Downloaded from GNOVELS.COM.NG This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG For feedback and support Facebook : https://facebook.com/gnovels Twitter : https://twitter.com/gnovels Telegram : https://t.me/gnovels  [6/4, 4:21 PM] Jakadiyar Arewa:                  RUƊIN ƘURUCIYA PERFECT WRITERS ASSOCIATION (WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS) https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ P. W. A *Story and written by* AISHA ADAM (AYSHERCOOL) Writer of WATA KISSAR..(Sai mata) ABDUL JALAL AƘIDATA (paid book) WUTA A MASAƘA NOW RUƊIN ƘURUCIYA (paid book) Free pages are not much, subscribe for ₦300 only. Contact 07063065680 for more information                              Page 1 Harabar makaranta ce babba sosai, ɗauke da manyan ajujuwa, da dogayen ƙawatattun benaye, wanda suka sha tiles, a kowane aji yana ɗauke da na'urar sanyaya guri, ko ina ƙal ƙal babu datti ko ƙazanta, kallo ɗaya zaka yiwa ɗaliban dake zirga zirga, da ita kanta makarantar kasan cewa tabbas duk ɗan dake wannan makaranta, ɗan masu ido da kwalline, ko wanda ya tsaya masa ya tara masu gidan rana. Ɗalibai mata sanye suke da shuɗin skirt me cizawa ga mata, maza kuma wando, se farar riga 'yar ciki me dogon hannu, se kuma 'yar saman kalar skirt ɗin, se ƙaramin farin hijabi ga musulmai mata, saka ƙaramin hijjabin ma ra'ayi ne, babu tilas saka shi ga ɗaliban, da yawa ɗalibai matan skirt ɗin nasu iya gwiwa ne, wasu kuma da kaɗan yafi gwiwar su, da yawansu Uniform ɗin nasu sun matsesu matuƙa, kuma galibin ɗalibai mata suna cire rigar saman kayan su bar ta cikin suna yawansu. Da yawa masu wannan shigar, za kaga matasan 'yan matane, da suke kan tashen balaga, gasu 'yayan gata, dan haka suna ɗauke da ƙirane me matuƙar kyau da ɗaukar hankali, haka ɓangaren ƙananan yaran ma da suke firamare, wasunsu kansu ko ɗan kwali babu, kai kace makarantar ƙasashen ƙetare ne, saboda yanayin tsarin makarantar da ɗaliban da ke ciki. Ɗaliban sunata hada hadarsu, sun fito break, wasu na ciye ciye, wasu wasanni wasu kuma suna hira, ƙararar sautin jiniyane ya karaɗe ilahirin makarantar, wanda hakan ke nuna lokacin komawa aji yayi, domin cigaba da ɗaukar darasi. Nan ɗaliban suka shiga komawa cikin azuzuwansu, dan cigaba da ɗaukar darasi. Gaba ɗaya makarantar tayi tsit, an koma aji, dan tuni wasu sun fara ɗaukar darasi ma. wata tawagar ɗalibai maza da mata ce ta ɓullo harabar makarantar, a ƙalla sun kai su goma, suma sanye da Uniform suna tafe suna hirarsu suna ƙoƙarin bin wata baranda dan komawa ajin su. Wani malami ne yai musu tsawa da harshen turanci "hey, from where are you? " Wata zaƙaƙura a cikinsu ta kalli malamin cikin iyayi tace. "we went out for breakfast" 'who gives you the permission to go out? Don't you know that you supposed to be in your classes by now?" Malamin ya sake maganar cikin tsawa. Wani ɗan kyakkyawan saurayi ne a cikinsu ya ɓata rai sosai, ya kalli malamin Yace "No need to seek permission from anyone, we have the right to go where ever we want at any time to have our break, we are semifinalist, and the teachers have to wait for us to come back, because our parents pay for it, hope I made myself clear?" Cikin zafin rai malamin Yace "Are You stupid?, is this the way you supposed to talk to me? Semi finalist ɗin banza, me ka taka a harkar karatu da kake gayamin wai You Are semi finalist" Matashin ya ɗage kafaɗa alamar oho maka, sannan Yace "it seems that you are New here, anyway this is our policy you have to go and know more about it" Shewa sauran ɗaliban suka dinga yi suna.  "Weldone The Lion prince, munga yazo da zafinsa yana ji da izza, zamu sauke masa duk wannan zafin kan nasa" Suka tafi suka bar malamin baki buɗe yana binsu da kallo, a ransa yace 'in dai dagaske haka yaran nan suke, to basu da tarbiyya sam" Ya juya ya nufi ofishin Director. Sukuwa ɗaliban ajinsu suka nufa, suna sake koɗa wannan matashin,ya kallesu Yace 'kuje class, ni zan tsaya inga sanyin idaniyata" Yai maganar cikin sanyin murya, wanda ke tabbatar da abunda yake faɗa har ransa. Ɗaya daga tawagar ɗaliban ya daki kafaɗarsa yace. "shegen kaya, kai dai ka dage akan yarinyar Nan' Murmushi yayi, bece komai ba suka wuce aji, shikuma ya nufi wata hanyar. Window wani aji yaje ya tsaya ta waje, ba malami a Ajin, ɗaliban ajin kowa na abunda yaga ze fishseshi, wasu na hira, wasu na waƙe waƙen su, suna rawa.  can ya hango ta a gefe ɗaya ita kaɗai, ta duƙufa tana ta rubuce rubuce, ta nutsu sosai ta maida hankali akan abunda take yi, fito ya yayi da ƙarfi wanda seda ya janyo hankalin da yawa daga cikin ɗaliban, suka waiwayo. Da sauri ita ma ta juyo dan ganin wanda yake fiton,  ta ganshi a jikin window yana kallon ta. Yai mata alama da hannunsa da tazo, mmurmushi tayi, sannan ta miƙe tana nufar hanyar fita daga ajin, cikin takunta na ƙasaita me cike da nutsuwa da kamala, me tafiya da zuciyarsa. Gaba ɗaya ya ƙura mata ido, gani take duk takun da take tamkar tana girgiza jikinta ne, ta fito tazo inda yake tsaye tace 'good morning' Seda ya gama ƙare mata kallo sama da ƙasa, sannan ya murmusa ya shafi sumar kansa da ke ta ƙyallin mai yace "Morning my love, baki zo class ɗinmu ba yau, lafiya dai ko?" Tai murmushi, wanda ya sanya fararen haƙoranta bayyana, ta ɗan rausayar da kanta  tace "lafiya ƙalau classwork nakeyi, shiyasa" Yai murmushi Yace "kinci Abinci kuwa?' Ta jinjina masa kai alamar eh. Ya ɗan gyara tsayuwarsa yace "Ƙarya kike, naji a jikina bakici komai ba, ga Abinci nan nazo miki da shi, kije ki ci, sannan ki bani classwork ɗin, zanje aji in Miki" Cikin shagwaɓa tace "what if I was asked, to explain how I did it?" Yace "You should tell them, that am the one who did it, bana son gaddama, karɓi takeaway ɗin nan, ki ɗakkomin littafin, zanje class ɗinmu in miki ki zauna ki huta" Tasan halinsa, idan ta cigaba da jayayya ransa ze iya ɓaci, dan haka ta koma class ɗin nasu ta ɗakko masa littafin da take classwork ɗin, ta dawo ina da ta barshi a tsaye ta miƙa masa, ya karɓa ya bata ledar hannunsa, ta karɓa cikin jin kunya tace "Thank you very much" "Meye wani Thank you kuma? Is my responsibility to take care of you baby, idan na gama zan kawo miki, koma class Ina kallonki, kar wani abu ya taɓa min ke" Tai murmushi ta juya, yabi bayanta da kallo, seda taje ta zauna yana kallonta ta window, sannan ya juya, ya koma nasu ajin. "Yallaɓai yaran nan basu da tarbiyya sam, baka ga yadda suke min magana ba ɗazu, duk premises ɗin makarantar nan be isa suyi break ba se sun fita? Kuma su dawo lokacin da suka ga dama, ana kallonsu na musu magana suna nema su zageni" Director ya gyara zaman Glass ɗin fuskarsa sannan Yace "Naji abunda duk ka faɗa corper Nazir, Amma abunda baka sani ba shine, wannan yaran na ss2 lallaɓasu muke mu rabu lafiya, dan ko na samansu ss3 basa bamu ciwon kan da suke bamu, duk yaran makarantar nan da yawansu yaran manyane, sedai kusan na Ss2 iyayensu manyane sosai masu faɗa aji, taɓa yaran nan tamkar barazana ne ga makarantar nan, shiyasa muke binsu sannu a hankali, hadda 'ya'yan ministoci da kwamishinoni a cikinsu" "amma Yallaɓai, bafa karatu kawai suke buƙatar a koya musu ba, harda tarbiyya fa, wannan zasu iya baka kunya wataran a gaban wanda bekamata ba, makaranta ba gurin koyon karatu bane kawai, yarane matasa da ake sa ran sune Manyan gibe, yakamata su tashi da tarbiyya" "Nazir, yaran nan jarine a gareni da makaranta ta, daga 'ya'yan manyan sojoji sena 'yan siyasa, kuma duk competition da aka fita da su se an ciyo shi, ga iyayensu suna sakin kuɗi sosai, mezesa in bari a ɓata musu rai? Kuma duk wata tarbiyya ai ana musu a gidajen su, su sun san yadda suke tarbiyyar yaransu, amma taɓa yaran nan matsala ne babba, kawai ka dinga kau da kanka, kana haɗawa da haƙuri dan ba kowane ubane yake yadda da a horar masa da yaro ba" Corper Nazir yabi director da kallon mamaki, be sake cewa komai ba ya tashi ya tafi, dan ze shiga Jss2 yanzu. Shikuwa matashin yaron nan ajinsu ya koma yaje ya duƙufa, yana solving classwork ɗin daya karɓo. "Prince, waime kake