cewa, ita yarinyace, sannan kuma tayi nadama har acikin zuciyarta."_ tura masa saƙon Ummi tayi tare da aje wayarta. Shi kuwa Saifuddeen yana gama karanta saƙon Ummin sake lumshe idanunsa yayi, zuciyarsa duk ba daɗi. Cikin sanyi ya rubuta cewa. _"Kiyi haƙuri Ummi banso na ɓata ranki ba, shikenan naji na amince zan rakata, amma dan Allah Ummi kiyi haƙuri zuwa gobe idan anyi sadakan uku saina kaita kafin nan mutane sun ɗan ragu a gidan nasu"_ Murmishin farinciki da samun nasara Ummi tayi, bayan ta gama karanta text message ɗin daya turo mata, nan tace dashi. "Allah ya kaimu goben." Sai alokacin ya ɗanji sanyi acikin ransa, saboda yasan zuwa yanzu, zuciyar Ummin nasa zata ɗanyi sanyi. Can ɓangaren Zaleeha kuwa kuka tasha sosai har taji babu daɗi, dan kanta haka ta share hawayenta saboda koma menene tasan ita ta jawa kanta, ko ahaka suka barta ma, tasan sunyi mata gata tunda suka bata muhallin zama, abun da ƴan uwa da mahaifinta suka kasa yi mata kenan saboda fushin da sukeyi da ita. Ganin kukan bazai kaita ba yasa ta tashi ta wuce toilet tare da wanko fuskarta wanda tayi ja sosai saboda kukan da tayi, fitowarta daga toilet ɗin kuwa yayi dai-dai da shigowar Ummi cikin ɗakin, ganin fuskar Zaleehan da kuma idanunta sunyi luhu luhu, yasa Ummi kamo hannunta suka zauna anan bakin gado. Cikin kulawa Ummi tace. "Kuka kikayi ko?" Sadda kanta ƙasa tayi, saboda bazata iya musawa Ummi'n ba, kanta Ummi ta shafa, tare da cewa. "Ki kwantar da hankalinki kinji, Insha Allah gobe Hammanku zai kaiki kuje ku bawa Baba Malam haƙuri, kuma Insha Allah Baba Malam zai yafe miki, ki daina kukan nan kinji!." Ummi tafaɗi maganar cikin lallashi, jin cewa Hamma Saifuddeen ɗin ya yarda zai kaita yasa taji wani irin farinciki ya lulluɓe Zuciyarta, hakanne yasa ta faɗa jikin Ummi ta saki kuka. Rarrashinta Ummin ta somayi tare da sanya hannu tana shafa bayan Zaleeha'n, cikin kukan tace. "Nagode sosai Ummi, haƙiƙa kin zame min uwa, nagode sosai..." saurin rufe mata baki Ummi tayi, cikin kulawa tace. "Kamar ƴa haka na ɗaukeki Zaleeha, saboda haka bama saikin min godiya ba, duk wani burina bai wuce farincikin ku, Allah Ubangiji ya muku al'barka, ungo wannan kayan ɗazun Hayatuddeen ya sayo miki su." Ummi ta faɗi maganar tana me miƙawa Zaleehan ƙatuwar ledan dake hannunta. Amsar ledan tayi cikin farinciki tace. "Nagode sosai Ummi." har cikin ranta taji daɗin kayan, saboda itama kayan jikin nata sun isheta, yau kwanansu biyu kenan ajikinta, abunda tunda take aduniyarta bata taɓayi ba kenan, dama haka rayuwa take tana juyawa da abubuwa kala-kala, wai ita Zaleeha me yawan ado da kwalliya uwa uba ƙwalisa, itace ke sanye da kaya ɗaya ajikinta har tsawon kwanaki biyu, bacin da arana ɗaya saita sanja kaya kusan kala uku, amma yau gashi komai ya juya mata, damuwa ya mata yawa, wani lokacin har takan manta wasu abubuwan da suka shafeta. Ummi kuwa tashi tayi inda da kanta ta shiga toilet ta haɗawa Zaleehan ruwan wanka me ɗumi, cikin kulawa Ummi tace da Zaleehan ta shiga tayi wanka, babu musu kuwa ta shiga rage kayan jikinta, ganin haka yasa Ummi fita daga cikin ɗakin, tare da jawo mata ƙofa. Jikinta aɗan sanyaye haka tayi wankan, ba laifi kuwa taɗanji damuwarta ta ragu, nan cikin kayan da Ummin ta kawo mata ta zaɓo wata doguwar abaya gown me kyau ta sanya, sam damuwar da take ciki kuwa bai hana zallan kyawunta fitowa ba, gashi rigar ta amshi jikinta tayi mata ɗas, mayafin doguwar rigar ta yafa, sannan cikin yanayin sanyi ta fito zuwa falo. Nan ta iske Raleeya da Hayatuddeen zaune, Raleeya karatun littafin hausa take, shikuwa Hayatuddeen game ya haɗa yakeyi. Yana ganinta ya ɗan waro idanunsa, tare da cewa. "Wow Adda Zaleehan mu kinyi kyau, yeah ashe dai niɗin gwanine wajen iya zaɓen kaya." Murmushi tayi masa, tare da zama anan kusa da Raleeya. Duban Raleeya tayi cikin kulawa tace. "Sister sannu da gida." cikin sakin fuska Raleeya tace. "Yauwa sannu my kyakkyawar Auntyn mu, halan wannan kwalliyan duk na hamma ne" Raleeya ta ƙare maganar cikin yanayi naɗan tsokana, murmushi Zaleehan tayi wanda har saida fararen haƙwaranta suka bayyana, nan ta sadda kanta ƙasa tana tunanin. Uhum Hammanku kam ko kallo ban isheshiba ba ai. Hayatuddeen kuwa tashi yayi ya wuce ɗakinsa, mintuna kaɗan sai gashi ya dawo da leda ahannunsa, nan kan cinyarta ya ajiye mata, cikin kulawa yace. "Aunty roasted fish ne da cake, please kici kinji, nasan kinaso." murmushi tayi tare da cewa. "Nagode auta." Dukansu murmushi sukayi sannan suka shiga ɗan taɓa hira, ita dai haryanzu akwai damuwa kwance aƙasan zuciyarta, hakanne ma yasa maganarta bai wuce. "Eh, ko A'a ba". Suna nan azaune Ummi ta fito ta samesu, zama tayi acikinsu, itane ma take ƙoƙarin jan Zaleehan da hira. Saifuddeen ne ke tura wheelchair ɗinsa, yana son ƙarasawa part ɗin Ummi, dai-dai lokaci Ameena wanda dawowarta daga aiki kenan ta shigo cikin gidan, ganin Saifuddeen ɗin yasa ta ƙaraso da sauri tana sakar masa murmushi, shiɗinma murmushin ya sakar mata, tare da miƙa hannu ya karɓi Adeel dake rungume akafaɗanta. Ɗan ranƙwafowa tayi tayi mishi kiss a forehead ɗinsa, cikin kulawa tace. "Nayi kewarka Mijina." murmushinsa me kyau yayi mata, tare dayi mata alaman cewa shima haka, nan ta riƙe saman wheelchair ɗin nasa, tana turasa shikuwa yana riƙe da Adeel haka suka nufi part ɗin Ummi. Ahankali suka tura ƙofar falon suka shiga bakin Ameena ɗauke da sallama, hakanne yasa gaba ɗayansu suka ɗago kai suka kallesu, Ummi ne ta fara amsa sallaman, kafun suma suka amsa, kallo ɗaya Zaleeha tayi musu ta duƙar da kanta ƙasa, cikin kulawa Ummi tace. "Mutanen asibiti kun dawo." Murmushi Ameena tayi, wanda ganin Zaleeha cikin shiga me kyau yasa duk taji zuciyarta ba daɗi, ɗan durƙusawa tayi tare da cewa. "Ummi barka da gida." Murmushi Ummi tayi tare da cewa. "Yauwa Ameena ya wajen aikin naki?" tana murmushi ta amsa da lafiya lau, Raleeya da Hayatuddeen ne sukayi mata sannu da dawowa, baki awashe haka ta amsa musu, duk dama dai aranta sam bataji dadin ganin Zaleeha ba, gashi kuma Zaleehan tayi kyau sosai, Ɗago kai Zaleeha tayi tare da ɗan kallon Ameena'n, cikin sanyin murya tace. "Ummu Adeel barka da dawowa." Cakwai haka Ameena taji muryan Zaleehan acikin kunnuwanta, take kuwa taji kaman an watsa mata ruwan zafi ajikinta, wani irin haushin Zaleehan ne ya cika mata zuciya, amma ganin idon su Ummi yasa ta ɗanyi yaƙe tare da cewa. "Yauwa Sannu." Ɗan ɗago kai Zaleeha tayi ta saci kallon Adeel dake kan cinyar Saifuddeen, Gani tayi Adeel ɗin na kallonta, hakan yasa ta sakar masa murmushi wanda har saida dimples ɗinta suka lotsa, shima yaron murmushi yake ta mata yana wangale mata haƙora tare da mutsu-mutsu har yana zamowa tare da miƙo mata hannu alamun ta ɗaya shi. Cikin dariya Hayatuddeen yace. "Aunty Zaleeha ke yakeyiwa hakafa". murmushi Ummi tayi tare da cewa. "Ae wannan ɗan naku saiku yaron ba dai ƙirniya ba abinda ya iya". Murmushi sukayi baki ɗaya su. Ita kuwa tashi tayi daga zaunen da take, gaba ɗaya ta gama mantawa cewar ma yaron akan cinyar Saifuddeen ɗin yaƙe, ƙarasawa tayi tare da ɗan ranƙwafawa tasa hannu zata ɗauki Adeel ɗin, daddaɗan ƙamshin turarensa ne ya daki hancinta, cikin tsautsayi kuwa hannunta ya gogi nasa, wani irin shock sukaji su duka biyun, ahankali ta ɗauki Adeel ɗin, sannan ta ɗagashi sama tana sakar masa murmushi, baki ya wangale mata harda tsalle shi, Allah ya sani tana son Adeel har cikin ranta kuma shima yaro yana sonta. Baki buɗe Ameena ke kallonsu, kishi kuwa haka takeji kaman zai fasa ƙirjinta, ƙwarai tazo iya wuya, dan kasantuwar Zaleeha akusa da Saifuddeen ɗin baƙaramin dacewarsu ta gani ba. Ummi kuwa jin wayarta dake cikin ɗaki na ƙara yasa tatashi ta bar musu falon, Raleeya ma miƙewa tayi ta haura sama. Nan falon ya rage daga Hayatuddeen, Zaleeha, sai su Saifuddeen ɗin, Zaleeha kuwa rungume Adeel ɗin tayi tana yi masa wasa, Saifuddeen kuwa ahankali yake ɗan satan kallon Zaleeha'n, saboda tayi masa kyau sosai, duk da kasancewar ma ya lura cewa idanunta aɗan kumbure suke kuma gaba ɗaya yanayin rayuwarta ta sauya ta zama mai sanyi, hakan yasa shi jin wani abu na tausayi acikin ransa. Ameena kuwa ganin cewa Saifuddeen ɗin na ɗan satan kallon Zaleehan ƙasa-ƙasa ne, yasa taji gaba ɗaya ranta ya ɓaci, wani irin matsanancin kishi ne ya taso mata, amma saita dake, cikin kirsa ta tashi ta dawo kusa da Saifuddeen ɗin, ɗan durƙusawa tayi tare da tallafo haɓarsa cikin son nunawa Zaleeha matsayinta tace. "Mijina Mekakeso na kawo maka kasha?" Shikuwa sanin cewa Zaleeha na falon, yasashi jawo hannun Ameenan kusa dashi, kissing ɗinta yayi, tare da nunata da hannunsa, alaman ita yake so, wani irin daɗi haɗi da farinciki ne suka cika zuciyar Ameena, wani irin fari tayi da idanunta, da ɗan ƙarfi yanda ta tabbatar cewa Zaleehan zataji tace. "Indai nice kasameni." Saman Wheelchair ɗinsa ta kama, tare da juya akalan keken suka fice daga cikin falon, sai sakin wani shu'umin murmushi takeyi. Duk da cewa duk abun da sukeyi tana jinsu, amma gaba ɗaya hankalinta ba akansu yake ba, sam kuma bataji wani abu na ɓacin rai dangane da hakan ba, gaba ɗaya ma ita hankalinta naga wajen yiwa Adeel wasa, sai dai tana jin zuciyarta na riƙe da abinda sukayi. Hayatuddeen kuwa sosai hakan da Ameenan tayi yasa yaji ba daɗi, saboda ya fahimci cewa, Ameenan so take ta ƙuntatawa Zaleeha, amma ganin cewa Zaleehan bata damu ba, yasashi girgiza kansa kawai ya ci gaba da game ɗinsa. Ameena kuwa suna isa part ɗinsu, cikin mazari tasoma ƙoƙarin rage musu kayan jikinsu, jin ranta take fari ƙal, saboda hakane ma zata gwadawa Saifuddeen ɗin soyayya kala-kala, tayanda sai tasa ya manta da wata Zaleeha. Afalon Ummi kuwa saida aka ƙira sallan Magriba, kafun Ummi ta karɓi Adeel, inda tace da Zaleeha taje tayi sallah. Koda ta idar da sallan kuwa bata tashi akan sallayan ba sai da aka idar da sallan isha, daganan bata ƙara leƙa waje ba, kifi da kuma cake ɗin da Hayatuddeen ya bata shi taɗan ci, sannan ta kwanta, take kuwa bacci ya ɗauketa. Saifuddden da Ameena kuwa, yau zagewa tayi ta nuna masa soyayya kala kala, babu laifi kuma shima ya biye mata, hakanne kuma yasa kasantuwarsu tayi mata armashi, dan bakaɗan ba takejin daɗin Saifuddeen. Haka ko da suka kwanta bacci tawani rungemesa, ranta kuwa fari ƙal, bata da wani damuwa, saboda kasantuwarsu na yau yasa tanajin kanta kamar wata sarauniya. Washegari Yau ya kama Lahadi, inda gobe Monday Amina zata fara zuwa aikin rana. kuma yaune ake sadakan Uku na rasuwar Adda Maryam, Inda sukejin mutuwar ta dawo musu sabuwa, sosai suka sha kuka har suka godewa Allah, yayinda mafi yawancin mutanen da suka zo musu ta'aziyya duk kowa ya kama gabansa. Haka gidan ya rage daga, su Yaya Ahmad sai kuma Hajja Inna da Goggo maryama, sai kuma su Ziyada da kuma wasu mata guda biyu, wanda suke ƙannen. Yaya Ameenu ne, wato Zainab da kuma Ubaida, sai wanda suma dukansu matan aure ne, sai Hajja Ma'u mahaifiyarta Ya Ameenu kenan rasuwar ne ya sasu zama anan gidan na Baba Malam, wanda suɗin ma yau zasu tafi, zuwa yanzu babu wani baƙo ko ɗaya da ya rage acikin gidan, iya su yasu ne, haka suka sha kukansu suka ƙoshi, daga ƙarshe sukayiwa Adda Maryam ɗin addu'a da fatan Allah ya raya ɗanta Ayman. Can gidan su Saifuddeen kuwa, Yau Zaleeha da wuri ta tashi, tana idar da sallah kuwa tawuce ɗakin Ummi ta gaisheta, anan ta iske Saifuddeen ɗin, koda ta gaishesa, saida ya ɗauki kusan second 30 kafun ya jinjina mata kai alaman ya amsa, haka tatashi ta koma ɗakinta jikinta duk asanyaye, shikuwa falon Ummi ya koma ya zauna. Wanka tayi sannan tasaka ɗaya daga cikin riga da sket ɗin da aka sayo mata, ganin kayan ya kamata yasa ta ɗaura hijab akai, murɗa handle ɗin ƙofar tayi tafita, dan tanason fara taya Raleeya aikace aikacen gidan. Tana fitowa falon kuwa anan zaune ta iskesa, sadda kanta ƙasa tayi sannan ta wuce kitchine, Sarai ya ganta amma saiyayi kaman bai ganta ba, saida ta wuce yabi bayanta da kallo, harda wani ɗan lumshe idanunsa. Tana shiga kitchine ɗin kuwa tasamu Raleeya na firan dankali, amsa tayi ta soma tayata suna ɗan taɓa hiransu. Ameena ce tashigo cikin falon, ɗauke da Adeel akan kafaɗunta, ganin Saifuddeen zaune afalon Ummin yasa ta sakin murmushi, shima murmushin ya sakar mata, har acikin ransa yaji daɗin ganinta yanzun, dan da itane zaina buga Game ɗinsa, wanda ya tabbata wata rana kuwa zaiyi winning, ƙarasowa cikin falon tayi, tare da ajiye masa Adeel akan cinyarsa, nan ta wuce ɗakin Ummi, koda taje ɗakin na Ummi kuwa cikin ladabi ta gaisheta, fuska asake Ummi ta amsa mata, tare da tambayanta Adeel, murmushi tayi tare da cewa. "Ummi yana falo suna tare da Abban shi." Itama Ummin murmushi tayi tare da jinjina kanta, dan tana lazumi ne, batason magana. Miƙewa Ameena tayi ta fice daga ɗakin, Tana fitowa falo Saifuddeen ya miƙo mata hannunsa, cikin jin daɗi ta ɗauke Adeel dake kan cinyarsa tayi, ta ɗaurasa akan kujera, raɓawa kan cinyar Saifuddeen ɗin ta ɗanyi dan taga falon ba kowa kuma tasan Ummi na lazumi ba yanzu zata fitoba, ahankali ya sanya hannuwansa, ya saƙalo waist ɗinta, harshensa yasa inda ya ɗan laso lips ɗinta, idanunta ta ƙura masa bata ko ƙiftawa, ganin haka yasashi ɗan ɗaga mata gira, murmushi tayi tare da sake shigewa jikinsa, fuskarta ya ɗago ya haɗe bakinsu waje ɗaya, jin haka yasa ta kamo laɓɓansa tana tsotsa sosai. Gaba ɗaya sun shagala, musamman ma Ameena, wanda idan tana shan laɓɓansa takejin kamar tana shan sweeet. Adeel kuwa sai wutsil wutsil yake, yanason jawo flowern dake gefen kujera, hakanne yasa har yazo bakin kujeran batare da sun ankara ba, Zaleeha ce ta fito daga cikin kitchine ɗin hannunta riƙe da flask, da sauri taja baya sakamakon abun da idanunta suka gane mata, ƙoƙarin komawa cikin kitchine ɗin take, idanunta suka sauƙa akan Adeel wanda saura ƙiris ya faɗo daga kan kujeran, cikin sauri ta ajiye flask ɗin hannunta, da gudu ta ƙarasa inda yake, dai-dai lokacin kuma har ya faɗo daga kan kujeran, saidai kuma bata bari yakai ƙasa ba, tayi saurin zubewa akan guiwowinta ta taro sa, yafaɗa jikinta, wani irin firgitaccen ihu ya saki har kamar zai shiɗe dan yayi masifar tsorita ruggumeshi tayi a jikinta da kyau, hakan yasa ya ƙanƙameta tare da kuma cilla ihu, wanda hakanne ya fargar dasu Saifuddeen, azabure suka juyo suna kallonsu, ɗagosa Zaleeha tayi tare da mannasa aƙirjinta, tana jijjigasa, Idanu Saifuddeen ya zuba mata, ita kuwa Ameena hakanan taji wani iri aranta, kukan Adeel ɗinne yafito da Ummi, daga ɗaki, harta Raleeya ma saida tafito, cikin kulawa da tsananin son yaron Ummi tace. "Lafiya kuwa me ya sameshi." ta ƙarasa maganar tana shafa kanshi tare da kallon Zaleeha Cikin damuwa murya a tausashe Zaleeha kamar zatayi kuka tace. "Faɗowa ya kusayi daga kan ƙujera, inaga shiyasa ya tsorata, gashi yana ta kuka." ta faɗi maganar tana me ci gaba da jijjigasa, saboda sam batason kukan Adeel ɗin, tanajin yaron sosai aranta, ganin baiyi shiru bane yasa ta sanya bakinta akunnenshi tana ɗan hurawa masa isaka tare da ɗan bubbuga bayanshi kana tana jijjigashi, wanda hakanne ya bawa jikinta damar rausaya wa, take kuwa yayi shiru, tare dayin lub ajikinta, jin yayi shiru yasa ta wuce ɗakinta dashi. Har zuwa lokacin kuwa idanun Saifuddeen akanta suke, Ameena kuwa gaba ɗaya ma takasa tantance meke damunta, tausayin ɗanta ne ko baƙin ciki da kishi takasa tantance wanne ne ɗaya, ganin lokaci na ƙurewa yasa ta juya ta fice daga falon dan batason tayi lattin zuwa wajen aiki dan yau ɗin mitin zasuyi da manyan likitoci. Zaleeha kuwa tana shiga ɗaki, ruwa me ɗan ɗumi ta haɗa, tayiwa Adeel ɗin wanka, Hayatuddeen ne ya shigo cikin ɗakin, hakan yasa tace dashi yaje ya karɓo mata kayan Adeel tasa mai. Part ɗin Ameenan yaje, ya amso kayan sannan ya kawo mata, tsab ta shirya Adeel ɗin cikin kayansa me kyau, sosai kuwa yaron yayi kyau, haka ta rungumesa aƙirjinta tana ta yi masa wasa. Ganin alamun bacci yakeji yasa ta ɗauki towel ta goyeshi ai tuni yayi bacci. Saida Ameena ta zo tafiya aiki sannan ta amshe sa, still agaban Zaleehan Saifuddeen ya sake jawo Ameenan yayi mata kiss abayan hannunta kafun ta tafi, Zaleeha kam idan ta kallesu sau ɗaya bata yarda ta sake kallonsu, zuwa yanzu ma mamaki suke bata dan ta lura basa gajiya da tsotse, saidai kuma idan ta tuna cewar rashin damuwa ne ke sasu hakan, sai taji matsanancin tausayin kanta. Tace su kam sunji daɗi da basu da damuwar duniya. Koda tayi break ɗaki ta komawa tayi ta kwanta, cikin zuciyarta kuwa fargaba ne, me tarin yawa, saboda batasan ta yaya zata fuskanci Baba Malam ba. Saifuddeen kuwa sanin cewa yau ne zaikai Zaleehan ta bawa Baba Malam haƙuri, yasa shi barin gidan ma gaba ɗaya, bashi ya dawo ba kuwa sai wajajen sallan azahar. Kaitsaye ɓangaren sa ya wuce, wanka yayi sannan ya shirya kansa cikin wata ɗanyar getzner me masifar kyau da tsada, kasancewar getzner ɗin na sa nada kalan coffee, shi yasa ya matuƙar amsar farar fatar jikinsa, yayinda akayiwa getzner ɗin dinkin half jumper da kuma wandon pencil, wata murzazziyar hula mai kalan light coffee ya ɗaura akansa, hatta takalmin dake ƙafansa me kalan dark coffee ya sanya, yayi kyau matuƙa ga kuma apple touch watch ɗinsa dake ta faman ɗauke ido, tabbas Saifuddeen yayi kyau ƙwarai, dan bazaka kallesa sau ɗaya ka ɗauke idanunka ba, haɗaɗɗiyar sajen dake kwance akan fuskarsa kuwa ta kwanta tayi lub lub, jajayen laɓɓansa kuwa sai sheƙi suke, ga wanda baisansa ba zaice wani abun ya shafa musu, amma ko ɗaya haka yake, sirrin kyau ajininsa yake. Wayoyinsa ya zura acikin aljihun rigarsa, sannan kai tsaye ya danna madannin wheelchair ɗinsa ya fita daga cikin ɗakin, sai baza ƙamshi yake. Anan compound ɗin gidan kuwa, sanin cewa zasu fita yasa Sule driver tuni ya gama tsabtace motar da zasu fita da ita ɗin, wata haɗaɗɗiyar mercedes benz ce me kyau, sabuwa dal sai sheƙi take tana ɗauke ido, fitowarsa compound ɗin gidan ne, ya hango Sule driver, hakanne ya sashi ƙarasawa wajen Sule driver'n, cikin kulawa Sule driver'n, yayi masa barka da fitowa, da kai ya amsa masa kamar koda yaushe. Buɗe murfin motar yayi, nan ɓangaren gidan baya ya shiga, dan dama shi baicika zama agaba ba, akomansa yafison sirri, musamman ma yanzu da yake mazaunin jami'in sirri, yana shiga ya jawo murfin motar ya rufe, wayarsa ya laluɓo daga cikin aljihunsa, cikin text message ya shiga, ataƙaice ya rubuta cewa. _"Ummi kice mata tayi sauri, dan tana ɓatamin lokaci."_ yana gama rubutun yayi sending, tare da maida wayan ya ajiye, laptop ɗinsa ya ɗauko yana dannawa. Ummin kuwa dama tuntuni tasa Zaleehan ta shirya, tsab cikin ɗaya daga cikin sabin rigunan da tasa aka sayo mata, duk da cewa akwai yanayin damuwa mai yawa akan fuskarta, amma hakan baihana kayan yi mata kyau ba, saboda doguwar rigace irin abaya ɗinnan ta larabawa me kyau, yayinda ta yane kanta da ɗan kwalin kayan, wanda ya sauƙo har zuwa ƙirjinta. Tunda ta gama shiryawan take zaune abakin gado, gaba ɗaya ta rasa mekeyi mata daɗi, tsoro da fargaba ne suka cika zuciyarta, ga kuma yawan faɗuwar gaba da takeji, ƙirjinta ne ke wani irin duka, gaba ɗaya atsorace take, koda tayi ƙoƙarin bawa kanta ƙarfin guiwa kuwa hakan baya yiwuwa, saboda fargaban daya cika zuciyarta. "Me zata tarar agidan Baba Malam? wata ƙila ma yaƙi yafe mata ya kuma sake koranta." Wannan abun shine abun daya tsaya mata arai, duk yanda taso jin sauƙi azuciyarta abun yaci tura, hakanne yasa kawai ta fashe da kuka, dai-dai lokacin Ummi ta turo ƙofar ɗakin ta shigo, ganin Zaleehan na kuka yasa ta ɗan dafe kanta, sam batason yawan kukan na Zaleeha, jin an shigo ɗakin ne yasata ɗago kanta, ganin Ummi yasa cikin hanzari ta tashi tare da ƙarasa gareta, cikin muryarta dake rawa tace. "Wallahi Ummi tsoro nakeji , idan mukaje Baba Malam ya koreni sannan yaƙi yafemin ya zanyi? shikenan nikam rayuwata tana cikin garari." taƙare maganar hawaye na silalowa daga cikin idanunta, Ɗan bubbuga bayanta Ummi tayi, cikin son kwantar mata da hankali tace. "Kada ki faɗi haka Zaleeha, share hawayenki, insha Allah Baba Malam zai yafe miki, nasan nanda ƴan wasu awanni zaki kasance cikin farincikin yafiyar Baba Malam, yanzu taho muje Hammanku nacan mota yana jiranki." Idanunta ta ɗan lumshe, ahankali taɗan gƴaɗa kanta kamar wata ƙaramar yarinya, haka hawaye ke tsiyaya daga cikin cikin idanunta, hannunta Ummi ta kama suka fice daga cikin ɗakin, anan falo suka samu Raleeya tsaye. Ummi na riƙe da hannunta, yayinda Raleeya ka biye dasu abaya, haka suka fito zuwa compound ɗin gidan, har jikin motar tasa suka ƙarasa, still hawaye Zaleeha take, Ummi kuwa na riƙe da hannunta, murfin motar Ummi ta buɗe tare da sanya Zaleehan aciki, ganin ankawo masa ita kusa dashi ne, ya sashi ɗago kansa ya dubi Ummi, amatuƙar shagwaɓe ya ɓata fuska, cikin body language ɗinsa yace wa Ummi da ke kallonsa, "Ni Ummi me yasa zaki kawomin ita kusa dani, baganan gidan gaba ba, dan Allah Ummi kisata agaba, ni banason ta zauna akusa dani." Daƙuwa Ummi tayi masa, tare da kama haɓanta, sosai take mamakinsa itakam, musamman ma yanzu da ya ari halin da ba nasa ba ya yafa. Sake ƙara shagwaɓe fuska yayi, cikin ransa yake ta ƙunƙuni, wanda ko bakin zuciyarsa bai je ba, dan duk abun da yakeyi pretending ne kawai, sam baisa azuciyar sa ba. Allah ya kiyaye Ummi tayi musu sannan Sule driver yaja motar suka fita daga gidan. Saida su Ummi suka ga, fitansu kafun suke komawa cikin gida. Koda tafiyan nasu tayi nisa, ƙanƙame jikinta waje ɗaya tayi, saboda sanyin AC'n dake tashi acikin motar yaso ya yiwa jikinta yawa, gaba ɗaya bata wani cikin nutsuwarta, domin suna fita daga cikin gidan na Ummi taji gaba ɗaya zuciyarta ya karye, haka hawaye keta fita daga cikin idanunta, yana sauƙa akan fuskarta, daga gefe guda kuwa daddaɗan ƙamshin turarensa ne ya gauraye numfashinta, haka take ta sakin sheshsheƙan kuka ahankali. Saifuddeen kuwa, duk da kasancewar bai ɗago kai ya kalleta ba, amma duk wani abu da takeyi, yana lure da ita, amma azahirance yi yayi kamar baisan da wata halitta agefensa ba, itakuwa gaba ɗaya damuwa ya cika mata zuciya, hakanan taji tana son kallonsa, amma wani irin abu me kama da tsoro ya hanata kallon sa, wanda kuma tunda take dashi bata taɓa jin irin hakan a dangane dashi ba. Cusa kanta atsakankanun cinyoyinta tayi, tana me sake sakin sheshsheƙa, can cikin zuciyarta kuwa sunan Allah. take ta faman ambato. Shikuwa Saifuddeen text message ya turawa Dirankadi kan cewa. "Yana neman al'farma idan yana gida, yanaso yazo ya ɗaukesa, akan maganan Zaleeha, dan suje su bawa Baba Malam haƙuri, saboda yana fushi da'ita sosai, sannan kuma idan yaje shi kaɗai baisan mezai faɗawa Baba Malam ɗin ba, wataƙila ma balallai Baba Malam ɗin ya sauraresu ba." Cikin fahimta kuwa Dirankadi yace masa. "Babu damuwa Sai sunzo ɗin, dama fita zaiyi, amma zaijirayi zuwansu.." Sosai kuwa Saifuddeen yaji daɗi, hakan yasa ya ɗan taɓa Sule driver, Juyowa Sule driver'n yayi yana fuskantar sa, miƙawa Sule driver'n wayarsa wanda yayi rubutu akan screen ɗin Yayi, koda Sule driver ya karanta saƙon jinjina kansa yayi, cikin kulawa yace. "Angama ranka ya daɗe." Nan take kuwa ya karkata akalar motar suka nufi gidansu Ishaq. Koda suka ƙarasa gidan nasu Ishaq kuwa, nan suka samu harma Dirankadi'n ya shirya, su kawai yake jira, koda Saifuddeen ɗin ya buƙaci da Dirankadi'n ya shiga motarsa, cewa yayi dashi. "A'a zaije da tasa motar, saboda daga gidan su Zaleehan zai wuce wajen aiki, saboda haka amotarsa zai tafi." Saifuddeen ne yayiwa Sule driver, alamar cewa ya yiwa Zaleehan magana tazo ta gaida Dirankadi ɗin, haka kuwa akayi Sule driver da kansa ya buɗe mata murfin motar ta fito, har ƙasa kuwa ta durƙusa ta gaishe da Dirankadi'n. Fuska asake ya amsa mata, tare dayi mata ta'aziyyan rasuwar Adda Maryam, haka ta amsa masa cikin yanayin sanyi, dan aɗan kukan nan da tayi, har muryarta ta dashe. Haka dai Dirankadi ya shiga motarsa, itakuma Zaleehan ta koma motar su ta zauna tare dayin jigum, saboda zuciyarta dake ƙara tsinkewa, Nan dai suka kama hanyar gidansu Zaleehan, inda motar Dirankadi ce agaba. Basuyi wani tafiya me nisaba suka iso gidan, jin motar ta tsaya ne yasata ɗago kanta amasifar tsorace, aikuwa ganinta acikin compound ɗin gidansu yasa gaba ɗaya duk wani kuzarinta ya kau, yanayin yanda zuciyarta ke bugawa kuwa, idan kaji zakai tunanin cewa faso ƙirjinta zatayi ta fito waje, sosai jikinta ya ɗauki rawa, tsoro ne yagama lulluɓeta, makomarta kawai take tunawa. Dirankadi ne yafara fitowa daga cikin motarsa, ƙarasowa jikin motar Saifuddeen ɗin yayi, cikin kulawa yace. "Saifuddeen ku zauna kada ku fito, duk yanda ake ciki zan maka text sai ku shigo." Kai Saifuddeen ya jinjina masa alamar gamsuwa, Nan Dirankadi ya nufi cikin gidan, kaitsaye ɓangaren Baba Malam ya nufa. Acikin falon Baba Malam kuwa, shi da Ya Ahmad, da kuma Malam Adam ne zaune, gefe dasu kuwa Ya Ameenu ne wanda ayanzu ya zama kamar wani mutum mutumi, komai nasa ya sanja, ya zama wani mutum me sanyi, magana kuwa inbanda "Eh, da kuma A'a." ba bu abun da yake iya fitawo daga bakinsa, sosai mutuwar Adda Maryam ɗin ya maidashi wani silently, hakanne ma yasa gaba ɗaya dangim suke masifar jin tausayinsa. Dirankadi ne ya shigo cikin falon bakinsa ɗauke da sallama, amutunce su Baba Malam da kuma Malam Adam suka amsa masa, cikin mutum tawa Baba Malam ya taso ya tarosa, tare da basa hannu sukayi musabaha, kujera Baba Malam ya nuna masa, zama yayi tare da bawa su Yaya Ameenu hannu suka gaisa, sake musu sabon gaisuwa yayi, tare da sake bawa Baba Malam hannu suka gaisa amutunce, hira kaɗan sukayi, kafun Dirankadi ya gyara zamansa, cikin nutsuwa ya dubi Baba Malam, a mutumce yace. "Kayi haƙuri Malam Bashir, domin ba haka kawai nake tafe ba, alfarma muka zo nema awajenka, wanda kuma nake saka ran cewa Insha Allah, zaka mana ita." Ɗan jim Baba Malam yayi tare da sauƙe ajiyar zuciya, tabbas Dirankadi nada kima da kuma mutumci a idanunsa, saboda haka zai iya yimasa alfarma kuwa kowacce iri ce, saidai kuma ayanzu baisan yaya girman alfarmar take ba, cikin halin dattako da nutsuwa irin nasa yace. "Ai Dirankadi kafi ƙarfin al'farma awajena, saidai kuma bazanyi hanzari ba, ina jinka wace al'farma ce wannan, dahar yasa ka taso da kanka kazo, ai da ko awaya kaƙira ka sanar dani zan iya yi maka ita." Kai Dirankadi ya jinjina cikin jin daɗi yace, "Nagode ƙwarai da wannan karramawar Malam Basheer, yanzu kuwa zanyiwa abokan tafiyana magana dan su samu shigowa." Nan ya ciro wayarsa ya turawa Saifuddeen text akan cewa. "Su shigo." Koda Saifuddeen ya karanta text ɗin na Dirankadi, buɗe murfin motar yayi ya fita, dan dama tuni Sule ya fito masa da wheelchair ɗinsa, ganin haka yasa Sule zagayawa ɓangaren da Zaleehan take ya buɗe mata murfin motar, asanyaye kuwa ta fito daga cikin motar, gaba ɗaya jikinta rawa yake saboda fargaba da kuma tsoro. Haka suka nufi ɓangaren Baba Malam ɗin, Saifuddeen na gaba, ita kuma tana biye dashi abaya, da ƙyar take iya taka ƙafafunta da suka mata nauyi, ga kuma wani masifaffen tsoro haɗi da faɗuwar gaba da takeji. Dai-dai sun kawo ƙofar shiga falon ne, tayi saurin kamo hannun sa, ɗan tsayawa yayi tare da juyowa ya kalleta, wasu irin hawaye masu zafi ne suka silalo daga cikin idanunta, sosai jikinta ke rawa, harta laɓɓan bakinta ma rawa suke, idanunsa ya ɗan lumshe jin yadda ta rumtse tafin hannunshi cikin nata tana mammatse mishi hannun da jan yatsunshi cikin yanayin tsoro, ajiyan zuciya ya sauƙe tare da girgiza mata kansa, hannunta yaɗan murza sannan suka nufi cikin falon Baba Malam ɗin. Jin an taɓa ƙofar falon yasa dukansu suka zubawa ƙofar idanu, dan ganin me shigowa, Ganin Saifuddeen Yasa Baba Malam ɗan sakin murmushi, take kuma saiga Zaleeha ta biyo baya, dan dama har yanzu Saifuddeen ɗin na riƙe da hannunta, da sauri Baba Malam ya ɗauke kansa daga kallonta, take yanayin annurin fuskarsa ya sauya, jiyayi kwata kwata ma bayason ganinta hakan yasa ya kawar da kansa gefe. Saifuddeen na riƙe da hannunta suka ƙaraso cikin falon, har gaban Baba Malam ɗin ya ƙaraso, ita kuwa Zaleeha kanta na ƙasa, hawayene kawai keta tsiyaya daga cikin idanunta, sake hannunta Saifuddeen yayi tare da sauƙa akan wheelchair din nasa, ya yasa guiwowinsa aƙasa, itama Zaleehan zubewa tayi aƙasa, wanda hakan yasa kusan rabin jikinta ya shiga jikin Saifuddeen, gaba ɗaya idanunta sun rufe, ƙwalla ne kawai acikinsu, hawaye wani na koran wani kaman an kunna sabon famfo. Kifa kanta tayi akan ƙafafun Baba Malam dake zaune, lokaci guda ta saki wani irin kuka mai taɓa zuciya, cikin kukan tace. "Dan Allah Baba Malam kayi haƙuri ka yafemin, kar in mutu da fushinka na tuba ka yafemin ko zan samu kekyawan rayuwa, Idan baka yafemin ba nima mutuwa zanyi, wallahi nayi nadamar abun da na aikata, na tuba Ka jiƙaina ka yafemin!!." Taƙare maganar tana Kuka sosai kamar ranta zai fita. Cikin fushi Baba Malam ya janye ƙafansa baya, hakanne yasa ta ɗago da kanta, tana kuka sosai haɗe hannuwanta waje ɗaya tayi alaman roƙo, cikin matsanancin kukan ta ɗaga idanu ta kalli Malam Adam, da kuma Ya Ahmad gani tayi sun kauda kansu daga kallonta, alaman har yanzu suna fushi da ita, duƙar da kanta tayi tana wani irin kuka mai taɓa zuciya, hakanne yasa Saifuddeen ɗaura hannunsa akan nata ya riƙe ƙam, jin haka yasa ta sake mannewa a jikinsa, tare da kama hannunsa tana jijjigawa kuka take sosai, wanda hakan yasa yakejin wani abu na taɓa zuciyarsa, kowani ɗigan hawayenta ɗaya tamkar ɗigan narkakken dalma ne, akan zuciyarsa haka yakeji. Dirankadi ne ya gyara zama zuciyar sa cike da tausayin Zaleehan, saboda yanda take kuka, wanda dagani kasan daga cikin ƙarƙashin zuciyarta da kuma ranta yake fitowa. Asanyaye yace. "Yafiya ga Zaleeha itace al'farmar da nake nema awajenka Malam Basheer, haƙiƙa Zaleeha ta aikata ba dai-dai ba, wanda alokacin ni kaina saida naji babu daɗi, amma ayanzu tabbas ta gane kuskurenta kuma tayi na dama, shikansa wanda ta gudawa ɗin na tabbatar da cewa ya yafe mata, tunda gashi shida kansa ya ɗaukota dan su zo su baka haƙuri, dan Allah Malam Basheer ku yafe mata, kada ku manta fa cewa ita macece me raunin zuciya, rashin yafe mata zai iya haifar da wata sabuwar matsalan, abun zaiyi mata yawa, har yanzu Zaleeha yarinyace ƙara ma, damuwa kaɗan zai iya haifar mata da matsala, da wanne ɗaya zataji? da rashin ƴar uwarta ko kuwa da fushin da kukeyi da ita, ayanzu Al'barkarku take nema, bawai ɓacin rai da fushi ba, nidai ina roƙa mata al'farma dan Allah ayafe mata." Kai Baba Malam ya girgiza, tare da miƙewa tsaye, sam bayajin zai yafewa Zaleeha'n, saboda har yanzu akwai ƙunci da baƙin cikin da ta shayar dashi kwance acikin zuciyarsa, kuma ma baisan niyartaba dole yayi wani abu dan gano meke cikin ranta. Juyawa yayi da niyar barin falon, cikin bazata yaji an riƙe hannunsa, ɗan juyowa yayi afusace dan yasan cewa Zaleehan ce kawai zatayi mishi haka, amma ga mamakinsa sai yaga Saifuddeen ne, wanda idanunsa gaba ɗaya sun ciko da ƙwalla, sannan sunyi jajir, sakin hannu Baba Malam ɗin yayi, tare da haɗe hannuwansa waje ɗaya alaman roƙo, kansa ya rinƙa jujjuya wa yayinda wayenshi ke gab da zubowa. Zaleeha kuwa sake shigewa jikin Saifuddeen ɗin tayi, tare da ɗaura kanta akan kafaɗansa, tana wani irin kuka me matuƙar tsuma zuciya, kukanta kuwa shikesa Saifuddeen yaji kansa kamar zai fashe, haka kuma har cikin ransa yakejin kukan nata, ci gaba yayi da jijjigawa Baba Malam kai, alaman yayi haƙuri yayi musu afuwa. Jikin Baba Malam ne yayi matuƙar sanyi, ganin hawaye acikin idanun Saifuddeen yasa yaji gaba ɗaya tunaninsa ya tsaya, idanunsa yaɗan lumshe tare da komawa ya zauna akan kujera inda ya yi ƙasa da kansa tare dayin shiru. Ya Ahmad kuwa duk yanda yaso shanye kukansa abun yaci tura, dole haka ya saki kuka kaman ƙaramin yaro, dama shi tun farko zuciyarsa me raunice akan Zaleeha, tausayinta ne ke maye ko ina najikinsa, ga kuma jimamin rasuwar Adda Maryam wanda yakejin ta dawo masa sabuwa, kansa ya kifa da jikin kujera yana kuka. Ya Ameenu dake zaune acan gefe kaman mutum mutumi kuwa idanunsa kawai ya zuba musu, shikam aduniya yanajin cewa tunda matarsa ta rasu ta barsa, shikenan duk wani jin daɗi da farinciki sun ƙare masa. Ɗago kai Baba Malam yayi da idanunsa wanda sukai jajur, cikin sanyin murya yace. "Tabbas kin shayar dani baƙinciki marar misaltuwa, kinyimin abun da duk acikin ƴaƴana babu wanda ya ta ɓamin, kin ƙi zaɓina sannan kika gudu kikabar gidan mijinki ɗanki aurenki ba tare da izinin mijinki ba." farin handkerchief ɗin dake hannunsa yasa, inda ya share ƙwallan dake ƙoƙarin fitowa daga cikin idanunsa. Ajiyar zuciya ya sauƙe, sannan yace. "Bani zaki bawa haƙuriba, shi kika saɓa kika wulaƙanta aureshi, shine al'jannarki take ƙarƙashin diga-diginsa dan haka shi zaki bawa haƙuri ba niba yafiyarsa zaki nema da kika fita bada izininshi ba, sai ya yafe miki kafin ni in yafe miki". Da sauri ta juyo ta fuskanci Saifuddeen murya na rawa kana murya a disashe tace. "Kayi hakuri Hamma Saif ka yafe min in sha ALLAH har iya raina da mutuwata bazan sake fita ba saida izininka ko bakin gate bazan sake zuwaba saida izininka". Haɗe hannayenta tayi alamu roƙo kana hawaye na kwaranya a fuskarsa, kanshi ya rinƙa jujjuya mata yana mai jin zazzafan tausayi ya, murya na rawa ta kuma cewa. "Dan Allah Hamma Saif ka yafe min". Kanshi ya kuma jujjuya tare da mata alamun ya yafe mata duniya da ƙiyama, sai kuma ta juyo da sauri ta kalli Baba Malam murya a harde tace. "Baba Malam ka yafe min shi yace ya yafe min". Gyara zama Baba Malam yayi kana yace. "To in na yafe miki me kuma shirinki na gaba zaki sake, gudawa ne? Ko dai kinyi tuba na gaskiya ne zaki zauna ɗakinki, ko bazaki zauna ba?." A hankali ta sunkuyar da kanta zazzafan hawaye na zuba murya na rawa tace. "Har Abadan bazan sake guduba, zan zauna iya raina da mutuwata har sai dai in na mutune zan bar gidanshi babu inda zanje duk rintsi koda ko ba daɗi zan zauna Baba malam zanyi biyayya kwatankwacin wanda Adda Maryam tayi maka, koda daɗi ko ba daɗi zan zauna." Gaba ɗaya jikinsu yayi sanyi hatta shi kanshi Baba malam tausayi ta ya rufeshi, cikin sanyi yace. "Kin san yayi aure bayan guduwanki?". Cikin kuka tace. "Ban saniba saida naje gidanshi naga matar da ɗanshi." Kai ya jinjina tare da cewa. "To ki koma gidanki ɗakinki, ban kuma yarje miki fitina da abokiyar zama kina ki zauna lafiya da ita da ƙanneshi da yayunshi, kada inji wani abu tsakanin ki da abokiyar zamanki, kada ki tsokaneta ko kaɗan in kuma itace ta tsokaneta ki mata uzuri ki yafe mata kada kice zaki rama duk abinda tayi miki". Cikin wani masifeffen kuka tace. "To Baba Malam in sha Allah zaka sameni mai bin umarni ka". Kanshi ya gyaɗa cikin tausayinta a ranshi sabida kukanta na ƙunshi da abubuwa da dama, cikin sanyi yace. "Koda ki tauye haƙƙin mijinki a kanki Zaleeha kada ki haneshi abinda duk Allah ya halattamishi a kanki". Cikin rawan murya tace. "To in sha Allah zan zauna dashi sai kuma in shine yace baya sona." Wani irin tausayinta ne ya rufesu baki ɗaya cikin taushin lafazi Baba Malam yace. "Tabbas kinci al'barkacin Dirankadi da kuma Saifudddeen, saboda haka kije na yafemiki duniya da ƙiyama, ina roƙon Allah Ubangiji kuma ya shiryeki, Ya sa miki imani azuciyarki ya baki zaman lfy da mijinki da abokiyar zamanki, haƙiƙa kin ƙuntatawa zuciyata, kin shayar da ahalinki baƙin ciki, Maryam harta koma ga ubangijinta bata taɓa saɓawa maganata ba koda kuwa sau ɗaya ne, na aurar da ita ga zaɓina, kuma ta amince duk da cewa bataso amma tayi Mini biyayya, haka kuma bata taɓa saɓawa mijinta ba, gashi Allah ya ɗauketa adai-dai lokacin da kowa yake da buƙatanta, Ya Allah kajiƙan Maryam kasa al'janna tazamo makoma agareta...". Kukane ya ƙwacewa Baba Malam ɗin, wanda hakan kuwa yayi matuƙar taɓa zuciyoyinsu, hakanne kuma yasa hawayen dake cikin idanun Saifuddeen samun daman gangarowa, zuwa kan ƙuncinsa, Zaleeha kuwa kuka take sosai kaman ranta zai fita, haka ma Ya Ahmad, wannan karon harta Malam Adam da Dirankadi saida sukayi hawayen, tausayin ahalin. Ya Ameenu kam, bai iyayin kuka ba, saboda ayanzu kukan zuci yake, wanda yafi na fili ciwo, adai-dai wannan lokacin kuwa shi kaɗai yasan me yakeji. Cikin matsanancin kukan, ta rarrafa inda ta ƙarasa gaban Ya Ahmad wanda ke kuka sosai, tana zuwa ta kifa kanta akan cinyansa, tana kuka sosai har kaman zata shiɗe, hannu Ya Ahmad ɗin yasa ya dafa kanta, lokaci guda kuwa ƙarfin kukansa ya ƙaru, gaba ɗaya falon haka ya ɗauki shiru babu abun dake tashi sai sautin kuka anrasa me rarrashin wani, hatta Malam Adam da Dirankadi gaba ɗaya jikinsu amace yake, gaba ɗaya zuciyoyinsu sunyi rauni. Da ƙyar Baba Malam ya iya share hawayensa, cikin muryarsa da ta ɗan dashe yace. "Nayafe miki Allah ya yafe mana baki ɗaya, ki tashi ki koma ɗakin mijinki, Sannan in mijinki ya amince miki duk sanda kuka samu lokaci kuje gidan Maryam ta barmin wasiyar tayi miki ajiya cikin durowar ta ta jikin gado." Hannu yasa ya share hawayenshi kana yaci gaba da cewa. "Kuma matuƙar kika sake mugun saɓawa Saifuddeen ba irin wanda dole akwaishi tsakanin ma'aurataba wallahi! bazan taɓa yafe miki ba Zaleeha, kuma daga wannan lokacin kiceri kanki daga mazaunin ƴata!!!." Jin furucin Baba Malam ɗinne yasanya cikin kuka ta ɗago daga jikin Ya Ahmad, dawowa gaban Baba Malam ɗin tayi tare da durƙusa guiwowinta a ƙasa, kanta ta ɗaura ajikin Baba Malam ɗin tana wani irin kuka me ɗaga hankali, gaɓa ɗaya jikinta rawa yake, ga kuma wani sheshsheƙa da take saki wanda yasa numfashinta keyi kaman zai ɗauke. Cikin kukan da kuma muryarta wanda bata fita sosai tace. "Nagode Baba Malam! Nagode sosai da ka yafemin, kuma insha Allah zaka sameni me biyayya agareka dashi Hamma Saif..." Kuka take sosai harda majina, Ahankali Saifuddeen ya haɗe hannuwansa, tare da ɗan lumshe idanunsa, alaman godiya, still kuma hawayene kwance akan fuskarsa. Murmushi Baba Malam yayi tare da sanya hannu ya shafi kan Saifuddeen ɗin, tabbas Saifuddeen mutunne me nagarta, da kuma zuciyar imani, sai yanzu yake ƙara aminta cewa bazai taɓa danasanin bawa Saifuddeen auren ƴarsa ba, haƙiƙa Saifuddeen yacika me kyakkyawar zuciya, tabbas irinsu aduniya basu da yawa. Malam Adam ne ya rarrashi Ya Ahmad wanda yake ta kuka, Dirankadi ne yayiwa Baba Malam ɗin godiya, ganin irin kukan da take, yasa Baba Malam yiwa Saifuddeen alama cewa ya ɗauki Zaleehan suje. Wheelchair ɗinsa ya hau, sannan ya sanya hannu ya ɗago ta, kuka take sosai, haka ya riƙe hannunta suka fice daga cikin falon. Anan cikin ɗan corridor ɗin ƙofar falon ya tsaya, tare da zaro handkerchief a al'jihunsa idanunsa wanda suka ɗan lumshe ya zuba mata, sannan ya miƙa mata handkerchief ɗin, Cikin wani irin zazzafan kuka ta faɗa jikinshi tare da kife kanta bisa cinyoyinshi ta saki kuka mai cike da rauni, wani irin tausayinta yakeji na ratsashi a hankali ya ɗan magoya kana ya kuma miƙa mata handkerchief din hannunta na rawa haka ta amshi handkerchief ɗin, ahankali take goge hawayen fuskarta tana sakin sheshsheƙa. Littafina na kuɗine in kina buƙata ga no 09097853276 Wannan shafin nakune NAKASA BA KASAWA BACE fans 3&4 inayi muku fatan al'khairi By *GARKUWAR FULANI* [15/09, 7:49 pm] +234 803 765 0266: Sbpejny Cikin sheshsheƙan kuka, da kuma muryarta dake dashe tace. "Ayyah Hamma Saif kayi haƙuri ka kaini na bawa su Mamy dasu Aunty Lubna haƙuri, dan suma fushi sukeyi dani." Kyawawan idanunsa ya ɗan lumshe, tare da jinjina mata kai, alaman "To." Hannunta dake cikin nasa ya ɗan murza, sannan suka nufi ɓangaren Mamyn. Har zuwa yanzu kuwa bata daina sakin sheshsheƙan kuka ba, hasali ma amaimakon kukan nata ya tsaya, ƙaruwa yayi, saboda wani irin yanayi da takejin kanta aciki. Anan bakin kofar shiga sashin Mamyn ya tsaya, saboda aganinsa bai kamata ya shiga musu kai tsaye ba tare da an masa iso ba. Ganin ya tsaya ne, yasa ta juyowa ta kalleshi, gani tayi ya zuba mata kyawawan idanunsa, wanda da zaran ta kalli cikinsu, to sai taji wani iri ajikinta. Ɗan lumshe idanun nasa yayi tare kuma da buɗe su alokaci guda, wani irin abu ne taji yabi jikinta, hakan yasa ta zare hannunta daga cikin nasa. Ahankali ta murɗa handle ɗin ƙofar falon, ta shiga bakinta ɗauke da sallama, wanda muryarta ko fita da kyau bayayi tsabar kukan da tayi. Mamy, Aunty Lubna, da kuma Goggo Maryama, da Ziyada, sai kuma su Zainab da Ubaida ne zaune a cikin falon, jin sallaman Zaleehan ne yasa su duka ɗago kai suka kalleta, ahankali take takawa har ta ƙaraso cikin falon, da ɗan sassarfa taje ta faɗa jikin Mamy, tare da sakin sabon kuka me sauti, rungume Zaleehan Mamy tayi, tana mejin matsanancin tausayinta aranta, jin Mamyn ta rungumeta ne, yasa ta ƙara volume ɗin kukan nata, haka falon ya ɗauki shiru ba abun dake tashi cikinsa sai sautin kukan Zaleeha, hakanne yasa hawayen dake cikin idanun Mamy suka samu daman gangarowa. Cikin sheshsheƙan kukan ta ɗago daga jikin Mamyn, muryarta na rawa tace. "Mamy dan Allah ki yafemin, kinga Baba Malam ma ya yafemin, kuma yace na koma ɗakin mijina na zauna, fushin Baba Malam ya tsoratani sosai Mamy, wallahi bazan sake gudun ku ba, nasan nayi kuskure me girma dana tafi na barku, bayan kuma aduniya bani da wasu sama daku, dan Allah Mamy kema kiyi haƙuri kinji, Ya Ahmad ɗina ma ya yafemin." ta ƙare maganar tana me kamo hannun Mamyn ta riƙe. Murmushi Mamy tayi tare da share hawayenta, tabbas taji daɗin jin cewa Baba Malam ɗin ya yafewa Zaleeha, dan ko itama adole taƙi kula Zaleehan, bawai dan tana fushi da ita ba, duk da ma tasan cewa abun da Zaleehan tayi bai dace ba, amma fushin da aka yi da ita yayi yawa, ba a fushi me tsanani ga ƴa mace irin haka. Ɗan shafa bayan Zaleehan tayi, cikin kulawa tace. "Kukan Ya isa haka Zaleeha, tabbas naji daɗi ƙwarai da Baba Malam ya yafe miki, nidama tuncan Zaleeha ba fushi nake dake ba, kuma na yafe miki, sannan dan Allah kada ki sake kamanta irin kuskuren da kikayi abaya kinji, sam guduwa ga ƴa mace ba ɗabi'a bace me kyau, ki zauna agidan aurenki kiyi zama me kyau, kada ki saɓawa mijinki, tasanadiyar hakan da zakiyi saikiga kin samu aljanna da yardan Allah." Cikin kuka ta jinjina kanta alaman gamsuwa, da kalaman Mamyn, ahankali taɗan janye jikinta tare da tashi ta ƙarasa gaban Goggo Maryama, durƙusawa tayi tare da, ɗaura kanta akan cinyar Goggo Maryama'n, cikin sheshsheƙan kuka tace. "Dan Allah Goggo Maryama ki yafemin, nasan kema kina fushi dani, dan Allah Kuyi hakuri, yanzu al'barkanku nake nema." Goggo Maryama kuwa Ɗan share hawayen dake cikin idanunta tayi cikin sanyi tace. "Babu komai Zaleeha na yafe miki, Allah ya yafe mana baki ɗaya, fatana dai shine ki nutsu kiyi zaman aurenki, insha Allah saikiga Al'barka nata bibiyan rayuwarki." Kanta ta jinjina, cikin sanyi tace. "Nagode sosai Goggo ." tashi daga jikin Goggon nata tayi, kai tsaye jikin Aunty Lubna ta faɗa, rungumeta tayi ƙam, tana ɗan sakin sheshsheƙa, itama Aunty Lubna'n hawayene cike a idanunta, saida sukayi kuka sosai kafun, Zaleehan ta sake riƙe Aunty Lubna'n, cikin dashashshiyar muryarta tace. "Aunty dan Allah ki yafemin, kidaina fushi dani, kinga Ya Ahmad ma ya yafemin." wani irin tausayin Zaleehan ne ya cika zuciyar Aunty Lubna, cikin kulawa tace. "Ni dama ban ƙullaceki da komai ba Zaleeha, wallahi na yafe miki har acikin zuciyata." Ziyada dake zaune agefe ne ta taso tare da ƙarasowa ta rungume Yayarta ta, nan tasaki kukan tausayinsu, juyowa Zaleeha tayi ta rungume Ziyada'n, wanda ayanzu take ganinta kamar Adda Maryam, dan sanyin zuciyar Ziyada dana Adda Maryam ɗin iri ɗaya ne. Acan ƙofar shigowa falon kuwa Saifuddeen ne zaune ya sunkuyar da kansa ƙasa, Zakariyya wanda shigowansa gidan kenan, hango Hamma Saifuddeen zaune akan wheelchair ɗinsa yasa shi ƙarasowa cikin sauri, fuskarsa ɗauke da ɗan murmushi ya taɓa kafaɗan Saifuddeen ɗin, tare da cewa. "La Hamma Saifuddeen kaine." murmushi Saifuddeen yayi tare da miƙawa Zakariyya'n hannu suka gaisa, fuskar Zakariyyan ce taɗan fidda rauni, asanyaye yace. "Hamma da Adda Zaleeha kuka zo?". ahankali ya jinjina masa kai alaman "Eh" wani irin daɗi Zakariyyan yaji acikin ransa shikenan yasan Baba Malam ya yafewa Zaleeha, cikin zumuɗi ya kama saman wheelchair ɗin Saifuddeen ɗin, tare da cewa. "Hamma mu shiga ciki to." Haka suka shigo cikin falon na Mamy, bakin Zakariyya ɗauke da sallama. Har tsakiyan falon Zakariyya ya ƙaraso da Saifuddeen ɗin, nan cikin body language ɗinsa ya gaishe da Mamy, da kuma Goggo Maryama, fuska asake haka suka amsa masa, gaishe da Aunty Lubna yayi itama ta amsa tanayi masa murmushi, dan Allah ma yasani itakam Saifuddeen ɗin na burgeta, mutum ne shi me mutunci da kamun kai, komai nasa daban, babu ruwansa da cewar shi nakasashshe ne, abunda ta fahimta ma shine shi nakasar tasa ado ta zame masa, dan idan yana kan wheelchair ɗinsa zaka ɗauka cewa wani sarkine mai cikakken iko,, sosai abun keyi masa kyau. Zainab da Ubaida ne suka gaidashi, cikin body language ɗinsa ya amsa yana ɗan murmushi, sukam daganinsa mamakine yakusan kashesu, sunsan dai Zaleehan gurgu kuma kurma ta aura, amma ko kusa basusan haɗuwa da kyawunsa har yakai haka ba, dan idan ma ba dan sunsan cewar shi gurgu bane, to zasuce ya hau keken ne kawai dan ƙarawa kwalliyarsa armashi, Ubaida ne ta jinjina kanta, acikin zuciyarta tace. "Lallai Zaleeha bata da hankali, wace macece zata samu wannan santalelen namijin sannan ta gudu ta barsa? hmmm ai irinsu Saifuddeen koda na kasarsu mata wawansu suke, saboda koba komai akwai kyau da cikar haiba." Ziyada ne ta taso daga jikin Zaleehan tare da taƙarasowa gabansa, ɗan durƙusawa tayi, cikin sanyinta tace. "Hamma Saifuddeen ina wuni." Murmushi yayi wanda yaɗan bayyana fararen haƙwaransa, hannu yasa ya ɗan shafa kanta, cikin kulawa ya jinjina mata kai alaman "Lafiya" Zakariyya kuwa ƙarasawa wajen Zaleeha wanda kanta ke jikin Aunty Lubna tana ta faman sakin sheshsheƙan kuka yayi, cikin sanyi yace. "Adda Zaleeha." ɗago kanta tayi ta kalleshi, sai kawai ta faɗa cikin jikinsa, tana sakin sabon kuka, shikansa Zakariyyan saida yayi ƙwalla, da ƙyar ya saitata ta iya tsaida kukan nata, hannunta ya kamo sannan ya haɗa dana Saifuddeen cikin kulawa yace. "Muje na rakaku part ɗin Mama." Hakan kuwa akayi har part ɗin Maman ya kaisu, anan falo suka iske, Mama, Aunty Ruda, da kuma Aunty Aisha, da Maman Mama da dai sauran ƴan uwanta arnataku, gaba ɗaya sunyi jigum dasu. Jin motsin shigowarsu, da kuma ƴar siririyar sallaman Zaleehan ne ya sasu ɗago Idanu suna kallonsu, Zaleeha na tafiya asanyaye, yayinda Zakariyya kuwa ke tura saman keken Saifuddeen ɗin, ahaka suka ƙaraso cikin falon, anan gaban Mama Zaleeha ta durƙushe tare da ɗan ɗaura kanta akan cinyar Maman, haƙiƙa uwa uwace komin munin halinta kuwa tana nan a mazaunin ta na uwa, sannan kuma ba'a taɓa sanjata, idanu Zaleeha ta lumshe, hakanan taji wani sabon kuka nason zuwar mata. Su Mama kuwa gaba ɗaya tun shigowarsu idanunsu akan Saifuddeen suke, musamman ma Aunty Ruda da Mama dan tunda suke basu taɓa ganinsa ba sai yau ɗin, ganin hakanne yasa Saifuddeen sakin ɗan murmushi tare gaidasu cikin body language ɗinsa da Aunty Ruda'n, da kuma Aunty Aisha, fuska asake kuwa Aunty Aisha ta amsa masa, Aunty Ruda kam idanu ta zuba masa, tana mamakin tsantsar kamala kwarjinin da kyaun sa. Juyowa yayi ya ɗan kalli Mama, cikin yanayin girmamawa ya gaisheta, idanu taɗan zuba masa, asanyaye da muryarta wanda ta dashe saboda tsabar kukan da tayi na rasuwar Adda Maryam ɗin ta amsa masa, lokaci guda kuma tayi ƙasa da kanta, saboda hakanan taga yayi mata kwarjini, acikin idanunta kunya mai ƙarfi da dana sani suka rufeta, dan kwata-kwata bata ɗauka haka yake ba, ta ɗauka irin musakan nan ne masu matacciyar zuciya wanda sun kele sun yaɗe sun shanye irin waɗanda ba zasu iya smfanan kansu Bama bare wani. Ɗago kai Zaleeha tayi ta kalli Maman, ɗan lumshe idanunta dake zubar da ƙwalla tayi, asanyaye tace. "Mama." Dubanta Maman tayi, tare da ƙura mata idanu. Ɗan jan sheshsheƙa tayi, cikin muryarta da bata fita sosai tace. "Na aikata laifi mafi girma, wanda yasa saboda haka Babana da kuma duka ƴan uwana suke fushi dani, sanadiyar haka har Adda Maryam ta rasu, bamu sake ganawa ba, nabar kowa da komai saboda idanuna sun rufe da son wanda ni kaina yanzu na yarda bazan sake ganinshiba, sai-dai kuma nasan awannan lokacin da ban samu goyon bayanki ba Mama, tabbas da bazan tafi nabar kowa ba, nayi kuskure me girma arayuwata, wanda kuma bana fatan sake maimaita irinsa agaba ɗaya rayuwata, fushin Baba Malam da Hamma Saif fushin Allah ne, bakuma zanso su sake fushi dani ba, ayanzu al'barka kawai nake nema, saboda na ɗauki al'ƙawarin zan zauna agidan aurena da daɗi ko ba daɗi, saboda haka ina buƙatar kyakkyawan fata daga gareki, domin har gaban abada ke uwace agareni, wanda kuma bazan taɓa sanjaki ba." taƙare maganar tana me kama hannun Mama, tuni hawaye kuwa wani nakoran wani akan fuskarta. Idanun Maman ne suka ciko da hawaye, tabbas tayi nadaman abun da ta aikata na bin zugar kafurar yauarta, tunda ga lokacin da labarin rasuwar Adda Maryam ya riski kunnuwanta, tayi nadama ƙwarai sannan jikinta yayi sanyi sosai, duban Zaleehan tayi sosai, ganin yanda Zaleehan ta rame, ta zama wata abun tausayi, lokaci guda ta fita hayyacinta, yasa taji kuka nason zuwar mata, cikin sauri ta miƙe tsaye ta nufi ɗakinta, dan tsayawarta zai iya baiyanar da raunin zuciyarta tana gab da shiga ne tace. "ALLAH ya baku zaman lfy Zaleeha." Ganin haka yasa Zaleeha kwantar da kanta ajikin kujeran da Maman tatashi, ta saki wani marayan kuka, Aunty Aisha ne ta share hawayen da suka cika idanunta, asanyaye tace. Ta kalli Zaleeha cikin sanyi tace. "Jiya Solomon da matarsa sunzo sunyi gaisuwa, sunce suna son ganinki akwai abu mai mahimmancin da sukeso sanar dake, to lokacin bamu san inda kikeba sun kira layinki kuma baya shiga, amman sunce zasu zo nan bada daɗewa ba." Wani irin sanyine ya ziyarci Zaleeha Allah yasa musulta zasuyi, Allah yasa musultan sune yayi sanadin zuwanta garin Numan". cikin nitsuwa Aunty Shatu tace. "Saifuddeen kamata kuje, Allah Ubangiji yayiwa rayuwar aurenku al'barka, ya baku zuri'a me al'barka." Kansa yaɗan jinjina, sannan ahankali ya murza wheelchair ɗinsa ya ƙaraso har gaban Zaleehan, hannunsa yasanya yaɗan ɗago kafaɗunta, tare da miƙar da ita tsaye, hannunta ya kama, cikin nutsuwa ya jata suka nufi hanyar barin falon, Aunty Ruda kuwa baki ta sake tana kallonsu, har suka fice daga cikin falon. Haka suka fito compound ɗin gidan yana riƙe da hannunta, yayinda Zakariyya kuwa ke biye dasu abaya sai kallonsu yake, sai ayau yasake ganin dacewar Hamma Saifuddeen ɗin da Zaleeha, kallo ɗaya zakayi musu kaga kaman dansu biyun akayi kowannensu. Sule driver na hangosu cikin hanzari ya buɗe musu murfin motar, zuwa lokacin kuwa tuni har ma Dirankadi yabar gidan, dan dama akwai inda zaije, sakin hannunta yayi, tare da juyowa ya sake bawa Zakariyya hannu sukayi musabaha, cikin ɗan jin daɗi Zakariyya yace. "Asauƙa lafiya Hamma, Allah Ya saka da al'khairi." Kai kawai ya jinjina masa, sannan ya shige cikin motar bayan itama ta shiga. Cikin nutsuwa Sule driver ya ja motar suka bar cikin gidan, Zakariyya kuwa saida yaga fitarsu kafun yake komawa cikin gida. Tunda suka baro gidan take sakin sheshsheƙan kuka, haka ta ɓoye kanta acikin cinyoyinta tana sakin wani numfashi me zafi, duk abun da takeyi yana lure da ita, amma sai ya kawar da kansa gefe yayi kamar bai ganta ba, saida tafiyar tasu ta ɗanyi nisa, kafun ta ɗago kanta, ahankali ta sauƙe idanunta akansa, wasu hawaye masu zafine suka sauƙo daga cikin idanunta, ji tayi gaba ɗaya zuciyarta tayi rauni sosai, wani irin ƙima da kuma girmansa ne suka cika idanunta, tabbas ayau ya taimaketa, yayi mata abun da mutane da yawa suka kasa yi mata shi, yau ya zame mata inuwa kuma majingina, ya kareta daga rana, sannan yayi ƙoƙarin haskaka rayuwarta, ya ɗaukota daga duhu ya kawota cikin haske, dame zata saka masa? wani irin kuka ne ya zo mata, hakan yasa ta faɗa jikinsa tare da rungumesa ƙam-ƙam tamkar zata haɗesu wuri ɗaya. asakamakon hakan kuwa wani irin shock yaji ajikinsa, karon farko kenan da ta fara shiga cikin jikinsa dan kanta, hannayenta ta sanya ta zagayeshi, tare da ɗaura kanta akan faffaɗan ƙirjinsa, ta saki wani irin kuka mai taɓa zuciya, cikin kukan nata ne ta cusa fuskarta acikin ƙirjinsa, wanda hakan yasa aninayen dake gaban rigarsa ɗan ɓallewa, take kuwa fatan ƙirjinsa ta bayya, hakanne kuma yasa ahankali hancinta da laɓɓan bakinta ke gogan skin chest ɗinshi, wani irin kuka takeyi me taɓa zuciya, still kukan take tana ɗan jujjuya kanta acikin ƙirjinsa, hakan da takeyi ne yasa gaɓa ɗaya jikinsa yayi weak, wani irin abu ne yakeji na yawo ajikinsa, wanda zai iya rantsewa, cewa tunda yake aduniya bai taɓa jin irin hakan ba, wani fitinannen feeling yakeji, gefe guda kuma ga wani pleasure wanda ko sex suke da Ameena bai taɓa jin irin wannan pleasure da kuma feeling ɗin ba, babu abun dake neman zautar da tunaninsa kaman yanda tausassun laɓɓan bakinta ke gogan fatar ƙirjinsa, A hankali ta ɗago kanta ta zuba mishi,ido shima idon ya zuma mata, goshinta na manne da haɓarss cikin Muryar me sarƙewa haɗi da sheshsheƙan kuka tace. "Nagode! Nagode!! Nagode!!! sosai Hamma Saif, tabbas ka taimakeni arayuwa, sanadinka gashi Baba Malam ya yafemin, nagode maka ƙwarai matuƙa, Allah Ubangiji ya biya maka buƙatunka na duniya da lahira, Allah yafaranta maka kamar yanda ka faranta min, Allahu rabbi ya gafarta maka zunubanka, kamar yadda kayi sanadin yafe min da Baba Malam yayi, tabbas kamin abun da kowa ya kasa min, nagode sosai Hamma S..a..i..f." Kukane ya ci ƙarfinta, sai kawai ta sake rungumesa sosai. Ahankali yaɗan lumshe kyawawan idanunsa wanda suka soma runewa zuwa kalan ja, hannunsa yasa ya tallafo haɓarta, tare da ɗan ɗago fuskarta, hakan shi ya bawa fuskokinsu daman kusanci da juna, idanunsa wanda suke ɗan lumshewa kaɗan kaɗan ya zuba mata, ahankali ya matso da fuskarsa gareta har hancinsu na gogan na juna, goshinsa ya ɗaura kan nata hancishi na bisa tsinin hancinta haɗuwar numfashinsu waje ɗaya, shiya sanya suka lumshe idanunsu atare, ahankali laɓɓanta suka ɗan buɗe, saboda sheshsheƙan kukan da takeyi. ɗan buɗe idanunsa yayi, kana ya ƙurawa kyawawan laɓɓanta, shanyayyun idanunsa, wani irin abune ke yawo acikin jikinsa, haka yakejin kamar ya kamo kyawawan laɓɓanta yayi kissing ɗinta, Idonshi ya maida ya lumshe tare da ɗan zaro harshenshi ya ɗan lashi tattausan lips ɗinta, da sauri ta buɗe ida nunta, ganin haka sai kuma ys janye fuskarsa baya yana sakin wata irin ajiyar zuciya yayi kamar bashi ya lashi laɓaɓɓan nataba, ahankali itama ta ɗan janye jikinta baya, nan kan kafaɗansa ta ɗaura kanta, ahankali take sakin ajiyar zuciya, har yanzu kuwa idanunta basu daina zubar da ƙwalla ba, saidai acikin zuciyarta farinciki ne me tarin yawa, ji take kaman anyaye mata duk wata damuwarta ta duniya, yafiyar Baba Malam da na Hamma Saif yasanya tanajin kanta, awata sabuwar duniya ta daban. Hannunta ta saƙala acikin nasa, yayinda hawayenta ke ɗiga akan kafaɗansa. Ahankali yaɗan jingina bayansa da jikin kujeran motar, tare da lumshe idanunsa, numfashinta dake sauƙa akan wuyansa, shiya sanya yaji gaba ɗaya jikinsa ya sake, yayinda tsikar jikinsa keta faman mimmiƙewa, dama akan Zaleeha shi namiji ne me yawan feelings, yanzu da take ajikinsa kuwa shikaɗai yasan me yake ji. Zaleeha kuwa daɗin jikinsa da kuma sassanyan ƙamshin turarensa dake shiga hancinta, su suka taimaka wajen bata wani irin nutsuwa na musamman, sake lumshe idanunta tayi, tana me busa masa iskan numfashinta akan fatar wuyansa. Gaba ɗayansu sun shagala, babu wani wanda yake cikin tunaninsa, musamman ma Saifuddeen daya tafi izuwa wata duniya ta daban, tsayuwar motar ne yasasu buɗe idanunsu, gani sukayi har sun iso gida. Akunyace taɗan janye jikinta daga na Saifuddeen ɗin, nan ta ɗan gyara mayafinta dake ƙoƙarin zamewa. Sule driver kuwa cikin hanzari ya zagayo ya buɗe mawa Saifuddeen ƙofar motar, bayan ya buɗe bot ya zaro masa kekensa. Cikin nutsuwa kuwa ya hau kan keken nasa, Zaleeha ma jikinta asanyaye ta fito daga cikin motar, idanu ta zuba masa ganin ya nufi part ɗinsa, kanta ta ɗan sunkuyar ƙasa, sannan ta share ɗan gun hawayen dake maƙale ƙasan idanunta, cikin ɗan sassarfa ta nufi part ɗin Ummi, tun kafun ta ƙarasa shiga falon, take ƙiran sunan Ummi, Raleeya dake zaune acikin falon ne ta ƙurawa ƙofar shigowa ido, musamman yanda taji Zaleeha nata faman ƙiran sunan Ummi. Murɗa handle ɗin ƙofar falon tayi ta shiga, fuskarta ɗauke da murmushi da kuma hawaye, ganin Raleeya yasa ta tafi da gudu ta faɗa jikinta, ganin murmushi da dariya akan fuskan Zaleehan yasa, Raleeya itama ta saki murmushi, ɗago kai Zaleehan tayi, tace. "Raleeya Baba Malam ya yafemin, haka Ya Ahmad dasu Mamy ma duk kowa ya yafemin, Raleeya Hamma Saifuddeen ya zama garkuwa agareni, ayau ya bani duk wani farinciki, sanadiyarsa Baba Malam ya yafemin, yanzu Baba Malam baya fushi dani." ta ƙare maganan hawaye na zuba daga cikin idanunta. Itama Raleeya Idanunta ne suka ciko da ƙwalla, murmushin jin daɗi ta saki, tare da ƙara rungume Zaleehan, cikin farinciki tace. "Masha Allah Zaleeha natayaki murna ƙwarai, yanzu kema zakiyi rayuwa cikin farinciki." Dai-dai lokacin Ummi ta fito daga ɗaki, dan tun tana banɗaki takejin ƙiran da Zaleehan keyi mata, ganin Ummi yasa cikin sauri tatashi daga jikin Raleeya, ƙarasawa tayi da sauri kaman wata ƴar ƙaramar yarinya ta raɓa jikin Ummi, tana sakin dariya me haɗe da hawaye. Cikin nuna farin cikinta tace. "Ummi Baba Malam ya yafemin, hakama su Mamy, Ummi har Ya Ahmad ɗina ma ya yafemin, kuma yanzu basa fushi dani, Ummi Hamma Saif ne yayi min komai, saboda shine duk kowa ya yafemin, shikenan yanzu Baba Malam ɗina baya fushi dani." taƙare maganan tana me sake rungume Ummi, sam ita bata ɗauki Ummi mazaunin suruka ba, ko yaushe amatsayin uwa take ɗaukanta, dan abun da za tayiwa Mama da Mamy shi zatayiwa Ummin, saboda acikin jininta soyayyar Ummin take. Cikin farin ciki Ummi ta shafi fuskarta, tare da cewa. "Alhamdulillah, tabbas kinzo da labari me daɗi, kuma naji daɗin hakan sosai, dama nasan ke ta gaban goshin Baba Malam da ya Ahmad ne, saboda haka yanzu kuka ya ƙare, idan kuma nasake ganin hawaye akan wannan fuskar to fa zamu ɓata, kindai ji kam." Murmushi me kama da dariya tayi, kamo hannun Ummin tayi cikin sanyi tace. "Nagode sosai Ummi haƙiƙa kin cika uwa tagari, samun irinki awannan duniyar zaiyi wahala, Inasonki Ummi na, dan Allah ki ƙara yiwa Hamma Saif godiya, duk ta dalilinshi ne Baba Malam ya yafemin, ku ɗin kunzama majingina agareni, sannan kunzaman to mini lema, wanda daku ne zan kare ruwa da zafin rana, nagode sosai!". tafaɗi maganar tana sakin wasu hawayen farinciki, tare da sake rungume Ummin. Murmushi Ummi tayi, sosai takejin soyayyar Zaleehan acikin ranta, tabbas tasan Zaleeha mutumiyar ƙwarai ce, kuma tasan bazata taɓayin danasanin samunta amatsayin suruka ba. Hayatuddeen wanda tun ɗazu ya shigo falon, ƙarasowa garesu yayi, tare da haɗasu su duka ya rungume ta gefen Ummi cikin farinciki yace. "Nima Inasonki Adda Zaleehan Hamma, saidai kuma zan iyayin kishi dake ako da yaushe, dan naga kaman kinason maidamin Ummi na taki ke kaɗai." Murmushi su dukansu sukayi. ɗan ɗagowa Zaleeha tayi, tana share hawayen dake kan fuskarta tace. "Ai dai kuma indai ina cikin gidannan Ummi tawa ce dan kai kayi ƙato. Ko Ummi?". ta faɗa tana mutsutstsuka idanunta, hakan yasa tadawo kaman wata ƙaramar yarinya. Ƴar dariya Ummi tayi tare da cewa. "Ƙwarai kuwa, amma fa saidai in kin ɗauki al'ƙawarin cewa bazaki sakeyin kuka ko abayan idanuna ba, sannan kuma kada kice zaki sakeyiwa Adda Maryam kuka, nasan kinsan cewa mamaci bayason kuka, addu'a kawai yake buƙata, saboda haka Adda Maryam addu'a take buƙata awajenki ba kuka ba, daga yau kuma banso na ƙara ganinki cikin ƙunci, tun da Baba Malam ya yafe miki, inason ki saki jikinki, ki zauna acikin ƴan uwanki, sannan kuma daga yau banason naga kina takura kanki kinji ko." Kanta ta jinjina alaman. "To." Murmushi Ummi tayi tare da shafa kanta, cikin kulawa tace. "Allah yayi muku al'barka, ya kuma baku zaman lafiya keda abokiyar zamanki." sunkuyar da kanta ƙasa tayi tana wasa da ƴan yatsun hannunta tace "Ameen" Hayatuddeen ne yaja hanunta suka dawo cikin falon, nan kusa da Raleeya suka zauna, kallonta yayi cikin nuna jin daɗinsa yace. "Wallahi Adda Zaleeha kinfi kyau idan kina murmushi, yanzu da kina murmushi bakiga yanda kikayi kyau ba, sannan kuma nasan yau da dare zamu buga game sosai tunda naga kina cikin farinciki ko?." Murmushi tayi tare da cewa. "Ni dai bazan buga game da kai ba, abunda duk nasan halinka, rinto kakeyi, ranan ai naga kanata yiwa Raleeya rinto." Ummi da Raleeya wacce waya takeyi da Raihana ne sukayi dariya, shikuwa Hayatuddeen murmushi mugunta yayi, cikin son tsokan Raleeyan yace. "Adda Zaleeha bakisan wacece Adda Raleeya bane, itace fa bata iya game ɗin ba, shine kuke ganin kaman rinto nake mata." Hararansa Raleeya tayi tare da cewa. "Faɗawa wanda baisan waye kai ba yaro,kowa ya sanka da rinto." Nan dai dukansu suka ɗanyi murmushi, daga haka kuma suka shiga ɗan taɓa hira. Acan ɓangaren Saifuddeen kuwa, yana isa part ɗinsa, kai tsaye bedroom ya wuce, yana shiga ya soma rage kayan jikinsa, cikin nutsuwa ya cire riga haɗi da wandon dake jikinsa, wani farin towel ya zaro daga cikin wani ɗan ƙaramin drawer, tare da ɗaurawa akan waist ɗinsa, ahankali yake tura wheelchair ɗin nasa, har ya kawo bakin ƙofar shiga bathroom, hannunsa ya ɗaura ajikin handle ɗin ƙofar sannan ya tura kansa ciki, komai na cikin toilet ɗin nasa tsab yake, ƙamshi ne kawai ke tashi, sanin cewa kwata kwata bayason ƙazanta yasanya Ameena ke ƙoƙarin gyara masa toilet ɗin nasa kullum dan Ameena akwai tsabta, cikin nutsuwa ya haɗawa kansa ruwan wanka me ɗan ɗumi, tare da zuba wani irin turaren wanka me daɗin ƙamshi acikin ruwan, kunce towel ɗin jikinnasa yayi, ahankali yaɗan matso da kekensa kusa da bathtube ɗin, kamar yanda ya saba, cikin nutsuwa yake komansa, koda ya shiga cikin bathtube ɗin, ɗan zamewa yayi ya kwanta, tare da jingina kansa da jikin saman bathtube ɗin, hakanne yabawa ruwan ɗumin daman ratsa ko ina najikinsa, ɗan lumshe idanunsa yayi tare da sakin wata irin ajiyar zuciya me ƙarfi. Ahankali moment ɗinsu da Zaleehan ke dawowa cikin tunaninsa, wani irin sabon yanayi ya samu kansa aciki, laɓɓansa ya ɗan lasa, saboda tunawa da sweet mood ɗinsu da yayi, musamman ma yanda ɗazun bakinta ke gogan ƙirjinsa, samun kansa yayi cikin wani irin shauƙi, baisan wani irin so yakewa Zaleeha, da har yakejin wani irin feelings na musamman akanta ba, Ameena ce ta fara faɗo masa arai, hakanan yaji gaba ɗaya jikinsa yayi sanyi, sam bai taɓajin abun dayaji ayau dangane da Zaleeha, akan Ameena'n ba, saidai kuma koma miye itama tana da nata matsayin acikin rayuwarsa, saboda itace mace ta farko daya fara sani acikin rayuwarsa, itace kuma wacce ta fara haifa masa ɗa, sannan tasoshi amatsayinsa na nakasashshe, nakasarsa baisa taƙisa ba, ta kuma rungumesa amatsayin miji, duk da tasan cewar baya sonta, amma hakan baisa taƙi yi masa biyayya ba, ko yaushe so take ta faranta masa, saboda haka ko kusa Ameena bata cancanci wulaƙanci daga garesa ba, koba komai tayi masa halacci, haƙiƙa Zaleeha itace mace ta farko daya fara so, kuma yakejin soyayyarta acikin jininsa, sannan itace zaɓinsa, Saɓanin Ameena da ta kasance zaɓin Ummi, sai-dai kuma duk da haka tana da nata matsayin awajensa, wulaƙanta ta kuma tamkar budulci ne ga Umminshi. Sake gyara kwanciyansa yayi, yana mejin kasala nasake sauƙar masa, gaba ɗaya abun da Zaleehan tayi masa, ya hautsuna tunaninsa, haka yayi wanka jikinsa duk amace, koda ya fito acikin bathtube ɗin wata rubber bathrobe yasanya, saida ya ɗauro al'wala kafun ya fito daga cikin toilet ɗin. Nan ya kimtsa kansa cikin wasu riga da wandon jeans masu kyau da tsada, feshe jikinsa yayi da turarensa me dadin ƙamshi, ɗan ɗaga kansa yayi ya kalli agogon dake saƙale ajikin bangon ɗakin. Ganin 3:30 pm yasanyashi ɗaukan wayansa da kuma laptop ɗinsa, ahankali yake tafiyar da wheelchair ɗinsa har ya fice daga cikin ɗakin, sam bayaso ya makara dan ƙarfe 4:00 pm daidai zasu gudanar da meeting acan ƙungiyarsu ta JONAPWD. Cikin nutsuwa ya fito compound ɗin gidan, nan ya iske Sule driver da kuma Bala megadi suna al'walan sallan la'asar, cikin body language ɗinsa yayiwa Sule driver alaman cewa yafito da mota zasu fita, kai Sule driver'n ya jinjina masa alaman "To." saida ya jira suka gama alwalan, sannan sule driver ya fito da motar, ya shiga ayarinsu suka wuce masallaci. Koda suka idar da sallan azkar yayi, sannan ya tashi ya hau kan kekensa, ganin haka yasa shima Sule driver miƙewa tsaye. Shi ya buɗewa Saifuddeen ɗin murfin motar ya shiga, sannan shima ya zaga ɓangaren driver ya zauna, Bala mai gadi ne yayi musu adawo lafiya, sannan sule yaja motar suka tafi, kai tsaye ƙungiyar Jonapwd ɗin suka nufa. Acan ɓangaren Ummi kuwa, bayan sunyi Sallan la'asar, Raleeya ne ta wuce kitchine dan ɗaura dinner. Zaleeha kuwa koda ta idar da sallan falo ta fito, ganin Raleeya a kitchine yasa itama ta nufi kitchine ɗin, amsan girkin tayi tare da cewa. "Raleeyan taje ta huta." duk yanda Raleeya taso suyi aikin tare Zaleeha taƙi, dole haka Raleeya ta koma falo ta zauna ita kuma Zaleeha ta ci gaba da aikin. Tana nan acikin kitchine ɗin, Ameena ta dawo daga wajen aiki, ɗakin Ummi tafara zuwa ta gaishe da ita, sannan ta wuce ɓangarenta. Zaleeha kuwa ana ƙiran sallan magriba ta gama girke-girken nata, nan kan dinning ta jere abincin wanda gaba ɗaya ƙamshinsu ya cika falon, Hayatuddeen dake zaune afalo kuwa sai faman haɗiye yawu yake, koda tana girkin ya shigo kitchine ɗin yafi sau uku, duk shigansa kuwa sai ya buɗe tukunya ya ɗanɗani stew ɗin da Zaleehan ta haɗa, wanda yaji naman kaji, ganin yanda yake lashe mata tukunya ne yasa ta saki murmushi, nan ta zuba masa pepper meat acikin wani ɗan plate, tare da kama hannunsa ta turasa falo, dan yaƙi ya barta tayi aikinta cikin nutsuwa. Hayatuddeen kuwa dama abunda yake nema kenan, haka ya bararraje ƙafafu yana cin pepper meat ɗin, sai faman kaɗa kai yake yana santi. Yana gamawa kuwa ya wuce masallaci. Itama Zaleehan ɗaki ta wuce, wanka tayi sannan ta ɗauro al'wala, wani body lotion ta shafa, tare da fesa turaren white oud ajikinta, take kuwa gaba ɗaya jikinta ya gauraye da ƙamshi. Wata ƴar siririyar pencil gown me stones ta sanya ajikinta, sosai kuwa rigan tayi mata kyau, dogon gashinta wanda ya kwanto har gadon bayanta ta ɗaure da ribbom sannan ta ɗaura hijab akan kayan, nan kan darduma ta hau tare da tada Sallah. Acan ɓangaren Saifuddeen kuwa, kusan awa biyu suka ɗauka a Jonapwd suna meeting, koda suka kammala kowa ya watse, hira suka ɗan taɓa shida Ishaq kafun ya shiga mota suka kamo hanyar gida, anan masallacin dake jikin gidan sukayi sallan magriba, koda suka idar da sallan zama yayi acikin masallacin, har lokacin sallan isha ya cika, bayan sun idar da sallan ne ya sanya hannuwansa ya dafa ƙasa, ahaka yake ɗan jan jikinsa har ya ƙarasa bakin ƙofar shigowa masallacin inda anan yake aje wheelchair ɗinsa, yana hawa kuwa controlling wheelchair'n yayi, inda ta soma tafiya da kanta, dai-dai zai shiga gida ne suka haɗe da Ahmad, wanda shima daga masallacin yake, yawan jama'a shiyasa basuga juna ba, saman keken Saifuddeen ɗin ya kama, haka suka nufi cikin gidan, cikin body language ɗinsa ya ke bawa Ahmad ɗin labarin meeting ɗin da sukayi yau. Ahaka har suka ƙarasa part ɗin Ummi, anan cikin falon kuwa, Ummi ne da kuma Raleeya, sai Hayatuddeen dake faman turo baki, waishi adole yunwa yakeji, kuma Ummi tace bazaici abinci ba sai yajira kowa yazo sun haɗu a dining area, dan daga yau gaba ɗaya ahalin gidan atare za suna cin abinci, daga kan break fast har zuwa dinner, lunch ne dai kowa zai iyayi aɗakinsa. Shigowar su Hamman nashi ne yasa ya ɗanji sanyi aransa, dan yasan yanzu Ummi zatace suje suci abincin, shikansa yasan idan aka tsananta bincike ba yunwa yake jiba, kwaɗayine kawai ke damunsa, musamman ma yanda yaga yau Adda Zaleehan ta girka musu abubuwan daɗi kala kala. Cikin girmamawa Ahmad yaɗan rusuna ya gaishe da Ummi, dan yau tun safe daya fita agidan baidawo ba sai yanzu, fuska asake Ummi ta amsa masa, tare da tambayansa ya aiki. Ya amsa mata da "Alhmdlh." Saifuddeen kuwa ƙarasowa wajen Ummin nasa yayi, tare da ɗan shafa gefen fuskarta, cikin kulawa haɗi da tsantsar soyayya yaɗan ɗaura kansa agefen kafaɗanta, murmushi Ummin tayi tare da shafa lallausan sumar kansa, tabbas yau yafaranta mata rai daya kai Zaleehan gida, har kuma Baba Malam ya yafe mata, cikin kulawa tace. "Ya meeting ɗin naku?" idanunsa yaɗan lumshe tare da jinjina kansa alaman, "Komai ya tafi yanda akeso." Jin sallaman Ameena ne yasasu duk suka ɗago kai suka kalleta, sanye take da riga da sket na atamfa, yayinda ta zuba meckup akan fuskarta, babu laifi ta kyau sosai, sannan kayan ma sunyi mata kyau, Adeel ne ɗauke a kafaɗanta, haka ta ƙaraso cikin falon, sai baza ƙamshi take, dan wani turare me shegen ƙarfi tasa, hwanda yasa gaba ɗaya falon ya ɗauka, murmushi ta sakarwa Saifuddeen wanda ke kallonta, shiɗin ma murmushin yayi mata, Ummi ne ta amshi Adeel tana yi masa wasa, Ameena kuwa nan kusa da Raleeya ta zauna, bayan ta gaishe da Ahmad, cikin sakin fuska kuwa ya amsa mata, harma da tambayanta ya aiki, tana murmushi ta amsa da "Alhamdulillah." Hayatuddeen ne ya miƙe tsaye, tare da duban Ummi, cikin shagwaɓa yace. "Ummi shikenan ai tunda dai kowa yazo ai sai muje muci abincin ko?". Murmushi Ummi tayi tare da cewa. "To acici." Shiya fara zama akan dinning ɗin, sannan Ahmad da Saifuddeen suka rufa mishi baya dan duk yunwa sukeji, babuma kamar Ahmad wanda tun lunch da yayi baisake sa komai abakinsa ba sai ruwa. atare Raleeya da Ameena suka ƙarasa kan dining ɗin, nan kujeran dake kusa dana Saifuddeen Ameena ta zauna, Raleeya kuma ta zauna akusa da Ahmad ɗinta, wanda keta jifanta da wani irin mayataccen kallo, ƙasa-ƙasa yake lumshe mata idanu, murmushi tayi tare da ɗan sa hannu ta muntsineshi, dan sarai ta gane me yake nufi, takarance sa tsab, da ta ga yana mata irin wannan kallon, to matsanancin feeling ɗinta yakeji. Ummi ne ta ƙaraso nan kan dining ɗin, rungume da Adeel ajikinta, cikin kulawa tace. "Hayatuddeen jeka ƙira Zaleeha tazo taci abinci." Jin cewa Zaleeha zai ƙira yasa batare da ya musa ba ya nufi ɗakin nata, nan Ummi taja kujera ta zauna. Ameena kuwa jin an ambaci sunan Zaleeha yasa taji wani abu ya tokare mata ƙirji, Allah ma yasani tana matsanancin kishin Saifuddeen, shiyasa ko sunan Zaleeha bataso taji anƙira, bawai tsanan Zaleeha takeji aranta ba, zallan kishine kawai sai kuma haushinta da takeji. Zaleeha kuwa tunda tayi sallan isha tana nan zaune akan sallayan bata tashi ba, suratul falaq take karantawa acikin ranta, dan nemawa Adda Maryam dama duk wani musulmin daya rigayemu gidan gaskiya gafara awajen Allah. Shigowar Hayatuddeen ne yasa taɗan ɗago kanta ta kalleshi, cikin kulawa yace. "Adda Zaleeha kizo muyi dinner inji Ummi." Kanta ta jinjina masa, sannan ta soma ƙoƙarin tashi daga kan sallayan, hijab ɗin jikinta ta cire, nan cikin drawer'nta ta ciro wani ɗan mayafi mai kauri, ta yafa ajikinta, sosai tayi kyau, dan kalan mayafin ya karɓi kyakkyawar fuskarta, duk Hayatuddeen na tsaye ajikin ƙofa yana kallonta, ganin tana ƙoƙarin fitowa batare da ta saka turare ba, yasashi kamo hannunta suka koma cikin ɗakin, turaren daya saya mata ya ɗauka ya ƙara fesa mata, murmushi ta saki tare da cewa. "Kaidai Hayatuddeen rigima ne dakai, ɗazu fa na fesa turaren kuma har yanzu akwai ƙamshin ajikina." Kansa ya jinjina tare da cewa. "Eh naji ai, amma so nake ki ƙara". Murmushi kawai tayi sannan tabi bayansa suka fice daga cikin ɗakin. Daddaɗan Ƙamshin turarenta shiya fara ziyartan hancinsu, ahankali yaɗan lumshe idanunsa tare da haɗiyan wani yawu daya tsaya masa amaƙoshi, Ameena kuwa da sauri ta juyo dan bakaɗan ba ƙamshin ya tafi da ita, idanunta na sauƙa akan Zaleeha taji gabanta ya faɗi, saboda wani irin kyau da taga Zaleehan ta ƙara, kau da kanta tayi tare da ƙara matsaya kusa da Saifuddeen, har jikinsu na gogan na juna, Zaleeha kuwa cikin nutsuwa ta ƙaraso kan dining ɗin, fuskarta ɗauke da ɗan murmushi tace. "Ummi barka da dare." Murmushi Ummin tayi, tare da cewa. "Yauwa dai Zaleeha sannunki, dan kema yau kinsha aiki, daga samun sauƙi kuma sai shiga kitchine". ɗan murmushi Zaleehan tayi tare da miƙa hannu ta karɓi Adeel, dai-dai lokacin Saifuddeen ya buɗe idanunsa ya sauƙesu akanta, murmushin daya bayyana dimples ɗinta tayi, tare da ɗan manna fuskar ta da ta Adeel ta sakar masa kiss akan bakinsa, cike da ƙaunar yaron tace. "I miss you my sweet papy na." Baki Adeel ɗin ya wangale yana yi mata dariya. Ɗan lumshe idanu Saifuddeen yayi, tare da lasan lips ɗinsa, dan kiss ɗin da Zaleehan tayiwa Adeel haka yaji kaman shi tayi wa, a ranshi yace. "Uhummm da yadda akeson Adeel haka akeson Abbanshi da duniya tai mana daɗi, kalli yadda take son yaron kamar tana son ubanshi". Kujera Zaleehan taja ta zauna, wanda kuma hakan yasa suke facing ɗin juna ita da Saifuddeen ɗin, ɗan kallon Ahmad tayi cikin muryarta me ɗauke da sanyi tace. "Barka da dare Ya Ahmad." Hakanan yaɗanji tausayinta ya kamasa, fuskarsa yaɗan saki sannan ya amsa mata. Fuskarta ɗauke da murmushi ta kalli Ameena wanda keta ƙara shigewa jikin Saifuddeen, murmushi tayi mata tare da cewa. "Ummun Adeel sannunki da dare." Duk yanda Ameena taso daure kishinta akan Zaleeha abun naneman fin ƙarfinta, dole haka ta daure ta ƙaƙalo murmushi, cikin muryarta da ta maƙale tace. "Yauwa." Ummi ne tasa hannu ta amshi Adeel ɗin, cikin kulawa tace. "Kawo sa yanzu saiki fa ke dashi kiƙi cin abinci, nasan halinki sarai, tashi ma kiyi seving ɗin mu." Murmushi Zaleehan tayi tare da miƙewa tsaye, food flasks da kuma plates ɗin ta jawo gabanta, cikin nutsuwa tashiga zubawa kowa abincin, Kyawawan idanunsa ya zuba mata, a ƴan kyawawan yatsunta yake kallo, komai tanayinsa ne acikin nutsuwa. Ameena da gaba ɗaya haushin Zaleehan ya cika zuciyarta, ɗan kallon Saifuddeen ɗin tayi, ganin ya ƙure hannun Zaleehan da ido, yasa taji kaman ta tashi awajen, wani baƙinciki da kishine suka tokare maƙoshinta, gaba ɗaya da zuwan Zaleehan sai duk taji ta raina kanta, hakanan taji babu ma irin ƙamshin da ta tsana kamar ƙamshin oud ɗin da ke jikin Zaleeha'n. Zaleeha kuwa sam hankalinta ma ba akansu yake ba, cikin nutsuwa ta gama seving ɗin kowa, ɗan matsowa gabansa tayi ta ajiye masa nasa abincin, komawa tayi ta zauna, tare da jawo plate ɗin da ta zubawa kanta abinci aciki, dubanta Ummi tayi cikin kulawa tace. "Zaleeha ɗan wannan abincin shi zaki ci kuma har ki ƙoshi". Murmushi ta ɗanyi, tare da cewa. "Eh Ummi, amma idan ban ƙoshi ba zanci na Hayatuddeen." Kai Hayatuddeen ya jinjina, murmushi kawai Ummi tayi, haka suka shiga cin abincin. Loman farko da yayi, ya lumshe kyawawan idanunsa, dan kuwa sosai yaji ɗanɗanon abincin abakinsa, tabbas Zaleeha ta iya girki sosai, wanda har yau yana mamakin a ina ta koyo girki kala kala haka. Abinda bai saniba ƙabilar su mama sunyi zarra a iya girki kuma Zaleeha Mama ta gado a iya girki kana ta samu horon Mamy iya sarrafa abin da za'aci. Ameena ma tun aloman farko da tayi, gaba ɗaya jikinta yayi sanyi, dan kuwa taji ɗanɗanon abincin ya banbanta da wanda Raleeya ta saba girkawa, maganan Hayatuddeen ne ya katse mata tunani, inda yace. "Kai Adda Zaleeha wallahi kin iya girki." Jin cewar Zaleehan ne tayi girkin yasa duk taji abincin yafita aranta, domin Zaleehan iya girki nesa ba kusa ba. Ahmad shi kansa yau ya yaba da abincin dan buɗe cikinsa yayi yaci sosai. Zaleeha kuwa ahankali take ɗan tsakuran abincin tana kaiwa bakinta, yanayin yanda take tauna abincin cikin nutsuwa shi yasa Saifuddeen yake ta faman satan kallonta. Ganin haka yasa Ameena tsaida cin abincin tayi shiru, hakanan taji idanunta na neman kawo ruwa, ɗan juyowa Saifuddeen yayi ya kalleta, ganin yanda tayi shiru ne, yasa ya ɗan tsiyayi drinks acikin cup, hannunsa yasa miƙa mata cup ɗin, Rau-rau tayi da ida nunta hawayen kishi na gab da zubo mata, Tuni Saifuddeen ya karanci Ameena tanada masifar kishi, har ga Allah yasan ta tsananin sonshi amman yana mata addu'a Allah ya sassauta mata zafin kishinta. Gani tana gabda zubda hawayene yasa yayi niyar bata abu mai sanyi tasha zataji sassaucin abinda takeji a ranta. A hankali yakai cup ɗin drinks ɗin bakinta, ɗan shagwaɓe masa tayi, tare da buɗe baki ya bata drinks ɗin, saida tasha rabin cup ɗin sannan ya ajiye, da ido ya nuna mata filet ɗin alamun taci abincin, kai ta sunkuyar cikin sanyi tasa hannu ta ɗauki spoon ɗin madadin taci sai tayi ta wasa da cikalin. Numfashi ya ɗan fesar kana yasa hannunshi akan nata, hannu dake gefenshi murza hannu yake ɗanyi a hankali alamun taci. itakam dama abun da take nema kenan, saboda haka saita biye masa, duk dan saboda tanason kawar da hankalinsa akan Zaleeha, Kallo ɗaya Ummi tayi musu ta watsar tare da girgiza kanta, dan ta fahimci cewa sam Saifuddeen bayajin kunyarta, Ahmad kuwa murmushi kawai yayi yaci gaba da cin abincinsa. Raleeya ma ƙasa tayi da kanta, hakanan taji wani iri, sam batason abun da zaisa Zaleeha taji babu daɗi aranta. Hayatuddeen kuwa baki ya sake yana kallonsu, har acikin ransa yana mamakin dalilin dayasa ayanzu Hamman nasa ke ƙoƙarin nunawa Ameena kulawa agaban kowa. Itakam Zaleeha kallo ɗaya tayi musu ta maida kanta ƙasa , kwata kwata abun nasu baya damunta, wani lokaci ma sai abun da sukeyi ɗin yana bata dariya, dan ta fahimci kamar Ameena'n bata iya sirranta soyayyarta ba, amma ganin ba huruminta bane, shiyasa ma takeyin kamar bata gani ba. Saifuddeen kam har acikin ransa da yakeyin hakan dan sassauta kishin Ameena, kana a wani sashin kuwa da gaggan yakeyi dan kawai Zaleehan taji wani abu aranta, Ameena kuwa gaba ɗaya ta sakankance, shiya dinga yi mata wani irin kallo, tana mejin wani irin daɗi acikin ranta, hakanan idan Saifuddeen na mata hakan agaban Zaleeha take jin kanta kaman tafi kowa a duniya. ganin ta girgiza mishi kai alamun ta ƙoshine yasa ya sake bata abin sha. Ɗagowan da Zaleeha zatayi ta gansu ahaka, take taji ƙirjinta ya buga. Cikin sauri ta kauda kanta wani sihirtaccen murmushi tayi kana ta miƙe a hankali hannu ta miƙa ta karɓi Adeel dake hannun Ummi, kana ta juya ta nufi cikin falon, sam Ummi batayi yunƙurin hanata ba. Wani irin murmushi Saifuddeen yayi, tare da ɗan cije laɓɓansa, cikin zuciyarsa yace. *"Ƴarinya yanzu aka fara wasan."* Hayatuddeen ne ya miƙe yayi ɗakinshi, Hakama Raliya ta miƙe tabi bayan Ahmad. Ido Ummi ta zubawa Saifuddeen ko ƙibtawa batayi, ganin haka yasa itama Ameena ta miƙe ta nufi side ɗinsu dan taje ta sake wonka dan ta lura yau Saifuddeen a matsaye yake. Shiru falon ba motsin kowa, gaba ɗaya Ummi ta hana Saifuddeen motsi dan yasan tun yana yaro in ya mata laifi taka hukunta shi da hakan, cikin fargaba ya ɗan gyara zama tare da yin rau-rau da ida nunshi wanda da gaske sun cicciko da ruwa dan bai fahimci abinda yayi yanzu bane ya ɓata mata rai. kai ya rangwafar tare da mata mgna da yarensu. "Ki gafar ceni Ummi ban san me nayiba, na tuba gaya min laifiba?". Kwaffa tayi tare da cewa. "Uhummmm yayi kyau Saifuddeen kaci gaba da cusawa ƴar mutane baƙin ciki". Kanshi ya jujjuya cikin alamun mgnarsu yace. "Ummi me kuma nayi, na kaita gidan su na tayata bada haƙuri, duk sun yafe mata nima na yafe mata, kuma yanzu meya rage?". miƙewa tsaye tayi tare da cewa. "Key ɗin ɗakinta zaka bani, ta koma ɗakinta,kuma ka raba musu kwana kamar yadda shariya ta buƙata". Wayarshi ya zaro tare da rubuta mata. "Wlh Allah Ummi na mance inda na ɓoye key ɗin amman insha Allah zan neme shi in na ganshi zan bakishi". kai ta jinjina tare da cewa. "Tom yayi kyau". Daga nan ta juya ta nufi ɗakinta. Shiru Saifuddeen yayi yana saƙa da warwara a ranshi, wani irin munafikin murmushi yayi kana ya wuce side ɗinshi, yana tafe yana rubuta wa Ameena saƙo ya tura mata kana kai tsaye ya wuce ɗakinshi. Wasa farin girki sannu-sannu bata hana zuwa sai dai a daɗe ba jeba, muna gab da shigo wani sashi mai ɗan karen zaƙi a littafinsa biya ɗarinki uku ki karanta ba tare da haƙƙin kowa a kankiba, in kina buƙata ga number ta 09097853276 ki turo katin mtn na 300 ko kimin transfer na 300 ta asusuna na 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. By *Garkuwan Fulani* [16/09, 6:49 pm] +234 706 370 3964: Ngs Bayan duk sun gama fita daga falon Ummi kaitsaye ɓangarensa ya nufa, ahankali yake tura wheelchair ɗin nasa, wayarsa ƙiran Samsung ya ciro tare da laluɓo number'n Ameena ya tura mata text, ganin saƙon ya tafi ne yasa ya maida wayar cikin al'jihunsa, ahankali ya murda handle ɗin ƙofar ɗakin nasa ya wuce ciki. Yana shiga kuwa yaɗan rage kayan jikinsa, tare da hayewa saman gadon ya kwanta. Can ɓangaren Ameena kuwa tana nan zaune taga saƙon text ɗinsa, koda ta karanta ɗan murmushi tayi tare da lumshe idanunta, ita dai dama tun ɗazu da suke cin abincin tagane take takensa, miƙewa tayi tare da ƙarasawa gaban mirror, turare ta ɗan fesa ajikinta, sannan ta fice daga cikin ɗakin, dan dama tun shigowarta ma bata shigo da Adeel ba, yana can wajen Zaleeha. Ahankali ta tura ƙofar ɗakin ta shiga bakinta ɗauke da sallama, duk da tasan cewar bayaji, amma ako yaushe idan zata shigo ɗakin nasa saitayi sallama, kamar yanda addini ya koyar. Ganinsa kwance akan gado ya sa taɗan saki murmushi, ahankali ta ƙaraso jikin gadon, anan bakin gadon ta zauna. Idanunsa ya zuba mata, ganin haka yasa tace. "Naga message ɗinka, shiyasa nace bari nazo ko kana da buƙatar wani abu ne." Ɗan lumshe idanunsa yayi, ahankali ya ɗago hannunsa ya nuna ta, alaman cewa. "Ita yake da buƙata." Ɗan murmushi tayi, dan har acikin ranta taji daɗin hakan, amma abayyane kuwa gyara zaman ta tayi, tana ɗan murmushi tace. "Indai nice ae kagama samu, saidai kuma banso shigowa wajenka yau ba, saboda nayi tunanin banice dakai ba yau Zaleeha ce, shiyasa har na kwanta ma ganin message ɗinka ne yasa na fito." Tafaɗi maganan, tana me zuba masa idanu, dan ƙwarai ta ƙagu tafahimci abun dake wakana atsakaninsa da Zaleeha, wanda yasa bata zuwa ɗakinsa, da kuma zaman da taga tanayi a ɓangaren Ummi. Take yanayin fuskarsa ya sauya, lokaci guda yaji ransa ya ɓaci, sam baiso jin sunan Zaleehan abakinta ba, dan kwata kwata atsarinsa babu irin wannan rayuwan, da wata daga cikinsu zata kawo zancen abokiyar zamanta agabansa, sam bayaso kwata-kwata, domin yin hakan shikesawa Namiji ya zama kamar munafuki a tsakanin matanshi, shi kuma ko kusa baya fatan haka wa kansa. Jikin Ameena ne yayi matuƙar sanyi, musamman ma yanda taga ya haɗe gabas da yamma, lokaci ɗaya annurin fuskarsa ta gushe, gaba ɗaya jin zuciyarta tayi babu daɗi dan kwata kwata bataso ɓata masa ba, saidai kuma azuciyarta tana mamakin abun da zaisa ransa ya ɓaci dan kawai ta ambaci sunan Zaleeha, wanda ita kuma tayi hakanne dan ko zataji wani ƙarin bayani daga garesa ta samu ta gwaggwafi sirrin Zaleeha. Ɗan matsowa kusa dashi tayi tare da kama hannunsa, cikin sanyin murya tace. "Kayi haƙuri, bansan maganan dana faɗa zai ɓata ranka ba." Ɗan kawar da kansa gefe yayi, dan yanason nuna mata cewar ko gaba bayason irin hakan. Ganin ya kau da kansa gefe ne, yasa Ameena ta saki ɓoyayyen murmushi, cikin ranta tace. "To kodai dama bayason zaleeha'n ne? sannan idan da ace ma yana sonta, ai da zaina ƙiranta part ɗinsa, to amma kuma mayataccen kallonta da nake yawan kamasa yanayi mata fa? da kuma zamanta asashin Ummi duk me hakan ke nufi?." Ɗan jim tayi tare da sauƙe ajiyar zuciya. " kodai Wataƙila Ummin ne tace ta zauna a part ɗin nasu saboda rashin da akayi mata, dan hakan zai ɗebe mata kewa." Duk acikin ranta take maganan, yarda da abunda zuciyarta ta faɗa mata ne, yasa ta sake kamo hannun Saifuddeen ɗin, tare da tallafo haɓarsa ya zamana suna fuskantar juna, murmushi ta sakar masa tare da sanya hannu ta kama kunnenta, cikin sanyi tace. "Kayi haƙuri kaji please." Idanunsa yaɗan lumshe, tare dayi mata alaman cewa. "Kada ta sake yi masa irin hakan." cikin ɗanjin daɗi tace. "Insha Allah." rungumesa tayi tare da haɗe bakinsu waje ɗaya. Kasancewar dama tun haɗuwarsa da Zaleehan na ɗazu a cikin mota yakejin kansa amatuƙar buƙace, hakan yasa bai ƙi biye mata ba, haka suka sha romance ɗinsu, bayan komai ya wakana, ya tashi daga kwancen da yake, tare da hawa kan wheelchair ɗinsa, kai tsaye ya wuce banɗaki yayi wanka, yana fitowa itama Ameenan ta shiga, sai sakin ɓoyayyen murmushi take, dan ƙwarai taji daɗin kasancewarsu na yau ɗin. Koda ta fito ta samu har ya koma ya kwanta, yana ƙoƙarin rufawa jikinsa blanket, kayan baccinta ta sanya sannan itama ta hawo gadon, idanu ya zuba mata, cikin body language ɗinsa yace. "Ina Adeel?" tana me ƙulle gashinta tace. "Ai tun ɗazu yana can wajen Amminsa." Ɗan jinjina kansa yayi tare da lumshe idanunsa, dan ya gaji ƙwarai so yake yayi bacci. Ganin baice komai ba yasa ta ce. "Na karɓoshi ne?" akasalance cikin body language ɗinsa yace. "No idan bazaiyi kuka ba, ki barshi kawai." idanu ta ɗan zaro tare da cewa. "Chab aikuwa zaiyi kuka kam, halan dai kamanta Adeel ne, abunda kusan kullum da dare sai ya tashi shan nono, ba naje na karɓosa kada ma ya tashi tsakiyar dare ya hanasu bacci." ta ƙare maganar tana me sauƙowa daga kan gadon, ficewa tayi daga ɗakin, shikuwa blanket yaja ya sake rufe jikinsa, kasancewar har wani sanyi sanyi yakeji saboda gajiya, waist ɗinsa kuwa ciwo yake mai, shikansa yasan me raunine shi awannan ɓigeren, zaiyi ƙoƙarin jurewa, amma fa da za'aran komai ya kammala zaiji gaba ɗaya gaɓɓan jikinsa nayi masa ciwo hakan kuma baya rasa nasaba da larurarsa. Ameena kuwa saida ta fara biyawa ta ɗakinta ta ɗauko hijab kafun ta wucewa sashin Ummi'n, koda taje haka ta samu falon shiru, sai Hayatuddeen kawai dake zaune yana ta faman latsa wayarsa, yayinda ya saƙala earpiece akunnensa, hakanne ma yasa ko shigowan Ameenan bai ji ba, murmushi kawai Ameena tayi, sannan ta wucesa, kai tsaye ɗakin Zaleehan ta nufa, anan bakin ƙofan ta tsaya tare da ɗan ƙwanƙwansawa, jin shiru babu amsa yasa ta ɗan tura ƙofar ɗakin ahankali tasaka kanta ciki. Hango Zaleehan tayi kwance akan gado, yayinda ta ɗaura Adeel asaman cikinta, baccinsu suke cikin kwanciyar hankali, bisa duk kan alama ma Adeel ɗin ya riga Zaleehan bacci, dan yanayin da suke cike ya nuna, kaman cewa Zaleehan na shafa bayansa ne bacci ya ɗauke ta. Ɗan tsayawa ajikin ƙofar tayi, tana tunanin yanda za'ayi ta tashe su. Ummi wanda fitowrta daga ɗaki kenan ganin Ameena tsaye aƙofar ɗakin Zaleeha yasa ta ƙaraso, cikin kulawa tace. "Ameena lafiya kuwa, dama bakije kin kwanta bane?". Ɗan murmushi Ameenan tayi tare da cewa. "Lafiya ƙalau Ummi, dama Adeel ne nazo ɗauka, gudun kada ya tashi cikin dare yayi ta muku kuka, shine kuma nasamu daga shi har Ammin nasa bacci suke." Murmushi Ummi taɗanyi, ganin yanda Zaleehan ke rungume da Adeel akan cikinta, cikin yanayin ɗan tsokana irin na jika da kaka tace. "Aikuwa gwara da kikazo dan ban yiyuwa yaro da tsamin murya yazo cikin dare yayita mana kuka, duk ya hanu bacci." Murmushi Ameena tayi, wanda yayi kama da dariya. Ƙarasawa Ummi tayi inda ahankali ta ɗan soma janye Adeel ɗin daga jikin Zaleeha, dan bataso ta tashe ta. Zaleeha kuwa dama baccin nata bawai wani nisa yayi ba, cikin bacci taji kaman Adeel din zai faɗi, arazane ta farka tana faɗin. "Innalillahi Adeel karka faɗi." Murmushi Ummi tasaki tare da cewa. "Au dama baccin naki beyi nisa ba kenan, to ba faɗowa zaiyi ba, mamansa ne tazo ɗaukansa, in kuma so kike abarmiki shi ya isheki da kukan dare to." Ɗan mutsutstsuka idanunta tayi, ƙoƙarin tashi daga kan gadon take. Ummi tace. "Koma ki kwanta, zan miƙa mata shi." Komawa tayi kuwa ta kwanta, ita kuwa Ummi miƙawa Ameenan yaron tayi, tare da sanya hannu ta ragewa Zaleeha hasken wutan ɗakin. Haka suka fito daga cikin ɗakin, Ameena sai murmushi takeyi, tabbas ita kanta ta shida cewar Zaleeha na matuƙar son Adeel, so kuma na tsakani da Allah bawai so na ganin ido ba, kuma har acikin ranta tanajin daɗin hakan, ita dai kishin Saifuddeen ne kawai kesawa taji batason Zaleehan takejin ta tsaneta, amma bacin haka batajin tsanarta acikin ranta. Saida safe tayiwa Ummi kafun ta ficewa daga cikin falon, Ummi kuwa kaɗa kan Hayatuddeen tayi tare da cewa. Maza yaje ya kwanta, dan tasan halinsa sarai idan ta biyesa sai yakai kusan ƙarfe 1:00 am yana ta faman latsa waya batare da yaje ya kwantaba, sai da asuba kuwa ayita faman tashinsa yaƙi tashi, yana cewa mutane, bacci ne bai ishesa ba, bayan ɓata lokacinsa yake wajen kalle-kalle da kuma rubuce rubucen banza. Falon Ummi ta rufe sannan ta koma ɗaki ta kwanta. Hayatuddeen kuwa yana shiga ɗakinsa, ya murzawa ƙofar key, nan kan gado ya kwanta, tare dayin playing sabon BF ɗin daya yi downloading. Ɓangaren Ameena kuwa tana komawa ta samu har Saifuddeen yayi bacci nan ta kwantar da Adeel akan ɗan gadonsa na yara, sannan itama ta haye gado ta kwanta. Washe gari. Zaleeha ne zaune nan kan ɗaya daga cikin kujerun falon, kamar kullum sanye take da baƙar doguwar riga, Adeel ne riƙ ahannunta, wanda yasha wanka aka kuma shiryasa tsab cikin wasu haɗaɗɗun riga da wando na yara. Sosai Zaleeha ke tayiwa Adeel ɗin wasa, shi kuma sai ƙyaƙyata dariya yake. Raleeya dake zaune agefensu kuwa murmushi kawai take ta yi musu, dan ita kanta tanajin daɗin yanda Zaleehan ke nunawa Adeel ɗin ƙauna. Ameena ce ta shigo falon cikin ɗan sauri sauri tare da shirinta na zuwa aiki, Raleeya ne ta dubeta da murmushi akan fuskarta tace. "Monday tushen aiki ko na sara na tsoranka, kina ta sauri karki makara kenan." Jakan dake hannunta ta rayata tare da cewa. "Eh wallahi, kinga lokaci nata tafiya, gashi sam banason yin late wallahi." ta ƙare maganar tana me ɗan miƙawa Adeel dake kallonta hannu, Murmushi Zaleeha tayi tare da cewa. "Ummun Adeel barka da safiya." Itama Ameenan murmushin tayi tare da cewa. "Yauwa Auntyn Adeel barka, yi haƙuri na ɗaura miki ɗawainiya, ai danaga idan na tsaya shiryasa zan makara ne, shi yasa naƙira Hayatuddeen nace kawai ya kawosa ashiryamin shi anan ɗin." Ɗan murmushi Zaleehan tayi tare da cewa. "Ayya to ki barmin shi yau kam mu wuni mana." Haɓa Ameenan ta kama tare da cewa. "Chab aikuwa zaki sha kuka, dan Adeel baya wasa da ci, nan da anjima zakiga ya fara neman nono." Murmushi Zaleeha tayi tare da cewa. "Ya gado Bappanshi autan Ummi a cici kazar birni." dariya sukayi baki ɗaya su, shi kuwa Hayatuddeen da yanzu yake fitowa tura baki yayi tare da cewa. "A,a zakarar birni dai." Ummi wanda fitowarta kenan daga ɗaki ta kawar musu rigimar autanta da cewa. " To ki barshi mana, ba akwai madara da kuma abincin nan na yara basai adama masa yasha ba." Ɗan murmushi Ameenan tayi, tare da cewa. "Ai idan na fita yau Ummi bazan dawo ba har sai bayan magriba, kuma kinga kafun nan zaita damunku da kuka, saidai gobe ƙarfe 5 zan tashi a aiki, kinga saina bar muku shi goben ko." Kai Ummi ta jinjina tare da cewa. "To Adawo lafiya, dan dama nasan idan kika barsa ni zai dama da wannan rakaɗin muryan nasa." Dukansu murmushi sukayi sannan Ameena, ta amshi Adeel ɗin ta saɓashi akan kafaɗunta, suka fice daga cikin falon, sai kallon Zaleeha yake, har yanayi kaman zaiyi kuka. Ita kuma Zaleeha hannu ta ɗaga masa tana murmushi. A can side ɗinsu kuma Saifuddeen ne zaune akan wheelchair ɗinsa, bayan ya gama shirya kansa tsab dan yanaso yaɗan fita. Har ya juya xai fita daga ɗakin, kuma sai ya ɗan dakata, wayarsa ya ɗauka tare da shiga Whatsapp chat ɗinsa, sunan Ahmad ya nemo dan dama yanaso suyi magana, cikin sa'a kuwa ya samu Ahmad ɗin online. typing ya shigayi inda yace da Ahmad ɗin. "Aikin kenan always online baka ko gajiya, dama magana nakeso muyi." Ahmad dake zaune nan kusa da Raleeya ganin saƙon Saifuddeen ɗin ya sashi buɗewa ya karanta, ɗan murmushi yayi tare da cewa "Inajinka wace magana ce?". ganin saƙon Ahmad ɗin yasa ya ɗan gyara zamansa ataƙaice yace. "Dama furnitures ɗin bedroom ɗina zan sanja, so na ga wasu a online kuma har na biya kuɗinsu, abun da dai ya rage kawai shine akawomin." Idanu Ahmad yaɗan zaro, cikin mamaki yace. "wani furnitures kuma Saifudeen, meya samu na ɗakin naka, kwata kwata ma yaushe ka saya da har kakeson sanjawa?". Ɗan guntun murmushi Saifuddeen yayi tare da cewa. "To nidai banason gulma, na faɗa mane dan katsaya min akan kayan saboda suna da tsada sosai, mungama yin magana da masu company'n kuma sunce zasu kawomin har gida, dan na fiso idan aka cire na ɗakina akaiwa Goggo Dada dan naga itama furnitures ɗinta sun tsufa." Kai Ahmad ya girgiza tare da ɗanyin murmushi yace. "Agaskiya yaron nan kana wasa da kuɗi da yawa." Ahmad ya ƙare typing ɗin yana sakin dariya. Ganin abun da Ahmad ɗin ya rubuta, yasa Saifuddeen ɗin cewa. "Lallaima Ahmad ni kake ƙira da yaro, koda kanmu ɗaya kardai ka manta cewar ƙanwata kake aure, saboda haka yazama dole kaƙirani da sunan Yaya." Dariya sosai Ahmad yayi, sannan yace wa Saifuddeen ɗin, "Bakomai zaiyi duk abun da ya dace, amma ya barshi yanzu lokacin matarsa ce tukun." Murmushi kawai Saifuddeen yayi, tare da aje wayar, dan yasan idan ya biye Ahmad, sai ya zaro masa wata maganar kuma. Ɗan jingina bayansa yayi da jikin wheelchair'n ɗinsa, tare da ɗan juyowa ya kalli gadon nasa, cute smile yayi, cikin zuciyarsa yace. "Wannan gadon ayanzu bashi da amfani agareni, saboda Ameena taci amarcinta akai son ranta, yanzu kuma lokacin Zaleeha yayi, saboda haka dole nakawo sabin furnitures kodan saboda Zaleeha, dan kamar yanda take sabuwa, haka ma dole gadona yakasance sabo bazan haɗa mata komi sauran ta'annabina ba." wani murmushi ya sake yi, wanda shi kaɗai yasan ma'anarsa da kuma abunda yake nufi. Ahankali ya tura wheelchair ɗinsa ya fice daga cikin ɗakin, kaitsaye part ɗin Ummi ya wuce. A falo ya sameta zaune ita da Raleeya, ƙarasowa cikin falon yayi, ganin haka yasa Raleeya tashi taje ta kawo masa kunun aya me sanyi, wanda ɗazu Zaleeha ta haɗa. Babu musu ya amsa kuwa yasha, tun aɗanɗanon farko yasan cewa ba Raleeya bace tayi, haka yaji kunun yayi masa daɗi, har baisan sanda yasha fiye da rabin ƙofin ba. Ɗan ɗagowa yayi ya dubi Ummi, cikin body language ɗinsa yake faɗa mata cewar, zai sanja bedroom furnitures ɗinsa. Da mamaki Ummi tace. "Zaka sanja kayan ɗaki kuma Saifuddeen, me ya samu waƴan can ɗin, da kake ƙoƙarin sanjasu ka kawo wasu?". Murmushi ya ɗanyi cikin body language ɗinsa yace. "Ummi basuyi komai ba, kawai dai naga furnitures ɗin Goggo Dada duk sun tsufa ne, shiyasa nakeso idan aka kawomin sabi sai akai mata waƴancan ɗin." Murmushi Ummi tayi tare da jinjina kai, cikin kulawa da jin daɗi tace. "Masha Allah, to Allah ya ƙara arziki, ai kuwa kam gaskiya Goggo Dada taci sabin furnitures, gaskiya ka kyauta." da "Ameen" ya amsa, sannan ya ce da ita "Zai dan fita wajen aiki." "Adawo lafiya." Ummi da Raleeya sukayi masa, sannan ya juya yafita daga falon, bayan ya shanye gaba ɗaya kunun ayan da Raleeya ta zubo masa cikin kofi. Cikin ikon Allah da yamma kuwa sai gashi ankawo furnitures ɗin, wanda kyawunsu ya zarta gaba ɗaya kayan ƴan gidan, wasu irin haɗɗaɗɗun white furnitures ne masu kyau da tsadar gaske, saboda tsabar haɗuwansu haka akayi design ɗinsu kaman na sarauta. Ma'aikatan companyn da kansu suka shirya masa kayan bayan suncire tsofin furnitures ɗin. Gadon da aka sanya masa, irin gadon nan ne da ake ƙira aljannar duniya. Makeken gadone me ɗauke da tambarin MEGO luxury furnitures, wanda aka ƙawata kwalliyan jikinsa, da white and golden colour, yayinda samansa kuwa aka ɗanyi masa wani abu kaman rumfa, wanda yasha decoration mai masifar kyau, shikansa gadon kaɗai abun kallone, domin ya isa tafiya da hankalin mutum, gefe dashi kuwa, wasu haɗaɗɗun bedside ne wanda samansu ke ɗauke da mirror gold, sunyi kyau har sun gaji, idan aka matsa daga gefen dama kuwa, wani irin haɗaɗɗen drawer ne mai girma da tsari, kusan duka murafensa mirrors ne amma me zubin gold, ga kuma design na royal da akayi ajikinsa, yayi masifar kyau da burgewa. Daga gefen hagu kuwa, wani dan ƙareren dressing mirror ne wanda shima aka tsara masa zane me kyau na royal, wanda suke shige da zubin gold, daga gefen mirrorn kuwa wani ɗan ƙaramin drawer ne, irin wanda ake aje takardu ciki, asaman sa anyi masa wani design na gold me masifar kyau da burgewa, har wani ɗan flower green aka sanya aciki. Sosai kayan furnitures ɗin sukayi kyau, sun kuma dace da ɗakin nasa ƙwarai, Ummi ita kanta da ta shigo ta matuƙar yabawa da kayan, gashi sun zauna aɗakin sunyi ɗas, saikace fadar shugaban ƙasa, saidai kuma kallo ɗaya zakaiwa kayan kasan sunja million's of Naira, dan kayane masu kyaun gaskene. Haka dai aka kwashi furnitures ɗin daya cire din, aka wuce dashi Dukku gidan Goggo Dada. Koda ya dawo daga wajen aikin nasa kuwa sashin Ummi ya wuce. Anan ne Ummi take sake tambayar sa kan cewa. "Har yanzu baiga key ɗin ɗakin Zaleehan ba?" wani irin murmushi yayi tare da jinjina mata kai alaman. "Eh." Idanu Ummi ta zuba masa, aɓoye itama tasaki murmushi, cikin ranta tace. "Hmm dama ni ai najima da sanin cewa akwai abun da kake ƙoƙarin shiryawa, ajuri zuwa rafi dai wata rana dai tulu saiya fashe." Hira suka ɗan taɓa kaɗan a falon Ummi kafun daga bisani ya tashi ya tafi ɓangarensa, shikansa ya yaba sosai da kyawun furnitures ɗin daya saya ɗin, wanka yayi sannan ya nufi ɗakin Ameena, dan yasa aransa cewar bazai sake barinta taje ɗakinsa ba, shi zaike binta ɗalibta , har sai randa ya amshe budurcin Zaleeha bisa gadon kenan, saboda kwata kwata shi bai sayi wannan gadon saboda ita ba ya sayane dan cin amarci in ya amshe m'budurcin in yaso suci gaba da zuwa turakanshi. Ameena kuwa koda ta gansa aɗakinta tayi mamaki ƙwarai, amma sanin cewa bayason yawan tambaye tambaye yasa taja bakinta tayi gum, sai hakan ma ya zame mata kamar abun farinciki, dan yaune rana ta farko daya biyota ɗakinta shiyasa hakan yayi masifar mata daɗi. Washe gari. kamar yanda ta faɗa jiya, yau awajen Zaleeha tabar Adeel, bayan ta aje madara da duk kuma wani abun daya kamata da za'a bashi. Sosai Zaleeha taji daɗin barin Adeel ɗin awajenta, haka ta saɓasa akafaɗanta tanayi masa wasa, cikin ikon Allah kuwa ko kuka baiyi ba. Da rana ne kuwa Hayatuddeen yaje ya kwaso su Zakariyya, Isma'il, Imran, Sulaiman, Zaleeha taji daɗin zuwansu ƙwarai, nan falon Ummi suka baje, haka suka kafe kai da fata wai dole ita zata shiga kitchine tayi musu ferfesu, acewarsu wajenta suka zo ba wajen Ummi ko Adda Raleeya ba, haka dole ta sauƙe Adeel ta shiga kitchine ɗin, cikin ƴan mintuna ƙalilan kuwa ta dafa musu indomie, da kuma ferfesun naman kaji, nan tsakiyan falon suka zauna su kaci, gaba ɗaya surutunsu ya cika gidan, haka sukayi wa Ummi kaca-kaca da falo. Sunjima sosai agidan dan sai wajen bayan sallan la'asar kafun suka tafi. Ameena kuwa yau ƙarfe 5 ta dawo, koda ta dawo kuwa bata karɓi Adeel ba, yana nan awajen Zaleeha, saima da akayi sallan magriba ne ta karɓeshi ta bashi nono. *Bayan Kwana ɗaya* Sannu ahankali haka rayuwa ta cigaba da tafiya, inda acikin kwanaki biyun nan kullum sai Ameena tabarwa Zaleeha Adeel, awajenta yake wuni harta dawo daga wajen aiki. Hakanne yasanya shaƙuwa me ƙarfi ta shiga tsakanin Adeel ɗin da kuma Zaleeha tana jin yaron har cikin ranta. Saifuddeen ne zaune kan wheelchair ɗinsa, wayarsa ya jawo sannan ya turawa Raleeya, text akan taƙira Hayatuddeen suzo tare yana son ganinsu, kasancewar yau Hayatuddeen ɗin baida lecture'n safe shiyasa baije school ba. Suna shigowa cikin part ɗin nasa ya miƙowa Hayatuddeen key tare da cewa. "Karɓi key ɗin part ɗin Zaleeha ne." cikin yanayin zumuɗi Hayatuddeen yace. "Nakai mata." Hararansa Saifuddeen ɗin yayi, cikin body language ɗinsa yace. "To sarkin azarɓaɓi bahaka nakeson cewa ba." Ɗan zumɓura baki Hayatuddeen ɗin yayi, cikin shagwaɓa yace. "To me za ayi dashi." Duban Raleeya Saifuddeen ɗin yayi, cikin body language ɗinsa yayi mata alaman cewa. "Su shiga ɓangaren Zaleehan, suɗanyi share share." Murmushi Raleeyan tayi, har acikin ranta taji daɗi, saboda hakan alama ne dake nuna cewa Zaleehan ta kusa dawowa ɓangarenta, jan hannun Hayatuddeen tayi suka wuce sashin Zaleehan, shikuwa Saifuddeen laptop ɗinsa ya ɗauka ya cigaba da aikinsa. Raleeya da Hayatuddeen kuwa suna shiga sashin Zaleehan, suka soma ƴan share share da goge goge, kafun awa biyu tuni sun tsab tace ko ina sun gyara komai, haka falon yadawo sabo fil sai sheƙi yake, inda suka fesa turaren air feshener, suna tsaka da aikin ne Ahmad ya ƙira Raleeya dan tun ɗazu ya dawo baiganta ba, ya kuma sauƙo har ƙasa bai ganta ba. Nan take sanar masa cewa tana ɓangaren Zaleeha Hamma Saifuddeen yaɗan sasu suyi mata share-share da gyare-gyare. Ƙwafa Ahmad yayi tare da cewa. "Lalle ma Saifuddeen so yake ya maidamin da mata baiwa ko? yarasa wazai sa yayiwa Zaleehan share-share sai ke, zanyi maganinsa ne badai yayi mata biyu ba yaseen zamu ƙaura." Dariya Raleeya tayi sannan ta kashe wayan, nan dai suka kammala komai suka fice daga sashin. Washe gari ne Goggo Dada taturowa Saifuddeen saƙon godiya, da kuma fatan al'khairi kala-kala, dan sosai taji daɗin kyautar nasa. Nan yake ce mata. "Bakomai, Goggo Dada ai kema uwace agareni kuma uba". ananne ma yake ce mata. "Lafiya ko batazo tayi ta'aziyyan rasuwar Adda Maryam ba". cewa tayi. "Itama tana tason zuwa to amma Allah ne baiyi ba." take kuwa yace washe gari zai turo sule driver ya ɗaukota, haka dai tayi ta masa godiya, daga nan sukayi sallama . Murmushi yayi bayan ya aje wayar, cikin zuciyarsa yace. "Awannan karon Goggo Dada dake zanyi amfani wajen dawo da Zaleeha ɗakinta, tun alokacin da Ummi ta bini akan na bada key ɗin ɗakinta ban nemeshiba, yanzu kuwa dana ga key ɗin bani da wani ƙarfin guiwan da zan iya tunkaran Ummi nace mata ga key ɗin ɗakin Zaleeha, amma yanzu tunda dai zakizo nasan lokacin dawowan Zaleeha ɗakinta yayi, zanyi komai asauƙaƙe tayanda Ummi bazata zargeni ba." Haka dai yayita saƙawa da kuncewa, sosai ƙudurinsa ke ƙara ƙarfafa acikin zuciyarsa. Kaman yanda ya faɗa kuwa washe gari yasa Sule driver yaje har Dukku ya ɗauko Goggo Dada'n, Raleeya ne ta rakata gidan su Zaleehan tayi musu ta'azziyya, daga nan kuma suka dawo gida. Yauma kamar kullum Zaleehan ne tayi musu girkin abincin dare, kusan atare sukaci abincin, koda suka kammala cin abincin, nan cikin falon ta koma ta zauna akan sofa tare da tanƙwashe ƙafafunta, sama sama take ɗan kallon tv, ahaka taɗan jingina kanta da jikin kujeran falon, bacci takeji sosai, saidai sanin cewa Goggo Dada na cikin ɗakin nata yasa bata shiga ta kwanta ba, saboda kallon suruka takewa Goggo Dada'n. Ɗan sake jingina bayanta da jikin kujeran falon tayi, tare da lumshe idanunta, ta kuma sake riƙe Adeel dake jikinta ƙam, bacci takeji tare da gajiya, amma sam tanajin bazata iya shiga ɗakin nata ba, saboda Goggo Dada dake ciki, kunyanta takeji, musamman ma da takeson kafun ta kwanta tayi wanka. Hayatuddeen ne ya lura da yanda Zaleehan keta lumshe idanunta, alaman bacci. Hannu yasa ya ɗan taɓa kafanta cikin kulawa yace. "Adda Zaleeha bacci kikeji, kije ki kwanta mana." ɗan buɗe idanunta tayi, tare da sakin sassanyar murmushi. Raleeya dake jinsu ne taɗan ɗago kai, tare da duban Hayatuddeen ɗin tace. "Ai tun ɗazu Goggo Dada na ɗakin." Ɗan marairaice fuska Hayatuddeen yayi yace. "To Adda Zaleeha ki tashi ki hau saman kujera mana." Ummi da fitowarta daga ɗaki kenan, duk taji abun da suka faɗa, duban Raleeya tayi, cikin kulawa tace. "Raleeya tashi kije kicewa Goggo Dada ta dawo nan ɗakina mu zauna tare, duk ai zai ishe mu, abu ba yaro ba ba komai ba." "To" Raleeya tafaɗa tana me miƙewa tsaye. Saifuddeen da tun shigowar Ummin yake kallon yanayin yanda bakinta ke motsi, hakan yasa shi danna madannanin wheelchair ɗinsa ya nufi hanyar fita daga falon, dama tuntuni wannan damar yake jira shiyasa koda suka kammala dinner bai tafi ba. Kai tsaye ɓangarensa ya nufa, yana shiga kuwa ya zaro wayarsa, text ya turawa Hayatuddeen akan cewar "Yazo yana son ganinsa." Hayatuddeen na zaune yaga saƙon Hamman nasa, tsam ya miƙe ya fice daga cikin falon, kai tsaye sashin Hamman nasa ya nufa. Anan falo ya iske Saifuddeen ɗin, yana shan Maltina, ƙarasowa cikin falon yayi tare da cewa. "Hamma gani." Kai ya jinjina tare da sanya hannunsa acikin al'jihun rigarsa ya zaro key, miƙawa Hayatuddeen key ɗin yayi, nan cikin body language ɗinsa yace. "Ka kaiwa Zaleeha, ta dawo ɗakinta tabarwa Goggo Dada wannan ɗakin." Yanayin yanda yayi maganan yana wani basarwa, shine abun daya sanya Hayatuddeen yaji wani irin dariya ta kamasa, amma sai ya share, da murna ya karɓi key ɗin, tare da cewa. "To zan kai mata." juyarda akalan kekensa yayi ya nufi bedroom, Hayatuddeen kuwa binsa yayi da kallo yana murmushi, yana ganin ya shige ɗakin, yayi ɗan tsalle tare da cewa. "Yess yanzu itama Adda Zaleeha zata koma ɗakinta." juyawa yayi cikin sauri ya fita daga falon. Anan falon Ummi kuwa har yanzu suna nan a zazzaune, gefe kuwa ga Ameena da zuciyarta keta raya mata abubuwa iri iri. Da murna Hayatuddeen ya shigo cikin falon, yana ɗan rawa, harda su shaku shaku, baki Ummi dasu Raleeya suka buɗe suna kallonsa, da mamaki Ummi tace. "Kai Hayatuddeen lafiyanka kuwa?." Murmushi mai ɗauke da dariya yayi, tare da miƙowa Raleeya hannu, cikin jin daɗi yace. "Adda Raleeya maza maza taso muyi rakiya ." Hannunsa ya miƙa ya karɓi Adeel dake kan cinyar Zaleehan, ɗaga Adeel ɗin yayi sama tare da cewa. "Adeel kaima kayi murna yau Amminka ta zama zata bar mana side ɗin Umminmu ta koma can ɗakinta." Ya faɗi maganar yana me cilla Adeel ɗin sama. Jin abunda Hayatuddeen ɗin ke faɗa yasa Ummi sakin murmushi tare dayin ƙwafa, dama ai ita ta jima dagane shirin Saifuddeen ɗin, kuma zatayi maganinsa ne. Ameena kuwa kalaman Hayatuddeen ɗinne suka zuciyarta tsananta bugawa, wani irin fitinannen kishin Zaleehan ne ya taso mata, take taji komai na duniya ya daina yi mata daɗi, ashe duk adacan baya ba kishi takeji ba haukan banzane kawai takeyi, ayanzu yanda ƙirji da zuciyarta ke tafasa, nanne ta tabbatar da cewar kishi take, idanunta ne suka kawo ruwa, sakamakon wani irin ɗaci da takeji azuciyarta, lokaci ɗaya ta shiga cikin yanayi marar daɗi, miƙewa tayi jiki asanyaye ta fice daga cikin falon. Tana fita Ummi ta gyara zama tare da cewa. "Babu inda Zaleeha zataje, ai ɗakina zai ishemu nida Goggo Dada'n, saboda haka bama sai taje ko ina ba." Goggo Dada wanda duk taji abun da suke faɗa ne ta fito daga cikin ɗakin, cikin kulawa tace. "A'a Ya zakiyi haka kuma, ki hana yarinya komawa ɗakinta, ai baiyi ba." Murmushi Ummi tayi tare da cewa. "A'a Goggo Dada barta dai anan ɗin". Kai Goggo Dada ta girgiza tare da cewa. "Sam baza'ayi haka ina gidan nan ba, ki barta ta koma ɗakinta, ai babu ma inda zatafi sakewa kamar ɗakin aurenta." Murmushi Ummi tayi, tare da cewa. "Shikenan, Zaleeha tashi ki koma sashinki, Allah ya muku al'barka." Wani irin kunyane ya lulluɓe Zaleeha'n, hakan yasa tayi ƙasa da kanta, Raleeya ne ta miƙe cikin jin daɗi tace. "Yauwa Aunty Zaleeha tashi mu rakaki." Akunyace ta tashi tsaye, Raleeya ne ta kama hannunta, Hayatuddeen na biye dasu abaya, kafaɗansa rungume da Adeel, suka fice daga cikin falon, Goggo Dada da Ummi suka bisu da kallo suna murmushi. Ummi kam bataso ace Zaleehan ta koma cikin sauri ba, so tayi ta bashi wahala sosai akan komawar Zaleeha'n, tun da dai da farko babu yanda batayi dashi ba akan ya kawo key ɗin ɗakin Zaleehan ta koma, amma yaƙi, sai yanzu daya ga dama zai zo ya wani ce ta koma. Su kuwa koda suka ƙarasa part ɗin, Hayatuddeen ne ya sanya key ya buɗe ƙofar falon, nan suka shiga, Raleeya harda sata ta shiga da bismillah da kuma ƙafar dama, saikace wata sabuwar amarya, har cikin bedroom ɗinta suka wuce, wanda ko ina keta tashin ƙamshin airfreshener, anan kan gado Zaleehan ta zauna, tare da war ware gyalen da ta yane kanta dashi. Wayar Raleeya ne ta fara ƙara alaman shigowar kira, koda ta duba ganin sunan Raihana yasa ta ɗaga wayan tare da karawa akan kunnenta, bayan sun gaisane Raihana da yaji kaman Raleeyan na cikin farinciki tace. "Mekuka samu ne haka keda Hayatuddeen, kuketa nishaɗi, daga nan mafa ina iya jiyo muryar Hayatuddeen." Murmushi Raleeya tayi tare da cewa. "Mun rako Adda Zaleeha ne yau ta dawowa ɗakinta." tsuka Raihana tayi daga can cikin wayar tace. "Aikin banza akan wannan shine kuketa wani farinciki? ai ni wallahi tunda tace batason Hamma nima banasonta." ɗan murmushin yaƙe Raleeya tayi, dan batason kowa ya fahimci abun da Raihanan ke cewa. Dai-dai lokacin kuwa Zaleeha ta ɗago kai ta kalli Raleeya, cikin sanyin muryarta tace. "Raihana ce ko?". Gyaɗa mata kai Raliya tayi alamar eh itace. Cikin yanayin sanyi tace. "Kice ina gaishe ta." Murmushi Raleeya tayi, take kuwa tace wa Raihana'n. "Aunty Zaleeha tace na gaisheki." A gyatsine Raihana tace. "Banaso ta riƙe gaisuwarta." jin hakanne yasa Raleeya ta fice daga cikin ɗakin, falo ta koma, nan cikin son nusar da ƴar uwarta ta tace. "Wallahi kedai Raihana kincika masifa, kuma kidaina ganin baƙin Zaleeha, wallahi tana da daɗin zama, saidai idan baki fahimceta ba, kuma koda da tace batason Hamma Saifuddeen me ta taɓayi mana? tana zaune damu lafiya, sannan kuma bata taɓa raihana mana mahaifiyar muba, kullum biyayya ne atsakaninta da Ummi, aganina ai hakan baizama abun da zaisa muƙita ba koda albarkacin hallacin mahaifinta." Baki Raihana ta taɓe tare da cewa. "Ohon muku dai, nidama naƙiraki ne dan naga tunjiya bamu gaisa ba, sai anjima ki gaishemin da Ummi na da autanta da Hamma na." da haka sukayi sallama, Raleeya ta koma ɗakin Zaleeha'n. Sun ɗan taɓa hira kafun suka tafi, inda suka barta ita da Adeel. Ummi kuwa da Goggo Dada ɗakin Ummi suka shiga suna hirarsu ta manya kuma ƴan uwa suna cikin hirane kiran Adda Rahma ya shiga wayar Ummi, da sauri ta ɗaga bayan sun gaisa ne Adda Rahma tace. "Ummi ni kam yaushe ne Saifuddeen zai koma India a yaga likita?". Ajiyan zuciya Ummi taja tare da cewa. "Uhummm ke dai barni da Baba na Rahma, kingafa wancan karonma da kyar na sashi yaje bayan aurenshi da Ameena da wata shida kinga lokacinma watanshi takwas da dawowa kafin yaje, wai shi ya worke me sai yayi ta bin kan likitoci ai haka Allah ke son ganinsa kuma shi yama worke gara harda cemin shifa lafiyar shi lau." Cikin sanyi Adda Rahma tace. "To Amman kuma ai in anyi dace zai sake miƙewa tsaye fa suke cewa. Ni yanzu nema Ya Adnan ke cemin Dr Acash prasat ya mishi mgna kan cewa, date ɗin kowanshi fa yayi har ya ɗan wuce, shine yake cemin in gaya miki kisashi ya fara shirin zuwa". Ɗan gajeren tsaki Ummi taja tare da cewa. "Bazai yarda bafa, mu barshi kawai tunda yaji ya gani yace shi ya godewa Allah a hakanma tunda yana iya yiwa kanshi komai, in na matsa mishima sai dai yaje don dole badon yasoba, shiyasa ni kuma ban fiye son takurashi ba." Kai Adda Rahma ta ɗan jinjina tare da cewa. "Uhum lfy yakeji ai in yaji ciwo ba sai ance ya komaba, Allah ya ƙara bashi lfy, dan na lura shi jin wannan kujerun nasa yakeyi kamar kujerun mulki". Dariya suka ɗanyi kana Ummi tace. "Ga Goggo Dadanku ma tazo". Cikin kula tace. "Bata waya". Cikin kula ta gaita kana ta ƙara da cewa. "Goggo Dada zamu kwana biyu ko?". Dariya tayi tare da cewa. "Tab ai gobema da safe zan koma". Cikin shaƙuwarsu tace. "Ayyah dai Goggo Dada zaki idoni ko?". Murmushi tayi tare da cewa. "Eh kafin in tafi zansa Ahmad ya kawomin". cikin happy tace. "To sai kinzo". Da haka sukayi sallama, sukuma sukaci gaba da hirarsu. Acan ɓangaren Saifuddeen kuwa ya riga daya gama tsara yanda rayuwar gidan nasa zata kasance, inda ya rabawa kowaccensu kwana bibbiyu, duk kuwa randa yake ɗakin ɗaya daga cikinsu ne kedashi, to zai na zuwa part ɗin wanda ya kasance ba itace ke dashi ba yayi mata saida safe. Yanzuma fitowansa daga wanka kenan, bayan ya gama shirya kansa tsab cikin wasu haɗaɗɗun kayan bacci, masu kalan pink da ɗigo ɗigon fari, sosai kayan sukayi masa masifar kyau, tare da bayyana zallan hasken fatarsa, kasancewar wandon irin mai tsayawa aɗan gaba da guiwa ɗinnan ne kaɗan, sai kuma rigar dake da hannu wanda shima ta wuce guiwa, sosai kayan sukai masa kyau, ga lallausan sajensa daya kwanta lub-lub akan fuskarsa. Kaitsaye ɗakin Ameena ya nufa, danyi mata saida safe kaman yanda ya tsara. Yana shiga cikin falon nata yaji shiru kaman babu kowa acikin sashin, kansa tsaye ya nufi ɗakinta, dan yana da yaƙinin cewa zai sameta acan, yana shiga kuwa ya hangota kwance akan gado tana kuka sosai harda sheshsheƙa, ɗan zuba mata idanu yayi yana nazartanta, sosai take kuka tamkar wacce akayiwa mutuwa, idonshi ya rumtse tare da sauƙe ajiyan zuciya sannan ya tura kekensa a hankali ya ƙarasa har gaban gadon nata, cikin kula dan yasan zafin kishi ke ɗawainiya da zuciyarta hannunsa yasa yaɗan ɗagota zaune, hakan yasa suka fuskanci juna, hannunta ya kama yana kallonta tare da nazartanta, ita kuwa Ameena ganin haka yasa ta ƙara sautin kukanta, tana mejin wani irin zafi aranta, shikenan yanzu tanaji tana gani, zaije ya kwana da wata ba ita ba, sosai takejin kishinsa gani take kamar yafi kullum kyau da ƙamshi sai take ganin kamar kolliya na musamman ma yayi dan waccar hegiyar matar tasa. Shi kuwa Saifuddeen Gaba ɗaya ya gama karantar abundake damunta, yasan ƙwarai kishinsa takeji cikin sanyi da kulawa. Ya zaro handkerchief daga al'jihunsa tare da miƙa mata, bazata iya amsa ba saboda kuka take sosai, hannunsa yakai kan fuskarta ya ɗan share mata hawayen nata, cikin body language ɗinsa ya tambayeta meya faru? kanta ta girgiza cikin muryan kuka tace. "Nima bansani ba, bansan me nake ji ba,amman inaji kamar zan mutu ji nake kamar zuciyata zata fashe. Dan Allah Ka tayani da addu'a Allah ya sauƙaƙa min abun da nakeji." Idanunsa yaɗan lumshe tare da sanya hannunsa ya ɗan shafi kanta, in body language ɗinsa yayi mata alaman cewa ta nutsu ta kwanta tayi bacci, madadin ta kwanta ɗin kawai sai ta faɗa jikinshi ta ruggumeshi tsam kamar mai tsoron kada a kwace mata shi, Shiru yayi tare da lumshe idonshi, Allah ya sani shi dai fatanshi da burinshi ya zama adali a garesu baki ɗayansu, dan haka ya ɗan fara ɗan bubbuga bayanta, jin tana sauƙe ajiyan zuciya ne yasa ya kwantar da ita sannan ya mata alamun ina Adeel. murya na rawa tace yana cikin gida, jin haka yasa yace to bari yaje ya karɓo matashi. Kaitsaye part ɗin Ummi ya nufa dan karɓo Adeel, koda yaje kuwa harya samu sun shiga, ƙofar Ummi ya ƙwanƙwasa, tana fitowa tace. "Lafiya kuwa Saifuddeen?" Kansa ya jinjina cikin body language ɗinsa, yayi mata alama kan cewar. "Adeel yazo ɗauka." Da ɗan mamaki Ummi tace. "Ai Adeel baya nan, ka duba wajen mamansa baya can." Kansa ya jinjina alaman "Eh." Hayatuddeen dake cikin ɗakinsa ne ya leƙo, domin yaji suna zancen, duban Hamman nasa yayi tare da cewa. "Adeel fa yana wajen Adda Zaleeha." Kansa ya jinjina sannan ya juya ya bar part ɗin. Kaitsaye ɓangaren Zaleehan ya nufa, cikin nutsuwa ya shigo cikin falon nata dake ta tashin ƙamshi, komai dake cikin falon tsab yake, banda kuma ƙaran AC ba abun dake tashi acikin falon, cikin nutsuwa yake tura wheelchair ɗinsa har ya ƙarasa bakin ƙofar bedroom ɗinta. Acan cikin ɗakin kuwa, ganin Adeel yayi bacci ne yasa Zaleeha rage kayan jikinta ta shige toilet, wanka tayi tare da shafa wani irin fitinannen turaren ajikinta, wanda yake musamman dama na jiki ne, idan anyi wanka kuma ake shafawa, wani ɗan fingil ɗin rigan bacci ne ta sska wanda ko cinyoyinta bai gama rufewa ba ta ɗaura daga sama kuma yan siraran hannu yake dashi kana gaban rigar yara-yara mai bakin lace, kasan cewar rigar baƙace yasa farar fatarta ta baiyana ras cikin huji-hujin gaban rigar, yayinda dogon gashin kanta wanda yajiƙe da ruwa, ya kwanta lub akan bayanta da kuma wuyanta, Towel ɗin data cirene ta meda cikin bathroom cikin nutsuwa ta fito daga toilet ɗin, yayinda jikinta ke fidda sihirtaccen ƙamshi. Shikuwa Saifuddeen ahankali ya ɗaura hannunsa akan jikin handle ɗin ƙofar, tare da murzawa take ƙofar ta buɗe, cikin yanayinsa na nutsuwa ya tura kansa cikin ɗakin, dai-dai lokacin kuwa Zaleeha na tsaye agaban gado gaba ɗaya rigar ɗin ya lafe daga jikinta, har hakan yasa naked skin ɗin bayanta ya bayyana, ƙoƙarin tattare gashin kanta takeyi da niyar tubkeshi take daga bajewa da yayi a bayanta, jin motsin mutum abayanta yasata juyowa amatuƙar razane. Da sauri ta saki gashin kana jiki na rawa ta zauna bakin gadon yayinda Adeel ke bayan ta, shi kuwa Saifuddeen kauda idonshi yayi daga kanta, yana mai jin yadda zuciyarshi ke lugude tara-tara, a hankali yake sarrafa keken nashi har ya isa gab da ita, ita kuwa Zaleeha sai mammatse cinyoyinta takeyi dasa hannu tanata jawo rigar wai a nufinta ya rufe mata cinyoyinta,yayinda janshi da takeyi kuma yasa gaba ɗaya hannayen rigar suka ɗan buɗe hakan yasa rigar ta zama har rabin ƙirjinta na woje, ganin ya iso gab da itane yasa tayi ƙasa da kanta hannayenta ta haɗe wuri ɗaya tana wasa da yatsun hannunta, ida nunta kuwa na kan fararen ƙafafunshi da gargasa ya musu ƙawanya, shi kuwa Saifuddeen ganin yadda ta sunkuyar da kantane yasashi ɗago kanshi ya kalli samanta, wani irin mayatacce ajiyan zuciya ya fizgo da ƙarfi, ganin gaba ɗaya surar ƙirjinta a baiyane wani irin maganaɗisu mayen ƙarfe ke fuzgar jiki da zuciyarshi, a hankali ya sarrafa kekenshi ya ƙara matsota da niyar sa hannu ya ɗauki Adeel dake ta baccinsa. Ita kuwa Zaleeha ganin yadda ya motsota yayi masifar firgitata, gaba ɗaya tsoronshi ya rufeta cikin ƙanƙanin lokaci sai ga jikinta ya ɗauki ɓari tamkar mazari, ganin yadda jikinta ke karkarwa yasashi meda hankalinshi kanta, shiru yayi yana nazartan yanayinta a fili yake ganin tsananin tsoronshi daya ziyar ceta. fuskantar ta yayi da kyau, cikin tsare girar sama data ƙasa, yasa hannu dai-dai kan ƙirjinta da yake a baiyane bata san a garin son kare cinyoyinta ta fiddo da rabin breast ɗinta ba, yatsunshi biyu yasa ya kamo bakin rigar,wanda hakan ya tsananta ɓarin da jikin Zaleeha keyi cikin tsanyi da tsoro ta ɗan ɗango kanta wanda tuni idanunta sun ciccika da hawaye, rau-rau tayi da idanun sai ga hawaye na shatata, sosai ta bashi dariya ace mutun tsoro kamar farar kura ko da can da takeda tsiwama matsoraciyace bare yanzu da duk ta sauya, murmushi yayi a zuciya kana a fili kuma ido ya jujjuya mata alamun. "Gyara miki rigar zanyi". buɗe wuyan rigar yayi tare dasa hannunshi ɗaya cikin rigar breast ɗinta na hannun hagu yasa hannunshi ya rumtse, wani irin tsalle mai haɗe da zamura Zaleeha tayi kana ta zazzaro idanunta kab ta fiddasu woje, yunƙura tayi da niyar zatayi tsalle ta koma ƙarshen gadon, sai kuma taji ya fizgota ta faɗa kanshi ta baya, wani zazzafan ajiyan zuciya ya fizga da azaban ƙarfi, hannu ɗaya yasa ya zagayo cikinta, kana ya ɗaura haɓar shi kan kafaɗanta hancinshi ya manna da wuyanta, cikin sanyi ya kuma maida hannunshi cikin rigar tata, wani irin rawa da mazari jikinsu ya fara a tare, wani irin karkarwa jikin Zaleeha keyi tamkar mazari rumtse idanunta tayi da azaban ƙarfi jin yadda ya cika hannunshi da Caɓɓullenta, shi kuwa Saifuddeen tagwayen ajiyan zuciya yan ur'uku yake sauƙewa, rigar tata ya gara mata yadda breast ɗin nata sukayi cib-cib da ƙoƙon da akayi a cikin rigar, jin ya kuma maida hannunshin kan breast ɗinta na dama ne yasata saka hannu ta kama hannunshi tana mai jujjuya mishi kai, bai wani bi ta kantaba, saida ya gyara zaman rigar yatsunshi biyu ya haɗe ya ɗan murza bakin caɓɓullen nata sannan ya janye hannunshin daga cikin rigar, ai tamkar ta samu tsira a gaban damisa ne haka ta koma dungun gadon ta dugungune wuri ɗaya. Shi kuwa baki ya taɓe tare dasa hannu ya ɗauki Adeel kana ya juya ya fita, Kai tsaye cikin falonshi yabi ya ɓula ta falon Ameena bedroom nata ya wuce, yadda ya barta haka ya sameta har yanzu kuka takeyi kusa da ita yazo ya kontar da Adeel kana yasa hannunshi ya shafi fuskarta, ita kuwa Ameena jin baƙon ƙashin a jikinshi ne yasa tayi wani irin.....! Littafina na kuɗine biya ɗarinki uku kacal ki karanta ba tare da haƙin kowa a kankiba, in kina buƙata turo min katin mtn na ɗari 300 kacal ta wannan no ɗin 09097853276 ko kimin transfer ta asusuna na 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. [13/09, 11:44 am] +234 706 370 3964: Sbpejddwl Cikin tsananin ruɗani da firgici Ummi ta ɗago kanta, ta kalli Raliya, cikin sauri tace. "Raliya bani ruwa na yayyafa mata maza-maza bani da sauri-sauri, kiyi sauri mana." Cikin sauri jiki na rawa Raliya ta nufi, fridge ɗin dake cikin falon, goran ruwa ta ɗauko, saboda tsabar sauri kuwa har tana haɗawa da tuntuɓe. Ummi ne ta karɓi goran ruwan, jiki na rawa ta ɓalle murfin tare da zuba ruwan ahannunta, ta watsa a fuskar Zaleeha, ko motsi batayi ba bare su saka ran farfaɗowanta, ganin haka yasa Ummi sake watsa mata wani ruwan, nan ma shiru, babu alaman cewa numfashinta zai dawo jikinta, hakanne yasa arikice Ummi ta ɗago da kanta ta kalli Adda Rahama, wanda itama gaba ɗaya ta gama tsorata da sha'anin Zaleehan, sake ɗebo ruwan Ummi tayi akaro na uku ta watsa da ƙarfi akan fuskar Zaleeha'n, minti ɗaya kacal taja wani irin ajiyar zuciya me ƙarfin gaske, wanda hakanne yasa Ummi dasu Adda Rahama wanda suke amugun tsorace suka sauƙe wasu tagwayen ajiyar zuciya masu nauyi. Batare da ta buɗe idanunta ba, sheshsheƙan kukanta ya soma tashi, kanta dake matuƙar sarawa da wani irin matsanancin ciwo ta shiga jujjuyawa tare dasa hannu ta riƙe kan, lokaci guda ta fashe da wani irin kuka mai tsuma zuciya, hannu Ummi tasa ta tallafota, cikin kulawa tashiga shafa bayanta, jinta ajikin Ummi yasa tasake jin wani irin fitinannen kukan tausayawa rayuwarta ya taso mata, hakan yasa ƙam ta rungume Ummin tana kuka sosai, kuka take mai tsananin zafi da gigita, kukane irin mai ɗauke da tsananin dana sani, haɗi da zallan na dama, kukane me ɗauke da zallan baƙincikin rayuwa, haka zalika kukane dake bayyana, gaskiyar abun dake cikin rai da zuciyarta, sannan kuma yake bayyana zallan tashin hankalinta. Cikin matsanancin tausayinta Adda Rahama ta miƙe tsaye, kaitsaye gaban fridge ta nufa, goran ruwa me ɗan sanyi ta ɗauko, hannu tasa taɗan dafa kafaɗan Zaleeha'n, wanda har yanzu take nan a jikin Ummi, kuka take sosai kamar ranta zai fita. Asanyaye Adda Rahama tace. "Kukan ya isa haka Zaleeha, dubi yanda jikinki duk ya ɗauki zafi jau, zakije kisawa kanki wani ciwon, kisha ruwa ko abun zai ɗanyi miki sauƙi." Kai Ummi ta jinjina cike da tausayin Zaleehan ta karɓi goran ruwan, ɗago Zaleehan tayi tare da cewa. "Karɓi ruwa kisha Zaleeha nasan zakiji sanyi acikin rai da zuciyarki, sannan kada ki manta kuka baya maganin komai, ki ya waita yin addu'a, hakan zaisa kiji sanyi acikin ranki, yanzu dai kidaina wannan kukan, karɓi ruwa kisha kinji." Kanta ta shiga girgizawa, take kuma numfashinta ya soma wani irin fusga kaman zai ɗauke, sosai jikinta ke ɓari, kukan ta shigayi kaman zata shiɗe, gefe guda kuwa ga wani irin masifaffen ciwon kai da yasa takejin kaman kanta zai rabe gida biyu. Ganin haka ne yasa Ummi ta kamo kafaɗunta, soma jijjigata tayi, hankali amatuƙar tashe tace. "Kinutsu Zaleeha, ki dawo cikin hayyacinki, kidaina wannan kukan, Insha Allahu Baba Malam zai yafe miki, dan Allah ki daina wannnan kukan kinji." Ummi tafaɗi maganar, hawayen tausayin Zaleehan na sauƙa daga cikin idonta, sosai take matsanancin jin tausayin Zaleeha'n, ganin haka ne yasa Raleeya komawa gefe itama ta fashe da wani irin kuka, sosai takejin tausayin Zaleeha'n, saboda ba' a iya matar ɗan uwa kaɗai ta ɗauki Zaleehan ba, tana jintane kamar ƴar uwarta ta jini. Kana tasan zafi da ƙuna da ciwo da ƙuncin zuciyar da mutun keji lokacin daya rasa ɗan uwanshi, domin har yau in begen Ya Nuruddeen ɗinsu ya dawo musu kuka sukeyi koda hotonsa suka gani, shiyasa takeji tausayi Zaleeha. Gaba ɗaya falon ya ɗauki shiru babu abun da ke tashi, sai sheshsheƙan kukan Raliya dana Zaleeha, wanda kuma takeyinsa cikin fitar hayyaci, duban Raleeya Ummi tayi, cikin sanyin murya tace. "Haba Raleeya ya kukeso inyine kunsan bana son kukanku, madadin ki lallasarmin ita sai kema ki tasata gaba kuna kuka ya kukeso inyi. Maza tashi ki haɗo mata tea me kauri tasha, dan nasan duk yau bataci komai ba." Miƙewa tsaye Raleeya tayi tare da share hawayen dake kan fuskarta, kai tsaye ta wuce kitchine don haɗawa Zaleehan tea kaman yanda Ummi ta buƙata. Ummi kuwa hannun Zaleehan ta kamo, tare da miƙar da ita, kaitsaye ta jata zuwa bedroom ɗinta, Adda Rahama wanda itama gaba ɗaya zuciyarta ta gama karyewa, ta rufa musu baya. Akan gado Ummi ta zaunar da Zaleeha'n, tare da kamo hannuwanta, ta riƙe, cikin halin tausayawa tace. "Kuka bashida amfani, sannan kuma baya magance damuwa, ki riƙa faɗin kalmar Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un, insha Allah zakiji sauƙi acikin zuciyarki." Cikin sheshsheƙan kuka ta jinjina kanta, ahankali ta soma motsa laɓɓanta wanda sukayi mata nauyi, so take ta furta kalman, amma harshenta rawa yake, kamar yanda duka ilahirin jikinta ke rawa. Ganin haka ne yasa Ummi soma faɗin kalman abakinta, take kuwa ta amsa, nan ta jingina kanta da cinyar Ummi tana faɗin 'Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un." tana magananne cikin matsanancin kuka da rawan murya. Dai-dai nan Raleeya ta shigo hannunta ɗauke da cup ɗin tea. Hannu Ummi tasa ta amshi cup ɗin, ɗan ɗago Zaleehan tayi, cikin kulawa tace. "Tashi kisha kinji, nasan ayanda kike ɗinnan, koda kika je gidan nakuma bakici komai ba." Cikin kuka ta girgiza kanta, don batajin akwai wani abu aduniya da take buƙata, batajin cewa zata iya sanya wani abu abakinta yayi mata daɗi, matuƙar kuwa Baba Malam bai yefe mata ba, yafiyar Baba Malam shi kawai take buƙata ayanzu da yafiyar wandake matsayin mijinta. Cikin muryarta dake rawa haɗi da sarƙewa tace. "Ummi bazan iya shaba, banason komai, bana sha'awar komai ayanzu idan ba yafiyar Baba Malam ba, dan Allah Ummi ki roƙeshi ya yafemin." Hawayene suka kuma cika idanun Ummi, amma saita shanye su, sam bata bari sun fito kowa ya gani ba, sake tallafo Zaleehan tayi, cikin sanyi, da lalllami tace. "Insha Allah Baba Malam zai yafe miki, ki kwantar da hankalinki kinji, yanzu kiyi haƙuri kisha ko kaɗanne, kinga shima zai taimaka sosai wajen ɗan baki ƙarfin jiki, gashi kuma naji jikin naki ma ya ɗauki zafi jau kamar wuta, buɗe baki kisha ko kurɓi biyune, yafi ace bakici komai ba." Ummi ta ƙare maganar cikin kulawa. Haƙiƙa Ummi nada matuƙar daraja da ƙima a idanunta, saboda haka batajin akowani yanayi take ciki zata iya yi mata musu, ganin ta buɗe baki ne, yasa Ummi da kanta ta shiga bata tea ɗin abaki, kurɓan farko da tayi haka taji tea ɗin kaman an surkashi da maɗaci, sam babu wani ɗanɗano acikinsa, wanda kuma ta tabbatar cewa rashin ɗanɗanon daga bakinta ne, bawai daga tea ɗin ba, kurɓa uku kawai tayiwa shayin ta kauda kanta gefe, cikin sanyin murya hawaye na zuba tace. "Ummi na ƙoshi". Gyada mata kai Ummi tayi, ita kuma zamewa tayi ta kwanta luf akan gadon Ummi, cikin sanyi take faɗin kalman "Innalillahi wa'inna Ilaihirraju'un." tana faɗi kana tana sakin sheshsheƙan kuka, Ummi kuwa ahankali take shafa lallausar sumar kanta, wanda gaba ɗaya ya baje akan pillow'n da ta ɗaura kanta akai, ko mintuna goma ba'a rufa ba kuwa bacci ya ɗauketa, wanda dagani kasan na dole ne, don ko acikin bacci'n sheshsheƙan kuka kawai take saki. Jigum haka Ummi da Adda Rahama suka zauna, tare da sakata gaba, sosai sukejin tausayinta, lokaci ɗaya gaba ɗaya ta rame ta fita hayyacinta, idanunta sun kumbura kamar wanda ta shekara guda tana kuka, wani abun mamakin da suka gani kuwa, shine har yanzu bacci take, amma kuma hawaye ne kebin gefen fuskarta, kamar ruwa, sai faman sakin sheshsheƙa take, ita dai Ummi al'amarin Zaleeha na matuƙar bata tausayi, sannan kuma zuciyarta me raunice. Can Ɓangaren Saifuddeen kuwa, tunda yabar falon na Ummi, kaitsaye side ɗinsa ya nufa, ɗakinsa ya wuce yayi kwanciyarsa, koda yaga lokacin sallan azahar yayi, banɗaki ya shiga tare da ɗauro alwala. Koda yaje masallaci ana idar da sallah, baiwani ɓata lokaci ba ya kamo hanyar gida. kaitsaye ɓangaren Ummin sa ya nufa, dan kuwa atunaninsa zuwa yanzun Zaleehan ta jima da komawa inda ta fito, ganin babu kowa acikin falon ne yasa shi nufar ɗakin Ummi'n, koda ya ƙarasa jikin ƙofar hannunsa yasa ya ɗan bubbuga ƙofar, Ummi da Adda Rahama wanda suke zaune sun saka Zaleehan agaba, sam aransu basu kawo cewa shi ne ke bugun ƙofar ba, atunaninsu Hayatuddeen ne ko kuma Raleeya, ataƙaice Ummi ta bada izinin shigowa. Shikuwa Saifuddeen ganin ba'abuɗe masa kofar ba, ya sashi jan handle ɗin ƙofar ahankali ya tura ta ciki, cikin nutsuwa ya turo kekensa zuwa cikin ɗakin, ganin su Ummi zaune akan gado jigum-jigum ya sashi ƙarasowa cikin ɗakin, daf daya kusa iso Ummin nasa ne, idanunsa suka sauƙa akan Zaleeha, dake bacci tana sakin sheshsheƙan kuka, ɗan zaro idanunsa waje yayi da alaman mamaki, dan duk atunaninsa bata gidan. harzuwa yanzu idanunta basu daina zubar da hawaye ba, kansa ya kawar gefe tare da taɓe bakinsa. Adda Rahama ne ta dubeshi, cikin sanyi da matuƙar tausayi tace. "Saifuddeen yarinyar nan tana da matsananciyar damuwa, baƙinciki ya mata yawa, wallahi tausayinta nakeji, ka duba fa kaga, lokaci ɗaya tafige ta fita hayyacinta, bata da wani abunyi sai kuka kowa nata ya juya mata baya." Fuska ya ya mutsa tare da sake taɓe bakinsa, bata damu da yanayin yanda taga fuskar tasa ba, ta sake cewa. "Yanzu ya za'ayi da ita kenan? kuma ma naji jikinta da zafi sosai, kodai zaka ƙira Abban su Faruq ne yazo ya duba ta." Cikin halin ko inkula ya ɗage kafaɗunsa sama, alaman. "Shifa babu ruwansa da duk wani abu daya shafeta." Baki Adda Rahama ta saki tana kallonsa, dan kuwa koda wasa bata taɓa tunanin zaiyi fushi da Zaleehan har haka ba, tunda yake a duniya bai taɓa nuna ƙulafacinsa kan komaiba sai a kanta. Shikuwa Saifuddeen ganin irin duban da Umminsa keyi masa ne,ya sashi murza wheelchair ɗinsa, kai tsaye ya fice daga cikin ɗakin, ko kallon inda Zaleehan ke kwance bai sake yi ba. Ganin ya fita ne yasa Ummi sakin ajiyar zuciya tare da lumshe idanunta, hannunta takai inda ta shiga ɗan jijjiga Zaleeha'n. Ahankali taɗan buɗe idanunta wanda suka ƙanƙance saboda tsabar kuka, da wani irin firgici haɗi da tsananin tsoro ta tashi, ɗan lumshe idanunta tayi, take mafarkin da tayi yanzun yadawo cikin tunaninta, kasancewar aɗan kwanciyan da tayi har tayi mafarki wai tasake komawa gidan Baba Malam, sannan awannan karon shi da kansa yaja hannunta ya fitar da ita daga gidan, tare dayin mummunan furuci agareta, inda yace. "Daga yau ta cire kanta daga sahun ƴaƴansa, ta manta da cewa shiɗin mahaifinta ne, saboda shi ya jima da manta cewa ya haifi wata ƴa me suna Zaleeha." wannan mafarkin shiya daɗa hautsuna tunaninta, kana ya ƙara mata fargaba me yawa acikin ranta, ƙoƙarin sakin wani sabon kuka take, Ummi ta dafa ta, cikin sanyi tace. "Dan Allah na roƙeki Zaleeha kibar kukan nan haka, kuka baya taɓa maganin damuwa, addu'a shi ya kamata kiyi ako da yaushe, nasan da cewa Baba Malam na fushi dake, amma hakan bawai yana nufin cewa bazai taɓa yafe miki ba ne. Insha Allah zai yafe miki, sannan kada ki manta Baba Malam yana fushi dake ne saboda kin baƙanta ransa, kin kuma ƙi yi masa biyyya, to idan har Baba Malam zaiyi fushi dake har haka, Allah' n daya halicceki kuma fa, wani irin fushi kike tunanin yakeyi dake? nasan kinsan da cewa fushin Allah Yana tare da fushin iyaye da miji, saboda haka kiyi sallah ki roƙi Allah gafara, sanadin haka sai kiga Allah yasa Baba Malam ya yafe miki, sannan kisawa zuciyarki nutsuwa, da salama, tashi maza kije ki ɗauro alwala kizo kiyi sallah." Ummi ta faɗi maganar cikin yanayin lallashi. cikin sheshsheƙa ta gyaɗa kanta, tare da soma yunƙurin tashi daga kan gadon, sai-dai gaba ɗaya babu ƙarfi ajikinta, Adda Rahama ne ta taimaka mata, ita ta kamata ta kaita har cikin bathroom. acikin toilet ɗin ma kuka take haka ta ɗauro alwala. Koda ta fito nan ta samu Ummi ta shumfuɗa mata darduma tare da aje mata sabon hijab, ganin bakowa acikin ɗakinne yasa, jiki asanyaye ta ƙarasa ta ɗauki hijab ɗin ta sanya, tare da tada sallah. Da ƙyar ƙafafunta suke iya ɗaukanta, saboda yanda takejin jikinta ba ƙarfi. Koda takai sujjadar ƙarshe na cikin sallan nata, fashewa tayi da wani irin kuka mai tsananin taɓa zucia, kuka take sosai tana me neman gafara awajen Allah, saida tayi kuka sosai har da shiɗewa kafun ta ɗago daga sujjadan, tana sallame sallan kuwa ta jingina bayanta da jikin gado. Ummi da tunɗazu ke tsaye abakin ƙofar shigowa duk wani kukan na Zaleeha akan kunnenta, hawayen da suka cika idanun ta ne suka samu daman gangarowa, saurin share hawayen nata tayi tare da ƙarasowa cikin ɗakin. Zama tayi tare da aje plate ɗin abincin dake hannunta, cikin sanyi ta ƙira sunan Zaleeha'n. Ɗago jajayen idanunta tayi ta kalli Umm'in, plate ɗin abincin Ummi ta turo mata gabanta, cikin kulawa tace. "Kukan ya isa haka, ki samu kici abinci." girgiza kanta tayi cikin muryarta dake rawa, haɗe da sarƙewa tace. "Bazan iyaba Ummi, bazan iya cin abinci ba, banajin daɗin bakina, komai na duniya baya min daɗi, inajin kamar ma babu yawu acikin bakina, banajin komai acikin zuciyata sai ƙunci da baƙincikin rayuwa, bana sha'awar komai yanzu aduniyata sai yafiyan Baba Malam da Hamma Saif, bazan taɓa iya cin abinci naji daɗinsa abakina ba harsai ranan da Baba Malam ya yafemin, zuciyata zafi takemin Ummi, Babana mafi soyuwa agareni yana fushi dani, Ummi Baba Malam bayason ganina, naje gidansa yasa Ya Habu ya koreni, ƴan uwana duk sun tsaneni, gashi ƴar uwata ta tafi tabarni, Adda Maryam ta bar duniya batare dana sake sanyata acikin idanuna ba, shikenan yanzu bani da wata Adda aduniya, Inama mutuwa ni ta ɗauka ba ita ba, inama da ace mutuwa zatamin gata wajen kusantani da ƴar uwata, bazan iya jure fushin Baba Malam akaina ba Ummi, nima mutuwa zanyi Ummi.....". Kasa ƙarasa maganan tayi, sakamakon kukan me tsananin ƙarfi da ya ƙwace mata, Ummi kanta kasa daurewa tayi, hakanne yasa ta jawo Zaleehan jikinta ta rungume. Jinta ajikin Ummi yasa ta ƙanƙame Ummin tana kukan fitar hayyaci, mai ɗauke da tsananin dana sanin abun da ta aikata a baya. Hawayene suka silalo daga cikin Idanun Hayatuddeen, wanda duk wani kalaman da Zaleehan ke faɗa, ya jisu raɗau akan kunnuwansa, dan yajima tsaye abakin ƙofar batare da sun san da zuwan sa ba, sosai jikinsa yayi sanyi, dajin kalaman nata, domin dama Raleeya ta faɗa masa cewa, Zaleehan har suma tayi ɗazu, shine Ummi ta ɗauketa takaita ɗakinta, jin cewa Adda Zaleehan na ɗakin Ummin ne yasashi nufo ɗakin, saboda halin ko inkula daya nuna mata ɗazu, yasan dole zataji ba daɗi acikin ranta. Ahankali ya shiga taka ƙafafunsa wanda sukayi masa nauyi, ƙarasawa inda suke yayi, tare da zubewa akan guiwowinsa, cikin wata irin murya dake fitar da tsananin rauninsa yace "Adda Zaleeha, meya sameki? meyasa kike kuka, dan Allah kibar kuka kinji." Jin sauƙar Muryar Hayatuddeen acikin kunnuwanta yasa, ta juyo da sauri, ganin shine kuwa yasa ta zare jikinta daga na Ummi, faɗawa jikin Hayatuddeen ɗin tayi, tare da sakin kukan da yafi wanda tayi abaya ciwo, dan jin Hayatuddeen takeyi tamkar Zakariyya. Shima Hayatuddeen ɗin kukane ya ƙwace masa, cikin kukan nata tace. "Hayatuddeen ya zanyi Baba Malam yayi fushi dani, haka Ya Ahmad ma da Aunty Lubna duk sunyi fushi dani, babu wani wanda yake saurara ta, basason ko ganina akusa dasu, Mamy ma fushi take dani, gashi Ya Ameenu ya zama abun tausayi, Adda Maryam ta tafi ta barmu." Ɗagowa daga jikinsa tayi tare da kamo hannayensa, cikin kuka taci gaba da cewa. "Baba Malam yace kar na sake zuwa gidansa, hatta Ziyada ƙanwata ma fushi take dani, Zakariyya ma nasan adole yake kulani, Hayatuddeen ya zanyi? ina zansa rayuwata? kowa baya sona, kowa guduna yake, babu wasu wanda ke rarrashina sai su Ummi, inajin kamar zuciyata zata fashe, duk wani majinginan danake tinƙaho dashi ya ruguje, rayuwata tayi mini zafi, har inajin gwamma mutuwa ta da rayuwata." taƙare maganar tana me sake komawa ta raɓa jikinsa ta riƙesa ƙam, kuka kuwa yinshi take harda majina. Duk yanda yaso shanye kukansa kasawa yayi, hakan yasa ya sake rungumeta ya fashe da kuka, saida yayi kuka sosai sannan ahankali ya shiga shafa bayanta, cikin sanyin murya yace. "Kiyi haƙuri kinji Adda Zaleeha, ki daina kuka, idan duka mutanen duniya zasu ƙiki, ni da Zakariyya bazamu taɓa kinki ba, kiyi shiru kinji, nasan Baba Malam yayi fushi, amma zai yafe miki." Kai Ummi ta jinjina cikin son kwantar mata da hankali tace. "Ƙwarai kuwa Insha Allah Baba Malam zai yafe miki, yanzu dai ki samu kici abincin kinji." Cikin sheshsheƙan kuka tace. "Ummi bazan iya ci ba, ko tea ɗin ɗazu dana sha haka najisa kaman maɗaci, gaba ɗaya kaman yanda zuciyata take babu ɗanɗano acikinta, haka bakina ma, banajin daɗin komai." cikin tausayawa Ummi tace. "To akawo miki fresh milk kisha ko kaɗanne?" Batason yawaita yin musu da Ummi hakan yasa ta ɗan gyaɗa kanta, dai-dai lokacin kuwa Raleeya ta shigo, nan Ummi tace da ita, ta kawowa Zaleehan fresh milk. Babu ɓata lokaci kuwa takawo fresh milk ɗin me sanyi. Karɓan cup ɗin Hayatuddeen yayi, cike da tausayinta yace. "Adda Zaleeha, ki tashi kisha kinji." bazata iya janye jikinta daga garesa ba, saboda tanajin ya zame mata kamar majingina, hakan yasa ahankali taɗan ɗago kanta dake masifar sarawa, cikin kulawa Hayatuddeen ya shiga bata fresh milk ɗin abakinta, sam kwata kwata batajin daɗi ko ɗanɗano abakinta, jima take kamar magani take sha, kurɓo huɗu kawai tayi ta janye bakinta daga jikin ƙofin, har yanzu sheshsheƙan kuka take, gashi jikinta ya sake ɗaukan zafi sosai, komawa jikin Hayatuddeen ɗin tayi ta kwanta, tana ta faman fusgar numfashinta dake neman ƙwace wa. Ummi, Adda Rahama, Raleeya, har zuwa kan Hayatuddeen babu wanda ya gusa da ga kusa da ita, wani irin kulawa haɗi da tattali na musamman suke bata, sosai suke faɗa mata kalaman dazai kwantar mata da hankali.. Suna nan azaune har aka ƙirayi sallan la'asar, Ummi ne tace da Adda Rahama da kuma Raliya su shiga kitchine su ɗaura abinci, kasancewar tunda akayi rasuwa'n kullum sai sunkai abinci gidan su Zaleeha. Nandai Hayatuddeen ma ya tashi ya wuce massallaci, itama Zaleehan sallah tayi, nan kan carpet ta kwanta tana masassara saboda zazzafan zazzaɓin ya soma cin ƙarfinta. Su Adda Rahama kuwa suna kammala girkin, nan cikin wasu manyan food flask suka juye abincin. Kamar kullum dama Hayatuddeen da Raleeya ne ke kai abincin, to yau ɗin ma dai hakanne, ta kasance dan sune suka kai abincin, Hayatuddeen ne ke driving, kasancewar yanzu hannunsa yaɗan faɗa wajen iya tuƙin mota, saboda Khamis na koya masa tuƙin time to time, babu laifi kuma yaɗan iya. Koda suka ƙarasa gidan su Zaleehan bayan sun sake yi musu gaisuwa, Hayatuddeen ne ya kamo hannun Zakariyya da Imran ƙanin Ishaq wanda da Babansu yazo, zagawa sukayi wajen da babu yalwar mutane. ɗan karyar da wuya Hayatuddeen yayi, cikin sanyi haɗi da damuwar dake bayyane akan fuskarsa yace. "Zakariyya Adda Zaleeha taje gida bata da lafiya sosai, gaba ɗaya jikinta zafi kaman wuta, har suma tayi, dan Allah abawa Baba Malam haƙuri ya yafe mata, tana cikin matsanancin damuwa, kuka yazama tamkar abinci agareta." Idanun Zakariyya ne suka cicciko da ƙwallan tausayin ƴar uwartasa, ɗan lumshe idanunsa yayi, yana mejin tausayinsu su dukansu, tabbas yasan akwai ƙauna me zafi atsakaninsu, wanda koda ace babu auren Hamma Saifuddeen akan Zaleeha, idan Hayatuddeen yaganta cikin damuwa zai ji ƙanta, kuma gashi nan damuwa ta bayyana ƙarara akan fuskarsa, sunyi imani cewa duk wani damuwan ɗayansu nasune su duka. Cikin sanyi yasa hannu ya share hawayensa, muryarsa asanyaye yace. "Hayatuddeen nima bansan ya zanyi ba, Baba Malam yace. Bayason sake ganinta, yana fushi da ita sosai, kuma ta basa haƙuri ma yaƙi haƙura." Sosai jikin Hayatuddeen da Imran yayi sanyi, dole da addu'a kawai zasu taya ta, dan basu da wani zaɓin daya wuce hakan. Fitowar Adda Raleeya daga cikin gidan ne, yasa sukayi shiru da zancen, ƙarasowa wajen da su Zakariyyan suke tayi, ganinta yasa Hayatuddeen duban Zakariyya murya asanyaye yace. "Mu zamu wuce." Har bakin mota Zakariyya da Imran suka rakasu, saida yaga tafiyarsu sannan suka komawa cikin gida, zuciyarsa gaba ɗaya ba dadi, sosai tausayin Zaleehan ke damunsa. Koda su Hayatuddeen suka koma gida kuwa kai tsaye ɗakin Ummi suka wuce. Har yanzun Zaleeha na duƙunƙune waje ɗaya, gefenta Ummi da Adda Rahama ne zaune. Ƙarasowa cikin ɗakin Hayatuddeen yayi tare da zama akusa da ita, hannunta ya kamo, hakan yasa ta ɗago ta dubeshi da idanunta wanda sukai jajur, murmushi yaɗan ƙaƙalo akan fuskarsa, cikin kulawa yace. "Adda Zaleeha kukan ki ya kusa ƙarewa Insha Allah, Baba Malam zai yafe miki nan bada jimawa ba, kuma Ya Ahmad ma da kansa yace agaisheki." Zabura tayi tare da matsowa gab dashi, idanunta ta zuba masa, kansa ya jinjina mata alaman dagaske yake, idanunta ta lumshe, take kuma wasu sabin hawaye suka zubo mata, matsawa kusa dashi tayi tare da ɗaura kanta akan kafaɗansa, hannunsa ta riƙe ƙam tana sauƙe ajiyar zuciya. Ganin haka yasa su Ummi sakin ajiyar zuciya suma, dan gaba ɗayansu burinsu bai wuce ganinta cikin nutsuwa ba. Da misalin ƙarfe 6:20 pm Ameena tashigo cikin gidan, wanda dawowarta daga wajen aiki kenan, kai tsaye falon Ummi ta nufa bakinta ɗauke da sallama, saidai rashin ganin kowa acikin falon yasa taɗan shiga mamaki, saboda yawancin lokuta falon Ummin bai rabuwa dasu Raleeya ko kuma auta Hayatuddeen, gashi yau kuma falon shiru babu motsin kowa. Ganin haka yasa kaitsaye ta nufi ɗakin Ummi'n, hannunta riƙe da Adeel. Ƙwanƙwasa ƙofar ɗakin tayi, Adda Rahama dake zaune gefen Zaleehan ne ta bada izinin shigowa, nan ta tura ƙofar ɗakin ta shigo, bakinta ɗauke da sallama. Kusan dukansu ne suka amsa mata sallaman cikin kula, ƙarasowa cikin ɗakin tayi tana me mamakin ganin yanda suka taru su duka acikin ɗakin, cikin nutsuwa ta gaishe da Adda Rahama, amsa mata tayi tare dasa hannu ta karɓi Adeel, idanunta ne suka sauƙa akan kyakkyawar matashiyar budurwar dake zaune ta jingina jikinta dana Ummi, kanta kuwa na kan kafaɗan Hayatuddeen, wani irin bugawa taji ƙirjinta yayi, cikin nutsuwa tace. "Ummi sannu da gida." cikin kulawa da so Ummi tace. "Yauwa Aminatu sannu, ya wajen aikin naku?" Ummi tayi mata tambayar batare da ta ɗago kai ta kalleta ba, saboda gaba ɗaya hankalinta naga Zaleeha, magungunan zazzaɓin da Hayatuddeen ɗin ya seyo, shi take ƙoƙarin ɓallewa dan bawa Zaleehan tasha. Ƙurawa Zaleehan idanu Ameena tayi, cikin ranta tace. "Ina su Ummi suka samo wannan balarabiya'n?" Tabbas tasan Zaleeha a hoto sai dai ashema rage kyanta hoto keyi, tabbas ita kallon balarabiya tayiwa Zaleeha'n, saboda kwata-kwata yanayinta baiyi kama dana mutanen Nigeria ba, musamman idan akayi duba da yanda dogon gashin kanta ya kwanto har zuwa gadon bayanta, ga kuma farin fatarta wanda yake na musamman ne, bawai irin farin fatar nan bane da wasu ke mutane ke ƙarawa da mai, natural fari ne me kyau da ɗaukar hankali, uwa uba matsanancin kyawun da tagani atattare da Zaleeha'n. Cikin zuciyarta ta ƙara tambayar kanta, ko itaɗin wacece. Tunaninta ne ya katse alokacin da taji Ummi tace. "Zaleeha tashi kisha maganin kinji, nasan zuwa anjima kaɗan zafin zazzaɓin zai sauƙa." Wani irin luguden duka Ameena taji ƙirjinta nayi, cikin ranta ta maimaita sunan Zaleeha, take tunaninta ya bata cewa, itace Zaleeha matar Saifuddeen, ƙura mata idanu Ameena tayi, take kuma sai taji wani irin abu ya tokare maƙoshinta, wani irin haushin da tsanar Zaleehan ne taji ya cika mata zuciya, duban Hayatuddeen dake riƙe da hannun Zaleehan tayi, gani tayi idanunsa sunyi rau-rau kamar zaiyi kuka, tunda ta shigo ma ko ɗago kai baiyi ya kalleta ba, Raleeya da Adda Rahama ta kuma kallo, suma gani tayi rabin hankalin na kan Adeel gaba ɗaya rabin hankalinsu nakan Zaleeha'n, Ummi kuwa dama tuni hankalinta akan Zaleehan yake. Laɓɓanta ta cije, tare dajin wani abu na zazzafan kishi akan Zaleeha'n, bakomai kuwa yasa hakan ba, face tsananin kyawun Zaleehan da ta gani, ga kuma yanda su Ummi ke nan nan da ita, ganin cewa gabaki ɗayansu hankalinsu a tashe yake hakan yasa taja da baya, tana sakin murmushin dayafi kuka ciwo, ta fice daga cikin ɗakin, sam su hankalinsu ma ba'a kanta yake ba, shiyasa basusan cewa ta fita daga ɗakin ba. Zaleeha kuwa asanyaye ta karɓi maganin tasha, lokacinne kuma aka soma ƙiraye ƙirayen Sallan magriba. Ameena kuwa tana shiga ɗakinta, tayi wurgi da jakanta ranta amatuƙar ɓace. Iska ta furzar ta bakinta, tare da sanya hannu ta kama ƙugunta, ahankali ta taka ta ƙarasa gaban mirrror, tsayawa tayi tare dayin shiru tana ƙarewa kanta kallo, idanunta ta rumtse da ƙarfi, sam koda  wasa, koda kuwa makaho bazai taɓa haɗa kyawun Zaleeha da nata ba, ita kamma mecece akyau?  idanunta ne suka sake hasasho mata Zaleeha, take taji gabanta ya faɗi,   tabbas hanyar jirgi daban haka ma kuma ta mota daban,  zamewa tayi ta zauna akan gadonta, wani irin haushin Zaleeha da matsanancin kishinta ne ke tokare mata maƙoshi,  taɓe baki tayi abayyane tace.  "Jiyanda suke wani nannan da ita saikace wata ƴar gold,  gaba ɗayansu kulawa suke nuna mata, jiyanda duk Hayatuddeen ya wani liƙe mata, hmmm."  kanta ta jinjina ganin zancen zuci bazai kaita ba, yasa ta miƙe tsaye kai tsaye ta wuce toilet.        Gaba ɗaya ta mance a fagen kishi da aurataiya ba'a surka kyau a mizani   ta mance cewa kowa ya iya Allonsa ya wonkene mata nawane munana na bugawa a mujalla kuma sune star a gidajensu            Can ɗakin Ummi kuwa ƙiran sallan magriba da akayi ne yasa Hayatuddeen tashi ya wuce masallaci, Raleeya ma ɗakinta ta koma don yin sallah, Adda Rahama kuwa shirye-shiryen   tafiya ta somayi,  sam bama da niyan kaiwa dare tazo ba, saidai ganin halin da Zaleeha take ciki yasa bata tafi da wuri ba.              Zaleeha kuwa babu laifi ta ɗanji sauƙin zazzaɓi da kuma ciwon kan daya rufeta.  Hakan yasa ta ɗauro alwala tazo ta gabatar da sallah, koda ta idar da sallan bata tashi akan sallayan ba, jingina tayi da jikin gadon Ummi, tare da lumshe idanunta, wasu siraran hawaye ne suka biyo ta gefen idanunta suka sauƙa akan fuskarta.             Dai-dai lokacin Ummi ta shigo cikin ɗakin,  ƙarasowa jikin gadon tayi ta zauna.   Cikin kulawa ta ƙira sunan Zaleeha'n,  ahankali taɗan ɗago kanta ta kali Ummi'n. kafaɗunta Ummi ta dafa cikin son sake bata karfin guiwa tace.        "ki kwantar da hankalinki, Insha Allah gobe  zamuje za'a bawa Baba Malam haƙuri, kuma nasan zai haƙura ya yafe miki, sannan kuma Baba Malam ba tsanarki yayi ba, hakama ƴan uwanki, kawai dai suna fushi dake ne,  saboda abun da kikayi baki kyauta ba sam, bawai dan kina auren Saifuddeen bane yasa nace haka, a'a  ina faɗa miki hakane dan ni matsayin  ƴa na ɗauke ki, ke macece Zaleeha, duk kuwa mace me tarbiya irinki ba a santa da gudu ta bar gida ba, haka kuma ɗabi'ar guduwa ma sam bai kamata ace mace ta ɗaukesa ba,  bazan tursasaki faɗamin dalilin dayasa kika gudu ba, saboda nasan dama tuntuni bakyason auren ki da Saifuddeen, bakya sonshi dole akayi miki amma kuma duk da haka bai kamata ki tsalleke iyayenki ki tafi can wata duniya ba,  nasan kinyi nadama kwarai,  kuma insha Allah Allah Zai karɓi tubanki, kuma Baba Malam ma nasan zai yafe miki,  kawai dai yana fushi ne saboda yanda kikayi watsi dasu, amma nasan da zaran anbasa baki zai yafe miki, saidai kuma ina fatan zaki kiyaye gaba,  sannan kowata kikaga zata aikata irin abun da kika aikata zaki haneta."       Tuni hawaye sun gama wankewa Zaleeha fuska, tabbas tasan bata kyauta ba, kunyar Ummi ta rufeta yadda ta gane cewa bata son ɗanta ita kuma duk da haka bai hanata so taɓa.   wanda dalilin hakanne kuma kowa ke fushi da ita, ƴan uwanta sun ƙita saboda abun da ta aikata, Babanta mahaifi ya koreta duk akan abun da ta aikata, tabbas Ummi ta cika uwa ta gari, abun so ga kowa, ta aikata musu laifi amma sun ƙaunace ta, alokacin da kowa ya nuna mata tsana, su kuma sunjawota jikinsu, Babanta ya koreta, su kuma sun amsheta duk da laifin da ta aika ta musu suka bata mafaka,  tayaya zata fara misalta girman halaccinsu agareta? abune me girma da bazai kwatantu ba,  kukane ya ƙwace mata sai kawai ta kifa kanta akan cinyar Ummi, ta saki kuka'n.   Awannan karon Ummi batayi yunƙurin hanata kukan ba, saboda ko ba komai shi kukanne zai rage mata zafi da raɗaɗin zuciya.   Saida Ummi taga kukan yayi yawa sannan tashiga ɗan bubbuga bayan zaleehan tana shafa kanta.      Sannu ahankali ta rage sautin kukan nata, shiru tayi tana sakin ajiyar zuciya.    Ganin haka ne yasa Ummi kamo hannunta suka fice daga cikin ɗakin, kai tsaye ɗakin dake gefen na Ummi'n,  Ummi takaita, wanda yake ɗakin su Raleeya ne wanda sukai budurci acikinsa, kuma nanne masauƙin Goggo Dada da Aunty Meena in sun zo, akimtse ɗakin yake sannan babu wani hargitsi acikinsa, akan gado Ummi ta zaunar da ita, toilet ɗin ɗakin ta shiga ta  haɗawa Zaleehan ruwan wanka me ɗan ɗumi.     Dubanta Ummi tayi cikin kulawa tace.    "Kishiga kiyi wanka, zuwa gobe an gane key ɗin side ɗinki, dan yanzu na tambayi Hammansu key ɗin yace baisan inda key ɗin yakeba sai ya nema, shiga na kiyi wonka sai kizo ki kwanta, ko za ki ci abinci nasa Hayatuddeen ya kawo miki." Asanyaye  ta  girgiza kanta alaman "A'a"   jinjina kai Ummi tayi sannan ta fice daga cikin ɗakin, tana mai tuna za'ayi daga da Saifuddeen dan tasan batun wai shi baisan inda key ɗin side Zaleeha yakeba duk cikin fushine ta lura ya fusata sosai da Zaleeha.    Ita kuwa Zaleehan       cikin sanyi ta tashi ta shiga toilet ɗin, wanka tayi sannan ta ɗauro al'wala'n sallan isha,  rigar da ta cire shi ta sake mayarwa, wanda dama doguwar rigar atamfa ce ajikinta.      Koda tayi sallan ta jima akan sallaya tana addu'o'i, har kusan ƙarfe tara na dare tana nan zaune akan sallaya'n, daga ƙarshe kuwa anan kan sallayan ta kwanta tare da lulluɓe jikinta da bargo, luf tayi tana sakin ajiyar zuciya, hawaye kuwa na tsiyaya daga cikin idanunta.                      A ɓangaren Saifuddeen kuwa dawowarsa daga sallan isha kenan, kai tsaye bathroom ya nufa, wanka yayi  haka ya fito jikinsa sai tashin ƙamshin turaren wanka yake, tura wheelchair ɗinsa yayi zuwa gaban dressing mirror, cikin nutsuwa ya shafawa jikinsa mai me daɗin ƙamshi,   body spray ya fesa, sannan yaja wheelchair ɗinsa ya ƙarasa gaban drawer'nsa, wani 3 quater jeans ya sanya tare da wata blue ɗin t-shirt me kyau,  sake feshe jikinsa da turare yayi sannan ya ƙarasa inda laptop ɗinsa yake, ɗauka yayi tare da ajesa akan cinyarsa, cikin nutsuwa ya soma ɗan daddanawa.          Ahankali ta turo ƙofar ɗakin ta shigo, tasha kwalliya cikin wata sleeping dress me kama jiki, kana ta sake ɗan gashinta wanda iya kansa ya kwanto kan wuyanta,    tsaye tayi ajikin ƙofan tana kallonsa, sosai yayi mata kyau, akullum indai ta ɓangarenta ne ƙara kyau yakeyi tana masifar sonshi shiyasa take tsananin kishinsa ji take tamkar dan ita ɗaya aka halicceshi, shikuwa Saifuddeen sam ma baisan da zuwanta ba, saboda ya bawa ƙofar shigowa ɗakin baya sannan kuma gaba ɗaya hankalinsa akan laptop ɗinsa yake.           Murmushi ta ɗanyi tare da takowa ta ƙaraso inda yake, hannuwanta tasa  ta bayansa kana ta rungumesa,  ɗan lumshe idanunsa yayi,  tare da cije laɓɓansa, dama yasan  aje azo dole saitazo ta katsesa daga abun da yakeyi.      Ameena kuwa zagayowa ta gabansa tayi ya zamana suna fuskantar juna,  wani irin annuri  ta hango akan fuskar tasa,   take taji ƙirjinta ya buga, shikuwa Saifuddeen ganin yanda ta ƙuresa da ido ya sashi ɗan sakar mata murmushi.    Itaɗinma murmushi ta mayar masa, tare da ɗan duƙowa tayi kissing ɗinsa akan forehead ɗinsa,   ɗago  kyawawan idanunsa yayi ya kalleta,  ɗan lumshe idanunsa yayi tare da miƙa mata hannunsa, kama hannun nasa tayi, shikuwa ya jawota cikin jikinsa ya ajiyeta kan cinyoyinshi ya zama suna fuskantar juna da kyau, wani sakalin murmushi yayi mata tare zaro harshensa  waje yana ɗan karkaɗa mata wani irin abu taji ya ratsa jiki da zuciyarta, ido ta zuba mishi ganin ya sanya lips ɗinsa yaɗan yiwa kumatun ta kiss,     wani irin sanyi taji acikin ranta,  hannayensa ya sanya ya tallafo haɓarta, haɗe fuskarsu waje ɗaya yayi, tare da kamo bakinta yana kissing,   cikin jin daɗi da farin cikin da ta samu kanta ciki, ta kamo tongue ɗinsa tana tsotsa,          tunaninta ne ya fara kwancewa, sakamakon irin salon da taji yanayi mata, wanda bata bai taɓa yi mata irinsa ba sai yau ɗin,  wani tunani da yazo zuciyarta ne yasa ta ɗan janye jikinta baya, idanu ta ƙura masa tana me ƙoƙarin karantar yanayin da yake ciki.   Kyawawan idanunsa ta kalla, wanda suka kasa ɓoye abun da ke zuciyarsa, wani irin zallan farinciki ta hango acan ƙasan idanunsa,   dubansa tayi sosai shaiɗan na ingiza kishinta, har yanzu fuskarsa ɗauke take da sahirtaccen murmushi wanda ke nuni da can ƙasan zuciyarsa na danƙare da tarin farin ciki mai ratsa jiki da zuciya gashi har ya baiyana bisa fuskarsa,  take wani tunani yazo ranta, nan kuwa taji wani abu me ɗaci ya tsaya  a maƙoshinta,  tabbas tasan cewa wannan farin cikin da ta hango akan idanunsa bawai na haka kawai bane,  tasan wannan farincikin da take hangowa acikin idanunsa, bai rasa nasaba da dawowan Zaleeha abinda ranta ya saƙa mata kenan,  take taji wani ɓacin rai ya zo mata,  matsanancin kishin da tsanar Zaleehan ne ya sake rufeta,     ahankali yasake matso da fuskarsa gab da nata, ƙoƙarin sake kamo laɓɓanta yake, cikin sauri tajanye jikinta baya,   ji tayi gaba ɗaya idanunta na neman kawo ruwa, hakan yasa cikin sauri ta juya ta fice daga cikin ɗakin.                       Binta yayi da kallon mamaki, saboda yanda yaga yanayinta ya sauya lokaci ɗaya.       Ɗan jim yayi, yana tunanin shi dai bai mata komai ba lokaci guda kuma ya saki murmushi, maida kansa ga laptop ɗinsa yayi  ya cigaba da aikin da yakeyi.                        Ameena kuwa tana fita daga ɗakin nasa, kai tsaye ɗakinta ta wuce, ranta nayi mata ƙuna, akan gado ta zauna, take kuma sai taji hawaye nabin gefen idanunta,  hannu tasa ta dafe kanta,       ita ta sani tabbas wannan farincikin da ta gani akan fuskarsa duk dan saboda dawowan wannan aljanar tasa ne,   tana sonsa   shiyasa take jin kishinsa sosai, bama kamar yau da ta hango soyayyar Zaleehan acikin idanunsa, bayan kuma tasan cewa Zaleeha tafita komai, kyau, sura, dama komai da komai.     Tashi tayi ta kashe hasken ɗakin nata, kana ta haye saman gado ta kwanta, gaba ɗaya ranta babu daɗi. Sai wajajen ƙarfe 11 kafun ya kammala abun da ya keyi, harzuwa lokacin kuwa Ameena bata dawo ba, sosai abun ya basa mamaki, dan a iya saninsa baiyi mata wani abu da zai ɓata ranta ba, wayarsa ya ɗauka tare da laluɓo number'n ta ya shiga rubuta mata text message kamar haka. _"Har yanzu fa ke nake jira banyi bacci ba, kuma baki zoba, Please kiyi sauri kizo, idan zaki zo ki taho, ki ta homin da Adeel."