yi ne haka?" Cewar wani daga ɗaliban, ya ɗago idanunsa ya ɗan kalleshi Yace "Farhan na kewa classwork" "amma meyasa kake mata? Naga yarinyar dai itama ƙwaruwace a ajinsu fa" "eh nasani Amin, na kai mata Abinci ne, idan ban karɓa na mata ba, ba zata maida hankali taci Abinci ba" Al'amin da sukewa laƙabi da Amin yace "gaskiya kana yin yarinyar nan over prince" "Ƙwarai kuwa, Farhan is my wife to be inshallah" Kwashewa da dariya Amin yai yace "How? Yaushe ka gama karatu, kayi jam'ia ka aureta? Jiranka zata tsaya yi, just enjoy your life with her, beauty one's are yet to born, zaka samu wata zazzafar da fita ne ka Aureta" Prince ya girgiza kai Yace "I have a plan for our feature, dan haka bana wannan lissafin da kake yi, Farhan kawai" Amin Yace "gaskiya ne mutumina, Allah ya kaimu lokacin, amma dai wannan kamar tayi ƙanƙanta kasamu mace me suna mace mana" Prince yace "Amin, ka kalli Farhan da kyau, za'ayi babbar mace nan gaba, nidai a haka nake sonta, size ɗinta da komai yai min yadda nake so" "To Allah ya barku Tare" "Ameen ya Allah" Ya duƙufa seda ya kammala mata class work ɗin, kasancewar yana da yawa , yana kammalawa ya miƙe ya tafi ajinsu Farhan, kamar kullum tana zaune a gefe ɗaya, 'yan ajinsu basa wani shiga harkarta kasancewarta ba 'yar masu kuɗi kamarsu ba, saboda ita scholarship ne ta samu, saboda wani competition da taci, aka bata scholarship ɗin, gata suna ganin bata waye ba kamar su, dan haka basa involving ɗinta a sabgarsu, itama bata musu shishshigi kullum tana gefe, ba ruwanta da kowa se karatunta, sekuma Yanzu da Prince ya shigo rayuwarta. Duk hayaniyar da ake a ajin, Prince na shiga sukayi tsit, dan juniors suna tsoronsa, saboda akwai dealing, baya son raini sam. Ya ƙarasa seat ɗinta ya zauna a kusa da ita Yace  "Baby gashi na gama miki" yai maganar yana ajiye mata littafin. Ta sa hannu ta ɗauka tana dubawa, ta ɗago tai murmushi tace "Nagode sosai Prince" Maimakon ya mata magana, seya kashe mata ido ɗaya. Sunkuyar da kanta tayi cike da jin kunya. Yace  "ya kika wani sunkuyar da kai? Ina fatan babu wata matsala dai ko?" Ta jinjina masa kai alamar eh. Yace "Ai idan ma akwai matsalr bazaki iya faɗa ba, ke naga maganar ma wahala take baki Farhan, nasan maybe yanzu malami ze shigo muku, bari in koma ajinmu, amma kisani zanzo musamman kimin hira, ina son dinga jin muryarki sosai, saboda tana sani nutsuwa" Ji take kamar ƙasa ta tsage ta nutse dan kunya, gashi ya tsareta da idanunsa, gaba ɗaya nauyinsa take ji. Corper Nazir ne ya shigo ajin, ɗaliban suka miƙe suna gaisheshi, banda Prince dake zaune, Nazir yabishi da kallo, yana tunanin meya kawo wannan fitsarraren yaron kuma Jss2. Prince ya miƙe ya kalli Farhan yace "Mu haɗu in an tashi' Daga nan ya juya ya fice abunsa. Corper Nazir Yace  "Ke Farhan, meye haɗinki da wannan yaron mara ɗa'a?" Farhan ji tayi kamar Nazir ya soketa, Sadik ɗinta ne wai mara ɗa'a. Shiru tayi ba tace komai ba, "Am talking to you Malama" yai maganar cikin tsawa. Sunkuyar da kai ta sake yi, jikinta na rawa amma ta kasa furta koda kalma ɗaya. Daga can gefe wani ɗalibi yace  "sir saurayinta ne" "Saurayi kamar yaya?" "Ai duk makarantar nan, babu wanda be san budurwar prince bace, saurayinta ne" cewar ɗalibin. Aikuwa Cikin faɗa Nazir Yace  "baki da hankali ne? Kina Jss2 harkinsan wani saurayi? Shi iyayenki suka turo ki yi? Kuma ma wannan shegen yaron mara ɗa'a kike kulawa, zakiga saurayi sena zauna da babanki na gaya masa, come out here and kneel down, stupid girl kawai, zaki ɓata rayuwarki kina jss2 amma kin san wani saurayi" Gaba ɗaya ido ya dawo kan Farhan, ta fito jikinta na rawa, kamar ta nutse tazo gaban class tayi kneel down. Nazir ya ƙaremata cin mutunci tsaf a gaban 'yan ajinsu, taji zafin abinda malam Nazir ya mata, dan haka nan da nan se ta fara hawaye, wani na bin wani kuka sosai, kamar ƙaramar yarinya. "Will you shut up your mouth, stupid girl kawai, a haka kamar mutuniyar kirki, kin biyewa wannan sakaran yaron" Sadik daya koma ajinsu kuwa, ya tarar classmates ɗinsa