_ yana gama rubutun ya tura mata, ƙoƙarin sauƙa daga kan wheelchair ɗinsa yayi inda ya haura saman gadon. Dai-dai lokacin da saƙon nasa yazo mata kuwa, tana nan kwance sai-dai ba bacci takeyi ba, gaba ɗaya tsananin kishinsa ya hanata sakat, ganin wayarta ta kawo haske yasa ta ɗauka ta duba, tana gama karanta saƙon nasa ta maida wayar ta ajiye, batare da tayi masa reply ba. Saifuddeen kuwa ɗan kishingiɗa yayi, yana jiran ko zata shigo, amma shiru babu alamarta, kuma sannan babu reply, jawo wayartasa yayi ya sake tura mata wani text ɗin. Shima sama da mintuna goma aka kwashe babu amsa, ganin haka ya sashi gyara kwanciyarsa tare da jawo blanket ya rufawa jikinsa, cikin ransa yace. "Meye hakan ke nufi kenan? fushi tayi ta tafi ko kuma me? To fisabilillahi ni me nayi mata da zatayi fushi dani? To ko dai tayi bacci ne?". kansa ya girgiza tare da ɗage kafaɗunsa, cikin ransa yace. "Allah ya sani ban mata komaiba a iya sanina kuma banyi komai da nufin baƙanta mata ko cutar da itaba, domin nasan son da take min shiyasa nake ganin kimarta sam bani da nufin tozartata duk rintsi zan kasance mata adalin miji jagora mai tausayinta. maganar zuci ya kumayi banyi mata wani abun da ya kamata ace taji haushi ba, well zata ma kawo kanta da ƙafafunta kwadayayyi kawai cingom ɗin na." sake gyara kwanciyarsa yayi, yana rufe idanunsa kuwa sai bacci, don dama agajiye yake. Ameena kuwa da ƙyar ta iyayin bacci, saboda duk juyin da zatayi shaiɗan da zafin kishi na zuzuta mata kyawun Zaleeha, da kuma zallan farincikin da ta hango acikin ƙwayan idanun Saifuddeen su ke yi mata gizo, haka nan taji gaba ɗaya ta raina kanta, sannan kuma wata zuciyar na faɗa mata cewa, kada tayi kuskuren wuce matsayinta, saboda Zaleeha zaɓinsa ce, ita kuwa zaɓin iyayensa ne bana saba, kuma dama Maza irin su Saifuddeen rayuwarsu zai tafi ne da kyawawan mata irinsu, tasan kai tsaye baza a ce mata mummuna ba, amma kuma idan aka sanyata alayin su Zaleeha, bazata ganu ba, dan ko stage ɗin farko na kyawunsu bata taka ba, domin kuwa a kyau su nasu stage ɗin acan sama yake, musamman Zaleeha da ta haɗa komai da komai, haka kishi yasa ta yita kuncewa da saƙawa, daga ƙarshe dai haka bacci ya ɗauketa, ranta duk ba daɗi. Ɓangaren Zaleeha kuwa ƙiran sallan farko na asuba akan kunnenta, kasancewar dama bata wani samu ishashshen bacci ba, duk yanda taso hana kanta kuka ta kasa, haka ta wayi garin yau ɗin ma da wani sabon kuka, cikin kukan haka taje ta ɗauro al'wala tare da zuwa ta gabatar da sallan Asuba, zama tayi akan sallayan, nan cikin muryarta me ɗauke da kuka take karanta Al'Ƙur'ani saboda tasan karantasa zai yaye mata damuwa. Tajima tana karatun saida taga gari yayi haske, kafun tatashi daga kan sallayan, zuwa lokacin idanunta sun sakeyin luhu luhu, gwanin ban tausayi, kallo ɗaya zaka mata, kasan ta kwana kuka, ƙarasawa jikin ƙofar ɗakin tayi, cikin sanyi ta fice daga cikin ɗakin. Kaitsaye ɗakin Ummi ta nufa, abakin ƙofa ta tsaya, tare da yin knocking, daga ciki Ummi ta bada izinin shigowa, ahankali kuwa ta murɗa handle din ƙofar tashiga, Ganin Ummin na zaune akan gado, yasa cikin sanyi ta ƙarasa tare da durƙusawa, cikin muryarta dake rawa tace. "Ummi ina kwana." Murmushi Ummi tayi tare da cewa. "Lafiya ƙalau Zaleeha ya jikin naki dai?" Asanyaye tare da muryarta dake bayyana rauninta tace. "Da sauki." Kai Ummi ta jinjina cikin kulawa tace. "Masha Allah, Allah Ya ƙara sauƙi, sannan ki ƙara kwantar da hankalinki kinji, komai yayi farko yana da ƙarshe, haka ma kuma komai yayi tsanani zaiyi sauƙi da yardan Allah, ako yaushe kina sawa zuciyarki nutsuwa, kinga ko yawan kukan nan ma da kike bashida amfani, kiyi haƙuri kinji, ƙaddara ce babu kuma yanda bata zuwa wa bawa, saidai neman sauƙi awajen Allah kawai." Kanta ta ɗan jinjina cikin muryarta dake rawa tace. "To Ummi, amma kullum zuciyata ƙara karyewa take, gani nake kaman Baba Malam bazai taɓa yafe min ba, tsoro nakeji Ummi, idan na mutu Baba Malam na fushi dani, samun aljanna zaiyi min wahala, kuma kowa nace ya roƙamin Baba Malam sai yaƙi, har Daddy (Malam Adam) shima nace ya bawa Baba Malam haƙuri, amma yace shi babu ruwansa, shima fushi yake dani." Ɗan jim tayi tare da sakin sheshsheƙa, asanyaye tace. "Zakariyya yace duk wanda na ɗauko dan yabawa Baba Malam haƙuri, bazai haƙura ba, har saidai in Hamma Saif ne ya rakani. Dan Allah Ummi ki roƙamin Hamma Saif ya yafemin, ya rakani mu bawa Baba Malam hakuri, idan Baba Malam baiyafemin ba, nasani haske bazai taɓa ziyartan rayuwata ba ." Taƙare maganar cikin yanayin ban tausayi, ga kuma hawayen da gaba ɗaya suka gama jiƙa mata fuska. Hannayen Zaleehan Ummi ta kamo cikin yanayin kulawa haɗi da tausayawa tace. "To kidaina kuka, insha Allah zan faɗa masa, kuma nasan zai yafe miki, sannan kuma zai rakaki kuje ku bawa Baba Malam haƙuri, ki tsaida kukan haka kinji." Ummi ta faɗi maganar cikin lallashi. kanta ta jinjina, saboda ta ɗanji sanyi aranta. Jan jikinta tayi ta zauna anan kusa da Ummin. Ahankali ya turo ƙofar ɗakin ya shigo, dan alokacinne dawowarsa daga masallaci, kusan atare suka ɗago kansu suka kalleshi, hakanne yasa idanunsu faɗawa cikin na juna, lokaci guda ya kawar da duk wata annuri dake kan fuskarsa, itama asanyaye ta yi ƙasa da kanta, cikin haɗe fuska ya ƙaraso cikin ɗakin, dan ma Ummi ta riga da ta ganshi ne, da ace bata gansa ba babu abun dazai hanashi komawa inda ya fito. Ƙarasowa kusa da Ummin nasa yayi, haɗe hannayensa biyu yayi, kana cikin body language ɗinsa ya gaida ta. Amsa masa gaisuwar Ummi tayi tana ɗan sakin murmushi. Asanyaye Zaleeha ta ɗago kanta, cikin wata irin murya me ɗauke da sarƙewa, akaron farko kenan na tarihin rayuwarta da zata fara gaida shi, cikin sheshsheƙan kukan daya taso mata tace. "Ina kwana." kasancewar yana iya kallonta ta gefen idanunsa ne,yasashi fahimtar abunda tace, amma sai ya share yayi kamar baigani ba, saima sake haɗe fuskarsa da yayi, tare da ƙoƙarin soma ciro wayarsa, daga aljihun rigarsa. Ganin hakane yasa Ummi sa hannu taɗan taɓashi, ɗago da kansa yayi ya kalli Ummi'n. Da idanu tayi masa nuni da Zaleeha kana tace. "Bakaga Zaleeha na gaisheka bane." Ai tunma kafun Ummi ta gama rufe bakinta, yasake maida kansa ƙasa, dan bama yaso ya fahimci abunda Ummin ke ƙoƙarin faɗa, ahankali ya tura wheelchair ɗinsa, ya nufi hanyar fita daga ɗakin, ko inda Zaleehan take bai kuma kallo ba. Baki buɗe Ummi ke kallonsa har ya fice daga cikin ɗakin, kanta kawai ta girgiza, tare da sakin ɓoyayyen murmushi, sarai tasan gano ƙasan zuciyarsa cewa wannan fushin nasa da yakeyi da Zaleehan hukunta yakeyi har cikin zuciyarsa, kuma yanayi ne dan ya gwada mata ɓacin ransa, akan abun da ta aikata, sannan kuma ya nuna mata kurenta ta kuma sani shima mutunne kamar kowa yanada zuciya kuma zai hukuntata muddin ta ɓata mishi. sanin irin zazzafar soyayyar da Saifuddeen ɗin keyiwa Zaleeha yasa Ummi sanin cewa bazai taɓa iyayin haƙiƙanin barranta da ita ba. Itakuwa Zaleeha asanyaye ta miƙe, cikin sanyin da ayanzu ya zama tamkar ɗabi'arta tace. "Ummi ina Raleeya, da Hayatuddeen." ɗan murmushi Ummi tayi tare da cewa. "Raleeya na kitchine, Hayatuddeen kuma kinsan yau weekend yanacan yana baccin nasa da baya gajiya dashi." Kanta taɗan jinjina, sannan tace. "To bari inje kitchin ɗin in taya Raliya aikin". Da sauri Ummi tace. "A a jeki kwanta". Zata kuma yin mgna Ummi tace. "Nace kije ki konta ki huta". ganin yadda Ummi tayi mgnar cikin bada umarnine yasata cewa. "To Ummi bari naje na ɗan kwanta." Kai Ummi ta jinjina mata, saboda duk wani koke koken da tayi adaren jiya, Ummin najinta, hakanne ma yasa tasan cewa Zaleehan bata wani samu ishashshen bacci ba. Tana fitowa daga ɗakin Ummin kuwa, sukai karo da Hayatuddeen wanda da dukkan alama yanzu tashinsa, dan sai hamma yake ta zubawa tare da miƙa. Ganin Zaleehan yasashi sakin murmushi, ƙarasowa yayi tare da kamo hannunta, cikin kulawa yace. "Good morning my beautyful Aunty, ya jikin naki?" Kanta taɗan jinjina masa alaman da sauƙi, idanunta ne suka sauƙa akan Saifuddeen wanda ke zaune akan kekensa ya basu baya, yana ta faman aikin danna wayarsa, saurin ɗauke idanunta daga kansa tayi, tare dayin ƙasa da kanta. Dai-dai lokacin Raleeya ta fito daga cikin kitchine, gaisawa sukayi cikin kulawa kuwa Raleeya ke tambayarta jikinta, nan tace mata da sauƙi. Hayatuddeen ne ya kamo hannun Zaleehan, tare da zaunar da ita akan ɗaya daga cikin kujerun falon, cikin kulawa yace. "Adda Zaleeha dan Allah minti biyu, ki jirani anan ina zuwa." kai ta jinjina masa tare da sadda idanunta ƙasa tana wasa da ƴan yatsun hannunta. Ameena ce ta buɗe ƙofar falon ta shigo bakinta ɗauke da sallama, shirye take tsab acikin kayan aikinta, ga kuma kekyawan ɗanta Adeel da ke riƙe ahanunta, shigowarta falon kuwa yayi dai-dai da fitowan Ummi daga ɗaki. Jin ƙamshin turaren Ameenan ne ya sashi ɗago kansa ya kalleta. ƙarasowa cikin falon tayi, da ganin Zaleeha kuwa sai taji gaba ɗaya ranta yayi ƙunci, ɗan durƙusawa tayi, aladabce ta gaishe da Ummi', fuska ɗauke da fara'a da kulawa Ummi ta amsa tare da miƙa hannu ta karɓi Adeel dake ta yi mata dariya irin tasu ta yara. Ɗago kai Zaleeha tayi, karab kuwa suka haɗa idanu da Ameena'n, kasancewar dama idanun Ameena'n akanta suke, ta tsareta da idanu kamar ta samu tv. Cikin sanyi Zaleehan ta janye idanunta, tare da cewa Ameena'n'. "Ina kwana." zazzaƙan muryar Zaleehan da Ameena taji shiya sanya bugun zuciyarta tsananta, wanda har yasa ta kusa daburcewa, cikin in ina ta amsa da "La fi..ya." dan zata iya rantsewa cewa bata taɓa jin murya me daɗin a zahiri irin ta Zaleehan ba. Kallon Adeel dake hannun Ummi Zaleeha tayi, cikin sa'a kuwa yaron shima kallonta yake, murmushi tayi masa sai kawai ya buɗe baki yana mata dariya, wani irin kyau yaron yayi mata, musamman ma yanda dimples ɗinsa suka lotsa da yana dariyan, lokaci guda taji ya shiga ranta, hakan yasa ta miƙa hannu dan ta ɗaukeshi, babu ƙiwa kuwa yazo wajenta, karɓansa tayi tana sakin sassanyan murmushi. Ummi ne itama tayi murmushi cikin kulawa tace. "Lallai Adeel yaga ɗiyarsa, tunda dai baiyi mata ƙiwa ba." Kallonta Zaleehan tayi da ɗan mamaki, kai Ummi ta jinjina tare da cewa. "Ai me sunan Baba Malam ne." Wani irin farinciki ne ya cika zuciyar Zaleehan, sai kawai ta rungume yaron ajikinta tanajin sonsa sosai aranta haka nan sai takeji kamar itace ta haifeshi in ba gizo idonta ke mata sai takega kamar yaron yana kama da ita, musamman dimples ɗinsa irin nata ne sak. Dai-dai nan Hayatuddeen ya fito daga kitchine hannunsa ɗauke da cup, wanda aka zuba yoghurt acikinsa, akusa da Zaleehan ya zauna tare da miƙa mata yoghurt ɗin, cikin kulawa yace. "Adda Zaleeha amsa kisha, al'ƙawari nayiwa Zakariyya cewar yau sai nasa kinci abinci, saboda haka dan Allah kisha kafun agama break fast." ɗan marairaice fuska tayi, sai dai kuma ita kanta tasan cewa tana matsanancin jin yunwa, hakanne ma yasa ta amsa, tare da ɗan sha kaɗan, kan Adeel da har yanzu ke kan cinyarta take shafawa, sosai yaron ya shiga ranta tana jin sonshi da ƙaunarshi har cikin ranta. Duk wannan wainar da ake toyawa Ameena idanu kawai ta zuba musu, itakam Allah yasani bata gajiya da kallon Zaleeha, to itama da take mace, bata gajiya da kallonta, inaga kuma Namiji haka yasa kishinta kuma ninkuwa a ranta. Hayatuddeen ne ya ɗago kansa ya dubi Ameena'n, murmushi yaɗan saki cikin kulawa da girmamawa ya fuskanceta tare da cewa. "Aunty Ameena ina kwana." itama murmushi'n ta mayar masa tare da cewa. "Lafiya Auntan Ummi, ya rigima." murmushi kawai yayi, batare da yace mata komai ba, ya maida hankalinsa wajen Zaleeha tare da kissing goshin Adeel dake kan cinyar Zaleeha, wanda da dane kuma ta tabbatar tsayawa zaiyi yayita mata rigima, amma yanzu gaba ɗaya hankalinsa naga Zaleeha. Hakanne yasa asanyaye ta juyar da kanta ɓangaren Saifuddeen, ai kuwa idanunsu ne ya haɗe, dan dama kallonta ya keyi, murmushi ta sakar masa, domin tuni haushin nasa da takeji ya gushe, ayanda take matsanancin sonsa batajin zata iya dogon fushi dashi bare ta ɓata rawanta da tsalle, shiɗin ma murmushi yayi mata tare da miƙa mata hannunsa, ganin Idanun su Ummi baya kansu yasa ta kama hannun nasa, gamamakinta sai gani tayi yajawota dab dashi, har jikinsu na gogan na juna, kasancewar jiyan ba'a ɗaki ɗaya suka kwana ba, hakan yasa bata gaishesa ba sai yanzun, ahankali tace. "Ina kwana." Kansa ya jinjina mata alaman lafiya, sannan ya tallafo haɓarta, kiss ya ɗaura mata akan kumatunta da kuma bakinta, baruwansa da wani jin kunya wai dan su Ummi na falon bare yasan idon Ummi baya kansu. Gaba ɗayansu sunga abun da Saifuddeen din yayiwa Ameena hakan ne yasa suka janye idanunsu gefe, Zaleeha ma da tsautsayi yasa ta ɗago, idanunta sun gane mata abun da ya faru, kawar da kanta gefe tayi, tare da ƙara manne Adeel ajikinta, ko ajikinta itakam, bata ma ji wani abu adangane dasu ba, saidai zuciyarta ta tsegunta mata cewa. "Halan Ameenan matarsa ce kenan." Ummi kuwa, tashi tayi gaba ɗaya ma tabar falon, dan ta gano cewa wannan sabuwar kulawan da Saifuddeen ɗin ya fara bawa Ameena agabansu wani salone, kawai yayi ne saboda wata manufarsa ta daban. Ameena kuwa da gangan ta kamo lips ɗinsa itama ta tsotsa, cikin sanyin murya tace. " I will miss you dear" sake manna masa wani kiss ɗin tayi, sannan ta ɗan janye daga jikinsa, Hayatuddeen kuwa baki ya sake yana kallon ikon Allah, Zaleeha kuwa sam bata ƙara ɗago kanta bama sai wasa takeyiwa Adeel wanda da ka gani kasan tana jin son yaron har cikin ranta. Ƙarasowa inda suke Ameenan tayi, tare da sanya hannu ta ɗauki Adeel, tana sakin murmushi me ɗauke da ma'anoni kala kala, haka ta saɓa Adeel akafaɗanta ta fice daga cikin falon, wani irin farinciki takeji acikin ranta, wannan kiss ɗin da Saifuddeen yayi mata agaban Zaleeha ji take kaman kyautar zuciyarsa ya bata a gaban Zaleeha ji takeyi ya gama mata komai dan ko ba komai ya nunawa Zaleeha itama matarsa ce kuma yana sonta murmushi kawai take tayi. Tashi Zaleeha tayi ta wuce ɗakinta, kusan rabin cup tasha yoghurt ɗin sannan ta kwanta. Acan falo kuwa Raleeya ce ta gama shirya musu abinci akan dinning area, Ummi ne tace da Hayatuddeen yaje ya ƙira Zaleeha tazo suyi beak, koda yaje ɗakin nan ya isketa tana bacci. Dawowa yayi ya faɗawa Ummi'n, hakan yasa Ummi tasa Raleeya ta ɗeba mata nata break fast ɗin daban. Saida suka kusa kammala break fast ɗin, Ummi ta ɗago kanta ta dubi Saifuddeen wanda yake tsakalan chips yana kaiwa bakinsa, ahankali yake tauna abincin, yanayin komai nasa cikin nutsuwa. Gyara zama Ummi tayi tare da ɗan muskutawa ta kamo hannunsa, ɗago kansa yayi, tare da sakarwa Ummin nasa murmushi. Itama Ummin murmushi tayi masa, cikin kulawa tace. "Ka bani key ɗin side ɗin Zaleeha," Fuska ya ɗan kwaɓe tare da mata alamu. Shiga baisan inda key ɗin yakeba". Kwaffa tayi tare da cewa. "Uhumm yayi kyau." Fuska ya ɗan kele, tsareshi da ido Ummin tayi tana mai nazartanshi kana tace. "To Inaso kashirya anjima ka raka Zaleeha ta bawa Baba Malam haƙuri, ko kuma shima car keys ɗin naka duk baka san inda sukeba." take yanayin fuskarsa ya sanja, kansa ya girgiza, tare da aje spoon ɗin hannunsa. Idanu Ummi ta zuba masa ganin ya mata alamun dan Allah tayi haƙuri, sai kuma yaja wheelchair ɗinsa yayi baya, tare da juyawa yabar wajen baki ɗaya, da idanu Ummi ta bisa har ya fice daga cikin falon. Wasa farin girki sannu sannu dai bata hana zuwa sai dai a dadde ba'a jeba Littafina na kuɗine. in kina buƙata ga number 09097853276 katin mtn zaki turo na ɗari 300 ko kimin transfer ta asusuna 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. By *GARKUWAR FULANI* [17/09, 7:29 pm] +234 803 620 1562: Ngs,ego Jin baƙon ƙamshi ajikinsa ne yasa ta rumtse idanunta kana ta tashi zaune tana jifansa da wani irin kallo me ɗauke da ma'anoni da yawa. Jitayi ranta ya ƙara matuƙar ɓaci, kirjinta kuwa har ƙuna yake mata, saboda tsabar kishinsa da take, menene ma'anar wannan ƙamshin da yake? wato hakan na nuni da cewa yazo ne ya nuna mata alaman da zata gane cewa ya je ɗakin Zaleeha. Wani irin haushinsa ne taji ya kamata, take taji ranta ya cigaba da tafasa, ɗan ƙanƙance idanunta tayi tana binsa da wani irin kallo mai cike da so da gaurayen kishi, wanda har hakan yasa yanayin zafin kishinta, ya kasa ɓuya akan fuskarta. Ganin irin kallon da takeyi masa ne, ya sashi ƙura mata ido cike da ɗan mamaki, dan zallan ɓacin rai da kuma kishi yake gani acikin ƙwayan idanunta. Ahankali yaɗan turo wheelchair ɗinsa kusa da ita, tare da ɗan kai hannunsa zai taɓa ta, afusace ta ɗaga masa hannu, cikin wutar kishin dake cinta tace. "Da Allah Karka taɓa ni banaso, kaje kawai, ka koma can inda ka fito, kaje can ka taɓa ta, tunda dama haka kakeso kuma ka zaɓa." taƙare maganar tana ne sake ƙara sautin kukanta, wanda yake ɗauke da tsananin takaici da kuma azababben kishi. Shiru yayi cike da mamaki ya zuba mata kyawawan idanunsa, sosai yake nazartar ta, wuta-wuta haka yake ganin kishi acikin ƙwayan idanunta, ɓoyayyan ajiyar zuciya ya sauƙe, batare da tunanin komai ba, ya sake ɗan tura wheelchair ɗinta ya nufo gareta, asonsa shine ya ɗan kwantar mata da hankali sannan ya kuma rarrasheta. Ganin haka yasa cikin matsanancin kishi tace. "Nace maka kada ka taɓani,sannan kuma kada ka matso kusa dani, kafita min aɗakina kawai, dama yarona ne ka kawomin saboda haka, kafitamin daga ɗaki, kaje can inda idan ka shiga kake jimawa, ka koma ka cigaba da jimawan ka!" Tafaɗi haka cikin kishin da ya rufe mata ido, har acikin ranta ƙuna takeji, kishin Saifuddeen din da kuma haushin Zaleeha da takeji suna neman tarwatsa mata zuciya ta mancema yau ranar Zaleeha ne sai takeji kamar girkinta ya kaimata abin kuwa baya rasa nasaba ne da saba ita kaɗai gareshi duk da tasan yanada wata matar amman yanzu sai takega kamar ita yayiwa kishiya. Ganin yanda gaba ɗaya idanunta suka rufe yasa shi girgiza kansa, tabbas yasan ayanzu idanunta sun rufe, bazata taɓa fahimtar komai ba, juyawa yayi cikin nutsuwa ya fice daga cikin ɗakin, ko waiwayenta baisake yi ba. Ganin ya fitane yasa ta fashewa da sabon kuka, tare da faɗawa saman gadon, hakanan takejin kaman tayi ta kurma ihu ko zataji sauƙin abun dake zuciyarta, ya zatayi da kishin Saifuddeen dake damunta? ina zata kai baƙincikin abun da takeji, akullum akuma koda yaushe, akullum zata ga Zaleeha saita ji duk ta raina kanta. Saifuddeen kuwa kaitsaye ɗakinsa ya wuce. Yana shiga ɗaga kai yayi ya kalli agogo, ganin ƙarfe 12:10 am na dare ne, ya sashi ɗan zaro idanunsa, dan ya shiga ɗakin Zaleehan ne tun 11, amma sai 12 yake fitowa kwata kwata baisan ya ɗauki lokaci acikin ɗakin har haka ba. Ahankali ya ƙarasa tare da rage hasken wutan ɗakin, kan haɗaɗɗen makeken gadonsa ya kwanta, kana ya jawo blanket ya rufa ajikinsa, wata irin sassanyar ajiyar zuciya ya sauƙe, tare da ɗan lumshe idanunsa, sosai yake mamakin mood ɗin da yaga Ameena aciki, sam bai taɓa ɗaukan cewa zafin kishinta har yakai haka ba, har yanzu yana mamaki, dan kwata kwata baiga dalilin da zaisa ta ɗau zafin kishi ta sanya aranta ba, aganinsa bai kamata ma tayi kishi da Zaleeha ba, dan idan da zata lura, Zaleehan ba wani damuwa tayi dashi ba, ko bayan haka ma bata nuna kishi akansa, amma ya lura gaba ɗaya tunda Zaleeha ta dawo gidan Ameena ta tashi hankalinta, Allah ma ya san zuciyarsa, shi adalci kawai yake son ya kamanta atsakaninsu bashi da niyar tauye haƙƙin kowa a cikinsu, domin ko wacce da matsayin ta a ranshi da zuciyarshi da rayuwarshi. Ɗan sake lumshe idanunsa yayi ahankali moment ɗinsu da Zaleehan ya dawo masa, lokaci guda yaji wani irin kasala ya saukar masa, take yaji tsikar jikinsa na zubawa, ga kuma wani irin fitinannen feeling dake neman hautsuna mai tunani, tunowa da taushin breast ɗinta dayaji a tafin hannunsa shi yasa yaji gaba ɗaya jijiyoyin jikinsa na miƙewa, harshensa yasa ya ɗan lashi kyawawan laɓɓansa, acikin ransa yace. "Uhumm komai nata me kyau ne, yanayinta, fushinta, kukanta, tsoronta, dama duk wani yanayin da take ciki kyau yake mata." tunowa da irin yanda take ta ƙif ƙifta idanu, yasa shi sakin wani killer smile, cikin zuciyarsa yace. "baki kam akwaishi cakwai-cakwai amma sai shegen tsoro, kamar farar ƙura." sake gyara kwanciyarsa yayi, tare da kai hannu ya ɗan dafe saman mararsa, da kuma manhood ɗinsa dake ta faman harbawa, tunanin Zaleeha kaɗai ya birkita masa lissafi, gefe guda kuwa ga kyawawan saman breast ɗinta, dake ta faman yi masa gizo acikin idanunsa, wanda yasa yaji yayi weak. Ɓangaren Zaleeha kuwa Saifuddeen ɗin na fita, ta sake hayewa can saman gado ta takure, tare da matse jikinta waje ɗaya, sosai wani irin tsoro ya shigeta, musamman ma akan abunda yayi mata yanzun, tuna abunne yasa taji gaba ɗaya tsikar jikinta na tashi, tana jin wani iri ajikinta, blanket ta ja ta rufe jikinta, tare da turo ɗan ƙaramin bakinta gaba, cikin sakalci haɗi da zallan shagwaɓa, kaman yana gabanta tace. "Allah saiya sakamin, wai har zai gyaramin wuyan rigana, saikace shiya sakamin rigar ko ance masa ni ƴarin yace da sai an gyara min rigata". Tafaɗi maganar tana me sake naɗewa acikin bargon nata, zuciyarta cike take da fargaban kada ya kuma dawowa, gashi bata da key ɗin ɗakin balle ta rufe, ahaka dai atakure bacci me nauyi ya ɗauketa. Ɓangaren Ameena kuwa kuka tayi sosai, duk kuwa yanda taso bacci ya ɗauketa abun yaci tura, dan zuciyarta tafasa take, baƙin ciki da kishi sun hanata sakat, ga kuma wani sabon ƙuncin rai da tasamu kanta aciki, musamman ma da ta tuna da irin jimawar da Saifuddeen ɗin yayi anan ɗakin Zaleehan, tasan cewa yana ɗakin Zaleehan ne, saboda taƙira Hayatuddeen ne kan cewar ya kawo mata Adeel, sai yake shaida mata cewa Adeel ɗin na wajen Zaleeha, kuma Saifuddeen ya tafi zai ɗaukoshi, wannan abun shiya sanya taji ta tsani komai, take wani irin zargi ya ɗarsu acikin ranta, zuciyarta ce keta raya mata abubuwa, musamman akan jimawan da Saifuddeen ɗin yayi aɗakin Zaleeha, gashi wani ƙarin haushin, shine kwaso ƙamshin jikin Zaleehan da yayi ya kawo mata ɗakinta. Haka ta dinga juyi tana ta sambatun baƙin ciki da kishi duk akan Zaleeha, da ga ƙarshe ma ganin bacci bazai ɗauketa ba, saboda fitinannen kishin dake damunta yasa ta tashi ta zauna, sake saka sabon kuka tayi, saikace kamun aljanu can kuma ta miƙe taje tayi al'wala tazo taita nafilfili tana addu'o'in Allah ya sassauta mata zafin kishinta kuma Alhamdulillah ta ɗanji sanyi. Washegari. Ƙiran sallan asuban farko ne ya sauƙa acikin kunnuwanta, azabure ta ɗan farka, tana me kakkame jikinta, dan dama baccin nata atsorace tayi shi, ahankali ta zuro da kyawawan ƙafafunta ƙasa, bayan tayi addu'an tashi daga bacci, kaitsaye toilet ta wuce, ruwan zafi ta haɗa tayi wanka, tare da ɗauro alwala, koda ta fito wani jan jallabiya mai kyau na mata ta sanya ajikinta, sosai tigan tayi mata kyau dan tana ɗaya daga cikin na aurenta, kasancewar rigar ƙiran tukish ne yasa aka ƙawata jikinta da wani irin haɗaɗɗen ado, harma da hula akayi mata, duk da cewar rigar bata bayyana shape ɗin jikinta ba, amma ta yi mata kyau sosai, hijab ta sanya sannan ta tada sallah, saida tayi raka'atanul fajir, sannan tayi sallan asuban, koda ta idar Azkar tayi sannan taɗan taɓa karatun Alƙur'ani. Tana kai karshe kuwa miƙewa tayi, wani ɗan ƙaramin vail ta yane kanta dashi, sannan ta fesa turarenta me dadin ƙamshi, wayarta ta ɗauka, sannan ta nufi hanyar fita daga ɗakin, cikin nutsuwa ta murɗa handle ɗin ƙofar ta fice. Kanta tsaye sashin Ummi ta nufa, bakowa afalon, hakan yasa ta nufi ɗakin Ummi kaitsaye, tana knocking kuwa aka bata izinin shigowa, murɗa handle ɗin ƙofar tayi ta shiga, anan kan sallaya ta samu Ummi najan carbi, durƙusawa tayi ta gaisheta cikin girmamawa, fuska asake Ummi ta amsa, mata. Bata wani jima aɗakin Ummin ba, ta miƙe tsaye, kaitsaye ɗakin Goggo Dada ta shiga, nan ta iske goggo dadan itama najan carbi, cikin girmamawa ta gaishe da goggo dada'n, haka goggo Dada ta amsa mata cikin kulawa da sakin fuska. Koda ta fito daga ɗakin goggo dadan, anan falo suka haɗu da Raleeya, bayan sun gaisane, suka nufi kitchine saboda ɗaura breakfast, Raleeya ne me fere dankali, ita kuwa Zaleeha ferfesu take haɗawa, sai kuma sandwich, aikin suke cikin nutsuwa suna ɗan taɓa hiransu. Koda Ummi ta fito falo, ganinsu a kitchine suna aiki,yasa tayi murmushi, nan kan kujera ta zauna, tare da maida hankalinta ga TV inda take kallon Sunnah tv. Saifuddeen kuwa tunda ya tashi da asuba ya wuce masallaci bai dawo ba sai yanzu, tafe suke Hayatuddeen na riƙe masa saman kekensa, sai zuba yake yana basa labarai kala-kala, ahaka suka ƙaraso falon Ummin. Ummi naganinsu haka ta saki murmushi, har acikin ranta tana godewa Allah daya haɗa mata kan ƴaƴanta, kana yasanya musu soyayyar juna azuƙatansu, wannan haɗin kan nasu shine matakin nasaran rayuwarta. Ƙarasowa gabanta Saifuddeen yayi, cikin body language ɗinsa ya gaisheta, amsa masa tayi tana murmushi. Hayatuddeen ne yazo ya zauna akusa da ita, cikin kulawa ya kamo hannunta yace. "Ummi kinsan me?" dubansa Ummi tayi da kyau, dan duk atunaninta serious magana ce, cikin nutsuwa tace. "A'a saika faɗa." pink ɗin laɓɓansa wanda suke shige dana Hammansa ya lashe, tare da cewa. "Wallahi Ummi ƙamshin girki nakeji tun fa kam mushigo cikin falon nan, tun da ga gate, to ni narasa a ina ƙamshin yake fitowa." ya kare maganar yana ɗan kallon ƙofar kitchine. Murmushi Ummi tayi tare da cewa. "Ehem aikin kenan, to su Raliya ne suke dafa break fast." Murmushi yayi tare da suɗe bakinsa, dan dama yunwa yakeji. Dai-dai lokacin kuwa Zaleeha ta fito daga kitchine din hannunta ɗauke da food flask, lumshe kyawawan idanunsa da suka sauƙa akanta yayi, sosai tayi masa kyau cikin jan rigar saikace wata sarauniya, Raleeya ne ta fito da sauran kayan abincin da suka girka, nan suka shiga jerawa akan dinning table. Ameena ce ta shigo cikin falon, Adeel rungume akan kafaɗanta. Sanye take da uniform ɗinta na aiki tayi kyau sosai cikin shigar nasu. Ƙarasowa cikin falon tayi, tare da durƙusawa ta gaida Ummi. Cikin kulawa Ummi ta amsa, tare da tsare Ameenan da ido, cikin kulawa hankalinta a tashe, tace. "Subahanallahi Ameena me ya samu idanunki haka naga sunyi ja?". Ɗan sadda kai ƙasa Ameenan tayi, murya aɗan sanyaye tace. "Babu komai Ummi, kawai dai mura ne keta damuna jiya kusan kwana nayi banyi bacci ba, saboda tari da atishawa." Kai Ummi ta girgiza cikin tausayawa haɗi da kulawa tace. "Allah sarki, sannu kinsha magani kuwa?" Kaita jinjina alaman "Eh" Hayatuddeen ne yace. "Ayya Aunty Ameena sannu ko." Ɗan murmushi tayi masa tare da jinjina kanta, Saifuddeen kuwa idanu ya zuba mata, yana me mamakin ƙaryar da ta zabga, yanayin yanda yaga fuskarta yasa shi gane cewa kwana tayi batayi bacci ba, shikam yarasa irin kishin Ameena, dan kishine da takeyinsa babu wani dalili. Zaleeha dake tsaye nan kan dinning area, jin cewar Ameenan bata da lafiya ne yasata ɗan ɗago kanta, cikin sakin fuska tace. "Ummu'n Adeel barka da safiya, ya jikin?" Jin muryan Zaleehan yasa ta ɗago dakai ta kalli inda taji muryar Zaleehan na fitowa, wani irin bugawa kirjinta yayi, take taji wani irin masifaffen kishi ya sake rufeta, musamman ma ganin yanda Zaleehan tayi kyau cikin doguwar rigan jikinta, haushi da takaicin Zaleehan ne suka turnuƙe mata zuciya, gudun kada su Ummi su zargi wani abu, yasa ta ɗan danne zuciyarta, murmushin yaƙe, wanda yafi kuka ciwo ta saki, can ƙasan maƙoshi tace. "Yauwa barka, jiki Alhmdlh." Kai Zaleeha ta jinjina cikin sanyin da ta dawo ɗabi'arta tace. "Masha Allah, Allah Yaƙara sauƙi." Kasa amsa mata tayi, dan kuwa wani abune yazo yayi mata tsaye acikin rai, jin muryar Zaleehan acikin kunnuwanta yasa taji kaman ta kurma ihu, ƙasa-ƙasa ta watsawa Zaleehan harara, cikin zuciyarta tace. "Shegen iyayi, koma menene ai duk sanadinki nasamu kaina ahaka, wallahi da ace ina da yanda zanyi Saifuddeen ya daina ganinki acikin gidan nan da nayi, lokacin da bakyanan ai hankali akwance yake, yanzu kuma da dawowarki da shegen farar fuska kaman mayya duk kin wargaza min nitsuwa ta." Ta ƙare maganar tana me sakarwa Zaleehan harara ƙasa-ƙasa, Zaleehan, ko zataji sanyi aranta. Ummi kuwa ganin su Zaleehan sun gama shirya break fast ɗinne yasa tace. "Dukansu su tashi suje suci abinci." Anan kan dinning suka zauna, yauma kamar kullum Zaleeha ne tayi seving ɗinsu, inda take komai nata acikin nutsuwa. Saifuddeen kuwa gaba ɗaya yau yakasa ɗauke idanunsa akan matan nasa Zaleeha'n, tayi matuƙar kyau, ga fresh skin ɗinta dake ta shinning, Ameena kuwa tausayinta yakeji da yanada hali da ya yaye mata wannan kishin ta huta, ahankali yake tauna abincin bakinsa, yana wani irin lumshe ido, sosai yakejin daɗin abincin Zaleeha'n, dan zai iya cewa agidan bayan Umminsa babu wanda yakai Zaleeha iya girki duk da yasan Ameena ma ba tayar bayaba bace. Ameena kuwa gaba ɗaya ko daɗin abincin ma bataji abakinta, cuccusawa kawai take, komai bayayi mata daɗi, saboda zafin kishin da ta sawa kanta, ɗan ɗagowa tayi ta kalli gefen Saifuddeen, dan tun da suka zauna bata ɗago kai ta kalleshi ba, kasancewar har yanzu fushi take dashi. Ganin yanda yake sakin murmushi da kuma yanda ya ke kallon Zaleeha wanda take tauna abincin bakinta cikin nutsuwa, yasa taji gaba ɗaya ranta ya ɓaci, wani irin maƙaƙi ne ya zo maƙoshinta, hakan yasa batasan lokacin da ta ƙware ba, take kuwa tasoma tari, kumburarrun idanunta suka kaɗa sukayi ja. Hankalin Ummi a tashe tace. "Subahanallahi Ameena tarin ne?". Kai ta jinjina alaman "Eh." tana me riƙe ƙirjinta dake mata zafi. Saifuddeen kuwa hannunsa yasa yana ɗan bubbuga bayanta cikin kulawa. Zaleeha da Raleeya kuwa atare suka haɗa baki wajen cewa. "Sannu." kasa amsa musu tayi saboda matsanancin kishi da kuma ɓacin ran dake cinta, Hayatuddeen cikin kulawa yace. "Ayya Aunty Ameena sannu, kisha ruwa kinji." Yafaɗi maganar yana me miƙo mata goran ruwan faro me sanyi. Babu musu ta amsa tasha, saida tasha sosai kafun take kifa kanta ajikin dinning ɗin tana meda numfashi. Ahankali Saifuddeen ya aje spoon ɗin dake hannunsa, tare da ɗanjan kujeransa baya, ƙoƙarin barin dinning area ɗin yake, Ummi tace. "Inakuma zaka ana tsaka dacin abinci?" Ɗan shagwaɓe fuska yayi, tare da sanya hannu ya shafi lafaffen cikinsa alaman ya ƙoshine. Kai kawai Ummi ta girgiza tare da maida hankali ta cigaba da cin abincinta, shikuwa Saifuddeen kai tsaye yafice daga cikin falon. Koda ya fita compound ɗin gidan, nan inda motar Ameena take ya nufa, yana zuwa kuwa yayi sa'a batayi locked motar ba, buɗe murfin motar yayi yashiga, anan ɓangaren me zaman banza ya zauna, tare da jawo ƙofar motar ya rufe. Ameena kuwa jin ta soma dawowa cikin hayyacinta, yasa ta miƙewa tsam, dan batajin za'a iya ƙare cin abincin da ita, tsayuwarta awajen kuwa dai-dai yake da hawan jini ya kamata. Ummi tayiwa saita dawo, tare da ɗansa hannu taja kumatun Adeel dake jikin Ummi'n, dan idan za'aci abinci kullum Ummin ne ke karɓan Adeel ɗin ta ɗaurasa acinyarta. Adawo lafiya Ummi tayi mata, haka ma su Zaleeha, al'barkacin Ummi yasa ta amsa musu fuska asake, jakarta ta ɗauka sannan ta fice daga cikin falon, sukuwa ci gaba sukayi da cin abincinsu. Haka ta fito compound ɗin gidan sam fuskarta babu alaman walwala, kaitsaye wajen motarta ta nufa, tana zuwa kuwa ta buɗe tashiga, ƙoƙarin ajiye jakar hannunta takeyi, idanunta ne suka sauƙa akan Saifuddeen wanda ya zuba mata kyawawan idanunsa, wanda ke masifar tafiya da duk wani tunaninta. Sosai ta ɗan tsorata da ganinsa, amma tunawa cewar fushi takeyi dashi yasa ta shiga ta dake tare da kawar da kanta gefe, can ƙasan maƙoshinta tace. "Lafiya?." Gane abun da tace yasashi girgiza kansa, kana ya gyara zamanshi da kyau yadda zasu fuskanci juna, dubanta yayi da kyau cikin body language dinsa yace. "Wannan itace sabuwar gaisuwar da kika koyo?." Sake haɗe fuska tayi, tare da ɗaura hannunta akan steering motar, ganinsa akusa da ita, da kuma tunowa da irin kallon da yake jifan Zaleehan ɗazu, da tayi yasa taji gaba ɗaya ma haushinsa takeji. Ganin haka yasashi ɗan lumshe idanunsa tare da kamo hannunta ya rumtseshi cikin nashi hannayen, sam baisan menene damuwar mata ba, akan Ameena kuwa bayaso ace ya sani, kwata-kwata baya ƙaunar abun da zai kawo masa matsala arayuwarsa, tabbas ya fahimci cewa tunanin Ameena ƙaramine, dole saiya nusar da ita kuma ya bita a hankali yasan zata gane zata kuma fahimceshi. gyara zamansa yayi akasalance cikin body language ɗinsa yace. "Azamana dake ina iya ƙoƙarina wajen ganin na sauƙe haƙƙin ki dake kaina, bansani ba Ameena, bansan mekikewa fushi ba, bansan me namiki ba, ban kuma san dalilin dayasa kika ɗauki kishi da zafi har haka ba, azamana dake bana cutar dake, ba kuma na musguna miki, kinsani na sani Zaleeha matatace kamar yanda kema kike matata, to menene aibuna dan nashiga wajenta na jima? kada ki manta ba haƙƙinki na ɗauka na kai mata ba, saboda ba ranan girkin ki bane nata ne, ashe kenan banyi haka dan na cutar dake ba, meyasa dole kikeson sawa rai da zuciyarki damuwa? ko kusa banason Ummi ta zargeni da rashin yi muku adalci ku biyun, bana kuma fatan ranan da zanyi rashin adalci atsakanin ku, amma saidai naga kaman haƙurin ki naneman gazawa, akullum ƙoƙarin bayyanar da kishinki afili kike, meyasa Ameena? meyasa bazaki daure zuciyarki ba? tunjiya kike fushi dani batare da wani dalili ba, me nayi miki? faɗamin ina jinki laifin me nayi miki?. " Gaba ɗaya jikinta ne yayi sanyi, hakan yasa ta sadda kanta ƙasa, lokaci guda kuwa saiga hawaye sun kwaranyo daga cikin idanunta, tabbas ita kanta tasani fushin da takeyi dashi bashi da dalili, saboda ba laifi yayi mata ba, bai kyareta ba, bai kuma zageta ba, babu abun da yayi mata asalima ya ninka kulawarshi a kanta ne ita kanta tasan baya son damuwarta, kawai dai zallan kishi ne ke ɗawainiya da ita, har yasa take ganin kaman yayi mata rashin adalci. Ɗago kanta tayi da idanunta wanda sukayi luhu luhu, cikin sanyin murya irin ta rashin gaskiya tace. "Kayi haƙuri, nima bansan me yasa nakejin hakan ba." Ta ƙarashi mgnar tare da manna kanta a ƙirjinshi. Idanunsa yaɗan lumshe tare da cije laɓɓansa, asanyaye cikin body language yace. "Banason irin wannan halin, ina dalilin ta kura kanki da kikayi? kinsa kanki cikin ƙunci, sannan kin kwana kuka, kin tashi kuma kina fushi dani, bayan ban tauye ɗaya daga cikin haƙƙoƙinki dake kaina ba, banason Ummi tafara tunanin cewa ina tauye miki haƙƙi, idan wani abu nayi miki ki faɗamin, kinsa kanki aɗaki kin kwana kuka, saboda kina yarda da abun da zuciyarki da shaiɗan ke raya miki, sannan sun tambayeki kince musu mura ne ke damunki, su mahaukata ne da bazasu gane cewar kuka kikayi ba, ki dubi fuskarki, ki dubi yanda idanunki suka bayyana alamun kuka, meyasa ba zaki nutsu ki maida hankalin ki ba? Meyasa kike haka?". Hawayen da suka zubo daga cikin idanunta ta sharce, murya na rawa tace. "Dan Allah kayi haƙuri." Kansa yaɗan jinjina mata alaman yaji, sannan kuma ta kiyaye, dan abun da tayi ɗin ya sosa ransa, bai kamata ace tana fushi batare da ƙwaƙƙwaran dalili ba, Allah Ma yasani yana iyaka ƙoƙarinsa wajen ganin bai tauye mata haƙƙinta ba. Buɗe murfin motar yayi ya fice, kaitsaye part ɗinsa ya nufa, dan yanaso yaje yaɗan huta. Itakuwa Ameena gaba ɗaya jikinta amace yake, dan tasan bata da gaskiya, gefe guda kuwa ga wani irin soyayyarsa dake ratsa ta, ita har ga Allah tasan Zaleeha batayi mata komaiba kuma itama bawai tsanar Zaleeha takeyi ba, sai dai tana jin kishinta, haka tayiwa motar key, asanyaye ta fice daga cikin gida. Ta tafi tasan in taje wurin aiki ƙawarta Samira zata ƙara kwantar mata da hankali, ita kanta tasan Samira ƙawace ta gari. Acan falon Ummi kuwa cikin nutsuwa suka kammala break fast ɗin, Zaleeha da Raleeya ne suka kimtsa dinning area'n, inda Raleeya ta zuba kwanukan da suka ɓata acikin injin wanke wanke, nan falon Ummi suka zauna suna ɗan taɓa hira. Ganin lokaci na ɗan jane, yasa suka sake komawa kitchine ɗin, lunch suka ɗaura, basu wani yi girki me wahala ba, hakan yasa cikin mintuna kaɗan suka kammala, Raleeya ne ta haye sama dan agajiye take jinta sosai, itama Zaleeha part ɗinta ta nufa, Adeel ɗauke akan kafaɗanta, koda ta isa ɗakinta, akan gado ta aje Adeel ɗin sannan ta jefa masa ɗan ƙaramin pillow dan yayi wasa dashi, kayan jikinta ta rage, sannan ta shiga wanka, koda ta fito wata ƴar riga marar nauyi tasanya, sannan ta haye saman gadon, jawo Adeel jikinta tayi tare da ɗaurasa akan cikinta, ahankali take shafa bayansa, ahaka har bacci ya ɗaukesu. Ahankali yaɗan buɗe idanunsa, wanda suka ɗanyi ja, saboda baccin da yayi, wayarsa dake ɗaure kan bedside ya ɗauka, ganin ƙarfe 12:15 pm yasashi tashi zaune, wheelchair ɗinsa ya jawo tare da hawa kai, kaitsaye toilet ya wuce, wanka yayi ya fito sanye da rigar wanka ajikinsa, ɗan ƙaramin towel ne ahannunsa, yana tsane gashin kansa, koda ya kammala body lotion me daɗin ƙamshi ya shafa ajikinsa, wasu riga da wandon shadda na getzner ya sanya wanda sukai masa masifar kyau, tsab yagama shirya kansa tare da fesa turare, wayarsa da kuma laptop ɗinsa ya ɗauka sannan ya fice daga cikin ɗakin. Kaitsaye part ɗin Ummi ya nufa. Babu kowa a falon Ummin, ko ina shiru, dan tun 11 Hayatuddeen ya tafi school, Raleeya da Ummi kuwa kowa na ɗakinsa. A falon ya ɗan tsaya jim ya ɗanyi dan yasan a irin wannan lokacin Ummi ma bacci takeyi, A hankali ya juya ya fita, a harabar gidan ya ɗan tsaya kamar zai wuce wurinsu Sule sai kuma ya juya ya nufi side ɗinshi da matanshi ƙofar falon Zaleeha ya buɗe ya shiga a hankali yake sarrafa keken nashi, shiru falon nata sai sautin AC da kuma karatun ƙur'an da ta saka wanda yake tashi a hankali, kamar zai juya ya fita kuma sai yaji zuciyarshi nayi mishi jagora zuwa cikin ɗakin nata, a hankali ya tura ƙofan, tare da sarrafa kekenshi cikin nitsuwa ya isa tsakiyar ɗakin, ido ya zuba mata ganin yadda take konce ruggume da Adeel, idonshi ya lumshe tare da fidda sassanyan numfashi, a ranshi yace. "Uhumm to wannan konciya a bakin gado ai juyi ɗaya zakiyi ki yarmin da yaro ƙasa ki fasa min kanshi." dan gaba ɗaya ƙarfin konciyar nata a bakin gadon ne, sarrafa kekenshin yayi a hankali ya iso bakin gadon, cikin nitsuwa yasa hannu ya tallafi Adeel tare da ɗauke shi daga kan ƙirjinta, ya ɗan roggofo da niyar kontar da Adeel ɗin bayanta kenan, cikin bacci taji kamar yaron zai faɗo ba tare data buɗe ido taɓa tayi maza ta ruggumeshi, madadin ta ruggumi ɗan sai ta ruggumi uban, da sauri ya kontar da Adeel daketa bacci sai, ido ya ɗan zaro jin yadda ta ruggumeshi gam a jikinta, idon ya zuba mata, yana mai maganar zuci. "Wayyo Allah zata lalata min al'wala". Ita kuwa Zaleeha cikin baccin ta fahimci wannan ba Adeel ta rugguma ba, da sauri ta buɗe idanunta tare dayi sauri ta sakeshi, ido ta zazzaro kana ta mirgina baya, da sauri ya riko hannunta ganin zata mirgina kan Adeel, cikin mayen bacci tace. "Bacci zanyi". Ido ya tsura mata tare da jujjuya mata su kana ya mata mgna da yarensu na kurame. "To na hanaki baccin ne, daga zuwana kin shaƙoni kin ruggume." Ya ƙare kwatance dayi mata nuni da rugguma, baki ta ɗan tura tare da cewa. "Ni ai Adeel nake son rugguma ba kaiba". Sake hannunta yayi tare da mata alamun. "Karya kikeyi". ita dai gefe ta koma ta konta tasa Adeel a gaba, shi kuwa juyawa yayi ya fita dan baison worwore al'walanshi. Yana fita ta maida ajiyan zuciya tare da shafa kan Adeel kana sukaci gaba da bacci su. Shi kuwa suna fita shida Sule kasuwa suka wuce, Nan ya zazzagaya shagunanshi dan duba hada-hadarsu dan sun kusa suyi zaman lissafin cinikin shekara da ribar da suka shigar da sanin zakkar daya dace su fidda, Sai da ya gama zagayawa shida Ahmad da Mudassir kana da Warisu. Sannan ya wuce, ya gaggaida su Alhaji Yawale, Ba miskila, Alhakin Isha, Alhaji kabiru, uban gidansu na dilan leda Alhaji Aliyu, domin baya mance duk matakin da yake ciki a rayuwa sanadin pure water da leda dasu magine ya kai wannan matsayin. Daga kasuwa ofishin su na Jonapwd ya wuce, yana shiga ciki ana ƙoƙarin shiga sallan azahar, nan ya shiga jam'i akayi salla. Bayan an idar ne ya wuce ofishin Ishaq, tare da jagoranci Sani, cikin yadda suka saba mgna yake mishi bayanin Malam Ishaq yana cikin G.S.U sai dai yanzu zai dawo, aiko suna nan zaune Ishaq ya shigo, Murmushi yayi tare dabin gefen table ɗinshi ya matso kusa da kujerar da yasan nan Saifuddeen ke zama hannu ya bashi tare da cewa. "Ango mai mata biyu, sai yau aka tuno mu?". Hannunshi Saifuddeen ya kama tare da rubuta mishi, "Kai Isha banda sharri last week mafa nazo dani akayi mitin". Murmushi Ishaq yayi lakacin daji saƙon aminin nashi, gyara zama yayi kana yace. "Eh ai yanzu zuwanka sati-sati ne." Murmushi sukayi baki ɗaya kana sukaci gaba da hira, A nanne Saifuddeen ke cewa Ishaq ya kamata fa ya tsaida batun aure duk abokansu sunyi aure sai shida Mudassir suka rage, a nan Ishaq ke ce mishi su shirya shima nashi nan tafe dan sun gama dai-dai tawa da Rashida ƙawar Zaleeha, sosai Saifuddeen yaji daɗin haka dan yasan Rashida tanada mutumci da kima, nan dai sukayi tashan hirarsu ta abokai. Sai da yamma ya baro wurin Ishaq kana, ya nufi gida. A gidan kuwa tuni Zaleeha da Raliya sun gama aikin abincin dare. Amina ma ta dawo wurin aikinta Duk suna zaune a falon Ummi sunata ɗan taɓa hira. Duk da Ameena najin zuciyarta babu daɗi dan har yanzu data dawo dataje ɗakinta saida taji ƙamshin turaren Zaleeha a jikin rigar Adeel amman ta danne. Shi kuwa Saifuddeen kai tsaye side ɗinsu ya wuce ganin magrib ta gabato, ruwa ya ɗan watsa kana ya zura jallabiya ya fito ya nufi masallaci, Hayatuddeen na biye dashi a baya, a bakin gate suka samu Ahmad ma nayin al'wala daga nan suka wuce masallaci. Sune basu dawo gidaba saida akayi sallan isha. Suna dawowa suka zauna duk sukaci abinci, daga nan Ahmad ya haura sama dan a matuƙar gajiye yake, in ya ɗanyi bacci kafin Raliya ta gama hiranta ta dawo zaiji dama-dama ya samu raya daren Hira suke ɗanyi yayinda Zaleeha ke zaune ƙasa kan carpet, tasa Adeel a kan cinya tana yanke mishi farce. Ameena kuwa ta zuba musu ido,har ranta tasan ba soyayyar ganin ido Zaleeha keyiwa ɗanta ba, to amman ita ta kasa jin ta dena kishin Zaleeha a ranta, ganin yadda tayi zugum tayi tagumine yasa Ummi ta kalleta cikin kulawa da nitsuwa tace. "Ameena zo". Tana faɗin haka ta wuce tayi cikin ɗakin ta. Cikin sanyi Ameena ta miƙe tabi bayanta, a bakin gado ta samu Ummi na zaune, cikin yin ƙasa da kai ta ƙaraso cikin ɗakin,inda Ummi ta nuna mata nan ta zauna sunkuyar da kanta tayi a hankali tace. "Ummi gani". ido Ummi ta zuba mata sai kuma ta gyara zama cikin kulawa da son gane matsalar Ameena tace. "Ameena meke damunki?". A hankali ta jujjuya kai alamun babu. Cikin kula Ummi tace. "Kinga Ameena kada kiyi min haka,kinji ni matsayin ƴa na ɗauke ku,muddin kinada matsala ki gaya min, in inada damar yaye miki ita zan yaye miki ita in kuma bani da dama, zan tayaki da addu'a da shawarwari, dan haka gaya min meke damunki yadda bazan so Ahmad ya tozarta Raliya ba bazanso Saifuddeen ya tozar takuba, gaya min me yayi miki,ni nasan na isa dashi". Cikin rauni da sanyin murya tace. "Babu abin da yamin Ummi,wlh Hamma bai min komaiba". cikin gamsuwa Ummi tace to menene matsalarki meke damunki?". Kai ta ɗan rausayar tare da cewa. "Ba komai Ummi wlh Hamma bai min komaiba." Cikin kula Ummi tace. "To Alhamdulillah dan ni shi na zarga, tunda kuma kince bai miki komaiba, shikenan, amman ki saki ranki ki dena sa damuwa a ranki, bana son ganin kina tagumi kinji ko tashi kije kuyi hiranku da ƴan uwanki". Cikin jin daɗi da ganin daraja da kimar Ummi da mijinta ta miƙe ta fita tana mai yin mgnar zuciya. "Ameena ki sassauta wa kanki kishi bayin Allah nan basu rageki da komaiba wacce kikeyi dominta ma bata saniba". A hankali ta fito falon gefen Zaleeha ta zauna, cikin kula Zaleeha ta kalleta tare da cewa. "Ummu Adeel bashi yasha nono naga yanata mutsu-mutsu". Murmushi ta ɗanyi kana ta ɗauke shi ta bashi nono. Shikuwa Saifuddeen ido ya zuba musu a yadda suke jeren, hamdala yakeyi da godewa Allah daya azirtashi da matan da ko wacce da nasabarta, murmushi yayiwa Ameena tare da jinjina mata kai alamun tayi kyau. kauda idonta tayi dan sai take ga kamar ba'a yayi mata ya za'ayi yace tayi kyau bayan ga Zaleeha kusa da ita bata san cewa kowa da irin sirrin kyanta ba. ganin yadda ta tsuke fuskane ya sashi jin ba daɗi. "To wai me nayi mata,ko dai ta daina so nane yasa duk abinda nai mata sai ta juyashi marar daɗi". Yana cikin mgnar zucin yaga ta miƙawa Zaleeha Adeel ta miƙe ta fita, da ido ya bita, Raleya ce ta kalleta cikin kula tace. "Aunty Ameena har zaki shiga?". Kai ta gyaɗa mata, jin Hayatuddeen yace. "To saida safe Aunty Ameena". Yasa ta ɗan juyo tare da cewa. "To auta Allah ya bamu al'khairi". Baki ya tura tare da cewa. "Wai auta nida har inada yara sai kuyi ta cemin auta yanzu in Adeel ya fara mgna shima ba sai yabi bakinku yace min autanba". Murmushi tayi ta fice, Zaleeha kuwa dariya ta ɗanyi tare da cewa. "Ya isa ya cema auta ai kai Appinshi ne". miƙa yayi tare da konciya bisa kujerar da yake. Amina kuwa tana shiga ɗakinta bakin gado ta zauna tanajin tana son danne zazzafan kishinta kenan yanzu yauma a ɗakin Zaleeha zai kwana, kwanciya tayi tare da kife kanta bisa pillow ta saki nannauyan numfashi. Ita dai ALLAH ya sani da Saifuddeen zai saki Zaleeha wlh da tanaso da kuma tafi kowa jin daɗi. ɗago kanta tayi ta ɗauki woyarta jin alamun saƙo ya shigo mata. buɗe saƙon tayi ganin sunan Abban Adeel hannu tasa ta share hawayenta lokacin data karanta abinda ya turo mata. "Kin tafi kinje kin fara kukan ko?." Da sauri ta tura mishi amsa. "A a wonkafa zanyi". ajiyan zuciya ta sauƙe sanda taga saƙonshi. "Kin tabbata ba kuka kikeyi ba?". Da sauri tace. "Eh." "Yauwa Ummu Adeel haka nake son ji,kinji ko kada in sake ganin kina min kukan da babu dalili,in laifi nayi miki ki gaya min banfi ƙarfin in baki haƙuri ba". Wannan text ɗin yayi masifar sata jin daɗin, sai kuma shaiɗan ya kisa mata. "Ke sokuwa kika san me yake gaya mata ita kuma?". Take ta kife kanta taci gaba tubka da worwora amman tana mai yiwa kanta faɗan ta zauna lfy da mijinta da abokiyar zamanta. A can falon Ummi kuwa, yana gama text ɗin da yakeyi ya fice ya nufi side dinshi dan zaije yayi shirin bacci. Ita kuwa Zaleeha bacci takeji sosai to amman tsoro tafiya da Adeel takeji tana son tafiya dashi tana kuma tsoro sabida kada Abbanshi yaje karɓanshi ya mata tijara irin ta jiya shiyasa take shirin kontar dashi a nan ta gudu ta barwa Raliya shi, ai in bata tafi da ɗanshiba bazai bitaba. Raliya ce ta miƙe tare dayi musu saida safe ta haura sama, Ummi ce da yanzun ta fito tare da Raliya ta kalli Zaleeha dake ƙoƙarin kontar da Adeel tace. "A a Zaleeha har yanzu kina nanne, dare yayi ai sha ɗaya saurafa, tashi ki ɗauki coffee ɗin Babana ki kai mishi". Da ƙarfi taji cikinta yayi wani ƙugi,wannan shine anyi gudun gara an tadda zago, amman ba halin yiwa Ummi musu bare gardama, a hankali ta miƙe goya Adeel tayi sannan ta ɗauki tray ɗin da aka shiryawa Hamma Saif ɗin coffee ɗin shi, jiki a mace tayi musu saida safe ta juna ta nufi side ɗinsu. A hankali ta tura ƙofar falonshi ta shiga da sallama, cikin nitsuwa take taku ta shiga falon nashi da bata taɓa gangancin shigaba, ganin ba kowa yasa tayi sauri-sauri gudu-gudu ta ajiye mishi tray ɗin bisa dinnin table ɗin shi, ta juya ta fita da sassarfa kamar wacce za'a kama ko tsarin falon bata gama ganinba. Shi kuwa Saifuddeen tuni yayi wonka shi ya shirya cikin wasu tattausan riga da wondo na bacci masu kalar sarararin samaniya, ya fesa turare yayi ras dashi sai ƙamshi yakeyi. Daga falonshi kai tsaye ɗakin Ameena ya nufa. A kan gado ya hangota tana zaune tasa kanta cikin guiwowinsa bisa alamu tunani takeyi, jin motsinshi ne yasata ɗan ɗagowa ta kalleshi, sai kuma ta meda kanta ƙasa da alamun bata son ganinshi ne ko haushinshine ma takeji bata dai son ta gaza danne kishinta ne. shi kam lamarin Ameena ya tsaya mishi a rai don ya rasa me zai mata ta saki ranta, a hankali ya iso bakin gadon hannunshi ya miƙa mata alamun tazo, cikin jin haushin sa dan gani take ai duk abinda yakeyi mata zaiyiwa Zaleeha, hararanshi ta ɗanyi cikin son danne kishinta tace. "Dan Allah ka fitarmin a ɗaki ka tafi can wurin maikai saida safe". Kanshi ya jinjina mata kana ya zuba mata ido. Da sauri ta sauƙo kan gadon jiyo muryar Zaleeha na sallama a falon ta. Hannunta tasa ta share hawayenta tare da fitowa, cikin kirsa take kallon Zaleeha sama da ƙasa, murmushin da bai kai zuci ba tayi jin Zaleeha na cewa. "Ga Adeel kar ya tashi dare-dare yayi ta kuka". Motsowa tayi jikin Zaleeha da ta ɗan sunkuya ta kunce abun goyon, cikin kirsa tace. "Ae kam ya iya rigama kamar na Abbanshi,shima gaya can a ɗaki yanata min rigama, nace inji da ɗanka inji da kai". Murmushi Zaleeha tayi tare da cewa. "Saida safe". Harara ta mannawa Zaleeha tare da cewa. "Allah ya bamu al'khairi". Amin Amin Zaleeha tace tare da ficewa ta koma side ɗinta. Kai tsaye bathroom ta shiga,wonka tayi soso da sabulu kana tazo ta kimtsa cikin tattausan rigan baccinta mai tsawo har guiwa. Kasancewar tana tsoron duhune yasa ta bar wuta ɗakin a kunne, konciya tayi bisa gadonta tare da jawo borgo ta shiga ciki ta konta tayi lib tana sauƙe numfashi dan tana tare da gajiya. Ita kuwa Ameena tana komawa cikin bedroom ɗinta gado ta hau cikin jin ba daɗi ta juyo ta kalli Saifuddeen baki ta tura tare da cewa. "To sai ka tafi ai tunda ga ɗana an dawo min dashi sai kuje can kuci juna". Zuwa yanzu dariya Ameena ke bashi dan fushinta mara daliline, dan haka juyawa kawai yayi ya fita. Falonshin ya shiga nan ya samu coffee ɗinshi, shida kanshi ya haɗawa kanshi dai-dai misalin abinda zai sha, saida ya sha sannan ya ɗan zaro wayarshi a saman lips ɗinshi yace. "Shabiyu harda kwata". Lumshe yayi lokacin daya nufi side ɗin zali a ranshi yace. "Itama tanada haƙƙi a kaina dole in san ya ta kwana ya ta tashi. A hankali yake sarrafa kekenshin har ya isa bakin ƙofar ɗakinta mamaki yayi ganin yadda ta bar wutan ɗakin a kunne, cikin nitsuwa ya tura ƙofar ya shiga, ita kuwa Zaleeha bacci ya ɗan fara fizgarta shiyasa bata san da shigowanshi ba, a hankali ya isa bakin gadon. Da sauri Zaleeha ta buɗe idanunta jin mitsin mutun wuƙi-wuƙi tayi da idanunta ganin shine, da sauri, ta ɗan matsa gefe cikin tsoronshi da muryar bacci tace. "Menene? Nifa na maida Adeel wurin Mamanahi,baya wurina! Kuma na kai maka coffee ɗinka falonka!". ta ƙarashi magar cikin tanayin rau-rau da idanunta, dan ita batama san lokacin data meda Adeel yana ɗakin Ameena ba. Baki shine ya ɗan taɓe tare da buɗa kafaɗu shi kana ya mata alama. "To an ce miki Adeel nazo karɓane? Ko dai bani da enci da damar shiga ɗakin ne sai kin bani izini ne?". Ya ƙarashi maganar cikin alamun tambaya. Kai ta karyar bisa kafaɗa cikin sanyi tace mishi. "A a". Kanshi ya jinjina tare da mata alamun. "To naza kwana a ɗakin nan ɗinne". A take sai ga hawaye shar-shar a fuskarta cikin rauni da sanyin ta tace. "To shike". Sai kuma ya zuba mata ido ganin ta ɗauki pillow ta sauƙo daga kan gadon da alamun zata fita ne. Da sauri yasa hannunshin ya fizgota kana ya ajiyeta kan gadon a gaban shi, ya zama suna fuskantar juna, cikin yarensu ya mata magana. "Ok yanzunma can cikin garding ɗin zaki koma ki kwana ne?". Kai ta jujjuya mishi kamar ƙaramar yarinya murya can ƙasa tace. "A a". Cikin tsareta da ido yace. "To ina zakije ki kwana? Sannan ni kurane da in na shigo kike gudana gaba ɗaya jikinki na rawa". Ya ƙarshe magar da mata alama da kyau yadda zata gane. A hankali tace mishi. "A a". Tare kuma da girgiza kai alamar a a yadda zai gane. Cikin bada ubarni da yaransa yace mata. "To hau ki kwana". Ba musu ta haura kan gadon ta dugungune wuri ɗaya. Cikin kula yake kallon yadda gaba ɗaya jikinta ke karkarwa, a hankali yake mata misali da cewa. "Nifa babu abinda zan miki,ki nitsu ki konta kiyi baccinki, sai da safe". Kai ta gyaɗa mishi tare da sauƙe nannauyan ajiyan zuciya. Shiru yayi yana ƙare mata kallo gaba ɗaya ta rame, fuskarta tayi fiyau, kuma har yanzu akwai damu da jimamin rashin ƴar uwarta. Da wannan tunanin ya juya ya fita bayan ya kashe mata wutan ɗakin, sabida bata cikin yanayi mai daɗin da zata iya fahimta ko jin daɗi wani abun da zaiyi mata shiyasa bari dai ya ɗaga mata ƙafa. Washe gari da, kuwa ranar Ameena zata karɓi Saifuddeen domin ya gama kwanakin shi biyu na ɗakin Zaleeha. Da yamma Ummi na zaune a ɗakinta tana kwaɓa lallen gargajiya da takeso tasa a daren yau ɗin Zaleeha ta shigo gefenta ta zauna, cikin nitsuwa ta gaidata, ganin tayi shirune yasa Ummi cewa. "Kinyi shiru Zaleeha me kikeso?". Cikin sanyin yanayin da rayuwarta ta dawo ciki tace. "Uhum Ummi dama gobene za'ayi sadaka bakwai ɗin Adda Maryam, kuma ina son zuwa Ummi a gayawa Hamma Saif mana dama ina son zuwane in na samu". Murmushi Ummi tayi tare da cewa. "To Zaleeha ni zan tamɓayan miki,keda mijinki kije ki tambaye shi da kanki kinji ko karkiyi haka". Cikin nitsuwa ta gyaɗa kanta alamar to kana ta miƙe ta fita, binta da ido Ummi tayi a fili tace. "Uhmmm Saifuddeen ya sawa yarinyar nan tsoronshi, da shakkarsa ban san meyasaba, yarinya duk ta zama shiru-shiru abar tausayi". Ita kuwa Zaleeha yau tunda safema bata kuma ganin Hamma Saif ɗin ba, dan yau tunda safe ya tafi Office ɗinsu na SS. Dan sun samu wani bayani kan Dalla ya kusa dawowa. To ta dai sa a ranta zata daure ta tambaye shi koda zai gwatsaletan ne. Gab da magriba ta fito daga falon Ummi kenan tana ruggume da Adeel tazo gab bakin kofar shiga side ɗinsune tayi kiciɓis dashi. yayinda Ameena kuwa tana falon Ummin dan yanzu ta dawo A hankali ta ɗan raɓa gefe, shi kuwa hannu ya miƙo mata alamun ta bashi Adeel ba musu ta miƙa mishi Adeel, cikin sanyi tace. "Ina wuni ya aiki?". Kai ya gyaɗa mata alamun Alhamdulillah, shafa kan Adeel yayi tare da miƙo matashi ya mata alamun. "Je ki ajiyeshi kiyi salla lokaci yayi kar kije ki tasashi gaba kuyita dariya." Kai ta jinjina kana a hankali tace. "Uhum Hamma Saif". Ido ya zuba mata dan duk duniya ita ɗaya yaji tana kiranshi da wannan sunan". Ganin tayi shirune ya sashi ɗaga mata hannu alamun lfy dai ko? Cikin inda-inda tace. "Uhum dama gobene za'ayi sadakan bakwai ɗin Adda Maryam to kuma ina son zuwa in ka amince ka yerje min?". Karo na forko kenan da Zaleeha ta nemi izininshi akan abu, shiyasa yaji kanshi tamkar wani sarki, ita kuwa ganin yayi shirune yasa ta rumtse idanunta da suka cika da hawaye, Cikin sanyi tace. "Dan Allah kayi haƙuri, ka bani izinin zuwa inaso inje inga ƴan uwana". Kanshi ya jinjina mata alamun "Allah ya kaimu". Cikin jin daɗi tace Amin Amin kana ta sunkuyo ta karɓi Adeel sannan ta wuce tayi ciki, shi kuma ya wuce ya nufi ƙofar gida. Amina kuwa dake tsaye bakin falon Ummin ta cika tayi fam tuni sheiɗan ya shiga ingizata, sunkuyowan da Zaleeha tayi ta bashi Adeel ɗin nan sai takega kamar, sumbatar ta Saifuddeen yayi, hakan kuma sheiɗan ya raya mata. "To ai dai duk iyayinta yau dai kam girkinkine, tunda taci kwana biyunta ai sai ta bar miki mijinki yau kam". Wani irin kishi da tsanar Zaleeha ne suka cika mata ciki da zuciya. gaba ɗaya ta hautsine a haka ta nufi side ɗinta dan yin sallan magriba. Koda sukaci abincin dere suka ɗanyi hira, ganin yadda Ameena ke watsa mishi harara ya sashi sanin lallai yau akwai aiki, A can gidan Baba malam kuwa, Ziyada ne ke zaune gaban Baba Malam a cikin falonshi sai ya Ahmad da Malam Adam , da kuma ya Ameenu, shiru sukayi baki ɗayansu, cikin tattausan lafazi Baba Malam ya kira Ziyada. "Ziyada". Cikin nitsuwarta irin ta Adda Maryam tace. "Na'am". A hankali yace. "Wata al'farma nake nema a wurinki in Allah yasa kin amince zanji daɗin hakan, Amman fa bawai umarni nake bakiba al'farmace nake nema". Ɗago kanta tayi wanda ida nunta tuni sun cika da kwalla cikin sanyin murya tace. "Baba malam al'farma kuma?". Kai ya gyaɗa mata alamar eh, da sauri tace. "A a baba ka bani umarni kawai, ko wanne irine zan bishi domin nasan bazaka sani yin abinda ya saɓawa shariya ba". Cikin jin daɗi ya fuskaceta da kyau, murya a tausashe yace. "Ga ɗan uwanki Ameenu mijin yayarki Maryam, ko zaki amince in aura masa ke in mishi madadin Maryam dake? Kije ki zauna ki raini ɗan ƴar uwarki?." Kai ta sunkuyar hawaye na zuba murya na rawa tace. "Na amince Baba Malam na yarda in dai Ya Ameenu ya amince nima na amince". Wani irin sassanyan ajiyan zuciya Baba Malam ya sauƙe, Ya Ameenu kuwa ido ya zuba wa Baba Malam cikin tsananin mamaki da kaɗuwa, Ya Ahmad da Malam Adam kuwa sosai sukaji daɗin wannan batun. Shiru ya Ameenu yayi jin Baba Malam na ce mishi. "Ameenu ga Ziyada na baka ita, gobe da asuba in sha Allah za'a ɗaura muku aure in ka amince ta koma ɗakin ƴar uwarta". Kai ya jinjina hawaye na zuba yace. "Nagode Baba Malam Allah ya saka da al'khairi ya jiƙan Maryam". Amin Amin sukace baki ɗayansu kana Baba Malam yace Ziyada ta tafi cikin gida. Nan suka ajiye batun ɗaura auren gobe da asuba. Ƙarfe tara dai-dai Mamy ta shigo falon Mama ta sanar mata kiran Baba Malam, wanda tunda ta dawo gidan bai kulata ba, Don tuni ya dai-dai ta larin aurenshi da ita. Jiki a mace ta nufi side ɗinshi. Ganin baya falo ne yasa tayi sallama a bakin ƙofar bedroom ɗin shi, A hankali yace mata. " Wa alaikissalam,shigo". Jiki da zuciyarta cike da kunya da nadama da dana sani ta shigo. Gefen ta zauna cikin zubda hawaye tace. "Gani". Ido ya zuba mata domin gaba ɗaya ta zama wata jibiri-jibiri ta zama abar tausayi. kanshi ya kawar tare da cewa. "Batun auren Ziyada da Ameenu na haɗa kuma duk sun amince, gobe da asuba za'a ɗaura auren me kikace a kai". Cikin sanyin murya da nadama tace. "Allah ya sanya al'khairi ya basu zaman lfy, ya kuma jiƙan Maryam da Rahma". Cikin mmki da tsananin jin daɗi yace. "Amin Amin,kin amince kenan ba fitina da masifa?". Cikin jin kunya tace. "Eh". Gyara zamanshi yayi tare da cewa. "To sai kuma batun yayarki Ruda, bana son zuwanta gidana". Da sauri tace. "Nima nace mata bana so". Kanshi ya jinjina tare da cewa. "To Allah ya kyauta ya shirya min ke". Amin Amin tace cikin jin kunya, kana ta miƙa zata fita, jin ya kamo hannunta ne yasa ta koma gareshi. Ƙarfe goma duk suka watse kowa yayi side ɗinshi, Koda ya gama shirin baccinsa, a tsastsaye ya leƙa Zaleeha yayi mata saida safe dan tunima ita ta fara bacci ji shine yasa ta ɗan ɗago ta kalleshi ganin ta zarro mishi ido alamun mmki ne yashi mata alamun ta konta saida safe. Yana fita ta meda kanta ta konta taci gaba da baccinta. 11 dai-dai Saifuddeen ya shiga ɗauki Ameena, hasken wayarshi ya kunna dan tuni ta kashe wutan ɗakin dan bata da niyar zuwa ɗakinshi. kan gadon ya hau ya konta tare da sa hannu ya ɗauki Adeel ya maidashi kan gadon shi dake kusa da nasun. Matsowa jikinta yayi tare dasa hannunshin ya juyata suna fuskantar juna. Da sauri ta sake komawa ta juya ta bashi baya....! By *GARKUWAR FULANI* [18/09, 8:38 pm] +234 703 367 5916: Ngs,eɗɗ Sake ɗan mirgino ta yayi, tare da sanya hannunsa ya kama waist ɗinta, da sauri ta ja baya, tare da ɗauke hannunsa daga jikinta, fushi takeyi sosai dashi, saboda haka batajin zata iya biye masa awannan daren. Asanyaye ya kuma kai hannunsa yana ƙoƙarin cire mata rigar baccin dake jikinta, ƙanƙame jikinta waje ɗaya tayi, tare da riƙe rigartata, fuska ta haɗe sosai tare da ɗan girgiza masa kai alaman bataso. Hannunsa ya zare daga jikinta, tare da zubawa bayanta idanu, dan dama ta bashi baya ne, shi kam yarasa meke damun Ameenan kwana biyu, yasan duk bai wuce zafin kishi ba. Ɗan lumshe idanunsa yayi, tare da gyara kwanciyarsa, cikin ransa yace. "Bazan taɓa takura miki ba, zanjira harsai kinyi ra'ayi dan kanki." Ameena kuwa ranta ne keta ƙuna, baki kawai take ta cijewa, da ace kuka zaizo mata ma da tayi, ko zata ɗanji salama acikin ranta da zaran ta rufe idonta sai taga lokacin da Zaleeha ta sunkuyo kanshi dan bashi Adeel ita kuwa a zatonta kissing ɗinta yayi. Suna ahaka bacci ya ɗaukesu dukansu. Washegari kuwa da sassafe ta wuce wajen aiki, ko gaisuwa ma, haka tayi masa fuskarta babu wata cikakkekiyar fara'a. Shidai idanu kawai ya zuba mata, dan yasan fushin nata na babu gaira babu dalili ne. Zaleeha kuwa ita da Raleeya sukayi komai na breakfast, kusan atare suka yi break fast ɗin inbanda Ameena da tatafi wajen aiki. Suna kammalawa kuwa, Zaleeha ɗaki ta wuce ta kwanta, dan anjima kaɗan ne tafiyarsu gidan Baba Malam. Saifuddeen kuwa anan falon Ummi suka zauna shida su Hayatuddeen yana ƙoƙƙofanshi kan sabon abokinshi da tuni ya dasa mishi ayar tambaya, kuma tuni ya liƙa bincikansa kan wayar ƙanin nashi. hira sukayi sosai, kasancewar yau ɗin jumma'a ne yasa dukansu ba da wuri zasu fita ba, Hayatuddeen kamma sai kusan ƙarfe 11 yake da lecture, nan ma kafin ƙarfe 2 zai dawo bawai wani jimawa zaiyi ba. Ƙarfe 12 Zaleehan ta dawo sashin Ummi, dan ɗaura abincin rana, zuwa lokacin kuwa su Saifuddeen din basa falon, kowa yayi ɓangarensa, dan shirin masallaci, ita da Raleeya ne sukayi lunch ɗin, sannan suka juye acikin manya manyan food flasks. Koda suka kammala ɗaƙi ta koma, inda tayi wanka, tare da ɗauro alwala'n sallan azahar tana tunanin zaman gidan na mata yawa da zata samu dai a barta ta koma aikinta, to amman ta inama zata fara maganar. Can ɓangaren Saifuddeen kuwa, kwalliya yasha cikin wata haɗaɗɗiyar shadda ƴar mita me kyaun gaske, wacce take da kalan dark greeen, sosai tayi masa kyau, ga kuma hulan zanna bukar daya kafa akansa, wani tsadadden agogo ya ɗaura atsintsiyar hannunsa, sosai yayi kyau, yayinda sajen fuskarsa ta kwanta lub-lub, turare ya fesa, wayansa kaɗai ya ɗauka, sannan ya fice daga cikin ɗakin, bayan yasawa ƙafansa takalma flat shoe irin na maza me tsadan gaske. Anan compound ɗin gidan ya haɗu da Ahmad wanda ya jiƙu da ƙyau shima cikin shigar shadda milk colour, atare suka wuce masallaci. Zaleeha kuwa koda ta fito daga wankan sama sama taɗan shafa lotion ajikinta, wata haɗaɗɗiyar powder ta shafa akan fuskarta, wanda tayi mata kyau sosai, kajol da kuma lipstick kawai ta shafa, bata wani cika kwalliya akan fuskar tata ba, wani haɗaɗɗen riga da sket na atamfa tasanya ajikinta, sket ɗin irin pieces ɗinnan ne, yayinda rigar kuwa ta kasance fitted, sosai kayan sukai mata kyau, kasancewar atamfar nada kalan ja ajiki, yasa ta yafa wani haɗaɗɗen mayafi me kalan ja, wani ɗan hill ta sanya aƙafanta me masifar kyau, waya da kuma ɗan jakanta ta ɗauka, tayi kyau matuƙa sai faman baza ƙamshi take, kallon kanta taɗanyi amadubi ta numfashi ta ɗan sauƙe ita kanta taga ramarta. Juyawa tayi cikin nutsuwa, ta fice daga ɗakin nata, kai tsaye sashin Ummi ta nufa, zuwa lokacin kuwa har sun dawo daga masallaci. Saida Numfashinsa yakusan ɗaukewa alokacin daya ganta, tayi masifar kyau, gashi skin ɗinta ya ƙara haske. Ummi ne tayi musu fatan al'khairi da kuma adawo lafiya, sannan suka fita, yana gaba yana me sarrafa wheelchair ɗinsa, ita kuma tana biye dashi abaya. Haka suka ƙaraso har wajen mota, Sule driver ne ya buɗe musu motar cikin hanzari suka shiga. Anan gidan baya suka zauna. Cikin nutsuwa kuwa Sule driver ke tafiya dasu, gaba ɗaya daddaɗan ƙamshin turarensu ne ya cika cikin motar, hakan kuwa ya bada wani irin yanayi me daɗi. Ɗan lumshe idanunta tayi tare da jingina bayanta da jikin kujera, shikuwa Saifuddeen wani aiki yake shiyasa gaba ɗaya hankalinsa nakan wayarsa ƙiran Samsung S20. Ahaka suka isa gidan Baba Malam ɗin, jin tsayuwar motar ne yasa duk suka ɗago idanunsu, wani ajiyar zuciya Zaleeha ta sauƙe, sannan ta buɗe murfin motar ta fito, Saifuddeen kuwa Sule driver ne ya buɗe masa murfin motar ya fito, bayan ya ware masa wheelchair ɗinsa. Kusan atare suka jera, sashin Baba Malam ɗin suka nufa. Zaleehan ce tafara tura ƙofar falon ta shiga bakinta ɗauke da sallama. Baba Malam, da kuma su Mamy sai Ya Ahmad da kuma Ya Ameenu ne zaune afalon, can gefe kuwa wasu ayarin mutane ne wanda aƙalla zasu kai su 15, Ciki kuwa hadda Uncle Solomon da kuma matarsa Elizabet, ga kuma Baffa wato baban Aisha. Cike da mamaki Zaleeha ta ƙaraso cikin falon tana ɗan rarraba idanunta, ganin Baffa yasa tace. "Laa Baffa kaine agarinmu?" ɗan murmushi Baffan yayi tare da cewa. "Ƙwarai kuwa ƴata nice." Nan ta durƙusa har ƙasa ta gaishesa, sannan ta gaishe dasu Baba Malam, wannan karon kam har Ya Ameenu ta gaisar kuma ya amsa mata. Ƙarasowan Saifuddeen cikin falon ne yasa, Baba Malam faɗaɗa fara'ar dake kan fuskarsa, cikin kulawa haɗi da mutuntawa ya tarɓi Saifuddeen ɗin. Cikin girmamawa kuwa Saifuddeen ɗin ya gaishe dasu Baba Malam ɗin, harma da Baffa'n Aisha. Haka Baffan Aisha ya amsa fuska asake yana yabawa da kyau haɗi da kwarjinin yaron. Anutse kuwa Saifuddeen ya gaishe dasu Mamy da kuma Mama. Fuska asake duka suka amsa masa, Mama kam sai faman sunne kai take, dan kunyar Saifuddeen ɗin takeji, uwa uba kuma kwarjinin da yake dashi. Zaleeha kuwa bayan ta gaishe dasu Mama, kusa da Ya Ahmad ɗinta taje ta zauna, zuciyarta fari tas, wani irin dadi takeji, musamman ma da take hango fariniki akan fuskar gaba ɗaya ahalin nata. Bayan sun ɗan nutsane Baffa keyi mata bayanin cewa. "Ai su Solomon musulunta sukazo yi, dan zamanta awajensu yasa sunji kwaɗayi da sha'awar addinin musulci, sun kuma gano cewa shine haske dake haskaka rayuwar duk wanda ke cikinsa, saboda haka suma suna so su musulunta, zasu musuluntan ne kuma ba saboda kowa ba, saidan suma su samu dacewa da rahamar Allah, sukuma samu daman ɗanɗana ni'ima da kuma baiwar dake cikin musulunci, saidai ance dama komai nada sanadi, to ita ce ta kasance sanadiyar musuluntar su Solomon ɗin wanda harda fastonsu suka zo wanda shima zai musulunta, shiyasa basu musulunta tun tana canba dan sunce sai sunar mishi koda suka gaya mishi ko shima yace zai musuluntan." Wani irin daɗi da farinciki ne suka cika zuciyoyin gaba ɗaya ahalin, wani irin ni'im taccen daɗine ke ratsa zuciyar Baba Malam da kuma Saifuddeen, Allah mai iko yaugashi asanadin Zaleeha mutum ɗai ɗai har goma shabiyar zasu musulunta, tabbas zuwanta garin Numan yazamanto al'khairi, zuciyar Baba Malam ne tayi wani irin haske, take yaji duk wani abu dake ransa ya kau, ƙaunar ƴar tasa ne ya shigesa, har takai ga yanajin kamar ma bata taɓa yi masa wani abu na laifi ba. Saifuddeen ma yaji daɗin haka, take kuwa Baba Malam da kuma Baffa'n, suka shiga bawa su solomon da kuma sauran maƙotansu da suka biyosu dan suma suna son musulunta, kalman shahada, wasu suyi dadai wasu kuma su kwaɓa harsai angyara musu, ahaka dai har dukansu suka musulunta, su Ya Ahmad ne suka ce. "Allahu Akhbar, haƙiƙa Allah da girma yake, yau gashi Zaleeha ta jawo sanadiyar musuluntan mutane 15, gaskiya wannan abun farinciki ne acikin zuri'arsu dama musulunci baki ɗaya." Haka dai duka zuciyoyinsu suka cika da farinciki da kuma jin daɗi. Daga nanne Saifuddeen ya basu kuɗi masu yawa, dan su saya ƙaton fili acan garin nasu, sukuma yi ginin masallaci da kuma makaranta, Baba Malam ne yace. Shi zai ɗauki nauyin ginin masallaci da kuma makarantar, sannan kuma zaiyiwa babban shugaban malaman izala dake can numan ɗin, akan cewa asama musu malamai waƴanda zasu riƙa koyar dasu addini. Ya Ahmad ma take yace zai bada gudumowarsa 1mil. A nan Man Lima ya nemi keɓawa da Baba Malam ya sanar mishi dukkan abubuwan daya samu a jikin Zaleeha na sihiri, Tabbas sihiri gsky ne yana kama ɗan adam tunda ya kama fiyeyyen halittama badon gazawar shiba ko tawayar darajarta ba a a sai dan nuna mana cewa zai iya kama mutun, sai dai tasirinsi ƙalilan ne, sosai Baba Malam yayi mamakin wannan al'amari, kana yayiwa Man Liman godiya mai tarin yawa. Kana anan take ya kira shugaban ƙungiyan izala reshen Adamawa dake cikin numan ya shaida musu abin Al'khairi daya samu, su kuma sun ɗauki niyar koyar dasu dukkan wani abinda ya kasance na addini, babban farin cikinsu ga masallaci da islamiyar da za'a gina a yankin da da babu hasken musulunci sai warin kafurci dana burkutu da kashin aladu. Zaleeha kam farin cikinta bazai misaltuba, kayan da tayi budurci dasu kab ta kwashe ta basu, dan ta san basu da wadattun suturu daya dace suke sawa, Mamy ma da Aunty Lubna sun basu kayayyaki da manya-manyan hijabai, Mama kuwa saida tayi kuka wato Allah yaso wasu da rahma ne yasa ita da kanta ta tura ƴarta can da nufin watsa sunnar manzo sai gashi sanadin haka addini ya samu ƙaruwa. Sune dai basu tafiba sai bayan sallan al'asar. Bayan tafiyan sune Baba Malam ke sheidawa Zaleeha batun an ɗaura auren Ziyada da Ya Ameenu, wannan al'amari yasata ƙara nitsuwa da jin tsoron Allah. Shi kuwa Saifuddeen sallamansu yayi cewa zaije wurin Ishaq, sai bayan magriba zaizo su tafi gida. Baba Malam kuwa shida kanshi ya ɗauki Ziyada da Ya Ameenu da Ayman ɗan Adam Maryam ya kaisu gida. Sosai ya zauna yayi musu nasiha mai ratsa jiki da zuciya, gaba ɗayansu kuka sukeyi sabida al'amarin ubangiji ya wuce wasa ko a zato ko a mafarki basu taɓa zatawa kansu zama mata da mijiba inba mutuwaba mai zai raba Adda Maryam da Ya Ameenu har ya aureta. Bayan tafiyan Baba Malam ne, ya Ameenu ya ari jarumtar dole dan kukan da Ziyada keyi ya tsananta dole ya fara rarrashinta da nuna mata suyi haƙuri ƙaddar suce haka kums kowa da irin tasa. Sai bayan sallan magrib Saifuddeen ya dawo shida Sule dan ɗaukan Zaleeha su koma gida, nan kuma ya Ahmad yasa dole suka zauna suci abinci ruwa kawai Saifuddeen yasha don yaci abinci a gidansu ishaq ita dai Zaleeha taci da Aunty Lubna tayi haniƙan dan yau tana cikin farin ciki. Kafin su gama kuwa an kira sallan isha'a dole sukayi salla kafin Zaleeha ta fito suka tafi gida. A can gidansu Saifuddeen kuwa tun ƙarfe shida Ameena ta dawo aiki, tayi mmkin ganin Zaleeha bata gidan ita da Adeel, hakama Saifuddeen baya nan, Hayatuddeen ta samu a falo bayan taje ta gaida Ummi cikin gajiya tace. "Autan Ummi Ina Adeel da Amminshi?". ruwan daya kurɓa ya haɗiye tukun kana yace. "Sunje anguwa". Murmushi ta ɗanyi tare da cewa. "Ayyah". Har ta nufi bakin ƙofar fita sai kuma tace. "Hamma Saifuddeen fa ya fita ne?". Hankalinshi na kan wayarshi yace. "Tare suka fita." Wani irin malolo taji ya daki ƙirjinta wani zazzafan kishi ya taso mata, sai kuma tayi ƙarfin halin dannewa murya a daburce tace. "Okay". Kana ta juya ta fita tana yaƙi da zuciyarta da kuma shaiɗan dake son ɓata mata daren yau ɗin bayan jiyama haka ta kwana tana fushi da mijinta ya nuna yanada buƙatar haƙƙinshima ta hanashi still yau kuma shaiɗan naso ingizata a fili tace. "A'uzubillah menene dan ya fita da marsa kuma da ɗana". A haka taje tayi wonka tayi al'wala kana tazo ta kabbarta sallan magriba dan lokaci yayi. Bata tashi bisa sallayanba saida tayi sallan isha kana ta can-canɗa ado cikin wani dandatsestsen boyel mai azabar kyau sosai tayi kyau sihirtaccen kyanta ya baiyana. Koda tazo falon Ummi dai-dai lokacin su Zaleeha ma suka dawo, su Ummi duk sunata farin cikin musulunta dasu Solomo sukayi wanda Zaleeha ne ta gaya musu, tana shiga Hayatuddeen ya kalleta tare da cewa. "Wow Anty Ameena kinyi kyau wannan gayu haka". Murmushi tayi tare da cewa. "Ngd". Sai kuma ta kalli Zaleeha dake juyo kan Adeel tana cewa. "Papy kalli Momy, oyoyo Momy! oyoyo Momy!!". ai kuwa Adeel na ganinta ya fara kaɗa hannu alamun oyoyo, kana Zaleeha na tayashi, shi kuwa yaro sai dariya yake yana miƙa hannu alamun ta ƙarɓeshi yakeso, hannu ta miƙo mishi tana kallon yadda Zaleeha ta biye mishi, tana karɓanshi ya fara wawure-wawure so yake a bashi nono. Dariya Ummi tayi tare da cewa. "Ɗan nema mai yawan ciye-ciye kalli yadda yake kokuwan a bashi nono kamar ya shekara bai shaba". Dariya sukayi baki ɗaya dan duk hankalinsu ya dawo kan Adeel da Momynshi. Zaleeha ce ta ɗanyi murmushi tace. "Allah ko Ummi Autanki ne ya ɓata min papy na da yawanci, shi ya gado". Tura baki Hayatuddeen yayi tare da cewa. "To wai waye baya cine da kuka tasoni gaba mijinku ma cine dashi kamar gara, amman da yake shi nakune bakwa faɗa". Dariya Zaleeha tayi tare da cewa. "A a kam Hamma Saif baida irin cinka, ko Ummi?". Ta ƙarishe mgnar tana murmushi, wani irin daɗi ne ya rufe Ummi ikon Allah yau Zaleeha ke suffanta Saifuddeen da mijinta har tana kareshi, Shima Saifuddeen ido ya ɗan zuba mata a fakaice. Shi kuwa Adeel zuƙan nono yake harda kamo ƙafarshi ɗaya, har wata zufa yake haɗawa, shafa kanshi Saifuddeen yayi cikin son yaron da ganin darajar da kumar Uwarshi, ya juya zai fita kenan Ummi tace. "Saifuddeen zo muci abinci tukun". Kanshi ya ɗan jujjuya tare da mata alamar. "Ummi kuci na ƙoshi". Murmushi Zaleeya tayi tare da cewa. "Autan Ummi ka gani ko". Tura baki Hayatuddeen yayi tare da cewa. "Waya san me kuka ciyo a woje". Dai-dai lokacin Raliya tace. "Dan Allah kuzo muje muci abinci ni yunwa nakeji". Miƙewa Zaleeha tayi tare da cewa. "Alhamdulillah wlh a ƙoshe nake, yau a gajiye ma nake zan konta da wuri". Cikin wani irin yanayin tuhuma da zato da zargi Ameena ta bita da lallo tana fita. A ranta tace. "Okay duk sun ƙoshi bazasu ciba, to me suka ciyo? Ina sukaje? Me suka wuni yi da tace a gajiye take?". Take shaidan ya fara haɗa mata zato da zargi ya kuma zauna ras dan komai da hujja yake bata. Abincin da itama bata iya ci ba kenan dan sai ruwa tayi tasha koda Ummi ta matsamata kan taci sai tace a ƙoshe take ƙawarta Samira ce ta kai musu awara shi sukaci shine sai ruwa suke tasha. Koda suka gama ta saɓa ɗanta a kafaɗa ta nufi side ɗin. Zaleeha kuwa dama kai tsaye ɗakinta ta wuce, rege kayan jikinta tayi kana ta shiga wonka, tana fita tayi shirin baccinta sannan ta konta. Shi kuwa Saifuddeen aiki ya ɗanyi a system ɗinshi, inda ya ƙara samun damar bin diddigin Dalla dan ya dawo da niyar, rarake yan mata huɗu da yayi al'ƙawarin dan dama ya tafine dan badda sawu, wannan dalilin yasa Saifuddeen bai bari direba ya kai Zaleeha ita ɗaya ba ko ɗaukota. Koda ya gama aikinshi wonka mai rai da lafiya yayi dan Allah ya sani yana begen cingam ɗinshi, ya rigada ta saba mishi ko yaushe tana liƙe dashi kuma hakan na mishi daɗi yanzu tunda ya rigada ya saba. Bayan ya gama kimtsa wa ne sai zuba ƙamshi yake, ya nufi side ɗin Zaleeha ganin tayi bacci sui ne yasa bai tada itaba rigarta ya ja ya ɗan gyara mata a hankali ya fice ya tafi. Ita kuwa Ameena da bata da niyar neman shi so take ya mata laifi kaɗan ta samu na ƙorafi, haka yasa ta konta tasa ɗanta a gaba. Jin motsinshi ne yasa ta rufe ida nunta, kunna hasken wayarsa yayi gane ba bacci takeyi bane ya sashi ɗauke Adeel cak ya medashi kan gadonshi kana ya dawo a hankali ya sauƙa kan kekenshi ya hau kan gadon ya konta inda ya ɗauke Adeel ya meye gurbin shi kenan, ya zama suna fuskantar juna. a hankali yasa hannu ya jawota jikinshi, da sauri taja baya tare da juyawa ta bashi baya. Hannunsa yasanya ya rungumota ta baya, fusge jikinta tayi, ranta amatuƙar ɓace, ta matsa daga kusa dashi, idanunta wanda suka kaɗa sukai jajur ta watsa masa, cikin fushi da ƙunan zuciya tace. "Kada ka taɓani, dan bani da buƙatar hakan, bani kaɗai bace matarka ai, kana da wanda kake ɗauka kutafi resturant da garden ai, ni dama menene amfani na awajenka, tunda na riga dana haifi ɗa, sannan kuma bankaita kyau ba, hakanne yasa kake ƙoƙarin fifi tata akaina, saboda kun fita yawon shaƙatawa, kunje kun more rayuwarku, dole ai kace bazaka ci abinci ba, tunda kana da ƴar gold kunje kun wuni liƙe da juna harda wani cewanta a gajiye take,ai ba sai ta faɗa min haka zan gane ta wuni a kanka kuna aurataiya ba." Taƙare maganan cikin matsanancin ɓacin rai, da kuma tafasar zuciya, Allah yasani kishin Saifuddeen yaci ƙarfinta, saboda hakane ma take yarda da duk wani abun da zuciyarta ta raya mata. Shiru yayi tare da tsura mata tsumammun idanunsa, ƙwarai yanda idanunta suka rufe, take faɗan duk wani abu da yazo bakinta, shine abun dake matuƙar basa mamaki, dan gaba ɗaya lokaci guda ta sauya, ta tashi daga Ameenan da yasani ada, ta dawo wata irin mace me yawan ƙorafi, da kuma yarda da zargi bata da wani mugun abu tare da ita illa kishi dake son fin ƙarfinta, wato dama duk ilimin mace dole kishi na tsaburarta sai dai wasu na iya dannewa, wasu basa iya, a zahiri dai babu matar da bata da kishi,kuma yaji ya sani ya yarda zazzafan son da take mishine yasa take tsananin kishinsa. Kansa ya girgiza tare da sa hannu ya kamo hannayenta, tabbas dole zaiyi mata uzuri saboda yasan zafin kishi ne ke ɗawainiya da ita, a wayarshi ya rubuta mata. "Zargi bashi da kyau, kin sani ko a addinance, meyasa Ameena? meyasa ako yaushe kike yarda da abun da zuciyarki ke faɗa miki, meyasa ba zakina ƙaryata zuciyarki ba? kada ki cigaba da bari shaiɗan yayi tasiri acikin zuciyarki, tayaya kike tunanin aranan girkinki zan ɗau Zaleeha mu tafi garden ko resturant duk dan kawai na baƙanta miki, sam ba haka nake ba, ya kamata ace ke dakanki ki zama shaida, dan bana iya tauyewa kowa haƙƙinsa, sannan da kiketa ihun cewa munje resturant, ayaushe ne mukaje resturant ɗin? ya kamata ace kina kyautata mana zato, domin kuwa ba resturant mukaje ba, gidan Baba Malam mukaje, saboda yau akayi sadakan bakwai ɗin rasuwar Adda Maryam, zargi bashi da kyau, yana lalata aure, saboda haka ya kamata kina iya controlling zuciya, kishi, da kuma fushinki sabida bana so ki lalata mana zamanmu." Hannunta dake cikin nasa ta janye, kwata-kwata maganganun da ya faɗa basuyi tasiri acikin kunnuwanta ba duk da wani sashi na zuciyarta ya yarda da batunshi, sai dai zafin kishi da takeji ya danne komai hasalima jinsa kawai take, dan ayanzu kam gaba ɗaya idanunta sun rufe, wutar kishi ne kawai kecin zuciyarta, hakan yasa ba zata gane gaskiya ko akasinta ba, ganin yanda take ta sakin huci tana fitar da numfashi cikin fushi, ya sashi girgiza kansa kawai, tabbas tana ƙoƙarin ɓarar da damar da ta samu, gyara kwanciyarsa yayi tare da kwanciya ya juya mata baya, saboda aduniya baya tunanin akwai wata mace da ta isa, yi masa fushi babu dalili, ya kuma rarrasheta taƙi ji, shiba sakarai bane, saboda haka bazai taɓa zama wawa akan mace ba, ko Zaleeha da ta kasance zaɓinsa ne takeyi masa haka, to tabbas bazai tsaya sauraranta ba, domin yariga dayasan ko awajen Allah bashi da wani laifi, tunda dai bai aikata ba dai-dai ba. Blanket ya ja ya rufa ajikinsa, tare da lumshe idanunsa. Ameena kuwa ganin yanda yayi kwanciyarsa ba tare da ya kara ce mata komai ba, yasa taji gaba ɗaya ranta ya ƙara ɓaci, can nesa dashi ta matsa tare da jawo Adeel jikinta. Saifuddeen kuwa dama baji yake ba, kuma gashi ya bata baya, hakan yasa baimasan tanayi ba, dan baccin gajiya ne ma keneman ɗaukarsa. Saida tayi kuka sosai kafun take maida ajiyar zuciya, jitake inama da ace Zaleeha bata dawo gidan ba, inama da ace Saifuddeen baikasance mijin Zaleeha ba, da duk hakan baifaru akanta ba, dan tanajin zata iya jure kishi da kowacce mace amma banda Zaleeha, ta jima sosai tana sheshsheƙan Washegari da asuba kuwa antashi da ruwa, hakan yasa bai samu zuwa masallaci ba, nan cikin toilet ya shiga ya ɗauro alwala, tare da shumfuɗa darduma ya tada sallah. Itama Ameenan miƙewa tayi, ta shige toilet ruwa ta ɗan watsa ajikinta, saboda ta tashi taji zuciyarta wasai, acikin kaso ɗari na damuwarta kaso saba'in ya ragu, hakanan taji cewar abun da tayi masa daren jiyan bata kyauta masa ba, sauda dama takanyi regreting abubuwan da takeyi mai, dan kuwa ita kanta tasan baiyi mata laifin komai ba hakama Zaleeha bata tare mata komai ba, kawai dai zafin kishi ne ke ɗawainiya da ita wanda kuma tana addu'an ALLAH ya yaye matashi tajin son Zaleeha koda al'barkacin son da takewa Adeel, nan kusa dashi ta shumfuɗa wani darduman, tare da ta da sallah, zuwa lokacin kuwa shikam ma harya idar, zaune yake akan guiwowinsa, yana gabatar da azkar, yana nan azaune harta idar da sallan itama azkar ɗin tayi, sannan ahankali ta ɗago ta kalleshi, gaba ɗaya jikinta asanyaye yake, ga kuma wani irin fitinannen ƙaunarsa da kuma sha'awarsa da takeji, hannunta takai ta dafa kafaɗansa, sarai yajita amma sai yayi kaman ma baisan tanayi ba, ganin haka yasa ta dawo gabansa suna fuskantar juna, ganin yana kallonta yasa taɗan sunkuyar da kanta, asanyaye tace. "Ina kwana." Kansa ya jinjina mata alaman. "Lafiya." ƙoƙarin hawa wheelchair ɗinsa yasomayi, ganin haka yasa ta faɗa jikinsa, cikin sanyin guiwa tace. "Dan Allah Abban Adeel kayi haƙuri, nima bansan meyasa nakejin wasu abubuwa akanku wani lokaci ba, kasan inasonka wannan dalilin yasa nakejin kishinka sosai araina, amman in sha Allah zan bari dan nacewa Mamana taita min Addu'a Allah ya yaye min kaima kaita min Addu'a kuma nima inayi." Idanunsa ya zuba mata, shi mutum ne me saurin fahimta da kuma uzuri, musamman ma ita da yasan cewa kishine ke ɗawainiya da zuciyarta. Ɗan lumshe idanunsa yayi, tare da jinjina mata kai alaman. "Shikenan komai ya wuce." murmushi ta sakar masa tare da sake shigewa jikinsa, bakinta har rawa yake haka ta shiga kissing ɗinsa tako ta ina, sam bai hanata ba, dan baiso ya tauye mata haƙƙi, jikinta na rawa haka ta taimaka masa ya kwanta akan gado, bin bayansa itama tayi, tare da haɗe jikinsu waje ɗaya. Duk wani abun da takeso baiƙi yi mata ba sabida shima yana buƙatarta, haka ya bata duk wani haƙƙinta dake kansa, after 22 minute gaba ɗaya jikinsa yayi weak, gajiya ne keta damunsa, da ƙyar ya iya tashi yayi wanka, fita yayi inda yaje ya gaishe da Umminsa, yana dawo wa kuwa nan kan gadon ya kwanta yana me da numfashi, ahaka har bacci ya ɗaukesa. Ameena kuwa jin ranta take fari ƙal, wani annushuwa takeji acikin ranta, koda ta fito daga wankan, mai kawai ta shafa sannan ta yiwa Adeel wanka, saida ta fara shirya Adeel ɗin, kafun ta shirya kanta cikin kayanta na zuwa aiki. Ganin Saifuddeen ɗin na bacci ne yasa taɗan ranƙwafo tare da yi masa kiss agoshinsa, Adeel na ɗauke akan kafaɗanta ta fice daga cikin ɗakin, kaitsaye sashin Ummi ta nufa, anan falo ta iske su azaune, yayinda Zaleeha ke zaune anan ƙasan sofa, tasha kyau cikin simple riga da sket ɗin dake jikinta, anutse ta gaishe da Ummi sannan Zaleeha ta miƙa hannu ta amshi Adeel, yau ko breakfast ma bata tsaya tayi ba, saboda taɗan makara. kuma tana son yau ɗin ta keɓe da ƙawarta, Samira tasan zata ƙara kwantar mata da hankali kuma zata bata shawarwarin yadda zata samu ta yaƙi wannan zazzafan kishin ta zauna da ƴar uwarta lfy. Saifuddeen kuwa sosai yayi bacci, dan bashi ya farka ba sai wajajen ƙarfe 10, bathroom ya shiga ya sakeyin wanka sannan ya kimtsa kansa cikin, wasu haɗaɗɗun riga da wando, sai baza ƙamshi yake haka ya nufi sashin Ummi, dan yunwa yakeji sosai. Ummi ce da Zaleeha kaɗai zaune afalon, Ummi nakan kujera, ita kuwa Zaleeha tana ta kaikoma acikin falon, sai faman jijjiga Adeel dake kuka yake, shigowarsa cikin falonne yasa Ummi cewa. "Yauwa gama babansa nan, Zaleeha miƙawa babansa shi ko zaiyi shiru, tun ɗazu ya cikamu da ihu, bansan meke damunsa ba, bacin kuma ƙiwa ba halinsa bane." Ɗan kallon Saifuddeen ɗin Zaleeha tayi, sai kuma ta sadda kanta ƙasa. Shikuwa ahankali yaɗan lumshe kyawawan idanunsa da suka sauƙa akan haɗaɗɗiyar surar jikinta, hips ɗinta wanda ya cika sket ɗin jikinta, yayi masifar kyau da tsaruwa yake kallo, jiyayi tsikar jikinsa sun mimmiƙe, asanyaye Zaleeha ta karaso inda yake, ɗan sunkuyawa tayi daniyar ajiye masa Adeel ɗin akan cinyarsa, hakanne yasa beautyful breast ɗinta suka ɗan bayyana ta saman wuyan rigar, ganin kyawawan saman breast ɗin nata yasa yaji wani abu na yawo ajikinsa, wajen miƙa masa Adeel ɗin ne kuwa, hannunta ya gogi nasa, take sukaji wani irin shock, hakanne yasa cikin sauri ta zare hannunta tare da komawa gefen Ummi ta zauna, ɗaga Adeel ɗin yayi yana yi masa wasa, take kuwa yaron yasoma sakin murmushi, harma da ɗan dariya, Ummi ne tace. "Kuji ja'irin yaro, wato yaga Babansa shine harda dariya, dama kenan mu kakewa ƙiwa." Murmushi kawai Saifuddeen ɗin yayi, yana riƙe da Adeel ɗin, ya ƙarasa dinning area, ganin haka yasa aɗan kunyace Zaleeha ta tashi, ta ƙarasa dinning table ɗin, cikin nutsuwa take seving ɗinsa haka nan take jin kamar ta zauna kusa dashi, shikuwa idanunsa ya zuba mata, dan sosai tayi masa kyau, yau ɗin zallan yarintarta ya bayyana sosai, gashi kayan jikin nata sunyi mata cif-cif, har gabansa ta kawo masa plate ɗin abincin, ɗan ɗagowa tayi, hakanne yasa idanunsu sarƙewa acikin na juna, rolling eyes ɗinsa yayi, take taji wani irin yaarrr yaarrr ajikinta, saboda yanda abun ya ƙarawa fuskarsa kyau, wani irin kallon shauƙin daya bita da shine yasa, takusa yin tuntuɓe wajen barin dining area'n, wani ƙawataccen murmushi ya sake, tare da ɗauke kansa ya maida hankali kan abincinsa. Nan kusa da Ummin ta dawo ta zauna, suna ɗan taɓa hira da Ummin, har ya kammala cin abincin, koda yazo fita, akan cinyanta ya ajiye Adeel ɗin, sannan ya fice. Yana fita kuwa Adeel yasa musu kuka, haka suka dinga rarrashinsa ita da Ummi, saida yayi bacci kafun suka samu salama, Zaleeha kam tuni kukan Adeel din ya ruɗata, har tanajin ƙwalla sun cika idanunta, sam batason kukan Adeel ɗin. Saifuddeen kuwa yana fita daga part ɗin Ummi'n, kaitsaye gidan ya bari, dan suna da meeting ɗin da zasuyi. Adeel kuwa wunin yau gaba ɗaya kuka ya dinga musu, da ƙyar suke iya rarrashinsa. Ameena kuwa yau da wuri suka tashi, a hankali suke tafiya ita da ƙawarta Samira, har suka iso bakin harabar inda suke aje motocinsu, shiru Ameena ta ɗanyi tare dacewa Samira. "Yau baki fito da motarki bane?". Murmushin Samira tayi tare da cewa. "Eh yau a napep nazo, ƴar uwatace motarta na wurin gyara, kuma sunada biki a danginta, shiyasa na bata nawan". Cikin fidda numfashi Ameena tace. "Uwar gidanki ko?". Kai Samira ta gyaɗa mata alamar eh, cikin sanyi Ameena tace. "Kinji dadi Samira inamw ace nima Allah zai yaye min kishi in samu in saki jikinda uwar gidana, dan wlh ita dai irin kice." Murmushi Samira tayi tare da cewa. "Uhum Ƙawata ai abin mai sauƙine muddin kika sauƙaƙawa kanki to Allah zai sauƙaƙa miki in kuwa kika tsananta wa kanki zakisha wuya, ni da uwar gidana wlh ko ƴan uwa sai haka, bamu da matsalar komai sabida mun sawa ranmu haƙuri, bawaifa bama kishin bane, no ai kishi kumallon matane, amman kishinmu mai tsari mukeyi, ina gaya miki ki saki ranki da abokiyar zamanki zakuji daɗin zama, tunda keda kanki kin shaida min ita bata da kishinki asalami ke gani kike wai kamar bata son mijin nakune, to wlh Ameena bawai bata son mijinku bane ba mamaki ma ta fiki sonshi kawai dai ta iya takunta ne, babu mamaki ma ta fiki sonshi sai dai wata ƙil ita sonta irin son nanne da zaka so miji ka kuma so duk abinda yake so, kawai dai ta iya sarrafa kantane." Cikin sanyin jiki Ameena tace. "Shiga motata muje in sauƙeƙi dama ina son muyi mgna". kai ta gyaɗa mata kana suka shiga Mota, shiru sukayi saida Ameena ta dai-dai ta hancin motarta kan titi kana ta juyo ta ɗan kalli Samira cikin sanyin jiki tace. "Wato ko Samira ni kaina nasan zuciyata bata min adalciba akan Ammin Adeel, na yarda na gane tana masifar son ɗana so kuma na gaskiya, kana tana kawar da kanta akan harkata da mijinta tamkar bata san me mukeyi ba, bawai ina jin na tsaneta bane a a wlh ni kaina ina sonta sai dai ina masifar kishinta,ina son Abban Adeel wani irin son da ni kaina bansa adadinshiba shiyasa nake kishinsa bana son yayi nesa dani, kinga tsabar zugar kishi wallahi yanzu sai yayi ta bina yana son haƙƙinshima sai inji to ai yanada wata matar." Juyowa Samira tayi ta fuskanceta da kyau cikin wayewa da iya salon kishi na Musulunci tace. "Kin wahala kin ɗorawa kanki dala ba gammo, ke ƙawata in banda tsaurin ido irin namu na mata ki samu mace da mijinta kice zaki zafafa kishinki yo in dai ita bata zafafabaai ke kuma bai dace ki zafafaba me ruwanki da ita zamanki da ban nata da ban, tsakaninku babu babbancin matsayi ku duk matanshi ne, ki dena sawa ranki yafi sonta, ko ganin wani ƙira nata, ki gyara zuciyarki zakiji daɗin zama da kowa a gidan". Shiru Ameena tayi jiki a mace dan ta ƴarda da batun Samira tasan gsky take gaya mata, ita kuwa Samira cikin kula ta kalleta tare da cewa. "Ni kam Ameena kiyi haƙuri ba gulma bane menene ya rabaki da mijinki na fari wanda kika cemin yayanki ne ɗan baffanki kuma a wurin iyaye shi kika girma". Wani nannauyan ajiyan zuciya Ameena ta sauƙe tare da maida numfashi, ganin haka yasa Samira cewa. "Sorry bawai na matsa bane in san sirrinki,ina son in fahimci wani abune inji ko laifin ya Amir ne". Kai ta rausayar cikin sanyi tace, "Akwai kam, akwai laifinshi". Cikin kula Samira tace. "Menene laifin nashi?" Hankalinta ta maida kan tuƙin da takeyi kana ta fara bawa Samira labarin. "DADY Baban Ya Amir ƙanin babane uwarsu ɗaya ubansu ɗaya, babanane babba, Allah ya azurta babana da dukiya da ilima kana da ƴara dan mu ƴaranshi mun kai goba. Yayinda Dady kuma Allah ya bashi tarin dukiya da ilimi amman ɗanshi ɗaya ne rak a duniya wato ya Amir ɗin, Mommo matarshi tana masifar sona tun ina ƙarama ita ta roƙi Mamana da Babana aka bata ni, shine sanadin da yasa na girma a Abuja dan iyayena asalin ƴan Jada ne. Ya Amir ya tashi cikin tsananin so da gata shiyasa ya zama sangartacce, kana Ya Amir irin mazananne masu azabar jaraba mace bata isarsu da wuri, Kuma tun ina ƙarama yake sona sabida Mommonshi ma tace shi tayiwa kamu, haka kuwa muka taso yana sona nima ina sonshi, to matsalar ya Amir ɗan bunsurune baya iya rayuwa saida mace. Amman ni a lokacin ban saniba hakama Dady bai saniba, amman ita mommo mamanshi ta sani ganin ya tsananta bunsuranci yasa tace, kawai ayi aurenmu in ƙarisa karatuna a gudanshi, ita a nata zaton tunda jarabace kuma mace yakeso to ai in an aura mishi ni zai daina neman mata. Kuma koda yaji batun aurenmu da iyayenmu suka tayar yaji daɗi sosai. Madadin iyaye ke tsuma amarya tofa shi ya Amir shine ma ke seyo min abubuwan gyara ya kawomin, kuma sosai na dage ina gyara kaina Alhamdulillah kuwa akayi aure lfy lafiya, muka tare a anan cikin gidan namu side ɗinmu nacan nesa dana Dady. A darena na forko da Ya Amir bai ɗaga min ƙafa bai sahir taminba, haka yayi ta caccakata kamar ba gobe, na wahala sosai a wurinsa, washe gari da safe, Mommo da kanta ta gyarani naji dama-dama ta kula dani sosai sanadin haka na ɗanji sauƙi dan mommo da zuciya ɗaya take sona, still a dare na biyuma haka Ya Amir yayi ta caccakata, abu kamar wasa ya maidani kamar abinci, rana ta uku nace ni kam na gaji bazan iyaba, mafarin matsalar kena, dan wlh ido da ido yace min. "Tunda bazaki iyaba bari in kira Dina tazo ta taimaka min". Wlh ni na ɗauka wasane, dina sakatariyar shi ce kuma arniya ce, in taƙaice miki a gabana ya kirata yace su haɗu a hotel, Shine ma farin kishina, dan ji nayi kamar zan mutu, duk da dare yayi naje na sanarwa Mommo ranta yayi masifar ɓaci ta kirashi baya ɗagawa, koda ta gayawa Daddy yaji baƙin cikinda bazai misaltuba yayi ta faɗa yacewa Mommo. "Wlh da nasan Amir mazinaci ne da bazan haɗashi da ƴar ɗan uwanaba, ƴarinya da ta kame kanta in haɗata da fasiƙi". Sosai mommo taita kuka. Ranan a side ɗinta na kwana washe gari daya dawo suka solleshi soso da sabulu, abin ta kaici sai yayi ta kuka wai to a ƙara mishi wata matar in munyi biyu zamu iya da buƙa tunshi, niko jin zai ƙara aurene tun satin forkoma bai ƙareba nace na yarda ni zan iya dashi". Ɗan rage gudun motarta tayi kana ta ɗan kali Samira da ta zuba mata ido cikin sanyi taci gaba da cewa. "Yanajin haka yace to shike nan in sha Allah ya dena bin mata, ke da haka muka koma side ɗinmu dake yana hutun amarci, ranar tare muka wuni yana ta bidirinshi dani, tun ina jin zafi har na dena ji, kamar wasa cikin kwanaki biyar, muka zama kamar tib da taya, dan nima na tsumu da mugunguna da yake bani kuma shiyasa nake jin daɗi in muna sex sosai Ya Amir ya liƙe min nima kuma na fahimci ina ɗaya daga cikin mata masu buƙata matsalar da aka samu, rashin sabo da kuma zafin amsar budurci yasa nake ɗan gajiya, randa mukayi kwana biyar ɗin ne ya wuni liƙe dani koda dare yayi na gaji yayi yayi in bashi kaina na gaza nace ya bari saida safe, ina fir yaƙi, nan na gane ya Amir Harijine, gashi dare yayi, ganin zai matsamin yasa na gudu na koma ɗaya ɗakinmu, ashe ya kira Dina tazo har cikin gidanmu a ɗakinmu na sunna akan gadona, sukayi masha'arsu tun dare har asuba. koda na dawo na samu Dina a ɗakina, na kusan kasheta dan da keret aka kwace a hannuna, kuma ina ihu da hargowa har Dady da Mommo sukazo suka samemu a nan da keret Dady ya kwace a hannuna gudun kar inyi kisan kai. To nan take Dady yasa Ya Amir ya sakeni. Haka kuwa yamin daɗi dan gaba ɗaya Ya Amir ya fice min a rai na tsanesa sabida Allah ya sani ina ƙyawar zina da mazinatan. Koda Baba na yaji yaso ya meda auren Dady yaƙi, daga nan na koma sashin Mommo kamar da mukaci gaba da zamanmu tana sona. To matsalar forko dana samu itace yawan sha'awa ina yawan shiga damuwa, in begen sex ya dawo min domin gaba ɗaya Ya Amir ya dawo dani irinsa cikin sati ɗayan nan da mukayi, ga magungunan daya ɗuɗɗura min sun kamani sosai. Allah ya sani Samira daga nan na zama jarabebbiya, ina tajin tsoro kar naje na samu lusarin miji in boni domin a zaman da nayi dole azumi na yawaita yi shiyake rage min kaifin fitinar da Ya Amir ya raɓa min. Randa kuma na fara ganin Abban Adeel naji tsoron wani abu da nagani, dan ya zarta ya Amir nesa ba kusaba, koda na koma gida wlh sai naita mafarki dashi muna sex, raina da zuciyata sun ƴardarmin shine irin mijin da zai iya magance min matsalata, na sani bazan iya jure zama da lusarin mijiba, shiyasa kikeji ina ce miki bana son Abban Adeel yayi nesa dani, Alhamdulillah kuma shima ɗin ba tayan baya bane". Ta ƙarishe maganar cikin jin kunya, ita kuwa Samira dariya tayi sosoi kana tace. "Wato ya Amir ne ya maida min ke fitinenniya". Murmushi kawai tayi, tare da karya konan shiga layinsu Samira. Ita kuwa samira cikin kula tace. "Yanzu ya Amir ɗin yayi aurene?". Da sauri ta gyaɗa kanta tare da cewa. "Ya musuluntar da Dina tayi istibira'i ya aureta dan itama harijace irinsa, yanzu yaransu biyu yamin takwara da yarshi ta biyun Amina sai ɗan farinsu Hisham ita kuma Dina yanzu sunanta Fatima". Cikin jin daɗi Samira tace. "Alhamdulillah kinga wani hanin ga Allah baiwace, yanzu dai ni bance kada ki liƙe mijinkiba amman ki dena kishin Zaleeha dan itafa matarsa ce ba karuwarsa bace kamar Dina da ya Amir so dan Allah ki sawa ranki salama, ki fauwalawa Allah lamarinki kamar forko, shi zai ɗaga daraja da kimarki a wurin mijinki wlh Abban Adeel yana sonki". Dai-dai lokacin suka isa ƙofar gidan Samira, cikin sanyi Ameena tace. "In sha Allah zan kula dan wlh ni kaina nasan Abban Adeel yana son farin cikina". Kai Samira ta jinjina tare da cewa. "Yauwa ƙawata ki kula gudun kada ki ɓarar da damarki sai gobe in mun haɗu zamu ƙara tattaunawar zan baki shawarwarin yadda zaki samu sauƙin kishin kuma ki yarda yana sonki." Cikin jin daɗi Ameena tace. "To Allah ya kaimu gashi yauma itace dashi gobema itace sai ran monday zan ƙarɓeshi kuma kinga ran monday ɗin munada off zan wuni a gida kusa da Mijina da ɗana, Allah dai ya bani ƙarfin hali irin naki, amman in sha Allah bazan sake tayar da hankali naba". Amin Amin Samira tace lokacin data fita, Kai tsaye cikin gidanta ta wuce, ita kuma Ameena taja motarta ta koma gida. Koda Ameena ta dawo nono ta bawa Adeeli take kuwa yayi shiru kamar ba shine ya wuni koke-koke ba. Anan sashin Ummin tayi magriba, tana idarwa kuwa ta tattara komanta ta wuce sashinta, dan yau ba itace da girki ba Zaleeha ce, shiyasa gaba ɗaya komai keneman dawo mata sabo donma tayi dace da shawarwari Samira aminiya ta gari mai imani ta nusar da ita ta koyi kauda ido kan miji da kishiyarta kada ta tsananta binciken cewar sai ta gano waya fi so a cikinsu ta kuma cire zargi, to Alhamdulillah kuma ta gamsu da shawarwarin Samira tasirin ƙawa ta gari kenan. Zaleeha kuwa koda ta idar da sallan isha, wani haɗaɗɗen riga da wando me taushin gaske tasa, rigan irin mai hannun vest ɗinnan ne, tabi gaba ɗaya surar jikinta ta lafe, har takai ga ana iya hango shatin nipples ɗinta, dan batasa bra ba, wandon kuwa meɗan faɗi ne, amma duk da haka bai hana mayataccen hips ɗinta bayyana ba, dogon gashinta ta tubke sannan ta feshe gaba ɗaya jikinta da turare, wani irin kasala haɗi da bacci takeji, saboda hakane ma yasa batajin zata koma sashin Ummi, hayewa saman gadonta tayi, tare da jawo hand bag ɗinta, diary milk ta ɗauko, tare da ɓarewa, kwanciya tayi tana ɗan gutsuransa kaɗan kaɗan, wayarta ce ahannunta tana ɗan kallon hotuna a IG wanda duk hotunan Hamma Saif ne take gani wanda Hayatuddeen ke sakasu kamar ba gobe ta rasa me take ji a kanshi a haka ko mintuna 15 batayi ahaka ba, bacci ya ɗauketa, da diary milk riƙe ahannunta, takarasa akusa da bakinta, wayarta kuwa tabar data akunne saƙonni sai shigowa suke. Ɓangaren Saifuddeen kuwa saida akayi sallan isha kafun yake shigowa cikin gidan, sashin Umminsa yaje suka ɗan taɓa hira dasu Ahmad, sai wajen ƙarfe 9 ya nufo part ɗin nasu, kaitsaye ɗakinsa ya wuce, wanka yayi tare da shirya kansa cikin wasu kayan bacci masu taushi, sun kuwa yi masa kyau sosai, turarensa maidaɗin ƙamshi ya fesa, sannan ya nufi ɓangaren Ameena. Ahankali ya murɗa ƙofar ɗakin ya shiga, tana nan zaune akan gado, ko kayan bacci bata saba, ta zuba uban tagumi, ga kuma idanunta da suka cika da ƙwalla, gaba ɗaya komai bayayi mata daɗi, sam arayuwarta bata ƙaunar taga ranan girkin Zaleeha ya zagayo, saboda batason abun dazai nesanta ta da Saifuddeen ko kaɗan. Ganin yanda tayi tagumi ne yasashi ƙarasowa cikin ɗakin, hannun da tayi tagumin dashi ya sauƙe ƙasa tare da ɗan shafa gefen fuskarta, cikin body language ɗinsa ya dubeta, tare dayi mata alaman cewa. "Meke damunta?" Kallo ɗaya tayi masa ta kawar da kanta gefe, zuciyarta duk ba daɗi, sanin cewa idan ya matsa mata da tambaya, zata sake bayyana kishinta ƙarara, yasashi ɗan ƙarasawa ya sakarwa Adeel kiss agoshinsa, hannunta ya kamo, tare da ɗan lumshe idanunsa, alama yayi mata kan cewar saida safe, sannan ya juya akalan kekensa, tana kallonsa ya fice daga cikin ɗakin. Samun kanta tayi da danne kishinta, kan gado ta faɗa tare da jawo pillow ta rungume tana fidda zazzafan numfashi. Shikuwa Saifuddeen yayi hakanne dan shine abun da yafi dacewa, saboda yasan tsayuwarsa awajen nata, tamkar ƙara mata wutar kishi ne acikin ranta. Ta cikin falonsa yabi, inda ya shiga sashin Zaleehan, dama baiyi tunanin ganinta acikin falo ba, hakan yasashi wucewa ɗakinta, ahankali ya tura ƙofar ɗakin ya shiga, sassanyan ƙamshin turare da kuma sanyin AC ne ke tashi acikin ɗakin, ɗan lumshe idanunsa yayi, tare da buɗewa, hangota da yayi akan gado ne yasashi ɗan ƙarasawa. Idanunsa ya zuba mata, tundaga kan ƴar yatsar ƙafarta yake kallonta, har ya gangaro zuwa ƙirjinta, wanda rabin breast ɗinta suka fito ta saman rigar, ga kuma shatin nipples ɗinta da suka bayyana kansu, ta cikin rigar, wani irin zubawa yaji tsikar jikinsa nayi, take yaji jijiyar jikinsa na neman miƙewa tsaye, saboda sexy dress ɗin dake jikin Zaleehan ya isa hautsuna tunanin duk wani ɗa namiji me lafiya, ahankali yaɗan lashi lips ɗinsa, tare da kai dubansa ga fuskarta, baccinta take cikin nutsuwa, ga kuma diary milk ɗin dake riƙe ahannunta, wani kyakkyawan murmushine ya suɓuce masa, saboda ya lura bata shiryawa baccin ba ya ɗauketa, gab da ita ya ƙaraso, tare da kai hannunsa yaɗan zare diary milk ɗin dake hannunta, ganin cewa chocolate ɗin yaɗan ɓata mata baki ne yasashi, kai hannunsa saman tausassun ƙaɓɓanta, yaɗan goge mata, wayarta ya ɗauka, tare da kashe mata datan, ya ɗaura mata wayar akan bedside, hannu yakai yaɗan shafi lallausan gashinta da ya watse akan pillow, anutse ya ɗan haɗe mata gashin nata waje ɗaya, idanu ya tsurawa kyakkyawar fuskarta, ji yake kaman ya buɗe cikin jikinsa ya sata aciki, kayan sunyi mata matuƙar kyau, ga kuma kyawawan breast ɗinta dake mugun ɗauke hankalinsa, saman breast ɗin nata yaɗan shafa, wani irin zut zut haka yaji mararsa nayi masa, take duk wani kuzarinsa ya kau, ahankali yaɗan ranƙwafo da kansa, kiss ya manna mata agoshinta, tare da ɗan shafa gefen fuskarta, jikinsa amatuƙar mace ya jawo blanket ya rufa mata, rage mata hasken wutan ɗakin yayi, sannan ya juya ya fice, gaba ɗaya jikinsa amace yake, wani irin fitinannen sha'awarta ne ke taso masa badan yasa a ranshi sai yaga ta nuna begenta gareshi zai kusancetaba tabbas da yau zai rabata da budurcinta, kaitsaye ɗakinsa ya koma ya kwanta, duk yanda kuwa yaso bacci ya ɗaukesa abun ya gagara, dan wani irin feeling ɗin Zaleehan yakeji, haka ya dinga juyi akan gado yana lumshe fitinannun idanunsa, sai wajen ƙarfe ɗaya kafun bacci ɓarawo ya sace shi. Ameena kuwa, yaƙi tasha da zuciyarta harta godewa Allah, babu abun dake ɗaga mata hankali kamar yanda zuciyarta, ke raya mata cewar. "Yanzu haka Saifuddeen ɗin nacan jikin Zaleeha, sai take tuno yadda ta samu Ya Amir da Dina sai tanaga yanzu shima Saifuddeen da Zaleeha suna can manne da juna." wannan tunanin shike ƙara dagula mata lissafi. Haka nan ta tsinci kanta da cewa. "To sai meye ba matarsa bace, in sha Allah daga yau bazan sake sawa raina damuwar kishin baiwar Allah nan da take son ɗanaba". a haka tayi bacci cikin sanyin rai. Washe gari da safe kuwa, Zaleeha ita kaɗai ta shiga kitchine tayi musu break fast, simple foods kawai tayi musu, sai kuma chicken egg rolls. Ko awajen breakfast ɗin gaba ɗaya fuskar Ameena babu wata alamar damuwa, haka takejin zuciyarta a sauƙaƙe, cin abincin kawai take hankalin na kan wayarta. Saifuddeen kuwa duk yana lure da ita, har acikin ransa yana fatan Allah ya ragewa Ameenan kishinta, dan yaga alama da kishin na sawa tana takura kanta da yawa, gashi kuma wacce take kishin dan ita, batasan ma tanayi ba, wannan shine sakai a wahala sai dai ya lura da nitsuwar zuciyarta. Tun kafun sugama break fast ɗin ta miƙe dan tafiya wajen aiki. Ya lura kamar bata fiyo son zaman gidanba yanzu tafi jin daɗin tafiya aikinta in ba ran girkinta bane. Cikin kula Saifuddeen ya dubeta cikin body language ɗinsa yace. "Ta tafi da Adeel, dan jiyama da tabarsa kuka yayi tayi." Gane hakan yasa Zaleeha ɗan marairaice fuska dan kwata kwata batason atafi da Adeel ɗin. Ameena kuwa ɗan jim tayi tana kallonsa, dan itama bawai tanason tafiya da Adeel ɗin bane, saboda idan taje dashi ma baya barinta tayi aikinta yanda ya kamata. Ummi ce tace. "A'a meyasa za a tafi dashi, dan kawai yayi kuka jiya, ai baizama lalle yau yayi ba." Cikin zumuɗi Zaleehan tace. "Eh kuma ma idan yayi kukan zan dama masa madaransa yasha, nasan ma bazaiyi kuka ba, jiyan ma halan wani abune ke damunsa, dan naɗanji jikinsa da zafi kaɗan, ko kuma kunnensa ne keyi masa ciwo." Tsumammun idanunsa ya zuba mata, da hannu ya nunata cikin body language ɗinsa yace. "Idan yana kuka kuwa, kyasan yanda zakiyi dashi." Kanta ta jinjina masa, alaman. "Eh taji ta yarda." Kansa ya jinjina, tare da ɗan sakin ɓoyayyen murmushi me ɗauke da ma'anoni kala-kala. Ameena kuwa ganin haka yasa, taɗan saki murmushin yaƙe, har acikin ranta tanajin daɗin yanda Zaleehan ke nunawa Adeel ɗin ƙauna, saidai kuma babu yanda ta iya da kishin dake cikin ranta, batare da ta karɓi Adeel ɗin ba, tayiwa su Ummi sallama, cewar ta wuce wajen aiki. "Adawo lafiya." suka mata sannan ta fice daga cikin falon. Ahaka dai suka kammala break fast ɗin, kowa yayi nasa ɗakin, Zaleeha kuwa anan falon Ummi ta zauna tana yiwa Adeel ɗin wasa, sai ƙyalƙyala dariya yake, har dimples ɗinsa na lotsawa. Hayatuddeen ne yazo ya zauna sunayiwa Adeel ɗin wasa. Saifuddeen kuwa wanka yasakeyi, bayan yagama kimtsa kansa ne yayiwa sule driver magana suka fita, kasancewar duk kwana biyun nan suna da meeting. Zaleeha kuwa yau gaba ɗaya asashin Ummi ta wuni, ita da Raleeya ne suka ɗaura dinner, koda suka kammala tuni yamma ta rufa, dan kusan ƙarfe 5 ake nema, nan wajen Ummi ta ajiye Adeel ɗin, tare da cewa Ummi zataje tayi wanka. Ai kuwa tana fita daga falon Ummin Adeel yasaka kuka, Ummi ne ta ɗaukeshi tana ta faman rarrashinsa amma fir yaƙiyin shiru. Zaleeha kuwa tana isa bedroom ɗinta, ta soma rage kayan jikinta, wani ɗan mini towel ta ɗaura ajikinta, sannan ta shige bathroom, ruwan wanka meɗan ɗumi ta haɗawa kanta, tare da zuba wani irin fitinannen turare acikin ruwan, wankanta tayi cikin nutsuwa tare da ɗauro alwalan magriba, wani baby pink towel ta ɗaura ajikinta, wanda iyakansa cinyarta, haka ta fito daga cikin bedroom ɗin tana tsane jiƙaƙƙen gashin kanta. Saifuddeen kuwa tun safe daya fita sai yanzu yake dawowa cikin gidan, kaitsaye sashin Ummi ya nufa, yana zuwa kuwa yasamu Ummi nata zirya afalo Adeel na ɗauke akan kafaɗanta, sai kuka yake, rarrashin duniya kuwa tayi masa ya ƙiyin shiru. Ummi naganinsa tace. "Yauwa Saifuddeen, wallahi Adeel tun ɗazu yaƙiyin shiru, nayi rarrashin amma abanza, anya kuwa ba wani abune ke damunsa ba?." kansa ya girgiza alaman rashin sani, tare da kai hannu ya amshi Adeel ɗin, jijjigasa yasomayi amma yaƙi daina kukan, kallon Ummi yayi cikin body language ɗinsa yace. "Ina Zaleeha?." "Zaleeha taje wanka, amma nasan yanzu zata shigo." Kansa ya jinjina, sannan ya juya akalan kekensa, yana rungume da Adeel ɗin haka yafice daga cikin falon. Kaitsaye sashin Zaleehan ya nufa, dan har yanzu Adeel ɗin kuka yake. Zaleeha kuwa tsaye take agaban mirror tana tsane gashin kanta, yayinda towel ɗin jikinta yasoma ɗan warwarewa. Ahankali ya tura ƙofar ɗakin ya shiga, dai-dai nan Adeel ya saka wani sabon kuka, amatuƙar razane Zaleeha ta juyo sakamakon jin kukan Adeel, ganin Saifuddeen ɗin rungume da Adeel yasa gaba ɗaya duk ta ruɗe, gaba ɗaya mantawa tayi cewar towel ne kaɗai ajikinta, cikin hanzari ta nufosu, hannu tasa ta amshi Adeel ɗin tana ɗan bubbuga bayansa, tare da ɗaurasa akan kafaɗanta, cikin kulawa tace. "I am so sorry papyna, natafi nabarka ko, am sorry bazan sake ba." ɗan bubbuga bayansa take tana jijjigasa, amma hakan baisa ya daina kukan ba, hankalinta aɗan tashe ta buɗe fridge, ruwa taɗan ɗiba ta bashi yasha, still kukan nasa ƙaruwa yayi, hankalinta amatuƙar tashe ta ɗauki flask tare da haɗa masa madaransa aɗan ƙaramin cup ta bashi, sha ɗaya yayi ya ɗauke kansa, tare da sa mata ihu, haryana ciccilla ƙafa, hankalinta ne yayi matuƙar tashi, dan taga kaman Adeel ɗin na koƙarin shiɗewa, gaba ɗaya ta manta cewar daga ita sai towel ajikinta. Saifuddeen kuwa idanu ya zuba mata, ya kasa koda kiftawa, sosai body structure'n ta ke tafiya da tunaninsa ga kuma kukan ɗansa. Hankalinta aɗan tashe ta ɗago ta kalli Saifuddeen ɗin, ɗan marairaice fuska tayi, tare da nuna masa Adeel ɗin, tace. "Hamma Saif me yakeso? Meya sameshi? Faɗuwa yayi ne?". dan kuka yaron yake sosai. Baki ya taɓe tare da ɗaga mata kafaɗa, alaman. "Ohon miki kisan yanda zakiyi dashi, ai dama nafaɗa miki, kikace kinji kin gani." Shagwaɓe fuska tayi, take idanunta suka ciko da ƙwalla, jikin Adeel ɗin ta shiga tattaɓawa, wai ko wani abune keyi masa ciwo, anan kan gado ta zauna tare da rungume Adeel ɗin ajikinta tuni hawayenta sun fara zubowa, cikin tausayawa tace. "Bani number Momynshi in kirata ta dawo". Ahankali ya ɗan turo kekensa, har ya ƙaraso gab da ita, Ido ya zabuma mata ganin gaba ɗaya a gigice take, hannunsa yakai jikinta, tare da kunce towel ɗin dake ɗaure kan ƙirjinta. Cikin tsananin tsoro da firgita haɗi da mamaki ta zaro Idanunta amatuƙar tsorace tana kallonsa, ƙoƙarin janye jikinta baya tasomayi tare dasa hannu zata janye towel ɗin ta rufe ƙirjinta, hannunsa yasan ya damƙi nata hannun, wuƙi-wuƙi tayi da idanunta gaba ɗaya jikinta rawa ya ɗauka, Shi kuwa Hamma Saif tallafo kan Adeel ɗin yayi da hannunsa ɗaya, ba zato ba tsammani taji ya sa hannunshin ɗaya ya kamo nononta tare da manna mata bakin Adeel akan nipples ɗinta. Wani irin gigitaccen zillo Zaleehan, tayi jin Adeel ɗin ya cabke bakin nononta yana yi mata wani irin fitinenne tsotsa. Idanu Zaleeha ta kuma zarowa afirgice, kanta ta soma girgiza tare da ƙoƙarin ƙwace jikinta, riƙeta yayi ƙam, cikin body language ɗinsa yace. "Sai kiyi ai! dole sai yasha, wayace ki hana mamansa ta tafi dashi, kinsan abun da yakeso ai zaki zauna ki sani a gaba yana kuka kina min kuka". Gaba ɗaya jikinta ne ya ɗauki rawa da karkarwa sai zazzare idanu takeyi tuni wani fitinenne zufa ya karyo mata, hannunta taketa yarfawa tare da fidda sautin. "Hshhhhhhh wayyo Hamma Saif wlh zafi dan Allah ka bari, wlh bazan sake cewa mamanshi ta barshi ba". Adeel kuwa ƙam ya kama nipples ɗin nata yana ta sha, duk da cewar babu abun dayake zuƙowa, amma bai sake mata nonon nata ba, sai ajiyar zuciya ya ke sauƙewa, idanunta ta rumtse tare da cije laɓɓanta, wani iri takeji ajikinta, yayinda zufa keta keto mata, ko ina ɗinta rawa yake ga riƙon da Hamma Saif ɗin ya mata bana wasa bane, cikin mintunan da basu wuce 7 ba bacci ya ɗauki Adeel, ganin haka Saifuddeen daya kafeta da mayun idanunsa, ya ɗan janye Adeel ɗin daga jikinta tare da kwantar dashi can gefe dungun gadon. Sauƙa daga kan wheelchair dinsa yayi tare da zama akusa da ita, jin ya zare Adeel ɗin ajikinta, yasa ta tashi da sauri cikin hanzari ta nemi hanyar guduwa, hannunta ya kamo, Da sauri ta janye hannunta tana neman hanyan gudu, murmushin mugunta yayi tare da kamo gefen towel ɗin jikinta, take kuwa towel ɗin jikin nata ya faɗi ƙasa, gashi dama banda towel ɗin babu komai ajikinta, Idanunta ta zazzaro da azaban ƙarfi, atsorace ta fasa ihu, tare da juyowa cikin hanzari ta faɗa jikinsa, ta rungumesa ƙam-ƙam dan wai kada ya samu ya ganta, ganin haka yasashi jawota saman gadon ta faɗo kansa, blanket ya ja tare da rufesu rib. Idanunta ta rumtse gaba ɗaya jikinta rawa da karkarwa yake, cikin zafin nama yaɗan mirgona da ita gefensa, yazamana fuskansu na kusanci dana juna. Idanunsa yaɗan lumshe asanyaye, ya ɗaura jajayen laɓɓansa akan nata, cikin wani irin fitinannen yanayi ya kamo lips ɗinta na ƙasa ya tsotsa, atare tsikar jikinsu suka shiga zubawa. hannunsa ya ɗaura adai-dai tsakiyan bayanta, ahankali ya zura harshensa acikin bakinta kana ya fara lalumo harshenta, dai-dai lokacin kuwa breast ɗinta suka haɗe da chest ɗinshi, atare suka sauƙe wani irin zazzafan ajiyar zuciya, mai dauke da wani irin rikitaccen numfashi. Sauƙan harshensa acikin bakinta, tamkar zuma ne yake lasa, haka yakeji, laɓɓansu ne suka haɗe waje ɗaya, ahankali ya ɗanyi sucking harshenta, wanda daɗinsa ya zarcewa sweet, cikin wani irin yanayi ta samu kanta, numfashi me zafi ta fitar tare da..... Wannan littafin na kuɗine in kina buƙata ga number da zaki yiwa mgn 09097853276 . _Wannan shafin nakine ke ɗayanki, Fatima About MRS Sardauna Tare Ali Ibrahim Wambai inayi muku fatan Al'khairi a rayuwarku dan manyan suna gareku sunayenku nada daraja a gareni sunan uwa da uba ba wasaba🤝🏻🥰🥰🥰_ [26/09, 1:17 pm] +966 59 285 4006: _Littafina na kuɗi ne, biya ki karanta halal ɗinki babu haƙƙin kowa a kanki, turo katin mtn na 300 ta wannan number 09097853276 ko kuma kiyi min transfer ɗin ɗari uku kacal ta Bank account na 0005388578 jaiz back Aisha Aliyu GARKUWA_ Sayan na gari maida kuɗi gida. Ngsett Da sauri ta rumtse idanunta da azaban ƙarfi, dan wani irin firgici da tsorone ya rufeta, kanta ta fara jujjuyawa a nufinta ta kwace kanta, gane hakan ne yasa yasa hannunshin duka biyu ya tallebe kanta da kyau, wani irin fitinenne kiss yakeyi mata tongue to tongue. Dib-dib haka zuciyarta ke harba da sauri-sauri, gaba ɗaya jikinta kerma yakeyi lokacin da taji ya sake kanta ya meda hannunshi kan breast ɗinta wani irin shafa yakeyi musu da matsesu tamkar zai maida hannunshin cikinsu, hannu tasa tana son ɗauke hannunshi daga kan ƙirjintan amman ina bata da wani sauran ƙarfi dan gaba ɗaya tsorone ya cikata, tattaro sauran ƙarfinta tayi ta tashi ta zauna ganin ya ɗan saketa jiki na rawa, ta koma gefe, cikin wani irin yanayi shima ya tashi ya zauna kan ƙafafunshi, hannu ya miƙa mata alamun tazo, da sauri ta fara girgiza mishi kai tuni hawaye na kwaranya murya na rawa cikin tsoro tace. "Dan Allah kayi haƙuri kayi haƙuri". ido ta rumtse jin ya matsota, kamar a mafarki taji ya jawota jikinshi ya ruggumeta tsam a jikinshi, hannunta ya kamo ya ɗaura kan wuyanshi tare dasa hannunshi kan nata, ya zama suna fuskantar juna, Idanunshi da suka koma kalan bacci ya jujjuyawa mata tare da ɗan zare harshenshi ya ɗan karkaɗa matashi, kai taci gaba da jujjuyawa cikin tsoro, wani zazzafan numfashi taja jin ya manne bakinsu wuri ɗaya, wani irin sahirtaccen tsotsa ya fara yiwa pink lips ɗin ta wanda yasa yaji, Wani irin harbawa Saif ɗinshi tayi wanda bai san lokacin da yayi wani irin zillo ba, ya sunkuyo ya manna bakinshi kan nipples ɗinta, da ɗan ƙarfi ta saki wani irin ƙara, tare dayi zille ta gantsoro ƙirjinta sai ta kuma ɗame jikinta a son ta ƙwace kanta, hannunta ta cusa cikin sumar kanshi, jin wasu abubuwa na shiga jikinta ata duk inda ƙofar gashi yake, yam-yam takeji abun na ratsata, shi kuwa yadda ta cusa hannunta cikin kanshi zuwa wuyanshi sai kawai ya rinƙa karkarwa dan ji yake Saif ɗinshi zata faso boxer ɗinshi zatayi yo woje zata nemi abincin ruhinta. yunƙura yayi da sauri ya zauna kan sawunshi, jawota yayi da ƙarfi ta faɗa jikinshi, hannunshi ɗaya yasa ya kunce mazargin wondonshin, kana yasa ɗaya hannun ya kamo hannunta duka biyu ya cusa su cikin wonɗon tare da kamo Saif ɗin nashi ya cusa mata shi cikin tafukan hannunta. Wani irin tsalle da ihu Zaleeha ta saka tare da zare hannunta, cikin tsananin firgita da tsoro ta koma can gefe dungun gado gaba ɗaya jikinta karkarwa yakeyi kuka mai cike da tsoro ta fashe dashi kana tanata yayyarfa hannunta, yayinda jikinta ke tsuma wata azabebbiyar zufa ta tsoro ta karyo mata, hannunta take yayyarfa da ƙarfi tana cewa. "Wayyo Allah na, Wayyo Ummi." shi kuwa Hamma Saif wani irin gigitaccen riƙo yayi Saif ɗinshi daketa neman inda zai shiga, ida nunshi duk sun juye sunyi kalan ƴan maye, wani irin fizgar numfashi yakeyi, ganin yadda jikinshi ke ɓari yasa, Zaleeha tattaro sauran ƙarfinta, ta sauƙa kan gadon, da sauri ya yunƙura dan kamota amman ina kafin ya miƙa hannunshima tuni ta isa ƙofar bathroom ɗin. Tana shiga kuwa ta meda ƙofar gib ta rufe, kan bakin bathtub ɗinta ta zauna ta cusa kanta cikin cinyoyinta, numfarfashi mai cike da tsoro ta saki tare da dafe ƙahon zuciyarta da takeji kamar zai faso ƙirjinta ya fito. Shi kuwa Hamma Saif, wani irin tsuma da ɓari jikinsa keyi, konciya yayi rub da ciki yanaji tamkar yaci babu, a hankali ya fara fidda zazzafan numfashi, can kuma sai ya fara sauƙe ajiyan zuciya kamar wanda yasha kuka ya ƙoshi, jiki a mace yaja kekenshi ya hau ya zauna, side ɗinshi ya nufa. Ita kuwa Zaleeha tsoro ta shiga sosai Allah ma ya sani tana jin tsoron shi, bare yau daya ƙara firgitata da wannan babban abun nashi mai ɗan karen ƙarfi da girma, ji takeyi kamar har yanzu abun na cikin hannunta, lokaci ɗaya taji, wani zazzafan zazzaɓi yana sauƙo mata, jin ƙaran an buɗe ƙofa an fitane yasa ta miƙe jiki na rawa ruwan ɗumi ta sakarwa kanta dan sosai takejin sanyi na ratsata, bayan tayi wonkan ne ta kuma yi al'wala sannan ta fito a hankali saɗab-saɗab haka ta isa tsakiyar, ɗan ƙaramin towel ɗin dake jikinta ta cire, bata tsaya goge jikinta ko sa bra and pant bata tsaya yiba, ta zura wata doguwar riga mai faɗin, hijabi ta kuma zurawa dan sosai takejin sanyin zazzaɓi da tsorone ya sauƙar mata shi, sallaya ta shimfiɗa dai-dai lokacin kuma taji anayin sallan isha, cikin ranta take cewa. "Allah zai saka min kazo tun ƙarfe shida kaita lallatseni kana luguiguitamin nono, har mu makara sallan magriba". sai kuma ta gyara lulluɓin nata ta kabbarta sallan. A can sashin Hamma Saif kuwa, ji yakeyi tamkar ya kirawo Ameena tazo ta rage mishi zafi ta amman ba hali. Kai tsaye bathroom ɗinshi ya wuce, ruwan sanyi ya saukarwa kanshi wai ko zaiji sanyi ƙarfin sha'awarsa ya ragu. Kuma Alhamdulillah ruwan sanyin ya rage kaifin fitinar da yake ji ɗin al'wala yayi, Koda ya fito ya dubi time tuni yasan an idar da sallan isha, hakanne yasa yayi sallam magriba da ishan a gida, yana idarwa ya cire jallabiyar da ya saka, wasu fararen kaya ya zaro yadin plen yadine fari ƙal irin yadi mai taushin nan, kintsawa yayi cikinsu sosai sukayi masifar mishi kyau, farar hula yasa, kana yasa farin takalmi, ya fito ras dashi gashin giran shin nan ya kwanta lib-lib dashi hakama sajenshi, red lips dinshi sai sheƙi sukeyi, wani irin farin ciki yakejin kanshi a ciki tamkar wanda akayiwa bushara da daddaɗan labari. Kai tsaye side ɗin Umminshi ya nufa dan a tunaninshi Zaleeha ta gudu can. Ita kuwa Zaleeha tana idar da salla, da kyar ta lallaɓa ta koma kan gado, jiki na rawa ta konta ba tare da ta cire hijabin jikinta ba, a hakanma kuma taja blanket ta rufu rif kana taja Adeel kusa da ita, lokaci ɗaya kuma zazzaɓin ya turnuƙeta. A falon Ummi kuwa ana gabda kiran sallan magriba Ameena ta dawo, so a nan ma tayi salla, magriba da ishan, ita da Raliya Ummi kuwa na cikin ɗakinta, Hayatuddeen kuwa yanzu ya shigo shida abokinshi Khamis wanda suna can yawonsu ne motar Khamis ta samu ƴar gyara shine suka miƙata wurin kanikawa, to kasan cewar suna kusa da gidansu Saifuddeen ɗin ne shiyasa Hayatuddeen ya jawoshi suka taho. A tare suka shigo da Ahmad, a falon suka zauna suna hira, koda Ummi ta fito Khamis kamar mutumin kirki haka ya duƙa ya gaidata a mutunci, cikin kula Ummi ta amsa, kana ta juyo ta kalli Ameena dake zaune cikin kula tace. "A a Ameena ina sarkin kukan?". Murmushi ta ɗanyi tare da cewa. "Yana can wurin Amminshi nima tunda na dawo ban gansuba, shiyasa nai sallana ananma dan nasan da zaran sunji motsina za suzo su liƙa minshi ya hanani salla akan lokaci yace sai yasha nono". Dariya Ummi ta ɗanyi kana tace. "Dama ai haka iyayen yara suke, kuma yau wuni yayi kuka inaga ya fara gajiya da barinshi da akeyi duk yau ya gigitamu". Hayatuddeen ne ya ɗan kalli Ummi tare da cewa. "Ato gobe in zaki tafi ki tafi dashi kar a shiga haƙƙinshi". Murmushi Ameena ta ɗanyi kana tace. "Gobe kam ma ina off, zamu wuni a gida ya kontar da hankalinshi". Raliya ce ta miƙe tare da cewa. "Ai yama yi ƙoƙari wlh". Ahmad kuwa hankalinshi na kan system ɗinshi, Khamis kuwa murmushin yake ɗanyi, dai-dai lokacin, Saifuddeen ya shigo, da sauri Hayatuddeen yace. "Kai masha ALLAH Hamma na kayi kyau". Wani irin yalwataccen Murmushin Saifuddeen yayi wanda da zaran ka ganshi kasan yana cikin farin ciki, gaban Umminshi yazo ya gaidata in boddy language ɗinsa cikin kula tace. "Ina sarkin kukan?". Ido ya lumshe tare da mata alamar yayi bacci. sai kuma ya ɗan juyo ya kalli Khamis dake gaidashi, amsa mishi yayi yana mai ƙara karantar yaron, sai kuma ya kalli Ahmad dake, ta aiki yasan tabbas aiyuka sunyiwa Ahmad yawa sabida sunata harharde komai da komaine nasu, wuri ɗaya nanda wata uku cikon shekara zaiyi kuma yana son ya ware haƙƙin Hayatuddeen da Adda Rahma da Raliya da Raihana ya basu nasu tunda kowa yasan haƙƙinshi daya mallaka Dan ma Allah yayi tuntuni ya warewa Bappa Ali da Goggo dada nasu, ya bar musu wannan filin na suka bawa MTN hayarshi, inda bappa Ali kan karɓi hayan shekara biyu kana goggo dada ta ƙarɓi na shekara ɗaya kamar dai yadda shariya ya tsara. Hannu ya bawa Ahmad sukayi musabaha, kana ya juya ya kalli Hayatuddeen dake ta tuttura baki wai Hammanshi bai ƙulashiba, murmushi yayi kana ya ɗan shafa gefen fuskar daya fara tara ƙasumba, yayi kyau sosai cikin shigar ƙananan kaya rigarshi mai kalar sararin samani da ratsin fari sai ya fito kamar adon gajumare a cikin sararin samaniya wondonshi baƙine mai ɗan rashin ruwan ƙasa-ƙasa. Sosai siffofin girma suka fara bayyana a jikin autan Ummi, in boddy language ɗinsa yace. "Fushin me kakeyi zaka bata fuskarka da yawan tura bakin nan da kakeyi gashi yanzu bakinka ya zama ƙato". Da sauri yace. "To na bari dariya sukayi baki ɗayan su. Ameena kuwa wani irin daɗi takeji dan, duk sansa zasu haɗa ido sai yayi mata signal da girarshi ɗaya, kana ya ɗan zaro mata harshe. Ummi ce tayi nufi dinnin area tare da cewa. "Kuzo muje muci abinci". miƙewa sukayi baki ɗayansu suka nufi dinnin table ɗin, har Khamis da Hayatuddeen ya kamo hannunshi, Raliya ce ta ɗan kallesu bayan sun zauna cikin kula tace. "Adda Zaleeha fa?". Ido Ummi ta zubawa Saifuddeen cikin yanayin tambaya, gane abinda take nufi yasashi mata alamun shi yana tsamman tana nan ai, Raliya ce ta miƙe tare da cewa. "To bari inje in kirata." To sukace kana Ummi tace. Ameena tasa musu. A hankali ta shiga cikin ɗakin Zaleeha da sauri ta ƙarasa ciki hangota konce a kan gado, cikin kula ta sunkuyo kanta tare da cewa. "Aunty Zaleeha! Aunty Zaleeha". Da kyar ta buɗe idanunta da takejin suna ciccikowa da hawaye dan haka take in dai bata da lfy tofa sai hawaye, cikin tsoro Raliya tace. "Aunty Zaleeha bakida lfy ne?". Kai ta gyaɗa mata murya na rawa tace. "Zazzaɓi nakeji, ƙirjina kuma nata bugawa". Cikin tausayawa Raliya tace. "To tashi mu tafi cikin gida kici abinci sai muje asibiti ko a kira Ya Adnan yazo ya dubaki". Hawayen da suka cika mata idone suka silalo kana a hankali tace. "Ya isheni bana jin yunwa, kije kuci abinci". kai ta girgiza tare da cewa. "A a kam me kikaci daya ishekin bari inje gayawa Ummi." tana faɗin haka ta fita. Tana shiga ta samu Ameena na zuzzuba musu abincin cikin sanyi tace. "Ummi Aunty Zaleeha fa ba lfy, gaba ɗaya jikinta sai karkarwa yakeyi zazzaɓi takeji". Juyowa sukayi baki ɗaya suna kallonta cikin mmki Ummi tace. "Ikon Allah bata da lfy kuma itacefa tai girgin nan lfy-lafiya ta gama komai, ta tafi taje tayi wonka ne, ta bar Adeel a nan da babanshi ya dawo nema ya ɗaukeshi suka tafi." Ahmad ne yace. "Ummi Ciwo ba wuya ai." Shi kam Saifuddeen shiru yayi ya zuba musu ido a ranshi yake cewa. "Uhummm uwar tsoro zazzaɓi tsoro ko, zanyi mgninki ne yarinya, Allah ya ƙiki kiyi gangancin shiga ɗakina wannan al'kwarari ne duk randa ƙafarki ta kaiki ɗakina bazaki fito da budurcinkiba". Ameena ce ta ɗan yuƙura alamar zata tashi, cikin kula Ummi tace. "Ina zakije?". A hankali tace. "Ummi zanje in duba Ammin Adeel ne, ko akwai taimakon da zan iya mata". Cikin jin daɗi Ummi tace. "Zauna muci abincin, in mun gama muje mu dubata, Ke kuma Raliya ɗebi abincin ki kai muku kuci da ita". To Raliya tace kana ta ɗaukar musu abinci ta juya ta fita. Ameena kuwa har ga Allah taji, ciwon Zaleeha a ranta sabida koba komai Zaleeha na nuna kulawarta kanta da ɗan ta. Saifuddeen kuwa ji yayi tamkar ya ruggume Ameena a wurin, kimarta da darajar ta keta hauhawa a idanunshi, yana hasaso yadda rayuwa zatayi musu sanyi in Ameena ta kwantar da hankalinta. A haka suka fara cin abincin. Ba jimawa Raliya ta dawo da kular abincin cikin sanyi tace. "Ummi taƙi taci fa, jikinta zazzaɓin yayi zafi". Kusan a tare Ummi da Ameena suka miƙe, suka nufi side ɗinta. A hankali suka shiga Ummi na gaba Ameena na baya, Suna shiga Ameena ta ɗan sunkuyo kanta, cikin kula tace. "Ammin Adeel Sannu zazzaɓi haka ko zamu tafi asibiti ne?". Cikin ƙarfin hali tace. "Yauwa sannu Ummu Adeel ngd". Gefenta Ummi ta zauna tare da cewa. "Tashi ki zauna". Yunƙura tayi zata tashi da sauri Ameena taimaka mata ta zauna, a hankali Ummi tace. "Yaushe ya fara miki?". Ido ta lumshe tare sunkuyar da kai dan bata son suga hawayenta a hankali tace. "Ɗazune". Ameena ce ta amshi zancen da cewa. "To bari in kawo miki mgni". Da sauri ta jujjuya kai tare da cewa. "A a zai bari bar shi kawai Ummu Adeel". Ido ta dan zuba mata ganin yadda taketa gyara Adeel konciyarsa a hankali tace. "To ko allura za'ayi miki". Da sauri ta gyara zamanta tare da ture blanket ɗin wai dan ta nuna musu alamun cewa ta worke, garin hakan har ta tada Adeel. Hannu tasa ta ɗaukoshi tare dayin murmushin dole tace. "Ah ah babu komaifa na worke karki damu". Ta ƙarishe mgnar a fili a ranta kuwa cewa tayi. "Uhumm nasan muddin kikamin Allura yaseen nasan zanyi kuka, in kuwa nayi kukan naji kunya gaban uwar miji da kishiya da ƙannen miji, babuma ya Hayatuddeen in ya tasoni gaba naga ta kaina". Murmushi Ummi tayi dan ta gano tsoron allurar takeyi, Cikin kula tacewa Ameena. "Je ki kawo mata mgnin ta haɗiya". da sauri Amina ta fice ta nufi ɗakinta. Jim kaɗan sai gata da magungunan ita da kanta ta ɓalla ta bawa Zaleeha ta shasu da tea ɗin da Raliya ta kawo mata. Koda tasha a take sai tai ta ɗan gyatsa, ganin yadda Ameena ke kula da itane yasa Ummi fita ta koma ranta fal farin cikin. Alhamdulillah burinta da addu'arta ga Ameena ya karbu Allah ya sassauta mata kishinta. Ita kuwa Ameena hannu tasa ta karɓi Adeel tare da cewa. "Kawoshi ki samu ki huta,". Shafa kanshi tayi ta miƙa mata shi kana ta koma ta konta, Raliya ce ta ɗan kalleta cikin kula tace. "Ya Ahmad yace in miki sannu da jiki". Kai ta gyaɗa tare da cewa. "To, ngd". Shiru suka ɗanyi ganin alamun ta fara lumshe ido alamun zatayi baccine yasa Ameena ta miƙe gyara mata rufuwanta tayi tare da cewa. "Sai da Safe Ammin Adeel Allah ya ƙara sauƙin" . "Amin Amin ngd matuƙa". Zaleeha ta faɗi tana kallon Ameenan Raliya ma miƙewa tai tabi bayan Ameena bayan ta mata saida safe. Saifuddeen kuwa falon Ummi ya dawo ya zauna shida Hayatuddeen da Khamis, cin boddy language ɗinsa yacewa Hayatuddeen ya bashi wayarshi. Cikin ɗan Mamaki yace. "Wayata kuma Hamma me zakayi dashi?". Fuska ya haɗe kana ya kalli Khamis tare da mishi alamun ya miƙo mishi wayarshi. A daburce Khamis ya miƙa mishi, Ganin haka shima Hayatuddeen ya miƙa masa tasa wayar dan a zatonsa baisan code numbers ɗinsuba. Shi kuwa yana amsar woyoyin ya zurasu a al'jihunshi kana, ya turawa Sule text cewa yazo ya maida Khamis gidansu. Zuru-zuru sukayi da idanu sabida sun sha jinin jikinsu gashi ya haɗe musu fuska ba alamun wasa, Shigowar Sule ne ya sasu, juyowa garesu, jin yana ce musu. "Khamis Hamma Saif. Yace kazo in maida kai gida dare yanayi". Da sauri Khamis ya miƙe tare da cewa. "To gani nan zuwa, sai ya kuma juyo ya kalli Hayatuddeen ya mishi alamun ya amsar mishi wayarshi, cikin tsoron Hamman nashi yace. "Uhum Hamma Saifuddeen zai tafi ka bashi wayarsa". Wani irin kallo ya watsa musu wanda yasa dole sukayi shiru. sai kuma ya musu alaman sai gobe yazo ya amshi wayar. To sai dai a zatonsu bashida damar sanin me woyoyin nasu suka ƙunsa Da haka suka fita. Bayan Khamis ya tafine, shi kuma Hayatuddeen ya biya wurin Zaleehan ya mata sannu da jiki. Shi kuwa Saifuddeen tattaunawa suka ɗanyi da Ahmad ganin har goma ta rufa ne yayi musu saida safe ya nufi side ɗinsun. Ameenan kuwa yau bata wani ji zafin kishinba hakan kuma ya samune sanadin karatun ƙura ɗin da tasaka a wayarta ta ajiye kan pillow data ɗaura kanta sai wani bacci mai ɗan karen daɗine ma ya ɗebeta. Saifuddeen kuwa yana dawowa ɗauki shi kayan jikinsa ya rage. kana ya ɗan watsa ruwa, sannan ya fito boxer kawai yasa kana ya zura jallabiya a kai, turare ya fesa sannan ya kashe wutan ɗakin gaba ɗaya, kana ya nufi sashin Ameena. Murmushi jin daɗi ya rinƙa yi ganin tana baccinta yau ba kuka, fuskarta ya shafa kana ya sunkuyo ya sumbaci goshinta, cikin ranshi yace. "Alhamdulillah ya ALLAH ka jiɓanci lamurana ka haɗa min kan matana". Da haka ya juya ya fita, kana ya nufi side Zaleeha, yana tafe yana mgnar zuci. "Kawai dan na ɗan raɓeki sai zazzaɓi to yau a gado ɗaya zamu kwana zamuga ta tsiyar, dole nema ki saba dani wannan tsoron ai cutar dani zaiyi". A hankali ya tura ƙofar ɗakin, baccinta takeyi hankali konce, shiyasa har ya ƙaraso gaban gadon bata saniba. Jallabiyar ya zare daga jikinshi kana ya ajiyeshi kan bedside, ya rage dagashi sai boxer ɗin. A hankali ya hau kan gadon bayan ya kashe wutan ɗakin. addu'ar konciya yayi sannan ya shafa a jikinshi, kana ya kuma ɗago hannunshi yayi addu'an ya tofa a hannunshi , a hankali ya sunkuyo kanta borgon ya ɗan yaye kana ya fara shafa mata addu'ar, can cikin bacci taji alamun ana shafata, da sauri ta buɗe Idanunta kana ta yunƙura zata tashi, kamota yayi tsam ya haɗe bayanta da ƙirjinshi, ƙam hakan yasa ta kasa kwace kanta wayarshi ya lalubu kana ya ɗanyi rubutu, tare da kai wayar saitin fuskarta, ido ta zubawa rubutun. "Ki nitsu, ni babu abinda zan miki, mu konta kiyi baccinki". Ajiyan zuciya ta ɗan ja tare da shaƙan ƙamshin turaren sa Idanunta ta lumshe. Jin ta ɗan nitsune yasa ya sassauta riƙon da yayi mata, a hankali ya tura hannunshin cikin hijabin jikinta shafa wuyanta yayi, zufa sosai ta haɗa alamun zazzaɓin ya sauƙa. Jin hakane yasashi, tashi zaune da kyau kana ya jawo hannunta ya tada ita, ba musu ta tashi, hannunshin yasa ya cire hijabin, tana jin zafi shiyasa bata hanashiba, Ƙara jawota jikinshi yayi da kyau, da sauri ta riƙo hannunshi jin ya kunce igiyar rigar dake jikinta alamun zai cire mata rigar, wayarshi ya kuma ɗauka ya rubuta mata. "Bana son gardama, rigar zan cire miki zafi yayi yawa". Shiru tayi, sabida ya gama zance tunda yace mata baya son garda, kana Baba Malam ya mata kashedi kan mishi gardama, tanaji ya zare rigar ya cillata gefe, tuttura pillows ɗin dake kan gadon yayi ya bar ɗaya rak, a hankali ya jawota jikinshi, wani irin sassanyan ajiyan zuciya suka sauƙe a tare, sabida jin yadda fatar jikinsu ta haɗe wuri ɗaya, a hankali yasa hannu saman kan gadonta ta gefe ya lalubo rimot din Ac, gudun ac'n ya ƙara kana a hankali ya gyara blanket ɗin ya rufesu. Shiru tayi jikinta nayi wani irin tsuma, wani irin yanayi takejin kanta da zuciyarta tana jin wani abu mai ƙarfi game dashi fatarsu dake manne jikin na juna sai takeji tamkar jininsu ne yake gaurayewa dana juna, haka nan takeji kamar zuciyoyinsu na liƙewa dana juna ne, wani irin fitinenne daɗi ƙamshin jikinshi keyi mata, karon forko yau gata ita da mijinta a makonci ɗaya, tana jinshi yasa hannu ya ɗan shafi ƙirjinta, sai kuma ya ɗan sunkuyo, bakinshi ya ɗaura kan Sweet lips ɗinta ɗan sumbatarta yayi, sannan ya maida kanshi kan filon, kana ita kuma ya gyara mata konciyarta bisa jikinshi, a hankali yasa tafin hannunshi kan bayanta yana ɗan shafawa, har zuwa kan mazaunanta, wani irin miƙa tayi tare da motsawa kanshi ta gyara konciyarta. Sun jima a haka, duk basuyi bacciba kowa da abinda ke cikin ransa ita tasan baiyi bacciba shima kuma yasan itama batayi bacci ba. Hamma Saif kam farin cikinsa bazai misaltuba, yau shine da Zaleeha a gida ɗaya ɗaki ɗaya gado ɗaya borgo ɗaya pillow ɗaya kana a ƙarƙashin igiyar aure, lallai kam mahaƙurci mawadaci. Ita kuwa Zaleeha dib-dib haka zuciyarta ke bugawa, yau itane dai a jikin Hamma Saif, lallai ne duniya idan zakayi so kayi dan Allah in kuma zakayi ƙi kayi dan Allah, ka kuma yishi saffa-saffa dan son kan juye ya zama ƙi haka kuma ƙi kan juye ya zama so, sannan tsaurara kafiya masiface. Tana cikin nazarin taga hasken wayarshi a gabanta. "Bakiyi bacci bako?". Kai ta gyaɗa mishi alamun eh. Rubutu ya sake yi mata. "To meya hanaki baccin?". Kai ta jujjuya alamun babu, rubutu ya ƙara yi mata mai tsawo. "Tsorone ya hanaki bacci. ki rage wannan tsoron, kin taɓa jin akwai macen da aure ya kasheta ne?". Kai ta juya alamun babu, gyara musu konciyarsa yayi kana ya rubuta mata. "Duk inda nasa hannunki a jikina ki barshi a wurin ba abinda zan miki, tsoron nakeso ki rege". Shiru tayi, shi kuma gyara konciyarsa yayi a hankali yaja hannunta, bata hanashiba, kiss bayan hannunta yayi, kana ya ɗaura shi kan ƙirjinta, yanaja a hankali har zuwa kan mararshi, wuƙi-wuƙi tai da idanu, sai dai kuma jin hannunshin na kan nata shike sarrafa hannunta ne yasa ta kasa janye nata, ido ta zaro jin ya cusa hannunta cikin boxer ɗinshi, hannunshi yasa ya kamo abinda take masifar tsoron, yasa matashi cikin tafin hannunta kana ya rumtseshi da hannunshi, karkarwa hannunta ya farayi, jin haka yasashi ruggumeta da kyau da ɗaya hannunshin, haka yasa ta gaza janye hannunta sai karkarwa da yakeyi, tanajin yanayin wasu abubuwa da hannunta bisa Saif ɗinshi ba damar kwace hannu, can kusan awa biyu sai taji yana nishi tare da ruggumeta gam, sai kuma taji damshi-damshi cikin tafin hannunta. jin ya sake mata hannunne yasata, zaro hannunta, baki ta ɗan tura jin hannunta da abu, kaman madara cikinsa tasa hannunta tana gogewa tare tura baki. Murmushi yayi mai cike da jin daɗi ya jawo hannun nata ba zato taji ya goga mata hannun kan fuskarta, da sauri ta cusa kanta a wuyanshi tana gogewa, dariya yayi kana ya ruggumeta, sun jima a jikin juna a haka kafin can, ya miƙe ya hau kekenshi yaje yayi wonka, kana yana fotowa yace taje tayi wonka, cikin bacci-baccin daje tai wonka, kana suka konta liƙe da jikin juna a haka sukayi bacci. Asuban fari ya farka, kai tsaye bathroom ɗin ta ya wuce wanka ya kumayi da sosonta da sabulu ta kana yayi al'wala, sannan ya fito da towel a jikinshi, Jallabiyar sa ya zura dan ya bar mata boxer ɗinshi a bayan gidanta, ido ya zubawa fuskarta da baya cikin borgon, a hankali ya motso jikinta har yasa hannu zai tasheta sai yaga kwayar idanunta na motsawa alamar ta farka kunya ne ya hanata buɗe ido ganin haka sai yasa hannu zai yaye blanket ɗin, ai da sauri ta riƙeshi, girarshi ɗaya ya ɗaga mata kana ya fita ya tafi side ɗinshi yaje sauya shiga sannan ya nufi masallaci. Ita kuwa Zaleeha bayan tayi wonka tayi salla ne ta gyara ɗakinta, sannan tayi shigar atampa kana ta nufi cikin gida. A falo ta samu Adeel na zaune shi ɗaya, da sauri ta ƙarasa gareshi ɗagashi tayi ta ruggumeshi tare da cewa. "Ayyah my papy aka bar min kai kaɗai a falon". Murmushin Ameena tayi wacce ta fito daga kitchen, da alamun breakfast take shirin haɗa musu, cikin kula tacewa Zaleeha. "Ina kwana". Murmushi Zaleeha tayi tare da cewa. "Naƙi wayon, ki ɗaga min gaisuwa ki samu lada mai yawa". Murmushin sukayi baki ɗaya kana Ameena tace. "To ai kullum kece kike samun ladan. Dan haka yau nawane,ina kwana ya jiki?". Cikin jin daɗin yadda Ameena ta sake mata fuska tace. "Lfya ji kam da sauƙi bari inje in gaida Ummi inzo muyi aikin". Tana faɗin haka ta wuce ɗakin Ummi. Raliya da ke sauƙowa kan step ne ta kalli Ameena cikin ganin darajarta tace. "Barka da safiya Aunty Ameena". "Barka dai Goggon Adeel ya gajiyan aiki?" "Gajiya tabi lfy". Raliya ta faɗi tana ƙoƙarin shiga kitchin. Dai-dai Lokacin kuma Ummi da Zaleeha suka fito, cikin sakin fuska, tacewa Raliya. "Kuje ku huta yau tunda ina off ni zan mana girki". Zaleeha ce tace. "Ato ai baki hutaba kenan, bari kawai muyi". Dariya Ameena tayi tace. "Uhum Ummi kiji mara lfy da ƙarfin hali, toma na gama komai saura kaɗan". Shigowar Ahmad da Saifuddeen da Hayatuddeen ne yasasu juyowa garesu. bayan duk sun gaggaisa ne, Ameena ta koma kitchin dan ƙarisa aikinta, tuni ta fara jera musu abin ci dana sha ɗin. A tsakar falon Ummi kuwa duk nacin Saifuddeen nason su haɗa ido da Zaleeha taƙi bashi dama, dan wata iriyar zazzafar kunyarshi takeji takanji wani daɗi a ranta in ta tuna yadda suka kwana jikin juna jiyan. A haka sukaje kan dinnin table, sukayi breakfast, kuma sosai girkin Ameena yayi daɗi, suna gama cin abinci. Hayatuddeen ya tafi school, Ahmad kuwa ya tafi kasuwa. Zaleeha kuwa dole ta bar falon Ummi dan ta lura Hamma Saif ƙureta yakeso yayi idanunshi na fitinar. Koda ta fita baccinta taje tayi a ɗakinta. Ita kuwa Ameena da Ummi da Raliya da hira sukayi tayi. Kana Saifuddeen kuwa ya tafi ofishin su na DSS. 12 dai na rana, Zaleeha na cikin baccinta taji ana jan ƙafarta da sauri ta buɗe idonta. cikin mmki ta tashi ta zauna ganin ƙawarta Rashida, cikin jin dadi tace. "Rashida kece a gidana kai yau naji daɗi". Dariya Rashida tayi tare da cewa. "Iye amarya Hamma Saif kina hutawanki wannan bacci haka, nayi sallama yafi baki biyar ba amsa". Musussuka ido tayi tare da fuskarta Rashida data zauna kan bedside cikin, yanayin bacci tace. "Wallah jiya da dare ban samu isasshen bacci bane, zazzaɓi ne ya rufeni". Dariya Rashida tare da cewa. "Ni bance ki gaya min abinda ya hanaki bacci ba". miƙewa tayi da sauri ta nufi falo da nufin kawowa Rashida ruwa, bin bayanta Rashida tayi, koda ta ciro goran ruwa a firiji da kuma juice, tsakiyar falonta suka zauna ita da Rashida, bayan tasha ruwa suka gaisa cikin sanyi tace. "Ban san kin dawoba sai shekaran jiya Ya Ishaq ya gaya min, wai ashe tun randa Adda Maryam ta rasu kika dawo. Nace meyasa bai gaya min da wuriba, sai cemin yayi wai suka sani ko zaki sake guduwa". Kanta ta sunkuyar cikin sanyi ta kamo hannun Rashida murya a sanyaya tace. "Kice ma Ya Ishaq bazan sake guduwa ba har gaban abadan sai dai in mutuwace ta gudu dani, kice masa tun a forkonma kaddarar zuwan Ummu Adeel da haifan Adeel ne ya korani da kuma sanadin musuluntar mutun har goma shabiyar. Kuma da tasirin zugar ƙawa da da kuma ƙarfin ikon uwa. Dan Allah Rashida ki bawa ya Ishaq haƙuri a bisa mugayen furucina garesu". Kai Rashida ta girgiza tare da cewa. "Ya Ishaq ya yafe miki Zaleeha yanzuma tare dashi mukazo, yana side ɗin Ummi ne, yana jiran amininshin ya dawo zasu iso wurinki." Ido ta zubawa Rashida cikin sanyi tace. "Rashida kodai da Malam Ishaq za'ayi bikin ne?". Murmushi Rashida tayi tare da gyaɗa mata kai alamar eh. Wannan abu sosai ya sata jin daɗi, nan sukaci gaba da hira cikin hirar ne ta kalli Zaleeha tare da cewa. "Bilkeesu tazo ko?". Haɗe fuska Zaleeha tayi tare da cewa. "Bana buƙatar zuwanta Rashida nayi dana sanin ƙawancena dan Bilkeesu ba ƙawar arziƙi bace". Sosai Rashida tayi daɗin yadda Zaleeha ta sauya ta kuma gane gskyar waye bilkisu, cikin wasa da dariya tace. "Yau dama lalle nazo inyi miki tunda baki bari an miki lallen aureba yanzu zan miki". Baki ta ɗan taɓe tare da cewa. "Kaiyya barni kawai banda lfy mafa". bata kulataba ta jawo hand bag ɗinta ta ɗebo sajan ta fara kiciniyar kwabashi. A can falon Ummi kuwa sosai take hira da Ishaq yayinda shi kuwa yake ruggume da Adeel, Ameena kuwa tunda suka gaisa suka ɗan taɓa hira ta koma kitchin ita da Raliya. Cikin kula Ishaq yacewa Ummi. "Ummi gobe za'a kawo miki kayan lefen ki ganshi kafin a kaishi". Fuska cike da mamaki tace. "Ishaq har an gama haɗa lefen bani da labari, haka zakayi min?". Murmushi yayi cikin sabonsu yace. "To Ummi ni kaina jiya naga lefen, ni duk a zatona sai next month za'a haɗa lefen, kawai jiya Saifuddeen yaje ya shida Aunty kubra suka sai komai suka kai gida ni sai da Umma ce ta kirani take sanarmin". Sosai Ummi taji daɗin halaccin Ɗan nata, cikin happy tace. "A to yayi kyau Allah ya bar muku zumuncinku yara da jikoki". Amin Amin yace cikin jin daɗi dai-dai lokacin kuma Saifuddeen ya shigo nan sukayi ta hira, sosai Ishaq yaso yayi godiyar amma Ummi ta hanashi. Cikin yadda suka saba mgna yacewa Saifuddeen tarefa suke da Rashida tana side Zaleeha ne, dariya Saifuddeen yayi kana ya gaya Ummi ai da amaryar sukazo tana ɗakin Zaleeha. Ameena da yanzu ta fito tace, "A a ashe da amaryar ake tafe shine ba'a gaya minba inje in ganta". Dariya yayi kana yace. "Uhum kuma yanzuma ta kirani tace in kai mata Adeel love". Cikin sakin fuska tace. "A akai matashi, bari in ƙare aiki zanzo mu gaisa". Kai Saifuddeen ya gyaɗa kana suka fita suka nufi sashin Zaleeha. Koda sukaje, hira suka kama sosai Zaleeha ta saki jiki da Ishaq, cikin kula take ce masa. "Malam Ishaq ina mutanena? Nayi kewarsu, ina son aikina, amman na rasashi". Gyara zama yayi tare da cewa. "Baki rasashiba in mijinki ya yarda, dan har yanzu bawai sun sallameki bane". Murmushin jin daɗi tayi ta ɗan kalli Saifuddeen, tura baki yayi alamun karki wani kalleni". jin sallamar Ameena ne yasa suka juyo gareta, trayn abincin ta ajiye musu tare da kallon Rashida cikin ƴar fara'arta tace. "Amaryarmu barka da zuwa". A kunyace Rashida tace. "Yauwa Ummu Adeel ya Adeel". "Lafiyar shi lau sai rigima". Ƴar dariya tayi tare da cewa. "Zaku bamu shi ai in munyi aur.." Sai kuma tayi shiru, Ishaq ne yayi murmushi tare da cewa. "Bari in karasa miki in munyi aure ko". mayafinya taja ta rufe fuskarta, cikin dariya Ameena tace. "Ga Amminshi in ta yarda dai mun baku". Da sauri Zaleeha tace. "A a kam ban yarda ba sai dai ki haifo wani ki basu wannan kam is my on". Dariya suka ɗanyi kana Ameena ta ce musu. "To ga abinci". Har taje bakin ƙofar fita Zaleeha tace. "Ngd Ummu Adeel". Murmushi Ameena tayi tana mmiki yawan godiyan Zaleeha ta lura ɗabi'artace ko me akayi mata sai tayi godiya, muryar Zaleeha ta kuma ji tana cewa. "Yauwa kuma in kin gama aiki Rashida zatazo tayi miki lalle naga kina son lalle". Cikin jin daɗin dajin ƙaunar Zaleeha tace, "To ba matsala in ta gama tazo ni na gama sai yamma kuma zan shiga kitchin ɗin". To rashida tace. Kana suka ci gaba da lallensu shi kuwa Saifuddeen da Ishaq falonshi suka shiga nan suka ci abinci. Ita kuwa Rashida sosai ta ƙenƙesawa Zaleeha zanen lalle, kana ta miƙe da nufin zataje tayiwa Ameena, cikin kula Zaleeha tace. "Yauwa Rashida dan Allah kiyi mata mai kyau kar nawa yafi kyau sabida kar taji ba daɗi taga ko kin fifitani danni ƙawarkice". Cikin fidda numfashi Rashida tace. "Allah mai iko kai Zaleeha Allah ya bani irin kishinki". Murmushin kawai ta ɗan yi a ranta tace. Kishin da yake sani inji kamar ba nunfashi a jikina, inba dagewa nake ina dannewa ba ai wata ran sai dai su ganni a sume. Koda sukaje a falon Ummi aka zanawa Ameena lallen ganin yamma tayine yasa Zaleeha ta shiga kitchin tana goye da Adeel dan yana son kwaɓa lallan Mamanshi. su kuwa nan suka zana lallensu ita tayi girki da Raliya ma an zana mata a hannu. Sosai Ummi taji son Rashida a ranta dan ta gane ƴar mutuncice. Ishaq kuwa da Saifuddeen tare suka fita Sai da yamman suka dawo, Nan Ishaq ya ɗauki Rashida suka tafi da direbanshi har gida suka maida ita. Suna nan falon Ummi gab da magriba Hayatuddeen da Khamis sukazo nan suka ce ya basu woyoyinsu, Ameenan ya aika ɗakinshi yace taje ta kawo mishi, wayar Khamis, koda taje tayi mmkin canjin gadon data samu, amman sai ta tuna Ummi tace mata, ya bawa Goggo Dada tsohon gadonshi so sai bata kawo komai a rantaba duk da tajin wani sashi na zuciyarta na raɗa mata wani fitinan. Koda taje wayar Khamis ya karɓar miƙa mishi, cikin tsoro Hayatuddeen yace.. "Hamma nawa fa". Fuska a haɗe ya mishi alamun bazai bayarba, ganin haka Khamis yayi sumai-sumai ya tafi shiko autan Ummi ya tura baki kana yana mai jin fargaba dan yasan dole akwai abinda yasa Hammanshi karɓar wayar. Ganin magriba tayine duk suka watse kowa yayi haramar al'wala. Bayan sunci abincin dere sun ɗan taɓa hira kamar yadda suka saba, kowa ya nufi makoncinya, Zaleeha tana zuwa ɗakinta wonka tayi ta ɗan kimtsa kana ta konta bacci. Ameena kuwa sosai ta kimtsa da tayiwa daren yau ɗin shirin tarban mijinta da kyau. Hayatuddeen kuwa har ya konta ya fito ya nufi ɗakin Ummi a bakin ƙofa suka haɗu tana ƙoƙarin fitowa zata rufe ƙofarta. ido ta zuba mishi ganin yadda yaketa zumbura baki cikin haɗe fuska tace. "To uban zumbure-zumbere me hakan?". Kanshi ya ɗan tonƙoshe cikin sanyi yace. "Ba Hamma Saifuddeen bane". A daƙile tace. "To me yayi maka?". Cikin son kuka yace. "Kwace wayata yayi ni Ummi kice masa ya bani wayata". Fuska ta haɗa sosai cikin faɗa da bai taɓa ganin ta mishiba tace. "Bazai bayarba, ya kwace kuma ya kwatu! In kanada ƙarfi ka danneshi ka ƙwata! yanzu kai auta in kana da hankali zakayi fushi da duk hukuncin da Hammanka ya yanke a kanka da wani abu na kane!?, anya kuwa kodai zargina dai-dai ne baka da gsky tsiya kake shukawa a woyar to kaji da kyau nice nace ya ƙwace wayarka ya binciki me kakeyi dan na lura ko ƙura'ani baka yawan dubashi kamar yadda kake duba waya, gaba ɗaya alamomin rashin gsky sun baiyana a kanka, bakasan idona dana Hammanka a kanka yakeba, to wlh a hir! ɗinka!! ko bayan raina!!! Saifuddeen shine madadin uba a gareku musamman kai kaɗai kayi mishi gardama a kan komai, domin yayi maka dukkan abinda uba keyiwa ɗansa, shi ya tare maka maraicinka kai baka san maraiciba duk ƙarfin maraicin a kansa ya sauƙa shine Garkuwa ku ko Rahma da take babba a kanshi yana hukuntata yasata abu kuma dole tai ko bata so bare ku ƙannenshi. wuce ka bani wuri". Sum-sum ya wuce domin ya gano an ramfoshi. Saifuddeen kuwa, wonka yayi ya kimtsa kana ya nufi side ɗin Zaleeha, koda ya shiga batayi bacciba tana riƙe da wayarta, hotonshi kuma take yawan zubawa idanu, Allah ya sani akwai wani abu da yake mata gizo a fuskarshi, da tanada dama da fuskarshi ta zahiri zata zubawa ido ko zata samu ta gano abinda take son tunowa, tana ji kamar ta taɓa ganin makamanciyar fuskarshi. batayi auneba taji yasa hannu ya amshi wayar, tashi zaune tayi ta zuba mishi ido. Shi kuwa hotonshin ya zubawa ido, fuskarshi ya nuna mata da ƴar yatsarshi alamun gani kalleni a zahiri, cikin jun kunya ta kauda kanta, shi kuwa, murmushi yayi dan yana hango wani abu a ƙasan Idanunta hannunta ya kamo yasa mata wayar sannan ya mata saida safe ya juya ya fita. Ƙeyarshi ta zubawa ido har ya ɓacewa ganinta Allah ya sani ƙeyarshi na mata kyau yadda suman wurin ke kwance lib-lib murmushi tayi kana ta kwanta tana tuno yadda sukayi daren jiya lips ɗinshi nada ɗan karen taushi, hakama fatar jikinshi abubuwan da yake mata kuma sunyi tasiri a ranta dan ko yanzu data tuna saida taji duk jikinta ya amshi saƙon. Shi kuwa kai tsaye sashin Ameena ya wuce, yana shiga ya hangota zaune bisa kujerar dressing mirror, a bakin ƙofa ya tsaya tare da buɗe mata hannunshi, ganin haka cikin jin dadi ta taso ta nufeshi, shima danna masarrafin kekansa yayi suka haɗu a tsakiyar ɗakin ruggumeta yayi da kyau tare da fara sunshina wuyanta itama ƙamashin jikinsa take shaƙa, cikin begen juna suka haura kan gado, ido ya jujjuya mata alamun yayi kewarta, lafewa tayi a jikinshi yau babu faɗa bare fushi bare raki, wani irin kula na musamman suka bawa juna, sun raya daren iya son ransu. Saida aka gama kashe arna sakalin Ummi ya lafe lub bisa gado yana maida numfashin gajiya. Washe gari talata Ameena zata koma zuwa aikin dare so ranar ma a gida ta wuni. Sai dai Ranar Saifuddeen bai wuni a gidaba domin ya samu labarin Dalla ta sanadin bibiyar wayarsa to tunda ya dawo ƙasar yana da labarin komai a kanshi to ya tsarawa yaranshi su samo mishi zazzafar budurwar da zai fara gigita gombawa dayi mata fyaɗen. Bayan sallan isha Ameena ke shirin tafiya aikinta, cikin nitsuwa. Yayinda Adeel ke can wurin Zaleehan tana shiryashi dan tafiyan dare dai dole a tafi dashi. A hankali Saifuddeen ya shiga ɗakin Ameena ido ya zuba mata tanata haɗa abincin Adeel a hand bag ɗin ta, Ganin yadda ya zuba mata idone yasa ta ɗan. Kalleshi ganin kamar ransa a ɗan ɓace. gefenshi ta zauna cikin sanyi tace. "Abban Adeel lfy naga kamar ranka a ɓace". Kan shi ya ɗan manna da jikinta rubutu yayi mata a wayarshi, "Bana son wannan aikin daren sam wlh ji nakeyi kamar na hana aikin gaba ɗaya, bana son kina nesa dani". Cikin jin daɗi da tsoron kadafa yace zai hanata aikinta tace. "To Abba Adeel menene a ciki yanzufa bani kaɗai bace ga Aunty Adeel in na tafi ta meye maka gurbina". Hararanta ya ɗanyi tare da rubuta mata. "In saci girkin ki in kaimata ne ko meye kike nufi". Da sauri ta girgiza mishi kai cikin sanyi tace. "Babu batun satan girki Abban Adeel,wlh wlh in dai bana nan na yafe maka duniya da lahira na yarje maka in kaji kana da ɓuƙata kaje gareta harga Allah na yafe". Idan yace baiji daɗin mgnar Ameena ba yayi ƙarya, kuma darajarta ta hauhawa a idanunshi, to amman shi adalci yake son wanzarwa a tsakaninsu shiyasa cikin hikima ya nunamata, yanafa buka tarta yanzu gashi yaga shiri takeyi zata tafi. Murmushi ta ɗanyi tare da cewa. "Kaje wurin Aunty Adeel na yafe". ta zugenshi ya fara kuncewa abin kamar watsa Saifuddeen ya tubure mata dole ya watsa mata shirinta suka shiga wata duniyar. Zaleeha kuwa Sauri-sauri ta gama shirya Adeel saɓashi a kafaɗa tayi tare da cewa. "My papy muje in kaika Mamanka nasan ta gama shiri". Ta ƙarishe mgnar tana barin side ɗinta. A hankali ta shiga falon Ameena bakinta ɗauke da sallama, sallama ta kumayi nanma shiru, karo na uku ta kuma yi sallama tare da shigowa dan a zatonta ko salla Ameena takeyi, tana gab da isa bakin ƙofar bedroom ɗin ta tsaya cik, sabida wani yanayi da take jiyowa a cikin ɗakin. A hankali da ƙarfi suke numfarfarshi, wani irin duhune taga ya rufe mata idanu jiyo sautin muryar Ameena na mgna a hankali. "Wayyyyyyyyyyo Hihhhhhhhhh ha ha ha Wash Abban Adeel na gaji". Cikin azaban sauri Zaleeha da ƙarfinta ta juya har tana cin karo da kujera, da gudu ta ƙarisa fita jin muryar Ameena na cewa. "Waaashhhhhhhhhhhh wayyoooo". side ɗinta ta koma kai tsaye bedroom ɗinta ta nufa, zama tayi a bakin gado ta ruggume Adeel, haka nan taji wani irin abu ya caki zuciyarta take taji numfarfashi na koran juna ji takeyi tamkar ta kurma ihu, sai kuma ta miƙe da sauri ta goyi Adeel a hankali ta fara maimaita. "Innalillahiwainllailaihirajiun, tanayi tana ɗan jin zuciyarta na sanyi". Kafin ta ankara Adeel yayi bacci ita kuma, ƙaho kishin daya tokareta yake neman kasheta ya ɗan saketa. Acan wurin Ameena da Saifuddeen, suna gamawa Ameena taje tayi wonka tana fitowa tace. "Ayyah karɓo min Adeel kafin nan na gama shiryawa, kai ya gyaɗa mata kana ya hau kekenshi ya nufi ɗakin Zaleeha. A bakin gado ya sameta yana shiga kallo ɗaya tayi mishi ta cire ido, shi kuwa a hankali ya mata nuni ta bashi Adeel ba musu ta kunto Adeel tazo ta bashi shi, kana ta matsa gefe. kallonta yayi da mamaki dan yaga kamar ɗan hararanshi tayi, ita kuwa Zaleeha ganin ya tsareta da idone ya sata tura baki tare da cewa. "Jarabebbe kawai ka iya sa mutun cikin fitina ka tafi can kayi ta biyan buƙatar ka". Wani irin masifeffen signal yayi mata, kana ya juya ya fita ranshi fes karon forko ya hango sonshi da kishinsa cikin kwayar idanunta. A ranshi yace. "Bakisan ni jarabebbe bane tukun da sauran ki, karki damu lokacin nan tafe". Yana zuwa Ameena ta amshi ɗanta ta tafi aikinta, shi kuwa ya koma ɗakinshi dan a gajiye yake haka yasa yayi baccinsa. Washe gari da Safe Ameena ta dawo, Ranar kuma Zaleeha ce da Saifuddeen. Tun wayewan garin yake kan system ɗinshi, ba abinda ke ɗagashi kanta sai salla da cin abinci aiki sosai yakeyi. Biyar dai-dai na yamma Bilkeesu ta fito daga cikin gidan Radio vision FM Gombe. A hankali take tafiya Har ta isa bakin titin wani taxi ta hango kusa da ma'aikatar nasu, cikin yauƙi ta ƙaraso kusa dasu tare da cewa, zakuyi cikin garine?". Da sauri Lado yaron Dalla yace. "Eh Hajia shiga muje". Ba tare da tunanin a a meya tsaidasu me sukeyiba a wurinba kawai ta shiga. Su kuwa dama abinda ya kawosu kenan, Domin tun a wurin auren Zaleeha sun gano Bilkeesu ƙawartace sun kuma samu cikekken bayanin ta a wurin Sululu ɗaya daga cikin yaran Dalla wanda ɗan unguwar su Bilkeesu ne, sanin ƙawar Zaleeha ne yasa Dalla yace ita yake son a kawo mishi kafin ya isa ga sauran. Suna gab da isa cikin gari bala ya turawa Dalla saƙon cewa, ga ƙawar Zaleeha mun kamota yanzu gaya mana inda zamu kawo maka ita amman text zakayi mana sabida kar ta gane. Jim kaɗan sai ga saƙon adireshin ya turo inda zasu kai mishi ita a gidanshi dake nan rumbuna, Sai kuma ma yace su watsa mata powder iblis su bugar da ita wanda dama saida powder ne babbar sana'ar Dalla da ita ya samun manyan kuɗaɗen. Sai dai duk saƙon da ake tura mishi Saifuddeen na gani. Su kuwa nan suka hurawa Bilkeesu powder a take tayi lib cikin motar. Ƙarfe biyar da rabi dai-dai na yamma, duk suna falon Ummi, cikin sauri Saifuddeen ya shigo ya sallami Umminshi cewa zai tafi Office DSS. A dawo lfy sukayi mishi kana ya fita ya tafi. Kai tsaye Office ɗin shugaban su ya nufa ya kwashi dukkan hujja daeshaidar daya haɗa a kan Dalla ya basu, kana ya basu adireshin da zasu kai Bilkeesu, Nan take shugabansu ya bada umarnin a kamo Dalla da adireshin inda yake. A take aka haɗa ƴan sanɗan ciki da sojoji suka tafi harda kuma Saifuddeen. Sai dai kafinma su isa Dalla ya samu nasarar yiwa Bilkeesu fyaɗe mai muni sosai ya rarake budurcinta. Suna isa kuma suka kamashi dashi da yaranshi baki ɗaya ga ƙarin shaida da fyaɗen ido da ido ga jakukkunan koken, Anan ne kuma Saifuddeen ya gane dalilin da yasa su Dalla ke bibiyar Zaleeha domin shi dai ya gane Dalla amman shi Dalla bai haneshiba. Take suka damƙa Dalla hannun hukuma, Bilkeesu kuwa akayi asibiti da ita. Koda ya dawo gida da dare sosai jikinsa yake a mace domin ya tausayawa Bilkeesu duk da bai mance rashin mutucintaba. Allah ya kare mishi Zaleeha'nshi kana ga farin cikin nasarar kama babban ɗan kalaren daya buwayi al'ummar gombe da kewaye. Koda aka gama hira kowa yayi shirin baccinsa. Tuni Ameena kuwa ta tafi wurin aikinta. A hankali ya shiga ɗakin Zaleeha konce ya zaune ya sameta bisa gado, cikin nitsuwa ya zauna gefenta, tare da, kamo hannunta, A hankali ya rubuta mata cewa. "Ina ƙawarki Bilkeesu?". Cikin sunkuyar da kai tace. "Nima ban saniba". Jawota jikinshi yayi kana ya rubuta mata. "Tana asibitin su Ameena bata da lfy." Ba tare da damuwa ba tace. "Oh". Ɗan gyara zamanshi yayi bisa tsakiyar gadon kana ya rubuta mata. "Fyade fa akayi mata". cikin tsoro ta zaro ido tare da cewa. "Innalillahi fyaɗe kuwa, Allah sarki Bilkeesu wanne azzalumin ne yayi mata fyaɗe?". Ta ƙarashi mgnar hawaye na zuba Allah ya sani taji tausayin Bilkeesu, shi kuwa rubutu ya mata. "Mutu minki ne ya mafa fyaɗe ya huce a kanta". Cikin tsoro tace. "Mutumi na kuma waye mutu mina, ni kuma a a ni bani da wani mutumin da zai mata fyaɗe". Kanshi ya jinjina dan ya lura tana da rainin wayo tasan abu sai ta nuna bata saniba a ranshi yace dole mana kice ba mutuminki bane tunda ba ke ya tsinkawa jijiyar bayaba nida ya kusan kasheni ai ban manceshi ba, A zahiri kuma haɗe fuska yayi tare da rubuta mata. "Dama ai ke haka kike kin san abu sai ki nuna kamar baki saniba, ai da ke ya kama da kin gane kurenki kinaga ina lallaɓaki in shine babu ruwansa da lallaɓaki yagaki zaiyi". Baki ta tura sabida wlh har ga Allah bata gane manufarsa ba kuma daya kira mata sunan Dalla da zata gane. Shi kuwa Saifuddeen cire jallabiyar cikinshi yayi ya ajiyeshi gefe kana ya kwanta tare dasa hannunshi ya jawota jikinshi, tare da fara tura hannunshi cikin rigarta, jin haka ta mirgina gefenshi, shi kuwa rongofowa ya ɗanyi ya zare mata rigar jikinta ya cillashi gefe rumfa yayi mata da jikinshi tare da manna bakinsu wuri ɗaya, da sauri ta ɗan lumshe idanunta, tanajin yanda tsikar jikinta ke zubawa, wani irin yarr yarr haka takeji ajikinta, gaba ɗaya abun yazo mata abaƙon yanayi. Saifuddeen kuwa wani irin ajiyar zuciya me ƙarfi ya sauƙe, tare da sake matseta ajikinsa, hannunsa ya ɗaura akan waist ɗinta, ahankali yake yawo da harshensa acikin bakinta, wanda hakan yasa lips ɗinsu haɗewa waje ɗaya, ahankali yake yawo da tausassun hannunsa akan waist ɗinta, wanda haɗuwar laushin fatarsu waje ɗaya, ya haifar musu da wani irin yanayi, gaba ɗaya duk wani tunaninta ya tsaya cak, sosai jikinta ke rawa, jin yanda hannunsa ke yawo akan lafaffen cikinta, yasa bugun zuciyarta tsanantawa. Ahankali ya haɗe harshenshi da kuma sweet lips ɗinta yana tsotsa, wani irin kissing yake mata mai ratsa jiki da jijiya, yayinda haɗuwar ƙamshin jikinsu waje ɗaya, ya bada wani irin ƙamshi me daɗi, da sanyaya zuciya, yanayin yanda yakejin taushin lips ɗin ta, shine ke ƙara zautar masa da tunani, wani irin ɗanɗano na musamman yakeji acikin yawunta, sosai wani irin fitinannen feelings ke taso masa, har hijiyoyin jikinsa na miƙewa. Sannu ahankali jikinta ya sake, wani irin yanayi tasamu kanta aciki wanda ta kasa tantance meke damunta, baƙon al'amari ne ke ziyartan sassajan jikinta, wani irin dogon numfashi taja, alokacin da yasanya laɓɓansa yana tsotsan harshenta. Ɗan zare bakinsa daga cikin nata yayi ahankali, ya sauƙe bakinsa akan wuyanta, tare da zura harshensa aƙasan haɓanta, yana lasa, kana yana me goga mata lips ɗinsa akan wuyanta. Wani irin numfashi taja, tare da sake lumshe idanunta dan bai kashe hasken ɗakinba, hannunta tasanya inda ta kama damtsen hannunsa, tare da sakin wani ɓoyayyar ajiyar zuciya da yin ƴar miƙa ta alamun sakar mishi linza minta, yanayin yanda yake yawo da harshensa aƙasan haɓar nata, shiya sanya jikinta ƙara sakewa, wani abu me kama da daɗi takeji, gefe guda kuwa ga idanunta dake lumshewa, tanajin wani abu har cikin ƙwaƙwalwarta. Wani irin numfashi mai kama da ɗan ƙaramin nishi yake fesarwa, ƴar yatsarsa yasanya, adai-dai tsakiyan cikinta, yana jujjuyawa, tare da ƙara tura kansa acikin wuyanta, yana shaƙan daddaɗan ƙamshin jikinta, wanda shi ya ƙara haukata tunaninsa. Atare tsikar jikinsu ke zubawa, cikin wani irin yanayi me wuyar fassaruwa suka samu kansu, yanayin yanda yake ɗan jujjuya kansa, yasa lallausan sajen dake kwance akan fuskarsa ke ɗan gogan jikinta. Mirginowa yayi, inda ya maida ita ƙasansa, ya zamana yayi mata rumfa da jikinsa da kyau, hakanne ya ƙara bawa jikinsu daman haɗewa waje ɗaya. Hannunsa ya sanya inda yaɗan ɗagota, hakanne yasa kyawawan breast ɗinta bayyana, tsumammun idanunsa dake cike da sha'awa ya lumshe, tare da ɗaura kansa akan saman ƙirjinta, ahankali yake tafiya da harshensa atsakankanin breast ɗinta, idanunta ta kuma lumshewa tare da ɗan buɗe bakinta kaɗan, ahankali ta kuma zura hannunta acikin lallausan gashin kansa, wani irin shock takeji ajikinta, abun da yakeyi matan ya zame mata baƙo abu kuka mai wuyar ta ƙishi, sannan ta kasa tantance cewa daɗi, takeji ko kuma daɗin daɗi e ji takeyi kamar ta tayashi ko zataji sauƙin zut-zut ɗin da takeji. Ganin yanda take mimmiƙe jikinta, yasa shi ɗan yin ƙasa da hannunsa, yana shafa kan saman mararta, hakan da yayi mata ne yaso zautar mata da tunani, take taji breast dinta nayi mata wani irin abu me kama da ƙaiƙayi, sake ɗan lusmhe idanunta tayi tare da danne lips ɗinta, gudun kada nishin da take ɓoyewa ya fito. Saifuddeen kuwa laushi da taushin jikinta yasa duk ya zauce, cigaba da shafa jikinta yayi, ahankali yakeyin sama da hannunsa, har ya kawo dai-dai breast ɗinta, sauƙan hannunsa akan breast ɗinta, yayi dai-dai da sakin ƙaƙƙarfan ajiyar zuciya da kuma wani irin nishi me ƙarfi da suka sake atare, hannunta ta cusa acikin gashin kansa, tare da riƙesa ƙam-ƙam, dai-dai-ta fuskarsu yayi, tare da kamo harshenta yana sucking, ahankali kuma yake yawo da hannunsa akan breast ɗinta, inda yasa yatsansa yana juya nipples ɗinta. Tabbas ya kaita wani mataki, wanda bata taɓa samun kanta aciki ba, hakan ne yasa asanyaye ta ɗaura harshenta akan nasa, wanda ke cikin bakinta, kusan atare sukayi sucking lips ɗin juna, wani irin zazzafan hug ya bata, tare da cigaba da murzata, ya riga daya shiga wata duniya ta daban, kaman yanda take ta daban, haka komai nata yake na daban, sosai yake shan sweet lips ɗinta, har wani ɗan taunasu yake, saboda yanda yakejin zaƙinsu abakinsa. Idanunta da ke aɗan lumshe ta buɗe, dai-dai lokacin shima ya ɗago idanunsa, wanda suke cike da mayen sha'awa da kuma zallan soyayyarta, ko adama bata iya jure kallon cikin kyawawan idanunsa, bare ayanzu da suka rikiɗe suka zama sexy eyes masu gusar da tunani. Kanta taɗan kawar tare da matse jikinta, haka takejin mararta wani iri kaman a kumbure, jikinta ne gaba ɗaya yake rawa, har wani ɗan zazzaɓi zazzaɓi takeji saboda wani irin tsoron daya ziyarceta. Ganin haka yasa Saifuddeen ahankali yaɗan migirna gefe yana sakin numfashi, jin yanda manhood ɗinsa ta kumbura ne yasa shi ɗan cije laɓɓansa, saboda amatuƙar buƙace yake da Zaleehan matuƙa, saidai kuma yasan samunta ayanzu abune me matuƙar wahala, ba kuma yaso ya fara abun da yasan bazai....! Kurman baƙi mai hakaline ke ganeshi. Komai yanada sanadi Littafina na kuɗi ne By *GARKUWAR FULANI* [26/09, 3:56 pm] +234 813 251 7737: Na sani kuma naji bazan iya sarrafa ƙuguna da bayana ba, ta yaya zan iya ratsa jikinta har in rabata da budurcinta. ɗan lumshe idanunsa yayi, yana me sakin nannauyan ajiyar zuciya mai cike da ƙuna, nakasarsa bata taɓa zame mishi kasawa a kan komaiba sai a yanzu akan abinda yafiso yafi ƙulafaci da muradi. Zaleeha kuwa sake ƙanƙame jikinta waje ɗaya tayi zuciyarta cike take da fargaba, haɗi da tsananin tsoro, musamman ayanda taji ƙatuwar saif ɗinsa na gogan jikinta, wannan abu shike ƙara hautsuna tunaninta, duk sai taji gaba ɗaya tsoro ya cika mata zuciya, ɗan janye jikinta tayi ta matsa nesa dashi, jikinta duk rawa da karkarwa yake, blanket taja ta rufa ajikinta, tare da sake takurewa waje ɗaya, ƙam ta ƙanƙame jikinta, numfashi kawai take fitarwa ahankali. Shikuwa Saifuddeen asanyaye ya sake matsowa gareta, hannuwansa yasa inda ya rungumota ta baya, ya zamana bayanta na gogan fatar ƙirjinsa, lumshe idanunsa yayi, tare da cusa kansa acikin lallausan gashin kanta, wanda ya watse akan pillown da suke kwance, ajiyar zuciya haɗi da wani irin numfashi yake sauƙewa ajere-ajere, yana me sake shigar da ita cikin jikinsa, dan yanayin ɗumin jikinta yasa shi jin wani sabon shauƙi na fusgarsa, Zaleeha kuwa idanunta taɗan lumshe, bata da ikon zare kanta daga cikin jikinsa, dan itama yanayin nasu na yanzu yayi masifar mata daɗi tana jin wani zazzafan abu a kanshi yana ratsa mata jiki da zuciya ji take kamar ta daure ta cire tsoron ta juyo ta ruggumeshi ta samar musu nitsuwa, a zatonta kamar tausayinta yakeji sabida yawan tsoronta ita kanta tasan Hamma Saif ɗin maƙurane a iya sarrafa mace, kasancewar akwai ɗan zazzaɓi kaɗan ajikinta, hakan yasa haɗuwar fatarta da nashi, ya zame mata kamar garkuwa. Lub tayi ajikinsa tana jin yadda zuciyarshi da Saif ɗinshi ke harbawa kamar zasu faso su fito su shiga cikin jikinta, wani irin sassanyan murmushi ta sauƙe tare da mirginawa ta juyo suna fuskantar juna, ruggumeta yayi da kyau, kiss ya manna mata a tattausan fatan goshinta, shiru yayi jin yadda taketa shiga jikinshi tana mammane mishi da murza sawunta a jikinshi, lokaci ɗaya kuwa wani irin fitinannen bacci ya ɗauketa. Saifuddeen kuwa duk ya kasa rumtsawa, haƙiƙa yana matuƙar buƙatar Zaleeha, yanajin wani irin matsanancin sha'awarta na fusgarsa ako da yaushe, yana tsananin son ya jisa acikin jikinta, saidai kuma zuciyarsa cike take da fargaba, dan baisan ta ina zai fara ba, saboda Zaleeha bakaman Ameena bace, akwai banbanci sosai atsakaninsu, musamman idan akayi duba da cewar, Ameena bazawara ce, saɓanin Zaleeha da take budurwa, hakan yasa yakejin fargaban yanda zai fara fuskantar Zaleeha'n, ta ina kuma ta yaya zai kusanci wannan uwar tsoron da yasan bazata iya kusantanshi da kantaba tunda ita dai ba bazawara bace. Da wannan tunanin ne bacci ya ɗaukesa batare da ya shiryawa hakan ba. Washe gari kuwa tun ƙiran sallan asuban fari ya buɗe idanunsa, ɗan jim yayi tare da zubamawa Zaleeha kyawawan idanunsa, wanda take baccinta cikin nutsuwa da kuma kwanciyar hankali, gaba ɗaya ta wani shigewa jikinsa. Ɗan murmushi yayi tare da lumshe idanunsa, ahankali yaɗan zareta daga jikinsa, yunƙura yayi inda ya tashi zaune, wheelchair ɗinsa ya jawo, saida ya hau sannan yakai hannunsa jikin Zaleehan yaɗan taɓa ta, kasancewar bata da nauyin bacci, hakan yasa asakalce ta ɗan buɗe idanunta, ƙaramin bakinta ta turo gaba, tare da kwaɓe fuska, kansa kawai ya girgiza, cikin body language ɗinsa yace. "Sarkin bacci, wato kinsamu jiki na me daɗi, shine harda wani narkemin da maƙalemi harda minshari kikeyi ko, to sai kitashi kiyi sallah." Ya ƙare yanayin maganar tasa yana me ɗan yi mata hararan wasa, kana ya juya yafice daga cikin ɗakin. Ganin fitansa yasa ta sake shagwaɓe fuska, cikin sakalci tace. "Nima ai dai jikina me daɗi ne ehe, kuma kaima ai kasan hakan, tunda saida ka riƙeni sannan ka iya bacci." Cike da kasala ta sauƙo daga kan gadon, kaitsaye toilet ta wuce, wanka tayi sannan ta ɗauro alwala. Ɓangaren Saifuddeen ma hakance ta kasance, dan yana fita daga ɗakin nata, kaitsaye ɗakinsa ya wuce, wanka yayi sannan yayi alwala, wata brown ɗin jallabiya ya sanya, sannan ya fice zuwa masallaci. Zaleeha kuwa koda ta idar da sallah, karatun Alkur'ani taɗan taɓa kaɗan, sannan ta miƙe, sama sama ta shafa mai ajikinta, sannan tabi ko ina na jikinta da body spray me daɗin ƙamshi, wani lallausan yadi tasanya ajikinta, wanda yaji ɗinkin riga da sket pencil, sosai kayan yayi mata kyau, kana kuma ya fitar da shape ɗin jikinta, kasancewar yadin mai kalan shuɗi da kuma ratsin pink, hakan yasa farar fatarta ya bayyana sosai, simple meckup tayi akan fuskarta, sannan ta kafa ɗaurin ɗan kwali wanda yayi matuƙar zama akanta sosai, wani ɗan siririn vail mai kalan pink ta yafa daga kanta zuwa ƙirjinta, tayi kyau sosai, ita kanta da ta ga kanta acikin madubi saida ta saki murmushi. Wayarta kawai ta ɗauka sannan ta nufi sashin Ummi. Kasancewar ta ɗan makara wajen fitowa yasa ta tarar har Raleeya ta shiga kitchine, tamaci kusan rabin aikin, inda gefe guda kuma Ameena ke taya ta, suna ɗan taɓa hiransu, cikinsu ta shiga tare da kama musu aikin, Ameena ce ta dubeta cikin kulawa tace. "Masha Allah Auntyn Adeel kinga yanda kikayi kyau kuwa." Murmushi tayi wanda har saida dimple ɗinta suka ɗan lotsa, cikin zazzaƙan muryarta tace. "Nagode sosai." Murmushi sukayi dukansu, nan suka ci gaba da aikin, cikin mintuna kaɗan suka kammala break fast ɗin, Zaleeha da Raleeya ne suka jere duka abincin akan dinning area, inda Ameena kuwa ta dawo cikin falon ta zauna nan kusa da Ummi da kuma Ahmad suna hira, Adeel dake hannun Ahmad kuwa sai wasan sa yake. Tsaye take tana ƙara gyara dinning area'n, ƙamshin turarensa da tajine yasata ɗan ɗago kanta, karab kuwa idanunsu suka faɗa cikin na juna, sosai yasha kyau cikin bugaggigar shaddan dake jikinsa, mai kalan shuɗi, wato kalan kayan Zaleeha'n kenan, yayi kyau matuƙa, fuskarsa sai ƙyalli take, kanta taɗan kawar gefe tare da turo bakinta gaba, cikin zuciyarta tace. "Kujisa dai har da wani sa irin kayana, ko wa yace masa yasama oho, thank god ma saida nasa kafun yasa, da sai ace na kwaikwayeshi." Ta ƙare maganar zucin nata tana ɗan jujjuya bakinta. Wani irin murmushi yayi tare daɗan lumshe idanunsa, kana ya buɗesu alokaci guda, yajima yana zargin cewa zuciyoyinsu