maza sun haɗa kai suna kallo a waya, matan kuma suma sun ja nasu gurin, suna Magana ƙasaƙasa suna shewa. Ya ƙarasa ya leƙa abunda su Amin suke kallo, sedai ƙirjinsa ne ya buga da ƙarfi, yaja uban tsakiya ja da baya. Amin ya ɗago ya kalleshi Yace  'babban yaro ya dai, ku matsa masa yazo ayi dashi mana" Cikin damuwa ya girgiza Kai Yace  "Ni bazan iya kallon wannan shirmen da kuke kallo ba" Nasir ya kalleshi yace  'ji banza sekace ba namiji ba, wannan ba shirme bane alaji, just come an enjoy" Sadik ya girgiza Kai Yace  "I can't, kuma Allah ya shiryeku, dan ubanku zaku makance da wuri ne, kawai ku kewaye waya kuna kallon blue Film, shegu zakuyi bayani idan Allah ya tona muku asiri" Amin Yace  'dan Allah malam ƙara gaba, tunda bazaka kalla ba ai shikenan" Sadik ya samu kujera yai zamansa ya ɗakko wayarsa, yana Game. Seniors ne suka shigo class ɗin Ss2, kansu ɗauke da colored ties, mazan kuma huluna alamun prefects ne, wata zaƙaƙura a cikinsu cikin harshen turanci kamar baturiya tace  "who ever knows he spoke vanacular, should come out and pay his 500, before I call names" Banza sukayi musu, basu ko ɗago kaiba balle su tanka musu. Nan ta ƙame ta fara kiran sunayen wanda sukayi Hausa, Sadik yana ji aka faɗi sunansa, amma ƙafafunsa na kan benci yana cigaba da game ɗinsa. Babu sunan kowa a ciki sena Sadik, dama shi duk wata doka a makarantar nan, shine ke fara karyata a makarantar nan. Ɗaya daga cikin prefects ɗin yace "Sadik, magana fa ake maka" "Bazan biya ba" ya basu amsa "You Are still speaking vanacular , you know you must pay' cewar wadda ta kira sunayen. "Ke wallahi bazan bayar ba, baza'ayi turancin ba, yaren uwatane kona ubana? Ko meye haɗina da wasu turawa da senayi yarensu, har a wani dinga cewa wanda yayi hausa seya biya, baza ai turancin ba, kuma bazan biya ba tunda ba ubankine yake bani kuɗin ba" Dukan benci tayi ta nuna Sadik tace "don't insult me Sadik" 'idan na zagekin me zakiyi? Jeki gayawa duk uban da zaki gayawa, yarene a makarantar nan se wanda naga dama zanyi, bazan turancin ba, uban turancin, ke uban mungo park da sarauniyar England, ƙaryar banza kawai ba za'ai turancin ba" Fitina sosai Sadik yaso tayarwa, dan da an ƙyaleshi ze iya dukan yarinyar nan. Wata ɗalibace ta shigo ajin tana faɗin  "Prince, ga Farhan can an sata kneeldown a rana, tayi wa wannan corper ɗin laifi, kuma wai tayi vanacular ance ta biya kuɗin vanacular tace "bata da kuɗi". Ashar Sadik yayi Yace  "what! Farhan ɗin?" Beyi wata wata ba yai waje, hakan yai daidai da shigowar wani malami, da aka sanar masa ana rigima da Prince a ajinsu, ya taho yai maganin abun, sukayi karo da Sadik a hanya, yana masa magana amma yayi masa shiru, ya ture malamin yai hanyar ajinsu Farhan da hanzari. Baiwar Allah, Farhan tana ƙofar ajinsu tayi kneeldown tana ta zubar da hawaye, ga zafin rana. Sadik yaji tamkar ya ɗora hannu a kai yai ihu, ya ƙarasa inda take da sauri Yace "waye ya saki wannan abun?" Kasa magana tayi, se kuka da takeyi beyi wata wata ba, ya jata office ɗin director. Sadik se huci yake, director ya kalleshi Yace "Prince Sadik, what's wrong? Why is she crying?" "Sir, ka shiga tsakanin mu da wannan new corper ɗin, why Will he gave her such kind of punishment, and that stupid Tina humilate her because of 500 naira, is she not a human being?" Director ya kalli Farhan dake ta faman kuka, idonta yayi jawur, shidai yasan Sadik bashi da alaƙa da Farhan,  amma yana gudun ɓacin ran wannan yaron, Yaron fitainanne ne, akwai taurin kai da rashin ji, sedai uwarsa zata iya ɗaure malami akan sa, ana ji da shi a gidansu kamar ɗan gwal, sama baya taɓuwa yarin nan, dan haka Yace "is ok my Boy, zan ɗau matakin daya dace, kayi haƙuri , Farhan kiyi haƙuri kinji" Farhan dai ba tace komai ba, se kuka da take yi, Sadik yai waje a zuciye tabi bayansa, ya rakata har bakin toilet,yace ta shiga ta wanke fuskarta, ya jirata ta shiga ta fito, ya kalleta Yace  "duk wanda ya kuma saki wani purnishment a makarantar nan, koya miki ba daidai ba kizo ki gayamin kinji ko? Ko " Ta jinjina masa kai, Yace  "Akwai inda yake miki ciwo ne?" Cikin muryarta me narkar da zuciya tace  "kaina yana ciwo, da ƙafata" "shikenan, muje class ɗinmu ki huta in Baki paracetamol" Ba musu ta bishi, dan bata iya kaucewa umarnin Prince Sadik, ko da wasa bata zaton zata iya kaucewa umarninsa. Tabbas nickname ɗin nasa na Prince ya dace da shi, saboda gashi Young adult be gaza shekaru goma sha shida zuwa sha bakwai ba, amma yana jida kansa, giyar arzikin iyayensa da tashen balaga na matuƙar ɗawainiya da shi. Suka je ajinsu, ya bata paracetamol, ta karɓa ta sha, ta kifa kanta akan benci ta lumshe idanunta. Babu daɗewa, aka kunna jiniya, alamar lokacin tashi yayi. Farhan ta tashi, Sadik yaje class ɗinsu Farhan ya ɗakko mata jakarta, suka fito harabar makarantar, inda dandazon motoci suke taruwa, domin ɗaukar yaran gata. Farhan tace "bani Jakar, zanje in hau napep in tafi gida" "No ga motar gidanmu nan, muje semu saukeki a gida, kinga baki da lafiya" A ɗan tsorace tace  "za'ayi min faɗa fa a gida, idan aka ganni a motar ku" "Karki damu, ba wanda ze miki komai" Haka yasa ta shiga motar, shima ya shiga, ta gayawa direban inda gidansu yake, suna tafe Sadik yana jera mata sannu, Tare Da yin ƙwafa lokaci zuwa lokaci. Aka zo bakin layin gidansu Farhan, ta kalli Sadik tace  "Nagode sosai Prince" "Ki kirani da suna irin na masoya mana, haba my Farhan" yai maganar yana sunkuyo da fuskarsa daidai tata. Rufe fuskarta tayi cike da jin kunya, yace  "idan baki faɗa ba, zamu yi ta zama a motar nan ne fa" yai maganar yana sake kafeta da idanunsa kamar wani babban saurayi. "Toni me zance?"  Tai maganar a shagwaɓe. Kasa magana yay, se ido da yake binta dashi, a hankali yace "koma meye kice kawai my wife" "Thank you my Love" ta faɗa cike da jin kunya, kamar wadda tai saɓo, kasancewar shine mutum na farko data furtawa kalma me girma haka. Ya lumshe idanunsa Yace  "ina sonki my Farhan, jeki gida kar ayi miki faɗa, idan aka yi miki faɗa bazanji daɗi ba" Tai murmushi ta buɗe motar, ta fita har direban zeja motar, Sadik Yace  "tsaya inga ta shiga gida mana" Direban ya tsaya yana mamakin, wannan taɓara da ƙarfin hali  gami da tsaurin ido na wannan Yaro, ko secondary school be kammala ba, amma yasan ya tsara yarinya ta soshi, itama kuma ta biye masa maimakon ta maida hankali akan karatunta, Koda yake duk RUƊIN ƘURICIYA ke damunsu. Sadik kuwa bin bayan Farhan yayi da kallo, duk da ta ɗora ƙaton hijjabi akan uniform ɗin nata, seda ya dena hangota sannan Yace  "mu tafi gida" Direba yaja mota suka nufi gida. Suna zuwa tangamemen gidan, direban ya kutsa da motar yai parking, Sadik ya buɗe motar ya fito, kai tsaye cikin gidan ya shiga, sakamakon shriye shiryen bikin Yayansu da ake, mutane suna ta shige da fice a gidan nasu. Yana kallon mutane a falo, amma ya hau bene, ba tare da ya kula kowa ba. Yayar mahaifiyarsa ce ta hangoshi ta shiga kiran sunansa  "Sadik, kana kallon mutane amma ka wuce baka kula kowa ba?" "Zan kulaku anjima idan kuka ragu, duk kun cika mana gida" Be jira me zata ce ba ya ƙara gaba, ɗakin mahaifiyarsa ya shiga, ya tarar da ita tana ɗakko kaya a wardrobe ɗinta, ta dubeshi tace  "sweetheart, ka dawo ya school ɗin?" Cikin shagwaɓa Yace "Am so much tired , gashi duk an wani zo an cika mana gida da hayaniya" "Sorry, kasan shirye-shiryen bikin yayanka ake yi, dole mutane suzo amma ko zaka ɗakinka na BQ ka kwanta ka huta?" Girgiza kai yayi Yace  "No, a ɗakin Daddy zan wanka in kwanta, a kawomin Abincina nan" Ta shafa sumar kansa tace  "considered it done my auta" Yace  "Mother dan Allah a miƙomin jallabiyata, idan kin sauka ƙasa" Ta jinjina masa kai, Sukayi murmushi tare, ta fita daga ɗakin. Banɗaki ya shiga ya watsa ruwa, ya fito daga shi se gajeren wando ya tsaya a gaban mudubi, yana ƙarewa kansa kallo, Farhan ce ta faɗo masa rai, a hankali ya lumshe idonsa, yana saƙawa da warware abubuwa da dama a ransa. Buɗe ƙofar ɗakin akayi tare da yin sallama, ya amsa ba tare da waiga ba, saboda yaga me shigowar ta