da jininsu haɗe suke awaje guda, baikuma gaskata hakan ba, sai ayanzu da gaba ɗaya tunani da kuma hankalinsa sun sanar dashi abun da take faɗi acikin zuciyarta. Ƙura mata ido yayi, itakuwa ɗan ɗago kai tayi, ganin cewa har yanzu kallonta yake, yasa afakaice taɗan murguɗa masa baki. Dariya ne yaso kamasa, wanda hakan yasa duk hankalin su Ummi ya dawo kansa, shikuwa yanayin yanda tayi da bakin nata ne yayi matuƙar burgesa, murmushin daya bayyana fararen haƙwaransa yayi, tare da ɗan hararan da taɓe baki sam baisan cewa hankalin su Ummi na kansu ba, su Ummi da Ameena kuwa ganin inda Saifuddeen ɗin ke kallo, yasa suma ɗan juyawa, ganin cewa Zaleeha yake kallo yasa Ameena yin ƙasa da kanta, cikin ranta tasoma ambaton sunan Allah, saboda wani abu da taji acikin ranta, Ummi kuwa girgiza kai kawai tayi tana murmushi. Miƙewa tayi tare da cewa. "To maza kutashi muje muyi break, kunsan yau jumma'a, kana zaune saidai kaga lokaci ya tafi." Babu musu haka dukansu suka ƙarasa kan dinning ɗin, Hayatuddeen sai fama suɗe baki yake. Zaleehan ce tayi seving ɗinsu, sannan itama tayi seving ɗin kanta. Haka sukai break fast ɗin cikin nutsuwa, har suka kammala, Ita da Raleeya ne suka kwashe kayan suka kai kitchine, sannan suka tsabdace dinning area'n, Saifuddeen ne yace Hayatuddeen ya taso yana so ya rakasa wani waje. Hakanan yaji gabansa yaɗan faɗi, amma sai ya dake, miƙewa yayi, ya bi bayan Hamman nasa, wanda tuntuni yayi gaba. Ameena kuwa miƙewa tayi, cikin yanayi naɗan gajiya tace. "Ummi zan shiga naɗan kwanta, wallahi nagaji sosai, ahakan ma waidan guduwa nayi lokacin tashina baiyi ba, dana zauna kam da ni dana dawo sai 8 to 9." Murmushi Ummi tayi tare da cewa. "Ai ma kuna ƙoƙari Ameena, night duty ai akwai wahala, jeki kwanta abunki kawo Adeel ɗin sai ariƙe mikishi, kinsan idan kika tafi dashi ma, hanaki bacci zaiyi wannan yaron naku da rigimarsa." Cikin jin daɗin kulawar Ummin gareta ta miƙowa Ummin Adeel, sannan ta wuce sashinta, dan har wani dishi-dishi take gani a idanunta, saboda rashin samun wadataccen bacci. Su Zaleeha kuwa anan falon Ummin suka zauna, inda ta karɓi Adeel tanayi masa wasa, hira sukayi sosai kafun Ummi ma ta tashi ta wuce ɗaki. Saifuddeen kuwa daga gidan nasu, kaitsaye Habu Hashidu Gombe Hausing Estate suka nufa, inda anan ne gidan su Khamis yake, tunda Hayatuddeen ya gansu cikin unguwan yaji gaba ɗaya tsoro ya kamashi, dan baisan me Hamman nasa ke nufi da zuwa unguwar ba, aƙofar gidan su Khamis sule driver yayi parking motar, idanu Hayatuddeen yaɗan zaro, sakamakon ganinsu aƙofar gidan su Khamis, kallon Hamman nasa yayi, saidai ganin yanda ya haɗe fuska, yasa shi yin gum da bakinsa. Sule ne ya buɗewa Saifuddeen ɗin murfin mota ya fito, bayan ya ware masa kekensa. Ganin haka yasa Hayatuddeen ma jiki asanyaye yafito daga cikin motar. Waya Saifuddeen ɗin yaɗan lallatsa, ko minti biyu ba ayi ba, wani ya fito daga cikin gidan, wanda yake driver'n gidan ne, shi yayi musu iso zuwa cikin gidan, har falon Baban Khamis kuwa suka ƙarasa, inda suka samesa azaune. Cikin kulawa ya tarbesu, bayan ya miƙawa Saifuddeen hannu sunyi musabaha. Dai-dai nan Khamis ya shigo cikin falon, ganin Hamma Saifuddeen da kuma Hayatuddeen yasa yaji jikinsa yayi sanyi, cikin ɗar-ɗar ya ƙaraso ya zauna. Duban Baban Khamis ɗin Saifuddeen yayi, cikin mutuntuwa ya miƙa masa wayarsa, wanda ke ɗauke da rubutun text message, wanda kuma gabatar da kansa ne yayi, duk dama Baban Khamis ɗin yasan da zuwansa, dan ya ɗauki numbernsa acikin awayar Khamis, bayan Baban Khamis ɗin ya karanta saƙon, ɗan murmushi yayi tare da sake bawa Saifuddeen din hannu suka gaisa, cikin kulawa yace. "Masha Allah Malam Saifuddeen ina maraba da zuwanka, sannan bama sai ka wahalar da kanka wajen yin rubutu ba, muyi magana ahaka, dan ina fahimtar body language sosai, dan inada aminina shima bayaji baya mgn." kai Saifuddeen ya jinjina cikin gamsuwa, ɗan gyara zamansa yayi, cikin body language ɗinsa yace. "Kaman yanda na faɗa maka maganace akan yarannan ke tafe dani, bansan tayaya zaka ɗauki maganar ba, kasancewar nasan idan na faɗa zakayi mamakin jinta, saboda abune da ba zamu taɓa zato ba, Hayatuddeen ƙanina ne na jini, kamar yanda na ɗaukesa kuwa haka na ɗauki Khamis, yanda nakejin zan hukunta Hayatuddeen haka ma zan hukunta Khamis, najima inasa musu ido, ina kuma bibiyan lamuransu, ada zarginsu nake, sai-dai tun jiya dana karɓi wayoyinsu na gano cewa suna aikata haƙiƙanin abun danake zarginsu dashi, wato neman mata da kuma kallace kallacen bad vedios waƴanda basu dace ba kwata kwata, bai kuma kyautuwa yara musulmai irinsu masu tasowa suna ganiba, wanda ya zama dole atsaya akansu gudun lalacewar tarbiyarsu da rayuwarsu." Cike da tashin hankalin fahimtar abunda Saifuddeen din ya faɗa yasa. Baban khamis zare hular dake kansa, ya somayi wa fuskarsa fifita, fuskarsa ɗauke da tsananin kaɗuwa da damuwa haɗi da tashin hankali ya dubi Khamis, wanda tuni jikinsa ya fara jiƙewa da gumi, sosai tsoro da rashin gaskiya suka bayyana ƙarara akan fuskarsa, cikin tashin hankali Baban nasa yace. "Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un, ya Allah ka dubemu da idon rahama lallai nasan tabbas kowa da irin jarabawarsa arayuwa, ya Allah kada ka jarabcemu da lalacewar tarbiyar ahlinmu ta hanyar aikata al'fasha ko wanne irine, tunda nake ban taɓa aikata zina ko fasikanci ba, haka ma kuma sam koda ina ƙiruciyata bana kula mata, har izuwa yanzu kuwa na tsare mutumcin kaina, Khamis kai ɗayane ɗana dana haifa aduniya, hakanne yasa na baka kulawa da duk wani gata, saboda rayuwarka tayi kyau ta inƙamta, yanda kowa zai amfana dakai gaba bawai inai maka gata dan lalata rayuwarkaba, ashe abun da kuke aikatawa kenan, ashe neman mata kakeyi Khamis da ƙananun shekarunka, so kake ka tozartani ko, ban taɓa tunanin haka daga gareka ba Khamis, ashe nuna maka gata, zai iya zama silan lalacewar rayuwarka." Hawaye ne suka cika idanun Baban Ƙhamis ɗin, wanda hakan yasa gaba ɗaya jikin Khamis yayi sanyi, take shima hawaye suka cika idanunsa, kansa ya ɗan soma jujjuyawa cikin muryarsa da tayi sanyi yace. "Dan Allah Baba kayi haƙuri, wallahi ni sau ɗaya ne ma na taɓa yin lalata da yarinya ɗayace , kuma ma daganan ban ƙara ba, kuma nan ma yarinyarce take ta bina, bani kuma na nemeta ba, dan Allah Baba kayi haƙuri, Allah bazan sake ba." Hayatuddeen kuwa can gefe ya koma tuni zufa ya keto masa, narai narai yayi da idanunsa, cikin tsoro yace. "Nikam ma wallahi ban taɓa aikata zina ba, na rantse da allah da Manzonsa ko hannun mace wallahi ban taɓa riƙewa ba, Khamis shima shaidane ban taɓa riƙe hannun wata mace ba wallahi." tuni hawaye sun cika idanunsa, wani irin tsoro da fargaba haɗi da matsanancin takaicin kansa da kuma nadama ne ya cika zuciyarsa. Kai Baban Khamis ɗin ya jinjina, cike da alhini da kuma tsoron abun da ɗan nasa ke aikatawa, tabbas yasha mamaki ƙwarai, dan ko kaɗan bai taɓa kawo aransa cewa Khamis ɗin na bin mata ba, kuma wai harma zina ya taɓayi, jiyayi gaba ɗaya jikinsa yayi sanyi, haƙiƙa Saifuddeen ya taimakesa, da bai ɓoye masa abun da yaran ke aikatawa ba, duk da cewa kuwa harda ƙaninsa aciki, yayi mamakin halin ɗan nasa ƙwarai, saidai kuma amma yasan cewa babu irin jarrabawan da Allah baya bawa bawansa, wasu tasu jarrabawan akaran kansu ne, wasu kuwa akan ƴaƴansu aka jarrabesu, kowa dai da irin nasa, tabbas basai ka kasance fasiƙi ko mazinaci Allah zai jarrabi ƴaƴanka ba, ita jarabawa da ƙaddara Allah kan ɗaurawa duk wanda yaso. Hawayen da suka cika idanunsa yaɗan share, cikin sanyi ya dubi Khamis da Hayatuddeen tare dayi musu alaman su ƙaraso gabansa yanason ganinsu, jiki asanyaye kuwa suka rarrafo kusa dashi, Khamis kam dan tsoro haka yakejin kaman ƙirjinsa zai fito waje. Cikin kulawa haɗi da sanyin jiki yace. "Da forko dai Khamis nida kaina zan kaika ayimaka Hukuncin Allah kaida yariyar ayi muku bulalin haddi, kana tayi istibira'i, kuma in aura maka ita in ta kasance mai yin tuba na gskya." Shiru ya ɗanyi ganin yadda Khamis keta gyaɗa mishi kai alamar to ya yarda, jiki a mace yaci gaba da cewa. "Ku yarane wanda asannu watarana zaku zama iyaye, shin alokacin da kuka kai munzalin zama iyaye, idan kuka kama ƴaƴanku suna aikata irin abun da kuke aikatawa ayanzu ya zakuji acikin ranku? shin kuna ma da tunanin cewa ayanzune ya kamata ku inganta rayuwarku? Nasha mamaki ƙwarai Khamis, ace kana matsayin ɗana kake aikata zina, har kana faɗi da bakinka cewa wai sau ɗaya kataɓa yi? kasan girman zina kuwa Khamis? kasan girman laifin zina kuwa? Kasan hukuncin zina kuwa? to wallahi kasani mazinata ko alahira wutarsu daban ne, ko kuma saboda kana ganin kai kaɗaine baka da ƴa baka da ƙanwa, kai kuma Hayatuddeen kana ganin cewa baka da ƙanwa, shiyasa kuke aikata abun da kukeso ko, haƙiƙa idan mu bama ganinku Allah na ganinku, kuma kome kuka aikata na zunubi sai an rubuta muku shi acikin littafinku, sai kuma Allah ya tambayeku akan hakan, kusani jin tsoron Allah shine gaba akan komai, yau idan akace baku da wani ginshiƙi me tsaya muku arayuwa, zakusha wahala, domin wannan halin naku da kuka ɗauko, bazai taɓa bari kucimma nasara arayuwarku ba, musamman ma kai Khamis, wanda wuyanka yayi kauri, har kayi riƙan da zaka iya aikata zina, wallahi wallahi rayuwar mazinaci ko mazinaciya baya al'barka, sannan komai nasu bashi da al'barka, kama daga kan dukiya da duk wani abun da suka mallaka, yanzu Khamis da wani ido kakeso na kalli mahaifiyarka nace mata ɗanta wanda har kusan rasa ranta tayi, wajen ƙoƙarin haihuwarsa mazinaci ne, kanaga akwai wani farinciki ko soyayyarka da zaiyi saura azuciyarta? Sabida gudun lalacewar tarbiyar ka yasa mukaƙi barinka ka tafi karatu ƙasashen turawa, ashe bamu saniba tana ƙasa tana dabo wai sai wanda yaje yayi karatu a ƙasashen woje ke lalacewa ba." Kuka Khamis ya fashe dashi me tsuma zuciya, wanda hakanne yasa Hayatudeen ma fashewa da kuka. Kai Saifuddeen ya girgiza, cikin takaicin rayuwar da ƙannen nasa suka jefa kansu aciki, ƙazamar rayuwa marar ɓullewa. Saida sukayi kuka sosai, kafun Baban Khamis ɗin yayi musu faɗa sosai, tare dayi musu nasiha mai ratsa jiki, wanda yasa atake sukaji duk sun tsani wayoyinsu ma, balle kuma akai ga kallace kallacen batsa da sukeyi. Sosai kuwa Baban Khamis yayiwa Saifuddeen godiya, dan yaji daɗin zuwan Saifuddeen ɗin, saboda yayi imani badon shi ba, da Khamis ɗinsa zai jima yana aikata aikin ashsha, wanda bazai tashi ganewa ba, sai lokaci ya ƙure masa. Haka dai suka ɗan taɓa hira da Baban Khamis ɗin, bayan sun sake yiwa yaran faɗa sosai, Khamis kam yasha kuka, musamman ma da Hamma Saifuddeen ɗin ya ƙara tunatar dashi, girman laifin Zina, da irin hukuncin da za'aiwa wanda ya aikata ta, yayi kuka sosai kuma yayi nadama ƙwarai, gaba ɗaya haka yaji ya tsani abokansa wanda su suka fara ɗorasa ahanyar, har shime yake ƙoƙarin ɗora Hayatuddeen, duk dama shi shaida ne kan cewa Hayatuddeen bai taɓayin zina ba, hasalima baya taɓa shiga sabgan ƴan mata, baya kula wata mace ko ɗaya. Haka dai sai kusan sallan jumma'a, kafun su Hamma sukayi yunƙurin barin gidan. Nan Baban Khamis ke ƙara yiwa Saifuddeen ɗin godiya, tare da cewa. "Ya bashi amanan Khamis ya kula masa dashi." kasancewar Khamis ɗin bashi da ɗan uwa ko ƴar uwa, shi kaɗai ne awajen su, saboda haka bayansu babu wani mesanya idan akanshi, wanda babansa kuma ɗan kasuwa ne, da kuma siyasa, hakan yasa baya yawan zama agida, mamansa kuwa babbar ma'aikaciyar banki ne, itama bawai ta cika zama agida bane. Saifuddeen yaji daɗin hakan kuma ya amshi, amanar da Baban Khamis ɗin ya basa, hakanne ma yasa koda suka tashi tafiya. Khamis ɗin yace zai bisu, suje masallaci, dan dama daga nan gidan su Khamis ɗin masallacin jumma'a zasu wuce. Direct kuwa daga gidan su Khamis ɗin, Buba Yero Central Mosque suka nufa, wato masallacin sarki kenan. Koda aka idar da sallan jumma'an, ba gida suka nufa ba, can ƙungiyar su Saifuddeen na Jonapwd suka nufa, anan cikin mota Saifuddeen ya barsu, shikuwa ya shige wajen amininsa Ishaq, sosai suka sha hira, anan ma sukayi sallan La'asar, daga nan ne suka biya suka sauƙe Khamis agida, su kuma suka wuce gidan Adda Rahma hira sosai sukayi ta ƴan uwan juna, Dr Adnan da Saifuddeen suna falo sunata hira, nan Ya Adnan yake tuntuɓarsa batun komawarsa India, dariya ya ɗanyi tare da mishi alamun, shifa ya worke. Adda Rahma kuwa da Hayatuddeen kitchin suke, gaba ɗaya gidan ya cika da ƙamshin zazzafan gashin kaji da Adda Rahma keyiwa Umminta duk bayan wani lokaci. Koda ta gama a kula ta juyesu da zafinsu sunata turiri, kana ta sawa auta kura a filet, ya fita falo yanaci yana sjishita. Ita kuwa Adda Rahma sanin Saifuddeen baya cin kazane, yasa ta zaro dangwaleliyar zabuwa a firijin, wonke zabuwar tayi a gudarta ba tare da ta yayyanka kataba ta sata cikin tukunya, wadataccen al'basa ta yanka ta zuba a kai kana ta watsa tafarnuwa akai, maggi da time da corry ta yaryaɗa, kana ta ɗebi dakekken citta da kanamfari ta yayyarfa dai-dai misali, sannan ta rufe ta ɗaura a huta, attaruhu da al'basa da tafarnuwa ta jajjaga mai rai da lafiya, wani irin fitinenne ƙamshi ya cika side ɗin nata gaba ɗaya, har zata ɗaura wata tukunyar jin kiran da Ya Adnan ɗinta ke mata yasa ta fito da sauri, Ganin Hayatuddeen a tsayene yasata cewa. "Ina zuwa?". Saifuddeen ne ya mata alamar. "Zamu tafi gida lokacin salla ya ƙara to". Kai ta juya tare da nunawa Hayatuddeen kujera kana tace. "Koma ka zauna bari in gasa mishi zabuwa nasan baya cin kaza". Zama yayi tare da cewa. "To amman dai hardani a zabuwar ma ko?". Ya Adnan ne yayi dariya tare da cewa. "Kai Auta wai kai baka gajiya da namane". Da sauri ya gyaɗa kansa alamar eh, Saifuddeen kuwa, hannun Adda Rahma ya kama tare da mata alamun ta bari karta damu ta sani shi ba wani damuwa da nama yakeba". Kai ta juya tare da cewa. "Bana son gardama Saifuddeen ku jira yanzu zan gama". Baya iya mata musu shiyasa yace to. Cikin awa ɗaya da ƴan mintuna tayiwa zabuwar nan wani irin fitinenne gashin tukunya mai ɗan karen daɗi da azabar ƙamshi, a wata kekyawar kula ta saka mishi ita da zafinta sai tururi takeyi, ta fitowa ta miƙawa Hayatuddeen tace. "Gashi wannan kuna komawa ka kai mishi ɗakinshi, ga madarar shanun shima ka kai mishi, bance da kaiba a zubuwar da madarar uban ciye-ciye". Tura baki yayi tare da cewa. "To ni dai gsky ki bani mgnar rabona in ba haka sai nasha nashin." Dr Adnan ne yayi dariya kana yace. "Ɗauko mishi gora ɗaya". Jin haka yasa ta ɗauko mishi ai da murnarshi ya amsa ya fita kana suka bishi a baya suna dariyar sangarcin autan Ummi saida Saifuddeen ya shiga gidan Baba Bello ya gaidashi kafin suka shiga mota suka wuce gida. Acan gida kuwa, gaba ɗayansu zaune suke afalon Ummi, Zaleeha wanda gama girkinsu yasa taje tayi wanka, wani sabuwar shiga ta sanja, inda tasha kyau cikin wata tighty gown sky blue me kyau, sosai tayi, kyau yayinda ta tubke gashinta ta bar jelanshi sake , hakan yasa ta zama kamar wata ba india. Zaune take agefen Raleeya yayinda taɗan jingina kanta da kafaɗan Raleeyan daketa kitse mata jelan gashin yana kuma koncewa sabida santsinshi kuma ba iya kitson tayiba, sai kuma Adeel dake gefenta yana ta wasan sa, shigowarsu cikin falonne yasa taɗan yunƙura tare da matse jikinta waje ɗaya, kasancewar babu mayafi akusa da ita, sam kuma batayi tunanin dawowarsa yanzu ba. Ƙarasowa cikin falon yayi, Ameena dake zaune ne ta sakar masa murmushi, shima murmushin yayi mata tare da lumshe mata ido, cikin nutsuwa ta miƙe ta ƙarasa gaban fridge inda ta ɗauko masa lemo maisanyi, karɓa yayi yaɗan sha, sannan ya juya ya ya karɓi kulan zabuwarshi da madararshi dake hannun Hayatuddeen kana ya juya ya koma part ɗinsa, dan yanaso yaɗan watsa ruwa. Raleeya kuwa kitchine ta shiga, inda ta haɗo musu fruit salad wanda ta cika madara acikinsa, Kaɗan Ameena tasha dan ita haka take kayan fruits basu wani dame ta ba kayan zaƙima duka bai dameta ba. Zaleeha kam dama abincinta ne, saboda haka sosai tasha, ɗago idanu tayi ta kalli Hayatuddeen wanda gaba ɗaya yazama wani silently dashi, da duk kan alama akwai abun dake damunshi, hakanan taji duk ba daɗi, saboda tasa aranta damuwar Hayatuddeen damuwarta ne, tashi tayi daga zaunen da take, tare da ƙarasawa kan kujeran da yake zaune, zama tayi gefenshi, cikin kulawa tace. "Sweet bro me yake damunka? ko baka da lafiga ne autanmu?." Ɗan ɗagowa yayi ya kalleta, asanyaye ya jingina kansa da da jikin kujera. Yana jin yadda ƙirjinsa ke bugawa, wani irin tsoro yakeji, yasan idan Hamma ya faɗawa Ummi halin da yake ciki, zatayi fushi dashi sosai, shi kuma tsoron hakan yakeji, gashi kuma yaga Hamman nasa ma, bawai ya sake dashi bane, ganin yanda ya marairaice fuska yasa Zaleehan ɗan gyara zama ta fuskanceshi da kyau, ahankali ta miƙa masa cup ɗin fruit salad din dake hannunta, babu musu kuwa ya amsa ya sha, cokali huɗu kawai, ta ɗan hararesa tare da cewa. "To ya isheka haka malam, dan naga alaman idan na biyeka zaka shanyemin." Dariya sukayi gaba ɗayansu, miƙewa tayi, tare da ɗaukan Adeel, ɗayan hannunta kuwa bowl ɗin fruit salad ɗinta ne, wanda bata gama shanyewa ba, zata je ta sanya acikin fridge. Kaitsaye part ɗinta ta nufa, nan cikin firdge ta sanya bowl ɗin fruit ɗin, sannan ta ajiye Adeel akan gado, jin anata ƙiraye ƙirayen sallan magriba ne, yasa taje ta ɗauro al'wala, koda ta fito daga toilet ɗin sallaya ta shumfuɗa tare da tada sallah. Tana idarwa kuwa taji anayi mata knocking ƙofa, tana buɗewa kuwa ta ga Ameena ce tsaye cikin shirinta na zuwa wajen aiki. Ɗan faɗaɗa murmushin kan fuskarta tayi tare da cewa. "Ummu Adeel har kin shirya." Murmushi itama Ameenan tayi tare da cewa. "Eh wallahi, kinsan idan na tsaya saina makara, ni kuma banason makara wallahi sam, ina Adeel ɗin yake sarkin son jiki, yazo na goyashi". Murmushi Zaleeha tayi, tare da komawa cikin ɗakin ta ɗauko Adeel ɗin, miƙawa Ameenan shi tayi, tare da cewa "Gashinan ai sai wasan sa yake tayi abinsa." Karɓansa Ameenan tayi tare da goyasa, sai wutsil-wutsil yake wai shi adole wajen Amminsa zai zauna, har bakin ƙofa Zaleehan ta rako Ameena, tare dayi mata adawo lafiya, da "Ameen." ta amsa, sannan ta juya ta koma ciki. Zama tayi akan sallayan tana ɗan addu'o'i, tana nan azaune kuwa har aka ƙira sallan isha. Tana idar da sallan kuwa ta wuce sashin Ummi, nan kan dining ta taradda Saifuddeen, da kuma Hayatuddeen ɗin azaune, sai kuma Ahmad, shigowarta yayi dai-dai da fitowar Ummi daga ɗaki, ƙarasowa tayi cikin girmamawa tayiwa Ummin "Barka da dare." fuska asake Ummi ta amsa mata, sannan suka zauna akan dinning table ɗin. Raleeya ne tayi seving ɗinsu, nan suka fara cin abincin cikin nutsuwa. Bata wani ci abincin mai yawa ba, dan ta ƙosa da irin kallon da Saifuddeen ɗin keyi mata, gaba ɗaya jinta take wani iri, kuma dama bawai yunwa takeji ba, dan tasha fruit salad, kuma shi kaɗai ma ya ƙosar da ita, miƙewa tsaye tayi tana goge bakinta, dubanta Ummi tayi tare da cewa. "Zaleeha ya kika tashi, badai kin ƙoshi ba." Kanta ta jinjina tare da cewa. "Eh Ummi naƙoshi sosai, kinsan ɗazu munsha fruit salad, kuma ma inaso ne naɗanyi aiki a system ɗina." Kai Ummi ta jinjina cike da gamsuwa tace. "To masha Allah, ayi aiki lafiya, Allah ya tashemu lafiya." da "Ameen" ta amsa, , cikin kulawa tace. "My Autan Ummi good night da safe zamuyi magana kaji." Kansa ya jinjina mata yana murmushi, duban Raleeya da Ahmad tayi, tare dayi musu saida safe, fuska asake duka suka amsa mata, sannan ta fice daga cikin falon, kaitsaye ɗakinta ta wuce. Su kuwa cikin nutsuwa suka kammala cin abincinsu, Hayatuddeen ne ya soma ƙoƙarin tashi tsaye, hannunsa Ummi ta kamo tare da zaunar dashi, ɗago idanunsa da sukayi rau-rau dasu yayi ya kalli Ummi'n, wanda tun ɗazu kunyan kallonta yake, idanu Ummi ta zuba masa, tare da ɗan watsa masa harara, cikin bayyanar masa da ɓacin ranta dan shi baida nitsuwar Saifuddeen shiyasa bata mishi irin Hukuncin da takewa Saifuddeen wanda shi da idoma yakan ɗimauce in tana hukuntashi da kallon tuhuma, to shi autanta yafi gane zahirin zance yafi gane yaren faɗa, cikin haɗe fuska tace. "Koma ka zauna, Hayatuddeen, wato abun da kake aikatawa kenan ko?, kai atunaninka cewa idanunmu ba akan ka su ba ne, hmmm najima ina zarginka da aikata rashin gaskiya da kuma abun da bai dace ba Hayatuddeen, musamman ma ga yanda bakaso ko wayarka aɗauka, wato shine wannan rayuwar daka zaɓawa kanka Hayatuddeen kana ganin me kyauce? ko irin tarbiyan dana baka kenan?." Hawayene suka cika idanunsa, sosai jikinsa yayi sanyi, ahankali yaɗan shiga girgiza mata kai alaman "A'a." cikin muryan kuka yace. "Dan Allah kiyi haƙuri Ummi, wallahi bazan sake ba, kuma hakan ba halina bane, bansan me ya ruɗeni ba Ummi, bansan meyasa nake aikata haka ba, bayan kuma nasan da cewa babu kyau, nasan nabiyewa sharrin zuciya da kuma na aboki, amma bazan ƙara ba, wallahi dama Khamis ne ya koya min, kuma nayi miki rantsuwa Ummi, Wallahi ko hannun mace ban taɓa riƙewa ba, tsoro nakeji Ummi, idan keda Hamma kukayi fushi dani, wallahi rayuwata watsewa zatayi, bazan iya jure fushinku ba Ummi, dan Allah kuyi haƙuri." Fashewa yayi da wani irin kuka, mai ɗauke da zallan nadama haɗi da danasani. Kai kawai Ummi ta girgiza cikin sanyi tace. "Bansan yaushe kazama haka ba Hayatuddeen, a iya sanina dakai babu ruwanka da duk irin waƴannan abubuwan na banza, saboda ban koyar daku hakan ba, nasan giyar samartaka ne ke ɗibanka daga kai har Khamis ɗin, kunajin cewa kuma kun tasa, kun fara zama samari, shiyasa kuke ƙoƙarin gurɓata rayuwarku amaimakon gyarata, bahaka na tarbiyantar dakai ba, wannan ɗabi'ar kuma ba irin ta cikin gidan nan bane, na lura kuma barinka da waya da mukayi ne, duk ya jawo hakan insha Allah kuma, daga yau kadaina riƙe babbar waya har abadan kenan, domin da mummunar rawa gwamma ƙin tashi." kuka ya sake fashewa dashi, har acikin ransa yayi danasani da kuma nadama. Ganin yanda yake kuka sosai ne, yasa Ummi kwantar da murya, cikin nutsuwa ta shigayi masa nasiha mai ratsa jiki, tana gamawa kuwa Ahmad da Saifuddeen harma da Raleeya suka ɗaura nasu, sosai jikinsa yayi, sanyi haka ya dinga sakin sheshsheƙan kuka, tare dayi musu rantsuwa kan cewar bazai sake ba. Nan dai sukayi masa faɗa sosai. Ummi ne ta fara tashi ta wuce ɗakinta, saboda akwai abun da zatayi aciki, Saifuddeen ne nabiyun tashi, saida safe yayiwa su Ahmad sannan ya fice daga cikin falon. Hayatuddeen kuwa cikin falon ya koma, ya zauna tare da kunna tv, tashar MBC Action ya kamo, inda ya samu suna haska film ɗin MULAN, sanin cewa yaga tallen film ɗin a net, ya sashi maida hankalinsa ga tv'n yana kallo duk hankalinshi na kan tv. Ganin haka ne yasa Ahmad sanya hannu ya jawo Raleeya jikinsa, ɗan shagwaɓe masa tayi, akasalance tace. "Nifa Allah ko Habibi jikina ciwo yake." Murmushi yayi, tare da sanya hannu ya shafi kyakkyawar fuskarta, harshensa yasanya inda yaɗan lashi lips ɗinta, cikin mayen sonta yace. "Muje maza namiki maganin gajiya my kyakkyawar matata." Yana gama faɗan haka, ya ɗagata sama, ƙoƙarin zillewa take amma yaƙi bata daman hakan, haka suka haura sama, yana ɗauke da ita kaman ƴar ƙaramar baby. Hayatuddeen kuwa baisan ma me sukeyi ba, dan gaba ɗaya hankalinsa naga tv. Acan part ɗin Zaleeha kuwa fitowarta daga wanka kenan, towel ta sanya inda taɗan goge ruwan dake jikinta, wani fitinannen body lotion mai ƙamshin gaske ta shafa ajikinta, tare da bin kowani lungu da saƙo na jikinta da daddaɗan turare. Wata irin fitinanniyar sleep gown ta sanya ajikinta, wanda gaba ɗayanta net ne, sannan an ƙawata gabanta da wasu igiyoyi, sosai rigar tayi mata kyau, yayinda kuma ta bayyana komai na jikinta, gaba ɗaya shape ɗin jikinta a bayyane yake, kasancewar rigar nada breast cup hakan yasa, bata sa brezia ba, wanda hakan yasa shatin pink nipples ɗinta suka bayyana acikin rigar. Wani perfumed ta fesa lungu da saƙo na jikinta tare da yin parking dogon gashinta, atsakiyan kanta. Tayi kyau sosai, A hankali ts hayewa saman gado, tare da jawo laptop ɗinta, wayarta ta shiga ɗan duddubawa, tunowa cewar ta manta shi a falon Ummi yasa taɗan dafe goshinta tare da cewa. "Mitsee wlh na gaji". tsai kuma ta tashi tare da zaro wani ƙaton hijab daga cikin drawer'nta, sanya hijab ɗin tayi, tare da zura wani bedroom slipper aƙafanta, har zata fita kuma sai idanunta suka sauƙa akan sweet ɗin da ta ciro acikin firij wanda har sun zama dutsen ƙanƙara, guda uku ta ɗauka sweet ɗin masu ƙamshin strowberry, ɗaya ta ɓarewa ta jefa a bakinta, kana ta riƙe biyu a hannunta tanajin sanyi su na ratsata, niyarta inma ta shanye ɗayan kafin ta dawo ga biyu a hannu, handle din ƙofar ta murɗa sannan ta fice daga cikin ɗakin, kaitsaye sashin Ummi ta nufa. Da sallama abakinta ta shiga falon, Hayatuddeen dake zaune ne ya amsa mata, ƙarasowa cikin falon tayi, tare da dubansa cikin kulawa tace. "Auta har yanzu bakayi bacci ba." Kansa ya jinjina mata, tare da cewa. "Wani latest film nake kallo Adda Zaleeha, yayi kyau sosai." Murmushi tayi, tare da ƙarasawa kan kujeran da ta zauna ɗazu, tana ɗage pillown dake jikin kujeran kuwa, taga wayarta, ɗaukan wayar tayi, dai-dai lokacin Ummi ta fito daga cikin ɗaki. Ganin Zaleeha yasa tace. "Ikon Allah Zaleeha dama baki shiga bane." Ɗan murmushi tayi tare da cewa. "A'a Ummi na shiga, harma na kwantama saina tuna nabar wayata shine na dawo na ɗauka." Kai Ummi ta jinjina tare da cewa. "Ai kuwa naji daɗin dawowanki, dama yanzu Hamman ku ya turo min text wai Hayatuddeen ya kai masa coffee, tunda gaki ai shikenan, shiga kitchine ki haɗa masa saiki kai masa ko." Kanta taɗan sunkuyar cikin yanayi na ɗan jin kunya tace. "To Ummi." kitchine ta wuce, inda Ummi kuma ta zauna anan falon. haɗaɗɗen coffee ta haɗa masa, wanda lokaci ɗaya ya cika falon da ƙamshi, fitowa tayi daga kitchine ɗin, hannunta ɗauke da ɗan tray wanda samansa ke ɗauke da ɗan ƙaramin flask da kuma cup, saida safe tayiwa su Ummin, sannan ta fice daga cikin ɗakin. Koda ta doshi sashin nasa, hakanan taji ƙirjinta na bugawa, wani irin fargaba ta samu kanta aciki, ɗan dakewa tayi tare da murɗa handle ɗin kofar falon nasa ta shiga. Komai dake cikin falon nead, babu abun dake tashi sai ƙamshi, da kuma wani irin fitinannen sanyin ac mai ratsa sassan jiki da zuciya, ɗan Adam lumshe idanunta tayi, ahankali take ƙarewa falon nasa kallo, komai na cikinsa me kyau da burgewa ne, musamman royal chairs din da suka matuƙar burgeta, ɗan waige-waige ta somayi, ganin baya cikin falon yasa taɗan turo ƙaramin bakinta gaba, ashagwaɓe tace. "To kuma ina yake?." ƙoƙarin aje tray ɗin dake hannunta tayi, wani tunani dayazo ranta ne, yasa ta juya tare da nufar ƙofar bedroom ɗinsa, sanin cewar idan ta ajiye masa coffee ɗin afalo, balallaine ya gani ba, maybe kuma yasake ƙiran Ummi yace akawo masa coffee, bata so kuma Ummi tayi zaton bata kai mishiba ne. ahankali ta murɗa handle ɗin ƙofar ta shiga, bakinta ɗauke da sallama, daddaɗan ƙamshin airfreshener ne ya daki hancinta da wani shegen sanyin ac daya ninka na falo, cikin ranta tace. "Na shiga uku wannan sanyin baya damunshi ne, haba shiyasa ko matarsa mutun ya shiga sai kaji sanyi har cikin ƴaƴan hanjinka, Allah sarki Sule shi kam har ya saba, da makaken gadonsa ta fara arba, ɗan zaro idanunta waje tayi, abayyane tace. "Wow, wannan wani irin gado ne?". Tsayawa tayi tana me ƙarewa ɗakin nasa kallo, cikin ranta tace. "Chab aljannar duniya kenan mutun komanshi kamar na ɗawisu". ɗan takowa tayi a hankali ta ƙaraso jikin gadon nasa, ahankali tasanya hannu taɗan shafa saman gadon, wanda design ɗinsa yayi matuƙar kyau. Sam ta shagala cewar coffee ta kawo masa, hasali ma kuma rashin ganinsa aɗakin baida meta ba sai dai tanajin sanyi sweet ɗinta dake cikin tafin hannunta. Ahankali ya buɗe ƙofar toilet ɗin yafito, sanye yake da white bathrobe, yayinda gaba ɗaya jikinsa ke ɗauke da danshin ruwa, da dukkan alama wanka yayi, ɗan tsayawa yayi, yana kallon ta fuskarsa cike da mamakin ganinta acikin ɗakinsa a ransa yace. "Uhum yarinya kin kawo kanki". Ita kuwa Zaleeha jin kaman motsin mutum abayanta, yasa tayi saurin juyowa, idanunsu ne suka sarƙe acikin na juna, da sauri taɗan ja da baya, tare da turo bakinta gaba, idanunsa ya ƙura mata, tare dayi mata alama kan in boddy language cewa. "Wayace kishigo min ɗakinna?." sake turo baki gaba tayi, ashagwaɓe tace. "To ni ba Ummi bace, tace na kawo maka coffee." tsumammun idanunsa yaɗan lumshe, tare da sakin wani irin killer smile, ahankali yaɗan soma turo kekensa zuwa gareta, ganin haka yasa da sauri ta ajiye tray ɗin, tare da juyawa ta nufi hanyar barin ɗaƙin, cikin azama ya rigata ƙarasawa bakin ƙofar ɗakin ganin guduwa takeda niyar yi, hannu ta ɗaura akan handle din ƙofar, dai-dai lokacin shikuwa ya sanya hannunsa ya kare ƙofar, ta yanda bazata iya buɗewa ba. Idanu taɗan zaro waje cikin mamaki tace. "To miye haka, nidai ka matsamin nafita, ai dama coffee akace na kawo maka, to kuma baga can coffee ɗin na ajiye maka ba." tafaɗi maganar tana kakkarya ƴan yatsun hannunta tare da sunkuyar da kanta. Rikitattun idanunsa ya watsa mata, wanda har saida taji, tsikar jikinta sun mimmiƙe. Ɗan rolling idanunsa yayi, tare dayi mata alaman cewa. "Ai tunda kika shigo ba zaki fita ba." Idanunta ta zaro, tare da ɗan murguɗa masa ƙaramin bakinta, asakalce tace. "Dan Allah nidai kabarni na fita kaji." ɗan karyar da wuyansa yayi, tare da girgiza mata kai, alaman yaƙi ɗin. Hannunsa yasa inda ya murzawa ƙofar key, tare da zare key ɗin yasa a aljihunsa, ganin haka yasa ta kwaɓe fuska, take idanunta sukayi rau-rau dasu. Ɗan janye jikinsa baya yayi, tare da ƙarasawa gaban dressing mirror ɗinsa, cikin nutsuwa ya ɗauko body lotion ɗinsa yana shafawa. Idanu ta zuba masa, sai faman tattaune lips dinta take, zuciyarta kuwa duka yake da ƙarfi, ganin cewa yama manta da ita, hidimansa kawai yakeyi, yasa ta ƙaraso har gabansa, ahankali ta shiga ɗan bubbuga ƙafanta, asakalce tace. "Dan Allah ni dai kabuɗemin ƙofa na fita, bacci nakeji." Ɗago idanunsa yayi ya kalleta, tare dayi mata nuni da gadonsa alaman ga gado nan ta kwanta. Fari tayi da idanunta, tare da cewa. "Nidai bazan kwanta akan wannan gadon ba, ai nima ina da nawa, nidai ka buɗemin naje na kwanta a ɗakina." Murmushin gefen baki yayi, tare da mata alamar. "Ai ni ba'a shiga ɗakina, a fita ba'a kwanaba, haka kuma ɗakina yanada dokoki". Cikin sanyin murya tace. "Ni dai ɗakina zan koma in kwana". A ranshi yace. "Eye yanzu dai kin yarda nan gidanki ne wato harda wani a ɗakinki zaki kwana, to saura in tabbatar miki ni mijinki ne kuma nan ɗakin mijinkine. Ba tare daya kulataba, ya ƙarasa gaban drawer ɗinsa, wani 3quater mai taushi ya ciro, ganin yana shirin zare bathrobe ɗin jikinsa agabanta ne, yasa tayi saurin kawar da kanta gefe tare da rumtse idanunta. Shikuwa babu wani ɗar ya cire bathrobe ɗin, tare da zura tattausan wondon ɗin ajikinsa. Body spray ɗinsa ya fesa, sannan ya ƙara gudun AC'n ɗakin, Wayarshi dake kan mirror ya ɗauka, juyowa yayi ya kalleta, da sauri ta janye idonta dan ganin yadda ya haɗe mata fuska, rubutu yayi a wayarshi kana ya miƙa mata, ba musu ta karɓa ta fara karanta abinda ya rubuta mata. "Ki shiga bathroom kije kiyi al'wala kizo, dan ni ba'a kwana ɗakina saida al'wala". Miƙa mishi wayar tayi cikin sanyi tace. "Inada al'wala, sweet kawai nasha". alama ya mata taje ta kurkure bakinta to. tura baki tayi da niyar zatayi mgna sai kuma tayi shiru ganin ya ɗaga mata hannun kana ya mata nuni da hanyar bathroom ɗin nashi. Sumai-sumai ta wuce jiki a mace, koda ta shiga tsayuwa tayi tana kallon tsari da zubin bayan gidan nashi, cikin sanyi tace. "Son kai komai nashi yafi namu kyau". Ta ƙarishe mgnar tare da kurkure bakinta kana ta juya ta fito. Ido ta ɗan zuba mishi ganinshi sanye da wani farin jallabiya kana yana bisa sallaya ga kuma wani sallayan a gefenshi, kai ta jujjuya ganin yana nuna mata kan sallayan, cikin mmki tace. "Ai ni nayi sallan isha'a na tun ɗazu kuma nayi shafa'i da wittirinama". Fuska ya tsuke babu alamar wasa ya miƙa mata wayarshi daya rubuta mata. "Na sani ai, ko ce miki akayi ni ɗin banyi sallan isha'a ɗin bane? Kizo Nafila zamuyi, in roƙa miki Allah ya shiryeki ya rabaki da guje-guje nan da kokenki na tsoro dan karki sake guduwa da kuka". Wani irin bugawa taji ƙirjinta yayi dan ta fara tsinkewa da manufarsa, cikin sanyi da ɗan tsoro tace. "Ɗan guntun rigar bacci a jikina fa". Kai ya gyaɗa mata tare da mata alamun ai hijabin jikinta ƙatone mai kauri kuma gashi har ƙasa". Babu damar wani musu dole ta matso gefenshi a hankali ta ajiye sweet ɗinta gefen kulan dake kan bedside sannan ta dai-dai-ta tsayuwar ta kan sallayar, shi ya limanceta sukayi nafila raka'a biyu. Koda suka idar juyowa yayi ya fuskanceta hannunshi ya ɗaura bisa kanta ya kama goshinta cikin ransa yayi addu'o'in kana, ya saketa, haka nan taji jikinta yana rawa kar-kar, shiyasa tana jin ya saketa ta yunƙura zata miƙe, da sauri ya kamo hannunta ya maida ita ta zauna gab dashi, cikin yin rau-rau da ido tace. "bacci nakeji". Bai kulata ba, sai hannunshi yasa ya sauƙo da wannan kular, da Adda Rahma ta sa mishi gasasshiyar zabuwar nan, ya ajiye kulan a gabanta, sannan ya buɗe ɗan madaidaicin firijin dake gefenshi, goran madarar nan ya fitar ya ajiye gabanta, Zuwa yanzu lamarinshi ya fara sata shakku, wani irin ƙamshine taji ya ziyarci ƙofofin hancinta sanda ya buɗe kular, a fakaice ta kalli dangwaleliyar zabuwar da tasha gashin tukunya mai ɗan karen kyan gani da daɗin ɗanɗano, to Zaleeha dai dama uwar kwalamace, bata san cewa kazar ci inciki bane, kazar bashi kanaci kaima ɗin za'a tsotseka, tura mata kular yayi gabanta tare da mata alaman taci. Kai ta ɗan jujjuya duk da yawunta da taji ya tsinke, cikin rauni tace. "Na ƙoshi". Kici-kici yayi da fuska cikin bada umarni ya mata alamu. "Maza taci, shi ba'a kwana ɗakinshi da yunwa". Sosai yayi mata kwarjini, kana ta kuma tuno al'khairin da taiwa Baba Malam na cewa zatabi umarninsh,a hankali tasa hannu ta ɗan yagi kaɗan daga jikin ƙunɗun zabuwar dai-dai irin farin tsokar nan tibis taji tsokar sai nason mai da takeyi, ido ya zuba mata ganin bata kai hannunta bakinta ba, hannunshin yasa ya kamo natan ya ɗagashi ya kai matashi kan bakinta, kana ya mata alamu da idonshi cewa ta buɗe bakinta, Rau-rau tayi da idonta kana a hankali ta buɗe bakinta tasa tsokar namar, wani irin tsinkewa yawunta yayi sabida yadda ɗanɗanon naman zabuwar ya ratsa mata jijiyoyin bakinta, a hankali ta fara sarrafa naman, shi kuwa Hamma Saif sake kamo hannunta yayi ya maidashi cikin kularar, kana ta kuma yago gutsuren naman, still ya kuma kai mata hannun bakinta, haka yai ta mata saida ta cinye rabin tsokar ƙungun, kana ya barta sabida taƙi sake yarda ta buɗe bakinta tunda tace mishi ta ƙoshi. Rufe kular yayi kana ya tureshi gefe, goran madarar ya buɗe wacce tayi sanyi kalau, rabinshi yasha, sannan ya kai mata bakin goran bakinta, tana buƙatan abu mai ruwa-ruwa tunda taci maiƙo shiyasa ba musu ta buɗe baki ta. Tasha mai ɗan yawa dan taji garɗin madarar da zuma sai ya tuna mata zamanta a numan. janye kanta tayi tare da yin gyatsa cikin sanyi tace. "Na ƙoshi, zanyi bacci". Rolling idonshi yayi tare da nuna mata hanyan bayan gida alamun taje ta wonke hannunta, dan shi bai taɓaba ko loma ɗaya. A hankali ta miƙe ta nufi bayan gidan da wonko hannun nata. Shi kuwa Hamma Saif ninke sallayoyin yayi ya ajiyesu wurin zamansu, kana ya ɓare sweet ɗin nan mai ɗan karen ƙamshi ya afashi a bakinshi, kana yaje gaban mirror ya kuma fesa turare sannan ya nufo jikin gadonshi da yafi kamanni da gadajen sarauta ko kuma na indiyawa dai-dai lokacin kuma ta fito daga bayan gidan. Ƙarasawa kan gadon yayi, ya kwanta kana ahankali ya lumshe idanunsa. Ganin haka yasa ta tako a hankali ta iso gefenshi baki ta tura tare da cewa. "Ni dai bazan kwana a nanba, ka buɗe min ƙofa in koma ɗakina zanyi bacci". Sauƙe wani sassanyan ajiyan zuciya yayi tare da gyara konciyarsa. Ganin hakafa ta shiga bubbuga ƙafafunta aƙasa, a shagwaɓe take cewa. "Nidai nagaji da tsayuwa, kabuɗemin ƙofa na fita, wallahi coffee kawai Ummi tace na kawo ma, dan Allah ka tashi ka buɗemin, kuma ma ai ni dai fitsari nakeji." taƙare maganar tana ɗan yayyarfa yatsun hannunta. Duk abunda takeyi yana ganinta ta ƙasan idanunsa, sosai yanayin yanda takeyi kaman wata ƙaramar yarinya ke burgesa, komai tayi kyau yake mata a hankali yake jin sanyi da ɗan-ɗanon da zaƙi da tarin ƙamshi sweet ɗin na ratsa bakinshi gaba ɗaya. Kusan mintuna 8 suka ɗauka ahaka, ganin cewa kaman yayi bacci ne, yasa ta siɗaɗo ahankali, ta iso kanshi saɗab-saɗab ta ɗan ranƙwafawa kanshi, tare da tura hannunta cikin aljihun wandonsa a hankali, wai so take ta zaro key ɗin. ba zato ba tsammani kawai taji ya fusgota jikinsa, idanunta ta zaro, tsorace tace. "Wayyo Allah na nidai ka sakeni." Hararan wasa ya watsa mata in a body language yace. "Naƙi ɗin bazan sake kiba, yau koni dodo ne anan ɗakin zaki kwana, in yaso idan dare ya raba tsakiya na cinyeki." Baki ta turo gaba, tare da soma ƙoƙarin tashi daga kan gadon, sake fusgota yayi ta faɗo kan jikinsa da kyau, lokaci guda ya yaye hijabin dake jikinta tare da wurgashi gefe. Cikin sauri ta sanya hannuwanta ta kare ƙirjinta, dan komai nata abayayyane yake. Saifuddeen kuwa wani irin fitinannen ƙamshinta daya daki hancinsa ne, yasashi lumshe idanunsa, tare da jan wani dogon numfashi, cikin sauri ta tashi daga jikinsa, tare da ɗan soma kare jikinta. Narkakkun idanunsa ya zuba mata, dan tayi wani irin asirtaccen kyau, ganin irin kallon da yake mata yasa taɗan soma ja da baya baya, fusgota ya kumayi tare da kwantar da ita akan gadon, lokaci guda ya maidata ƙasansa, inda ya zama shine asamanta, sakamar mata gaba ɗaya nauyinsa yayi, hakan yasa ta soma ƙoƙarin saka masa kukan sakalci da shagwaɓa, hannu yasa ya shafi kyakkyawar ƴar siririyar sarƙan gold ɗin dake wuyanta, ɗago idanunsa yayi ya kalleta, ita ɗinma kallonsa take, jin yanda tsikar jikinta ya zuba, yasa tayi saurin maida idanunta ta rufe, dan bata iya jure kallon cikin idanunsa. ƴar yatsan hannunsa yakai dai-dai kan lips ɗinta yana shafawa ahankali, wani irin yarr yarr haka ta soma ji ajikinta, ahankali ya sake matseta ajikinsa, tare da ɗaura bakinsa akan nata, harshensa yasa inda ya kamo lips ɗinta na ƙasa, yana lasa, kaman wanda ya samu alawan madara, jin taushin lips ɗinta na ratsa shi, yasashi manne bakinsu waje ɗaya, a hankali ya ɗan turo mata sweet ɗin bakinshi kan harshenta, ido ta ɗan buɗe da sauri tare da mishi kallon. "Laa sweet ɗina ka ɗauke to bani abuna". Gane nufinta ne ya sashi ɗaga mata gira ɗaya tare da mata alamar. "Ki karɓar to". A hankali ta fara worwore harshenta data naɗe tana ɗan turoshi saman nashi harshe da nufin zata kwace sweet ɗin ta, wani irin fitinenne shauƙi ne ya fara fizgarsu a tare, shi kuwa Hamma Saif yana jin ta kawo harshenta kusa da sweet ɗin yayi maza ya maida sweet ɗin gefen, Wani irin masifeffen shock yaji jin yadda Zaleeha tayiwa harshensa wani irin zazzafan laluma, ita a nata zaton sweet ɗinta take nema, ruggumeta yayi da kyau jin yadda ta cafe tongue ɗin shi, wanda zaƙi da ƙamshi da ɗanɗanon sweet ɗin ya ratsa harshen a zatonta mintin ne, ai kam kissing nashi ta farayi da zafi-zafinta, cikin rawan jiki ya kamo harshenta ahankali yake sucking. Zaƙin da ƙamshin strowberry sweet ɗin da yasha, ne ya game masu baki, hakan yasa ya ƙara kame harshen nata acikin bakinsa, ahankali ya ɗaura hannunsa akan bayanta, yana shafawa, ɗif haka tayi ajikinsa ƙirjinta da zuciyarta na wani irin bugawa, sosai yake kissing ɗinta suna tsotsar sweet ɗin, in ta sa tsanan tsotsan sweet ɗin sai ya kwace ya bata harshenshi ai kuwa cikin shauƙi take amsar harshenshi taita tsotsa, ruggumeta yayi da kyau kana yana me yawo da hannunsa ajikinta, dai-dai kan cikinta yasanya hannunsa, tare da ware igiyoyinn da ya haɗe rigar, take kuwa gaban rigar ta bude, har hakan ya baiwa beautyful breast dinta bayyana. Idanunsa yaɗan lumshe tare da jan wani irin marayan numfashi, ahankali yaɗan zare harshensa daga bakinta, akan fuskarta ya soma yawo da harshen nasa, har zuwa kan wuyanta, yanayin yadda yake tafiyar da harshen nasa akan jikinta, shiyasa taji gaba, ɗaya jikinta na wani irin yammm yammm, gaba ɗaya tunani da lissafinta ne yaso ƙwacewa, alokacin da taji harshensa na yawo kan tsayayyun breast ɗinta, wani irin dogon numfashi taja, tare da tura hannunta acikin gashin kansa, ahankali ta soma yunƙurin ƙwace jikinta, ganin haka yasashi ɗaura lips dinsa akan nipples ɗinta, lokaci ɗaya taja wani irin dogon nunfashi tamkar zata shiɗe, tare dayin wani irin zillo, har saida ƙirjinta ya sakeyin sama." hannayensa ya ɗaura akan nata, tare da riƙeta gam, ahankali yake ɗan tsotsan nipples ɗinta, yana kuma goga mata harshensa, ɗayan hannunsa ya ɗaura akan ɗayan breast ɗin nata, yana murzawa, a hankali hankali, Wani fitinenne abu Zaleehan takeji ajikinta, wanda takasa fassara shi daga zuciyarta har ƙasanta zut-zut sukemata, cikin nutsuwa ya sauƙo zuwa kan cikinta yana kissing ɗinta, alokacin daya zura harshensa cikin cibiyanta, kuwa wani irin numfashi taja tare dayin wani dogon miƙa, hannunsa yasa yana yi mata tafiyan tsutsa agefe da gefen cikinta, hakanne yasa gaba ɗaya tsikar jikinta suka mimmiƙe, sosai jikinta ya saki, saidai kuma daga wani sashi na zuciyarta tsoro da fargaba ne sukayi tasiri. Tashi yayi inda ya zauna akan ƙafafunsa, ɗagota yayi zuwa jikinsa, hakanne yasa kirjinsu haɗewa waje ɗaya, wata irin ƙaƙƙarfan ajiyar zuciya ya sauƙe tare da ƙara shigar da ita jikinsa, bakinsa ya ɗaura akan wuyanta, wani irin hot kiss yake bata, wanda yasa gaba ɗaya taji nutsuwarta na neman ƙwace mata, da wannan damar yayi amfani wajen rabata da ƴar fingilan rigar baccin dake jikinta, sake matseta ajikinsa yayi, ahankali yakai bakinsa dai-dai saitin kunnenta, cikin nutsuwa yaɗan zura harshensa acikin kunnen nata, tare da ɗaura hannuwansa duka biyu akan breast ɗinta, yana murzasu ahankali, yayinda yake sucking ear ɗinta, wani irin abune ke bin jikinta, hakanne kuma ya haifar da tsayuwar duk wani tunaninta, zazzafan numfashi me ɗauke da shiɗewa yake sakar mata acikin kunnen nata, ga kuma yanda yake sarrafa hannayensa akan breast ɗinta. Ɗan zame hannunsa yayi, ya sauƙar dashi zuwa kan mararta, ahankali yake shafa saman maran nata, tuni jikinta yayi weak saboda haka bataji zata iya hanasa abun da yake aikata wa, dan ita kanta tanajin masifar daɗin abun ajikinta, duk da irin barazanar da zuciyarta ke mata na tarwatsewa saboda tsoro, duk da shegen daɗin da takejin. Saifuddeen kuwa gaba ɗaya ya gigice, wani irin fitinannen feelings ne yake taso masa, gaba ɗaya jikinsa rawa yake, tuni saif ɗinsa ta jima da kumbura ta miƙa tayi samɓal, har wani irin harbawa yakeji tanayi tamkar zata faso wondon jikinsa tayi woje, taushi, ƙamshi, da kuma daɗin jikin Zaleehan gaba ɗaya sun gama kunce masa lissafi, matsananciyar sha'awarsa ya riga daya motsa shi kanshi bai taɓa ganin Saif ɗinshi tayi irin wannan miƙewa da kumbura ba irin na wannan ranar sai harbawa takeyi kamar zataci babu, jin yanda jikinsa ke rawa ne yasashi ƙara rungume Zaleehan, ahankali yake sakeyin ƙasa da hannunsa dake kan mararta, ɗan ɗagota yayi batare da yabari ta dawo cikin hayyacinta ba, ya tura mata ɗan yatsarsa acikin bakinta ai kuwa take ta kama tsotsan yatsarshi. Shi kuwa Hamma Saif a hankali yayi ƙasa da kansa zuwa mararta, wani irin masifaffen ƙamshi ne ya daki hancinsa, hakanne yasashi lumshe idanunsa, take yaji manhood ɗinsa na daɗa harbawa kaman zata fasa wandon ta fito, akasalance ya ɗan buɗata, tare da zura tongue ɗinsa ƙasanta. cikin wani irin fitinannen yanayi ya ɗanyi sucking ɗinta, tare da flicking tongue ɗin nasa. Wani irin zullewa Zaleeha tayi, sakamakon wani abu da taji, ya taso daga cikin ƙwaƙwalwa zuwa ƙasan ƙafarta, wani abune wanda tunda take aduniya bata taɓa jin koda makamancinsa ba da ƙarfi ta ƙanƙanme kanshi tare da cewa. "Shheeesssssss Hshhhhhhh uhuhhhhhhh Wayyyyyyyyyyo Hamma Saif". Shikuwa ganin yanda jikinta ya ɗauki rawa da karkarwa da tsumane yasashi ƙara nutsa harshensa, cikin wani irin gigita ya ƙara tsotsarta jin yadda take tsastsafo sweetness sperm da yaji acikin jikin nata mai ɗan karen yauƙi daya kuma gigitashi, cikin yanayin fitar hayyaci Zaleeha ta soma girgiza masa kanta wanda takejinsa kaman ya kumbura, baƙon yanayi ne awajenta. Wanda bakuma zata taɓa iya jurewa ba, tuni hawaye sun silalo daga cikin idanun nata, hannunta dake rawa, ta sanya inda ta riƙe kansa, cikin muryarta dake rawa tace. "Pleaseeeee! am sorry pleaseee, kabarni na tafi, bazan iyaba, inajin kaman wani abu zai fito daga cikin marana pleasseeee ka sakeni na tafi.....". kasa ƙarasa maganan tayi saboda yanda muryarta take kracking. Sam baya sanin tana cewa wani abu, dan yayi nisa sosai aduniyar da yake, saima ƙoƙarin zame tree guater tattausan wondon dake jikinsa da yake, cikin wani irin yanayi mai wuyar fassaruwa ta ɗago kanta, idanunta ne suka sauƙa akan manhood ɗinsa wanda tayi tsaye, kaman andasa ƙaƙƙarfan itace, gashi gaba ɗaya jijiyoyin jikinta sun tashi, cikin wani irin yanayi tare da matsanancin tsoron da masifeffen fargaba daya lulluɓeta, ta soma yunƙurin janye jikinta baya, kuka ta fashe masa dashi lokacin da taji ya kamo Saif ɗin nashi ya damƙa mata shi cikin tafukan hannunta. A gigice ta janye hannayenta, tare da sanya hannu ta ƙare ƙirjinta, sosai jikinta ya ɗauki rawa, sakamakon wani irin baƙon yanayin da kuma tsoro da takeji, cikin muryarta dake rawa tace. "Ni ka ƙyaleni na tafi, banaso ka daina taɓani, babu abun da zaka iya min saboda haka ni ka ƙyaleni, saikayi ta jagwal gwala mutum bayan kasan ba abun da zaka iya mai, nidai kabuɗe min kofa kada ka tayar min da hankalin da kasan bazaka iya kontarmin ba ka buɗe min ƙofa in tafi" Kasa ƙarasa maganan nata tayi, sakamon ganin yanda jikinsa ke wani irin ɓari, idanunsa tuni sun kaɗa sunyi jajur, sosai kalamanta suka daki zuciyarsa wato bazai iya mata komaiba ko, lokaci ɗaya yaji kaman ana kwaɗa masa guduma atsakar kansa, jikinsa duk rawa yake kaman an kunna masa vibrating, hannunsa yasa ya fusgota jikinsa da ƙarfi, bakinsu ya haɗe waje ɗaya, cikin zafi-zafi ya ke sucking harshenta, ahankali ya buɗa ƙafafunta, hakan yasa ya zama yana tsakiyanta, cikin matuƙar kiɗima haɗi da gigicewa take girgiza masa kanta, tare da cewa. "Wayyo Ummi kin ganshi ko, zaici zalina". sake danne bakinta yayi. Shikansa bazai iya faɗin, tayaya ne ko kuma ya akayi ba, haka ya samu kansa da ƙoƙarin shigewa jikinta bayan yayi addu'ar saduwa da iyali, sai-dai kuma duk da kasancewar gaba ɗaya ajiƙe take da sperm, hakan baisa yaji alamun cewa manhood ɗinsa zata kai ga samun abincin ruhinta ba, wani irin abune yaji yazo masa mai kama da ƙarfi a bisa ƙugunshi sai wani harbawa yaji jijiyoyin bayanshi nayi, lokaci ɗaya yaji bayansa na sakewa, kaman wanda ake zarewa ƙaya, gefe guda kuma ga wani irin masifaffen sha'awan da yakeji, har yanajin kaman mararsa zata fashe, ya fara fita hayyacinsa, gaba ɗaya ji yake duniyar na juya masa, wani irin abu yakeji agadon bayansa, tare da wani ƙarfi ji yake duk jijiyoyin bayanshi suna tattare da wuri ɗaya, idanunsa ya rumtseshi da tsananin ƙarfi cikin fitar hayyaci, ya nufi hanyar babbar fadar shiga jikinta da wani irin gigita da azaban ƙarfi. Hakanne yasa ta saki wani irin azababben ihu wanda ƙara da kuma sautinsa yakaraɗe ko ina dake cikin gidan gaba ɗaya. Dai-dai lokacin kuwa acan sashin Ummi harta kwanta, saita tuna da maganin ulcer'n ta, wanda ta aiki Hayatuddeen ya karɓo mata, wajen Adda Rahama wanda shine ma dalilin zuwansu gidanta, tashi tayi ta fito falo, ƙarasawa jikin ɗakin Hayatuddeen ɗin tayi, tare da ƙwanƙwasawa, Hayatuddeen kuwa jin ana ƙwankwasa ƙofarsa yasa shi tasowa cikin magagin bacci haka yazo ya buɗe ƙofar, Ummi ne ta dubeshi tare da cewa. "Ina maganin dana aikeka ka karɓomin agidan Addanku." Ɗan mutstsuke idanunsa yayi, cikin magagin bacci, yace. "Ummi maganinfa yana mota, dan Allah kibari saida safe, Allah bacci nakeji." hararansa Ummi tayi cikin dafe ƙirji, tace. "Da Allah Ni banason shashanci, yanzu haka ƙirjina ƙuna yake, saboda haka maza jeka ɗauko min nasha ciwon ƙirjin ya hanani bacci." ɗan zaro ido yayi, ashagwaɓe yace. "Ummi yanzu fa kusan ƙarfe 1 ne na dare, dan Allah Ummi ki bari saida safe, ko kuma ki rakani saimu ɗauko, amma ni kaɗai wallahi tsoro nakeji." Kai Ummi ta girgiza, tare da cewa "Wuce muje, kaidai kam kaji jiki, kana namiji amma sai shegen tsoro kaman farar kura." Haka Ummi ta tasa shi gaba, suka fito dan zuwa ɗauko maganin daya bari amota. Sun kusa isa parking space ɗinne, Hayatuddeen ya juyo azabure, cikin yanayin tsoro da zare ido yace. "Ummi bakiji ba kaman ihun Adda Zaleeha." Hararansa Ummi tayi tare da cewa. "Ihu kuma, kaidai tsoro ne kawai ya maka yawa babu wani ihu, yi maza ka ɗaukomin nikam." Acan ɗakin su Saifuddeen kuwa cikin wani irin zautuwa, haɗi da gigicewa da fita haiyaci cikin ƙarfin shawa'a Saifuddeen yasake tura manhood ɗinsa cikin jikinta, cikin wani irin raɗaɗin azaba, da zafi tare da tashin hankali, da kuma shiɗewa ta kuma zunduma wani irin gigitaccen ihu mai ɗan karen sauti wanda har ya zarce na farkon. Wani irin juyowa Hayatuddeen autan Ummi yayi a firgice ya......! Littafina na kuɗine in kina buƙatan karantawa bada haƙƙina a kankiba turo katin mtn na ɗari uku kacal ta wannan number 09097853276 ko kimin transfer ta asusuna 0005388578 jaiz back Aisha Aliyu Garkuwa, kada ku rena haƙƙin wani a kanku masu karanta na sata, ba sai nace Allah ya isa domin shi dama issasshene, abinda na sanidai ban badashi kyautaba. By *GARKUWAN FULANI* _Littafina na kuɗi ne in kin ganshi a wojema na satane, biya ɗarinki uku kacal ki karanta ba tare da haƙƙin kowa a kankiba. Turo katin mtn na ɗari uku ta wannan number 09097853276 ko kimin transfer 300 ta asusuna na 0005388578 jaiz back Aisha Aliyu Garkuwa. Sai ki turo shaidar boyanki ta wannan number dai ta 09097853276. In kuma kika karanta na sata Yaseeeeeeeeeeeeeeeeen doguwwwwwwwwwwwa bulluƙutu baƙar mutuwa_🤣🤣🤣😂😂😂🤗🤗🤗 Masu fitar da littafi daku bahaushe yake kyauta da kayan wani mugunta! Masu zuwa suce yai! Yai! Yai! GARKUWA ni part two nakeso na karanta dan haka zan bada 2oo, to one ɗin babarkice ta rubuta min? Ko ce muku nayi one ɗin kyauta ne? Dan haka ku dena tunanin zan saku a 200, 300 ne saya ko bari. Masu neman tsoffin littattafaina kufa kiyayeni🤣😂 dan nima bani dasu, ku nema a cikin groups zaku samu. INA CEKIYA DA BABBAR MURYA DAN ALLAH DAN ANNABI DUK MAI LITTAFINA MAI SUNA RIGAR KOWA TA TAIMAKA MIN DASHI GA NUMBER 09097853276 IN KUN GANO MINSHI KYAUTA ZAN ƘARASA MUKUSHI BABU KO ASI, ƳAN SON NA BATI KU SHIRYA KARATU🤣😂🤝🏻 Fans 1,2,3,4 wannan shafin nakune i love You all kuma lodi-lodi, ƴan group ɗin azumin mgna kuma ban mance kuna. Da ƙarfi Hayatuddeen ya juyo a guje zai koma cikin gida side ɗin Ummi. Cikin azama Ummi ta riƙo hannunshi tare da cewa. "Kai me hakan? Lafiyanka kuwa?". Ido ya zazzaro cikin tsoro da haki yace. "Ummi! Wlh tallahi ni dai naji ihun Aunty Zaleeha". Ya kalli Ummi da da itama tayi kasake, cikin fargaba tace. "Hayatuddeen kasa ke jin ihun ne ko?". Cikin yanayi tsoro yace. "Eh Ummi kuma gashi, muryar Adda Zaleeha ce". jinjina kai Ummi tayi cikin ɗan dakiya tace ɗauko min mgnin, in mun koma ciki zan kirata a waya, dan dai gashi cikin gidan kam lfy lau yake babu komai". To yace kana ya nufi cikin motar gaba ɗaya jikinshi na ɓari. A can sashin Saifuddeen kuwa, wani irin yunƙiri yayi da azaban ƙarfi dan kamar fizge mishi ƙugunshi akayi, cikin gigita ya kuma, kusanta Saif ɗinshi da sashinta, wani irin karkarwa jikinta ya farayi cikin azaban da taji yana neman ratsa ta kuma sakin wani irin gigitaccen ihu mai azaban ƙarfin amo. kamar daga sama! Saifuddeen yaji ƙaran sautin ya shigo kunnensa, a take ya jin wani abu na bugan kansa, kaman wanda ake kwaɗawa guduma haka yakeji, dan kuwa wani irin bugu kan nasa keyi, yanajin kamar zai fashe, gawani irin abu dayakeji acikin kunnensa mai kama da ƙara, kaman bugun ƙararrawa, haka yakejin abun gau! gau!! gauuuuuuuuuuuuuuu!!!!!!!!! babu ƙaƙƙautawa. Acan waje kuwa sautin ihun Zaleehan da ta kumayi ne, ya ziyarci kunnen Ummi, cikin sauri ta kalli Hayatuddeen dake ƙoƙarin buɗe murfin mota, fuskarta ɗauke da ɗan mamaki tace. "Hayatuddeen da gaskiyan kafa, tabbas yanzu kunnena kaman ihun Zaleeha suka jiyemin." Aɗan tsorace Hayatuddeen yace. "To Ummi me yake faruwa, kodai wani abune ya sameta, muje mu duba Ummi kar wani abune yake faruwa da ita." Ɗan jim Ummi tayi, tare da girgiza kanta, cikin sanyin murya tace. "Wata ƙila fa kunnen mune yake ji mana ba dai-dai ba, amma bayan haka mezai sa Zaleeha ihu acikin daren nan kaji gidan tsit babu wani mugun abu, gacanma mai gadima a barandarsa bisa alamu ma nafila yakeyi." ɗan jim sukayi su dukansu, wai ko zasu sakejin wani ihun nata. Saifuddeen kuwa gaba ɗaya ya gigice, jiyake kaman kansa zai tarwatse, abubuwa biyu ne suka haɗu masa a lokaci ɗaya, samun kansa acikin wata sabuwar duniya da yayi, wanda baitaɓa sanin akwai ta ba, duniyace wanda zaƙi da daɗinta ya zarce duk wani misali, haka yakejinsa kaman yana shawagi asararin samaniya bisa gajumare, gefe guda kuma wani irin bugawa zuciyarsa keyi, kansa na bala'in yi masa ciwo, babban tashin hankalin daya fara samun kansa aciki kuma shine yanda yakejin wani irin sauti na tashi acikin kunnensa, kaman kunnen nasa na ƙoƙarin jiyo masa wani sauti. Zaleeha kam ta shiɗe, ta kuma gigice dan ta fara fita hayyacinta, wani irin azaba da kuma raɗaɗi me zafi ne ke game dukkan sassan jikinta, zafi takeji ga kuma wani abu dake ratsa ƙwaƙwalwarta, cikin azababben wahalan da takesha tasakeyin wani ihu tana bugun ƙirjinsa tace. "Hamma Saif zafi! zafi!! Zafi!!!. Wayyo Allah na Hamma Saif zan mutu, wayyo Allah na wani ya taimakeni mana, Hamma S...a...i..f zan mutu, zafi nakeji, ahhhhhhhhhhhhhh!!!...." tasaki wani irin ƙara. Kaman acikin mafarki haka yaji ihu da kuma abun da ta faɗa sun daki dodon kunnensa, haka yaji muryar ta cikin wani irin amo ta ambaci sunanshi, jiyayi gaba ɗaya duniyar na juya masa, samun kansa yayi cikin wani sabon al'amari, wanda koda wasa baitaɓa zato ko tsammani ba, cikin zaucewa haɗi da fitar hankali ya ɗan ɗagota, dan gaba ɗaya ya ruɗe ya kuma zauce, hakanne kuma ya bawa manhood ɗinsa dama wajen sake nutsuwa cikin jikin Zaleehan. Wani irin razanannen ƙara ta saki, tare da nutsa hannunta acikin dantsen sa, kuka take irin na fitar hayyaci da raɗaɗi. Ga mamakinsa ji yayi, yanajin ihun nata da kuma kukanta acikin kurmantattun kunnuwansa, wanda suka jima da toshewa tsawon shekaru 20, Allah mabuwayi me iko, karon farko kenan aduniyarsa bayan shekaru 20 da suka wuce, da yaji sauti da kuma magana acikin kunnuwansa, jikinsa ne gaba ɗaya ya ɗauki rawa, sam baya cikin hayyaci da nutsuwarsa, so yake ya buɗe idanunsa, amma ya kasa saboda nauyin da suka masa, ji yayi jijiyoyin idanunsa da kuma na kansa dana kunnuwansa, sun riƙe gam har yana jin yadda jijiyoyin gadon bayanshi ke mimmiƙewa. Zaleeha kam ta riga da ta sadakar saboda ita kaɗai tasan azaban da take sha, kuka take sosai tana buga ƙirjinsa, tare da ƙiran sunansa, wanda duk kalma ɗaya da zata fito daga bakinta sai yajisu acikin kunnensa, saidai jin muryar tata yake tana fita da wani irin amo, wanda yakeji kaman jijiyoyin kansa zasu tsinke. Acan waje kuwa jin shiru basu sake jin wani ihun ba yasa Ummi kai dubanta ga Hayatuddeen cikin kulawa tace. "Maza ɗauko min maganin mu tafi, dama inajin kunnuwan mune kawai suke mana gizo ba ihun Zaleeha bane." Jiki asanyaye Hayatuddeen ya ɗauko maganin suka nufi falon Ummi'n. A can wurin Hamma Saif da Zaleeha kuwa. Wani irin riƙo Saifuddeen wanda baya cikin hankali da tunaninsa yayi wa Zaleeha, gaba ɗaya jikinsa rawa yake, ahankali yaɗan soma motsa laɓɓansa wanda suke rawa, cikin zuciyarsa ya ambaci sunan Allah, amatuƙar firgice yaji sautin muryar tasa ta fito, tare da dukan dodon kunnensa, jin haka yasashi ƙara gigicewa, sunan Allah ya kuma ambata,. "Lailahalillaha Muhammadu Rasulullah Sallallahu alaihi wasallam, Lahaulawalaƙuta illabillah, Hasbinallahuwani,imalwakil Subahanallah". still kuma ya sake jin muryarsa ta fito raɗau, fashewa yayi da wani irin kuka me matuƙar ƙarfi, lokaci ɗaya yaji wani irin ƙarfi ajikinsa tamkar zaburarren doki cikin zafi-zafi ya rinƙa sarrafa ƙugunshi da bayanshi yana iya motsa ƙugun yana sama da ƙasa kuma da azaban ƙarfi dan kamar fizgarsa akeyi, hakan ne yasa cikin kiɗima da zaucewa ya sake tura manhood ɗinsa da ƙarfi cikin jikin Zaleeha'n, wani irin azababben ihu ta saki, wanda har ya fin na farko ƙarfi, saboda ayanzu ne ya shiga jikinta sosai ya kuma fasa virgin ɗinta, ihun ta kumar a gigice take murza kanta tare da riƙo damatsan hannunshi da ƙarfi take cewa. "Wayyyyyyyyyyo Allah na, Wayyo Baba Malam, Wayyo Mamy Wayyo Mama Hamma Saif zai kashe miki Zaleehanki, wayyo Ya Ahmad, wayyo Adda Maryam zai kasheni". Jin yadda ya kuma cusa Saif ɗinshi da ƙarfin ya gama ratsa gaba ɗaya budurcinta ne yasa tayi wani irin zillo tare da sake hannunshi kana ta buɗa ƙafafuwanta da ƙarfi rumtse idanunta tayi da iya ƙarfinta tace. "Wayyo Ummmmmi kizo Hamma Saif zai kasheni Ummi kice ya barni kar in mutu". Ihun nata yayi dai-dai da shigan su Ummi falo, wanda kuma dukansu sunjiyo ihun ta da kuma abinda duk ta faɗan. Hayatuddeen ne ya zaro ido, cikin tsoro yace. "Kinji ko Ummi, wallahi ihun Adda Zaleeha ne wannan, munshiga uku Ummi meya sameta? kinji sunanki fa take kira me Hamma na keyi mata, ko dai dukanta yakeyi ne?." Dai-dai lokacin kuwa Ahmad ya sauƙo daga sama, wanda shima yana daga cikin ɗakinsu, ya jiyo ihun da Zaleeha keyi maganganun da takeyi cikin kiɗima da rawar muryarta magiyar Zaleeha'n, Aɗan tsorace Ummi ta dubeshi, hankalinta amatuƙar tashe tace. "Ahmad kaima kaji ihun Zaleeha'n ko, me yake faruwa ne wai, me tayi mishi zai kama dukan ƴar mutane a tsakar dare, karfa yayi mata illa bamu sani ba!." Ummi ta ƙare maganar cikin tashin hankali. Kai Ahmad ya jinjina, cikin nutsuwa da zallan jin daɗi dan ya gano cewa yau Saifuddeen yana magance ƙafafuwan guduwan ne, kanshi ya ɗan kauda kana yace. "Eh naji, amma inaga bawani abun tashin hankali bane, wata ƙila ko mummunan mafarki tayi." Raleeya dake sauƙowa daga kan step, amatuƙar ruɗe tace. "Mafarki kuma, nidai tsoro nakeji wallahi, kada ya mata illa kasan Hamma baji yakeyi bare yasan tana ihu da magiyar ya barta, dan Allah nikam muje mu dubata." Ta faɗi maganar tana yayyarfa hannuwanta alaman tsoro. Murmushi Ahmad ɗin yayi, danshi hakanan jikinsa ya basa cewa, Saifuddeen ne yayi ritsi yake kwasar ganima da ladan sadakinshi, ɗan hararan wasa yayiwa Raleeyan tare da cewa. "Kije ki duba kuma? me zaki duba dan kece uwar dube- dube, mace na tare da mijinta dan tayi ihu saikice zakije ki duba dan kece uwar taimako da dube-dube ke waya dubaki randa kikayi naki ihun?, nina faɗa muku wata kila mafarki ne, idan ba mafarki bane to zallan raki ne kawai irin na Zaleeha." Duban Ummi yayi wacce take can gefensu dan yanzu ta gano dalilin ihun Zaleeha, cikin son kwantar mata da hankali yace. "Dan Allah Ummi kije ki kwanta, kinga fa yanzu dare ne, koma miyene ni inaji ajikina cewa ba wani babban abu bane, bare ma nasan ba komai." ya faɗi maganar yana ɗan sakin murmushi, har da ɗan ciza lips ɗinsa, Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe, tare da ɗan jinjina kanta, ita kam dai tabbas ta tsorata dan tasan koma menene wannan dai kukan wahala takeyi hakan ya nuna Saifuddeen bai bita a hankali ba, sannan haka nan takejin ƙirjinta na bugawa, saidai jin kalaman Ahmad ɗin yasa ta ɗanji sanyi, musamman ma yanda taga Ahmad ɗin yana ƴar dariya ƙasa-ƙasa, duban Hayatuddeen tayi, cikin kulawa tace. "Hayatuddeen wuce kaje ka kwanta, sai da safe." Ɗan karyar da wuya Hayatuddeen ɗin, yayi dan har ga Allah shi bai gane komaiba cikin sanyi yace. "To Ummi amma bazamu je muɗan duba ta ba, wallahi tsoro nakeji." Kai Ummi ta girgiza tare da cewa. "Kaje ka kwanta nace, wataƙila ma ba ita bace, kunnen mune kawai ke mana gizo." Jiki asanyaye haka Hayatuddeen ya tafi ya shige ɗakinsa, itama Ummin bata sake cewa komai ba, ta nufi ɗakinta. Ganin haka yasa Ahmad ya kama hannun Raleeya suka haura sama, sai murmushi yakeyi, wanda yasa Raleeya ta saki baki tana kallonsa, Suna shiga ɗaki ya jawota jikinshi suka faɗa kan gado, cikin tsoka yace. "Ni kizo ki bani abin daɗina, itama a hankali watarana ita da kantama zata nema yau dai ta kira rayayyu har ta kira matattu, kema haka kikayi in kin manta in tuna miki, harda Ya Nuruddeen da Abba kika kira dan kawai na ɗanyi aikin samun ƙofar lamɓun daɗin mu". rufe idonta tayi tare da faɗawa jikinshi a hankali tace. "Allah ni tausayinta nakeji sabida nasan irin azabar da take sha, ku ba ruwanku sai kun kai mutun hanyar lahira ku kuna jin daɗi ku". Mirginata yayi ta konta kana ya durƙusa tare da zare wonɗon jinshi kana ya zare mata rigarta, rumfa yayi mata da jikinshi, ido ta lumshe tare da ruggumeshi, da sauri ya yunƙura kamashi tayi ƙam a jikinta, dariya ya ɗanyi tare da cewa. "Daɗi ko?". Kanshi ta gyaɗa mishi, fuskarta ya ɗan shafa kana yace. "To muma maza ran forko wahala muke sha, ance miki buɗe hanyar sauƙi ne dashi, yadda kukejin zafi muma munaji musamman in namiji saurayine". kai ta gyaɗa mishi kana tajawo musu blanket. Acan ɓangaren Zaleeha kuwa, wani irin azaba Saifuddeen ke jiyar da ita, zafi da raɗaɗi sun soma zautar da brain ɗinta. hakanne yasa lokaci ɗaya numfashinta ya soma wani irin fusga, take kuma duk jikinta ya sake, idanunta ne suka rufe, lokaci ɗaya numfashinta ya ɗauke, komai na jikinta ya daina aiki. Saifuddeen kam yayi nisa tayanda bazai iya sanin cewa tana motsi ko batayi ba, shikansa baisan awani hali yake ciki ba, har yanzu jikinsa rawa yake, ga kuma wasu irin hawaye masu zafi dake fita daga cikin idanunsa, ya kasa sanin awace matsaya ko duniya yake, duk da kasancewar azauce yake, amma hakan bai hanashi jin zallan ni'imar Zaleehan ba, wanda take ratsa gaba ɗaya ilahirin jikinsa, har kuma tayi nasaran ciresa a hayyacinsa. Ummi kam koda ta koma ɗakinta kwanciya tayi, zuciyarta cike da tarin saƙe-saƙe iri iri, tabbas ta tsorata, amma ganin yanda Ahmad ke sakin murmushi, yasa taji wani sabon tunani ya ziyarci ƙwaƙwalwanta, lokaci ɗaya taji zuciyarta ta karye, tausayin Zaleehan ne matuƙa ya kamata, dan hakanan ta tuna da ranan da aka kai Raleeya ɗakin Ahmad, kwana tayi batayi bacci ba. Da tunani kala-kala acikin ran Ummi haka bacci ya ɗauketa. Sama da 50 minute ya ɗauka yanajinsa acikin wata duniya ta daban, cikin abun dabai wuce 3 minute ba ya fara sakin wani irin gurnanin nishi, mai ɗauke da wani irin sauti, lokaci ɗaya yaji bayansa na riƙewa, kaman wanda ake buga masa wani abu gaba ɗaya jijiyoyin bayanshi yaji suna ta riƙewa, wani irin nishi me ƙarfi yayi azauce cikin wata irin muryar dake bayyana zallan yanayin da yake ciki, bakinsa na rawa yaƙira sunan "Za....l..eee...haaa...." Murya ararrabe, wani irin jiri ne yazo masa, hakan yasashi faɗawa saman jikinta, inda ya ɗaura bakinsa adai-dai saitin kunnenta, wani irin numfashi me zafi yake fitarwa, komai na jikinsa yayi rauni, lokaci ɗaya wani irin zazzafan zazzaɓi ya dirar masa, harta haƙwaransa saida suka soma rawa suna haɗewa da juna. Ɗan mirginawa yayi daga kanta, cikin azaban ciwon da kansa yakeyi masa ya zuro da ƙafafunsa ƙasa daga kan gadon. Baisan tayayane ko kuma yaushe ne ya iya yunƙurin tashi ba, saidai ga mamakinsa samun kansa yayi atsaye tsam da ƙafafunsa, idanunsa wanda sukai ja kaman anzuba masa barkono ya zazzaro waje, yana kallon ƙafafunsa dake rawa kaman wanda aka jona musu shocking, take yaji bayansa na duka kau! kau!! kauuuuuu!!! haka kaman ƙashin bayanshi zai ɓalle, jiri ne ya ɗebesa, take ya zube akan gadon, zazzafan zazzaɓi me tsanani ne yasake hawansa, haka yaji ko kansa bazai iya ɗagawa ba, ga kuma bayansa dake masa azabebben ciwo. Hannunsa dake rawa ya kai kan fuskar Zaleeha tare da shafawa, ƴar yatsansa yasa adai-dai ƙofar hancinta, jin bata numfashi ne yasashi rumtse idanunsa da ƙarfi, take wasu irin hawaye masu zafi suka silalo daga cikin idanunsa. Duk bayan second ɗaya kuwa bugun zuciyarsa ke tsananta. Gaba ɗaya ɗan kuzarin da ya rage masa ya tattaro tare da yunƙura ya tashi zaune. Ƙokarin miƙewa yake kaman yanda yaga yayi ɗazu, amma sai ya kasa, saboda yanda bayansa ya riƙe sosai, awahalce ya jawo wheelchair ɗinsa ya hau, ko zama da kyau bai iya ba, saboda yanda yakejin bayansa na sarawa. Dishi-dishi yake gani haka ya nufi bathroom, adaddafe ya ƙarasa gaban shower, inda ya sakarwa kansa ruwa. Jikinsa na kakkarwa haka yayi wankan tsarki, tare da alwala, koda ya fito daga toile ɗin baya wani gani sosai, take kuma yaji wani irin fitinannen sanyi na huda kowani ɓulin gashi na jikinsa, yana shiga ko ina a sassan jikinsa, ciwon kai, zazzafan zazzaɓi, da kuma matsanancin ciwon baya sune abun da suka kassara gaba ɗaya kuzarinsa, har kuma yakejin raɗaɗinsu acikin ƙwaƙwalwarsa jiki na rawa ya buɗe firiji ya ɗauki goran ruwa mai sanyi. Da ƙyar ya iya kai kansa kan gadon kwanciya yayi, abayanta buɗe goran ya watsa mata ruwan amman a banza kuma watsa mata yayi, wani dogon numfashi taja, jin haka ya ajiye goran kan bedside, jiki na rawa ya jawo rigar baccinta ya saka mata a daddafe ya lalubo hijabinta ya rufe mata daga cikinta zuwa ƙasa, kana ya konta tare da jan blanket ya rufa gaba ɗaya jikinsu, wani irin runguma yayiwa Zaleehan wanda da ace tana cikin hayyacinta, da sai tayi kuka, saboda yanda ya maƙalƙaleta sosai jikinsa ke rawan sanyi, haka haƙwaransa ke haɗewa suna kakkarwa, idanunsa ne suka rufe saboda sunyi nauyi sosai. Ita kuwa Zaleeha daga numfashi ɗayan bata kuma sake waniba bare tasan inda take. Ahankali cikin ransa yasoma karatun alƙur'ani, wanda tun yanayi azuci, har karatun ya fito fili, wanda ma da ƙyar muryarsa take fita, dan ciwon kan nasa bawai ya ragu bane, gashi bayansa nata ciwo kaman zai ɓalle. Haka ya dinga karatun al'ƙur'ani, da zaran ya kai ƙarshen sura sai ya kamo wata surar ma ya karanta, shikam ayau bashi ma da bakin da zaiyiwa Allah godiya, tabbas tsarki ya tabbata ga Allah Ubangiji, majin ƙan kowani bawa, me amsa addu'a, me cuta me kuma waraka da yayewa, sarkin da babu kamarsa, mamallakin abun dake fili da ma wanda ke ɓoye. Sosai yake karantun, tun muryarsa naɗan fita har yazamana ko ya motsa bakinsa muryarsa baya fita, saboda yanda kansa ke masifaffen ciwo, ga kuma ciwon bayan nasa daya tsananta, Wasu irin hawayene suka silalo daga cikin idanunsa, alokacin da yaji ƙiran sallan asuba acikin kunnensa, wanda rabonsa da jin hakan yau sama da shekara 20 kenan, tun yana ɗan shekara 13 rabanso daji da mgna, lokacin Hayatuddeen bai cika shekara uku bama a duniya wani irin kuka ya fashe dashi mai tsuma zuciya, take kuma ya zamo daga kan gadon, durƙushewa yayi ƙasan tiles tare dayin sujjada, ya kuma fashewa da wani sabon kuka mai tsuma zuciya, me zaicewa mahaliccinsa? wani irin godiya zaiyi masa? haƙiƙa bashi da wannan bakin, saida yayi kuka sosai, sannan ya ɗago daga sujjadar, adaddafe ya shiga toilet ya ɗauro alwala yana fito ya zura jallabiya bisa gajeren wondon da ya saka, sallah raka'a biyu yayi, ko acikin sallan saida yayi kuka sosai, haka da zazzaƙar muryarsa ya dinga yiwa Allah kirari da sunayensa tsarkaka, yana idar da sallan, yaɗan janyo jikinsa ya jingina da bango, hannunsa yakai yaɗan taɓa Zaleeha, gani yayi komai nata asake yake gashi kuma bata numfashi, hawayen tsananin tausayinta da kuma ƙarin ƙaunarta ne suka kwaranyo daga cikin idanunsa, hannunta ya kama ya riƙe gam, haka yakeji kaman ya maida ita cikin jikinsa. Tabbas Zaleeha rayuwarsa ce, itace silan komai na nakasarsa, itace gaba ɗaya duniyarsa kuma yanzuma gashi itace silar warakanshi. Samunta HASKE ne acikin rayuwarsa. Jin ana ƙoƙarin shiga sallan asuba, yasa adaddafe yayi sallan dan bayajin zai iya zuwa masallaci, saboda ko zama me kyau baya iyawa, koda yazo yin sallan ma saida yaɗan jingina, saboda yanda jiri da kuma zazzaɓi me zafi da suka rufeshi ga ƙugunshi da yakeji kamar ya ida gwamɓalewa, idan yayi sujjada kuwa da ƙyar yake iya ɗagowa, saboda yanda bayansa ke riƙewa. Yana idar da sallan, adaddafe yajawo kekensa ya hau, ko iya jingina bayansa da kyau bayayi, saboda yanda yakeji, haka ya nufi sashin Ummi, yana ganin dishi-dishi a idanunsa. Da ƙyar ma ya iya bude ƙofar falon yashiga, babu kowa afalon, kaitsaye ɗakin Umminsa ya nufa, jikinsa gaba ɗaya ba ƙarfi, hakan yasa ahankali ya ɗan murɗa handle ɗin ƙofar, jin ƙofar arufe gam yasashi, juyawa, ya nufi ɗakin Hayatuddeen yana zuwa kuwa, ya samu ƙofar abuɗe, koda ya shiga ɗakin bai taradda Hayatuddeen ba, da alama baidawo a masallaci ba. Ƙarasawa cikin ɗakin yayi, inda yaɗan zamo daga kan kekensa, akan lallausan gadon Hayatuddeen ɗin ya kwanta, tare da jawo blanket ya rufa ajikinsa, har yanzu jikinsa rawan sanyi yake, saboda tsabar karkarwan da jikinsa keyi kuwa, hatta gadon ma saida ya ɗauka. Hayatuddeen kuwa tare da Ahmad suka dawo daga masallaci, sai faman zuba hamma yake dan bacci bai ishesa ba. Kai tsaye ɗakin Ummi suka nufa, Hayatuddeen ne yayi knocking, Ummi wanda idar da sallanta kenan tasowa tayi ta buɗe ƙofan dan tasan bazai wuce suɗin ba, cikin girmamawa Ahmad ya durƙusa ya gaisheta, fuska asake ta amsa masa, Hayatuddeen kuwa cikin gigin bacci ya gaisheta, amsa masa tayi tare daɗan ranƙwashin kansa, murmushi sukayi su duka, sannan Ahmad ya juya ya haura sama, shi kuwa Hayatuddeen juyawa yayi ya nufi ɗakinsa. Yana shiga kuwa ya ja kofar ya rufe, juyowan da zaiyi ne idanunsa suka sauƙa akan wheelchair ɗin Saifuddeen, da kuma shi kansa Saifuddeen ɗin dake kwance yana ta masassara, har kana iya jiyo hucin numfashinsa daga bakin ƙofar ɗakin. Idanu Hayatuddeen ya zazzaro, atsorace ya ɗan dafe ƙirjinsa, cikin sauri ya juya ya fice daga ɗakin har yanacin tuntuɓe. "Ummi! Ummi!! Ummmee" Haka yake ƙiran sunan Ummi da ƙarfi. Ummi dake zaune aɗaki jin yanda Hayatuddeen ke ƙiranta, yasa taji gabanta ya faɗi haka yasa jiki na rawa ta miƙe ta buɗe ƙofar ɗakin jin yadda Hayatuddeen ke danna mata kira babu ƙaƙƙawautawa, tana saƙo kanta woje shi kuma yana sako kansa ciki haka yasa sukayi kiciɓis a bakin ƙofar. A birkice Hayatuddeen ya kamo hannunta cikin firgita yace. "Ummi Hamma Saifuddeen! zo muje kiga Hamma a ɗakina baida lfy sai rawan sanyi yakeyi". A take Ummi taji wani zufa ta karyo mata haka nan taji jikinta na rawa, dan kuwa mafarkin da tayi daren jiya ne ya faɗo mata wai ƙugun Saifuddeen ɗinta ya ida gwambulewa. Cikin sauri tabi bayan Hayatuddeen. Ahmad kuwa har ya haura sama jin yadda Hayatuddeen ke ƙiran Ummi a gigicene ya sashi juyowa zai sauko dan hakanan yaji a jikinsa cewa ba lafiya ba. Cikin sauri Ummi ta shiga ɗakin Hayatuddeen ɗin, hankalinta a tashe isa zuwa jikin gadon Hayatuddeen ɗin wanda Saifuddeen ke kwance, akai yanata faman masassara, cikin sauri Ummi tasa hannunta ta ɗan yaye blanket ɗin daya ya rufe jikinsa dashi, ganin yadda gaba ɗaya jikinshi karkarwa ne yasa tace. "Subahanallahi Saifuddeen meya sameka? dama baka da lafiya ne?." Tayi maganar tana ɗan jijjigashi sanin da tayi cewa idan bata taɓashi ba bazai gane tazo ɗinba, saboda ya bawa ƙofar shigowan ɗakin baya. Shi kuwa Saifuddeen Jin muryar Umminshi ne cikin kunnuwanshi wanda rabon da yajita tsawon shekaru 20 kenan. A hankali ya ɗago kansa wanda yake jinsa kamar zai rabe biyu, wasu irin zafafan hawaye ne suke zubo mishi daga ida nunshi. Ganin haka Ummi tayi masifar gigicewa cikin tashin hankali da kiɗima tace. "Innalillahi wa innalillahi rajiun, Saifuddeen meya sameka?, ina Zaleeha meya meya sameka?" a hankali ya lumshe Idanunshi tare da motsa lips ɗinkin cikin wata iriyar murya mai ɗauke da rauni da baiyanar da azabar da yakeji yace. *"Ummy"* cikin wani irin fitinenne ruɗani fargaba da kuma kaɗuwa Ummi taja da baya, lokacin ɗaya taji wani irin shock ya shiga jikinta gaba ɗaya wanda hakan yasa jikinta karkarwa idanunta suka firgita woje jin sauƙar muryar da bazata manceba tsawon shekaru 20 kenan da ta daina jin amo da kuma sauti wannan muryar, tun tanasa rai da jinta har ta cire, mafarki takeyi ne ko kuwa da gaske ne?so take ta tantance hakan yasa ta dafe kanta dake juyawa da kuma ƙirjinta dake barazanan fitowa waje, hannu tasa ta soma mutsstsuke idanunta. Ahmad ne wanda shigowarsa cikin ɗakin kenan yajie sautin muryar Saifuddeen ɗin ya daki dodon kunnenshi muryar da bazai taɓa mancewa da itaba komin yawan shekarun da aka kwashe bai jitaba kuwa. Ji yayi gaba ɗaya jikinsa ya soma rawa tsikar jikinsa na mimmiƙewa idanunsa ne suka ciko da wani irin ƙwalla. Saifuddeen kuwa ganin irin kallon da Ummi keyi mashine mai ɗauke da tantama yasashi miƙo hannunshi jiki na rawa ya kamo hannunta, cikin tsananin rawan jiki da kaɗuwa Ummi tace. "Saifuddeen!!!". Ido ya rumtse da ɗan ƙarfi yace. "Na'am Ummi!". wani irin tsuma da karkarwa jikinsu keyi gaba ɗayansu, Hayatuddeen kuwa samun kansa yayi cikin wani irin masifeffen tashin hankali da kuma firgici abune da wanda shi dai zaice bai taɓa zaton ko tsammanin ba asalima kuma shi zai iya cewa bai san kalan muryar Hammanshin ba tunda yana ɗan ƙarami Hamman nashi ya kuramce, bai taɓa jin yayi maganaba sai yau, cikin wani irin razana ya fasa wani ihu na tsananin kaɗuwa da farin ciki take kuma ya tafi luuu ya faɗi a sume, da sauri Ahmad ya tareshi ya kontar dashi bisa carpet, dan sam hankali Ummi baya kanshi, shi kuwa Saifuddeen zafin ciwo yasa bai kula da suman da Hayatuddeen yayiba shima kanshi Ahmad hankalinshi na kan Saifuddeen shiyasa kawai sai ya kontar da Autan Ummi kamar maiyin bacci. A kiɗine Ummi ta matsoshi tare da cewa. "Babana kana jina kana mgna, Ya Allah na in mafarki nakeyi ma ka tabbatar min dashi". Cikin dauriyar ciwon da yake ji ɗin yace. "Ummy a zahiri ne, ba mafarki kikeyi ba, ƙudurar ubangiji ce, dare ɗaya ya ɗauke jina da mgnata, kana bayan tsawon shekaru ashirin ya dawo min jina da mgnata a dare ɗaya". Cikin wani irin kaɗuwa Ummi tace. "Yaushe ka fara magana yaushe ka fara jin mgna? Saifuddeen". Wani irin rumtse idonshi yayi dan jin kanshi kamar zai rabe gida biyar ga wani irin sarawa da ƙugunshi keyi a fizge yace. "Ummi daren jiya na fara jin Zaleeha tana kiran sunana, tana ihu, Ummi sunana da kuka da ihun Zaleeha na fara ji tamkar zai fasa min dodon kunne Ummy kuka Zaleeha tai tamin". Sai ya kuma saki hannun Ummi ya riƙe kanshi da hannu biyu da ƙarfi ya matse kan nashi murya na rawa yace. "Wayyo! Allah na wayyo bayana Ummy bayana zai ɓalle inaji kamar ana haɗa jijiyoyin ana ɗinkewa Ummy bayana, kaina, wuyana, ƙuguna, cinyana, ƙafata, Cikin tsananin kiɗima Ahmad ya matso Saifuddeen ɗin tare da kiranshi. "Saifuddeen!." Ɗago idanunsa da suka kaɗa sukai jajazir yayi, murya na rawa yace "Na'am Ahmad." Idanu Ahmd ya zazzaro cike da shock, sai kawai ya fashe da wani irin kuka, tare da jawo Saifuddeen ɗin jikinsa ya rungumesa sosai. Dai-dai lokacin kuwa Raleeya ta shigo cikin ɗakin aguje, ganinsu ahaka yasa ta yi turus tana me ƙare musu kallo. Ganin yanda Ummi da Ahmad ke kuka yasa taji gaba ɗaya ƙafafunta sun fara rawa, ƙoƙarin buɗe baki take dan tayi magana, ta hango Hayatuddeen a yashe aƙasa baya motsi, kansa tayi agigice ta durƙusa tana jijjigasa, hankalinta amatuƙar tashe tace. "Hayatuddeen ka tashi dan Allah, me yake faruwa, Yaya Ahmad me kukayi masa? meyasa baya motsi? wayyo dan Allah Ummi kizo kiga Hayatuddeen baya motsi.." tafaɗi maganan tana me jijjiga Hayatuddeen ɗin dan gaba ɗaya ta ruɗe. Saifuddeen ne ya ɗan janye jikinsa daga na Ahmad ɗin dan ji yake kamar gatari ake kima mishi a bayanshi komawa yayi ya konta tare da rumtse idanunsa, dan ciwo yakeji sosai acikin jikinsa. Ummi ne ta tashi daga durƙuson da take inda ta ƙarasa kan Hayatuddeen zuwa lokacin kuwa tuni Raleeya ta ɗauko goran ruwa ta yayyafa masa, wata iriyar ƙatuwar ajiyar zuciya ya sauƙe. Ganin haka yasa Raleeya itama sakin ajiyar zuciya. Ummi kuwa akan gadon ta zauna, har yanzu hawayene ke tsiyaya daga cikin idanunta, Hannun Saifuddeen ta kamo, cikin muryarta dake rawa tace. "Saifuddeen Babana hankali ya tashi gani nake kamar mafarki nakeyi, meya sameku ina Zaleeha." tafaɗi maganan tana me ɗan shafa gefen fuskarsa. Idanunsa da suke lumshe ya buɗe tare da zubawa Ummin nasa su, sake riƙe hannunsa dake cikin nata yayi, laɓɓansa yaɗan motsa ahankali yace. "Ummi baya na zai golɓole. Allah ya bani lafiya ayanzu na zama akaman kowani meji da faɗa amman kuma baya zai tsinke." sabon kukane da fargaba ya sake ƙwacewa Ummi, cikin zuciyarta take ambaton sunan Allah tare da neman agajin Allah. Raleeya kuwa haka ta zama kaman gunkin da aka sassaƙa, ganin abun take kaman awata duniya ta daban, jikinta ne ya ɗauki ɓari, saboda yanda taga Hamman nata na magana, abune wanda bazatace ga lokacin da ta taɓa gani yayi ba, ko adacan baya lokacin daya kurumce bata da wani isashshen wayo. Hannu tasa ta dafa kanta dake bugawa, muryarta na rawa tace. "Hamma Saifuddeen." Jin muryan Raleeya acikin kunnensa yasashi daurewa ya kalleta, tare da sakar mata murmushi, cikin muryarsa me fidda azabar da yakeji yace. "Na'am Raleeya." Wani irin kukane yazo mata, take ta tafi da gudu ta faɗa jikinsa, lokaci guda kuwa ta saki kuka me sauti, tare da ƙanƙamesa, cikin kukan tace. "Alhamdulillahil lazi bini'imatihi tatimussalihat, Alhamdulillah Ya Allah, Hamma Saifuddeen kaine, kake magana, Alhamdulillah Allah." Sai kawai ta sake sakin sabon kuka. Shi kuwa Saifuddeen ji yayi kamar anja bayanshi da ƙarfi hakanne ya sashi zubda wasu hawayen azaba. Hayatuddeen wanda farfaɗowansa kenan, janyo jikinsa yayi, inda ya raɓa jikin Hamman nasa, ya saki wani irin kuka me taɓa zuciya, wace irin ranace yau tazo me cike da al'khairi agaresu?. Saida sukayi kuka sosai kafun suka ɗan janye jikinsu daga nashi, dan jin yanda jikin nasa ya ɗauki zafi zau kaman wuta, gashi sai rawan sanyi yake, haka Raleeya ta fita daga ɗakin da gudu kaman wanda aka tsikara. Ummi ne ta matso kusa dashi, tare da kamo hannunsa ta zuba masa ido, tanajin wani irin farinciki da fargaba na neman fasa mata zuciya. Shikuwa zuwa lokacin shikaɗai yasan me yake ji ajikinsa, ciwo sosai yakeji. Hannun Ummin ya kuma damƙewa, cikin muryarsa dake fitar da rauninsa yace. "Ummi ciwo nakeji acikin jikina, bayana inajinsa kaman zai ɓalle, kaina ciwo yake Ummi, zazzaɓi nakeji, ko zama bazan iyaba Ummi bayana zai ɓalle." Hawayen da suka cika idanunta ne suka samu daman gangarowa, hankalinta amatuƙar tashe tace. "Saifuddeen me yasamu bayan naka? ,mekakeji ajikin ka? kafaɗamun ko wani irin ciwo kakeji sai na ƙira Dr Adnan yazo ya dubaka." Duka Ummi tayi masa tambayar tana me shafa gashin kansa. Awahalce yaja numfashi, murya asanyaye yace. "Ummy bayana." Hannu Ummi tasa ta rufe fuskarta tana sakin sheshsheƙan kuka, tare da ambaton Allah acikin ranta, tanayi masa godiya tare da rokowa ɗanta lfyar bayanshi da yaketa ce mata zai tsinke, lallai Allah ma buwayi ne gagara misali, meyin yadda yaso alokacin dayaso, ya bada alokacin da yaso, ya kuma hana alokacin da yaso, yakanyin duk yanda yaso, babu wani meyi masa shamaki, shine sarkin kowa da komai. Ahmad ne ya kamo hannun Saifuddeen ɗin ya riƙe, jin haka yasa Saifuddeen ɗin, awahalce yace. "Ahmad Bayana, inajin zogi da zafi sosai." Hawaye Ahmad ya share tare da cewa. "Sannu kaji Saifuddeen, zaka daina jin hakan insha Allah, ko wani abu ya samu bayanne?." Kai ya gyaɗa alaman "Eh." dan zuwa yanzu maganan ma daƙyar yake saboda yanda yakeji. Ummi ne cikin matsanancin tausayawa. tace. "Saifuddeen ina Zaleeha?." Dogon numfashi yaja asanyaye yace. "Zaleeha bata da lapiya Ummi, tun jiya da daddare ta suma, dan Allah Ummi kije ki taimaka mata, kada wani abu ya same ta." Idanu Ummi ta ɗan zaro cikin tashin hankali tace. "Innalillahi wa inna ilaihirraju'un, ta suma kuma?." Kansa kawai ya iya jinjina mata alaman "Eh." cikin sauri Ummi tatashi daniyar zuwa ɗakin Zaleehan. Hannun Ummin ya kamo hakan yasa ta juyo tare da zuba masa ido. Kansa yaɗan girgiza akasalance yace. "Dan Allah Ummi karku faɗawa Zaleeha cewar nafara magana, banaso tasan cewar kunnuwana sun dawo, dan Allah kumin al'kawarin cewar bazaku faɗa mata ba." Ɗan jim Ummi tayi, wani tunani dayazo ranta ne yasa ta jinjina kai, tare da cewa. "Insha Allah bazamu faɗa ba harsai ka nemi hakan." Sakinta yayi, ta fice daga cikin ɗakin da sauri, Hayatuddeen ne ya matso kusa dashi,Yanzu Hammansa najin duk wani motsi, kuma yana faɗin duk abun dake rai da zuciyarsa, me yafi hakan daɗi da farinciki awajensu? farinciki, lafiya, da kuma jin daɗin Saifuddeen shine nasu baki ɗaya. Raleeya kuwa tana fita daga ɗakin, da gudu ta haura sama, wayarta ta ɗauka hannunta har rawa yake wajen dannawa numbern Adda Rahama ƙira. Bugu biyu kuwa Adda Rahama ta ɗauka, kuka me haɗe da Dariya Raleeyan tasa, jin haka yasa Adda Rahama dake zaune miƙewa tsaye, hankalinta ne yasoma tashi jin kukan Raleeya'n, cikin ɗan tashin hankali tace. "Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un, lafiya kuwa Raleeya, meyake faruwa?." Ɗan tsaida kukan Raleeya tayi, murya na rawa tace. "Adda Rahama, ranan yau takasance mana rana mafi al'barka agaremu wanda bazamu taɓa mantawa da ita ba, Adda Rahama kunnuwan Hamma Saifuddeen sun buɗu, yanzu yanajin duk abun da mutum zai faɗa, haka kuma idan kaƙira sunansa zai amsa, Adda Rahama Hamma Saifuddeen ya warke daga cutan kurumta, yanzu yazama mutum me lafiya ji da magana." Wani irin shock Adda Rahama taji ajikinta, sosai maganan ya daki zuciyarta, saboda abune wanda bata taɓa zato ko tsammani ba, tasan tabbas Raleeya bazata taɓa yi mata wasa ƙo ƙarya akan irin wannan babban al'amarin ba. Samun kanta tayi itama da fashewa da kuka, kasa cewa komai tayi, haka tayi wurgi da wayan nata, da gudu ta nufi falo inda Dr Adnan ke zaune. Tana isa falon kuwa ta faɗa jikinsa, tare da sakin wani sabon kuka. Hankalin Dr.Adnan ne ya tashi, ɗagota yayi cikin kulawa yace. "Subahanallahi lafiya kuwa me ya faru?" Kanta ta shiga jinjina masa, cikin kuka me ɗauke da murmushi tace. "Ya Adnan Kunnuwan Saifuddeen sun buɗe, Saifuddeen ya fara jin magana da yin magana." Idanu Ɗr Adnan ya ɗan zaro cikin yanayin mamaki haɗi da kaɗuwa yace. "Kinsan me kike faɗi kuwa Rahama, Saifuddeen ya fara jin magana fa kikace?". Kanta ta jinjina masa, tare da ɗan sharce hawayen farin cikin dake kan fuskarta, cikin farinciki tace. "Eh Ya Adnan wallahi dagaske yanzu Raleeya ta ƙirani tana kuka take faɗamin". wani irin matsanancin farinciki ne ya lulluɓe zuciyar Dr Adan jawo Adda Rahma'n jikinsa yayi tare da rungumeta ƙam, take suka shiga yiwa Allah godiya. miƙe Ya Adnan ɗin yayi tare da mikar da ita cikin tsantsar jin daɗi yace. "Maza tashi muje gidan Ummi'n, tashi da sauri mu tafi". cikin farinciki kuwa ta miƙe ɗaki tashiga ta ɗauko mayafinta, Shi kuwa Ya Adnan miƙewa yayi, zuciyarsa cike da farinciki, ya nufi ɗakinsu Faruq yana shiga ya kamo hannun Farouq da kuma Adam tare da cewa. "Yaran kirki kuzo mu tafi gidan Ummi". Cikin Mamaki Faruq ya kalleshi tare da cewa. "Daddy da sassafen nan". Kai ya gyaɗa mishi tare da cewa. "Uncle Saifuddeen ne ya worke shi zamuje mu dubi". Wani irin zabura sukayi a tare tare da cewa. "Dady ya worke? yana yanaji? kuma yana magana? da tafiya?". Cikin sauri Ya Adnan yace. "Ku dai kuzo muje". aifa tuni sunyi gaba, Adda Rahma kuwa tana fitowa suka ɗunguma zuwa mota. Raleeya kuwa tana jin Adda Rahama ta katse wayan, numbern Raihana ta nema, wayar bata wani jima tana ringing ba, Raihanan ta ɗauka, kaman yanda Raleeya ta sanarwa Adda Rahma muryarta na rawa, haka ma ta sanarwa da Raihana, kusan sumewa Raihana tayi saboda tsananin mamaki da kuma shiga shock, sosai taji abun wani iri acikin kunnuwanta, saboda abune da bazasu taɓa zato ba, duba da irin yanda aka kwashe tsawon shekaru baya ji ba kuma ya magana, kuka ta fashe dashi, dan takasa jurewa bare ita dama saurin kukane da ita, ji take kaman tayi tsuntsuwa ta ganta acikin garin Gombe, Sameenu dake zaune agefenta, wanda shima yaji komai ne ya jawota ya rungumeta ƙam acikin jikinsa, shi kansa saida idanunsa suka kawo ƙwalla, sosai shima yaji hankalinsa ya taho Gombe, take ya miƙe cikin kula ya janyeta daga jikinshi cikin tsananin farin ciki yace. "Zauna Ummu Affan, bari yanzu inje airport inda in bincika man in akwai jirgin da zai tafi Gombe, yau ko gobe zamu taho Gombe'n. Cikin tsananin jin dadi tace to. Kana ta kuma jawo wayar ta kira Raliya kan zata ce mata ta haɗata da Hammansun taji muryanshi to kuma wayar Raliya sai tana sa mata line busy dole ta haƙura. Raleeya kuwa suna gama waya da Raihana, numbern Bappa Ali ta dannawa ƙira, yana ɗagawa taji wani sabon kuka yazo mata, saboda jin Bappa Alin suke kaman Babansu mahaifi, hankalin Bappa Ali ne ya tashi sosai, jin yanda muryan Raleeyan ke rawa, cikin nuna damuwarsa yace. "Raleeya lafiyanki kuwa, me yake faruwa? Meya samu gidan?." Ɗan jan sheshsheƙa tayi murmushi ne kuma yazo mata, cikin zumuɗi tace. "Bappa Ali kunnuwan Hamma Saifuddeen sun buɗu, yanzu Hamma yanajin magana kuma yana iya mayarwa." amatuƙar ba zata Bappa Ali yaji sauƙar maganan Raleeyan acikin kunnensa, wani irin farinciki ne yaji ya lulluɓe zuciyarsa, irin wanda bai taɓa jiba a rayuwarsaba ko randa aka haifa mishi Dady baiji wannan farin cikinba, Idanunsa ne suka ciko da ƙwalla, jiyayi gaba ɗaya jikinsa yayi, sanyi, cikin ƙarfin guiwan da ya samu kansa aciki, yace. "Alhamdulillah, Allah abun godiya. Tabbas dama idan da rai to tabbas da rabo, sannan ba acire rai da ni'ima haɗi da kyautar Allah, ni dama tun can bancire rai da cewar Saifuddeen bazai sake ji ko magana ba, tunda dama ciwo ne daya sameshi a sama, bawai da shi aka haifesa ba. Alhamdulillah Raliya mun godewa Allah mai rayawa mai kashewa mai badawa mai hanawa mai cuta da waraka". Sosai ya nuna farincikin sa akan hakan, har ma yace gashinan zuwa Gombe'n, dan idan ba zuwa Gombe'n yayi ba, kwata-kwata bazaiji zuciyarsa ta gamsu ba. Suna gama waya da Raleeyan ya shige cikin gida dan ya faɗawa Aunty Meena, fuskarsa cike take da fari'a, kallo ɗaya zaka masa ka fahimci cewa yana cikin matsanancin farinciki. Kai tsaye makullin matarshi ya ɗauka wacce Baga daɗe da saya mishi ita kuma hannunshi bai gama faɗawa a tuƙin sosaiba. Kai tsaye unguwar Sirankiyo ya nufa gidan ƙanwarsa Goggo Dada mahaifiyar Ahmad, koda taji wannan dadɗan labarin da sanyin safiya cewa tayi ƙafarshi ƙafarta da ita zaije. Acan ɗakin Hayatuddeen kuwa, Ahmad ne ya ƙira Ishaq ya faɗa masa buɗuwan kunnen Saifuddeen ɗin, sosai Ishaq ya shiga shock dajin haka'n, lokaci ɗaya kuwa ya zube akan guiwowinsa inda yayi sujjada, tare da yiwa Allah godiya, sannan ya fashe da kukan farinciki, wanda shi dama yanaji ajikinsa cewa, watarana Allah zai dubi Saifuddeen ya yaye masa koda ɗaya daga cikin larurorinsa, kukan farinciki yayi sosai cikin gida ya shiga ya sanarwa Ummanshi da Babansu sosai sukayi farin cikin wannan labarin inda shima sukayi mishi addu'ar Allah ya yaye mishi tasa larurar shima ɗin. , take kuma ya miƙe tsaye, waje ya nufa, dan so yake yaji muryan abokin nasa acikin kunnuwansa. Shi kuwa Saifuddeen har yanzu akwance yake, sai nannauyan nishi yake saki akai akai, dan har zuwa yanzu bayan nasa bai sake ba. Ummi na fitowa daga sashin nata, sukayi karo da su Adda Rahama, wanda zuwansu kenan. Cikin sauri Adda Rahama ta faɗa jikin Ummi tare da sakin kuka mai ɗauke da dariya. Saboda farinciki Ummi ma rungume Adda Rahaman tayi, cikin matsanancin farinciki Adda Rahama'n tace. "Ummi ina Saifuddeen, inason naji muryarsa, ina kuma so yaji magana ta, wanda tsawon shekara 20 kenan da ya daina jinta". Hawaye ne suka silalo daga cikin idanun Ummi, hannun Adda Rahman ta kama. cikin sanyin murya tace. "Zakiga Saifuddeen Rahama, amma yanzu mutafi zuwa ɓangaren Zaleeha, saboda Saifuddeen yace min tariga da ta suma, muje tana buƙatar taimakon mu". Idanu Adda Rahama taɗan zaro atsorace, bakinta na rawa tace. "Subahanalli Ummi me yake faruwa ne?". ɗai-dai lokacin Dr Adnan ne ya ƙaraso inda suke tsayen, cikin girmamawa ya durƙusa har ƙasa inda ya gaishe da Ummi'n, amsa masa tayi tana murmushi, cikin kulawa dan Ya Adnan kamar Nuruddeen take ganinshi cikin jin daɗin zuwansu tace. "Yauwa Adnan kaje ciki, Saifuddeen yana ta kukan cewa bayansa na riƙewa ka isa ka duba shi yana ɗakin auta". Cikin sauri Dr.Adnan ɗin yace. "To." take ya wuce sashin Ummi'n. Ummi kuwa hannun Adda Rahama ta kama suka nufi sashin Saifuddeen, dan dama Saifuddeen din yace mata Zaleehan nacan sashinsa. Gaba ɗaya hankalin Ummi, da kuma na Adda Rahama atashe yake. tun daga falo suka hango ƙofar bedroom ɗin nasa a buɗe, cikin sauri Ummi ta ƙarasa Adda Rahma na biye da ita, inda suka kutsa kansu cikin ɗakin, hango Zaleehan da sukayi nannaɗe acikin bargo ne, yasasu ƙarasawa cikin ɗakin da sauri. Hankalin Adda Rahman a tashe ta ɗan yaye bargon, tare da ɗago hannun Zaleeha'n, luuu haka taji hannun ya sake, idanu taɗan zaro, tare da kai hannunta saitin hancin Zaleeha'n, jin har yanzu bata numfashi yasa hankalinta sake tashi cikin kiɗima ta kalli Ummi data ɗan kauda kanta dan surkunta. Atsorace Adda Rahman tace. "Ummi Zaleeha fa bata numfashi, meya sameta ne?". Cikin fargaba Ummi ta janye blanket ɗin da Zaleehan ke lulluɓe dashi dan ganin akwai sutura a jikinta, idanunta ne suka sauƙa akan jinin da ya ɓata farin zanin gadon, wanda har aƙafan Zaleehan, akwai ɗigo ɗigon jini da ya bushe ajikin fatarta. Wani irin matsanancin tausayin Zaleehan ne ya daki zuciyar Ummi, har saida taji ƙwalla sun cika mata ido. Adda Rahama ma da idanunta suka sauƙa akan jinin dake jikin zanin gadon, ji tayi gaba ɗaya jikinta yayi sanyi, tausayin Zaleehan ne ya kamata, cikin sanyi hawaye na tsastsafo mata cikin ƙwayar idonta ta zauna abakin gadon tare da tallafo kan Zaleehan ta ɗaura akan cinyarta, dan dukkansu sun fahimci me ya faru da Zaleeha'n. Cikin sauri cikin kiɗima Ummi ta wuce toilet, da kanta ta haɗa wa Zaleehan ruwan wanka me zafi acikin bathtube, wanda tasan idan ta shiga zata ɗanji dama dama, saida ta haɗa komai daya dace, sannan ta fito daga cikin toilet ɗin dan tama mance a samu ta farfaɗo yafi dacewa. Haryanzu kuwa Adda Rahama na riƙe da Zaleehan, ɗan ƙaramin fridgen dake ɗakin, Ummi ta buɗe, tare da ɗauko goran ruwa, dawowa kan gadon tayi ta zauna, hannu tasa taɗan ɗago kan Zaleeha dake cinyar Adda Rahama, buɗe murfin goran tayi, tare da ɗan tsiyayan ruwan ahannunta, ɗan yayyafa ruwan tayi akan fuskar Zaleeha, waiko zata farfaɗo amma shiru, hakanne yasa zuciyar Adda Rahama soma bugu da sauri sauri, saboda tsoro. Ummi ma kanta ta tsorata da hakan, sai-dai batayi ƙasa a guiwa ba, saida tayi hakan kusan sau uku, kafun taji Zaleehan ta saki wani irin numfashi, tare da sauƙe nannauyan ajiyar zuciya. Ganin ta farfaɗo yasa su Ummi sauƙe ajiyar zuciya. Ahankali ta shiga ɗan jujjuya kanta, batare da ta buɗe idanunta wanda sukayi nauyi haɗi da kumburi, cikin muryarta da ta dashe wanda ko fita da kyau batayi, amatuƙar wahalce batare da ta dawo cikin hayyacinta ba tace. "Dan Allah Hamma Saif kayi haƙuri, zafi nakeji zan mutu, wayyo Allah na Hamma Saif kayi haƙuri dan Allah zafi....". Wani irin kuka ta fashe dashi me tsuma zuciya, still bata buɗe idanunta ba. Matsanancin tausayinta ne ya cika zuciyar Ummi, ahankali cikin sassanyar murya tace. "Zaleeha, buɗe idanunki kinji, ba Hamma Saif ɗinki bane nice Umminkune, buɗe idanunki kinji." Jin muryan Ummi acikin kunnuwanta, yasa ahankali taɗan soma bude idanunta wanda sukayi dishi-dishi, suka kuma kumbura kaman wanda ta yi sati guda tana kuka. Ganin Ummi yasa ta faɗa jikinta tare da ƙanƙameta ƙam, sosai ta fashe da wani irin kuka mai taɓa zuciya dan gani take kamar zai sake zuwa ya danneta. Bayanta Ummi ta soma shafawa, cikin tausayawa tace. "Ya isa hakanan yi haƙuri ki daina kukan kinji, sannu ko." Kanta ta shiga girgizawa, dan bazata iya tsaida kukan nata ba, saboda wani irin ciwo da zafi da takeji aƙasanta, ga kuma wani irin zazzafan zazzaɓin da lokaci ɗaya ya sauƙar mata, Ummi ne ta dubi Adda Rahma, wanda tausayin Zaleehan yasa yanayinta ya sauya, idanunta duk sun kawo ruwa. Cikin sanyi Ummi tace. "Nahaɗa mata ruwan wanka, kamata kuje toilet, dan Allah Rahma kiyi mata duk wani abun daya dace duk wani abu da kika san zaki iya yiwa Raliya ko Raihana kiyi mata". Sai ta kuma kalli Zaleeha cikin tausayawa tace. "Daure Addanku ta taimaka miki,ki ɗauketa kamar Adda Maryam ɗinki kinjiko." Kai Zaleeha ta gyaɗa cikin sanyi da zubda hawaye tayi ƙasa da kanta dan azabar kunyar Ummi da takeji. Ita kuwa Ummi murya a tausashe tace. "Bari naje nasa anemo mata magani, dannaji jikinta da zafi kaman wuta." Kai Adda Rahama ta jinjina, cikin tausayawa ta jawo Zaleehan, da ƙyar ta iya ɗago ta, saboda yanda ta kasa tsayuwa da ƙafafunta, Cikin lallami Adda Rahama ta jata zuwa cikin toilet ɗin dake cikin ɗakin. Dr Adnan kuwa koda ya isa ɗakin Hayatuddeen, duƙufa yayi akan Saifuddeen wanda zuwa yanzu bayan nasa ya sake riƙewa sosai. Hankalin Dr Adnan ne ya tashi saboda yanda yaga jikin Saifuddeen ɗin, ya sake ɗaukan zafi. Hayatuddeen kuwa ganin Dr Adnan yazo ya sa ya tashi ya fita daga ɗakin, zuciyarsa cike da murna ya ciro wayarsa daga cikin aljihu, inda ya dannawa numbern Zakariyya ƙira. Wayar bata wani jima tana ringing ba Zakariyya ya ɗauka. Murmushi Hayatuddeen yayi, cikin jin daɗi yace. "Zakariyya kunnuwan Hammana sun buɗu, Hammana ya warke daga cutar kurumta Zakariyya". Jin maganan Hayatuddeen ɗin yasa jikin Zakariyya ya ɗauki rawa, samun kansa yayi cikin wani irin farin ciki, dan sosai abun ya taɓa zuciyarsa, cikin matsanancin farinciki yace. "Masha Allah Alhamdulillah, Hayatuddeen yanzu Hamma Saifuddeen najin magana kenan?" Cikin matsanancin farinciki Hayatuddeen yace. "Eh Zakariyya, ni narasa inda zansa kaina ma saboda farinciki, yanzu Hammana ya zama kaman kowa, saidai kuma dan Allah kada ka faɗawa kowa hakan, dan Hamma Saifuddeen da kansa yace bayason Adda Zaleeha ta sani, wanda kuma bansan menene dalilinsa nayin hakan ba." Kai Zakariyya ya jinjina, cikin tsananin jin daɗi yace. "Insha Allah bazan faɗa mata ba Hayatuddeen, anjima kaɗan nima zanzo, bazan iya jurewa ba Hayatuddeen zanzo naga Hamma na kuma ji muryarsa." Kai Hayatuddeen ya jinjina, tare da cewa. "Shikenan Zakariyya sai kazo, saidai kuma tun ɗazu Hamma Saifuddeen ke cewa bayansa nayi masa ciwo, amma yanzu Ya Adnan yazo yana dubashi." Cike da zumuɗi Zakariyya yace. "Ganinan zuwa Hayatuddeen, kuma insha Allah komai zai dai-da-ita." Acan sashin Saifuddeen kuwa, Ummi naganin shigansu cikin toilet, ta fita daga cikin ɗakin, saboda tanaso taje ta duba Saifuddeen. Adda Rahama kuwa cikin kulawa haɗi da lallami tace da Zaleeha ta cire kayan jikinta, tare da miƙo mata towel tace ta ɗaura kana ta juya mata baya dan kauda idonta kanta, da ƙyar ta iya cire kayan nata, sannan ta ɗaura towel ɗin cikin hikima yadda bata tsaya ba komai a jikinta ba. Da ƙyar Adda Rahama ta iya zaunar da ita acikin ruwan zafi'n, wani irin narkekken ƙara ta sake, saboda yanda taji ƙasanta na mata zafi da raɗaɗi kaman an watsa mata barkono, kuka ta saka tana ɗan yayyarfa hannunta. Cike da tausayinta Adda Rahama tace "Sannu ko kiyi haƙuri kinji, idan ruwan ya gama ratsaki, insha Allah zaki ɗanji sauƙi." Asakalce ta ɗan jinjina kanta, duk da zafin da takeji haka ta ɗan daure ruwan ɗumin ya ratsa cikin jikinta, saida ruwan yaɗan fara salancewa, sannan Adda Rahama ta sake zuba mata wani ruwan me ɗumi, tana sake shiga ruwan kuwa gumi ya fara fesowa daga jikinta, taji zafi sosai saidai bakaman na farko ba. Saida Adda Rahama tasa mata ruwan ɗumi sau uku, sannan ta fita inda tace mata taɗan ƙoƙarta tayi wanka tsarki. Ummi kuwa daga ɗakin kaitsaye sashinta ta wuce, anan ɗakin Hayatuddeen tasamu Dr Adnan ya saka Saifuddeen ɗin agaba, yana ta faman auna jikinsa. Cikin kulawa, akuma sanyaye tace. "Dr Adnan ya jikin nasan dai? Babu wata matsala kam dai ko?". Ɗan numfasawa Dr Adnan yayi, haɗe da cewa. "To jikin nasa dai da sauƙi, za 'ace, yanzu so nake naji problem ɗin nasa, dan ina tunanin ma saina ƙira Dr.Aleeyu na faɗa masa ko akwai shawarwarin da zai bamu". Kai Ummi ta jinjina, tare da sakin wani gauron numfashi, ganin yanda Saifuddeen ɗin keta cije lips ɗinsa ne, yasa ta juyawa ta fice daga cikin ɗakin, kaitsaye kitchine tawuce, dan tanaso taɗan haɗawa Zaleeha tea. Zaleeha kuwa da zazzaɓi yayi mata wani irin mummunan kamu, da ƙyar ta iyayin wankan tsarki da kyar ta ɗaura towel a jikinta kana ta zauna bakin baf ɗin, akasalance da muryarta wanda bata fita ta shiga ƙiran sunan Adda Rahama, Adda Rahama wanda ta gama kimtsa kan gadon da suka ɓata, jin Zaleehan na ƙiranta ne yasa ta nufi banɗakin, tana shiga Zaleehan ta miƙo mata hannu, cikin sheshsheƙan kuka tace. "Ki riƙeni Adda Rahama jiri nakeji, cikin jikina da ƙafafuna duk ciwo sukemin". Cikin tausayawa Adda Rahama ta riƙota, haɗe da cewa. "Sannu kinji kiyi hakuri kinji, Ummi zata kawo miki magani zai daina insha Allah." ahaka suka fito daga cikin toilet ɗin, duk taku ɗaya da Zaleehan zatayi saita rumtse idanunta, saboda yanda takejin zafi aƙasanta. Akan gado Adda Rahama ta zaunar da ita, sannan ta fice daga cikin ɗakin, kaitsaye tanan cikin falon Saifuddeen ɗin ta samu shiga sashin Zaleeha, direct ɗakin Zaleehan ta wuce, wata ƴar doguwar riga marar nauyi tare da hijab Adda Rahama ta ɗauko mata, sannan ta dawo ɗakin. Akwance tasamu Zaleehan tana ta faman sakin ajiyar zuciya akai akai alamun tasha kukanta daren jiya ta ƙoshi. Tashinta Adda Rahama tayi, tare da bata rigan tace ta saka, akasalance haka ta saka rigan, sai faman sakin sheshsheƙan kuka take. Hijab ɗin Adda Rahama ta sanya mata sannan tace da ita, ta tashi tayi Sallah. Haka kuwa tayi sallan tana sakin sheshsheƙan kuka, ko tsayuwa mekyau bata iyawa, dole saida ta jingina, tana idar da sallan kuwa ta fashe da kuka, dai-dai lokacin Ummi ta shigo cikin ɗakin hannunta ɗauke da cup ɗin tea, wanda ta haɗa sa me kaurin gaske. Ganin Zaleehan na kuka yasa ta ƙaraso cikin ɗakin da sauri. Zama tayi akan gado, tare da jawo Zaleehan ta zaunar da ita, cikin kulawa tace. "Yi haƙuri kinji, ga tea nan na haɗo miki, kisha nasan zaki ɗan samu ƙarfin jikinki." Awahalce ta girgiza kanta, cikin sheshsheƙan kuka tace. "Ummi bazan iya sha ba, banajin dadin bakina, kuma jiri nakeji, kaina ciwo yakemin." Cikin tausayawa haɗi da lallashi, Ummi tace. "To naji kiyi haƙuri kisha kinji, idan kika ɗansha saina kawo miki magani." Adda Rahama ne ta karɓi kofin tea ɗin takai kan bakin Zaleehan, ashagwaɓe hawaye na tsiyaya daga cikin idanunta haka ta ɗansha tea ɗin, ko rabin cup ɗin bata shaba, ta koma ta kwanta, jikinta sai rawan sanyi yake saboda zazzaɓi, ganin hakane yasa Ummi rufa mata blanket, tare da gyara mata kwanciyanta. Adda Rahma kuwa ganin ta konta yasa ta fita da sauri dan tana marari da begen jin muryar ƙanin nata kai tsaye ɗakin Hayatuddeen ta nufa. Acan ɗakin Hayatuddeen kuwa Raleeya ce taturo ƙofar ɗakin ahankali ta shigo. Ɗan tsaye tayi tana kallon Dr Adnan wanda tazo da niyar gaidashi ganin hankalinshi kab na kan Saifuddeen ne yasa ta tsaya kallonshi shida Ahmad wanda suka saka Saifuddeen ɗin agaba, Dr Adnan ne yake ta faman auna tempreture'n Saifuddeen ɗin. Jin motsin shigowa ɗakin, yasa Dr Adnan juyowa , ganin Raleeya tsaye ya sashi cewa. "Taɗan basu guri yanaso ya duba Saifuddeen ɗin." Babu musu kuwa ta fita, ganin ba abun da zatayi ne yasa ta wuce kitchine dan ɗaura musu break fast, ahanzarce kuwa ta soma haɗa musu break fast ɗin asauƙaƙe, wanda tasan bazai ɗauki lokaci ba. Adda Rahma kuwa kai tsaye ɗakin Hayatuddeen ɗin ta nufa dan su Faruq sunce mata can yake, da sassarfa ta ƙarasa cikin ɗakin, tana cewa. "Salamu alaikum, ina ɗan uwana yake?". Murmushi Ahmad yayi tare da cewa. "Gashi nan Adda Rahma yana ta mana raki". Dai-dai lokacin ta ƙarasa cikin ɗakin da sauri ta iso gabanshi har tana gogan jikin ya Adnan cikin kaɗuwa tace. "Saifuddeen kayi magana mana inji". Wani irin murmushin ƙarfin hali yayi dan ciwon da yakeji, murya a sarƙafe yace. "Na'am Adda Rahma,". wasu irin zafafan hawayen farin cikine suka wonke mata ido cikin ɗaga sauti tace. "Alhamdulillah, Allah mun gode maka da wannan ni'imar ya Allah ka ƙara mana nima da samun lafiyar sawunshi". Amin Amin sukace baki ɗayansu, kana Dr Adnan yace to ta matsa mishi yayi aikinshi, cikin jin daɗi ta nufi kitchin inda take jiyo muryar Hammanshin da Raliya murna sukayiwa juna kana ta fita ta koma side ɗin Saifuddeen ɗin wurin Zaleeha. Dr Adnan kuwa ganin Rahama ta fita, ya sashi ɗan ɗago kansa ya dubi Saifuddeen ɗin, cikin kulawa yace. "Nakasa gano sanadin tashin ciwon bayankan nan tunda babu cikakkun na'urorin a wurina wanda zanyi bincike dasu, ka faɗi akan bayan naka ne? ko kuma wani abu ne ya samu bayan?." Ɗan lumshe idanunsa, yayi cikin sassanyar murya yace. "Ba faɗuwa nayi ba." Idanu Dr Adnan ya zuba masa, saida ya nazarce sa naɗan wasu sakanni kafun yace. "To meya faru?." can cikin ƙasa da murya yace. "disvirgin ɗin Zaleeha nayi, tun alokacin naji bayan ya riƙe yana min ciwo sosai. please Ya Adnan mu koma india, inajin bayana kaman zai ɓalle." Ajiyar zuciya Dr Adnan ya sauƙe, dan sai yanzu ne ya gano cewa, saboda Saifuddeen ɗin yayi sex da Zaleeha ne hakan ya faru. Ahmad kuwa dariyar mugunta yayi tare da cewa. "Hege uban ƴan longomi, wani ne ya aikeka ka jogalo ɓalgaceccen ƙugunka kazo kana mana raki da sakalci ji yadda kuka gigita mana Ummi kaida matarka mai shegen raki ko kunya bakwai". Ya Adnan kanshi saida yayi dariya, shi kuwa Saifuddeen fuska ya tsuke. Cikin nutsuwa motar Ameena ta kutso kai cikin gidan, wanda dawowanta daga wajen aiki kenan, anutse ta gama dai-dai-ta parking ɗin motar, saɓa Adeel akafaɗanta tayi, sannan ta buɗe motar ta fito, kaitsaye sashin Ummi ta nufa, duk da cewar agajiye takejin kanta, amma ta riga da ta saba, kullum idan ta dawo sashin Ummi take fara zuwa. Da sallama ɗauke abakinta ta shiga cikin falon. Shigarta kuwa yayi dai-dai da fitowan Raleeya daga kitchine. Ganin Ameena yasa Raleeya ƙarasowa gareta da gudu, faɗawa jikinta tayi ta rungumeta ƙam, fuska ɗauke da mamaki Ameena tace. "Raleeya farincikin me kikeyi haka?." Murmushi me kama da dariya, Raleeya tayi, cike da farinciki tace. "Ranan yau ta kasance ranar farin cikinmune baki ɗaya mu yau ranace mafi kyau acikin rayuwarmu, bansan tayaya zan nuna miki farincikin danake ciki ba Aunty Ameena". Idanu Ameena ta zuba mata, hakanan taji zuciyarta na bugawa, cike da zaƙuwa tace. "Meyake faruwane Raleeya, dan Allah faɗamin, inajin kirjina na bugawa da sauri-sauri" Murmushi Raleeya tayi, tare da yi mata nuni da ɗakin Hayatuddeen, cikin farinciki tace. "Kishiga ɗakin Hayatuddeen Hamma Saifuddeen nacan." Jin haka yasa Ameena cikin sauri ta nufi ɗakin Hayatuddeen ɗin. A ƙarfi ta tura ƙofar ɗakin ta shiga. Jin motsin shigowan mutum yasa su dukansu suka kai kallonsu ga ƙofan shigowa ɗakin. Idanu ta zubawa Saifuddeen dake kwance wani irin tsorone ya rufeta ganin yadda yake konce to farin cikinme Raliya keyi bata bayan kuma taga alamun mijinta ba lfy, bata kao aya a tunanin nataba taga, yana miƙo mata hannu, cikin sassanyar muryarsa mai nuna baida lfy yace. " _Aminatu_ bani Adeel." Kamar amafarki haka Ameena taji sautin muryarsa acikin kunnuwanta, a razane taɗan zaro idanunta, sosai jikinta ya ɗauki rawa, bakinta na rawa haka ma muryarta tace. "Abban Adeel, kaine kake magana ko kuwa gizo ido da kunnuwana suke yimin." Idanunsa yaɗan lumshe tare da jinjina mata kai, cikin son bata ƙarfin guiwa yace. "Ni ne Aminatu, ba gizo kikeji ba." Cikin wani irin yanayin farin ciki da wani irin gudu mai kamar sassarfa ta ƙaraso cikin ɗakin tare da faɗawa jikinsa ta ruggumeshi gam-gam kamar mai tsoron a kwace mata shi, cikin tsananin farin ciki tasaki wani irin kukan farinciki, sam ta ma manta da su Dr.Adnan dake cikin ɗakin. Hannunshin yasa ya dai-dai ta kanta dake kanshi cikin sanyin murya tace. "Aminatu Zaki ƙara ɓalle bayan ki rasa na yin lilo gaba". Cikin wata irin yar salama da jin daɗi tasa hannu ta shafi gefen fuskarsa, cikin matsanancin farinciki tace. "Alhamdulillah Ya Allah, Alhandulillah." Murmushin ƙarfin hali yaɗan sakar mata, tare da sanya hannu ya amshi Adeel, dake ta dariya yana wutsil-wutsil da ƙafafunsa kamar yasan farin cikin da sukeyi. Rungume yaron nasa yayi, yanajin wani matsanancin farinciki acikin ransa. Ameena kuwa ɗan sharce hawayen dake cikin idanunta tayi, tuna cewa su Dr Adnan na ɗakin yasa ta ɗan janye jikinta baya, tare da cewa. "Abban Adeel yaushe ka fara magana?." Kasa amsa mata yayi saboda yanda yaji bayansa na wani irin duka, idanunsa ya rumtse da ƙarfi sosai, Dr Adnan ne yaɗan riƙe masa hannu, tare da zaro wayarsa, numbern Dr Aleeyu ya laluɓo, sannan ya danna masa ƙira. Bugu ɗaya kuwa ya ɗauka. Bayan sun gaisane Dr Adnan ya ɗan gyara zamansa. Cikin nutsuwa yacewa Dr Aleeyu. "Sir jikin Saifuddeen ne fa ya tashi sosai fa, amman kunnuwansa kuma sun buɗu yanzu duk wani motsi yanaji, sai-dai amma tun ɗazu yake ta complain cewar bayansa ya riƙe, yanzu haka ko zama da kyau baya iyawa, nakasa gano kan matsalan nasa, dan harma yace wai ko zamu koma India ne." Sosai Dr.Aleeyu yaji daɗin buɗuwar kunnuwan Saifuddeen ɗin, saidai jin wata matsala da ta kunno kai duk sai yaji babu daɗi acikin ransa, sai-dai yasan hakan ma wani matakin nasara ne a jinyar tasa dogon numfashi yaja cikin kulawa yace. "Ai dama lokacin komawarsa india yayi harma ya wuce, bansan me yasa bayason komawa asibiti ba, lalle ya zama dole amaidashi india, dole anjima zan biyo jirgi nazo, zan taho da wasu allurai da magunguna wanda xasu ɗan rage masa pain kafin a samu wucewa dashi India, ka gayawa Ahmad ya fara nema musu damar tafiya tun daga yanzu yayi musu bukin ta online." Cikin jin daɗin hakan Dr. Adnan yace. "Okay Sir shikenan sai kazo". da haka sukayi sallama, yana ajiye wayar kuwa Ummi ta shigo cikin ɗakin. Ganin Ummi yasa Ameena tashi da sauri ta ƙarasa jikin Ummin cikin tsananin farinciki tace. "Alhamdulillahi Ummi, kunnuwan Abban Adeel sun buɗe ya fara jin magana, Alhamdulillah Ummi, tabbas Allah abun godiya ne." Kai Ummi ta jinjina tare da cewa. "Tabbas Ameena Allah abun godiyane, gashi cikin ikonsa ya buɗe masa kunnuwansa." Murmushi Ameenan tayi tana kallonsa, ji take kaman ta maidashi cikin jikinta tsabar murna. Dr Adnan ne yayiwa Ummi bayanin yanda sukayi da Dr Aleeyu, sosai Ummi taji zuciyarta, ta gamsu da zuwan Dr Aleeyun saboda, yanda taga Saifuddeen nacije laɓɓansa, tasan yanajin ciwo sosai. Ameena ne ta kalli Umm'in, cikin kulawa tace. "Ummi ina Zaleeha?" Ɗan jim Ummi tayi cike da tausayawa tace. "Zaleeha bata da Lafiya, yanzu haka tanacan sashin Saifuddeen, akwance sai rawan sanyi take, zazzaɓi ne me zafi ya sauƙar mata, so nake idan Dr Adnan ya gama da Saifuddeen, sai muje yaɗan duba ta." Idanu Ameena ta zaro tare da cewa. "Subahanallah, Allah sarki bari naje na duba ta, ko akwai wani taimakon da zan iya bata". Kai Ummi ta jinjina, sannan Ameenan ta juya nufin fita, sai kuma ta tsaya jin an riko hannunta ganin Saifuddeen ne yasa ta matsoshi cikin lumshe ido yace. "Aminatu Kada ki ce mata kunnena ya buɗu kuma ina iya mgna, kinji ko Ummu Adeel". Cikin jin daɗin yadda yake yawan kiranta da yadda yake kiranta Aminatu kana da mmki ta gyaɗa kai a ranta tace. "To meyasa za'a ɓoye mata wannan abin farin ciki, to ko dan bata da lfy ne". Kai kawai ta gyaɗa kana ta juya ta fita daga cikin ɗakin. Kamar yanda Ummi ta faɗa mata kuwa, kaitsaye sashin Saifuddeen ɗin ta wuce, ganin bata ganta afalo ba, yasa tayi tunanin cewa tana ɗaki. Tana shiga kuwa ta samu Adda Rahama zaune agefenta, dan har yanzu Zaleehan bata daina sakin sheshsheƙan kuka ba. Ƙarasowa cikin ɗakin tayi, cikin kulawa ta zauna abakin gadon tare dakai hannu taɗan taɓa wuyan Zaleehan, jin jikin Zaleehan zafi zau yasa tace. "Subahanallahi Ammin Adeel sannu ya jikin naki?". Kai kawai Zaleeha ta iya jinjina mata dan batajin zata iya wani dogon magana. Ɗan sake taɓa jikin Zaleehan tayi, tare da duban Adda Rahama, tace. "Adda Rahama miyene yake damunta bayan zazzaɓi?." Ajiyar zuciya Adda Rahama tayi, asanyaye tace. "Tace min tanajin jiri da kuma ciwo acikin jikinta, danko tafiya ma batayi da kyau, nadaiyi mata sit bath, amma gashi nan dai sai rawan sanyi take." Wani irin ƙaton abune ya daki ƙirjin da ran Ameena, har saida taji kanta yaɗan juya mata duhu ya gilmawa ganinta, take ta gano matsalan Zaleeha'n, murmushi taɗanyi tare dayin ƙasa da kanta tana jin wani sassanyan abu a ranta da zuciyarta da sauri ta katse shaiɗan da yin tasbihi, gaba ɗaya ji tayi jikinta yayi sanyi, sai-dai kuma yauɗin ranace ta daban agaresu ranace ta farin ciki su budurcin Zaleeha ya zame musu abin al'fahari tunda sanadin ƙarɓarsa a samu gagarumar nasara a rayuwar mijinta abin soyuwa. Wayarta ta ciro inda ta laluɓo numbern wata ogarsu Dr Fateema, wanda take nan kusa dasu dan gidanta baida wani nisa, Dr Fateeman na ɗagawa, ta matsa ɗan gefe tare dayi mata bayani, kan cewa suna da patient agida, sannan tayiwa Dr Fateeman bayani, kan cewa ita bazata iya aikin ba. Da yake Dr Fateema'n, macece mai sauƙin kai hakan yasa tace wa Ameenan gatanan zuwa, dan dama tana gida bata fita ba. Babu wani jimawa kuwa, saigata tazo, ganin yanda jikin Zaleehan yayi zafi sosai yasa tace su bata waje, zata dubata. Babu musu kuwa Adda Rahama da Ameena suka koma falo. Duba Zaleehan tayi, sosai, ganin babu rauni sosai aƙasan nata yasa ta bata wasu magunguna tasha, wata alluran kashe zafi da zogi tayi mata, sannan ta ɗaura mata drip tare dasa alluran zazzaɓi. Cikin abun da baiwuce 10 minute ba bacci ya ɗauki Zaleeha. Dr Fateema na fitowa daga ɗakin su Ameena suka nufota cikin sauri. Ameena ce tace. "Dr Yajikin nata?." Ɗan murmushi Dr Fateema'n tayi, tare da cewa. "Ku kwantar da hankalinku, jikinta da sauƙi, dan harma ta samu bacci, kuma bawani babban damuwa bane, kunsan dama yawanci irin haka yana faruwa idan akayi dis virgin ɗin mace, mussamman idan ya zamana namijin yaje mata da ƙarfi, ko kuma manhood ɗinsa ya zamana, yafi ƙarfin privet part ɗinta, wanda sai ahankali ne kuma zata saba, thank god ma babu rauni sosai ajikinta, yanzu dai tana da buƙatar hutu, so please abarta taɗan huta." Jinjina kai sukayi su dukansu cike da gamsuwa, Ameena kuwa ido ta rumtse jin hawayen kishi zasu zubo mata a ranta tace. "Ashe da kam duk kishin banza nakeyi nagodewa Allah dayasa bai kusanceta tun ina kan jahilin kishin nanba na sani da mutuwa zanyi. Har waje kuwa Ameena ta raka Doctor ɗin. Saida taga tafiyarta sannan ta dawo gida tana tafe tana mgnar zuciya da share hawaye. "Ai kam dole taji azaba dan Abban Adeel ingarman namiji ne". Ganin Zaleehan na bacci, yasa Adda Rahama jawo ƙofan ɗakin ta rufe, sukuma suka koma sashin Ummi. Suna zuwa kuwa suka samu Raleeya ta kammala breakfast, da ƙyar Adda Rahama tasa Saifuddeen ya ɗanci wani abu acikinsa, dan yace musu ji yake bayansa na harbawa. Ɓangaren Zakariyya kuwa suna gama waya da Hayatuddeen, cikin gida ya wuce, anan falon Baba Malam yasamu Mama da kuma Mamy, harma da Ya Ahmad, anan yake sanar musu cewa, jikin Saifuddeen ɗin ya tashi. Sosai Baba Malam ya shiga damuwa, nan yace su Mama su shirya idan akayi sallan azahar zasuje su dubashi. Ameena ma ta kira Daddy ta sanar mishi batun jikin Saifuddeen kuma yace yana nan tafe gobe, hakama ta kira Mamanta ta sanar mata, inda ta haɗata da Ummi suka gaisa, ta jajanta mata jikin Hamma Saif ɗin kana tace suma in Allah ya nufa gobe zasu taho. Kusan atare motocin Su Wareesu dana Ishaq Salisu suka shigo cikin gidan. Dan dukansu Ahmad ya ƙira ya sanar musu. Koda suka shiga cikin gidan, Raleeya ce tayi musu jagora zuwa ɗakin Hayatuddeen ɗin. Lokacin da sukaji muryan Saifuddeen wanda ganinsu ne ya sashi buɗe muryarshi ya amsa Salllamarsu da ƙarfi yadda duk zasuji muryarshi ai kuwa dukansu babu wanda bai ji muryar tashiba. Hannu yasa ya kamo hannun Ishaq dake ƙoƙarin kamo nashi cikin tsanyi yace. "My Ishaq gani nan kusa da kai". Wani irin riƙo Ishaq yayiwa hannun Saifuddeen cikin tsananin farin ciki yace. "Allahu akbar Allah mai iko da girman buwaya. Buwayi gagara misali Alhamdulillah ko yanzu na mutu Allah ya cika min burina laruran Aminina sun ragu". Wani irin raunine ya baiyana a fuskar Saifuddeen murya na rawa yace. "Ni kuwa ina roƙon Allah ya aramin rai da lfy, ya nuna min lafiyarka inga kaima kana gani da idanunka". Kusan a tare Ahmad da Salisu ds Mudassir da Warisu sukace. "In sha Allah, shima Allah zai bashi lfy". Salisu kuwa tuni hawaye sun wonke mishi ido sai yake tuno irin gogormoya da suka sha shida Saifuddeen a cikin bulayin neman halal ɗinsu a lokacin badon ƙarfin imaniba sai su kauce hanya, sabida tsananin uƙubar talauci da wahalar rayuwa hannu Saifuddeen yasa yana share masa hawayenshi, shi kuwa sai maimaita kalmar Alhamdulillah yake tayi. Warisu kuwa murmushi yayi tare da cewa. "Ya Allah ka nuna mana randa zaka tsaya da kafafunka kamar yadda ya jiyar damu mgna da muryarka". Amin Amin yace kana ya kalli Salisu tare da cewa. "Haba Salisu godewa Allah zamuyi ba kuka ba". Cikin sauri duk suka rinƙa maimaita Alhamdulillah, Ahmad ne yayi dariya tare da cewa. "Daga dare ɗaya Zaleeha tayi sanadin dawo mana da bakinshi da kunnenshi, a dare na biyu kuma ƙugu kam zai ida ɓalgawacewa in mutun bai jira kanshi ba". Dariya sukayi baki ɗaya dan sun gano kurman baƙin da Ahmad ya musu, shi kuwa Saifuddeen mare ƙeyan Ahmad yayi, lokaci ɗaya kuma ya riƙe hannun Ishaq da karfi dan sarawar da yaji ƙugunshi nayi cikin dakiya yace. "To mugaye masu cewa Allah yasa ƙuguna ya ida ɓalgacewa, kunji daɗinku ya ɓalgace ɗin". Dariya sukayi baki ɗayansu. Ganin alamun yana cikin ciwo ne yasa suka sarara mishi suka koma falo. Kafun sallan Azahar tuni gidansu Saifuddeen ɗin ya cika da jama'a, ƴan uwa da abokan arziki da maƙota, harma dasu Bappa Ali da suka samu isowa, acikin gidan fuskar kowa ka kalla zaka ganta ɗauke da zallan farinciki, da kuma jindaɗi. Kusan ƙarfe 3 na yamma, su Baba Malam suka samu isowa gidan. Tarba me kyau Ummi tayi musu, inda Baba Malam yashiga har ɗakin Hayatuddeen ya gaishe da Saifuddeen ɗin. Mama ma haka ta gaishesa tana ta faman sunne kai, dan kunyansa takeji. Ahamad ne yaja Baba Malam gefe ya sanar dashi buɗewan kunnen Saifuddeen. Sosai Baba Malam yaji daɗi, sam baiga laifin Saifuddeen ɗin ba kuma da yace a ɓoyewa Zaleeha hakan, dan yasa komai Saifuddeen yana yinsane cikin hikima da kuma dalili tabbas yasan yanada dalilin da yasa yace a ɓoye matan. Jin cewar Zaleeha na kwance bata da lafiya, yasa Mamy zuwa ta dubata, Mama kam da Baba Malam basuje ba, saboda abun akwai nauyi sosai. Har zuwa tafiyansu kuwa Zaleeha bacci take batasan ma da zuwansu ba. Haka gidan nasu ya cigaba da amsan baƙi har kusan dare. Sai Bayan sallan la'asar Zaleeha ta farka daga nannauyan baccin da take. Dai-dai lokacin kuwa Adda Rahma da Raleeya suka shigo, da taimakonsu tayi wanka, dan taɗanji dama daman jikinta, sai-dai tafiyan natane har yanzu bai dawo dai-dai ba. Da taimakon Adda Rahama ta koma ɗakinta, sallan Azahar da la'asar tayi.sanna Ta kwanta. Ƙarfe biyar dai-dai Dr Aleeyu yaso daga Abuja kai tsaye gidan su Saifuddeen ɗin ya Adnan ya kawoshi, ya dubashi yayi da kyau kana yayiwa Saifuddeen allurai da kuma magunguna, ba laifi kuma yaɗanji sauƙi. Bayan sallan isha ne Ya Ahmad da Aunty Lubna suka zo suma dan dubashi da jiki Bayan sun gaishe da Saifuddeen ɗinne. Raleeya tayiwa Aunty Lubna jagora xuwa ɓangaren Zaleeha. Zaune suka sameta akan sallaya, tayi jigum, ganin Aunty Lubna yasa ta kwaɓe fuska, sai kuma ga hawaye sun soma tsiyaya daga cikin idanunta. Ƙarasowa cikin ɗakin Aunty Lubna tayi tare da zama akan wani ɗan stoll ɗin dake gefen gado, a hankali ta kamo hannun Zaleehan cike da kulawa tace. "Sannu Zaleeha ya jikin naki". Kasa amsa mata tayi, saima samun kanta tayi da ɗan jan jikinta, ta ɗaura kanta tayi akan cinyar Aunty Lubna'n, lokaci ɗaya ta kwaɓe fuska cikin zallan shagwaɓa tai rau-rau da ido. Ganin haka yasa Aunty Lubna ta ɗanyi murmushi dan tasan mai neman kukane aka jefa da kashin awaki, ahankali ta soma shafa kanta, cikin sanyi da kuma lallashi tace. "Ya isa haka Zaleeha kada kiyi kukan, ciwon me kuma yake damunki harda kuka?" ɗago kanta daga cinyar Aunty Lubnan tayi cikin naƙe murya tace. "Zafi nakeji Aunty duk jikina ciwo yake min, sabida muguntar da Hamma Saif yamin." Danne dariyarta tayi tare da cewa. "Kenan nima sai ince ya Ahmad ɗinki ma mugunta yaita min". Kai ta jujjuua tare da cewa. "Allah nasan da kinyi ta magiya da roƙon ya Ahmad ya barki yadda nai ta mishi jiya da dare nasan zai barki. Shi dai mugune, babu irin kuka da roƙon da banyi masa ba, amma yaƙi jina, zafi nakeji sosai Aunty ko tafiya mai kyau bana iyawa, gashi ma harda zazzaɓi nakeyi." Sosai Aunty Lubna ta gane sanadin ciwon Zaleeha'n, ɗan sake shafa kanta tayi. Cikin kulawa tace. "Kiyi haƙuri Zaleeha kowa ma yaji hakan, amma da sannu yake wucewa, banaji Ummi tace likita ta dubaki ba." Ashagwaɓe ta gyaɗa kanta, cikin lumshe ido tace. "Amma Aunty Lubna meyasa zaimin haka, yanzu fa ko ƙarfi banaji ajikina." Ɗan guntun murmushi Aunty Lubna'n, tayi, tare da cewa. "To yanzu ai yayi mgnin guduwa da bakin tsiwa. Ai haƙuri kawai zakiyi , shima dakike magana akai ai ba daɗi yakeji ba, yanzu haka ma fa shi mukazo dubawa, jikinsa babu daɗi, ciwonsa ya tashi, ko ɗazu ma su Baba Malam harma da Mama sunzo dubashi." Idanunta ta zaro waje, cikin yanayin damuwa da fargaba tace. "Bashi da lafiya kuma Aunty, to me ya sameshi?." "Bayansa ne ke ciwo, dan ma naji ance sai an fitar dashi India, yanzu dai ki lallaɓa kije ki duba shi, yana can sashin Umminsa." Hakanan taji wani irin matsanancin tausayinsa ya dirar mata azuciya, take taji zuciyarta ta karye taji tana son ganin shi. Miƙewa tsaye Aunty Lubna tayi tare da cewa. "Ni kam zan wuce, dan tare ma muke da Yayanki, nace bari na shigo naɗan dubaki." Hannun Aunty Lubnan ta kama sannan ta miƙe tsaye, cikin yanayin shanye ciwon da takeji, tace. "Aunty muje na gaishe da Ya Ahmad, tunda dai yaƙi shigowa." A cikin ranta kuwa cewa tayi. "Daga nan zan ganshi ai, in banda Hamma Saif kai kamin fyaɗe kuma kaima wai baka da lfy mu duka mun zama majinyata". Murmushi Aunty Lubna tayi, tace. "Baƙin shigowa yayi ba, suna tare da me sunansa ne." (Wato Ahmad mijin Raleeya.) Kaita ɗan jinjina, sannan ta kama hannun Aunty Lubna'n, haka suka fito daga cikin sashin nata, ahankali take tafiya, sai faman ciccije baki take, kasancewar tana ɗanjin zafi acikin jikinta. A compound ɗin gidan, suka iske Ya Ahmad da kuma Ahmad atsaye, suna ɗan tattaunawa, wanda kuma duk akan matsalan Saifuddeen ɗinne, kana anan Ya Ahmad ke ce mishi suma gobe zasu koma Abuja. Ganin Zaleeha yasa Ya Ahmad ɗin sakin murmushi, cikin kulawa yace. "Ha'a marar lafiyance da kanta, har kin warke kenan?." Ɗan shagwaɓe fuska tayi tare da turo ɗan ƙaramin bakinta gaba, asakalce tace. "Nidai Ya Ahmad nayi fushi, kazo har gidan nan shine kuma sai kaƙi zuwa sashina, bayan kuma kasan cewa bani da lafiya." Murmushi yayi tare da kamo hannunta, ya shafi gefen fuskarta cikin kulawa yace. "Sannu ko, Mangana yanzu ya jikin naki? Ko dai yanzu kam Mangan Hamma Saif ne?." Jin yace mata manga, Hamma Saif ta sake shagwaɓe fuska, cikin mamul mamul da baki tace. "Da ɗan sauƙi kaɗan." ɗan murza hannunta yayi tare da cewa. "Good Allah Ya Ƙara sauƙi." Kanta taɗan jinjina sannan tace Ameen. Bayan motarsa ya buɗe inda ya ɗauko wata leda miƙa mata yayi, yana murmushi yace. "Gashi dama saboda ke kaɗai kawai na saya, ki kula da kanki kinji Shagwaɓaɓɓiyar Mijinta." Amsan ledan tayi tana murmushi, jin yace da ita wai Shagwaɓaɓɓiyar mijinta, yasa tayi saurin basa baya, wai ita adole taji kunya. Murmushi yayi, kawai nan sukayi sallama, Saida taga fitansu daga cikin gidan kafun suka juya ita da Ahmad suka nufi sashin Ummi. Ahmad ne ya ɗan kalli yanda take tafiya, tausayinta ya ɗanji saboda ya tuna da Raleeyansa, haka itama tayi first night ɗinsu. "Ya jikin?." Ya tambayeta, yana ɗan sakin ɓoyayyar murmushi. A hankali tace. "Da sauki." Murmushi Ahmad ɗin yayi, tare da girgiza kansa kawai, dan yasan daga Zaleehan har Saifuddeen ɗin jirgi ɗayane ya kwasosu, dan komai nasu iri ɗaya ne, sakalci, raki, da kuma zallan shagwaɓa. Koda suka ƙarasa falon Ummi, Raleeya suka samu da Adda Rahama azaune sai Hayatuddeen. Ganin Zaleehan yasa Adda Rahama tace. "Masha Allah Jiki yayi sauƙi kenan." Ɗan ƙasa tayi da kanta, dan wani irin kunyansu takeji, su dukansu sabisa sai take ga ai duk sun fahimci sanadin ciwonta. Hayatuddeen wanda yake kusa da Adda Rahama ne kuma shi sam bai fahimci sanadin cutar ta duba ne yace. "Ba dole jiki yayi sauƙi ba, tunda rabin ranta ba lafiya, ae yana buƙatar kulawanta". Daga jin maganan kasan zallan tsokana yakeson takalowa. Ɗan sunkuyar da kanta tayi tare da ɗan hararan wasa, Daga Raleeya har Ahmad dariya sukayi, Adda Rahama kuwa cewa tayi. "Manta da Autan Ummi kinji, jeki ɗakin Hayatuddeen ɗin ki duba Saifuddeen dan shima yana fama da jiki." Kanta ta jinjina, tare da ɗan kallon Hayatuddeen ganin yana binta da idone yasa ta ɗan haɗe fuska kana ta juya. Cikin sanyi ta nufi ɗakin Hayatuddeen din. Murmushi Ahmad yayi, cikin zuciyarsa yace. "Marar kunyan ƙarya, lokacin da kikaji maza, ina da ga kwance saida najiyo ihunki, fitsarerriya ai yamin mgnin ki, ko yau na mutu ban mutu da baƙin cikin ba yamin dai-dai dan daga yawau bakin ya mace." Ahankali ta tura ƙofar ɗakin Hayatuddeen, bakinta ɗauke da sallama, taɗan kutsa kanta ciki. Kwance yake akan gadon Hayatuddeen, ya ɗan jingina bayansa da jikin pillow, dan Dr.Aleeyu yace masa yanayin hakan, zai ɗan taimaka bayan nasa ya ware. Gefensa kuwa Ameena ce, zaune tana ƙoƙarin ɓare magunguna zata bashi yasha. Ahankali tayi ƙasa da kanta, cikin muryarta da ta ɗanyi sanyi tayi sallama. Ameena ce ta amsa, tare da cewa. "Masha Allah jiki yayi sauƙi kenan Ammin Adeel." Kanta ta jinjina kana ta ɗanyin guntun murmushi, tare da kama ƴan yatsun hannunta ta shiga yin wasa dasu, Idanunsa ya ɗago ya watsa mata, wani irin so, ƙauna, haɗi da zallan tausayinta ne suka cika masa zuciya ya kamata ace a irin ya wannan ranar ta samu kulawarshi irin kulawa mai nuna jin daɗi to ciwo ya hana. A hankali ya ɗan nago hannunsa ɗaya ya miƙa mata alaman tazo. lumshe idonta tayi, kana ta buɗesu ganin har yanzu yana miƙo mata hannun ne sai taji bazata iya ƙi ko musa masa ba, ahankali ta ƙaraso tare da sanya hannunta acikin nasa, jawota yayi ya zaunar da ita kusa dashi, har gaba ɗaya jikinsu na manne da juna. Kanta taɗan ɗaura akan kafaɗansa, tare da ɗan lumshe idanunta. Wani irin ajiyar zuciya suka sauƙe atare su dukansu uku, ganin haka yasa Ameena ɗanyin ƙasa da kanta, tana ambaton sunan Allah acikin ranta, kana sai ta kumayi ɗan murmushi jin ya kamo hannunta. Ahankali ya kamo hannun Ameena'n, ya riƙe acikin nasa gam ya haɗe tafukan hannunsu wuri ɗaya, Murmushi tayi, cikin son basu waje tace. "Bana bari to kuɗan gana, nasan ma Adeel nacan yana neman nono, anjima ina dawowa." Ɓuɗe idanunsa yayi, ya kalleta, tare da ɗan yi mata murmushi sannan ya jujjuya mata kai alaman "A a shi dai karta fita." Tafin hannuntan yasa tsakanin wuyanshi da kafaɗanshi cikin yanayin mai wuyar fasalta sirrin zuciyarshi. yayi mata wani irin kallon da taji tamkar ta faɗa jikinshi, zaro hannun nata yayi ya ɗaura shi kan bakinshi a hankali yayi mata wani fitinenne kissing bayan hannunta, ido ta lumshe cikin tsananin farin ciki ta ɗan janye hannunta tare da miƙewa cikin sakin fuska da zuciya tace. "To bari inje in ɗauko Adeel kajishi can yana kuka". Kai ya gyaɗa mata alamar to. Tana fita kai tsaye side ɗinsu ta wuce, dan Adeel kam wurin Ummi ma yake. Shi kuwa Saifuddeen yana kallonta har ta fice daga cikin ɗakin. Hannunsa yasa yaɗan tallafo haɓar Zaleeha data sunkuyar da kanta tallaɓo haɓarta ya kumayi. Hakanne yasa taɗan bude idanunta ahankali, ɗan ƙaramin bakinta ta turo, take kuma saiga ƙwalla sun cika idanunta. Ɗan rolling beauty eyes ɗinsa yayi, cikin body language ɗinsa yace. "Menene kuma?." Ɗan hararannsa tayi, cikin muryarta da ke fidda zallan sakalcinta tace. "Ka sani ai". Kanshi ya jujjuya da sauri tare da waro idanunshi alamu a a ni ba abinda na sani. Narke fuska tayi tare da cewa. "To bakai bane kajimin ciwo". Jin muryarta acikin kunnuwansa, ya sashi lumshe idanunsa, wani irin ni'ima da daɗi ne yakeji na ratsa sa, take daɗin muryar tata ta sauƙar masa da kasala. Shagwaɓewa yayi shima cikin body language ɗinsa yace. "Nima bake bace, kika sa duk jikina yayi weak, ko tashi da kyau bana iyayi bayan ma ya ida golɓalewa kun huta keda Ameena baku da mijin da zai lilaku." Hannu tasa taɗan daki ƙirjinsa, cike da wani zazzafan shauƙi tace. "Wai ni, wallahi bani bane, kaine ai kuma sai Allah ya sakamin..." Murmushi yayi tare da jawota gaba ɗaya jikinsa, ta zauna akan cinyansa, hannunsa yasa ya kamo waist ɗinta, tare da ƙura mata ido kana ya mata alaman, kan me Allah zai saka miki?. Tura masa baki tayi, asanyaye tace. "Zalina da kaci mana". Murmushi yayi tare da jawo wayar shi ya rubuta mata. "A a ni banci zalinki ba, ni amarci da budurci naci, kuma halal nane. sadakina na amsa". Nuna mata rubutun yayi yana mata ɗan murmushin ƙeta. Karya wuya ta ɗanyi a hankali tace. "Nidai Allah zafi nakeji, kuma sai na faɗawa Ummi irin ciwon da kaji min." Murmushi yayi, cikin body language ɗinsa yace. "Haba da gaske naji miki ciwo?". Still baki ta sake murguɗa masa, ahankali ya ɗaura ƴan yatsunsa yana zagaye laɓɓanta. Cikin shammata ta kamo hannun nasa ta tura abakinta, kan babban yatsansa ta ɗaura haƙorinta, tare da ɗan cizawa. Hakanne yasashi sakin wani irin nishi da ɗan ƙarfi, tare da rumtse idanunsa, alaman zafi, ganin haka yasa ta sakin dariya har dimple ɗinta na lotsawa. Dariya take sosai inda ta ɗaura duka hannayenta akan wuyansa ya zama suna fuskantar juna da kyau dariya takeyi sosai tare da cewa. "Kaji ai kaida cizone ma kaɗai ni kuma kana wani cemin baka ji min ciwo ba". Dariya ta kuma saki ganin yadda yayi mata da fuskarshi dariya takeyi sosai harda rufe Idanunta. Sake jawota yayi, tare da matseta ajikinsa, kansa ya soma ƙoƙarin cusawa acikin wuyanta, tare da saka bakinsa yana ƙoƙarin kamo fatan wuyanta wai zai ciza shima zai rama. Hakanne yasa dariyanta ƙaruwa sosai, dan tanajin kaman cakulkuline yake mata. Sosai take dariya tana son zillewa amma ya riƙe ta gam. Dai-dai lokacin Ummi ta nufo ɗakin dan a zatonta Ameena na nan har yanzu shiyasa da Adeel ya fara kuka ta ɗaukoshi zata kawo mata shi. A hankali ta murɗa handle ɗin ƙofar ɗakin tana shiga tai saurin...! Littafina na kuɗi ne biya ki karanta halal ɗinki turo katin mtn na ɗari uku ta wannan number 09097853276 ko kimin transfer ta asusuna na 0005388578 jaiz back Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo min shaidar biyarki ta nan 09097853276. In kin karanta na sata 😂😂😂 yaseeen doguwa bulluƙutu baƙar mutuwa aradu🤣🤣 Allah sarki yarinta duk sanda nace yaseen doguwa bulluƙutu baƙar mutuwa, sai na tuna yarinta, Brother Usman wannan shafin nakane Dr Usman Aliyu Garkuwa ɗan uwana rabin jiki, yau da gobe mai nesanta yan uwa, in tuno da mu kwana gida ɗaya mu tashi tare muyi faɗa mushirya, randa ka tashi cin zali ka dagani kamar zaka karni, inja maka yaseen doguwa bulluƙutu baƙar mutuwa, ince babu ni babu kai😂🤗 yana da ciwon ciki tun yana ƙarami randa ciwon cikin ya tashi kuwa inyi ta kuka ina ce mishi na yafe maka Mamamu haka nake kiranshi, duk da bani ke binshiba amman akwai tsamar saƙo da saƙo a tsakaninmu kodan mai binshi ɗin ya rasu, Kullum mukayi faɗa shine da gsky kuma nuce da ɓare baki inyi ta zunɗuma ihu sabida nasan ni yar gaban goshin Kakaninmu ne, nice jika mafi soyuwa duk rashin gsky na sai suce to ai shine babba yayi haƙuri mana ai yarintace ke damuna, wani lokacin sai ince ni da an kyautar dashi ma na huta, gashi yau shekara ɗaya cib sai dai muyi waya in ganshi video call ko a hoto miss You Mamamu ɗan uwa rabin jiki, yayu maza akwai daɗi Ya Muhammad Ya Abubakar🙏🏻😭 Ya Usman Ya Rabi'u Ya Adam, duk yayune masu daraja da soyuwa a rayuwata, muna rayuwa cikin ƙaunar juna mutuwa ta zare mana ya Abubakar daga cikinmu😭😭, shiysa rauni nane akoda yaushe zanyi rubutu da abin tausayi sai nayi kukan tuno rasuwar shaƙiƙaina Ya Abubakar, ƙanin Auwal Sadiq kakata Innayi duk wanda ya karanta littattafan Mi wasmiti zai san sunayensu, ya Allah ka jiƙansu da Rahama🙏🏻😭😭 Tana buɗe ƙofar idanunta ya sauƙa akansu, kasancewar sun shagala, basu ma san dap zuwanta ba, da sauri ta saki ƙofar, tare da juyawa  ta koma baya, murmushi ɗauke akan fuskarta ta nufi bedroom ɗinta ta.  Gaba ɗaya farinciki takeji acikin rai da zuciyarta, hakan har ya kasa ɓuya abayyane tace. "Alhamdulillah Allah, Lallai dukkan tsanani yana tare da sauƙi, sannan kuma shi haƙuri ribarshi nada yawa, dan gashi kuwa Saifuddeen na samun alfanun haƙurinshi."     Tabbas samunsu da tayi cikin yanayi na wasa da dariya, da kuma  tsantsar farin ciki, shi yasa itama taji zuciyarta ta wadatu da farin ciki, da kuma jin daɗi, a wani sashi na zuciyarta kuwa Allah take roƙo, daya basu zaman lfy da matanshi duka biyu. Murmushi ta kumayi a baiyane tace. "Uhum mata da miji sai Allah". A can ɗakin Hayatuddeen  kuwa, cikin dariya Zaleeha tasa hannunta cikin suman kanshi aɗan shagwaɓe  tace. "Wayyo na tuba bazan sake ba, please kabarni na tafi, ni gaisheka fa kawai nazo yi". Ƙara cusa kanshi yayi cikin wuyanta tare da shaƙan ƙamshin jikinta, a hankali ya ɗan ciji fatar wuyanta, wani irin ɗan zillo tayi tare da gantsarewa, hakan yasa ƙirjinta ya ɗan turo  gaba, tura baki tayi cikin shagwaɓa tace. "Auchhh Allah Akwai zafi, nidai bazan yarda ba sai na rama ehe". Jin yadda ya kife tafukan hannu wanshi akan ƙirjinta data turo mishi, yasa cikin sauri ta zame gefe, tana me  sake shagwaɓe masa fuska, tare da turo baki. Dariya yayi, tare da jawota jikinsa ya gyara mata zamanta kan cinyarshi ahankali ya rubuta cewa. "Ina ciwon da jimikin yake nuna min na gani". ya nuna mata fuskar wayar tashi, tare da karyar da wuya, kafaɗanta ta maƙe cikin shagwaɓe murya tace. "Hummm a'a nidai naƙi wayon". Dariya yayi mai ɗan sauti ganin yadda tayi kamar yarinya ƙarama, hannu yasa ya tallafo kanta tare da haɗe goshinsu wuri ɗaya. ido ya lumshe  tare da  ɗan zaro mata harshenshi yana me ɗan karkaɗa mata  shi. a hankali ta tsurawa fuskarsa ido, haka nan sai take ga kamar tasan  wannan fuskar nashi tun da daɗewa, idan ma ba fuskarsa bane, to wata ƙila  me kama da  fuskarsa ce, ido ta ɗan zaro, sakamakon jin yanda yasa harshenshi yana lasar lips ɗin ta. Hakanan taji wani irin diffrent feeling ya taso mata, ɗan lumshe idanunta tayi,  cikin wani irin zazzafan shauƙi da ya taso mata, ta sake kusanta fuskarsa da tata waje ɗaya, hakanne yasa bakinsu  sake kusanta dana juna. Ahankali ta ɗaura lips ɗinta akan nashi liips ɗin,  wani irin kissing tayi masa irin me tsayawa arai,  wanda har saida yaji wani abu ya taso tun daga tsakiyar kanshi har zuwa babbar ƴar yatsar ƙafarshi, Ahankali ta kuma sakin lips ɗin nashi,    tattausan harshensa ta kamo, da laɓɓanta biyu tayi amfani, wajen sucking tongue ɗin nasa,  shi kuwa  jin yadda take kissing nashine ya sashi ƙara gigicewa, hannu yasa akan bayanta, tare da  fara zuge zip ɗin rigarta, jin haka yasa tai maza ta saki tongue ɗinshi,  lips ɗinshi ta kamo, a hankali ta ɗan ciji laɓenshi na ƙasa, wani irin tsalle yayi tare da buɗe idanunshi, Ganin haka yasa ta bar jikinshi da sauri, ganin kuma ya miƙo  zai kamota ne tai maza ta sauƙa daga kan gadon, kyakkyawan dariya  tayi cikin dariyar tace. "Thank God, nima na rama, kaga yanzu munyi one one , saboda haka, good night and sweet dreams". Kanshi ya jujjuya  mata alaman tazo, baki ta turo gaba tace. "A'a nidai saida safe, ai ciwon da ka jimin jiyama bai  warke ba, nidai kawai saida safe". Tana gama faɗin haka ta juya, cikin sauri ta fita daga ɗakin. ido ya lumshe bayan fitanta a hankali ya gyara konciyarsa,  wani irin zazzafan shauƙi ne yake ratsa sassan jikinshi, yanajin so da ƙaunarta kaman zasu fasa ƙirjinsa. Ita kuwa Zaleeha tana fita daga ɗakin, kaitsaye ta wuce side ɗinsu kasancewar babu kowa a falon. Tana shiga  bathroom gasa jikinta ta kumayi, kana tayi wonka tana fitowa kuwa tayi shirin baccinta. Koda ta konta da zaran ta lumshe idanunta fuskarshi dake murmushi take gani a haka  har tayi bacci. Ɓangaren Ameena kuwa wonka tayi mai rai da lfy sannan tayi shirin baccinta. Tana kammalawa kai tsaye side ɗin Ummi ta nufa, a falo ta samu Ummi da Ahmad suna zaune, hannu tasa ta amshi Adeel daketa miko mata hannu gefe ta zauna tana kiciniyar bashi nono. Cikin kula Ahmad yace. "Yauwa Ameena kinada E passport a kusa ne?". Kai ta gyaɗa tare da cewa. "Eh inada dashi". Ummi ce ta gyara zama tare da cewa. "Yauwa to ki kawo mishi, dan zaiyi muku booking ɗin tafiyarku India ta online dan Dr Aliyu yace ya tafi da ke tunda Dr Adnan bazai samu damar tafiya a kuma ana buƙatan masanin jinyar kusa dashi". cikin mamaki da jin daɗi tace. "Ummi tafiyar har ta zone kenan kuma dani za'a je". Ahmad ne ya gyaɗa mata kai tare da cewa. "In sha Allah tafiya tazo, dan jibi  ma akwai jirgin da zai tashi zuwa India, sai dai New Delhi zai sauƙa kuma a Mumbai za kuga likitan, to amma dana sanarwa da Dr Acash prasad  yace ba matsala, shi zai taho da Dr zuwa New Delhi ɗin". A hankali tace. "Alhamdulillah, to amma  wurin aikina fa Ahmad". Kai ya rausayar tare da cewa. "Eh Ya Adnan yaje ya sanar musu uzurinki harma an baki daman  kuyi tafiyar tare". Wani irin daɗi ne ya cika mata zuciya, cikin jin daɗin tace. "To Allah ya kaimu lfy ya kuma bamu sa'an tafiya". Amin Amin sukace baki ɗaya kana Ummi ta miƙe ta nufi ɗakin Hayatuddeen dan yiwa Saifuddeen saida safe. Konce ta sameshi system ɗinshi na gabanshi, a hankali ta zauna gefenshi, ido ya zuba mata cikin jin daɗin yace. "Ummi meya hanaki bacci har yanzu?". Kanshi ta shafa tare da cewa. "Farin ciki mana, yau babana yana magana da bakinsa". Murmushi yayi tare da cewa. "Hakane fa Ummi". Murmushi tayi kana tace. "Yauwa batun tafiyarka India, zaku tafi da Ameena, dan Ahmad zaije Dubai sari, Ya Adnan ɗinku kuma ba'a bashi dama ba a wurin aikinsu, saboda Dr Arabi baya nan, ba yadda za'ayi a bar sashinsu ba kowa". Kanshi ya jinjina a hankali yace. "To Ummi ba matsala, Allah ya kaimu lfy". Amin Amin tace tana mai son karanto haƙiƙanin abinda ke ƙasan zuciyarsa, amman saidai ta kasa gane shin yaji daɗin tafiya da Ameenan ne ko baijiba, Abinda kuma nima kaina ban gane ba kenan, because  duk wani yanayinsa sirrin zuciyarsa ne. Kanshi ta kuma shafawa  tare da cewa. "Saida safe". Tattausan murmushi yayi yace. "Allah ya bamu al'khairi".  "Ameen" tace kana ta fita daga ɗakin. Ameena da Hayatuddeen ta samu a falon cikin bada umarni tace. "Ameena kije ki kula dashi, kai auta kazo ɗakinsu Raliya". To sukace mata baki ɗayansu. Daga nan ta wuce, kana Hayatuddeen na biye da ita a baya. Ita kuwa Ameena ɗakin ta nufa. Konce ta sameshi yayi lib a gadon jin sallamarta ne ya sashi buɗe ido, wani irin sassanyan murmushi ya sakar mata, tare da miko mata hannunsa alamun tazo. Kontar da Adeel tayi can gefe kana tazo kusa dashi, jawota jikinshi yayi cikin sanyin murya yace. "Zanyi wanka". Da sauri tace. "To". bathroom ta shiga ta haɗa mishi dukkan abin buƙata, tana fitowa ta sameshi zaune bisa kekenshi amman gaba ɗaya jikinshi rawa yake, sai wani irin zufa ke tsastsafo mishi sabida azaban ciwo da bayanshi keyi. Ahankali tace. "Sannu". Kai ya gyaɗa mata alamar yauwa kana ya nufi bayan gidan. Ganin shigansa toilet, yasa ta gyara gadon, tare da ƙara gudun A/C. Ba jimawa ya fito daga wankan,  cikin ƙarfin hali da dauriya, ya sauƙa kan kekenshi ya zauna bisa gado, man Hayatuddeen da turarenshi ya shafa sannan ya konta. Jawota jikinshi yayi tare manna mata kiss a goshi cikin sanyin murya yace. "Kinyi bacci ne?". A hankali tace. "A a idona biyu". ajiyan zuciya ya sauƙe tare da cewa. "Shine ko ki kulani". Juyowa tayi da kyau kana ta ɗan raɓa jikinshi a hankali tace. "Yanzufa jinyan bayan zamuyi". Murmushi yayi tare da cewa. "To ban ceba, ni lafiyata lau, karki wani ce ai banda lfy ne in kina so dai gani nan ras". Dariya tayi sabida ganin ƙarfin halinshi, shima dariyar yayi kana ya ruggumeta sukayi baccinsu a haka. Washe gari da Safe Dr Aliyu da ya Adnan sukayi sammakon zuwa dubashi, dan Dr Aliyu zai koma Abuja, bayan sun bashi duk taimakon da zasu iya bashi ne, suka sallami Umminshi suka tafi. Jirgin da ya kawo su Saminu da Raihana shine ya juya dasu Dr Aliyu. Sosai Raihana taji daɗin ganin Hammanta na mgna da bakinshi. A ranar dai haka baƙi suka rinƙa zuwa tako ina, Masha Allah. Zaleeha kuwa sosai Ummi ke kula da ita Alhamdulillah kuma jiki yayi ɗan sauƙi dan ta samu kula na musamman. Maman Ameena da babanta ma sunzo sun duba Saifuddeen ɗin da jiki. Hakama manya-manyan ƴan kasuwa, da ƴan ƙungiyar Jonapwd, da kuma jami'an sirri na  SS suma sunyita zuwa dubiya a wannan wunin, shiyasa bai samu keɓewa da matanshi ba, Baba Bello ma  da matarsa sunzo haka abokanshi baki ɗaya. Ishaq kuwa hadda Rashida nshi yazo a daren shida Saifuddeen sukayi ta hirarsu ita kuwa Zaleeha da Rashida sukayi ta hirarsu. kafin su tafima tara tayi ganin haka Zaleeha tayi mishi saida safe. Adda Rahma kuwa yauma da ita aka wuni. sai yanzu ya Adnan yazo ya ɗauketa, haka su Goggo Dada da Aunty Mina duk sun zo. Hakane yasa Ummi tace Hayatuddeen ya haura sama ya kwana a ɗaya ɗakin, Goggo Dada kuma tazo ɗakinta Aunty Mina kuma da Raihana su kwana a ɗakinsu, Ranar ma dai Ameena ce ta kwana dashi. Washe gari kuma, shine ta gama kwana biyunta, kuma gobene da sassafe zasu wuce Abuja dan tuni an gama musu shirin tafiyarsu. Bayan sallan isha'i  suka ɗan taɓa hira, a falon Ummi ganin tara ya kusa yasa Ameena ta miƙe ta shiga ɗakin Hayatuddeen dan yiwa Saifuddeen saida safe. Gefenshi ta zauna bisa dukkan alamu mgna yakeyi da Dr Acash dan taji bayanin yadda yakeji yake faɗa. juyowa yayi  ya kalleta bayan ya gama wayar cikin kula yace. "Ameenatu ya akaine naga kinyi shiru". Kai ta rausayar tare da cewa. "Kawai zazzaƙar muryarka ne nakeji, tabbas na godewa Allah daya nufeni da jin muryarka, ji yadda kake zuba turanci kamar cikakken ɗan America". Murmushi yayi tare da riko hannunta a hankali yace. "Gobe iwar haka muna hanya, ko mun isa ko mun kusa isa, kinyi shiri ko?". Kai ta gyaɗa mishi tare da cewa. "Shiyasa ma zanje in shiga da wuri,  inyi bacci  dan nasamu in tashi kan lokaci". Gefen fuskarta ya shafa tare da cewa. "Da wuri haka, bazaki tayani hira ba". Miƙewa tsaye tayi tare da rungume Adeel fuska a sake tace. "Bari inje in turo ma Ammin Adeel tazo ta tayaka hirar ban kwana". Yi yayi kamar bai jitaba, ita kuma juyawa tayi ta fita daga ɗakin. Saida safe tayiwa su Ummi da Raihana da Raliya kana ta wuce side ɗinsu. Kai tsaye falon Zaleeha ta shiga, ita kuwa Zaleeha ta gama shirin baccinta kenan har ta konta taji sallaman Ameena, a hankali ta tashi ta buɗe ƙofar cikin sakin fuska suka kalli juna a hankali Ameena tace. "Abban Adeel na kiran ki". Kai ta gyaɗa alamar to kana ta miƙa hannu zata karɓi Adeel,  da sauri Ameena tace. "A a barshi kije kiji da rigimar tsohonshi". Kai ta ɗan sunkuyar, tana murmushi. Itama  Ameena murmushi tayi kana ta juya ta tafi. A hankali ta zauna abakin gado, abayyane  tace. "Uhum ni bana son zuwa side ɗin Ummi tunda Raihana tazo, ni ban san me nayi mataba, har ga Allah har raina ina sonta ita da ɗanta, amman ita na lura ko ganina bata sonyi, ya Allah ka sani ni babu abinda nai mata." Jiki a mace ta ɗauki ƙaton hijabi tasa kana ta fito ta nufi sashin Ummi. A falon ta samesu baki ɗayansu, a hankali ta koma gefen Raliya cikin sanyi ta gaida Ummi da Goggo Dada da kuma Aunty Mina. Hayatuddeen ne ya ɗan kalleta cikin kula yace. "Adda Zaleeha jikin ne?". Kai ta jujjuya lokacin da taga Raihana nata hararanta ƙasa-ƙasa, cikin sanyi da neman yadda zatayi ta samu ta shiga ɗakin Hayatuddeen ɗin tace. "A a,  na fara bacci ne, to kuma na bar wayata a ɗakinka, ɗauko min its mana". Kanshi ya ɗan rausayar kana ya miƙe yana shiga ba daɗewa ya fito yace. "Nifa na dudduba ban ganiba, Hamma Saifuddeen yace kije ki duba da kanki". Kai ta ɗan gyaɗa kana ta miƙe ta nufi ɗakin. Su kuwa Ummi  ce ta fara miƙewa tayi musu saida safe. daga nan duk suka watse kowa ya tafi makoncinsa. Ahankali ta tura ƙofar ɗakin tare dayin sallama. "Salamu alaikum". ido ya zuba mata cikin yanayin shauƙi da bege, juyo kekenshi da yake zaune a kai yayi ya fuskanceta, ganin haka yasa ahankali tace. "Gani Ummu Adeel tace kana kirana". juya idonshi yayi kalan bacci, kana ya motsota, hannunta ya riko suka taho bakin gadon, ajiyeta yayi sannan shi kuma ya yunƙura ya tashi kan kekenshi gaba ɗaya jikinshi karkarwa yake, ido ta zuba mishi saboda da ka gani kasan azaban zafin da yakeji. taune leɓenshi yayi kana ya zauna bakin gadon, hannunshin duka biyu yasa ya dafe gadon bayan nashi sai zufa daketa tsastsafo mishi ta suman kanshi, cikin tausayawa tace. "Sannu, to ka konta mana". Bai kulata ba, sai dai numfarfashi yaketa sauƙewa ajere-ajere, tausayinshi ne ya cika mata zuciya,  Allah ya sani tanada rauni, kuma haka nan bata son ganinshi cikin mawuyacin hali, miƙewa tayi a hankali ta sunkuyo ta gefenshi, pillows ta jere mishi a bayanshi cikin, sanyi tasa hannunta duka biyu ta tallabo bayanshi, jin haka yasashi sa hannunshin kan kafaɗunta, jingina shi tayi jikin pillows ɗin, kusan atare suka sauƙe ajiyan zuciya, miƙa ƙafafuwan shi yayi cikin zuba mata ido ya jawo hannunta ya zaunar da ita kam sawunshi, cikin karya wuya ya mata alamun zafi yakeji. Ga mamakinshi sai yaga tayi rau-rau da ido cikin rawan murya tace. "Sannu Hamma Saif Allah ya baka lfy". jawota yayi suka konta, lib tayi a jikinshi,  tana shaƙar ƙamshin jikinshi, shi kuma wayarshi yaja ya ɗan mata rubutu ya miƙa mata wayar. "Ya ciwonki ya warke ne?". Kai ta jujjuya alamun bai workeba, murmushi yayi tare da shafa fuskarta a hankali ya kuma rubuta mata. "To tashi, tashi, maza tashi ki nuna min ciwon zan sa miki magani zai bar ciwon". Ido ta zaro tare da maƙale kafaɗa alamar a a kam, hannunshin ya cusa cikin hijabin jikinta, jin riga da wondone a jikinta ya sashi cire hijabin, rubutu ya kuma mata. "Ai shiyasa ciwon bazai warkeba kinata ɓoye min shi, da kin nuna min dai da ya warke". ido ta rufe dan kunya ya rufeta, shi kuma hannunshi ya cusa cikin rigarta ya rarumo breast ɗinta da sauri ta buɗe idon, sai kuma tayi sauri ta rufe idon jin ya kamo hannunta ya cusa cikin boxer ɗin jikinshi. murmushi yayi ganin yadda hannunta keta karkarwa tamkar mazari hannunshi ya haɗa da nata ya matse Saif ɗinshi daketa tsastsafo mishi da ruwan kwaɗayi, jin ta ɗan rumtse tafin hannunta yasashi zaro hannunshi ya bar nata kaɗai akan saif ɗin nashi, hannunshi ɗaya na cikin rigarta ɗaya hannun nashin yasa ya rubuta mata magana a wayarshi ya miƙa mata. "Ummi ta gaya miki gobe zamu tafi India da Ummu Adeel ko? Zanje inga Doctors ɗina". Kai ta gyaɗa mishi alamar eh Ummi ta gaya mata, kanshi ya ɗan manna da nata a ranshi yake mgna. Yana jin wani zafi a ransa tabbas da shawararaa aka nema wlh da da Zaleeha zai tafi, domin yana buƙatarta tana buƙatar kulawarsa a irin ya wannan yanayin, to amman saida Ummi ta gama yanke hukunci ta sanar mishi, kuma sunce Dr Aliyu ne yace dole aje da Ameena. Ajiyan zuciya mai zafi ya sauƙe kana a hankali ya hura mata iska a kunneta. wani irin yar-yar haka taji tsikar jikinta na tashi haka nan taji tana ƙara shigewa jikinshi, sai miƙa takeyi kamar wacce kejin bacci. gyara zamanshi yayi da kyau rigar jikinta ya fara kiciniyar cirewa, a hankali ta riƙe hannunshi murya can ƙasa tace. "Bari mana Hamma Saif". Ta ƙarishe maganar dayi mishi alama, kanshi ya jujjuya tare da rubuta mata. "A nan zamu kwana ai". Ido ta zazzaro cikin kunya tace. "Tab a a kam ni dai ɗakina zan koma in kwana". Ƙarisa cire rigartata yayi tare da ajiyeta gefe jin zata zaro hannunta daga inda yasashi ne yasashi girgiza mata kai. Alamu a a . Kwaɓe fuska tayi a hankali tace. "Su Ummi suna falo fa kar wani ya shigo". Rubutu ya mata a waya ya miƙa mata. "Babu mai shigowa, dan sun san kina nan ai". shiru tayi jin ya kontar da ita kan cinyarshi, botur ɗin gaban boxer ɗinshi ya buɗe, da sauri ta rufe idonta ganin bayyanan jikinshi, shi kuwa kanta ya jawo ya kife kan Saif ɗinshi daketa harbawa kan lips ɗinta ya fara gogashi a hankali a hankali, wani irin taushi da tsantsine suka haɗe wuri ɗaya wanda yasa dole ta buɗe bakinta a hankali dan ta gane me yake son tayi mishi. A hankali ta fara ida mishi nufunshi. Wani irin marayan numfashi yaja tamkar zai tafi da ransa, hannu yasa yana shafa dukkan sassan jikinta tamkar zautacce, da ƙarfi ya danna mata Saif ɗinshi cikin bakinta dan jin yadda taketa cika da kumbura, danna kanta yakeyi a hankali yana jin ɗumin bakinta na ratsashi,  wani irin zazzafan shauƙi ne ya bijiro musu baki ɗayansu, ƙarisa cire wondon yayi sai sautin. "Ahhhhhhh aushhhhhhhh hahhhhh."   yake fiddawa, dan Zaleehan na neman zautar dashi, a hankali take murza cinyoyinta dan wani irin abun da takeji, shi kuwa hannunshi yasa ya riƙe mata Saif ɗinshi da kyau, kusan minti 35 tana mishi abu ɗaya madadin ya sauƙa sai ƙara hawa da cika yakeyi, hannunshin yasa ya riƙe kanta yana ɗan dannawa akan saif ɗinshi, jin abin takeyi har cikin maƙogoronta shiyasa ta fara yunƙurin amai, to Amma ina bai bata daman hakan ba, can kusan bayan mitin 30 bayan 35 ɗin forko taji, ya fara tsirta mata sperm ɗinshi, da sauri taso janye bakinta amman ina yaƙi, A take ya cika mata bakinta da ruwan fitinarshi, wanda dama al'ƙawari ne yayiwa kansa, cewa sai ya shayar da ita ruwan fitinarshi tun randa tace Allah ya sauwaƙa tasha yawunshi, ganin zai tafi gobe ne kuma yayi niyar shayar da ita kafin ya tafi. saida ya cika mata bakinta tib sannan ya janye jikinshi, kana ya jawota da ƙarfi ya kontar da ita kan cinyarshi a rigingine,  da sauri yasa tafin hannunshi ya rufe bakinta da take son burzo madarar daya tsiyaya mata, yatsunshi biyu yasa ya toshe hancinta ai take ta fara jujjuya kai, jin numfashinta na tafiya ne yasa ta haɗiye kab madarar, jin tana laso tafin hannunshi ne yashi janye hannun, murmushi yayi mata mai cike da zallan farin ciki haɗida ƙauna da bege. Ita kuwa tura baki tayi ta tashi zaune, kan cinyarshi ta hau, sai kuma tayi maza ta sauƙa da sauri jin ya kama Saif ɗinshi zai saita da jikinta, dariyar mugunta yayi tare da mata alamun "Da kin tsaya ai". Miƙa tayi tare da kamo hannunshi ta ɗaura kan bakin nipples ɗinta da sukeyi mata azabebben ƙaiƙayi. miƙa tayi da ƙarfi lokacin da taji ya fara murza mata su, narkewa tayi jikinshi tare da cewa. "Aahhhhhhhhh Hamma Saif da daɗi". Dan ita a zatonta baya jinta, wani irin ɗan iskan murmushi yayi tare da kontar da ita, bakinshi ya kai bisa ƙirjinta ya fara yi mata wani irin rikitaccen salon da babu ƴa mace mai lafiya da zata iya jurewa. sucking nipples ɗinta yakeyi da kyau, tun tana ƴan ƙananun surutai,  har ta fita haiyacinta, hannunshi ta kamo ta kai bisa ƙasanta, gaba ɗaya ta jiƙe, kyaunta yayi mata abinda tayi mishi to amman bazai iya sunkuyowa ba,  ya sani wani bidirin kam sai ya dawo". hannunshin yasa bisa mararta yana shafawa a hankali a hankali kamar dai yana gudun fama mata ciwon da yasan yaji mata ɗin, ahankali yake ɗan fingering ɗinta, gaba ɗaya santsi da kuma taushin wajen yasa saif ɗinsa sake kumburowa, haka ya cigaba da yi mata, yana me ɗan nutsa yatsarsa cikin jikinta, wanda sperm keta fita, ga wani irin taushi me gigita tunani. Sama da 20 minute yana mata haka, can ta saki wani ƙara tare da ruggumeshi gam-gam a jikinta, wani zazzafan numfashi take fitarwa, jin yadda jikinta ke karkarwane yasashi jawo musu blanket ya rufesu. Shiru sukuyi kamar sunyi bacci, can ta ɗan juyo suka fuskanci juna, dubanta yayi da kyau girarshi ɗaya ya ɗaga mata tare da rubuta mata. "Tashi muje muyi wonka". Jiki a mace tace. "Hamma Saif bazan iyaba". Kanshi ya gyaɗa mata dan yaga alamun hakan, rubutu ya kuma yi mata. "Zamu tafi gobe, ban saniba ko zamu daɗe ko bazamu daɗeba, bana dai son yawo, in kina buƙatan wani abu akwai kuɗi a ɗakina, a cikin drawer". Shiru tayi data karanta haka nan taji tana masifar son kusanci da shi. A hankali taji idonta na ciko da hawaye kai ta rausayar tare da cewa. "Uhumm Hamma Saif ngd, kaji min ciwo kuma zaka gudu kayi tafiyarka India". jin hawayenta suna zubowa ne yasa tai saurin juya mishi baya. ruggumeta yayi da kyau dan ta ƙaryar mishi da zuciya, maganarta  gaskiya ce duk da azatonta bai jitaba, dukkan amare suna buƙatar kulawa ta musamman a irin ya waɗannan kwanakin da aka keta budurcinsu bare kuma ita da yake masifar so da ƙaunw. Rubutu ya ƙara yimata koda ta karɓi wayar ido ya ƙura mata ganin tana karanta maganarshi. "Bashin kulawa dake  yana kaina kuma zan biya, zamuje ne kawai dan zuwan ya kama dole". Bata kuma cewa komaiba, tashi zaune yayi ya jawota itama ta zauna, boxer ɗinshi ya jawo a hankali yasa sannan ya jawo wani towel ya saka mata, kasancewar idan yace zai sa mata pant zata ɓata shi, saboda duk tayi staining da sperm. lokacin da zai tashi daga kan gadon zuwa kan kekenshi ne ya tuno da ciwon bayan da yake, kasancewar dama in a koncene bayaji. da kyar ya zauna kana ya jawo hannunta, bayan gida suka shiga, cikin bath ya shiga ita kuwa a bakin bath ɗin ta zauna, tare da sa ƙafafuwanta aciki, jin yana zame towel ɗin jikinta ne yasa ta ɗan kalleshi, kai ya gyaɗa mata alamun ta ɗan buɗe ƙafafuwan nata, bata kulashiba, ganin hakane yasa hannu ya ware sawunta, a hankali yakai bakinshi kan privet part ɗinta, jin abinda zai matane yasa tayi saurin zamowa cikin bathtube ɗin, daga haka sukayi wonka. Bayan sun fitone ta maida kayan jikinta tasa hijabi, kallonshi tayi tare da cewa. "Saida safe zanje in kwanta". Ogogon dake jikin ɗakin ya nuna mata, da sauri tace. "Ƙarfe biyu da rabi". Kanshi ya gyaɗa mata a hankali tace. "Ni dai bazan kwana a nanba". Jawo hannunta yayi ya kontar da ita, tare da mata alaman kwana kuma na nawa. Hira suka ɗanyi kana bacci ya kwashesu, kiran sallan forko a kunnenshi. Da kyar ya lallaɓa yayi wonka da al'wala kana ya fito ya tada ita, ya rubuta mata ta tashi ta tafi tunda bata son asan tazo, ya ƙara da ce mata in taje tayi salla ta kawo mishi kayan da zaisa. sanna ta haɗo mishi wanda zai tafi dasu ta kuma haɗa mishi da system ɗinshi. Hakan kuwa akayi Ƙarfe shida dai-dai duk suna falon Ummi Ishaq ma yazo, Ahmad ne ya kalli Zaleeha tare da cewa. "Ko dai za'a bar miki Adeel ne?". Da sauri ta gyaɗa kai alamar eh. murmushi sukayi baki ɗaya kana Ummi tace. "Ahmad ku tafi ina kunje jirgin karfe bakwai zai tashi". To Ahmad yace kana duk suka mimmiƙe, Ameena ce ta karɓi Adeel tare da cewa. "To Ammin Adeel sai mun dawo". Cikin sanyi Zaleeha tace. "Allah ya kaiku lfy yasa ku dawo lfy". Amin Amin sukace baki ɗayansu kana suka nufi hanyar fita, Shi kuwa Saifuddeen gefen Zaleeha ya koma ganin hakane yasa suka fita suka barsu. A hankali ya kamo hannunta duka biyu, mannasu yayi da fuskarta a hankali ya mata alamun zamu tafi. haka nan taji rauni ya rufeta a hankali ta faɗa jikinshi cikin rawan murya tace. "Ban san me nakeji a kankaba, inaji bana son kayi nesa dani, hakanan na fara kewarka tun kafin ka tafi, inama ace zaka jini da na gaya maka yadda nakeji a zuciyata, ban taɓajin begen rabuwa da waniba a duniya sai kai, Hamma Saif anya zan iya jure tsawon wani lokacin ban gankaba, Ban san meyasaba bana gajiya da ganinka, bansan yaushe mukayi shaƙuwar da har nakejin cewa kaine farin cikina ba". Wani irin fitinenne runguma Saifuddeen yayi mata shi kaɗai yasan irin daɗin da yakeji a cikin rai  da jikinsa dama dalilinshi kenan na ɓoye mata warakarshi, kanta ya ɗan tallafo ya haɗa da nashi suna kallon juna murya a sanyaye tace. "Ina roƙon Ubangiji mai dukkan isa daya kaiku lfy ya dawo daku lfy, zanyi tayi maka addu'a a cikin dukkan sallolina, Allah ya baka lfy ya dawo mana daku lfy". Kissing lips ɗinta yayi ganin yadda suke rawa, alamun tana gab da fashewa da kuka. rungume juna sukayi tare da sauƙe ajiyan zuciya a tare, sun kai 3 minute a haka kafin ya saketa, kana ya jawo hannunta suka fito. A harabar gidan su ka samesu baki ɗayansu, nan suka sallamesu suka tafi Yayinda su kuma suke tayi musu addu'a. Saida sukaga fitansu kafin suka koma cikin gida. Ita kam Zaleeha side ɗinta ta wuce. Su kuwa bakwai dai-dai jirginsu ya tashi Sun isa Abuja lfy, Ƙarfe ɗaya da rabi sukayi sallan azahar biyu dai-dai jirginsu ya ɗaga daga Abuja Nigeria zuwa New Delhi India. Sun jima suna keta gajumare kafin suka isa india, inda suka sauƙa a babban birnin india wato New Delhi, inda tuni dare ya fara nisa, Suna sauƙa a airport ɗin *INDARA GANDHI international airport New Delhi* Bayan duk sun firfito, suka samu Dr Malik Khan da kanshi yazo tarbansu, sabida yasan isan dare zasuyi, daga airport ɗin tafiya kaɗan sukayi suka isa babban hotel ɗin Hyatt regency Delhi,  wanda yake kusa da asibitin da za'a duba Saifuddeen. Kusan Dr Malik ne ya musu komai, hatta sim card ya sayawa Ameena dan sauƙaƙa musu, kuma ya kama musu masauƙi mai kyau a ƙasa, Saida yaga an kawo musu komai da zasu buƙata,  sannan ya sallamesu a kan sai da safe zaizo ya ɗauke su. Yana fita sukayi wanka suka ɗanci abinci,  kana suka konta dan tafiya dai duk sunanta tafiya tanada gajiya. Shiyasa suna kwanciya sai bacci. Washe gari da safe bayan sun gama komai,  Dr. Malik yazo ya ɗaukesu, Kai tsaye asibitin suka nufa, Sosai Ameena tasha mamakin ganin irin cigaban da suke dashi daga matakin ma'aikatansu da kuma na kayan aiki. Suna zuwa manya likitoci suka ƙarɓeshi matakin forko goje-goje aka fara yi mishi,  ginin MRI scanning  da kuma X-ray, CT scan MRI ɗin da sauransu. Alhamdulillah dukkan goje-gojen da zasuyi suna samun karsashi kan aikinsu,  domin ciwon da bayanshi keyi su farin cikine a wurin su, bayan da, da ko reza za'a a yankeshi bazaijiba sai gashi yau kuma yana kukan bayan alamun nasarane babba a wurin. Kwana uku akayi ana gwaje-gwaje kana ran na huɗu, duk sakamakonsa zai fito ta hannun doctors ɗin da suka dace. Shi kam Saifuddeen yanzu gaba ɗaya ma a asibitin yake, Ameena ce dai kan koma masauƙinsu itama gari na wayewa zata dawo asibitin. A gida Nigeria kuwa sosai su Ummi suka sha mamakin lamarin Zaleeha,  dan ko bata faɗaba ana gane tana cikin kewa, duk ta ƙara zama shiru-shiru, tunda suka tafi batayi mgna da shiba, tana dai jin lbrinsu a wurin Ummi, amman kullum sai sun gaisa da Ameena takan tambayi ya mai jiki. Yau Rashida ta kawo mata ziyara dan yaune za'a kai lefenta bisa al'adar gombawa kuwa in za'a kai lefenki zaki ɓuya. To shiyasa yau ɗin tazo wurin Zaleeha. Zaune suke bayan sunyi sallan la'asar hira sukeyi tayi kan batun auren, jin wayar Rashida na tsuwane yasa suka ɗan tsagaita, amsa kiran tayi tare da karawa akan kunnenta,  ahankali tace. "Barka da yamma Ya Habibi". Daga can gefen Ishaq kuwa gyara zama yayi tare da cewa. "Barka dai Matar kirki, wato dan kinji za'a kai lefe ne kika gudu ko?". dariya ta ɗanyi kana tace. "A a ba guduwa nayi bafa gani gidan Zaleeha". Dariya ya ɗanyi kana yace. "Kice gidan gwauruwa, bata waya mugaisa". Miƙawa Zaleeha wayan  tayi wacce ita kuma ta maida hankalinta kan wayarta. jin ta kara mata waya a kunnenta ne yasa ta ɗan ɗago, jiyo muryar Malam Ishaq na ce mata. "Zaleeha ya gida ya labarin mutanen India?". Kai ta ɗan rausayar tare da cewa. "Gidan ba daɗi Malam Ishaq, tunda Adeel ya tafi bana jin daɗin gidan. Mutanen India kuma banyi magana da suba, sai dai naji labarin yau zasuga Dr.Mahesh Deera". Cikin nitsuwa Ishaq yace. "Eh gaskiya koni tunda yaje bamuyi magana da shi ba,  sai dai ina jin labarinshi wurin Dr.Malik, sabida a sabiti yake woyoyinshi kuma suna masauƙinsu, amman ana zaton gobe zasu fito dashi". Ajiyan zuciya ta sauƙe tare da cewa. "Dama ɓoyeshi akayi ne?". Dariya ya ɗanyi kana yace. "Eh to kusan haka dan likitocin physiotherapist  suke dubashi a tsawon kwanakin, saboda sune ke ƙoƙarin farfaɗo da aikin lakar ga wanda akaiwa aiki. To sun bada yaƙinin yanzu kulawarsu yake buƙata, shiyasa suka duƙufa kanshi, kuma Alhamdulillah sunce yanzu bayan nashi da sauƙi sosai". Ajiyan zuciya mai ƙarfi ta sauƙe tare da cewa. "To Allah yasa mudace ya bashi lfy". Amin Amin yace kana yace ta bawa Rashida waya nan yake ce mata anjima zaizo ya ɗauketa. Randa sukayi kwana biyar da tafiya a ranar Saminu da Raihana suka koma KD. To Alhamdulillah shiyasa Zaleeha ta ɗan samu sakewa a tsakiyar gidan dan ta lura sam Raihana bata sonta. Yau kwanansu bakwai a India kuma yaune Dr Acash prasat ya shigo New Delhi da Doctor'n, da zai ƙara duba Saifuddeen. Bayan duk sun gama aune-aunensu ne, suka nufi wani ɗakin kuma da Saifuddeen, kafin su wucene Dr. Malik Khan ya kira Ameena aka wuce da ita. A wani ɗaki na musamman aka shiga dashi Ameena kuwa Office ɗin Dr. Acash prasat suka nufa ita da Dr. Malik. Su kuwa sauran Doctors ɗin suna shiga, Dr. Arjun ya kalli Saifuddeen cikin kula yace ya tashi zaune. yunƙura yayi tashi jin bayanshi sakayau ba azabebben ciwon da yake jine yasashi yunƙurin miƙewa tsaye. Kusan atare Doctors ɗin suka bashi hannunsu da nufin ya riƙe, kai juya alamun su bari, miƙa tsawonshi yayi ya tsaya cur kan ƙafafuwan shi, sai dai ƙafafuwan sai rawa sukeyi kar-kar. Tafi sukayi a tare domin wannan shine matakin nasara, wasu rubuce-rubuce sukayi tayi a na'urorin dake gabansu, Dr Acash prasat kuwa kiran Dr Aleeyu yayi video call ya saita komai yadda zaiga Saifuddeen a tsaye car da ƙafafuwanshi, kabbara Dr Aliyu yayi tare da cewa. "Alhamdulillah jiki yayi sauƙi da izinin Ubangiji". Kai Dr. Acash ya gyaɗa mishi alamun haka. Bayan sun gaba duddubashine sukace ya gwada takawa da ƙafafuwanshi, to amman ina ya kasa ɗaga ƙafafuwan dole suka haƙura, nan suka bashi magunguna da allurai na tsawon sati uku,  cur wanda kullum sai an mishi allurar biyu ɗaya da safe ɗaya da yamma, Alluraine da ko wanne ɗaya kuɗinshi ya kai dubu ɗari da ashirin. Nan suka bashi damar komawa masauƙinshi. Koda suka fito suka dawo Office ɗin Dr Acash inda suka samu Ameena da Dr Malik. Da sauri Ameena ta miƙe ganin kyakkyawan mijinta zaune bisa kekenshi mai masifar kyau, rungumeshi tayi cikin jin daɗin tace. "Alhamdulillah Abban Adeel ya jiki". Murmushi yayi tare da rungumeta murya ras yace. "Alhamdulillah Ummu Adeel jiki kam da sauƙi sosai ma". Dr. Arjun ne dake bayanshi yayi ɗan dariya tare da cewa. "Duk nasarar aikinsu bayan nawane, dan jinyar da nayi tafi kyau". Dr. Arjun shine likitan dayayi aikin kunnen Saifuddeen, tun zuwansu wancan kuma dama tun a lokacin ya shaida musu aikinshi yayi kyau." Zama sukayi baki ɗayansu, Dr. Malik ne ya kira Dr.Adnan  dan yaji dukkan bayanan da zasuyi. Dr. Mahesh Deera ne ya ɗan gyara zama,  cikin harshen nasara ya fara musu kyakkyawan bayani inda yace. "Yanzu dai ana iya ganin Saifuddeen ya mike yana tafiya da ƙafafuwanshi a cikin ko wanne lokaci, domin sanadin sex ɗin da yayi ya motsa ƙugunshi, hakan kuwa  ya taimakawa babbar jijiyar bayanshi na laka daman harbawa, sanadin harbawan da yayi ne kuma dukkan ƙananan jijiyoyin dake sarƙafe da jijiyar wanda yake kamar wayarin na wutan lantarki, shine ya isar da saƙon dukkan sauran jijiyoyin, cikin hakane jijiyoyin kunnenshi dana wuyanshi dama na sauran sassan jikinsa duk suka amsa,  shiyasa tun a lokacin jinsa da maganarsa suka dawo. Akwai ɓuƙatar ya fara ganin Orthopeadic surgeon likitocin da suka kware fannin ƙashi, da kuma Neurosurgeon waƴanda suka ƙware  fannin ƙwaƙwalwa, sune zasuke dubashi duk bayan sati ɗaya zasuna mishi aiki na tsawon sati uku,  alluranshi da magungunan shi da aikin likitocin duk na sati ukune, sai bayan wata ɗaya zamu sake dubashi daga nan kuma sai bayan wani wata ɗayan zamu kuma dubashi." Gaba ɗaya duk sunji baya nan sun kuma gamsu sosai ya ƙara yi musu bayani, Nan Ameena ke tambayarsu za'a iya bata alluran su tafi dashi masauƙin su, in yaso ita ta rinƙa yi mishi sai bayan sati satin su rinƙa zuwa likitocin na dubashi, Sun amince da hakan sun bata dama, Dr. Malik da kanshi ya maidasu masauƙinsu. Wonka yayi kana ya canza kaya, itama wonka tayi ta canza kaya, sannan sukazo suka konta zuciyoyinsu fal farin ciki, A hankali yace. "Ameena miƙo min wayata sati guda banyi magana da Ummina ba". Miƙewa tayi ta ɗauko mishi wayar kana tazo ta miƙa mishi, Number Umminshi ya kira da layinshi nan ƙasar India. A can gida Nigeria kuwa  kasancewar da yamma ne duk  suna zaune a falon Ummi, Raliya nata cakuɗa gashin Zaleeha wai zatayi mata kitso. wayar Ummi dake gefensu ne ta fara ringing, da sauri Raliya ta miƙe da wayar a hannunta tana cewa. "Ummi ga wayarki anata kira". ta ƙarishe mgnar tana shiga ɗakin da sauri ta amshi wayar tana ta amsa kiran jin muryar Saifuddeen ne yasata cewa. "Alhamdulillah babana Alhamdulillah Allah abun godiya". Shi dai sai murmushi yakeyi. "Babana ya jikinka, ya bayan dai yau sun fito da kai kenan?". Murmushi yayi tare da cewa. "To Ummi kaddai wata taji kina magana dani, gwara ki koma ɗaki musha hirarmu ba wanda ya sani". Dariya tayi tare da cewa. "Ba kowa kusa dani sai Raliya itama ta fita, wacce kake ɓoyewa lafiyar taka duk ta sauya tunda kuka tafi tasa damuwa a ranta,  kullum a ƙalla sai tayi maganarka kaida Adeel sau biyar ko sau bakwai". Murmushi yayi mai kama da dariya kana yace. "Uhum ashe ana sonmu?". Dariya sosai Ummi tayi tare da cewa. "Sai an gaya maka".Dariya yayi kana yace. "To Ummina ya gida ya ayyuka ina auta, ya Raliya Ahmad ya tafi ko, an kai kayan auren Ishaq ko, ansa ranar bikinne?". Ya ƙarishe maganar yana ɗaura kanshi akan cinyar Ameena. Hannu tasa tana shafa fuskarshi. Ummi kuwa cikin dariya tace. "To wacce tambaya ɗaya zan amsa maka?". A hankali yace. "Ummi duka". Cikin jin daɗi ta zauna bakin gado tare da cewa. "Gaya min tukuna ya bayanka?". Dariyar shagwaɓa ya ɗanyi tare da cewa. "Ummi baya yayi garau, ina zamana yadda nakeso, ba ciwon baya". Nan yayi mata bayanin da likata ya musu. Sun dade suna hira kafin Hayatuddeen ya shigo nan ta bashi suka gaisa. Hakama ta bawa Raliya dan Lokacin Zaleeha ta tafi ɗakinta, sun daɗe suna hira kafin sukayi sallama, har zai katse kiran yaji Ummi na cewa. "Kayiwa ƴarinyar nan magana fa kota WhatsApp ko hankalinta zai ɗan konta". Cikin jin daɗi yace. "To Ummi yadda kikace haka za'ayi". Daga nan yayi sallama da ita. Ahmad ya kira suka sha hira kana ya kira Ishaq. Ya Adnan kuwa shi yayiwa Adda Rahma bayanin komai, sosai yayi ta kiran ƴan uwanshi da abokanshi. Kafin ya gama wayar magriba tayi. Shafa fuskar Adeel daketa bacci yayi yatashi zaune ya kalli Ameena yace. "Kin barshi yana baccin yamma kin sanshi sarai anjima zai tasomu gaba ya hanamu bacci". Miƙewa tayi tare da cewa. "Ya zanyi na hanashi na hanashi yaƙi". Kai ya jinjina kana ya hau kekenshi ya nufi bathroom. Bayan sun idar da sallan magriba zama sukayi kan sallayan dan  yin azkar. Har saida lokacin isha yayi sannan sukayi sallan ishan, daga nan sukaci abincin da Ameena tasa aka kawo musu. Wonka ta shiga dan yin shirin bacci bayan tayi wonka ta fitone ta tsaya tana kallon Adeel da sai yanzu ya tashi daga baccin yamman sai jujjuya kai yake a kan gado, babanshi nata ɗaukan shi  hoto, cikin sanyi tace. "Oh ni Aminatu yanzu Adeel ina shirin bacci kai kuma kana farkawa?." Shafa kanshi Saifuddeen yayi tare da cewa. "Kizo ki bashi nono yasha kiyi mishi wonka da ruwan ɗumi sosai wata ƙila zai maida baccin". Isowa tayi tsakiyar ɗakin tare da cewa. "Uhmmm Adeel ɗin ai wlh da nasanima da na barshi wurin Ammin shi." Kissing goshin yaron yayi kana ya shiga wonka, Mai ta shafa tare da feffesa turare kana ta kimtsa cikin wasu  kayan bacci masu kyau da taushi, tana gama shiryawa yana fitowa wonka, shafa mai ya ɗanyi kana ya gama jikinsa da turare kayan baccin da take miƙo mushi ya amsa tare da cewa. "Sannu". Cikin jin daɗi tace  "Yauwa". Riga da wondo ne masu taushi farare ƙal-ƙal. Yana gama kimtsawa ya hau kan gadon. Ita kuwa tana ƙasa bisa tattausan carpet dake gaban gadon, madara take bawa Adeel ɗin. A hankali ya koma ya kwanta ganin tana hidiman yaron su. Wayarshi ya jawo, data ya buɗe, Sosai yaji saƙonni nata shiga, saida ya bari suka gama shiga kana ya lalubo number Zaleeha "My Happiness"  shine sunan dake liƙe a jikin numbern nata. da sauri ya duba hoton dake jikin dp ɗinta, hotonsu  ne shida ita, wanda a wurin diner aka ɗaukesu, sunyi masifar yin kyau a hoton kuwa, wani irin murmushin ne ya suɓuce mishi, ganin abinda ta rubuta ƙasan hoton. _Ranace mai daraja ranar da inada dama da na maimaimata sau babu adadi a rayuwata_ Assalamu alaikum ya tura mata ganin tana online. sai kuma ya ƙara da cewa. "Wacce ranace haka mai daraja?". Dai-dai lokacin itama Zaleeha a konce take, hotunanshi sun zame mata abin ganinta,  har yau tana son tuno inda ta taɓa ganin makamanciyar fuskarshi. Ganin an mata magana da sabon number  kuma code ɗin India sai tayi sauri ta shiga wurin saƙon. murmushi tayi dan idonta ya hango mata hotonta ita da Adeel a dp wani irin fitinennen daɗi taji dan ta gane shine, Wa alaikassalam ta amsa sallamarshi, tare da cewa. "Waye?". murmushi yayi duk da yasan ta gane sai ya rubuta mata. "Mijinki". Wani irin sanyi taji a ranta cikin kunya tace. "Hamma Saif ina wuni ya jikinka?". "Lfy lau , Alhamdulillah jiki da sauƙi." da haka ya maida mata amsa,          _"ina my love?"