mudubi. "Sadik manya, ashe ka shigo amma ba labari, ko neman mutane baka yi" Murmushi yayi Yace "ai ban san kina gidan nan ba, na dawo kawai na tarar an wani cika falon, babu ma hanyar da zanbi in wuce ɗakina, shiyasa kawai na taho nan" Ta ƙarasa inda yake tsaye, ta ajiye kayan Abincin, sannan ta ɗora masa ash ɗin Jallabiyarsa a kafaɗarsa tace "gashi nan, Mother ce tace in kawo maka, sarkin rashin son Mutane" Yai murmushi, yana ƙoƙarin zira jallabiyarsa, ta ƙura masa ido sannan tace  "Semi finalist, next year by now insha Allah an kusa grad, kaima ka wuce Dubai" "Waye yace miki zanyi SS3, this year zan gama makaranta ni" Tace  "meyasa zaka gama this year? Jumping zakayi kenan?" Ya juyo ya fuskanceta sosai sannan Yace  'Khairat, jumping zanyi in kammala secondary School this year insha Allah, saboda Aure nakeso, Aure zanyi nan kusa" Kwashewa Khairat tayi da dariya tace  'look at you, dan kaga kana da girman jiki? Secondary school fa zaka gama, Yaya Usman ma daza'ayi Aurensa Yanzu, seda yayi PHD, wakake tunanin ze maka wani aure yanzu?" Ƙurawa khairat ido yayi sannan Yace "kina ganin nayi ƙanƙanta inyi auren ne?" 'ƙwarai kuwa, guda nawa kake zakayi zancen wani aure? Better build your future my friend, and stop talking this rubbish" Tai maganar tana dariya, ta bar ɗakin. Sadik ya daɗe a tsaye a gurin yana tunani, sannan ya ɗakko sallaya ya tada salla, bayan ya idar yaci Abincinsa ya kwanta. Farhan ma harta koma gida, ta shirya ta tafi islamiyya, tunanin Sadik ɗinta ne a zuciyarta, tana tuna yadda yake yawan kyautata mata, amma abun tambayar anan shine, zasu iyayin aure kuwa ita da Sadik? Ita dai tana jin ƙaunarsa sosai a cikin ranta. Se yamma sosai Sadik ya tashi, yai sallar la'asar sannan ya sakko ƙasa, har yanzu gidan da mutane sedai sun ragu ba kamar ɗazu ba, Yayyansa ne maza zaune tare da Yayar mahaifiyarsu, suna shirya atamfofi a cikin akwati, wanda za'a kaiwa Usman na lefe. Sadik ya nemi guri ya zauna, yana bin kayan da kallo. Mamansu Khairat ta kalli Sadik tace "dan ƙaniyarka ina maka magana ɗazu, amma kamin banza ko?" Yai murmushi Yace 'na gajine, kaina na ciwo, gashi kuma an cika falon, shiyasa ban tsaya ba, wai wannan kayan duk na lefen ne?" Maman Khairat tace  'eh gasu nan, jibi zamuje mu kai masa insha Allah" Usman Yace "Autan mother Babu ko kara, ko 'yar sarƙa baka siya ka bani ba, a matsayin gudunmuwa" Sadik Yace  "gaba ɗaya fa siyayyar nan kaɗan ce akayi maka a Nigeria, duk a waje aka yota, kowa yazo baka kuɗi kawai yake kaida Mummy, kuma kace Sena saimaka abu na  baka duk kuɗinka Bross" Faruk Yace  'ji ɗan rainin hankali yaron nan dan Allah, duk gidan nan babu wanda ake sakarwa kuɗaɗe kamar ka fa" Usman yace  "wallahi kuwa, yaron nan kuɗine dashi kamar banza a account bema san me zeyi dashi ba" Sadik ya karkace ya gyara zamansa akan kujera yace  "aini na dena cin kuɗina, nima lefe zan fara tarawa, next year by now za'a kamin nawa lefen" Maman khairat tace "Usman, dan Allah makemin mara Kunyan yaron nan" Sadik yace "Nifa Mummy dagaske nake, aure zanyi nima, zamu yi magana da Daddy idan ya dawo gari, nifa banƙi a haɗa bikina dana Yaya Usman ba" Umar ne ya kai masa duka Yace "yi mana shiru dan ubanka, mara kunya kawai, ubanwa ze maka auren? Ko dan kana ganinka ƙato haka? Better concentrate on your study, shikansa Bross Usy seda ya haɗa PHD ze aure balle Kai, da yanzu Balagar ta zo maka " Harar Usman Sadik yayi Yace  "meye wani PHD?  Aure ze hanani karatune? Ai da sauƙi tunda balagara ta zo, Zan baku mamaki kwanan nan. Ya miƙe yana zumɓura baki ya bar falon. Ayshercool 07063065680 [6/4, 4:21 PM] Jakadiyar Arewa: ✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨ RUƊIN ƘURUCIYA PERFECT WRITERS ASSOCIATION (WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS) https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ P. W. A *Story and written by* AISHA ADAM (AYSHERCOOL) Writer of WATA KISSAR..(Sai mata) ABDUL JALAL AƘIDATA (paid book) WUTA A MASAƘA NOW RUƊIN ƘURUCIYA (paid book) _Labarin RUƊIN ƘURUCIYA, na iya zuwa da wani salo, wanda baku saba ganinsa a rubutuna ba, hakan ya biyo bayan akan abunda aka gina labarin, wani abun ze ɓoyu wani Abun baze ɓoyu ba sakamakon labari ne akan teenegers, yara masu tashen Balaga, but hakan ba ya na nufin na sauka daga kan tsarin yadda nake Rubutu bane, ƙofata a buɗe take dan karɓar ƙorafi, gayra ko shawara_                             Page2 Sadik na fita harabar gida, ya tarar abokansa sunzo wai zasu snuka, ya bisu suka fice dan yaje ya sarara. Corper Nazir kuwa ya sha faɗa a gurin director, saboda ƙararsa da Sadik ya kai, ya dinga mamakin wannan lamari, shikenan dan yaran masu kuɗine baza'a basu tarbiyya ba? Yara duk ba ɗa'a? Ai makaranta ba iya gurin koyon karatu bane, hadda tarbiyya shikenan se a zuba musu ido su lalace, baza'a tsawatar musu ba dan kar iyayensu suji haushi? Abun ya dameshi sosai, Tare da ganin rashin ma'anar wannan lamari akwai buƙatar a duba, idan bahaka ba rayuwar yaran zata ɓaci a banza. Da wannan damuwar ya koma gidan daya kama, da yake ba'a camp yake a zaune ba, gida ya kama yake zaune a ciki. Washegari ya shirya Domin zuwa makaranta, kamar kullum anyi assembly an gama, Farhan nata rarraba ido taga ta ina zata hango Sadik, sedai bata samu ganin nasa ba, ta duba inda yake tsayawa amma baya nan, duk setaji ta damu, haka aka sallamesu suka tafi azuzuwansu. Sadik kam yau makara yayi sosai, corper Nazir yana harabar makarantar a tsaye yana zazzagawa, dan tabbatar da komai ya tafi daidai. Motar gidansu Sadik ce ta kunno kai cikin makarantar, har Corper Nazir ze shiga cikin makaranta, yaga zuwan Sadik, dan haka ya tsaya. Sadik ya fito daga mota, ya rufe motar ya saɓa jakarsa, ze shiga cikin makarantar. Cikin shouting corper Nazir yace "hey come here' Sadik ya juyo ya kalleshi, sama da ƙasa kamar kar yaje, sukuma yaje kiran, yana wani bossy walking yaje inda Nazir yake tsaye, Nazir ya kalleshi yace  "why are you just coming?" Sadik ya kalleshi ya ɗauke kai. "Check your watch, what's the time now?" Sadik ya ɗauke kai kamar ba dashi ake magana ba, principal ne ya taho inda suke tsaye, yana faɗin"what's going on here?" Nazir Yace  'Sir, wai Babu wani penalty na makara kowani laifi, idan yaran nan sun karya doka? Kalli lokacin da yazo makaranta, kuma na yiwa director magana akan haka amma ya nuna min is like you don't punish them" Principal ya kalli Sadik yace  Yace  "Sadik, why are you late? Baka san lokacin da Yakamata kazo school bane?" Tura baki Sadik ya shiga yi, yana hararar Nazir. PC yace  "idan ka sake makara, sena baka punishment me wahala, ɗau jakarka ka bar gurin nan kafin in ci mutuncin ka" Sadik ya ɗau jakarsa fuuu yai cikin makarantar, yana tunanin yadda ze koyawa Nazir hankali. Principal ya kalli Nazir yace  "ka manta da director, duk abunda yakama na hukunci a hukuntasu, shi yana la'akari da yadda ze samu kuɗine kawai, shiyasa baya goyon bayan hukuntasu, kuma wasu daga yaran iyayensu nada kuɗi yanzun nan se su ɗaureka, amma dan dai punishment wanda zasu iya, in sunyi laifi kar a saurara musu" Nan suka cigaba da tattaunawa akan matsalolin yaran. Koda Sadik yaje ajinsu da malami a ciki Yana lesson, amma babu neman izinin shiga ko makamancin haka, ya kunna kai cikin ajin nasu, yaje gurin zamansa ya zauna, Tare da ajiye jakarsa, fuskar nan tasa a ɗaure yana ta jan tsaki. Duk ajin suka waigo suna kallonsa, daga bisani malamin ya cigaba da Koyarwarsa. Sadik be saurari me Malamin ke koyarwa ba, ya kifa kansa akan benci, zuciyarsa cike da jin haushn irin yadda Nazir ke zaƙewa da son cusawa hukumar makaranta wani ra'ayi na daban akansu, dole yayi maganin Nazir. Malamin na fita su Amin suka zo inda Sadik yake, Nasir Yace"babban yaro ya dai? Meyafaru ne mun ganka Wani iri" Sadik yayi tsaki Yace  "dan Allah ku rabu dani" Amin yace "haba Sadik, Ya hakane? Mun tambayeka meyafaru kana wani cin magani" Banza Sadik yayi musu, suka gama surutunsu 'yan matan class ɗin ma sukazo kan Sadik suna nasu surutun "Babban yaro waye ya taɓo mana kaine?" Kamar