_ ta kuma tura mishi dariya ya ɗanyi tare da cewa. _"Na ɓoy eshi cikin boxer ko in fito mikishi ki ganshi ne?"._ Ido ta zaro da sauri tace.   -"A'a Adeel nake nufi"._ juyawa yayi rigingine tare da shafa fuskarshi kana yace. "Gashi can ya hana Mamanshi bacci". "Uhmmm". tace dan kada ta sake wata mgnar ya kuma rarako mata wata mai zafi. Shi kuwa rubutu ya kumayi, inda yace. _"Ya jikinki?"._    a nitse tace. _"Da sauƙi"._       kamar tana gabanshi ya ɗaga gira tare da cewa. _"Da gaske ciwon ya worke?"._ _"Eh da gaske ya worke"._ Tabasa amsa ataƙaice. Murmushi ya ɗan yi kana ya rubuta mata. _"To bari in gayawa mai jiyar da ciwon ya shirya Rafin daɗi kuma koginsa da yafi zuma zaƙi, ya samu sauƙi, mu dawo kawai"._ Ƴar dariya tayi tare da cewa. _"No ban workeba"._ Shima ƴar dariya yayi kana yace. _"Ƙarya ne"._   Kwabe fuska tayi tare da rubuta mishi. _"Da gaskene Hamma Saif"._ hannunshi yasa ya shafi Saif ɗin shi da fara tashi, cikin kasala ya rubuta mata. _"Naƙi ƴarda, sai dai ki turo min hoton wurin in ga zahiri"._ aljanin nan na WhatsApp  wato emoji, mai zare ido ta tura mishi tare da rufe ido, shi kuwa fuska ya ɗan sha tare da cewa. _"Da gaskefa nakeyi, ki turo min inga ciwon dana jiyar ɗin"._ Rubutu tai mishi. _"Ni bani da ciwo a jikina"._ kanshi ya ɗan ɗago ya leƙa Ameena yaga tuni tayiwa Adeel wonka har ta kwantar  dashi kan carpet  alamu so take tasashi bacci, miƙa yayi da kyau saida Saif ɗinshi ta miƙe samɓal, a cikin wondon ta tashi sama kamar zata fasa wonɗon ta fito, hoton wurin ya ɗauka kuma hoton ya fita ras. tura mata hoton yayi tare da rubutu a ƙasan hoton, inda yace. _"Abokinki na gaisheki, kuma yace yayi missing ɗinkin"._ Tana ganin hoto ta danna buɗewa dan ita a zatonta hoton Adeel ne, tana buɗewa taga abu him, da sauri ta rufe idonta, tare da ajiye wayan agefe. Shi kuwa Saifuddeen chat ɗinshi da ita ya gigitashi, a hankali ya fara kiran. "Ameena! Ameena!! Ameena!!!". Cikin ɗan baccin daya fara ɗibanta tace. "Na'am Abban Adeel". miƙa yayi tare da cewa. "Yayi baccin ne?". Cikin sanyi tace. "Eh yayi". Kanshi ya ɗan maida tare da cewa. "To barshi a wurin kizo kiji dani". A hankali ta miƙe hannunshi yasa ya kamo nata hannun. kan Saif ɗinshi ya ɗaura hannunta tare da cewa. "Yaƙi muyi bacci, yace dole in kira mishi aminiyarshi". raɓawa jikinshi tayi ta konta cikin sanyi tace. "Uhummm". Shi kuwa jawota jikinshi yayi da kyau  a hankali ya zare kayan jikinshi da nata, cikin sanyi yace. "Taimaka kar ya tsinke". Ya ƙarishe maganar yana haɗe bakinsu, sosai suka shigewa juna, suna gudanar da romance. Zaleeha kuwa  kife wayartata tayi akan ƙirjinta da haka  bacci ya ɗauketa. Su Ameena kuwa, washe gari da safe bayan sun gama karyawa, ta haɗa ruwan alluranshi tazo ta sameshi a  zaune a falo yana ganinta da allurar ya kwaɓe fuska, dariya tayi tuno yadda sukayi jiya da yamma hannu yasa ya ɗan janye rigarshi yace. "Zo kiyita, naga daɗi kikeji in zakimim allura, kiyi yadda kike min allurar haka nima zanyi ta miki tawa allurar, dan yadda zata ƙarawa ƙashin bayana ƙarfi haka take ƙarawa ko wacce jijiyar jikina ƙarfi." Dariya tayi bayan ta mishi allurar tace. "Ato ai dai ni ba raguwa bace". Kanshi ya gyaɗa alamar zanyi maganinki a zuciyarshi kuwa cewa yake. "Kin saba shiyasa ai zaki daure, amma Zaleeha kam da take sabon shiga, sam ba dauriya, harda su suma, well nasan very soon zata saba itama". Haka rayuwarsa taci gaba da tafiya, yau ne suka cika sati da fara alluran, dan haka yau zasuje asibiti ganin doctor. Shiyasa sukayi sammako cikin sa'a kuma suka samu ganin doctor ɗin a sauƙaƙe kusan awa biyu sukayi suna murza mishi ƙashi da jijiyoyin bayanshi dama na jikinshi baki ɗaya, kuma Alhamdulillah jinya na tafiya yadda akeso. Yau kwanansu  goma da fara alluran sunyi kwana 17 kenan da zuwa kuma. Da yamma bayan sunyi sun dawo daga ɗan yawon ganin gari Ameena tazo da Allura tana isa yace mata. "Ina Adeel?." Tace. "Yayi bacci". Kai ya jinjina kana yace. "Muje ciki to". Ba musu tabi bayanshi, suna shiga yace. "Kai Adeel falo kizo". Nanma ba musu ta kaishi tana dawowa tayi mishi allurar, ta juya zata koma falo kenan ya riƙota cikin sanyi yace. "Kinyi taki allurar yanzu kuma ni zanyi tawa". Kamar da wasa taga dafa gaske yakeyi. Sosai ta fahimci yanzune asalin jarabarsa ke baiyana, Zaleeha kuwa kullum sai ya birkita mata lissafi da irin zafafan kalamanshi  ta chat, wani lokacin sai taji kamar ta nitse ƙasa dan kunya. Sun saba sosai. Yana yawan magana da Ummi  har ma da su Ahmad Ishaq dasu Adda Rahma. Randa ya suka cika sati ukun ya gama alluran likita yace yanzu sai bayan wata ɗaya zasu kuma ganinshi. nan yace likita, shi zai koma, saboda baison sake ƙara wani wata ɗayan a India. To basu hana shiba tunda ya nuna musu yanada babban uzurin da zai koma yayi. Alhamdulillah Hayatuddeen da Khamis sun nitsu sosai yanzu babu ruwansu da fitina, karatunsu kawai sukeyi, ko chat din kirki ma basayi, saidai time to time always karatu kawai suke, sannan abotansu kuma ya ƙara ƙarfi. Ummi kuwa wani sabon yanayi take gani tattare da Zaleeha, sam bata da kuzari kamar da. Kana bini-bini tasha tea, abinci kuwa sai ta girka kowa yaci amman ita sai dai tasha tea, koda Ummi ta tambaye ko bata da lfy ne, tace lfyarta lau sabida, bawai wani ciwo takejiba. Auren Ishaq da Rashida kuwa Ishaq yace baza'asa rana ba sai amininshi ya dawo, dan acewarsa Saifuddeen ɗan uwa rabin jikinsa ne. Yau tun safe da suka dawo ganin doctor ɗin sukayi wonka suka fita Suka jejje wuraren shaƙatawa da wuraren sayayya, nanne a yawace-yawacen nasu yaga wani babban asibitin ido _Shroff eye sentre New Delhi_ daga nan yayi niyar insha Allah zai kawo Ishaq ɗinsa. Basu koma masauƙinsu ba sai dare. Wonka sukayi kana suka konta dan dama sunci abinci a wojen, Kiran Ishaq yayi bayan sun gaisa yace. "Ishaq next week fa zamu dawo, asa bikin aure nan kusa, dan inaga bayan wata ɗaɗɗayan da sukace in dawo da kai zamu dawo dan naga wani babban asibitin ido  sunada manyan ƙorarrun likitoci zasu duba min kai". Dariya ishaq yayi tare da cewa. "Uhum ɓarnan kuɗi ko, koda yake baifi musha amarci a nanba nida Rashida na". Dariya ya ɗanyi tare da cewa. "Oho muku ni dai likitan ido zan kawoka ka gani ba cin amarci ba". Dariya sukayi baki ɗaya kana sukaci gaba da hira. Bayan sun gama hirar ne ya taɓo Zaleeha, tana chatting da Rashida ne taga mgnarsa ta shigo. "Salama Boɗɗin kinyi bacci ne?". Murmushi tayi dan tun kafin aurensu da akace mata shine Malam Saifuddeen, ɗinta bata wani tuno komai a kanshiba sabida lokacin tana ƙarama, ko sunanshi bata iya kira da kyau sai dai tace Malam Caifuddeen shi kuma yana kiranta Boɗdi na,  wato kyakkyawata kenan. to kiranta da sunan da yayi yaune sai wasu abubuwan suke ɗan dawo mata na ƙuruciyarta. cikin murmushi ta rubuta mishi. "Na'am Malam Caifuddeen". murmushi yayi sosai wato ta tuno haka take kiranshi dariya yayi tare da cewa. "Bani haddar dana baki inji kin itane?". Murmushi tayi cikin jin daɗi tace. "To Malam Caifuddeen in na iya zaka saya min sweet?". Shauƙine mai ƙarfi ya rufesu domin sun tuna baya can lokacin tun yana magana bai kuramce ba, lokacin shekaranta 5 shi kuma 13. Da sauri ya rubuta mata. "Eh zan baki Boɗɗi na karanta min inji". Ido ta lumshe tare da rubuta mishi. "To Malam Caifuddeen bani sweet ɗin a hannuna tukun". A lokacin in tace hakan sai ya bata sweet din yanzu kuma sai ya rubuta mata. "Sai na dawo zan baki sweet ɗinki kisha ki more yanzu yana cikin wondo sai motsi yakeyi yaji muryarki kin ganeshi ai yanada zaƙi ko?". A kunyace tace. "Sai da safe". Da sauri yace. "Karki wani ce saida safe nasan kema yanzu kina tsiyaya, dan jinina da naki iri ɗaya ne duk yanayin da nake ciki kina ciki, tun kina karama ko zazzaɓi kikayi sai nayi, kece kika raɓa min baƙon daura da zazzafin sankarau har suka sankaremin kunne da maƙogoro, so nasan duk motsin bugun zuciyarki". Cikin sanyi tace. "In sha Allah zaka samu lfy". Da sauri yace, sabida kuma ni kurmane akace ba'a sona. Alhalin kecema sanadin kuramtar". Da sauri tace. "Waya ce maka ba'a sonka?". Gyara konciyarsa yayi tare da cewa. "Ke mana bakya son Nakasasshe". Da sauri tace. "Wallahi Wallahi wallahi baki uku kenan narantse da mahaliccina ni ban ƙika da Nakasarkaba". "To don me kima ƙini harda guduba?". Cikin sanyin jiki tace "Saboda wani daliline da kuma yin halacci ga wanda ya sadaukar da rayuwarsa a kaina". Da sauri yace. "Kada ki sake kira min wani, ba dai bakya sonaba?". Da sauri tace. "Ina sonka mana!". Saida har ta tura text ɗin kuma sai tai maza ta goge dan bata san ya akayi ta rubuta hakan ba. Shi kuwa dariya yayi dan tuni yaga saƙon, cikin jin daɗi yace. "Sai na dawo ki nuna min zahiri, in baki minti mai madarar nan kisha minshi sosai". A hankali tace. "Allah ya dawo da kai lfy". Amin Amin yace kana ya ɗaura da cewa. "Zaki sha ko?". Cikin kunya tace, "Duk abinda zai saka farin ciki ko jin daɗi zan makashi Malam Caifuddeen". Dariyar jin daɗi yayi tare da cewa. "To tashi kije kiyi tsarki da ruwan ɗumi kizo ki kwanta dan nasan dai yadda nake haka kike gwara ni ga wata kusa dani". Wani abu taji a ranta mai zafi, kishi kumallon mata cikin kishi tace. "Sai ka cinyeta ai". Tana faɗin haka ta rufe data. Shi kuwa Saifuddeen dariyar jin daɗi yayi shi kanshi ya yasan Zaleeha na sonshi amman bai gamsuba, kuma yafi son ta soshi a kurma gurgu, shiyasa yake ɓoye mata lfyarshi ta soshi a nakasasshene da izina ne ga mutane shima Nakasasshe yana da damar da zai nemi zazzafar macce, kyakkyawa yar gayu wayayya kuma ta soshi kamar sauran lafiyayyu dan NAKASA BA KASAWA BACE. Cikin ɗan bacci Ameena taji yana shasshafata, a hankali ta juyo, ta shige jikinsa, hannunta ya ɗaura kan Saif ɗinshi a hankali yace. "Sorry har kinyi bacci na tada ke ko? Yaƙi muyi baccin ne". Kai ta gyaɗa mishi cikin sanyi tace. "Jikina ba ƙarfi Abba Adeel bazan iya maka yadda kakesoba". gyara mata konciyarta yayi tare da yunƙurawa yayi mata rumfa. Ida nunta ta buɗe da kyau jin wani sabon lamari yau shida kanshi zaiyi abinda bai taɓa yiba. Yunƙurowa tayi zata tashi da sauri ya meda ita tare da cewa. "Barni mana hanani zakiyi ne?". Cikin sanyi tace. "A a to amman zaka iya n...". Wani irin fitinenne rugguma tayi mishi tare da haɗiye regowar magarta jin yadda ya ratsata. wani irin sakalin nishi tayi tare da cewa. "Wayyyyyyy Abba Adeel zan mutu". Shiru yayi a jikinta tare da cewa. "Shiii bazaki mutuba". a hankali ya kuma sarrafa ɓalgaceccen ƙugunsa da ya fara miƙewa, da ƙarfi ta kuma sakin nishi. "Ohhhhhhh numfashina zai gudu". gyara kinciyarsu da kyau yayi tare da fara fatauci da zafin nama. cikin wata duniya da Ameena taji kanta ta saki wani kuka tare da surutai. "Wayyo Abba Adeel dama ka iya haka". zuwa yanzu shima nishi yake, sama sama yake ɗan fitarda numfashi. gaba ɗaya ya gigitata sai yau Ameena tasan ashe da kam duk shafa-shafa sukeyi tunda duk gwazonta bata wuce minti 30 ashe ba isanshi takeyiba tunda gashi yanzu da yake da kanshi yayi 1hour cas yana fatauci". Koda suka gama wonka sukayi kana suka konta. Washe gari da safe sai tsiya yake mata wai taji kayan aiki harda masa ihun daɗi dariya tayi ta sunkuyar da kanta. Ranar ya gayawa Ummi sati mai zuwa zasu dawo ranar al'hamis kenan. Ranar ne kuma Ummi ta ƙara zarginta kan ko Zaleeha nada ciki, dan sosai alamun ciki suka baiyana a jikin Zaleeha tayi fiyau da ita. Cikin mmki Ummi ke mgnar zuci lokacin da ta karewa Zaleeha dake fita kallo. "To anyama kuwa tasan tanada ciki? To in ma dai ta sani Babana bai saniba dan nasan tabbas in ya sani zai gayamin". Wayarta ta kuma jawowa da niyar zata kirashi sai kuma ta fasa tare da cewa. "Tunda sati mai zuwa zasu dawo bari sai sun dawo muyi mgnar". Sabida ita kanta bata gama tabbatarwa ciki bane tana dai zatone. Haka kuwa ranar Al'hamis da la'asar jirginsu ya sauƙa a babban birnin taraiya. Ƙarfe huɗu dai-dai kuma jirgin da zai kaisu gombe ya tashi. A nan gida Gombe kuwa anata shirin tarbansu.... *Kuyi haƙuri dan Allah akan rashin jina da wuri wlh wani babban uzurine ya tsareni* *Wannan shafin nakane kai ɗaya ban haɗaka da kowa ba, YUNUSA ADAM LAPAZEEE lallai kam sunanka yayi dai-dai tsananin harcenka. Da farin duk wacce ta karanta HUKUMCIN ALLAH tasan sunan da nasawa wannan littafin a yadda nai tallanshi Babu Nakasasshe sai rago, shine ya canza sunan labarin da LAPAZEEN'nshi ɗaya tak ya canza min sunan littafin bai yi daɗi. Bama dashi naka mgnarba amman buɗar bakinshi sai cewa yayi kisa. NAKASA BA KASAWA BACE! a take kuma zuciyata ta yarda da kaifin lafazinshi, domin kalmar daya bada ɗin itace tafi dacewa da sunan lbrin, sai da nai tambaya anka ce min sunanshi YUNUSA ADAM (LAPAZEE) nace lallai ya amsa sunanshi (Lapazee), yayi zarra a fagen sarrafa harshe aminanshi, abokanshi, dama maƙota sukace Dai-dai tacciyan (LAPAZEE) ne kaɗai ke fita a bakinshi duk sanda yayi mgna ko anƙi mgnar da forko daga bisani sai an bita, sabida mafi akasari in yayi mgna sai abin ya tabbata a yadda yace ɗin, hakan yasa suka saduda cewa Allah ya mishi baiwar harshene da tsabtatettun (LAPUZU,) shiyasa inkiyar sunanshi ya kasance (LAPAZEE) ya zama kamar shine ma sunanshi. Fatan al'khairi a gareka Yususa Adam Lapazee dan ka bada babbar gudumowa sunan littafi nan, GARKUWA na al'faharin kasancewar abokin ƙaninta, Allah ya rayaku ya inƙanta rayuwarku ya sanya al'barka a lamuranku, na sadaukar da wannan shafin gareka Lapazee gaba ɗayanshi* Acan Gida ɓangaren Zaleeha kuwa, sanin cewar yau zasu dawo yasa tun safe bayan tayi breakfast ta shiga side ɗin Hamma Saif ɗin, ta kimtsa masa bedroom ɗinsa, da falonsa bathroom, ta gyara komai tsab tsab, ta canza mishi sabon zanin gado wanda yake cikin sabbin zannuwan gadonta ne sannan ta feshe ɗakin da airfreshener me daɗin ƙamshi, sanyinsa har ratsa zuciya yake. Jawo ɗakin nasa tayi ta rufe, sannan ta koma sashinta. Kayan jikinta taɗan rage, towel ta ɗaura sannan ta shige bathroom, bayan ta haɗawa kanta ruwan wanka. Kwanciya tayi acikin bathtube tare da ɗan lumshe idanunta, wani irin diffrent feeling takeji akan Hamma Saif ɗin, bazata iya faɗin yaushe ne ko kuma ta yayane ta fara jin wani abu dangane dashi acikin zuciyarta ba, saidai kuma tasan koma menene ayanzu babu abun da take so da ɗokin gani kamar shi, so take ta kalli kyakkawaar fuskarsa da ta jima bata gani ba, sannan ta kuma kalli kyawawan idanunsa masu tsuma mata zuciya. Cikin nutsuwa tayi wanka'n, sannan ta fito daga cikin toilet ɗin. Agaban dressing mirror ta zauna, tare da jawo body lotion ɗinta ta shafa, sama sama taɗan murza fowder akan fuskarta, kana ta goga kwalli da kuma lipstick me kalan pink. Tashi tayi tare da ƙarasawa gaban drawer'nta, wata baƙar abaya gown ta zaro wanda taji adon stones, koda ta sanya, da ɗan kwalin abayan ta yane kanta, sosai tayi kyau, duk dama ba wani meckup tayi ba. Flat shoe ɗinta kawai ta zura, ahankali ta murda handle ɗin ƙofar ta fita. Kai tsaye sashin Ummi ta nufa. Da sallama ɗauke abakinta ta shiga falon, rashin ganin Ummi afalon yasa kai tsaye ta nufi ɗakin Ummin. Ɗan knocking ɗin ƙofar tayi. Daga ciki Ummi ta bada go ahead ɗin shigowa. Hakan yasa ahankali ta tura ƙofar ciki, ta shiga bakinta ɗauke da sallama. A zaune Ummin take akan gado, Raleeya kuwa fitowarta kenan daga cikin bathroom ɗin Ummin, da alama wanke mata tayi. Ganin Zaleeha yasa Ummi sakin murmushi. Ƙarasowa cikin ɗakin tayi, tare da ɗan durƙusawa agaban Ummi'n, cikin girmamawa tace. " Ummi dama inaso ne naje saloon, shine nace bana tambayeki idan kin barni sai naje." Murmushi Ummi tayi cikin kulawa tace. "Haba Zaleeha idan zakije saloon ɗin kuma sai kin nemi izinina, ai idan dai mijinki ya yardan miki kije kawai." Ƙasa ta ɗanyin da kanta, cikin wasa da ƴan yatsun hannunta tace. "Shine yace duk inda zanje ina tambayanki, idan kinbarni sai naje." Murmushi Ummi tayi, tare da jinjina kanta, fuskarta ɗauke da zallan fara'a tace. "Na amince miki, kije saloon ɗinki, Allah ya kiyaye hanya, akwai Sule driver, nasan zai kaiki ko kinaso kiyi driving da kanki?." Raleeya ce tayi carab ta cabke maganan cikin sauri tace. "Ummi dan Allah nima zanje, dama two days ban yi saloon ba, kinga idan yaso bama sai Sule driver ya kaimu ba, ita zatayi driving ɗinmu ko?." tafaɗa tana kallon Zaleeha'n. Kai Zaleeha ta jinjina mata tana murmushi, dan taji daɗin hakan, saboda itama bawai tanason fita ita ɗayan bane, dan ance wata tafiyar bibbiyu tafi dadi. Murmushi Ummi tayi tare da cewa. "Kai Raleeya son yawo, to shikenan ai saiki tambayi mijinki idan ya barki ƙofa abude take." Cikin zumuɗi Raleeya tace. "Ai namasan zai barni, bari naje na ƙirashi a waya." taƙare maganan tana me fita waje. Zaleeha na ƙoƙarin miƙewa, Ummi ta zage zip ɗin jakan dake aje gefenta, kuɗi ta ciro wanda aƙalla zasu kai 10k miƙawa Zaleehan tayi, murya atausashe tace. "To gawannan sai ki biya saloon ɗin dashi." Idanu Zaleehan taɗan zaro tare da cewa. "Ummi ai kuɗin sunyi yawa." Murmushi Ummi tayi, tare da girgiza mata kai, cike da ƙauna tace. "Idan Raleeya ne na bata, bazata ce sunyi yawa ba, saboda haka kema banaso kisake faɗin haka, ki amsa maza ku tafi sai kundawo, sannan kuyi driving a hankali." Cikin mutuntawa tasa hannu ta amshi, kudin tare da yiwa Ummin godiya, sannan ta fice daga cikin ɗakin, taji daɗin kuɗin da Ummin ta bata, duk da cewa ma tana da kuɗi, amma duka basu wuce 12k ba, dan koda Saifuddeen ma yace da ita, akwai kuɗi a drawer ɗinsa, idan tana da buƙata ta ɗauka, sam bata ɗauka ba. Tana zama afalo kuwa Raleeya ta fito itama cikin shirinta na doguwar riga, saidai nata me kalan ja ne, dan ta tambayi Ahmad ya barta, dama shi bame hana fita bane. Atare suka fito compound ɗin gidan, zuƙeƙiyar motar Saifuddeen ƙiran mercedess benz Zaleehan tasawa key ɗin data ɗauko a ɗakinshi ta buɗe musu, Zaleehan ne ke driving, Raleeya kuwa na gefen me zaman banza, me gadi ne ya wangale musu gate ɗin gidan suka fice. Kaitsaye babban shagon saloon ɗin da Zaleehan ta saba zuwa suka nufa, suna zuwa kuwa akayi musu saloon ɗin, harma da wankin ƙafa akayiwa Zaleeha. Basu wani ɗau lokaci ashagon ba, kwata kwata basu wuce 1hour and 30minute ba, aka kammala musu komai. Koda suka dawo gida kuwa, lokacin har anyi sallan azahar, sallah kawai sukayi, suka wuce kitchine, sosai Zaleeha ta baje basiranta wajen shiryawa su Saifuddeen ɗin abincin tarba me rai da lafiya. Basu gama abincin ba kuwa har tsawon awa 2 harma da wasu mintuna. Koda suka kammala agajiye suke hakan yasa kowacce ta wuce ɗaki taɗan kwanta, Zaleeha kuwa koda aka ƙira sallan la'asar, tashi tayi ta ɗauro alwala, tana idarwa kuwa ta sake komawa ta kwanta. Da misalin ƙarfe biyar da rabi kuwa ta kuma faɗawa bathroom, wanka tayi me rai da lafiya. Tana fitowa ta shafe jikinta da mai haɗi da turaruka masu azababben ƙamshi me kama zuciya, zama tayi agaban mirror tare da tsantsarawa fuskarta kwalliya me kyau, duk da bata cika meckup ɗin akan fuskarta ba, amma tayi kyau sosai, drawern ta ta buɗe, inda ta zaro wani jan yadi na mata me masifar kyau da kuma tsada, dan aƙalla kuɗinsa yakai kusan 30k, ɗinkin riga da sket pieces akayiwa yadin, wanda aka ƙawata gaban rigan da black ɗin stones, sosai kayan suka zauna mata ajiki, sun kuwa fito da zallan kyawun surarta, dogon gashinta ta tubke, kana ta ɗaureshi da ribbom me golding colour, saboda akwai ratsin golding ajikin kayan nata. Wani irin haɗaɗɗen material saree me kalan golding ta ɗan yane jikinta dashi, kasancewar yana da shara shara sosai hakan yasa ko kaɗan bai ɓoye ado da kwalliyan nata ba, saima ƙarawa shigar tata kyau da yayi, dan tafito kaman sarauniya. Ɓangaren su Saifuddeen kuwa ƙarfe 5:40 pm jirginsu ya sauƙa cikin Gombe International Aiport, Ahmad da kuma Ishaq sune waƴanda sukaje tarosu, ƙwarai sun ji daɗin ganin yanda jikin Saifuddeen yayi kyau, suna shiga mota kuwa suka kamo hanyan gida. Acan gidan nasu kuwa, tuni sashin Ummi ya karɓi baƙoncin su Adda Rahama, harma dasu Wareesu, Zakariyya ma yazo suna nan tare da Hayatuddeen da kuma Khamis. Horn ɗin motarsu da Zaleeha taji alaman cewa sun iso, yasa ta cikin sauri ta ƙarasa jikin windown ɗakin nata, ɗan yaye labule tayi waiko zata hangosu, amma gaba ɗaya shuke shuken dake wajen sun hanata ganinsu, hakan yasa ta koma cikin nutsuwa ta cigaba da kimtsa kanta. Saifuddeen kuwa, sashin Ummi suka wuce, baƙaramin farinciki Ummi tayi ba da ganinsa, musamman ma yanda taga jikin nasa ya miƙe ya samu lafiya, yana zaune abunsa, yasake kyau da burgewa, da'alama bashi da wani abun dake damunsa. Shima yaji daɗin ganin Ummin nasa sosai. Gasu Adda Rahama da farincikinsu ya kasa ɓoyuwa. Zaleeha wanda ta fito daga sashinta, ahankali take tafiya tamkar wata tauraruwa, tayi kyau matuƙa, ƙamshi ne kawai ke tashi ajikinta, kaman wanda akayiwa ɓarin turare. Tun isowarta kusa da sashin Ummin take jiyo surutan su Raleeya da kuma nasu Ishaq, idanunta taɗan lumshe sannan ta murɗa handle ɗin ƙofar, cikin ƴar siririyar muryarta tayi sallama anutse ta shigo cikin ɗakin, jin daddaɗan muryarta ya sashi juyowa, sauƙe idanunsa da yayi akan kyakkyawar fuskarta yasa shi ɗan lumshe idanunsa, zuciyarsa ce ta amsa saboda yanda yaga tayi kyau sosai. Wani irin lallausan murmushi ya sakar mata, tare da ɗan sake lumshe tsumamun idanunsa. Itama idanun ta lumshe dan ganinsa, yasa taji wani irin sanyi acikin ranta, ƙarasowa cikin falon tayi, kaitsaye wajen Ameenah ta nufa, fuskarta ɗauke da murmushi tace. "Barka da dawowa Ummun Adeel ya hanya?". Murmushi Ameena tayi tana meƙarewa Zaleehan kallon dan ko ita kanta, tasha jinin jikinta da kyawun Zaleehan. Cikin sakin fuska tace. "Yauwa Ammin Adeel, sannu da gida, hanya kam munshata saidai gajiyan zama da kuma ciwon jiki, shima nasan asannu zai watse." Murmushin Zaleehan tayi tare da sanya hannu ta ɗauki Adeel da tun shigowarta yake ta wuntsil wuntsil da hannunsa, yanaso yazo wajenta. Rungumeshi tayi tanayi masa wasa, ɗan juyowa tayi inda Saifuddeen ɗin ke zaune taɗan saci kallonsa, idanunsune suka gauraye acikin na juna dan dama shidinma kallonta yake, saurin lumshe idanunta tayi, asanyaye cikin daddaɗan muryanta tace. "Sannu da dawowa ya jiki?." Shiɗinma idanunsa ya lumshe saboda yanda yaji zazzaƙan muryarta ta ƙara daɗi, ga kuma ƙamshinta da gaba ɗaya ya cika masa hanci. Kansa ya jinjina mata alaman lafiya, tare da binta da wani irin fitinannen kallo, mai ɗauke da zallan kewa da kuma ƙauna. Zama tayi agefen Zakariyya da kuma Hayatuddeen, sama sama take ɗan satan kallonsa, dan baƙaramin kyau taga ya ƙara ba, shiɗin ma dai satan kallonta yakeyi, dan tayi masa kyau sosai. Basu wani jima afalon Ummin ba, aka soma ƙiran sallan magriba. Saida ya koma part ɗinsa yaɗan watsa ruwa sannan ya wuce masallaci, Zaleeha kam kasancewar tana da alwala anan part ɗin Ummi tayi nata sallan ita da Raleeya, dan Ameena ma tatafi part ɗinta saboda tanaso taɗan watsawa jikinta ruwa. Basu dawo daga masallacin ba saida akayi sallan Isha, atare dukansu dasu Ishaq suka dawo daga masallaci, nan falon Ummi suka baje, Zaleeha da kanta ta jere musu gaba ɗaya abincin da ta girka musu kala, da kuma drinks. Ita da kanta tayi seving ɗinsu, duk motsin da zatayi kuwa akan idanunsa, dan baya ko ƙaunar ɗauke idanunsa akanta. Atare suka zauna dukansu sukaci abincin, hira sukeyi sosai, saidai duk acikin hiran nasu, Saifuddeen da body language yake magana, kasancewar Zaleeha na wajen. Suna kammala cin bincin, Zaleeha ne ta tattare wajen, ɗaukan Adeel tayi ta ɗaura akan kafaɗanta, sannan ta fice daga cikin falon. Tana fita Ahmad ya saki dariya tare da ɗan dukan kafaɗan Saifuddeen ɗin cikin yanayin tsokana yace. "Kurman dole." dariya sukayi dukansu, ahankali yaɗan ja jikinsa tare da kwantar da kansa akan cinyan Ummi, hannu Ummi takai tana shafa gashin kansa, cikin kulawa haɗi da soyayyar dake tsakanin ɗa da uwa tace. "Babana sannu ko, yanzu ya jikin naka." Akasalance haɗi da zallan shagwaɓa yace. "Da sauƙi sosai Ummina, yanzu ina iya kwanciya, da kuma tashi aduk sanda nakeso, banajin ciwon komai." Murmushi Ummin tayi cikin jin daɗi tace "Masha Allah. Allah Ubangiji ya ƙara maka lafiya da nisan kwana, ya kuma sa nan bada jimawa ba ka tsaya akan ƙafafunka." Gaba ɗayansu da Ameen suka amsa, hira suka taɓa sosai, sai wajajen ƙarfe 9 sannan su Ishaq dasu Saleesu suka tafi, Hayatuddeen kuwa shida kansa ya maida Zakariyya gida. Adda Rahama ma Dr.Adnan ne yazo ya ɗauketa, ita dasu Farouq, haka dai duk suka watse gidan ya zamana saura su kaɗai, Hayatuddeen da ya dawo daga kai Zakariyya gida, shi ya kwashi trollys ɗin Hamman nashi, ya fita dasu dan kai masa part ɗinsa. Yana dawowa daga kai kayan kuwa, ya baje atsakiyan falon tare da ɗagowa ya kalli Hamman nasa, ɗan marairaice fuska yayi tare da cewa. "Hamma Saifuddeen kaga part ɗinka kuwa? wallahi komai tsab tsab, sai sheƙi yake, Adda Zaleeha ta gyara maka komai, ga ƙamshi da sanyi kaman karna fito, amma da yake babu wanda ba a damu dashi ba kamanni, haka akabarmin ɗakina kaca kaca kaman turken jaki, bayan kuma kune kuka ɓata." ya ƙare maganan yana me ɗan turo bakinsa gaba. Dariya suka sa masa su dukansu, cikin dariya Ameena tace. "Ya isa kwantar da hankalinka tunda Ammin Adeel ta gyara masa nima zan gyara maka naka." Murmushi ya ɗanyi tare da cewa. "Yauwa dayafi kam, dan ai dama kune kuka ɓata." Murmushi sukayi dukansu, daga haka suka ci gaba da hiransu, sai wajajen goma sannan dukaninsu suka watse daga sashin Ummin, Kowa part ɗinsa ya nufa, Ameena ma sashinta ta wuce, saboda tanaso ta bar Saifuddeen ɗin suɗan gana da Zaleeha. Saifuddeen kuwa, yana komawa part ɗinsa kwanciya yayi, idanunsa yaɗan lumshe yana jiran zuwan Zaleeha ko kuma Ameena da ya zati zata zo ta mishi saida safe, jin shiru har kusan 11 babu ɗaya daga cikinsu yasa shi gyara kwanciyarsa tare da ɗan lumshe idanunsa, kasancewar akwai gajiya ajikinsa, jiyasa yayi lib yana tsumayin Zaleeha, mintuna kaɗan bacci ya ɗaukesa. Ɓangaren Zaleeha kuwa tana shiga sashinta kayan bacci ta sanya sannan ta kwanta, zuciyarta cike take da saƙe-saƙe kala-kala, tabbas tanason kasancewa dashi, saidai kuma haka ta samu kanta da kasa zuwa wajensa, idanunta ta lumshe tuna kasantuwarsu na ranan yasa taji wani irin feeling na taso mata. Idanunta ta lumshe, tare da soma sauƙe ajiyar zuciya, bata wani jima tana tunaninsa ba, bacci ɓarawo ya ɗauketa. Washe gari da sape kuwa kusan atare Saifudeen da Ameena suka shigo sashin Ummi, Raleeya na kitchine, Zaleeha kuwa itace ke zaune afalon Ummi, dan Ummi tana ɗakinta bata fito ba tukum, Bayan Zaleehan sun gaisa da Ameena ne taɗan saci kallonsa asanyaye tace. "Ina kwana." Sam bai amsa mata ba, saima kallonta da yayi ya kuma ɗauke kai, haka taji wani iri acikin ranta, amma saita ɗan kawar da tunanin abun, kusa da ita Ameena ta zauna, hakanne yasa ta sanya hannunta ta ɗauke Adeel.Idanunta ta lumshe, tare da soma sauƙe ajiyar zuciya, bata wani jima tana tunaninsa ba, bacci ɓarawo ya ɗauketa. Washe gari da safe kuwa kusan atare Saifudeen da Ameena suka shigo sashin Ummi, Raleeya na kitchine, Zaleeha kuwa na zaune a falon, kasan cewar yanzu ta fito ɗakin Ummi Bayan Zaleehan sun gaisa da Ameena ne taɗan saci kallonsa asanyaye tace. "Ina kwana." tura bakinshi yayi tare da kauda fuskarshi ba tare daya amsa mata ba, saima kallon Ameena da yayi ya kuma ɗauke kai, haka taji wani iri acikin ranta, amma saita ɗan kawar da tunanin abun, kusa da ita Ameena ta zauna, hakanne yasa ta sanya hannunta ta ɗauki Adeel, wasa ta somayi masa tana ɗan jagwal gwalasa, dubansu Saifuddeen ɗin yayi, tare da ɗan ɗaure fuska, cikin body language ɗinsa yace. "Ba ruwanku dani". cikin mmki Ameena ta kalleshi fahimtar abinda yake nufi yasa cikin kula tace. "Ba ruwanmu da kai kuma? Me mukayi?". Fuska ya tsuke dan sosai abinda sukayi mishi ya ɓata mishi rai, ganin yadda ya haɗe fuskane yasa Zaleeha ɗan kallonshi ido cikin ido, haɗe fuska ya kuma yi tare da mata wani irin kallon mai wuyar fassara wa. Ameena ce ta kuma cewa. "Kayi haƙuri Abban Adeel me mukayi?". Rubutu yayi a wayarshi kana ya juyo musu fuskar wayar. "Kun san abunda kukayi ai! Kun kyauta, hakan yayi dai-dai ku tafi ku barni ni kaɗai a ɗaki kamar gouro mara mata, ace ina da mata biyu amman dan ba sona kukeyi ba, shine ku duka babu wacce ta leƙani kun barni ni ɗaya kamar mara gata". Sosai fa ya nuna ɓacin ransa, Ameena kuwa ido ta ɗan zaro cikin sanyi ta kalli Zaleeha tare da cewa. "To Abban Adeel ni kuma me laifina a ciki? Wata biyu har kusan uku muna tare, tunda mun dawo gida ai sai in ɗan huta tunda bani ɗaya bace". Kai ya jinjina mata alamar. "Yes yayi kyau ki huta tunda ni jidali na zame muku". Da sauri ta jujjuya kai tare da cewa. "Am so sorry ba haka nake nufiba". Sai ta kuma kalli Zaleeha data maida hankalinta kan Adeel cikin sanyi tace. "Ammin Adeel meyasa? Zaki barshi shi ɗaya, dole yanada buƙatar kulawarmu, Please karki sake yin haka". Kanta ta gyaɗa ba tare data kallesu ba, shi kuwa Saifuddeen kwaffa yayi ya nufi ɗakin Ummi. Su kuwa ƴar hira suka ɗanyi kana suka miƙe suka taya Raliya ƙarisa aiyukan, Bayan sunyi breakfast ne, duk suka dawo falon Ummi, suna ɗan taɓa hira. Ameena nace ta ɗan miƙe cikin sanyi tace. "Ammin Adeel ga Adeel mana bari inje in ɗan yi bacci". Cikin sanyin da kallon da Saifuddeen yake mata ya sakarmata tace. "To ba matsala". Bayan fitan Ameena ba jimawa, Ummi ta kalli Hayatuddeen tare da cewa. "Auta tashi mana in ai ke ka, Gidan su Imran". cikin zumuɗin yawo yace. "To Ummi kawo aiken". Ɗaki ta shiga jim kaɗan ta fito da wasu jakukkunan guda biyu tace. "Yauwa gashi, in kaje kace, Ummanku ga wannan, ta rabawa sauran aminamta dashi zamuyi fitan biki". To yace tare da amsarsu kana ya miƙe ya fita. A hankali Zaleeha ta miƙe riƙe da Adeel a hannunta alamun zata fita. cikin kula Ummi tace. "Kin gaji da zaman ko?". Murmushi tayi tare da cewa. "Eh bacci nakeji". Kai Ummi ta gyaɗa mata alamar taje tayi. A hankali tabi bayan Hayatuddeen, tazo bakin ƙofa kenan tayi kiciɓis dashi, da sauri taja da baya tare da cewa. "Lafiya?". Cikin falon ya nufa tare da cewa. "Kai Ummi kunga wani irin hadari kuwa, gaba ɗaya garin yayi baƙƙirin kamar dare ashe dan wuta a kunne yake shiyasa bamu ga duhunba. Dariya Zaleeha tayi tare da cewa. "To hadarin cinyeka zaiyi? Ina a motace zakaje?". Kai ya jujjuya tare da cewa. "Tab wlh bazan fitaba". Murmushi tayi kana tasa kai ta fita. Sai kuma ta dawo da sauri cikin ɗan zare ido tace. "Hhhh Ummi kinga hadarin nan kuwa kai nima ya bani tsoro". miƙa Ummin tayi ta window ta ɗan leƙa, ai kuwa da sauri ta rurrufe windows ɗin cikin sauri tace. "Maza Zaleeha jeki side ɗinku ki rurrufe muku windows ɗinku, dan hadarin daga ƙasa yake tasowa, Allah ya bamu dai-dai ƙarfi mu". Amin Amin sukace baki ɗayansu. Da sauri Zaleeha ta fice. Shi kuwa Hayatuddeen ɗakinshi ya wuce. Raliya kuma dama tana sama ita da Ahmad ɗin ta. Ita kuwa Ummi komawa tayi ta zauna cikin kula tace. "To sai ka buɗe bakin kai mgna wacce kake ɓoyewa warakar naka ta tafi. Murmushi yayi tare da cewa. "To Ummi ai dole ne a ɓoye mata dan asan ina ta dosa". Daƙuwa Ummi tai mishi tare da cewa. "Wato har yanzu baka yarda da itaba". Kanshi a jujjuya alamar a a ya yarda yana dai son tabbatarwa ne. Murmushi ta ɗanyi kana tace. "Yauwa batun auren Ishaq fa saura sati biyu ne ko?". Gyara zamanshi yayi tare da cewa. "Eh saura sati biyu ni sun sa lokacin yayi tsawo ma". tv ta ɗan kalla tare da cewa. "Bai wani tsoba, kasan shirye-shiryen biki yawane dasu ga cin kuɗi". Kallonta ya ɗanyi tare dacewa. "To Ummi mu dai a gefenmu mun shirya komai sai dai ko in su can wurin amarene". Gyara zama tai da kyau kana tace. "Yauwa dama ina son muyi batun aikin Zaleeha, ya kamata ayi mata adalci, ta koma bakin aikinta, tunda ita tanada aiki ba adalci mu ajeta a gida, ƴar uwarta kuma na zuwa wurin aiki". Kici-kici yayi da fuskarshi kamar zaiyi kuka yace. "Ummi itace tace tana son aikin ne?". Da sauri tace. "Eh ai ba sai tace ba". Baki ya ɗan tura tare da cewa. "To Ummi ki bari sai ta gaya min in ta nema shike nan in bata nemaba sai tayi ta zama a gida tana mana girki, dan kinji Ahmad ya nace yace min shi wai dole zai ƙaura zai koma gidanshi dan zai dauko Goggo Dada da babanshi, naso in hanashi, sai naga kuma gskyanshi a takure yake a nan". Ya ƙarishe mgnar a ranshi kuma cewa yake. "Ni da zata haƙura da aikin taji da aikina ai da yafi min, in wuni da ita shima ai aikine". Ummi kuwa kai ta kawar tare da cewa. "Eh nima haka yace min, harda cewa ya lura wayo muke mishi mun maida mishi mata ƴar aiki. Batun Zaleeha tai mana aiki in sun ƙaura kuma bata tasoba dole dai in nema mana ƴar aiki". Dariya suka ɗanyi dan su kansu sun san Raliya na aikatawa. shiru suka ɗanyi jin wani irin sanyi mai ɗan karen daɗi da yake ratsa saƙo da luggu na jikin ɗan adam, a take garin ya wani irin duhu mai ban mamaki, daga can nesa kunnuwansu ke jiyo musu, sautin tahowan ruwa, shuuuuuuuuuuuuuuuuuuuuuu. cikin azama Ummi tace. "Baba tafi side ɗinku ruwa na zuwa". Kanshi ya ɗan juya tare da cewa. "Ummi zanyi bacci a nan". Da sauri tace. "A a tashi ka tafi ka bar ƴara su kadai a sashin naku babu na miji, jeka". da sauri yace. "Ummi akwai na miji mana, ga Adeel". Dariya tayi tare da cewa. "Ana batun mutune kana batun babyn roba". Dariyar sa mai sauti yayi tare da cewa. "Kai my Adeel ɗinne babyn roba". Dariya tai tare da cewa. "Ƙaton baby ma kuwa, maza tafi sai anjima ni zanje inyi bacci". Juyawa yayi tare da cewa. "To Ummi na tafi tunda korata akeyi". Allah ya kiyaye hanya tace mishi. Amin Amin yace kana ya fita. Ita kuwa Ummi bedroom ɗinta ta wuce tana tafe tana mgna, "Laah na mance bamuyi mgnar Zaleeha'n ba". jinjina kai tayi tare da cewa. "Koda yake na fasama bazanyi mgnar ba, bari mu gani ai in dai cikine zai baiyana kansa". tana shiga ta shiga bathroom al'wala tayi kana ta fito tayi walaha, ta dade tana tasbihi kafin ta konta bisa gado, tuni kuma an kece da ruwa kamar da bakin ƙwarya. Shi kuwa Saifuddeen yana fita, yazo dai-dai mashigar side ɗinsu kenan aka kece da ruwan, duk da ƙara gudun kekenshi da yayi saida ya jiƙe, kasan cewar ƙofar Ameena zai fara wuce, haka yasa yabi ta cikin falonta, Yana shiga ya maida ƙofar ya rufe. Yana zuwa tsakiyar falon da nufin zai wuce falonshi ya ganta konce bisa tattausan carpet ɗinta dake malale a tsakiyar kujerun, tayi pillow da pillow kujerunta, ga cup a gabanta da alama tea tasha, murmushi yayi ganin baccinta takeyi cikin salama. Wucewa yayi falonshi, kai tsaye bathroom nashi ya wuce, cire jiƙaƙƙun kayan yayi ya shanyasu, kana yayi wonka, da ruwan ɗumi yana fitowa ya fasha mai tare da fesa turare, kana yasa farar jallabiya har ƙasa ba tare daya sa komai a cikiba, kan gadonshi ya hau, ya konta, sai kuma ya jawo wayarshi, time ya duba. du du du tara da arba'in da mituna biyu ne. Lumshe ido yayi kana ya buɗesu text yayiwa Zaleeha ya tura mata. Ita kuwa Zaleeha tunda ta dawo side ɗin nasu wonka tayi kana tasa riga da zani na tattausan atampa, rigar tayi cib-cib da jikinta, Adeel kuwa yanata wasan shi. falo suka fito, ta kunna tv ta fara kallo kenan aka kece da ruwa, sai lokacin ta tuno da rufe windows ɗinta, haka yasa ta miƙe da sauri ta rurrufesu, kana ta dawo ta zauna dariya tayi ganin Adeel nata lumshe ido alamun zaiyi bacci, cikin son yaron tace. "My papy zakayi bacci ko, zo abunka zo in goyaka, kasha ɗumin bayan Amminka". Hannu ta miƙa mishi da sauri kuwa shina ya miƙa mata hannu, ɗagashi tayi ta saɓashi a baya. ɗan kwalin kanta ta worwore ta goyashi, kana ta ɗan fara jijjigashi, a take kuma yayi bacci. jin wayarta ya ɗanyi ƙarane yasa ta ɗauka *"Nooryat"* ta gani wanda shine sunan data sa bisa number Saifuddeen, murmushi tayi tare da buɗe saƙon. "Kizo". Jim ta ɗanyi kana ta rubuta mishi. "Ana ruwafa zan jiƙe in na fita". Dan ita a zatonta yana side ɗin Ummi. shi kuwa yana ganin text ɗinta ya rubuta mata "Ina ɗakin da kike ƙin zuwan ɗin". haka nan taji wani murmushi ya subce mata, shiru ta ɗanyi sai can kuma ta miƙe ta nufi ƙofar falon nashi, a hakan dan ta mance da babu ɗan kwali a kanta, da sallama ta shiga falon nashi, da sauri ta kunna wutan falon dan duhun dake ciki yayi yawa ga wani fitinenne sanyi, ɗan tsayawa tayi ganin baya cikine yasa ta nufi bedroom ɗin shi, a hankali ta tura ƙofar cikin sanyi tace. "Salamu alaikum". Can cikin ransa yace. "Wa alaikissalam". A fili kuma, ɗan ɗago kanshi yayi, ido ya zuba mata, ganin tana tsaye bakin ƙofar, numfarfashi ya ɗan firzar tare dayi mata nunin. "Bazaki shigo bane?". Kai ta jujuya a lamun a a kana a hankali ta kutso kanta cikin ɗakin. Lumshe idonta tayi a hankali dan wani irin sanyi da ƙamshi da suka cika ƙofofin hancinta, a hankali take taku har ta iso kusa da gadon shi da yafi kama dana sara kuna. cikin sanyin murya tace. "Na'am gani". Hannunshin yasa ya kamo nata hannun juyata ya ɗanyi yadda zaiga fuskar Adeel, ganin yana baccine yasa ya sake mata hannun tare da mata rubutu a wayarshi ya nuna mata. "Yayi bacci ai, jeki kontar dashi a falo, kizo kimin wani aiki". Kai ta gyaɗa cikin sanyi tace. "Ba matsala zan iya yin aikin ina goye dashi, ruwa akeyi, kuma in kontar dashi shi ɗaya." Fuska ya ɗan haɗe tare da rubuta mata. "Kije ki kontar dashi kizo bana son gardama". Ganin yadda ya haɗe mata fuska ne yasa tace. "To". Har ta juya sai kuma taji ya riko hannunta a hankali ta juyo, wani tattausan towel dake gefenshi ya miƙa mata tare da mata alamun. Ta rufe Adeel da towel ɗin ta kuma kashe ac falon. Amsar towel ɗin tayi kana, ta juya ta fita. A falonshi ta kontar da Adeel ɗin a ƙasa bisa carpet dan kar yayi juyi ya faɗo, rufeshi tayi da kyau da ɗan kwalinta sannan ta rufeshi da towel ɗin, ac'n ta kashe sannan ta juya ta nufi bedroom ɗin nashi. A hankali ta shiga tare da sallama, kanta a ƙasa har ta iso bakin gadon, cikin sanyi tace. "Ina aikin?". Bakinshi ya ɗan tura kana ya nuna mata bakin gadon, babu musu ta zauna a hankali, hannu tasa tana ɗan shafa damtsen hannunta da hannun rigarta bai gama rufewa ba cikin sanyi tace. "Shhhh wlh sanyi yayi yawa a ɗakin nan, ga sanyin damuna ga sanyin AC ga sanyin tayis ga sanyin garding dake zagaye da ɗakin". kanshi ya ɗan mirgina kana a hankali yasa hannunshi ya kamo jelan gashinta da yake har kan gadon bayanta, da sauri tayi baya da jikinta tare da cewa. "Wash Allah Hamma Saif zafi fa,". da sauri ta konta jin yaja gashin nata da kyau, mirginawa yayi ya koma can tsakiyar gadon, kana yasa hannunshi ya jawota jikinshi, da sauri ta rumtse idanunta jin yadda ta faɗa jikinshi, shi kuwa wani irin sauti ya sake mai tattare da shauƙi. Hannunshi yasa can saman gadon nashi ta gefe ya kashe wutan ɗakin, da sauri ta juyo ta ruggumeshi da kyau dan ganin wani irin fitinenne duhu ga wani irin igiyan walƙiya daya gilma. Cikin sanyi taita ƙara shiga jikinshi, tare da cewa. "Wayyo Hamma Saif sanyi". ruggumeta yayi jikinshi kana a hankali yayi ƙasa da hannunshin ya lalubi ɗan wani abu a jikin kan gadon, a hankali ya danna abun. A take sai ga wani irin haske daga saman tsakiyar rumfar gadon. da sauri Zaleeha ta buɗe idanunta dan hasken irin haskenanne mai kala-kala irin hasken cikin club music, ido ta zaro tare da yunƙurowa zaune ganin wani tattausan labule yana sauƙowa kansu, yana bajewa a take sai gashi yayi musu ƙawanya,ya zagaye gadon, yayi musu rumfa ga hasken kuma daketa walai-walai, ajiyan zuciya ta sauke ganin ashe ba rumfar gadon bane zai faɗo kansu, sai kuma tayi saurin zamewa zaune ganin, ya kuma kashe wutan, da sauri shima ya tashi zaune tare da riƙota, kana ya mata rubutu a wayarshi. "Dan Allah ki rege tsoron nan, ki nitsu barin in ɗanyi wani abu zan kunna wutan". Kai ta gyaɗa mishi kana ya haska mata hasken wayarshi sannan ta konta, kife wayar yayi ƙasan pillow'nshi sannan ya ɗan matsa, a hankali ya zare jallabiyar jikinshi ya turata can ƙasa, hannunshin ya miƙo zuwa jikinta ba tare daya matsota tasan yanayin da yake cikiba, juyata yayi ta kifu, hannunshi yasa ya kunce ɗaurin da tayiwa zanin, tana jinshi tayi shiru sai wani dib-dib da zuciyarta keyi, shi kuwa zare zanin yayi daga jikinta ya turashi ƙasan gadon, bayan rigarta ya maida hannunshin, zip ɗinta ya zuge har ƙasa, zuwa yanzu ta fahimci abinda yake nufin yi zai tuɓeta dukane, bata kuma yi yunƙurin hanashiba dan tasan hanashin kamar saɓa umarnin mahaifinta ne, a wani sashi na zuciyarta kuma, itama tana son ta sake jin yanayin daya suka daɗe basu haɗuba, shi kuwa zare rigar yayi ya cilla gefe, a hankali ya fara ɓalle maɓallan bra ɗin ta, saida ya gama ɓalle su kana ya juyata rigingine, zare bra ɗin yayi wanda ya ɗan matseta kassncewar sabone, numfashi ta sauƙe a hankali, ido ta rumtse da ƙarfi jin yasa hannunshi ya zare tattausan odawuya dake ƙugunta, ya rage daga ita sai pantie, shiru tayi kamar maiyin bacci. Shi kuwa Hamma Saif a hankali ya matso gareta, konciya yayi tare da jawota jikinshi yanajin yadda take sauƙe numfashi, wata ƙatuwar ajiyar zuciya mai nauyi ta sauke lokacin da taji fatar jikinsu ya haɗe wuri ɗaya, ido ta ɗan zaro cikin duhun daminan daya rufe ɗakin, a hankali ta yunƙura zata tashi, sai kuma ta koma ta konta jin ya ruggumeta tsam a jikinshi da sauri da sauri ta fara fidda numfarfashi jin shima jikinshi babu komai, shi kuwa Hamma Saif hannunshi yasa ƙasan pillow'nshi ya jawo wayarshi rubutu ya ɗan mata kana ya miƙa mata. "Wato ke baki iya bada haƙuri bako? Kunmin laifi na gaya muku ƴar uwarki ta bani haƙuri ke kuma ko oho ko?". Da sauri ta jujjuya mishi kai tare da cewa. "To ni laifin me nayi maka, kaida matarka kunje kun gama liƙewa juna ka dawo baka nemeni ba in kwaso kaina in kawo maka, na sani ko kuna tare tunda kuna nan kamar tib da taya". Tai maganar da ɗan ƙarfi dan a saninta baya ji, a zahiri kuma amsar wayar tashi tayi a hankali ta rubuta mishi. "Kayi haƙuri, bazan sakeba, ka gafarceni". Wani irin mashahurin farin cikine ya cika masa zuciya ya gane Zaleeha tama fi Ameena kishinsa, sai dai ita ta iya takunta kishinta sirinta ne bata taɓa ƴarda wani ya gane, ya fahimci taji zafi da ciwon tafiya India da yayi da Ameena al'halin ita bata da lfy ya tafi ya barta a haka, abin ya masifar cin ranta sai dai da yake ta iya takunta babu wanda ya gane ciwon kishinta, ita kuwa Zaleeha jinsa shirune yasa ta tura baki cikin sanyin murya tace. "Ko wacce macce tana matuƙar buƙatar kulawar mijinta randa ya amshi budurcinta, tafi son kusancinshi dana kowa a duniya tafi son shi ya rarrashinta akan kowa a duniya, amman ni ko ɗaya ban samuba, ka amshi tukuici budurcina da naketa tattalawa kamar raina, kamin abinda babu wanda ya taɓa yimin ka kusanceni da ƙarfi nayi kuka har na suma, ka jimin ciwo a jikina ciwon da babu wanda zan iya gayawa bare in nunawa, sannan ka ɗauki matarka ka tafi ka barni a haka, sabida ba sona kakeyi ba, Baba malam ya liƙa maka ni a dole shiyasa ko tausayinta baka yi". Daga cikin zuciyarta kalamanta ke fitowa wanda har ranta taji ciwon abun. Amman da yake wayeyyiyace mai iya sarrafa kishinta da fushinta babu wanda ya gane, shiru tayi hawaye na zubo mata, Jin ya sunkuyo kanta kissing nata yakeyi tako ina, sabida jin kala manta sun sashi jin ba daɗi tabbas da Ummi ta shawarceshi da zaice a tafi da ita, to amman umarni kawai Ummi ta bashi, tausayinta ne ya cika mishi zuciya, hakan yasa ya ruggumeta ya rinƙa sumbatar ko wani sashi na jikinta, ajiyan zuciya ta sauke dan abin da yake matan yasata jin sanyi a ranta, saida ya sumbaceta sama da sau goma kana ya koma ya konta rigingine jawota yayi ya kontar da ita kan jikinshi, wayarshin ya amsa a hannunta rubutu ya mata. "Na yafe miki! Allah ya miki al'barka!. Ya jikinki?". Kai ta kawar gefe cikin sanyi tace. "Kamar ya damu da jikin nawa". Wayar ya kuma nuna mata, ganin haka ta amshi wayar ta rubuta mishi. "Amin ngd, jikina kam ba sauƙi". Dariya ce taso kubce mishi ganin wai jikinta kam ba sauƙi. Ba sauƙi kamar ciwon arne. Rubutu ya kuma mata. "Ciwon bai workeba kenan?". Kai ta gyaɗa alaman. Eh, da sauri ya kontar da ita gefe, kana ya tashi zaune hannunshin yasa yana murza pant ɗin dake jikinta yana ƙasa dashi, da sauri ta riƙo hannunshi alamun ya bari, shi kuwa rubutu ya kumayi mata. "Sake min hannu zanga ciwon ne, zan miki tofi mu samu ya worke". Da sauri ta amshi wayar ta rubuta mishi. "Na workefa". Komawa yayi ya konta suna fuskantar juna kana ya rubuta mata. "To zan ƙara". Shiru tayi kamar bata gane nufunshi ba, shi kuwa juyata yayi rigingine kana ya matsota, a hankali yasa hannunshin ya rinƙa yin ƙasa da pantien har saida ya cireshi baki ɗaya. ya cillashi gefe, wayarshi ya amsa a hannunta ya kifeshi bisa bedside, sannan ya matsota da kyau, a tare suka sauƙe ajiyan zuciya jin jikinsu ya haɗe wuri ɗaya, hannuntan ya kamo a hankali ya ɗaura kan Saif ɗinshi dake tsaye, wata iriyar fuzgar numfarfashi sukayi a tare, da sauri ya kamo hannuta jin zata janye hannun, hannunshin yasa kan nata ya haɗe Saif ɗinshi ya matse, wani irin fitinenne rugguma yayi mata tare da haɗe bakinsu wuri ɗaya, harshensa ya zira mata cikin bakinta yana ɗan karkaɗawa a hankali hankali, wani irin fitinenne shauƙi ya fara sakar mata wanda yasa dole tasa harshenta ta kamo tattausan harshensa ta fara yi mishi wani sahirtaccen kiss tongue to tongue. jin ta saki jikinta dashi ne yasashi sassauta ruggumar da yayi mata, hannunshi ya manna bisa ƙirjinta a hankali yake sarrafata, wata nakasasshiyar miƙa tayi tare da sake mishi akalar rayuwarta, gaba ɗaya tayi lib a jikinta, jujjuya ta yakeyi iya son ranshi, a hankali ya maida bakinshi bisa breast ɗinta, da sauri tasa hannu bibbiyu ta ruggumeshi tare da shaƙar ƙamshin jikinshi, tsuru-tsuru tayi da idanu jin yasa harshenshi yana lasar ko wani sashi na jikinta a hankali ya fara yin ƙasa da kanshi, kana ya meda hannunshi biyu kan ƙirjintan, harshen shi ya zira cikin hudar cibiyar ta, kana yana manna hancinshi cikin tattausan fatan cikinta, hannunta, ta cusa cikin sumar kanshi, tare da shafawa, a hankali take fidda sautin. "Ahhhhhh". Yana jin yadda taketa miƙa tamkar wahainiya, dawo da hannunshin yayi ƙasa ya ɗan buɗa ƙafafuwan, kana a hankali yasa hannunshin yana shafan sashinta, da sauri ta yinƙuro ta tashi ta zauna, ya zama suna fuskantar juna, faɗawa jikinshi tayi tare da haɗe bakinsu, kana tasa hannunta ɗaya bisa ƙeyarshin, ɗaya hannun kuma, tayi ƙasa dashi ta kamo Saif ɗinshi daketa tsastsafo da madara, da sauri ya kontar da ita, kana ya sunkuyo tsakanin ƙafafunshi ta, kanshi ya kife kan pravet part ɗinta, ware sawunta yayi da kyau ya zira harshenshi, yayi mata wani irin fitinenne lasa, da yasa tayi wani irin sassanyan ƙara tare da cewa. "Ohummmmm Hamma Saif, I miss you". sai kuma duk jikinta ya fara tsuma da karkarwa dan ya sata duniyar da ta fara fita haiyacinta, shi kuwa Hamma Saif dama gigitatan yake son yi, shiyasa yake mata wasu irin wasannani da in dai mace ba dutse bace dole taji a jikinta tana hannun na miji, gaba ɗaya jikinta da muryarta rawa sukeyi, daga cikin yatsarta takeji yake zoƙo mata wani fitinenne daɗin da yake gigita mata ƙwaƙwalwa numfarfashi taketa fiddawa a hargitse, hannunshi ta jawo ta ɗaura kan breast ɗinta da suke masifar mata ƙaiƙayi har wani zut-zut sukemata, da sauri ya kamosu tare dasa yatsunshi kan nipples ɗinta yayi ta murzasu a gigice. Kana bakinshi kuma na tsotsarta. ƙafafunta ta buɗe da kyau. cikin rawan murya ta saki nakasasshen kuka da gigita take surutai. "Ohwyyyyyyy! Wai! Wai!! Wai!!! Hamma Saif daɗeeeee, wayyo! Wayyoooo!!!". A gigice ta kuma tashi zaune kanta ta kife ta kamo Saif ɗinshi ta danna a bakinta, a tare sukace. "Waiiyyyyyo". Amman da yake Zaleeha bata cikin haiyacinta batasan yayi bama, wani irin fitinenne tsotsa take mishi tamkar ta samu Lolly pop, gaba ɗaya jikunsu ɓari yakeyi. Ruwa kuma ya kece kamar da bakin gwarya, jiki na rawa ya jawo jikinshi ya jingina da kan gadon, hannunshi yasa ya kunna wannan wutan mai kala-kala. ita kuwa Zaleeha da sauri ta konta kanshi tare da ruggumeshi gam a jikinta, jawota yayi bisa ruwan cikinshi, ya zama suna fuskantar juna, hannunshi yasa kan ƙiejinta yana matsesu kamar zai meda hannunshi cikinsu, a gigice ta zuba mishi idanu, ga mmkinshi sai yaga hawaye ne keta kwaranya a fuskarta, sai kuma tasa hannunta ta kamo kanshi ta haɗa da nata, lips ɗin shi ta cabka da ƙarfinta ta fara kissing nashi, tanayi kuma tana kuka, dariyar mugunta yayi a zuciyarshi dan ya fahimci bata cikin haiyacinta ya rigada ya gama gigitata, jin kamar zata tsinke mishi lip ɗinshi na ƙasa ne ya sashi janye jiki kanshi, da ƙarfi ya kontar da ita, kana ya buɗe ƙafafuwan ta, ya shiga tsakaninsu, konciya yayi kanta, bakinshi ya sa cikin kunnenshi murya can ƙasa yace. "Zaki tsinke min lips, me kike so inyi miki". Ina Zaleeha dai bata cikin haiyacinta bare tasan yana magana, asalima itama surutai takeyi, dariya yayi kana yayi kissing goshinta, a hankali ya kafa guiwowinsa ya durƙusa, idonshi ya lumshi ganin duk ta jiƙe, a hankali ya ronƙofo jikinshi kanta, cikin tausayawa da tsananin kula ya fara cusa Saif ɗinshi jikinta, da sauri ta rumtse idanunta tare da jan dogon numfashi mai tsawo sannan ta ƙara buɗa ƙafafuwan da ƙarfi, fahimtar taji ɗan zafine yasata yin hakan ne, yasa shi kuma, maida hankalinshi ta yadda zai shigeta, a hankali hankali yake haɗe jinkisu wuri ɗaya, har ya zama rabin jikinshi na jikinta, sai kuma ya ɗan tsaya ganin yadda gaba ɗaya jikinta yake karkarwa, duk da sanyin da taketa cewan sai gashi kan goshinta ya ɗan tsastsafo zufa. a hankali ya mata rumfa hannunshi yasa ya sharce mata zufar, ita kam Zaleeha bata san me ke gudana ba, ta dai san tanajin yana ratsata tana ɗan jin zafi-zafi amman ba yadda tai zatoba, kuma ita kanta tanaji a jikinta tanason yanayin da suke cikin. Shi kuwa Hamma Saif, ƙara buɗa ƙafafuwan nata yayi cikin rawan jiki ya nutsa Saif ɗinshi jikinta, wani irin gigitaccen rugguma Zaleeha tayi mishi tare dasa kuka murya a hargitse take cewa. "Hamm Saif I love You very! very!! very!!! so much!!!". farin ciki da jin daɗi duk a tare suka dirar mishi cikin zuciyarshi da ruhinshi, a hankali cikin lallaɓawa dan kada taji zafi ta kurma mishi ihu irin na wancan karon, yasa ya fara caccakata a slow, murya a tsarƙe yake maganar da yanda tabbacin Zaleeha ba jinshi zatayiba. "Ashhhhh ohhhhhhh Owhuuu baby I love you too, I love you 3 I love you 4,5,6,7,8,9,10,11. I love you dozin-dozi ". da ɗan ƙarfi take numfarfashi tare da surutai. "Oh my God Hamm Saif Hamma Saif, Saifuddeeeeeeeeeeeen". A gigice yake amsa mata. "Na'am Zaleeha mene?". Ta kasa fahimtar komai sai dai cikin fizgar numfashi tace. "So sweeeeeeeeeeeet". Jin yadda tai mgna da ƙarfine yasashi yin maza ya danna mata yatsarshi a bakinta, dan ya tuno Ameena na bacci a falon ta. kuma har ga Allah baya son tajisu bare ta fahimci halin da suke ciki dan yasan ita bata iya iya sarrafa kishinta, Alhamdulillah ma yanzu kaso 80 cikin 100 na kishinta ya gushe. ita kuwa sambatunta tai tayi. A can falon Ameena kuwa a hankali ta buɗe idonta sabida kukan Adeel da ta fara ji cikin baccinta, a hankali ta mirgina daga koncen, tabbas kukan Adeel take jiyowa, da sauri ta tashi zaune ta jujjuya baya nan, kasake tayi ta kasa kunne jiyo a falon Babanshi yake kukane yasata miƙewa a hankali bakin ƙofar shiga falon Hamma Saif ɗin ta ɗan tsaya, a hankali ta ɗan bubbuga ƙofar, kana ta ɗan jinkirta na one minute jin shirune yasa ta tura kofar ta shiga, Konce ta hangoshi a tsakiyar falon yana kuka, da sauri ta ƙaraso gareshi, ta sunkuya zata ɗaukeshi kenan taji sautin kukan Zaleeha da surutan Hamma Saif ɗin nasu. Da sauri tasa hannu ta ɗago Adeel ta ruggumeshi cikin ƙarfi tasa hannuntan ta toshe kunnuwanta jin Hamma Saif ɗin na wani abu daya yafi kama da kuka yana kuma surutai. "Thanks my happiness daɗi, daɗi, daɗi. Allah ya miki al'barka". da sassarfa ta fice daga falon, tana jiyo muryar Zaleeha can ƙasan maƙoshinta tana cewa. "Hamma Saif so sweeeeeeeeet". Kai tsaye ɗakinta ta wuce. Wani irin abu takeji can ƙasan zuciyarta, wanda yafi kama da baƙin ciki ko kishi, hawaye ne taji suna ciko mata ido, Da sauri ta fara ambaton sunan Allah, a take kuma taji sanyi a ranta tace. "Shi da matarsa, wata biyu har kusan uku dake yake tare yau kawai dan sun kasance tare kada ki damu". Sai kuma ta lumshe idonta tare da cewa. "Kai Abba Adeel ba dai jaraba ba, ji yadda yake abu kamar wanda bai taɓa yin sex ba wai Daɗi,daɗi,daɗi, yanata sambatu uhumm ashe har haka ya iya". Kwaffa ta kuma yi ranta take mgnar zuciya. "Uhumm Wannan mutumin inaga ko mata huɗu aka bashi zai iya damu". Ido ta lumshe tuno yadda ya rinƙa caccakarta a India gabanin dawowarsa haka zai ta gigita da sata surutai, sai ya gama yazo yai ta mata dariya yanai mata tsiya. Konciya tayi tare dasa Adeel a gabanta tasa mishi nono a baki, a hankali tace. "In dai badon ya iya gigita mace in suna sex ba har ka rasa gane komai, ai zata gane yana mgna, yadda yaketa ihun sa mata al'barka kamar bai taɓa cin maceba sai a kanta mitseeee jarabebbe ji yadda yaketa santi haka. ko meye dalilin ɓoye matane?". Konciya tai lib tayi shiru tai tare da ambaton sunan Allah. Acan Side ɗinsu Zaleeha kuwa, sosai Saifuddeen ya kwashi gara son ransa har saida yaji ta fara tureshi daga kanta alamun ta gaji, konciya yayi jikinta yayi lib har saida ya gama zazzage mata madar fitinarshi, sannan ya mirgina ya koma gefenta, ya konta, jawota kanshi yayi jin yadda taketa shessheƙan kuka mai dadin sauraro, kan ƙirjinshi ya ɗaura kanta, wayarshi ya jawo ajiyan zuciya ya sauƙe ganin har shabiyun rana tayi, rubutu ya ɗanyi ya miƙa mata wayar. "Sannu ko, kin kyautawa Hamma Saif ɗinki, kin samu lada mai yawa kin jiyar dani daɗin duniya. Allah ya miki al'barka ya miki rahama da jannatul firdausi." Numfashin gajiya taja kana ta kife kanta a wuyanshi tare da tura baki a hankali tace. "Kaima Allah yayi maka al'barka, Hamma Saif ɗina, Allah ya barmin kai cikin lfy da wadata, ina sonka hamma na, son da ban san yaushene ko ta yayane ya shigeniba, ina jin sonka kamar bugun zuciya ta". Lumshe idonta Saifuddeen yayi wato tunda tasan in yana ganin bakinta zai gane me take cewa shiyasa ta ɓoye kanta a zatonta baya jinta wannan salon yakeso shiyasa ya ɓoye mata warakarshi, wata sahihiyar ruggume tayi mishi jin ya shafa mararta, a hankali ya rubuta mata. "Kin gamsu ko?". rufe idonta tayi tare da juyawa mishi baya, kana ta jawo hannunshi ta ɗaura kan mararta a hankali tace. "In dai mace ta bani adam ce ba jinnuba to ko daga romance kana iya gamsar da ita, bare kuma ka kai matsayin taraiya". shiru yayi yana jin kalamanta na ratsashi, a ranshi kuwa tunani yake ya lura Zaleeha bazata iya jurar caccakarsa ba kamar Ameena, ko dan ita har yanzu bata saba bane, ruggumeta yayi jikinshi sukayi lib suna maida numfashi har tsawon wani lokaci kana A hankali ya rubuta mata. "Jeki haɗa min ruwan wonka". Kai ta gyaɗa mishi alamar to kana, ta juya ta kalleshi a shogoɓe tace. "Ina zanina?". Hannu yasa ya miƙo mata zanin, Amsar zanin tai ta ɗaura kana ta miƙe ta sauƙa kan gadon tare da cewa. "Wash Allah na, Hamma Saif wlh yauma abun kannan yaji min ciwo, zafi nakeji". Dariya yayi cikin rumfar gadon nashi. Ita kuwa bathroom ta shiga, ruwan ɗumi ta haɗa ta shiga ciki, Shi kuwa Saifuddeen a hankali ya zuro ƙafafunshi ajiyesu yayi a ƙasa a hankali ya yunƙuro ya miƙe, cikin ikon Allah sai gashi a tsaye cas da sawunshi basa wannan rawa da karkarwan, sai dai yanaji kamar an dashi ne, idonshi ya rumtse da azaban ƙarfi, tare dasa duk ƙarfin shi ya ɗago ƙafarsa ta dawa, wai zai gwada tafiya, da sauri ya koma ya zauna a bakin gadon sabida jin zai faɗi, hamdala ya rinƙayi tare da godewa Allah. kana yaja kekenshi ya hau ya zauna sannan ya nufi bathroom ɗin. Tana cikin taji shigowanshi. Murmushi tayi ganin ya shigo nan sukayi wonkan tare. A cikin gida kuwa yau Ummi da kanta ta haɗa musu lunch, ta shirya komai a dinning table ganin yau duk ƴaƴan nata babu motsinsu ga ruwa da aketa tsugawa. Shabiyu da rabi dai-dai ruwan ya ɗauke cik, dai-dai lokacin kuma Ameena da Raliya suka iso falon a tare. Cikin mmki Raliya tace. "Ummi ke kikayi aikin?". Murmushi Ummi tai tare da cewa. "Eh yau Babana yace girkina yake son ci". Dariya Ameena tai tare da cewa. "Ya sa mana ke wahala dai Ummi". Dariya sukayi baki ɗaya. Ita kuwa Ameena a ranta tace. "Ai fa dole ya nemi abinci tunda kowa bacci yayi ya huta ammanshi sukawa yaje yayi tayi yana ihu da sambatun sa al'barka. Ahmad ne ya iso tsakiyar falon a hankali yace. "Raliya yunwa nakeji a bani abinci". Hararanshi ta ɗanyi alamar, "Eh dole ai kaji yunwa". Dai-dai lokacin Saifuddeen ya shigo cikin falon cikin shigar kayan sanyi, wannan shima wani babban alamane na sauƙi wato jin sanyi ga masu larurar spinal cord injury, sabida su basa jin sanyi sunada yawan jin zafi. Yana shiga ya kalli Ameena a hankali yace. "Aminatu bani tea insha". murmushi Ummi tayi tare da cewa. "Sanyi ko Babana?". Cikin sakalcin da yake mata yace. "Eh Ummi sanyi da yunwa da gajiya". Dariya ta ɗanyi kana tace. "To ai na gama abinci muje kuci". Dinning area ɗin suka nufa a tare, bayan duk sun zauna ne. Ummi tace. "Raliya kira Zaleeha a waya tazo, ki shiga ki tada autana kuma shina yazo". To tace tare da juyawa ta nufi ɗakin Hayatuddeen, kana tana kiran Zaleeha a waya. Ita kuwa Zaleeha tunda suka fito wonka ta wuce ɗakinta, tayi ɗan kolliya ta canza kaya, jin yunwa na ƙwaƙularta ne yasa ta shiga kitchin ɗin ta, tea ta haɗa tare da soya kwai guda biyu rak, kana ta dawo lafonta tanaci tana ɗan latsa wayarta, ta gama kenan kiran Raliya ya shigo tana ɗagawa tace. "Goggo Raliya ya akayi?". Dariya Raliya tayi tare da cewa. "Kizo muci abinci". To tace kana suka katse kiran Cikin ɗaga murya Raliya tace. "Hayatuddeen! Hayatuddeen!!". Da sauri ya fito falo tare da cewa. "Menene?". Juyawa tayi ta fita tare da cewa. "Kazo muci abinci". Biyo bayanta yayi yana cewa. "To". Suna fitowa suka zauna. Ita kuwa Zaleeha mayafi ta ɗauka ta yane jikinta kana ta nufi sashin Ummi. Tunda ta shiga yaketa satan kallonta in sun haɗa ido ya kashe mata ido ɗaya, tare da karkata bakinshi gefe. Yasa hannunshi ɗaya kuma ya riƙo hannun Ameena ta ƙasan table ɗin, yana ɗan murza yatsarsa cikin tafin hannunta. A haka dai suka ci abinci Ummi na cewa Zaleeha bataci abin kirkiba, kana tacewa Ameena. "Ameena kici kada ki biye musu kinga ke shayarwa kikeyi bare wannan ɗan naki sarkin tsotso". Murmushi tayi a ranta tace. "Uhum suma ɗin ai sun tsotse juna". Bayan sun gama cin abincin ne, Saifuddeen ya fita shi da sule direbanshi. Ahmad ma ya tafi kasuwa. Kwana biyu yayi da Zaleeha kana Ameena ta amshi girki itama tayi kwana biyunta. Rainaha dasu Goggo Dada duk sunzo sun ƙara dubashi da jiki. Shirye-shiryen bikin Ishaq da Rashida kuwa yanata kankama. Ahmad ma yanata gyare-gyaren gidanshi dan ya kafa ya tsare zasu ƙaura, yace kuma suna ƙaura Raliya zataci gaba da karatun ta. Yau auren Ishaq da Rashida saura, kwana daya rak, tuni anataa hidima a biki amare. Yau akayi walima, Zaleeha da Ameena da Raliya da Adda Rahma duk sunje, Washe gari asabar aka ɗaura aure. Da yamma cin ranar ne kuma ƙarfe biyar dai-dai lokacin da za'a je ɗaukan Amarya. Gidan Ya Aminu Gidan shiru, kasan cewar Ayman ma ya tafi islamiya, Ya Aminu ne komce a ɗakinsa kasan cewar ana hutun weekend yau babu inda yaje tunda gari ya waye, tunani yakeyi irin zaman da sukeyi da Ziyada, sam sun kasa sakin jiki da juna suna zamane kamar da ɗinsu matsayin ƙanwa da wanta, zuwa yanzu rasuwar Adda Maryam ta fara bin jiki da zuciyarsu, sai dai time 2 time in Ziyada ta tunata takan zauna taita kuka. Kamar yadda yanzuma tana ɗakin tana konce a kan gado tanata kuka sabida hotunan ƴar uwar tata data gani, tana begen ƴan uwanta rayayyu da matacciyar tun ramda aka ɗaura aurensu da ya Aminu bata ƙara ganin Zaleeha ba hakama Zahira, ga begen Adda Maryam. Shi kuwa ya Aminu, rumtse ido yayi sabida Allah ya sani yana jin begen mace, ta yaya sai fiskamci Ziyada ƴarinya mai kunya, tabbas yanada buƙatar mace, yana cikin yanayin yaji sautin kukanta na tashi daga can ƙasa. a hankali ya miƙe tare da fitowa, a hankali yake taku har ya iso ƙofar ɗakinta, inda take sautin kukanta ya cika mishi kunne, A hankali ya tura ƙofar ɗakin, cikin sanyi ya maida ƙofar ya rufe, Bakin gadon ya zauna a hankali ya kira sunanta. "Ziyada". Jin bata yi shiru bane yaci gaba da cewa. "Kiyi haƙuri, ki dena kuka". Da sauri ta tashi zaune murya na rawa tace. "Ayyah Aminu ka kaini gidan Adda Zaleeha mana ina son ganinta, ina kewar ƴan uwana". Juyowa yayi suna fuskantar juna cikin sanyi yace. "To ki bar kukan, ko dai so kike nima ki sani kukan ne?". A hankali tace. "A'a". Hannunshin yasa ya kamo hannunta a hankali ya kontar da ita, cikin tausayin kanshi da kanta ya konta gefenta abinda bai taɓa yiba, ido ta rufe ganin yadda ya konta kusa da ita shi kuwa a hankali yace. "Zan kaiki gidan Adda Zaleeha amman sai gobe kinji ko?". A hankali ta gyaɗa kanta alamar to, cikin sanyi ya ƙara matsowa jikinta, a hankali ya haɗeta da jikinshi murya can ƙasa yace. "Haka muke konciya da Adda Maryam ɗinki, bata bari inyi nesa da ita, in kuma zatayi kuka a jikina takeyi". yana kaiwa nan yaji muryarshi na rawa, alamun kuka zai kwabce mishi, a hankali yaci gaba da cewa. "Baba Malam ya aura min kene, dan ki zama min madadin Maryam, Ziyada ina son kulawarki, ki zama matata a aikace. Ziyada ina da rauni, akan Maryam sabida ta nuna min so da hallacin da bazan taɓa mancewa ba, ki amince min in raɓi jikinki ko zanji sanyi a raina". Cikin kuka ta manna kanta a jikinshi murya na rawa tace. "To ya Aminu ka gaya min duk abinda Adda Maryam takeyi maka, in sha Allahu zanyi maka". Cikin rawan jiki ya fara janye rigar jikinta a murya na rawa yace. "Maryam bata hanani jikinta a duk sanda na buƙaceta, kuma bata konciya da kaya a jikinta in muna tare, tana daurewa buƙatuna har sai taga na gamsu". Jin kalamanshi yasa bata hanashi cire mata rigarta da yakeyin ba. yana cire mata rigar ya tashi zaune kana ya jawota zaune cikin rawan murya yace. "Idan na cire mata rigarta ita ke cire min nawa". faɗawa jikinshi tayi dan bazata iya cire mishi rigarshi ba, fahimtar hakane yasa, a hankali ya zame rigar jikinshi kana ya zare mata nata, meda ita yayi ya kontar cikin muryar kuka yace. "Ran darena na forko na da Maryam ce min tayi. Ya Aminu ina tsoro". Da sauri Ziyada ta kalleshi murya a hargitse tace. "Ya Aminu nima tsoro nakeji". Ruggumeta yayi jikinshi tare da cewa. "Karkiji tsoro Ziyarda a hankali hankali zan......! "Karkiji tsoro Ziyada ahankali hankali zan miiki, bazan iya cutar dake ba, bakuma zan miki da zafi ba, saboda keɗin har yanzu matsayin ƙanwa kike awajena, bazan miki abun da zanyi miki dan son zuciya ba, kiyi hakuri kinji Ziyada, mukarɓi ƙaddaranmu ayanda tazo mana, saboda babu wanibawa da ya isa gujewa ƙaddaransa, Allah ya tsara hakan tunkan ya halicce mu, nasan hakan abune me matuƙar girma, saidai hukuncin ubangiji ne bamu da iko ko ƙarfin musawa, kiyi hakuri kinji Ziyada". Ya faɗi maganan yana me shafa gefen fuskarta, idanunta da suka cika da ƙwalla ta lumshe, gaba ɗaya tsoro,fargaba, da kuma nauyi sune suka cika zuciyarta, tayaya zata iya ɗaukan nauyin Yayan nata, takanji kaman kanta zai fashe idan ta tuna da cewa, shiɗin mijin yayarta ne kuma yayanta, tabbas tanajin abun wani iri, girmansa take gani sosai, saidai kuma haƙiƙa itama tayarda cewa ƙaddara ce da babu me iya kauce mata, duk kuwa abun daya faru ga bawa, rubutuccce al'amarine kuma tabbatacce, tuntuni Allah ya riga daya tsara hakan. Ahankali taɗan motsa laɓɓansa, cikin muryanta dake rawa tace. "Zanyi maka dukkan abun da Adda Maryam take maka Insha Allah." idanunsa ya lumshe tare da ɗan ranƙwafowa ya manna mata kiss akan goshinta, ahankali yake kusanta fuskarsa da nata, har takai ga tsinin hancinsu yana gogan na juna, ga numfashinsu daya gauraye waje ɗaya, wani irin fat fat zuciyar Ziyada keyi, ƙirjinta ne ke wani irin dukan uku-uku, hakan yasa ahankali jikinta keɗan rawa, shikansa Ya Ameenu wani iri yakeji ajikinsa, jin abun yake wani iri kaman badai dai ba, saidai kuma amatsayinsa na musulmi dole ne yayi imani da ƙaddara, me kyau ko marar kyau, sannan idan yace zai bari sucigaba da zama ahaka, zai cutar da kawunansu ne, saboda yasan yana da buƙatar mace, kuma koma ba haka ba, ayanzu Ziyada takai munzalin da dole watarana zataji feeling, ya kuma san tana ganin girmansa, tayanda bazata iya faɗa masa halin da take ciki ba ya sani ko auren so sukayi bazata iya kai mishi kantaba a matsayinta na yarinya mai kunya kuma budurwa bare kuma irin wannan auren nasu na ƙaddara. Ahankali ya sauƙe laɓɓansa akan nata, cikin sanyi ya haɗe bakinta da nasa waje ɗaya, dukansu saida sukaji wani irin abu yabi ta cikin jikinsu, jawota jikinsa yayi sosai har saida fatan jikinsu suka haɗe waje ɗaya, sake tura bakinsa acikin nata yayi, cikin sanyi da nutsuwa ya laluɓo harshenta yana ɗan tsotsa, gaba ɗayansu hawayene ke tsiyaya daga cikin idanunsu, zuciyarsu kuwa bugawa suke sosai, kowannensu da abun dayakeji, acikin rai da zuciyarsa. Tun yana Kissing ɗinta ahankali,har ya soma yi da ɗan ƙarfi, zare bakinsa yayi daga nata, ya gangaro zuwa kan wuyanta, cikin nutsuwa yake kissing ɗinta, har ya kawo zuwa kan ƙirjinta, wani irin gigitaccen romance yake mata, saboda yanaso ta fita hayyacinta, dan hakanne kaɗai zaisa koda ya shigeta bazata jigata ba, hakanne kuwa yakasance dan tun Ziyada bata enjoying mood ɗin har ya soma shiga jikinta, hakanne yasa duk jikinta ya sake, ta ƙara shigewa cikin jikinsa, hannunsa yakai yayi light off ɗin wutan ɗakin, ahankali ya ɗan buɗe ƙafafunta, tare da rungumeta sosai... Cikin nutsuwa yakeyi mata komai, yayinda yake tattalinta kaman ƙwai, komai ahankali yake mata saboda bayason ya jigata ta. Lokacin daya samu ƙofar shiga jikinta ne ta sakar masa sassanyan kuka me sauti, haɗe bakinsu yayi, yana kissing ɗinta, asannu kuwa ya samu daman daidaita komai. Yanayin yanda yake sarrafata da nutsuwa yasa bata ji wani zafi sosai irin me gusar da hankalin nan ba, sosai kuma tayi iya ƙoƙari wajen daure ciwo da zafin da takeji. After 45 minute ya ɗagota tare da ɗaurata asaman ƙirjinsa, ya rungumeta ƙam, tabbas ya samu gamsuwa hundred percent daga gareta, ya kuma ji daɗi sosai, dan itama Allah yayi mata baiwar ni'ima, jin yanda sakin sheshsheƙan kuka ne yasashi ɗagata caɗak ya nufi bathroom, ruwan zafi ya haɗa mata a bathtube, da kansa yayi mata sit bath har sau biyu, saida yasa tayi wanka, sannan shima yayi, shida kansa ya shiryata, sannan ya jawota suka kwanta akan gado, rungumeta yayi ahankali yake shafa bayanta, jinta ajikinsa yasa ta ƙara ɓoye kanta aƙirjinsa, cikin sassanyar muryarta tace. "Dan Allah Ya Ameenu, ka kaini gidan Aunty Zaleeha". gashin kanta ya shafa, cikin kulawa yace. "Kiyi haƙuri kinji, zan kaiki gaba idan Allah Ya kaimu, kinga yanzu yamma tayi, kuma gashi naji jikinki da zazzaɓi, zan sayo miki magani kishi saikiyi bacci kinji." Kai ta gyaɗa masa alaman. "To." sumbatar goshints yayi, tare da cewa. "Yauwa mar'atus saliha na, nagode sosai, tabbas kinyi ƙoƙari matuƙa da kika iya ɗauke buƙatana Allah Ya miki albarka." Kanta ta ɓoye acikin jikinsa dan nauyinsa takeji sosai. Sama da 10 minute suna kwance ahaka har bacci ya ɗauketa, jin tayi bacci ne yasa ya zare jikinta, shirya kansa yayi ya fice daga gidan baki ɗaya. Acan gidan su Saifuddeen kuwa, wanka yayi inda ya shirya kansa cikin wata maroon ɗin shadda wanda taji aiki, yayi kyau sosai, haka ma Ameena wanda da itane za'aje ɗauko auren Ishaq ɗin, itama shigan atamfa me ɗan ratsin maroon colour tayi, itama tayi kyau dan atamfar ya amshi jikinta sosai. Yau da kansa yayi driving, dan yanzu Alhamdulillah yana ɗan iya motsa ƙafarsa sosai yana ƙoƙari wajen sarrafa mota, kasancewar dama ya ƙware awajen iya tuƙi, dan koda can dayana cikin yanayin kurumtansa, Salisu shine wanda ya fara koya mishi mota, Alhamdulillah dan kuwa ya ƙware sosai, dama matsalan ƙafartasa ne tasa baya tuƙi da kansa. Haka dai suka tafi suna hiransu acikin motan, koda sukaje ɗauko auren ya iske abokansu da yawa acan, haka dai suka gaggaisa sannan aka fito musu da amarya, da kuma ƙawayenta, saida amarya ta shiga mota sannan dukansu suma suka koma nasu motocin, daga gidan su Amaryan kuwa kaitsaye gidan Ishaq ɗin suka nufa, wanda yake nan cikin shango estate yayi gininsa me matuƙar kyau da burgewa, basu wani jima agidan amaryan ba suka dawo gida, kasancewar yau ɗin Ameena nada night duty, suna dawowa kuwa ta shirya cikin uniform ɗinta, ganin idan ta tsaya diner zata makara ne, yasa Ummi da kanta tasa mata abinci a food flask tace mata tatafi dashi wajen aiki', hakan kuwa akayi tana amsan food flask ɗin tayiwa Ummi sallama tatafi. Da dare kuwa ƙarfe 8 dai-dai za'a fara diner, wanda kuma shida Zaleeha ne zasu je, koda ya dawo daga sallan isha, part ɗinsa ya wuce, sabon wanka yayi, koda ya fito daga wankan rigar wankane irin fara ƙal ɗinnan ajikinsa, gaban dressing mirror ya ƙarasa, mai ɗinsa me daɗin ƙamshi ya shafa sannan ya feshe jikinsa da turare, ƙarasawa gaban drawer'nsa yayi, wata irin haɗaɗɗiyar getzner me masifar kyau da tsada ya zaro, wanda taji ɗinkin half jamfa da kuma wando, sosai aka ƙawata gaban blue colour getzner ɗin da haɗaɗɗen aiki me burgewa, koda yasa kayan sosai suka zauna ajikinsa, yayi matuƙar kyau, wani haɗaɗɗen blue half cover shoe ya sanyawa fararen kyawawan ƙafafunsa, wata haɗaɗɗiyar hula mai ɗan ratsin blue ya sanya akansa, tare da ɗaurawa wrist ɗinsa tsadadden agogon apple, yayi kyau sosai sai baza ƙamshi yake. Acan sashin Zaleeha kuwa saida tayi wanka, sannan tayi sallan isha, tana idar da sallan mai ta shafa, kana tabi jikinta da daddaɗan humra me ƙamshin gaske, zama tayi akan stull inda ta shiga tsantsarawa fuskarta meckup, take zallan kyawunta ya sake bayyana, tana kammalawa kuwa ta ƙarasa gaban drawer glass ɗinta, wani tattausan yadi me kalan blue and peach colour ta ciro, yadi ne me azabar kyau da tsada, dan sai shining yake yana ɗauke ido, ɗinkin doguwar riga akayiwa yadin, wato fitted shape gown, dikine da yayi matuƙar kyau, koda tasa kuwa ɗas ya zauna ajikinta, yayinda ya bayyana haɗaɗɗen surar jikinta, ga kuma shape dinta daya ƙara bayyana, hips ɗinta sun ƙara girma sabida jaririn cikin dake gareta, tubke dogon gashinta tayi, sannan ta kafa ɗaurin ɗan kwali me kyau akanta, take ta fito ɗas da ita, wani haɗaɗɗen sarƙa da ɗan kunnen gold ta sanya, wanda ya ƙarawa shigar tata armashi, dogon takalmi ƙiran kamfanin Italy ta sanya aƙafanta, wanda yake shima blue ne me ratsin peach, ganin yanda shape ɗin jikinta ya bayyana yasa, ta yane jikinta da wani zazzafan lafaya babban mayafi me shara shara, saidai har sama ta ɗaura mayafin akanta ta yane kanta tamkar balarabiya, tayi kyau sosai sai baza ƙamshi take, ƙoƙarin fita daga cikin ɗakin take, ya rigata, ahankali ya turo ƙofar ɗakin nata ya shigo. Idanunta taɗan lumshe sakamakon wani daddaɗan ƙamshinsa da ya bugi hancinta, ahankali taɗan ware idanun nata ta sauƙe su akansa, yayi mata masifar kyau, har batasan sanda ta saki wani irin ƙawataccen murmushi ba, shiɗinma idanunsa ya zuba mata, dan hakanan yake ga kamar yaune ranan daya fara ganinta, tasake kyau da cika, ga wani irin hasken da ta ƙara, fatarta so smoth har ɗauke ido take, murmushi ya sakar mata, tare ta bude mata duka hannuwansa alaman ta zo, babu musu kuwa cikin nutsuwa ta ƙarasa garesa, saidai bata shiga jikinsa kaman yanda ya buƙata ba, saboda yana zaunene akan wheelchair ita kuma tasaka hill shoe, hannunsa ta kama ɗan ƙasa tayi da kanta, cikin nutsuwa tace. "Kayi kyau sosai, saidai kuma gaskia am jealousy." Idanu yaɗan zaro cikin body language ɗinsa yace. "Because of what?." Idanunta taɗan juya, akasalance tace "Saboda nasan bani kaɗaice zanga wannan kyawun naka ba, nasan ƴan matan wajen diner ɗinma zasu gane mana kai" ƙasa-ƙasa tayi maganan tayanda tasan bazai fahimci abun da take faɗa ba, saidai abun da bata sani ba shine, yajita raɗau da kunnuwansa, wani irin haɗaɗɗen murmushi yayi, ahankali yaɗan murza ƴan yatsunta dake cikin tafin hannunsa, yi yayi kamar baiji maganan ba, cikin body language ɗinsa yace. "Kema kinyi kyau sosai, kina ta shining like sabuwar amarya." Murmushi kawai tayi masa, tana ɗan satan kallonsa, cikin ranta kuwa moment dinsu na ɗazu take tunowa, tabbas yasata acikin wata duniya me daɗin gaske, batasan cewa sex na da daɗi ba sai ayau, duk da cewa ta ɗanji zafi, amma zafin ɗan kaɗanne daɗin da taji yafi zafin yawa. Hannunta dake cikin nasa ya kama suka fita daga cikin ɗakin, kaitsaye sashin Ummi suka nufa, ganin sun kusa kaiwa falon Ummi yasa ta janye hannunta daga nasa, suna shiga falon kuwa suka iske Ummi da Raleeya da kuma Ahmad azaune suma cikin shirgarsu ta alfarma da shirin fita, gefe Hayatuddeen ne ke zaune yasaka roban Ice cream agaba sai sha yake, yana jujjuya kai, dan earpiece ne akunnensa. Ummi na ganinsu haka ta saki murmushin jin daɗi, dan tabbas sunyi kyau sosai, ga kayansu kala ɗaya, sunfito ras dasu gwanin burgewa. Saida Ahmad yaɗan tsokane su sannan sukayiwa Ummi sallama, har bakin mota Hayatuddeen ya rakasu, saidai awannan karon ba Saifuddeen ɗin bane zaiyi driving, Sule driver ne Ahmad kuwa da Raliya suma motarsu suka shiga, saida Hayatuddeen yaga tashinsu sannan ya koma cikin gida shima ya ƙarisa shirinsa dan Khamis zai biyoshi suje suda Imran, Sulaiman, Isma'il Zakariyya. Suna ɗaukan titi taɗan jinginar da kanta akan kafaɗansa, lumshe idanunta tayi tana shaƙan ƙamshin jikinsa, ganin haka ne yasa shi zura hannunsa a ƙugunta ya rungumota, ahankali yake ɗan hura mata iskan bakinshi akan fuskarta, hakan kuwa sosai yayi mata daɗi, gaba ɗaya sun shagala hannunta tasa tanata shafa sajenshi, ahaka suka ƙaraso wajen da za'ayi diner'n, wato Madugu Guest Palace, sosai wajen ya ƙawatu da decoration me kyau da burgewa, gaba ɗaya wajen cike yake da jama'a, kusan kowa yazo, amma Ishaq yakafe kan cewar baza'a fara gudanar da diner ɗin ba, har sai anjira Amininsa wato Saifuddeen ya ƙaraso. Da isowarsu kuwa MC yafara shelan zuwansu, nanfa jama'a suka zubawa ƙofar shigowa ido, dan ganin wanene shi Aminin Ishaq ɗin, da kusan inbashi babu biki. Cikin nutsuwa suka raso cikin hall din, hannunsu sarƙafe acikin na juna, sunyi wani irin fitinannen kyau da dacewa. Suna shigowa kuwa waje ya ɗinke da surutu, dan kowa ganinsu yake tamkar taurari ne suka sauƙo ƙasa, saboda tsabar haɗuwa, kyau, da kuma dacewa, har wani irin yanayin kama sukeyi, wanda hakan yasa suka ƙara ƙayatarwa. Har suka ƙarasa wajen zaman da aka tana da musu na musamman, MC baidaina wasa suba, mutane da yawa saidai kawai suce. "Masha Allah." dan kuwa su Saifuddeen ɗin sunyi kyau matuƙa. Suna zama kuwa aka soma gudanar da diner ɗin, sosai abun ya ƙayatar, dan babu laifi Ishaq ya kashe kuɗi sosai, hakama Saifuddeen kusan komai shiyayi, dan wani abun ko Ishaq yace bazaiyi ba, saboda kashe kudin zaiyi yawa, Saifuddeen ne ke tuburewa, yace sai anyi, babu wani nuƙu-nuƙu kuma ya buɗe bakin al'jihunsa, dan yanason bikin abokin nasa kuma amininsa yayi armashi. Alhamdulillah anyi diner lafiya, taro yayi daɗi, haka kuma anci ansha ankuma yi ɓarin naira, biki dai saidai ace masha Allah. Ƙarfe 10 dai-dai aka tashi awajen diner'n, saida amarya da ango suka tafi, kafun suma su Saifuddeen suka kamo hanyar gida. Tun acikin mota takejin cikinta na hautsunawa, ga kuma wani irin jiri dake ɗan sanɗanta, haka duk takejin bakinta ba daɗi ita sai lokacin ta tuna rabonta da jin wani abu tun jiya da dare sai dai in taji yunwa tasha ruwan tea to kuma yanzu tun rana bata kuma cin komai ba. Suna shigowa cikin gida, direct sashin Ummi suka nufa, afalon kuwa suka tarar da ita, tana zaman jiran dawowansu, dan bazata taɓa iya bacci, batare da taga dawowansu ba, saida safe suka mata, suna fitowa daga sashin Ummi, ya riƙo hannunta, dan yaga kaman gaba ɗaya gauraya hanya take, shiyasa yayi tunanin ko bacci ne yaci ƙarfinta, direct part ɗinsa ya nufa da ita, har cikin bedroom suka ƙarasa, sakinta yayi ta zauna akan gado, ɗan jingija bayanta da jikin gadon tayi, tare da lumshe idanunta, tun rana rabonta da abinci, amma kuma batajin zata iya sawa cikinta wani abu, wani irin tashin zuciya da amai takeji, saidai abun beyi ƙarfi ba ga wani fitinenne gajiya da takeji. Shikuwa cikin nutsuwa yaɗan rage kayan jikinsa, ganin ta lumshe ido kaman me bacci ne yasashi wucewa toilet, ya sakarwa kansa shower, har ya fito daga wankan tana nan zaune a inda ya barta, still idanunta arufe suke, saboda jirin da takeji, shirya kansa yayi, cikin wasu riga da wando na bacci, masu taushin gaske, wanda suke da kalan navy blue, sunkuwa yi masa kyau. Ahankali ya turo wheelchair ɗinsa, har zuwa inda take, hannunta ya kamo, tare dasa ɗaya hannunsa ya shafi gefen fuskarta, hakanne yasa taɗan bude idanunta wanda suka ɗan soma lumshewa, giransa ɗaya ya ɗaga mata, tare da yi mata alaman "Kingaji ne?." Kanta taɗan jinjina masa, tare da karyar da wuyanta gefe, dan gajiya takeji ajikinta sosai, jawota jikinsa yayi, cikin kulawa ya zuge zip din rigar dake jikinta, sam bata hanasa ba, dan dama tana da buƙatar hakan, kawai dai kuzari ne da bata dashi, anutse ya cire mata doguwar rigan, tare da ɓalle mata maɓallin bra ɗinta, wani farin towel ya ɗaura mata, shida kansa ya kama hannunta suka shiga toilet, ruwan wanka me ɗan ɗumi ya haɗa mata, tare da zaunar da ita acikin bathtube, duk yanda yabi da ita haka take binsa, wanka yayi mata sannan ya kuma ya ɗauka mata towel, yana riƙe da hannunta suka fito daga cikin toilet ɗin, shida kansa ya zura mata doguwar rigan bacci, irin me lafewa ajikin nan, wanda take sak kala da nasa, ganin yanda jikinta duk ya sake ne yasashi ɗanjin tausayinta ya kamashi, akan gado ya kwantar da ita, tare da zama akusa da ita, yana shafa lallausan gashin kanta. Cikin abun da baiwuce 15 minute ba kuwa bacci ya ɗauketa, ganin hakane yasashi ɗan janye jikinsa daga nata, laptop ɗinsa ya jawo, cikin nutsuwa ya soma gudanar da binciken da aka basa, wanda zaiyi akan wani riƙaƙƙen robber, wanda yake ta bawa manyan jami'an tsaro wahala, dan duk yanda suka kai ga ƙwarewa sun kasa kamashi, hakanne yasa suka damƙa aikin ahannunsa, dan sunyi matuƙar yabawa da ƙwazonsa, kasancewar idan yasa aiki agaba, sai ya cimmasa. Yajima yana aikin sosai, sai kusan ƙarfe 12 sannan ya kwanta, bayan yayi nasaran samun duk wani imformation da yake so ya tattara ya turawan shugabansu, abayanta ya kwanta tare da jawota jikinsa, yayi hugging ɗinta, sannu ahankali yake shaƙan daddaɗan ƙamshin jikinta har bacci ya ɗaukesa. 2:00 am, ahankali take ɗan bude idanunta, har ta gama waresu tas, ahankali taɗan zare jikinta daga nasa, tare da tashi zaune, wani irin amai da tashin zuciya na murɗar yunwa ne, suka taso mata, take taji kaman ana sukan ƴaƴan hanjinta, cikin sauri ta diro daga kan gadon, har tanayin tuntuɓe wajen shiga toilet, tana isa bakin sink kuwa ta soma kakarin amai, saida ba komai a cikinta sai aman ruwan takeyi, aman tayi sosai sannan ta wanke bakinta, awahalce ta jingina bayanta da jikin bango, tana meda numfarfashi ahankali, saida ta ɗauki kusan mintuna 10 tana maida numfashi, jin ɗan dama dama yasa ta fito daga cikin toilet ɗin, komawa tayi ta zauna, ai ko wasu mintuna goman ba'a ciki ba, taji sabon amai yasake zuwar mata, nan ma dai toilet ɗin ta shige ta dinga kakari kamar zata amayo da ƴaƴan hanjinta, tana gamawa kuwa ta sake wanko bakinta, saidai kuma tunkan takai ga fita daga toilet ɗin, ta kuma sake sakin wani ama'n. Cikin baccinsa yake jiyo ƙaƙarin amai, tun yanajin abun sama sama, har ya maye jinsa, aɗan zabure ya tashi daga baccin, jiyo sautin aman Zaleeha'n acikin toilet yasashi jawo kekensa cikin sauri ya hau, jikinsa na rawa ya nufi toilet ɗin. Zuwa lokacin kuwa gaba ɗaya ta galabaita, dan har ta durƙushe akan ƙafafunta, dan kuwa amai ɗinta na uku kenan. Da sauri ya ƙaraso cikin toilet ɗin, hannayensa yasa duka biyu ya ɗagota jikinsa, dai-dai lokacin kuwa wani sabon amai ya sake zuwar mata, saida ta amayar da duk wani abu na cikinta, faɗawa jikinsa tayi tana me fitar da nishin wahala, dan ta jigata ƙwarai, hankalinsa ne yayi matuƙar tashi, tallafo haɓarta yayi, cikin body language ɗinsa yace. "I'am sorry my happiness, am so sorry, sannu ko kinji, dama baki da lafiya ne? tun yaushe kika fara amai? please tell me what happened dear?." Idanunta wanda sukayi narai narai dasu ta ɗan juya, awahalce tace. "Wayyo Hamma Saif jiri nakeji, sannan inajin kaman zan amayar da ƴaƴan hanjina, please helf me." Cikin matsanancin tausayinta in boddy language yace. "Oh My God am sorry kinji, zaki samu sauƙi insha Allah, taso na wanke miki jikinki kinji My Love ɗina, yanzu 2am, da sasssfe zan ƙira Dr. ya dubamin ke." Kanta kawai ta iya jinjina masa, cikin kulawa kuwa ya ɗagota, inda ya wanke mata jiki da kuma bakinta, ɗagota yayi jikinsa kaman ƴar baby, haka suka fito daga bathroom ɗin tana liƙe ajikinsa, jin jikinta da zafi ya sa ya shumfuɗeta akan gado, tare da bin bayanta ya kwanta, acikin jikinsa ya sata, yana me shafa bayanta ahankali, kasancewar yaɗanji jikinta da zafi. Sake lafewa ajikinsa tayi, tare da sakar masa sassanyan kukan shagwaɓa. Jin sheshsheƙan kukan nata ya sashi hugging ɗinta tide, ahankali ya zura harshensa acikin kunnenta yana ɗan lasa. Hakanne yasa tun tan kukan ahankali, har tayi lub ajikinsa, wani wahalallen bacci ne ya ɗauketa, ganin tayi bacci ya sashi shima ɗan lumshe idanunsa. Ai kuwa baccin nata baiyi nisa ba, wani sabon amai ya sakota gaba, da sauri ta yunƙura ta sauƙa daga kan gadon, saidai tun kafun ma ta ƙarasa toilet ta riga da ta sheƙasa akan tiles. Hankalin Saifuddeen ne yayi masifar tashi, dan yaga yanda take kwara ama'n, gaba ɗaya babu ƙarfi ajikinta, duk tayi weak, saida ya bari ta gama, sannan ya gyara wajen, ɗaukanta yayi ya maida ita kan gado, zama yayi sannan ya ɗaura kanta akan cinyarsa, sosai yakejin wani irin matsanancin tausayinta. Itakuwa zuwa yanzu ko ƙarfin kirki bata dashi, hakanne yasa take ta faman sauƙe ajiyar zuciya akai akai, tana kuma ɗan numfasawa awahalce. Suna nan zaune ahaka har aka ƙira sallan asuba, da ta fara bacci amai zai taso ta gaba, dole kuma saitayi take ɗan samun relief, ganin ta soma bacci ne yasashi janye jikinsa, toilet ya shiga yayi alwala, yana fitowa kuwa jallabiya ya zura ajikinsa, saida yayi kissing ɗin goshinta, sannan ya fice daga cikin ɗakin. Kaitsaye sashin Ummi ya nufa, ba kowa afalon sai sautin A/C dake tashi, ƙarasawa jikin ƙofar Ummin yayi, tare dayi mata knocking, Ummi wanda fitowanta daga toilet kenan ta ɗauro alwala, jin ana buga ƙofar ɗakinta yasa ta ƙarasowa ta bude, ganin Saifuddeen yasa tayi mamaki ƙwarai, dan tasan baya taɓa zuwa gaisheta sai ya dawo daga masallaci, cikin yanayin mamaki tace. "Saifuddeen lafiya kuwa, naganka adai-dai wannan lokacin?." Ɗan shagwaɓe fuskansa yayi, cikin bayyana damuwarsa yace. "Ummi Zaleeha ne bata da lafiya, tun cikin dare take ta amai, gashi jikinta duk ya ɗau zafin zazzaɓi." Idanu Ummi taɗan zaro, cikin jimami tace. "Subahanallah amai kuma? dama bata da lafiya ne?." Narke fuska yayi akasalance yace. "A'a Ummi lafiyanta fa ƙalau har muka dawo daga wajen diner." Ɗan jim Ummi tayi tare da cewa. "To bari nayi sallah sai naje na duba ta ko, amma kafun nan kaƙira Dr. yazo ya duba ta." Kansa ya jinjina, sannan ya juya ya koma cikin falon, wayarsa ya ciro tare da dannawa number'n Dr.Adnan ƙira, ringing biyu kacal Dr.Adnan ya ɗaga wayan. Bayan sun gaisane Saifuddeen ɗin keyi masa bayanin rashin lafiyan Zaleeha'n, cikin tausayawa kuwa Dr.Adnan ɗin yace idan ya idar da sallah zaizo saiya duba ta, da haka sukayi sallama Saifuddeen ɗin ya wuce masallaci. Koda aka idar da sallan baiwani tsaya acikin masallacin ba, dan bayaso yayi nisa da Zaleehan, koda ya koma ɗakin nasa har yanzu tana nan ayanda ya barta, har yanzu kuwa sama sama take fitar da numfashi. Akusa da ita ya zauna, cikin lallami ya tasheta, ahankali taɗan bude idanunta, kanta ya shafa, cike da soyayyarta ya mata mgna da yarensu. "Sannu ko dear, tashi kiyi sallah kinji, ya jikin naki?." Kai kawai ta iya gyaɗa masa alaman. "Da sauƙi." Hannunta ya kama suka wuce bathroom shi ya taimaka mata ta ɗauro alwala, shida kansa kuma ya sa mata hijab ta tada sallah, koda ta idar da sallan jingina kanta tayi ajikinsa, har yanzun dai jiri take ji, ga kanta dake ɗan sarawa, kamo hannunta yayi ya maida ita kan gadon, tare da rufa mata blanket, kallon agogon dake saƙale jikin bangon ɗakin yayi, ganin ƙarfe 5 ɗin asuba, ya sashi sauƙe ajiyar zuciya, dai-dai lokacin kuwa yajiyo knocking ɗin ƙofar falonsu, take kuma wayarsa ta kawo haske alaman shigowar saƙo, koda ya duba saƙon Dr.Adnan ne, inda ya rubuta masa cewa. "Na iso." ahankali yake sarrafa wheelchair ɗinsa, har ya fice daga cikin ɗakin, dakansa ya ƙarasa jikin ƙofar falon ya buɗe, ganin Dr Adnan tsaye yasashi ɗan sakin murmushi tare da bashi hannu sukayi musabaha, iso yayiwa Dr.Adnan ɗin har cikin ɗakin nasa, Ƙarasawa jikin gadon Dr.Adnan yayi, anutse ya ƙira sunanta, jin muryan Ya Adnan ɗin yasata ɗan ɗago kanta, kansa yaɗan jinjina cikin kulawa yace. "Sannu ko, ya jikin naki?." Kanta taɗan jinjina masa alaman da sauƙi, ɗan ƙaramin jakan dake hannunsa ya ajiye, yana ƙoƙarin saka hand clobes ahannunss yace. "Ina da ina ke miki ciwo?." awahalce taɗan karyar da wuyanta, murya asanyaye tace. "Amai da jiri nakeji, sai kuma tashin zuciya da zazzaɓi, gashi bakina duk ba daɗi". Idanu yaɗan zuba mata, lokaci guda kuma sai ya ɗan saki murmushi, bargon da take rufe dashi yaɗan yaye, hannunta ya kamo tare ɗa ɗaura mata wani abu kaman igiya, ganin ya fito da allura ne yasata rumtse idanunta da ƙarfi tare dasa hannu ta riƙo hannun Hamma Saif ɗin. Jininta yaja sannan yayi mata wata allura, wanda yasan zata ɗan taimaka mata, dai-dai lokacin Ummi da Raleeya suka shigo cikin ɗakin, amutumce suka gaisa da Dr.Adnan ɗin, nan yace musu zai koma asibiti dan yanaso ya gwada jininta daya ɗiba, "to" sukace sannan ya fita. Ummi ne ta ƙaraso jikin gadon, kan Zaleehan ta shafa, cikin kulawa tace. "Ayya Zaleeha sannu kinji, ya jikin naki?." Jin muryan Ummi ya sa ta buɗe idanunta ashagwaɓe tace. "Da sauƙi, amma Ummi jiri fa nakeji kuma har da amai". dagajin yanayin maganan nata kasan ba iya zafin ciwo bane, harda zallan shagwaɓa ne da raki. Sake shafa kanta Ummi tayi cikin kulawa tace. "Sannu ko, zaki samu sauƙi insha Allah." Raleeya ne tayi mata ya jiki, jinjina mata kai tayi alaman da sauƙi. Zama sukayi awajenta suna ƙara shagwaɓata da kuma tattalinta, Saifuddeen ma kasa barin ɗakin yayi, idanunsa kawai ya zuba mata, ita kuwa kasancewar alluran da Dr.Adnan yayi mata nada ƙarfi, hakan yasa wani irin bacci me nauyi ya ɗauketa. Ba'awani ɗau lokaci sosai ba Dr.Adnan ya dawo, fuskarsa cike take da wani irin annuri haɗi da zallan farinciki, ahankali ya buɗe ƙofar ɗakin ya shigo, ganin yanda yake sakin murmushi hannunsa riƙe da wata farar takarda yasa suka zuba masa ido, Saifuddeen ne ya fara cewa. "Lafiya kuwa Dr. me yake damunta?." Ƙarasowa cikin ɗakin yayi tare da miƙawa Saifuddeen ɗin hannu, alaman su gaisa, da ɗan mamaki Saifuddeen ya basa hannunsa, cikin bayyana farinciki Dr Adnan yace. "Congrats Bro, Zaleeha na ɗauke da cikinka almost 2 to 3 month." Tamkar shigar shock haka duka sukaji maganan acikin kunnensu, Jikin Saifuddeen ne ya soma ɓari, cikin matsanancin mamaki, jin abun yayi kaman al'amara, duk da yasan cewa shiɗin baida matsalan rashin haihuwa, amma hakanan yakejin batun cikin Zaleehan kaman amafarki, Allah mabuwayi me yin yadda yaso a lokacin da yaso, yau gashi Zaleeha macen da zuciyarsa ke tsananin so da muradi, tana ɗauke da cikinsa, zamewa yayi daga kan wheelchair ɗinsa yayiwa Allah sujjada, dan nuna godiya da kuma tsantsar farincikinsa. Ummi da Raleeya kuwa ba abun da suke cewa sai. "Alhamdulillah Masha Allah." Cike da matsanancin farinciki, Ummi ta dubi Zaleeha, wanda ita bata ma san meyake gudana ba, dan baccinta ya ɗanyi nisa, Murmushi me ɗauke da farinciki tayi, cikin jin daɗi tace. "Allah sarki Zaleeha yarinyar kirki, Allah Ya miki albarka, ya kuma sauƙeki lafiya". Sai alokacin Saifuddeen ya ɗago daga sujjadan da yayi, kan wheelchair ɗinsa ya hau, sannan ya ƙaraso jikin gadon, wani irin farinciki ne bayyane akan fuskarsa, rungume Ummin sa yayi ƙam, tamkar wani ƙaramin yaro, cikin kasa ɓoye farincikinsa yace. "Alhamdulillah, Ummi na kinga Allah me iko ko, yabani kyauta me mahimmanci alokacin da ba zata ba, Ummi ki taɓa zuciyata kiji, har wani tsalle take saboda tsabar farinciki." murmushin jin daɗi Ummi tayi, cikin kulawa tace. "Nasan kana cikin farinciki Babana, kuma muɗinma hakane muna cikin farin cikin." Ɗan janye jikinsa daga na Ummi'n yayi, inda ya ƙurawa Zaleeha mayun idanunsa, cute face ɗinta yake kallo, wanda tayi fayau da ita, lokaci ɗaya har taɗan rame. Wani sabon zazzafar soyayyarta da ƙaunarta ne ke ratsa duk jikinsa, haka yakeji kaman ya jawota ya rungumeta. Fahimtar hakane yasa. Ummi miƙewa, ta fita cikin jin daɗi, hakama Raliya ta bita a baya, suka tafi cikin tsananin jin daɗi. A ɗakin Saifuddeen ɗin kuwa cikin kula ya Adnan ya ɗaura mata wani ɗan leden ruwa ƙarami, dasa mata alluran cin abinci, daurewa iya daurewa Zaleeha tayi amman duk da haka saisa ta fidda hawaye da anasa mata allurar ruwan a hannunta, Hamma Saif kuwa cikin kula da lallama yake in boddy language yake cewa. "So sorry Sannu ko, da zafi ko? Ya Adnan ayimata a hankali". Dariya Ya Adnan yayi kana ya tattara kayan aikinshi yace. "Raki da raki sun haɗu, a kula da cin abin cinta, domin bawai cikinne ya sata amai da jirinba, rashin cin abinci ne yasa yunwa yayi ta murɗanta, yunwarce kuma tasa mata jiri da kasala da duhun da take gani, so dole a kula da ita da cin abinci." cikin gamsuwa Hamma Saif in boddy language ɗinsa yace. "In sha Allah zan kula ya Adnan, na lura kam tunda na dawo bata son cin abinci". ƙarishe haɗa kayanshi yayi kana ya sallamesu ya tafi. Yana fita Hamma Saif ya hau gadon da kyau, hannunshi yasa yana shafa gashin kanta, ita kuwa Zaleeha tunda taji Ya Adnan ya ambaci kalmar ciki sai tayi shiru tana bin Hamma Saif ɗinta da ido, cikin tsananin jin daɗi yayi mata rubutu a wayarshi ya miƙa mata, "Maman Baby, maman yara Ammin Adeel, my happiness my life my Everything. Ngd Ngd Ngd matuƙa, Alhamdulillah Zaleeha Allah ya azurtamu da samar da abu ɗaya, jinina da jininki sun kasance a sashi ɗaya, burina da fatana sun cika kina da ciki har na tsawon wata biyu da sati uku". Sai kuma ya sunkuyo yayi kissing goshinta, ita kuwa Zaleeha lumshe ido tayi da sauri bayan ta karanta abinda ya rubuta mata, hannunta tasa bisa lafeffen cikinta, wani irin daɗi farin ciki salama ne suka cika mata zuciya a baiyane tace. "Alhamdulillah. Allah na gode maka da kyautar da kayi min, ya Allah ka al'barkacin abinda ke cikina, ka bani shi mai kama da mahaifinsa". Sai kuma ta ɗan buɗe ido ta, Hamma Saif ɗin nata, rubutun da yayine ta kuma karantawa. "My dear meyasa!? Meyasa!!? Meyaaa!!!? Baki sanarmin kinada cikiba, meyasa kika ɓoye min abin farin cikinmu?". A hankali ta kalleshi cikin sanyi tace. "Hamma Saif nima bansan ina da cikiba". Da sauri ya rubuta mata. "Kamar yaya baki sani, tunda bakiga al'darkiba har wata biyu har na uku, ai yaci kisan kinada ciki". A hankali tace. "Hamma Saif ni ba ko wanne wata nake al'adaba, ina tsallake wata, wani lokacin har wata biyu nake tsallakewa sai ana uku sai ingani, shiyasa yanzunma da ban ganiba ban damuba dama duk zatona wata ƙil ƙarshen watannan zanyi dan ban taɓa tsallake wata ukuba a tunanina nanda kwana biyar zan gani". Da sauri yasa hannu ya zare alluran ruwan dan ganin ruwan ya ƙare, ɗagota yayi ya ruggumeta a jikinshi tsam, yana kissing nata tako ina. A cikin gida kuwa, Dr Adnan na fita Ameena na shigowa. A can falon Ummi kuwa cikin farin ciki Ummi tace. "Ni dama na daɗe da zargin Zaleeha nada shigar ciki, dan har kamar zan gayawa Saifuddeen sai kuma nace bari dai in barsu inga zasu gane da kansune ko sai an ganar dasu, kuma da yake sabbin shigane duk basu ganeba, kai yarinta da daɗi ƙuruciya dangin hauka. Hayatuddeen ne da Ahmad dake ta farin cikin labarin suka haɗa baki wurin cewa. "Au Ummi itama Zaleeha bata san tana da cikinba". Raliya ce tace. "Ato da alama kam bata saniba, dan in ta sani ai Hamma Saif zai sani". Dariya sukayi baki ɗayansu. Dai-dai lokacin Ameena ta shigo. bayan sun gaisa da sune ta kalli Hayatuddeen daketa cilla Adeel sama suna dariya tace. "Autan Ummi yau farin ciki da sassafe babu baƙin halin tashi daga bacci mai ka samu haka?". Cikin dariya yace. "Yo Aunty Ameena ai dolena in girma tunda naga kun dage tuƙuru zaku cika mana gida da yara, Adeel zaiyi ƙani ai dole in daina yarinta kada ayi uban banza". Cikin mmki da rashin fahimta ta kalli su Ummi dake dariyar mgnar Auta, a hankali tace. " Ummi me muka samune". Cikin kula Ummi tace. "Ammin Adeel ne, ta kwana ba lfy, to shine da Yayanku yazo ya gwada yake cewa cikine gareta". Wani irin sassanyan murmushi Ameena tayi cikin jin daɗi da kekyawan zuciya tace. "A a Alhamdulillah. Adeel ya girma, ya zama babban yaya, Allah ya sauketa lfy". Amin Amin suka amsa baki ɗayansu. Sosai sukayi farin ciki, Nan Ameena da Raliya suka shiga kitchin. Ummi kuwa ɗakinta ta koma, a waya ta sanarwa Raihana dan tasan Adda Rahma kam mijinta zai gaya mata. ta kuma sanarwa Goggo Dada da Aunty Mina ma sosai yan uwa da abokan arziki sukayi ta murnar cikin. A can sashin Saifuddeen kuwa, shi da kanshi ya taimaka mata, a tare sukayi wonka, kana suka shirya, rigar daya cire mata ta maida, daga nan ta nufi ɗakinta dan canza sakekkiyar riga. Shi kuwa Saifuddeen tana fita ya fara kiran abokanshi yana sanar musu, sosai sukayi ta farin ciki sunayiwa Zaleeha tsiya wai ai dolema ta gudu ta kuma dawo da kafarta, wai Adeel ne ya korata, cikin kuma shi ya dawo da ita. Ishaq ne ƙarshen kira dan yasan angone kar ya takurashi da sanyin safiya. Ishaq kuwa yana jin wayarshi na rigging amman bai samu damar ɗagawa ba, sabida yana lallaɓa amrya Rashida da yayi mata Dalla Dalla, sabida sam ya kasa ɗaga mata kafa, kun san riƙaƙƙun tuzurai ba sauƙi. Yana tafe yana kuma gwada kiran Ishaq, yana shiga falonshi Ishaq na amsa kiran cikin tsokana yace. "Ango kasha mai". Dariya Ishaq yayi tare da cewa. "Caɓa-caɓa ma kuwa mai kam harda lagwada, ai da nasan haka abin yake da ɗan karen daɗi da tuntini nayi aure". Dariya sukayi baki ɗayansu, Rashida dake manne jikin Ishaq ɗinne ta ɗan sune kanta a jikinshi. shi kuwa Saifuddeen cikin happy yace. "Al'bishirinka". Da sauri Ishaq yace goro". dariyarsa mai sanyi yayi cikin jin daɗi yace. "Ka kusa samun ƙanin Adeel, jiya tunda muka dawo Baby keta amai ashe, cikine ni bamu saniba sai ɗazu ya Adnan ke sanar min." Cikin tsananin jin daɗi Ishaq yace. "Alhamdulillah, kai nayi farin ciki, kai mutumina ba sauƙi kai ko yaushe bugu ɗaya kake jefa ƙollo a raga". Dariyar keta Saifuddeen yayi tare da cewa. "Sune zalamammu daga na basu sai su ƙarɓa, kuma dama Zaleeha kam addu'ar da nayi tayi kenan, har a kaba na roƙi Allah ya azirtamin samun haihuwa da ita akai-akai kafinma ta ankara, gidana ya zame mata farin cikin duniyar ta, ta haifo min yara dozin-dozin". Dariya sosai Ishaq yayi kana yace. "Mugu, to Allah ya sanya al'khairi ya sauƙeta lfy". Amin Amin yace kana sukayi sallama". Daga nan ya shiga falon Zaleeha a falon suka haɗu cikin kula ya miƙo mata hannu, kana suka nufi falon Ummi. Suna shiga, duk suka gaggaisa, hannu Zaleeha tasa ta karɓi Adeel dake hannun Hayatuddeen, cikin kula sukayi mata sannu da jiki. Ameena da Rayila ne da suka gama shirya breakfast a dinning table suka iso falon cikin sakin fuska Ameena ta kalli Saifuddeen fuska a sake tace. "Congrats Abban Adeel, Allah ya sauƙeta lfy". Amin Amin sukace baki ɗayansu, Ita kuwa Zaleeha sunkuyar da kanta tayi ƙasa cikin tsananin jin kunya. Shi kuwa Saifuddeen wani irin fitinenne kallo yakewa Ameena kallo mai cike da mutun taka, ji yake tamkar ya kamota ya ruggumeta, amman ba dama, ita kuwa ganin kallon da yake matane yasa ta meda kanta kan Zaleeha sabida taga Saifuddeen kallon farin cikin tayashi murnar da tayi yake mata ta hango wani baiyanenne farin ciki a fuskarshi cikin kula tace. "Ammin Adeel ya jikin?". A hankali tace. "Na worke fa Ummu Adeel". Dariya Raliya tayi tare da cewa. "In kinci abinci ne zamu yarda kin worke". Da sauri Saifuddeen ya jinjina mata kai alamar da kyau. Ahmad kuwa dariyar ƙeta yayi tare da cewa. "Allah ya fito mana da _Sodangi_ mu lfy, dan dai shine ya somu yasa aka gudu aka kuma dawo, Jingudo haka sunan yake ko macece ko na mijine". Dariya sukayi dukansu, Ameena kuwa shiru tayi. Kalmar Jingudo da Ahmad ya kira ta amsa mata tarin tambayoyin dake ranta na cewa ina Zaleeha taje Dan duk cikekken bafulatani in yaji an kira yaro da Jingudo ko Sodangi to yasan auren dole akawa mace, ta haifeshi a gidan wanda aka aura mata dolen, to shi ake cewa Jingudo." A ranta ta tuno kalmar Adda Rahma inda take cewa mata. "Kan Abu ɗaya ya taɓa nuna ƙulafashinsa a duniya a kanta ne kaɗai, Sai ta kuma nazarci kalmar Ahmad na cewa Allah ya fito mana da Sodanginmu lfy don dai shine ya somu an gujemu an dawo". Kai ta rausayar jin Ummi na cewa suje suci abinci. kan dinnin table ɗin suka nufa, tana mai magar zuciya. "Uhumm Ahmad kenan da kenan ka sani yanzu son Abban Adeel da nake hangowa cikin idonta ya wuce zaton mai zato, Allah sarki wato auren dole akayi mata, da alama kuma guduwa tayi lokacin da Adda Maryam ta rasune ta dawo ikon Allah to meyasa Zaleeha zataƙi Abba Adeel duk da tarin kyanshi da dukuyarshi basu ruɗeta ba." Jin Saifuddeen ya murza hannunta alamun taci abinci ne yasa tasa hannu ta fara ci. Zaleeha kuwa sanadin alluran da akayi mata to ta samu taci abinci sosai, shiyasa duk jiri da murɗa da duhun suka tafi sai ɗan kasalar da ba'a rasaba. Ranar dai Saifuddeen wuni yayi yana jinya, shida kanshi kuwa ya kira Ya Ameenu da ya Ahmad ya sanar musu batun cikin Zaleeha, sosai Ya Ahmad yai tawa Zaleeha wasa wai ashe yanzu kam girma yazo zata bar guje-guje. A can gidan ya Ameenu kuwa suna gama yin mgnar ya kalli Ziyada dake zaune gefenshi hannunta ya rike a hankali yace. "Kinji Adda Zaleehan takima bata da lfy, tanata aman laulayi ciki gashi kema har yanzu tafiyarki bata gama gyaruwa ba, kiyi haƙuri sai kin ƙara samun sauƙi sai in kaiki ku wuni kinjiko Mar'tus saliha na tuba". Kai ta jinjina cikin sanyinta irin na adda Maryam tace. "To Ya Ameenu". Jawota yayi ya ruggumeta domin biyeyyarta sak Maryam yake gani sam basu da gardama. Bayan sati ɗaya lokacin cikin Zaleeha ya cika watanni uku cib-cib kuma Alhamdulillah ba laulayi sosai yanzu sai yawan cin abinci. Da dare Ameena ce ke zaune gefen Saifuddeen wanda yake waya da Dr Acash prasat, nan yake gaya mishi. "Lokacin dawowarka fa ya kusa". Kanshi ya gyaɗa dan video call sukeyi cikin nitsuwa yace. "Eh inata shirin zuwa ai". Da sauri Dr Acash prasat yace. "No karka taho India, ƙarshen watan nan zamuyi taron ƙarawa juna sani na duniya baki ɗaya, zamuyi taron ne kuma a Istanbul na kasar Turkey. So kayi ƙoƙari mu haɗu a can, zan haɗaka da wani babban Dr da zai dubaka wanda duk ya fimu sanin matakan warakar ciwon insha Allah zaka samu dace". Cikin gamsuwa da wani sahirtaccen jin daɗi Saifuddeen yace. "To ba matsala". Daga nan suka katsa wayar, cikin kula Ameena tace. "Kai ƙasa mai daɗi kena Instabul weather su akwai masifar daɗi." Murmushi yayi tare da cewa. "Sanyi su ne keda yawa, tsarin ƙasar is Gud, a dai irinmu masu larurar spinal cord injury jikinmu irin garin yakeso". miƙewa tayi tare da cewa. "Eh sosai ma kuwa". A hankali yace. "Ina zakije kuma kika tashi." Hannu tasa ta tallaɓe ƙirjinta tare da cewa. "Zan ɗauko Adeel ne naji mamanshi nata tsastsafo alamun ya tashi a bacci kenan". Dariya yayi tare da cewa. "Tsakanin uwa da ɗanta sai Allah". Murmushi tayi kana ta fita. Shi kuwa text message ya turawa Zaleeha. "Salam, Baby maman baby kinyi bacci ne?". da sauri ta maida mishi amsa. "A a banyi ba, ina cin abin daɗin ne Ummi na ta dafa min." murmushi yayi tare da rubuta mata. "Abin daɗin kam ai yana wurina". Murmushi tayi. da sauri ta duba sakon daya kuma tura mata. "Kinada E Passport ne"?". a hankali ta rubuta mishi "Eh to gsky nawa ya daɗe bazaiyi aikiba yanzu". "To ki shirya gobe da safe zamuje imagireshon Office, aiyi miki E Passport ɗin". ido ta lumshe cikin tsananin farin ciki dan dai tasan ƙasar za'a bari da ita kenan tunda taji ana neman E Passport a zahiri kuma sai cewa tayi to. Washe gari kuwa da safe sukaje akayi mata E Passport ɗin ta, daga nan airport suka wuce, ya fara nema musu damar barin ƙasar, sai azahar suka dawo gida. Alhamdulillah yanzu tana cin abinci ba laulayi, kamar yadda Ameena ta raini cikinta a sauƙaƙe, to haka itama ko dan jinin mutun ɗaya ke gudana a jikinsu. Rashida da Ishaq kuwa sunata dandatsa Amarci baba kama hannun yaro. Yanzu cikin Zaleeha ya shiga wata huɗu, kuma ya ɗan fara baiyana duk da ƙugunta da mazaunanta ne suka fi buɗuwa sukayi tib-tib gwanin sha'awa sai ƙirjinta da yayi tamtsan-tamtsan Yau tunda safe Ziyada keta shirin zuwa gidan Adda Zaleehanta, sai dai Ya Ameenu ya mata tsiya yana ganinta shirya ta shirya Ayman murmushi ya ɗanyi tare da cewa. "Ayman zo in ai keka wurin baba maigadi, kace ya tsinko maka nunnen maggoro ka kawo min". Da sauri yaro yace. "To Daddy innce adda ni ko a bani mai yawa dana Aunty Ziyada ko?". Kai ya gyaɗa mishi tare da cewa, "Eh maza yi sauri ɗan al'barka". Ai kuwa a guje ya fita, yana ganin fitan yaron ya jawo hannunta sukayi cikin ɗaki a hankali ya rufe ƙofar da sauri tace. "Ya Ameenu ka rufe ƙofar kuma?". Kanshi ya gyaɗa mata tare da cewa. "Kizo mu ɗanyi wata mgna kafin ya dawo, nasan zasu dade a cikin labbun kafin su samu nunnenen mangoro". Ba musu ta bishi suka hau gadon cikin raɗa yace. "Kullum in Maryam zataje anguwa, in tayi kolliyar sai mun ɓata kolliyar forkon muyi wonka tare kafin tayi na biyu". Cikin sanyi ta tace. "To in da zaka kaini?". Zip ɗin rigarta ya fara zugewa tare da cewa. "In kin min duk abinda nayi mikiba". Da haka ya shagalar da ita ya biya musu buƙatarsu sannan, suka sake wonka suka sake sabon shiri sannan ya kaita gidan Zaleeha, yana sauƙeta ya juya ya fita Ita kuwa a hankali ta nufi sashin Ummi tana tafe cikin nitsuwa. A hankali ta murɗa ƙofar falon tare da yin sallama. Da sauri Raliya tace. "A a Ziyada maraba da zuwa." Zaleeha dake kitchin ne ta fito da sauri jin an kira sunan ƴar uwarta. Da sauri ta nufesu tare da cewa. "Oyoyo my Ayman miss you so much". ɗagoshi tayi tsam ta riƙeshi. Kana ta kalli Ziyada dake ɗan murmushi cikin jin daɗi tace. "Allah sarki Ziyada sai yau kika tunani?". Murmushi Ziyada tayi kana ta juyo ta kalli Ummi da yanzu ta fito ɗakinta cikin kula tace. "A a lale marhabin Ziyada sannu da zuwa". A hankali tace. "Yauwa Ummi sannu, ina kwana?". "Lafiya lau ya mai gidanki?". Ummi ta faɗi cikin kulawa ita kuwa Ziyada a sanyaye tace. "Alhamdulillah Ummi yace in gaidaki ma, yace ince miki sai yazo ɗaukarmu zai shigo ku gaisa, yanzu yana sauri ne". Cikin kula Ummi tace. "Ayyah to mgd sosai". Raliya ce ta kalli Ziyada tare da cewa. "Ina kwana ya gida?". Fuska a sake tace. "Lfy lau Alhamdulillah, ya ayyuka?". Alhamdulillah tace. cikin girmamawa Ziyada ta kalli Zaleeha dake ta shafa kan Ayman tuni ida nunta sun cicciko da hawaye, kanta ta kawar dan ganin hawayen Zaleeha zaisa nata hawayen fitowa a hankali tace. "Inna kwana Adda Zaleeha". Murya a sanyaya Zaleeha ta kalleta tare da cewa. "Lfy Ziyada ya gida, ina ya Ameenu?". "Alhamdulillah gida lfy Ya Ameenu yana lfy yace in gaidaki". Shiru suka ɗanyi ganin haka ne Zaleeha ta miƙe tare da cewa. "Taho mu isa". To Ziyada tace kana tabi bayanta, har sunje bakin ƙofane Zaleeha ta ɗan juyo ta kalli Raliya tace. "Yauwa Goggo Raliya na gama aikin gaba ɗaya sauran kwashe abincin ne ki ɗan ƙarisa mana". To Raliya tace kana ta nufi kitchin ɗin. Su kuwa Zaleeha na gaba riƙe da hannun Ayman, Ziyada kuma na biye da ita a baya, Har cikin bedroom ta wuce dasu Bisa tsakiyar gadonta suka zauna, cikin sauri Ziyada ta kwanta tare da cewa. "Wash Allah na, Adda Zaleeha nayi kewarku, kuma babu wanda yake leƙeni sai Baba Malam nane kawai duk ran jumma'a zaije mu gaisa". Murmushi Zaleeha tayi Cikin son ƴar uwantata tace. "Ke kinma ji daɗinki ke yar gatar Baba Malam ce, tunda har zuwa yake har gidanki, ni da yazo nanma bai iso yaga ɗakina ba". Murmushi jin daɗi Ziyada tayi tare da cewa. "A a wlh Adda Zaleeha ba batun ƴar gata, ai ranan da yaje nace mishi yazo wurin kine? Sai yace min a a , Ya za'ayi yazo gidanki, ga surkanki ga ƙannen mijinki ga abokiyar zamanki, sai yace min ranan dai da yayi kewa ki kuma yaji baki da lfy, yasa Hamma Saif ya kai mishi ke ya ganki". Dariya sosai Zaleeha tayi cikin jin daɗi tace. "Oho dama shine yasa Hamma Saif yace muje gida aifa nayi mmki ban tambaye shi zuwa ba kawai yace muje gida, Allah sarki Baba Malam, Allah ya bar mana shi". Amin Amin Ziyada tace cikin jin daɗi. Nanfa sukayi ta hirar yaushe gamo hirar ƴan uwa sun sa Ayman a tsakiyarsu sunata shafa kanshi, sai kiran sallan azahar da akayine suka tashi sukayi salla. Daga nan kuma suka fito falo, Abincin da Raliya ta kawo musune suka zauna sunaci suna hira. Cikin hirar ne Zaleeha ta ɗan ƙoƙƙofi Raliya dan ta fahimci irin zaman da sukeyi da Ya Ameenu cikin kula tace. "Uhum ni kam Ziyada, a ɗakin Adda Maryam kike ko?". Cikin sanyi tace. "Eh ana baba Malam yace in zauna". Kansu suka ɗan sunkuyar dukansu hawaye na son zubo musu sai kuma suka shanye, cikin sanyin murya Zaleeha tace. "To Ya Ameenu kuma ina yake". Ɗan jim Ziyada tayi kana a hankali tace. "A ɗakinsa yake mana". Kai ta gyaɗa kana tace. "Kece kike kwana da Ayman ko?". Da sauri tace. "Eh".spoon ɗin hannunta ta ajiye tare da cewa. "To shi ya Ameenu ne yake zuwa ɗakinki ko kece kike zuwa ɗauki shi?". Cikin rauni da nitsuwarta da ƴarda da kusancin ƴar uwarta tace. "Uhum last 2 week ya fara shiga ɗakina, Adda Zaleeha nasha wuya ranan nai kuka har na kusan mutuwa, na tuno Adda Maryam in ba mutuwaba ya za'ayi in auri mijinta har mu haɗa makonci, ya Ameenu yana ban tausayi komai zai sai yace min haka sukeyi da Adda Maryam". Cikin sauri suka share hawaye su a tare jin motsin shigowar Saifuddeen, ido ya zubawa Zaleeha tare da jujjuya mata kai in boddy language yace. "Kuka kuma, ba Addu'a zakuyi mataba, ke babba ke ya kamata ki rarrasheta taji sanyi sannan ki tasata gaba kina kuka". Da sauri tace. "Na bari". Ita kuwa Ziyada cikin sanyin rai da murya tace. "Hamma Saifuddeen ina wuni". Lfy lau ya gida, ya amsa in boddy language. A hankali ta kuma cewa. "Ya Adda Zaleeha da jiki?". Da sauƙi ya kuma amsa mata da yaren kurame. sannan yayi musu nasihar kada su sake kuka daga nan ya wuce side ɗin shi. Su kuwa nan sukayi ta hira har la'asar kafin suka tashi sukayi salla, daga nan sukaje cikin gida, Suka shiga kitchin su biyu, koda Raliya tazo zatayi aikin Ziyada tace. "Ke kam zauna ki huta muyi ta hira, yau na karɓa miki". Cikin dariya Raliya tace. "Ai nima yanzu na ban kwana nake musu dan, mun kusa ƙaura". Da sauri Zaleeha tace. "Wai yanzu fisabilillahi Ya Ahmad da gske yake nufin zaku ƙara?". Dariya Raliya tayi kana tace. "Sosai ma kuwa, kinga har yafa nema min gurbin karatu a G.S U yace muna ƙaura zan fara karatu, wai tunda Allah bai bamu haihuwa inyi karatu har sai inda nace na tsaya in kuma yi aiki." Haka nan sai Zaleeha taji tausayin Raliya sabida tasan suna son haihuwa ita da Ahmad Allah bai basu, cikin sanyi tace. "Ɗanki yana kan hanya in sha Allah, nakine ni na baki tun yanzu nasan kuma Hamma Saif bazai hanaku ba". Cikin wani irin jin daɗi Raliya ta ruggumeta tare da cewa. "Aunty Zaleeha ko baki baniba kin gaya min mgna mai daɗi ngd ngd matuƙa Allah ya sauƙeki lfy". Murmushi Zaleeha tayi kana a hankali tace. "Amin, karki damu kema zaki haifa, kuma zan baki wannan tunda mu ga Adeel". Dariya sukayi dukansu ita kuwa Ziyada sai murmushi yakeyi tana kallon ɗan tudun cikin yayar tata. A haka suka gama abincin dare. Suka shirya komai a dinning table, Zaleeha ta ɗauki food flask data sa nasu suka sallami Ummi sukayi side ɗin ta, Raliya kuwa ta haura sama ɗakinta. Suna gab mashagar side'nsu suka haɗu da Hamma Saif yana fito da alamun al'wala yayi cikin kula ya jawo hannun Ayman dake hannun Zaleeha ya mishi alamun yaje yayi al'wala yazo su tafi masallaci. Ganin kamar Ayman bai gane bane yasa Zaleeha ce mishi. "Ayman kaje can pom-pom kayi al'wala kazo kuje masallaci. ai kuwa da gudu yaje yayi al'wala kana ya kama hannunshi suka tafi masallacin. Su kuwa suka shiga sukayi salla kana suka ɗanyi hira kafin isha'ayi tayi sukayi salla kafin suka zauna cin abinci sunaci suna hira. Saifuddeen kuwa da Ahmad da Hayatuddeen da Ayman kai tsaye falon Ummi suka shiga nan suka samu Ameena ma ta dawo, nan sukaci abinci, kana suka dawo cikin falo suna hira suna nan a zaune, Ya Ameenu ya shaidawa Saifuddeen ya iso, Ahmad ne yaje ya mishi jagora, ya shigo suka gaisa da Ummi kana ya fita tare da Saifuddeen da Ayman. cikin kula Saifuddeen yace. "To Ya Ameenu har yanzu fushin akeyi da mune baza'a shiga ba?". Murmushi mai kama da Dariya yayi kana a hankali yace. "No ba fushi bane saurine". Kai ya gyaɗa kana yace to bari inje in kirawo ta, dariya ya ɗanyi kana yace. "Nama kirata a waya". Dai-dai lokacin kuma suka iso wurin, a hankali Zaleeha tace. "Ya Ameenu ina wuni?". Cikin ɗan sakin fuska yace. "Lfy, ya jiki?". "Alhamdulillah jiki da sauƙi". Ta bashi amsa. har sun shiga mota sai kuma Ziyada tace. "Ab ya Ameenu nayi mantuwa tsaya". Cikin kulawa yace. "To na tsaya Saleeha". fita tayi cikin sanyi tace. "Adda Zaleeha ya Ameenu yace in gaya miki, kije ki ɗauki saƙon da Adda Maryam ta bar wasiyar ta bar miki, to tunda nazo na manta sai yanzu na tuna". Cikin sauri tace. "To Ziyada in sha Allah zanje". sai ta kuma kalli Hamma Saif a hankali tace. "Hamma Saif zaka kaini ko?". Kai ya gyaɗa mata alamar eh. Ganin haka Ziyada ta shiga mota suka tafi, su kuma suka koma cikin gida. Bayan kwana biyar da zuwan Ziyada, Zaleeha ta tambayi Saifuddeen batun zuwa gidan Adda Maryam ɗauko saƙon da ta bar mata, sai yace ta bari ranar yanada hidima duk randa yake free zai kaita. A ranar ne kuma komai na shirin tafiyarsu Istanbul ya kammala, saura kwana uku zasu tafi, ita harma ta mance da batun E Passport da akayi mata. Da safe bayan duk sun gama cin abincin, kasancewar ranar Ameena zata karɓi girkin, kuma su da safe, zaka amshi miji ba sai yamma ko dare ba so daga anyi breakfast mai karɓan girki ita ke dashi, shiyasa yanzu girkin Ameena ce, sai ya nufi side ɗin ta, a falon tama ya konta bisa 3 str Yana danne-danne a system ɗin shi. Ita kuwa Zaleeha falonshi ta leƙa ganin baya nanne ta dawo falonta ta tura mishi text. "Salam Hamma Saif ka fitane?". Yana ganin saƙon yace mata. "A a. Ina nan kina buƙatan wani abune?". "To ina kake nazo falonka baka ciki, na leƙa bedroom ma baka ciki". "Ina falon Ummu Adeel, kizo". Jin haka yasa ta miƙe ta ƙofar falonshi tabi, gefenshi ta zauna, tana zama yasa hannunshi kan cinyarta a hankali ya cusa hannun cikin rigarta ɗan tudun cikinta ya fara shafawa a hankali hankali. cikin sanyi tace. "Hamma Saif dama batun zuwa gidan Ya Ameenu ne nace bari in tuna maka tunda yau weekend ne baka da fita, ko zaka kaini." Kai ya ɗan rausayar kana ya rubuta mata. "Sai gobe, zamuje, gidan Baba malam yayi mana addu'an ALLAH ya raya inƙanta mana babynmu ya kuma fito mana dashi lfy daga nan sai muje gidan Ya Ameenu ɗin". Cikin jin daɗi tace. "To Allah ya kaimu". Daga nan ta miƙe ta fita. Washe gari, bayan anyi sallan la'asar, wanda ya kama kuma gobene zasu tafi Istanbul, kusan a tare suka shiga falon Ummi cikin shiga ta, al'farma sunyi kyau dasu, bayan sun sallami Umminshi ne, suka fita suka tafi. Kai tsaye, makey suka nufa. Suna shiga taga ya fara tsintan abubuwan da kamar su turamen zannuwa Getzner turaruka, sabulai da dai sauransu, saida suka gama kuma ta sashin suka shiga sashin kayayyakin taɓa ka lashe. Sai kuma taga yana shiga layin kayayyakin sanyi masu ɗan karen kyau riguna masu kyau na sanyi irin na mutanen ƙasashen da ake musu ruwan dusar ƙanƙara. saida ya zaɓi masu kyau kusan kala biyar biyar na maza dana mata. Daga nan sukaje wurin biya aka ya biya, aka zuba kayan a ledodi uku. Atampopi da yadin mazan da turaruka a leda ɗaya. Kayan kwalamace kuma leda ɗaya kana sai kayan sanyin suma a lede ɗaya, Yana gaba tana binshi a baya, sunzo dab ƙofar fita, tayi maza tayi baya ido ta zubawa matar da tani a gefenta, Tabbas bazata mance matarnan ba cikin nitsuwa tace. "Sanunki". Da sauri matar ta juyo tare da cewa. "Yauwa sannu". Saifuddeen kuwa a bakin baranɗar ya tsaya daya juyo yaga tana ciki bata fitoba kuma da alama mgna takeyi da mata police ɗin dake bakin mashigar wurin wacce ita ke kula da shige da ficen matan dake shiga Makey ɗin, baya jiyo muryarsu sabida hada-hadar mutane, Zaleeha kuma baya ta bashi bare ya karanci motsin bakinta. Ita kuwa Zaleeha cikin nazari tace. "Sunana Zaleeha Bashir Sulaiman Dukku". Ido matar ta zuba mata cikin son tuno fuskar a hankali tace. "Kamar dai na sanki". Da sauri Zaleeha tace. "Shekara biyu da ƴan watanni na taɓa kai riport a police station ɗinku na Gombe division, wata rana bayan sallan mangariba, na kai muku riport cewa ƴan kalaren sun tare wani mutun a cikin sitadiyom, suna dukanshi, kin tunani kecema, kika matsa aje a duba". Cikin sauri Matar tace. "Yes! Na tunaki ai kuma dan na tuna yadda kikazo a gigice mugun DPO mara mutunci yai ta zaginki". Da sauri Zaleeha tace. "Ayyah, wanda yayi tamin masifa ya gargaɗeni cewa kar in yarda in kai ƙarar wani Police station ɗin". Da sauri matar tace. "Eh shi dai". Cikin kaɗuwa Zaleeha tace. "Dan Allah kunje kun taimaki mutumin da aka daka ɗin ne? Dan washe garin ranar nazo station ɗinku sai na samu duk bakwa wurin sai wasu sabbin fuskoki na samu, da namusu mgnar kuma sai sukace babu wannan mgnar a wurinsu. Bayan nan nafi wata biyu kullum sai nazo station ɗinkin amman bana samun kowa". A hankali matar tace. "Ayyah ai mutumin munje an taimakeshi an kaishi asibiti, to DPO ne ya caccanza mana wurin aiki tun a ranar sabida, da tun lokacin da kikayi bayani ya gane Yaran Dalla ne sukayi dukan, shi kuwa karen Dalla ne, shiyasa ya koreki ya miki barazana, da ranki da ran mara lfyar dan dama jami'an tsoro na neman Dalla kuma in aka kama Dalla yasan shima bazai tsiraba, ni kaina daga baya na koma can dan in duba takardar rahotonki ko zan sameta a maida case ɗin hannun DGP gaba to sai na samu babu, Yanzu haka shi DPO an koreshi a aiki kwana kin baya da aka kama Dalla dan ya tona musu asiri, Ni kuma yanzu a ƙarƙashin DGP nake aiki yanzuma tare muke dashi shiyasa nake bada kariya wa ƙofar shiga dan uban gidana yana ciki". Sai kuma ta ɗan kalli Zaleeha dake ta nanata sunan Dalla a bakinta, ya abubuwan suke son haɗe mata a kaine suna dagula mata lissafi. matarce ta kalleta tare da cewa. "Ɗan uwanki ne suka sassare?". Da sauri tace a a. Kana tace. "Allah sarki, to Allah ya saka mishi kenan? Bani number ki zamuyi mgna daga baya, yanzu sauri nake". Murmushi matar tayi kana ta bata number tata. Daga nan bi bayan Hamma Saif ɗin tayi. Suna shiga mota Sule yaja suka tafi. Daga nan kai tsaye New G.R.A suka nufa shiru tayi tana ta son tuno wasu abubuwan sam ta kasa samo bakin zaren tunanin nata har suka isa. Suna zuwa gidan su Zaleeha da farin ciki suka shiga, kai tsaye falon Baba Malam sukaje bayan sun gaisa ne, Yayiwa sule text akan ya shigo da ledan atampopin ya kawo, koda ya kawosu sosai Baba Malam yayi godiya bayan yayi mishi faɗan ya daina musu hidima, cikin nitsuwa yayiwa Baba Malam bayani, cewa gobe zasu tafi yayi musu addu'a. Fuska a sake dottijon ya gyara zama tare da cewa. "To Allah ya kaiku lfy ya dawo daku lfy, Allah ya bada sa'an aikin da duk za'ayi maka". Amin Amin Mama da Mamy da ya Habu da ita Zaleeha suka amsa a zahiri. shi kuwa Saifuddeen murmushi jin daɗi yayi tare da amsawa a zuciyarshi, shiko Baba Malam cikin nitsuwa yace. "Zaleeha ki kula dashi da dukkan motsinshi a tafiyar nan da za'ayi kinga zakuje inda bashi da kowa baki da kowa, dukkan taimako da tallafawa a wurinki zai samesu, bana son gardama, na haneki dayi mishi musu". Cikin sanyi tace. "In sha Allah Baba malam zan kula". Cikin jin daɗi yace. "Allah ya miki al'barka ya kaiku lfy". Amin Amin sukace duka. Mama kuwa da Mamy sai kallon ɗan cikin Zaleeha sukeyi wanda yanzu ya cika wata huɗu cib ya kuma fara baiyana kanshi, duk da ƙaton hijabin da ta zumbula wai duk dan ta ɓoye cikin dan kunya. Hira suka ɗanyi kana, suka sallamesu suka nufi gidan Adda Maryam. Kasan cewar Ya Ameenu na gida shiyasa da kanshi ya musu jagora har falon Ziyada, bayan sun gaggaisa ne, jin ana kiran sallan magriba Ya Ameenu da Hamma Saif suka fita a harabar gidan sukayi al'wala, suma su Zaleeha al'wala sukayi kana sukayi sallan basu tashi a kan abin sallan ba ba sukaci gaba da hira, har saida aka kira isha sukayi salla kana suka fito falon, nan suka ci abinci, hira suka ɗan fara, ganin dare ya ɗan fara nisane Hamma Saif yayi mata alamun to su tafi dare nayi". Gane abinda yake nufine yasa ta miƙe tare da kamo hannun Ziyada cikin sanyi tace. "Ziyada muje ciki". Sai ta kuma kalli Ya Ameenu cikin sanyi tace. "Ya Ameenu a ina soƙon da Adda Maryam ɗin ta ajiye min yake?". Ido ya lumshe a hankali yace. "Tace ki duba a bedside drower'nta na gefen gado ta jikin window". Kai ta gyaɗa kana suka juya suka nufi cikin ɗakin. Shi kuwa Ya Ameenu da Hamma Saif miƙewa sukayi suka nufi woje, tunda yanzu zata fito su tafi. Su kuwa suna shiga, Ziyada ta zauna a bakin gado, ita kuwa Zaleeha gaban durowar ta zauna ɗabas, a hankali ta buɗe durowar, wasu robobi ta gani a jere a ciki, sai kuma wata farar takarda a ninke a akan robar da tafi girman, da sauri tasa hannu ta ɗago takarda, da taga anyi rubutu da manyan baƙin. "Zaleeha, ki buɗe takardar ki karan tata a cikin ɗakina, kisa a ranki kamar da bakina nake gaya miki ina gabanki kina gabana". Da sauri tasa hannu ta sharce hawayen da tuni suke kwaranya, buɗe takardar tayi jiki na rawa ido ta ware sosai dan ganin rubutun da kyau. "......! "Inaji a jikina Zaleeha bazaki dawo ki sameni a rayeba, shiyasa na rubuta miki abinda na fahimta dan in ankarar da ke. Ina fatan ko kin dawo bayan raina zaki saurari abun da zan faɗa miki, da kunnen basira, kuma inaso kiyiwa kalamaina kyakkyawar fahimta, ki zauna kiyi nazari akan abun da yake faruwa. *Dan inaga kina tare da wanda kike ta wahalan nema kina tare dashi shi kike nema kuma shi kika gujewa* ina kyautata zaton cewa Saifuddeen shine mutumin daya taimaka miki! saboda bayan kin gudu naje gidan Ummin Saifuddeen, naje munyi magana da'ita, ta bani wani labarin daya bani mamaki, wanda kuma labarin irin makamancin labarin da kika bani ne, time ɗin da kika faɗamin haɗuwarku da Dalla, har wani mutumi ya taimakeki, lokacin din da kika faɗamin, lokacin ɗin Ummi ta faɗamin, tace dukan Saifuddeen akayi da magriba, kuma wasu ƴan kalarene suka dakesa da time da date duk iri ɗayane. suma kawai zuwa kawai police ya sanar musu aka ce musu yana medical centre bashi da lafiya kuma ƴan kalare ne suka dashi, to su a lokacin ta ranshi lfyarsa sukeyi basubi ta kan waɗanda sukayi dukanba, daga wannan rashin lafiyanne kuma ya rasa ƙafafunsa, saboda abayansa suka dakesa, wannan shiya jawo masa matsalan rashin tafiya, saboda haka ne nakeji ajikina Saifuddeen shine wanda ya taimakeki, dan tace bada gurguntakan aka haifesa ba, kwata kwata faruwar abun shekara ɗaya ne da ya wuce, kuma da aka kaisa medical centre, Abuja suka tura su, daga Abuja kuwa aka wuce dashi India, sai bayan shekara ɗaya ya dawo, hakanne yasa nake kyautata zaton Saifuddeen shine wanda ya taimakamiki, amma kiyi bincike akan hakan, wata ƙila hakan ya zama gaskiya, amma ina roƙonki koda bai kasance shiɗin bane, kizama maiyi masa biyyaya, Zaleeha ki zauna agidan aurenki da zuciya ɗaya, darajar ƴa mace shine ɗakin mijinta, dan Allah Zaleeha kizama me biyayya ga mijinki da kuma Baba Malam, ki nutsu kicire tunanin wani acikin ranki, ki rungumi mijinki hannu bibbiyu, insha Allah Zaki ga riban hakan naso in sanar miki a waya to in na kiraki bata shiga." Cikin wani irin yanayi Zaleeha tayi wani zazzafan numfashi tare da sauƙe ƙaƙƙarfan ajiyan zuciya, da kuma sauƙan wasu irin razanennun hawaye, take taji kanta na jujjuyawa, wasu abubuwane suka shiga dawowa cikin ƙwaƙwalwanta, sai yanzu tunaninta ke ƙoƙarin daidaita, cikin yanayin mamaki da ruɗu da gigicewar tunani tace. "Ziyada Hamma SAIF shine wanda ya taimakeni, tayaya hakan zai kasance?." Cikin mamaki Ziyada tace. "Haba dai Adda Zaleeha?". Kai ta shiga ɗan girgizawa, domin kuwa tashin farko taji zuciyarta na neman gamsuwa da zancen, amma kuma abun tambayar shine wazai tabbatar mata da hakan? idan kuma dagaske shiɗin ne me yasa ya ɓoye mata kansa? Turo ƙofar ɗakin akayi, hakan yasa ta ɗago kanta da sauri, Ya Ameenu ne, cikin kulawa yace. "Inkin gama kiyi sauri, dan yana jiranki awaje." Kanta ta jinjina, shi kuma ya juya ya fice daga cikin ɗakin Ziyada na biye dashi dan yafitota da yayi alamun tazo, ko minti 2 basuyi da fita ba, cikin sauri ta juya ta fita daga ɗakin, abakin shigowa cikin ɗakin sukayi karo da Ziyada, hannun Ziyadan ta kamo, cikin wani irin yanayin da ta kejin kanta aciki tace. "Shine Ziyada, inaga da gaske Hamma Saif ne, shine wanda ya taimaka min." Cikin yanayin mamaki Ziyada tace. "Shi kuma?." Kai ta jinjina alaman "Eh." dan gaba ɗaya tashiga mamaki da ruɗu. Sakin Ziyadan tayi, cikin sauri ta nufi waje. Dai-dai lokacin kuwa Saifuddeen sun gama magana da Ya Ameenu, harma ya shiga cikin mota, Sule driver ne ya buɗe mata murfin motar ta shiga, bayan tayiwa Ya Ameenu sallama. Tana shiga kuwa Sule driver yaja motar suka tafi, da sauri ta juyo da fuskarta garesa , akiɗime takai hannunta ta tallafo haɓarsa, juyo da fuskarsa yayi ya zamana suna fuskantar juna, wani irin abune taji yana shiga zuciyarta, cikin muryarta da tayi sanyi, take kuma fidda yanayin da take ciki, tace. "Hamma Saif wai kaine? kaine wanda ka taɓa taimakona? ka tuna fuskata Hamma Saif, please kafaɗamin, kaine wanda ka taimakeni lokacin da yaran Dalla suka so cutar dani?, kafaɗamin Hamma Saif dan Allah ka tabbatar min da hasashena ka tuna a bakin A.A ALIYU." Idanu ya zuba mata naɗan wasu daƙiƙu, lokaci ɗaya ya saki wani irin murmushi me tsayawa azuciya, bayajin zai iya amsa mata wannan tambayan ayanzu, ba kuma bazai faɗa mata bane, kawai dai yafi so ne ya koyar da ita zazzafan soyayyarsa, amatsayinsa na kurma kuma gurgu, duk dama dai ayanzu yasan ta zurma cikin kogin sonsa. Ganin ya kawar da kansa gefe, yasa ta kamo hannayensa, tare da zubawa gefen fuskarsa ido, wani irin sabon yanayi takeji na ratsa zuciyarta, ahankali ta matsa jikinsa, kan kafaɗarsa ta ɗaura kanta tare da lumshe idanunta, har yanzu jin abun take wani iri, sai-dai murmushin da taga ya mata, ya matuƙar sata a ruɗani. Ahaka har suka isa baice da ita komai ba, Sule driver na gama parking ɗin motar, ya fito, ware wheelchair din saifuddeen ɗin yayi, cikin nutsuwa ya buɗe murfin motar ya fito, anutse ya hau kekensa ya wuce cikin gidan, da sauri Zaleeha ta rufa masa baya, cikin sassanyar muryarta take ƙiran sunansa, sam bai tsaya ba balle har tayi tunanin zai juyo ya kalleta, sun kawo dai-dai bedroom ɗinsa ne cikin sauri ya shige tare da jawo ƙofar ya rufe, hakanne yasa bata samu daman shiga ba, fuska ta kwaɓe tare da ɗan karyar da wuyanta gefe, a bayyane tace. "Me yasa bazaka amsa min tambayoyina ba Hamma Saif why?." asanyaye ta juya ta fice daga cikin falon. Shikuwa yana shiga cikin ɗakin nasa ya saki wani irin murmushi, dariya ya ɗanyi me sauti, cikin tsantsar nishaɗin daya samu kansa yace. "Kina yarinya ƙarama amma bakya iya gane mutane to in kin tsufa kuma wato wata ranama cewa zakiyi ni ba mijinki bane ki sani uku". daga haka kayan jikinsa ya ɗan rage sannan ya wuce toilet. Zaleeha kuwa daga sashin nasa part din Ummi ta wuce, rashin ganin kowa acikin falon yasa taɗan ɗaga murya, tana ƙiran sunan Ummi'n, jin shiru babu amsa ne yasa ta nufi ɗakin Hayatuddeen kasancewar ta jiyo muryar Hayatuddeen ɗin yana ce mata. "Ummi ta shiga wonka". kana taga ƙofar ɗakin nasa abuɗe, ahankali ta tura ƙofar ɗakin ta shiga bakinta ɗauke da sallama. Shi kuwa Hayatuddeen zaune yake akan sofa, yayinda ya baje hotunan Abbansu da Ya Nuruddee da Saifuddeen tun kafin ya samu matsalar tsayuwa, kasan cewar in Ummi taga hotunan tana kukane yasa suka ɓoyesu, yanzuma begen ganin mahaifinsu da babban yayansune yasa ya fito dasu. Hotunan Saifuddeen ne agabansa yana kallo, wanda kuma yayi hotunan ne tunkafun yasamu nakashewar ƙafafunsa, hankalinsa ya ɗanyi nisa shiyasa baiji sallaman nata ba, Ahankali ta ƙaraso cikin ɗakin, tare da baza idanunta akan hotunan dake gaban Hayatuddeen ɗin, wani irin bugawa taji zuciyarta tayi, alokacin da ta sauƙe idanunta kan wani hoton Saifuddeen wanda yake tsaye akan ƙafafunsa shidasu Ahmad dasu Salisu Ishaq yana murmushi, ga fuskarnan tasa fayau ta bayyana, babu wani cikar ƙasumba asamanta, saɓanin yanzu da saje yayi mata ƙawanya, hannunta dake rawa tasa ta ɗauko hoton, gaba ɗaya jikinta ɓari yake, bakinta na rawa tace. "Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un, Hayatuddeen waye wannan?." jin muryanta yasashi ɗago kai, murmushi yayi yana ɗan kaɗa kai yace. "Kaman yaya waye wannan kina nufin baki ganeshi bane?." Cikin ruɗani tace. "Please Hayatuddeen kafaɗamin waye shi, karkacemin shine Hamma Saif kuma na kasa gane shine dan zan jawa kaina Allah ya isa, ka cemin wanine daban ba Hamma ba." Cikin yanayin mamaki yaɗan shafi sumar kansa, shaye da mamaki yace. "Ikon Allah yau kuma Hamma Saif ɗinne baki gane ba, to ki wanke idanunki wannan ba kowa bane face Hamma Saif, nasan kinyi mamakine saboda kin ganshi tsaye kan ƙafafunsa, lokacin bai samu matsalan spinal cord injury bane shiyasa." Durƙushewa tayi akan ƙafafunta, murya na rawa tace. "Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un, wallahi shine, shine mutumin daya taimakeni Hayatuddeen Hamma Saif ne, shi ya ceceni daga hannun ƴan iskan da suka so tarwatsamin rayuwata, shine wanda ya zamemin Garkuwa alokacin da babu me iya taimakona, shi ne wanda ya zama makari kuma madubin dubawata, da ace alokacin babu shi, da yanzu rayuwata wani babin take fuskanta ba wannan ba, Wallahi Hamma Saif ne Hayatuddeen, shi nake ta nema tsawon shekaru Wlh Hamma Saif ne!!!." Ta ƙarishe mgnar da ƙarfi Baki Hayatuddeen ya buɗe yana kallonta, shikam cike yake da mamakin Zaleehan, dan kalamanta sun ɗaure masa kai. Dai-dai lokacin Ummi ta shigo cikin ɗakin da sauri, kasancewar fitowarta falo kenan, taji tashin maganganun Zaleeha'n, Zaleeha kuwa ganin Ummi yasa ta ƙarasa gabanta cikin sauri, tuni hawaye sun kwaranyo daga cikin idanunta, hannuwan Ummin ta kamo tana jijjiga kai tace. "Shi ne Ummi Hamma Saifuddeen ne, wallahi da gaske shi ne! Gskyan ADDA MARYAM tayi gsky." Da mamaki Ummi ke kallonta, cikin rashin gane inda maganganun Zaleehan suka dosa tace. "Bangane me kike faɗa ba Zaleeha, shi ne wa?". Ganin Ummin kaman bazata fahimceta ba, yasa cikin sauri ta nufi hanyar fita daga ɗakin, baki buɗe Ummi ta bita da kallon mamaki. Hayatuddeen kuwa zuwa yanzu ya fahimci abun da Zaleehan ke nufi, dan baya taɓa mantawa sun taɓa taɗin da Zakariyya, wani irin dariya yayi, tare da shafa sumar kanshi, cikin matsanancin farinciki yace. "Yess dama ashe akan mune aketa wannan badaƙalar, wannan shine rashin sani yafi dare duhu, mu ake so kuma mu ake gudu, batare da ansani ba." Dariya yayi sosai, hakanne yasa Ummi da Raleeya wanda ta shigo yanzu, suka zuba masa ido, cikin ƙufula Ummi tace. "Wai kam lafiyanka, kaketa dariya?." gyara zamansa yayi, cikin zumuɗi ya labartawa su Ummi duk abun daya sani. Ai kam su Ummi sosai suka shiga mamaki, sun kuma yi farinciki sosai, tabbas sun yarda cewa Allah Babu yanda baya abunsa. Raleeya kuwa cewa tayi. "Lallaima Aunty Zaleeha ashe dama duk wannan guje gujen naki, akan Hamma ne batare da kinsani ba." ita kuwa Zaleeha tana fita part ɗinsa ta nufa da gudu, dai-dai ta kawo bakin ƙofar shiga falon nasa, shima ya bude zai fito. Cikin wani irin tsananin sauri da rawan jiki da wani irin sabon shauƙi ta faɗa jikinsa, wani irin zazzafan runguma tayi masa me ratsa jiki da zuciya, azauce ta soma sakar masa wasu irin zazzafan kisa-kisai aduk fuskarsa harma da wuyansa, lips dinsa ta kamo tana tsotsa kana hannunta na shafa tsakiyar kanshi zuwa ƙeyanshi da kuma wuyanshi, duk ta zauce ji take kaman ta maidashi cikin jikinta, wasu irin hawayen farinciki ne suke kwaranyowa daga cikin idanunta, hannayenta tasa ta kamo kumatunsa, cikin wani irin mood da ɗaga murya tace. "I love you Hamma Saif, I really love you, I love you so so much, i can't live without you, nd I love you forever nd ever...." Amatuƙar zauce ta ƙare maganar. Wani irin kyakkyawan murmushi ya sakar mata, tare da zuba mata kyawawan idanunsa. Harshenta tasa ta lashi lips ɗinsa, cikin wani irin sanyi tace. "Inasonka Hamma Saif, Inasonka Sosai da sosai, meyasa baka faɗamin ba? meyasa ka ɓoyemin? tsawon lokuta da yawa ina bege da jiran zuwanka, mutane da yawa sunyi mini kallon zautacciya kuma mahaukaciya akan ka, natsumayeka, na kuma soka tamkar raina, Inasonka jiya, yau, yanzu, dama gobe, da jibi, kuma zanci gaba da sonka har gaban abada, kaine rayuwata Hamma Saif, bugun numfashi da zuciyata, tana tafiya ne da naka, kaine gaba ɗaya duniyata Hamma Saaaaaiiiiffff!!". Yanayin yanda taja sunan nashi shiyasa yaji gaba ɗaya duk gaɓɓan jikinsa sun amsa, idanunsa ya lumshe, alokacin da yaji ta kamo harshensa tana succking, ga kuma hannunta da ta ɗaura akan ƙirjinsa, tana murza kan nipples ɗinsa, kasancewar rigar jikinsa irin me aninayen nan ne, ɗayan hannun nata kuwa cusa shi tayi acikin gashin kansa, wani irin hot romantic kiss takeyi masa, wanda yasa gaba ɗaya sassan jikinsa ya amsa, bayajin zai iya jure salon da Zaleehan keyi masa, hakan yasa shi ƙara mannata da jikinsa, azafafe cikin matsanancin shauƙi suke kissing ɗin juna, sama da 20 minute suka ɗauka ajikin juna, duk sun gigita kansu, wani irin romance sukayi me tsayawa arai, ya sha mamakin yanda ta ciresa a hayyacinsa ƙwarai, saida aka ƙira sallan magriba, sannan suka iya janye jikinsu, baƙaramin dauriya yayi ba, na hana kansa kusantarta, dan kuwa ta kaisa ƙololuwa, saidai sanin cewa ba itace da shi ba, yasa baiyi yu ƙurin yin sex da ita ba, saboda hakan dai-dai yake da shiga haƙƙin Ameena. Ɗakinsa ya wuce dan dole saiya sake sabon wanka, dan ko tantama bayayi yanda suka murza juna yasan tuni sperm ya zo masa, ita ɗin ma Zaleeha hakanne ya kasance da ita, dan tuni ta jiƙe, saida tayi wanka sannan tayi alwala, cikin wani irin nishaɗi takejin kanta. Koda tayi sallah godiya tayi tayiwa ugangiji, bata iya barin sai tayi sallan ishaba ta kira Aunty Lubna tana jin ta ɗaga wayar cikin tsananin farin ciki tace. "Alhamdulillah Aunty Lubna, yau na gano wanda ya taimakeni ya ceceni a hannun ƴan iska". Tsoro da mamaki Lubna tace. "Innalillahi Zaleeha a ina kuma to me ruwanki dashi karfa ki mance ke matar aure ce". Cikin zumuɗi tace. "Mijina ne Aunty Lubna Hamma SAIF shine wanda ya taimakeni, shine naketa nema, ashe sanadin dukanshi da sukayi ya samu larurar nakasar tafiya My Aunty wlh I very very very love him, shine rayuwata". Tana gama faɗin hakan, ta katse kiran, ta kira Ya Ahmad ɗin ta, wanda yaketa dariya dan yana kusa da Lubna yaji duk magar da sukayi, jin yana dariya yana ce mata. "Aha ƴar uwarta na tayaki murna kice abin nema ya samu matar ɗan sanda ta haifi kulki an gano ɓoyeyyen masoyi ko". Da sauri ta katse kiran dan kunyarshi jin yadda yaketa mata dariya. Daga nan ta kira Rashida ta gaya mata nan itama tai ta mata tsiya harda cewa, "Allah ya sa dai yau kece dashi ki samu ki nuna mishi soyayyarki". Dogon tsaki tai tare da cewa. "Ke dai bari ai wlh kishiya bata haɗu ba". Dariyar Ishaq da tajine yasa ta katse kiran da sauri.shiko Ishaq da yake gefen Rashida akan sallaya da alama salla sukayi, dariya yayi sosai tare da cewa. "Masha Allah, ashe yanzu kam ana kishin aminina bare yau an gano shine masoyin da ake nema." Dariya sukayi baki ɗayansu. Hayatuddeen kuwa tuni ya kira Zakariyya ya shafa mishi zancen, shima Zakariyya jiki na ɓarin gulma ya shiga falon Baba Malam ya gaya musu, Dariya sukayi tare da sanya al'khairi. Saifudden kuwa tunda yaje sallan Magriba bai dawo gidan ba saida akayi sallan Isha. Yana dawowa kuwa dukansu suka haɗe a falo danyin diner, hadda Ameena dan tun kafun magriba ta dawo, saidai ta tsaya a sashin Ummi, bata ƙaraso sashin su ba. Koda suka zauna akan dinning ɗin Zaleeha ne tayi serving ɗinsu, gaba ɗaya jinta take awata duniyar farinciki, sam takasa ɗauke idanunta akan Saifuddeen, ji take kaman ta maidashi cikin jikinta, bataƙi ace su kasance tare ajikin juna ba, daga nan har zuwa ƙarshen rayuwarsu, shikansa yau kasa ɗauke idanunsa akanta yayi, dan shima yanajin kansa acikin nishaɗi, saboda yasan kome tayi masa abaya tayi ne abisa rashin sanin, cewa shi ne muradinta, tabbas yasan Zaleeha tayi masa wani irin mahaukacin so, wanda kuma ayanzu hakan ke bayyana acikin idanunta ƙarara, su Ummi kansu yau saida suka fahimci farincikin Zaleeha'n, dan ko abincin kirki bata iya ci ba. Haka dai suka kammala diner'n cikin nutsuwa, hira suka ɗan taɓa kaɗan kafun kowa ya nufi sashinsa, shida Ameena suka wuce part ɗinsa. Ita kuwa Zaleeha ta wuce part ɗinta, yaune karon farko da taji cewa inama da ace ita kaɗaine awajensa, tabbas da ace yau aɗakinta yake, da ta shayar dashi wata madaran soyayya wanda bai taɓa jin irinta ba, zata nuna masa tattali, da kuma soyayya me tsada da kuma tsabta, zata mantar dashi duniyar da yake ciki, da ma kuma shi kansa, lallai tashirya masa wani abu na musamman wanda ta tabbatar zaiyi alfahari da hakan, koda ta kwanta akan gado, hannu tasa ta shafi cikinta, idanunta ta lumshe saboda wani irin tsabar daɗin da taji, haƙiƙa Allah Na sonta, ya bata Hamma Saif ɗinta, ya kuma bata ɓoyayyen masoyinta, sannan ya bata ciki dashi, Baba Malam ɗin ta kuma ya yafe mata kafurai da dama sun musulta sanadinta aduniya ta gama samun komai. Can ɓangaren Saifuddeen da Ameena kuwa, a daren yau morewansu sukayi, dan sosai ya dage wajen bata haƙƙinta, bai barta ba kuwa saida ya zautar da ita, ya sata kuka da sambatun daɗi, dan har jin kanta take kaman ba'a duniya ba, lallai ta yarda Hamma Saifuddeen gwanine wajen iya sarrafa mace, lokaci guda yake gigita tunanin mutum. Washe gari da sassafe kuwa misalin ƙarfe 6 flight ɗinsu ya ɗaga zuwa sararin samaniya zuwa garin Lagos, har aiport kuwa su Ummi suka rakasu, haka suka rabu cike da kewar juna. Ci gaba da luluƙawa jirgin nasu yayi asararin samaniya, ahankali taɗan zame jikinta ta kwantar da kanta akan kafaɗansa, hannayensu kuwa dama sarƙafe suke acikin na juna, jin ta kwanta ajikinsa yashi ɗan shafa kanta, ahankali ta ɗago kanta, take kuwa idanunta suka sauƙa akan wata matashiyar budurwa da ta kafesu da ido, idanu Zaleehan ta zuba mata, tanason sanin inda tasan fuskar budurwan, take sunan budurwan ya faɗo mata wato Asma'u Ahmad Matawalle, ganin yanda Asma'un ke kallon Saifuddeen kaman zata cinyesa ɗanye ne, yasa taji wani irin zazzafan kishi ya cika zuciyarta, ƙasa-ƙasa ta harari Asma'u Ahmad Matawalle'n, ahankali ta ƙara shigewa jikin Saifuddeen ɗin, tare da juyo da fuskarsa gareta. Shikuwa sarai tun ɗazu ya lura da Asma'u Ahmad Matawalle'n, amma sai ya kawar da kansa, yayi kaman bai ganta ba, Zaleeha kuwa tayi hakanne saboda ta nunawa Asma'un cewa fa yana da mata, ga kuma tanan akusa dashi. Ganin hakane yasa Asma'un ɗauke idanunta daga kansu, dan kuwa sunyi masifar dacewa da junansu. Cikin zuciyarta tace. "Ikon Allah, yanzu kenan matansa biyu, ni dama tunda naji ance ya kara aure, na ciresa araina saboda najima da gane cewa, me aurensa sai me sa'a, bare irin wannan matar tasa gogaggiya wayayya, ga ta kyakkyawa, dole bazai kallemu ba, dan da dukkan alama balarabiya ce, dan wannan tsantsar kyaun ba abanza ba, me irin wannan macen ai bazai taɓa kallon wata mace ta burgeshi ba, dan duk wani kyau anƙaresa ajikin matarsa." Shi kuwa Saifuddeen ganin yanda Zaleeha ta lumshe idanunta ne, ya sashi ɗaura hannunsa akan cikinta, asanyaye ya hura mata iskan bakinsa me daɗin ƙamshi. Jin sauƙan iskan bakinsa, akan fuskarta, yasa ta buɗe idanunta, wani kyakkyawan murmushi ta sakar masa, tare da ƙara rungume sa, shiɗin ma murmushi ya mata, tare da ɗaura kansa akanta, haka suka kasance manne da juna, har jirginsu ya sauƙa a babban Airport ɗin dake Lagos DAN International Airport Lagos. Suna riƙe da juna suka fito daga cikin jirgin, already sun samu jirgin da zai kaisu ƙasar Turkey har zuwa garin Instanbull a ready, hakan yasa basu wani ɓata lokaci ba, suka shiga, ciken jirgin, suna shiga cikin jirgin kuwa, bai wuce da 30 minute ba jirgin ya tashi zuwa sararin samaniya. Saida sukayi tafiya me nisa, kafun ahankali ya ɗaura ƴan yatsunsa biyu akan wuyanta yana shafawa, akasalance taɗan ɓude idanunta, giransa ɗaya ya ɗaga mata alaman "Ya dai?." ɗan kwaɓe fuska tayi, cikin sakalci da kuma shagwaɓan daya zame mata jiki tace. "Na fara jin yunwa." kyawawan Idanunsa ya ɗan zaro, cikin yanayin mamaki, dan kuwa ko 30 minute ba'ayi ba, da ta gama cin su biscuits da snacks amma yanzu wai har tana maganan yunwa takeji. Murmushin daya ƙara bayyana kyakkyawar fuskarsa yayi, ahankali yasa hannu ya ja dogon hancinta, in a body language ɗinsa yace. "To acici kazar birni, ni kam har tsoron wannan yawan cin naki nake, kodai kin zama rumbun gwamnati ne." Ya ƙare yanayin maganan yana ɗan dariya. Ɗan ƙaramin bakinta ta turo gaba, mintsininshi tayi tare da cewa. "Ni ce ma acicin ko? to ai naga koma me kai ka jawo, tunda kaine kasamin yaro me ci acikin, haka kullum sai yata ƙwaƙulana, da zaran naci abinci sai ya kwashe, haka fa nakejin cikina kaman ba komai acikinsa, nidai wallahi kasan yanda zakayi dani ehe." ta faɗi maganar tana me shafa cikin ta, yanayin yanda tayi maganan yasa gaba ɗaya alamomin yarinta suka bayyana akan fuskarta. Jawota jikinsa yayi da kyau, tare da zuba mata ido, acikin jirgin nasu kuwa kowa harkan gabansa yake, kasancewar ba a normal sit suke zaune ba, wajen nasu na musamman ne VIP, ahankali yake ɗan goga hancinsa da nata, cikin nutsuwa ya kamo lips ɗinta masu taushi, wani irin tsotsa yake mata me kwantar da zuciya, sannu ahankali yake tura mata yawunsa abakinta tana haɗiyewa, sosai taji komai ya fara lafa mata, dan tayi imani yawunsa kaɗai sinadari ne ajikinta, kissing ɗin juna sukayi sosai sama da 25 minute, saida sukaji suna neman wuce gona da iri, sannan suka tsagaita, lub tayi ajikinsa tana sakin ajiyar zuciya. Tafiya suka sha asararin samaniya kafun jirginsu ya sauƙa airport ɗin, dake babban birnin Turkey wato _*Sahabi Gokcen International airport Instanbull*_ Yana riƙe da hannunta suka soma sauƙowa daga kan matattakalan jirgin, wani irin daddaɗan iska da kuma matsanancin sanyi ne ya soma ratsa duk ilahirin jikinta, haka ma Saifuddeen ɗin, saidai baza'a haɗa jin sanyinsa da nata ba, because ita me lafiya ce, shikuwa lafiyar tasa har yanzu da ɗan saura, saidai shima kuma yanajin sanyin. maƙalewa tayi ajikinsa ƙam, tana me ƙarewa yanayin garin kallo, Gari ne wanda ya haɗu sosai komai nasa atsare yake gwanin burgewa ko ina korayen itatuwa ga ruwan dake malale a lugguna da soƙoƙin garin, duk da cewa dare ya ɗan soma yi, hakan baisa mutanen cikin garin sun tsaida hada hadan da sukeyi ba, kowa rayuwarsa yake babu ruwan wani da wani, ganin yanda take ta kakkame jikinta alaman sanyin na shiga jikinta ya sashi tsaida musu me taxi wanda duk na cikin airport ɗin ne, me taxi ɗin da kansa ya sa musu kayansu abayan motan, sannan suka shiga suka zauna, wata ƴar farar takarda ya ciro daga aljihunsa, rubutu yayiwa akan paper'n sannan ya mikawa mai taxi ɗin, karɓan takardan yayi ya karanta, sunan hotel ɗin. _*Swissotel The Bosphorus Luxury Instanbull Hotel*_ ya rubuta masa, hakan kuma na nufin cewa, wannan hotel ɗinne yake so ya kaisu, take kuwa babu ɓata lokaci suka kama hanyar hotel ɗin. Basu wani jima suna tafiya ba suka iso bakin tangameme kuma haɗaɗɗen hotel ɗin, hotel ne da akayi masa tsari me kyau, komai gwanin burgewa kana a saman ruwa yake. Biyan me taxi ɗin, yayi sannan suka shiga cikin hotel ɗin, daga gefe Zaleeha ta zauna, inda shi kuma ya ƙarasa yayi musu duk wani abun daya dace. Wani haɗaɗɗen ɗaki ya kama musu, me shegen tsada da kyau, dan ko anan wajensu VIP ne sukafi kama ɗakunan dake area'n, wato Very Important People, hannunta ya kama suka nufi ɗakin nasu. Key yasa ya bude ƙofar ɗakin, da addu'a acikin zuciyarsa ya kutsa kansa cikin ɗakin, kana itama ta rufa masa baya, yayin da suka samu kansu acikin haɗaɗɗɗen falo, wani irin sassanyan ƙamshi ne ya daki hancinsu. Cikin mamakin haɗuwan falon Zaleeha tace. "Wow, gaskiya wajen nan ya haɗu, can you imagine seriously ban taɓa tunanin haka wajen nan ya haɗu ba." yanayin yanda tayi maganan tana ɗan yawo acikin katafaren falon, shi ya sashi sakin murmushi, yasan Zaleeha tanason abubuwan ƙyale-ƙyale, da kuma duk wani abu daya shafi shaƙatawa, shiyasa yayi amfani da hakan, wajen kama musu ɗakin da yasan zai gamsar da ita, burinsa akullum shine ya faranta mata, saboda bayan so da ƙaunarta dake kwance acikin zuciyarsa, akwai tarin tausayinta, shi me rauni ne akanta ƙwarai. Zaleeha dake ta santin falon nasu, wanda yake ɗauke da two bedrooms acikinsa, sai gefe kaɗan kuma wani haɗaɗɗen dinning area ne, idan ka ƙara gaba kuwa, wani haɗaɗɗen decoration akayi, sannan aka kewaye wajen da wani haɗaɗɗen cottings me shara shara, daka yaye cotting ɗin kuwa, wani haɗaɗɗen swimming pool ne wanda aka masa tsari me kyau, ruwan cikinsa sky blue me masifar ƙamshi. Juyowa tayi ta kalli Saifuddeen ɗin, wanda tun shigowansu idanunsa akanta suke, murmushi tayi masa tare da masa waving fingers ɗinta, cikin son tsokanansa tace. "Hey Bravo, wannan kallon fa duk na miyene? wato kaga big girl, big ajibo, shine kake neman haukacewa akaina ko, well kacigaba da kallo na, maybe anjima na iya kula ka." Dariya irin marar sautin nan yayi sosai, dan yasan zallan tsokana ce kawai ke damunta, ƙwafa yayi tare dayi mata alaman cewa. "Hmmm zan kamaki ne ƴan mata." Tagefenta ya raɓa ya nufi ɗaya daga cikin bedroom ɗin falon, ita kuwa Zaleeha tsayawa tayi tana ƙarewa kowani kusurwa dake falon kallo kujerune ɗika-ɗikane suka zagaye da falon sai wani tattausan carpet dake malale a tsakiyar falon da akayiwa daɓe da katakon ƙasashen wajen, ga wani ɗimemen tv a manne wanda kana zaune a gefe ma zakiyi control ɗinshi da wayarka, sai wani ɗan danda mali da akayi aka zagayeshi irin ɗan abun nan da suke hura wuta a ciki dan ɗumama ɗakunan, itakam har acikin zuciyarta wajen yayi mata hundred percent. Saifuddeen kuwa rage kayan jikinsa yayi, sannan ya shige bathroom, shi kansa bathroom ɗin abun kallo ne, dan sun tsarasa sosai yayi kyau, duk da madai duka jikinsa Glass ne, koda ta shigo ɗakin taga bayanan abakin haɗaɗɗen gadon ta zauna, tare da ɗan jingina kanta, numfashi take fitarwa ahankali, dan kowani gaɓa na jikinta ya amsa da sanyin Instanbull, dan idan tana taka ƙafarta ji take kaman tana taka ƙanƙara, aranta tace. "Gaskiya garin nan akwai sanyi, dashi da Mascow ko wanne yafi sanyi oho." Fitowarsa daga cikin toilet ɗinne yasa ta kalleshi, ganin ya nufi gaban mirror yasa itama ta tashi ta shiga toilet din, ruwan zafi ta haɗawa kanta, cikin nutsuwa tayi wanka, wani jibgegen bathrube tasa ajikinta, kasancewar duk da tayi wanka bata daina jin sanyi ba. Koda ta fito ta samu har ya kimtsa kansa cikin dogon wando da kuma wata jibgegiyar rigan jeans, wayar dake ɗakinne a hannunsa, da alama saƙo yake turawa. Jakar kayanta ta buɗe ta zaro wata doguwar riga me ɗan kauri, duk da tasa kayan, sai faman rawa jikinta yake saboda sanyi, sam bata saba da irin yanayin ba, shiyasa takejin sanyin sosai, amma idan ta zauna agarin na wasu lokuta asannu sanyin zaibi jikinta. Ƙaton darduma ya shumfuda musu, da hannu yayi mata alaman cewa tazo suyi sallah, babu musu kuwa tasa jibgegen hijab ɗinta, shi ya jasu sallan ƙasaru raka'a bibbiyu, dan lokacin har ma locakin sallan isha ya cika, koda suka idar da sallan, basuyi gaggawan miƙewa ba, saida suka ɗanyi karatun Alƙur'ani, lokacin daya gama karatun yana ƙoƙarin rufe alkur'anin ne, ta kwanto jikinsa, cikin shagwaɓa tace. "Allah Hamma Saif yunwa nakeji." Ajiye Alƙur'anin yayi, ya ɗagota, hannunta ya kama, sannan ya hau wheelchair ɗinsa, kallonta yayi cikin body language ɗinsa yace. "Naga alama nanda mintuna kaɗan, idan ban kaiki kin ci abinci ba, ni zaki cinye." Dariya tayi sosai, tana ƙoƙarin cire hijabin jikinta tace. "Shikenan ma ai da yaron cikina ya huta, dan nakusanta shi da Babansa." Murmushi kawai yayi mata, ita kuma wani mayafi ta ɗauka ta yane kanta, hannunta ya kama suka fita daga cikin ɗakin, cikin nutsuwa suke tafiya har suka iso, wani katafaren Restaurant dake cikin hotel ɗin, Oasis Restaurant kenan, restaurant ne me kyaun gaske dab kusa da ruwa yake haske a wurin tamkar da rana, suna da delicious foods da yawa, kan wani parmanent sit suka zauna. Ɗaya daga cikin ma'aikatan hotel ɗinne yazo, dan tambayansu abun da suke so, abun da Saifuddeen ɗin ya zaɓa itama shi ta zaɓa, saida suka ci abincin, kafun yasa aka kawo nusu new sim, wanda zasuyi amfani dashi, tun kafun su kammala cin abincin Zaleeha keta kakkame jikinta, saboda sanyin da takeji, shiɗin ma dai yanajin sanyin amma ba sosai ba, hannunta ya kama suka koma ɗakinsu, suna shiga ta faɗa kan luntsumemen gadon, tare da jawo babban blanket ta rufe kanta dashi, shikuwa Saifuddeen ɗayan ɗakin dake cikin falon ya shiga, yana shiga kuwa yayi locked ɗin ƙofar, wayarsa ya ciro tare da dannawa numbern Ummi ƙira, dai dai lokacin kuwa Ummi na zaune afalo, ita da Hayatuddeen, ganin ƙiran Saifuddeen kuma vedio call yasa ta ɗaga cikin sauri. Sallama ya mata, cike da kewarsu yace. "I miss you Ummi na." Murmushi Ummi tayi, tare da cewa. "I miss you too Babana, ya kuke fatan kun sauƙa lafiya." Kansa yaɗan shafa asakalance yace. "Lafiya ƙalau Ummi, yasu Hayatuddeen." tun kafun Ummi tace wani abu, Hayatuddeen dake gefe jin an ambaci sunansa ya sashi matsowa jikin Ummi da sauri yanda Saifuddeen ɗin zai gansa, cikin zumuɗi yace. "Gani Hamma Lafiyata ƙalau, ina Adda Zaleeha, nasan tana nan tana ta fama da sanyin Instanbull ko." Murmushi Saifuddeen din yayi tare da cewa. "To sarkin surutu, ita ta faɗa maka haka." Dariya sukayi dukansu, ganin baiga Raleeya bane ya sashi cewa "Ummi ina Raleeya?" murmushi Ummi tayi tare da cewa. "Raleeya tana sama, ko aƙira maka ita ne." Kansa ya girgiza alaman a'a, bama sai anƙirata ba, dama yana son sanin lafiyarta ne. Hira suka ɗan taɓa da Ummi da kuma Hayatuddeen sannan sukayi sallama. Yana katse ƙiran ya laluɓo numbern Ameena. Ita kuwa zuwa lokacin harta fara bacci, amma jin ana ƙiran wayanta yasa ta buɗe ido, ganin shine ke ƙiran yasa ta ɗaga da sauri, ganin fuskarta ya sashi sakin murmushi, cikin daddaɗan muryarsa yace. "Amaryata." Murmushi tayi tare da ɗan kashe masa ido, cikin shauƙin sonsa tace. "Kun isa lafiya." "Lafiya ƙalau, ya gida ya Adeel ɗina yayi bacci ko." Kai ta jinjina masa, tare da cewa. "Ya Ammin Adeel." Murmushi ya ɗanyi asanyaye yace. "Tana nan lafianta ƙalau." kai ta jinjina cikin kulawa tace. "Kai fa ya kake?." Ɗan shagwaɓe fuska yayi, akasalance yace. "Ina nan lafiya sai kewarki kuma daya cikamin zuciya, kinyi missing ɗina kuwa?." Cikin sanyi tace. "Sosai ma kuwa, nayi kewarka Abban Adeel, musamman ma daddaɗan ƙamshinka da kuma lips ɗinka." idanunsa ya kashe mata, ahankali ya lashi laɓɓansa, cikin salonsa yace. "Nasan ba iya ƙamshi da lips ɗina kikayi missing ba, gwamma ki faɗi abun dake zuciyarki, ko kinaso kicemin kin mata da abokinki ne, wanda yake saki ihu da kukan daɗi." Dariya tayi sosai tare da sa hannu ta rufe fuskarta, dan taji kunya ƙwarai, amma inda sabo yaci ace zuwa yanzu ta saba da halin Saifuddeen ɗin, dan shi babu abun daya dameshi, yanzu sai yasa mutum yaji kunya. Ganin tana dariya ne yasa shi cewa. "Ko dai na ciro miki itane ku gaisa." Da sauri ta girgiza kai, cikin son koransa tace. "A'a nagode ni bacci ma nakeji saida safe zamuyi waya, karka sani wankan dare." Dariya yayi, itakuwa da sauri ta katse wayan. Maida wayar tasa aljihu yayi, sannan ya fito daga ɗakin, direct ɗakin da suka sauƙa ya nufa. Har zuwa lokacin kuwa Zaleeha na kwance, sai rawan sanyi takeyi. Kayan jikinsa ya cire, inda ya saura daga shi sai boxer, hawa saman gadon yayi, tare da buɗe blanket ɗin da ta rufa kanta dashi, ya shiga ciki, jin motsinsa yasa cikin kasalalliyar murya tace. "Helf me Hamma Saif sanyi nakeji sosai." Hannuwansa yasa ya ɗagota jikinsa, cikin nutsuwa ya soma ƙokarin cire mata kayan jikinta, sam bata hanashi ba, saida ya rabata da komai na jikinta, daga ita sai pant ya barta, idanunsa da suka sauƙa akan tsayayyun beautyfull brast ɗinta ya ɗan lumshe, dan har tsakiyan ƙafarsa yaji wani abu, ya tsarga mai, ita kuwa jin ya maida ita naked yasa ta shige cikin jikinsa, wani irin ƙatuwar ajiyar zuciya suka sauƙe atare, sakamakon wani irin ɗumin daɗi da sukaji ya ratsa su, ahankali ya sanya hannunsa ya tallafo fuskarta, hakan yasa numfashinsu gauraya waje ɗaya, idanunta da ke cike da mayen sonsa ta lumshe, dan ganin wani irin shu'umin kallo da yake binta dashi, harshensa ya zaro ahankali ya laso fatar wuyanta, tare da sakar mata wani zazzafan kiss wanda yasa numfashinta kusan ɗaukewa, dogon ajiyar zuciya taja tare da ɗan ɗaga kanta sama, hakanne ya bashi daman tura kansa acikin wuyanta, wani zazzafan kiss yake sakar mata wanda har saida kan nipples ɗinta suka tsuke, sosai yake yawo da harshensa akan wuyanta, wanda yasa lokaci ɗaya ta soma sakin numfashi, cikin matsanancin sha'awarsa dake taso mata da son nuna mishi zazzafa sonshi dake binne a ranta, ta ɗago fuskarta, asanyaye ta haɗe bakinta da nasa waje ɗaya, wani irin hot kiss suka bawa juna, inda ya zamana laɓɓanta na ƙasa na cikin bakinsa, shi kuma lip ɗinsa na sama na cikin nata bakin, yanayin yanda suke sarrafa bakin juna ne yasa gaba ɗaya ta fara manta inda take, cikin yanayin son gigita mata lissafi, ya gangaro da hannunsa zuwa kan breast ɗinta, ahankali ya shiga shafa su da kuma murzasu, wani irin shishita tasoma yi masa, tare da ƙara kama lips ɗinsa tanayi masa tsotson lolli pop, wani yanayine takeji na ratsa gaba ɗaya jikinta, dan yanda yake murza breast dinta, yasa duk ta gigice, haka shiɗinma ya fara loosing controll ɗinsa, saboda tsotsan da takewa lips ɗinsa, sun isa zautar dashi. sama da mintuna 10 ya ɗauka yana murza breast ɗinta, ahankali yasomayin ƙasa da hannunsa, inda yake yi mata tafiyan tsutsa, har ya gangaro zuwa kan mararta, cikin ƙwarewa ya tura hannunsa acikin pant ɗinta, ahankali yake shafa saman mararta, cikin son ƙara zautar da ita, ya kai ƴar tsarsa dai-dai bakin pp ɗinta, slowly haka yake ɗan shafa wajen da tuni ya koma damina. Wani irin zillo me cike da shauƙi Zaleeha tayi, dan hakan da yake yi mata baƙaramin gigita takeji ba. Ahankali yake sake sarrafata , jin santsi da taushin wajen, ne yasa yaji tsikar jikinsa na tashi, ga kuma Saif ɗinsa dake ƙara hauhawa har wani zut zut takeyi masa, ahankali hankali yake sarrafa ta wani irin daddaɗan dumi yaji acikin jikin nata, ahankali yake lailaya tongue dinta dake cikin bakinsa, yayinda ɗaya hannunsa kuwa ke kan breast ɗinta yana murzawa. Ya gigita Zaleeha, dan har wani irin kwaranya take, gaba ɗaya jikinta rawa yake, babu abun da take buri da fata, kaman tajisa sun kasance abu ɗaya, hannayenta ta cusa acikin gashin kansa, tana sakin wani irin gigitaccen numfashi, miƙar da ita yayi ahankali ya bude kyawawan ƙafafunta, tundaga kan tafin ƙafanta yake lasa da sumbata har ya kawo kan santala santalan cinyoyinta daketa sheƙi, pink lips ɗinsa ya ɗaura akan mararta yana ɗan gogawa, wani irin zubawa tsikar jikinta ya somayi, agigice ta ƙira sunansa cikin wata irin murya, dake ɗauke da zallan shauƙi. Adai-dai wannan lokacin kuwa bazai iya amsa mata ba saboda shima ya gigice, harshensa ya kawo dai- dai saitin pp, cikin wani irin masifaffen shauƙi, ya ɗaura bakinsa akan pp ɗin nata, ahankali yake zuƙe duk wani fitinar dake wajen, wani irin numfarfashi haɗi da zafafan nishi ta soma fitarwa, tuni ta gigice ta kuma fita hayyacinta, wasu irin sambatu take masa, wanda ita kanta bata san me take faɗa ba, Saifuddeen kam jinsa yake asararin samaniya, dan haɗuwan taushin bakinsa da kuma na privet part ɗinta, yasa duk ya zauce, sam bayajin me Zaleehan ke faɗa, wanda ayanzu har kuka ta sakar masa saboda shiɗewa. Jin kaman zata sume masa ne, yasa shi sanya hannayensa ya ɗan ɗagota, faɗawa jikinsa tayi tana sakin wani irin nishi, hanneyenta dake rawa tasa ta kamo Saif dinsa, dake neman mafaka, bakinta ta ɗaura akan Saif ɗin tana goga harshenta akai, wani irin zazzafan numfashi yake fitarwa, me haɗe da nishi. Sosai take sucking Saif ɗinsa, wanda ta sake gigitashi. Ganin suna neman sumar da kansune ya sashi kwantar da ita ahankali ya mata ƙawanya, bakinsu ya haɗe waje ɗaya, tare da haɗesu suka zame abu ɗaya a wuri ɗaya alokaci ɗaya suka sake wani irin gurnani, sakamakon wani irin abu daya game duk jikinsu, agigice ya saki wani irin ƙara haɗi da sambatu, saboda wani irin dumin da Saif ɗinsa ta samu kanta aciki, lokacina da Saif ɗinsa ya gama samun mazauni, wawan ajiyar zuciya suka sauƙe, Saboda wani irin gigitaccen dadi daya ratsasu, kukan daɗi ta saka masa, tana sakar masa sambatu, shikansa baya cikin nutsuwarsa, sambatu yake mata haɗi da guranani me kama da kuka, ji yake kaman saif ɗinsa zata fita daga jikinsa tsabar dadin daya samu kansa aciki, haka yakejin kansa kaman yana iyo acikin kogin zuma, surutai yake tayi yana zuba mata wasu haɗaɗɗun kalamai da kuma sambatu, dake nuna zallan fitar hayyacinsa, daga ita har shi babu wanda yasan aduniyar da suke. GIGITAN yayi gigita wa Hamma Saif ya mance yana ɓoyewa Zaleeha warakarshi na ji da magana ya mance yanata zanga surutu da rakaɗi, wanda ita kuwa Zaleeha can cikin yanayin da takeɗin take tsinkayo muryarsa....! By *GARKUWAR FULANI* Downloaded from GNOVELS.COM.NG This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG For feedback and support Facebook : https://facebook.com/gnovels Twitter : https://twitter.com/gnovels Telegram : https://t.me/gnovels