da Dutse suke Magana, yai musu shiru ƙarshe se haƙura suka yi suka ƙyaleshi. Farhan kuwa gaba ɗaya ta kasa nutsuwa, ta kasa samun kwanciyar hankali saboda rashin ganin Sadik, ɗalibai kowa yana harkokinsa amma banda Farhan. Ganin da tayi zaman baze fishsheta ba, yasa ta miƙe ta nufi hanyar ajinsu Sadik. Tana zuwa gaba ɗaya ta kasa shiga, ta tsaya a waje tana leƙa ajin, ba zata iya shiga ajin ba, saboda na Seniors ɗintane, gashi bata san kowa a ajinba se Sadik, dan haka tana jin nauyi sosai. Ta window ta tsaya, tana leƙawa dan taga ko zata hango Sadik ɗinta. "What are you doing here?" Da sauri ta waiga dan ganin me Maganar, Nasir ne abokin Sadik, ya kalleta yace "ko kina Neman Sadik ne?" Farhan ta ɗan sunkuyar da kai, cike da jin kunya. Nasir ya ɗan tsaya yana ƙare mata kallo, da jinjinawa mugun jin kunya na Farhan, se dai babu mamaki irin wannan halayyar ga 'ya'yan talakawa, sam basu da wayewa. Yace "to ki shiga mana, yana ciki ai" Kamar wadda aka yiwa dole, ta shiga ajin can ta hango Sadik, zaune ya kifa kansa, gabanta ne ya faɗi tai tunanin ko bashi da lafiya ne? Da ɗan hanzari ta ƙarasa bencin da yake zaune. Jin mutum a kusa da shi ne yasa ya ɗago da sauri dan yiwa wanda yazo kusa da shi ɗin masifa, sedai kuma yayi tozali da fuskar Farhan. Ajiyar zuciya ya sauke, bece komai ba. A hankali tace "baka da lafiya ne?" "No Farhan, lafiyata ƙalau" "Amma ban ganka a gurin assembly ba?" "Nazo a makare ne, kuma wancan corper ɗin ya ɓatamin rai, sena gyara masa zama tukuna" Farhan tace "me yayi maka?" "Yana min shishshigine, dan yana saka wannan koɗaɗɗun uniform ɗin na NYSC, idan be kiyayeni ba zan koya masa hankali" Farhan tace  "kasan meyasa ya sani punishment jiya?" Sadik ys girgiza mata kai, tace  "wai saboda kaje gurina, ya tambayeni meke tsakanina da kai, shine 'yan ajinmu suka faɗa masa, shine yaita min faɗa ya sani kneeldown" Sadik ya daki benci yace "har akwai wani sakaran daze sawa soyayya ta ido a makarantar Nan? Wallahi idan mutumin nan be kiyayeni ba sena sa an karairayamin shi"  yai maganar a harzuƙe wanda seda hankalin 'yan ajin ya dawo kansu. Aminu Yace  "wai kai Sadik meke damunka ne?" "Wannan Nazirun ne, da gemu kamar soson wanka wallahi ya cigaba da shiga sabgata kota Farhan wallahi sena masa illa" Farhan ta kwantar da murya tace  "dan Allah kayi haƙuri, dana sani ban gaya maka ba" Wata cikin 'yan class ɗinsu Sadik me suna Amina amma suna cemata meenal ta taɓo ƙawarta tace  "Taslim, kina ganin wani abu kuwa, wannan budurwar Sadik ɗin akwai iya barikanci, kalleta saliha kuma yarinya amma ta dabaibaye zuciyar ɗan mutane ji yadda take masa magana" Taslim tace "ke dai Bari, kina gani Tun ɗazu muke tambayarsa meya dameshi, yai banza damu amma tana zuwa ya ɗago kansa, na rasa meya ja ra'ayin Sadik akan yarinyar nan, kaf class ɗin nan Sadik bashi da budurwa,  ya rasa a inda zeyi budurwa se a Jss2, duk wannan iyayin nasa. Meenal tace  "lallai ma ke ɗin nan, Sadik wayone da shi ya samo yarinya fresh, wadda bata san komai ba ya koya mata sonsa, zeyi tattalin kayarsa kuma ki ƙare mata kallo, yarinya ce amma me ƙirar manya, tana da zubin halitta me jan hankali sosai" Suka cigaba da gulmarsu a gefe, Sadik kam se banbami yake akan Corper Nazir, Farhan tace  "ni ka dena wannan faɗan ko in tafi" "Farhan ya bazanyi faɗa ba, yana nema ya kassaramin soyayya, ina ruwansa damu?" Nasir Yace "Sorry Prince, ai komu ba zamu bari a kassara wannan soyayyar ba, wadda muke saka rana ta shiga kundin tarihi kamar ta su Laila majnun" Kamar Farhan za tayi kuka tace"dana sani ban gaya maka ba, nace fa kayi haƙuri" Sadik yai shiru yana cigaba da huci, Farhan tace  "kayi haƙuri mana, dan Allah ka dena fushi Kaji, ka ga malamnmu ne, koba komai ya koyar damu, ka dena zaginsa" Sadik Yace "ke dalla ƙyaleni, na tsani mutumin nan wallahi" Miƙewa Farhan tayi zata tafi, jin yadda yayi mata magana a tsawace, ya riƙo hannunta da sauri, wanda hakan ya haddasawa Farhan mummunar faɗuwar gaba, taga kamar kowa suyake kallo. Tace "ka dena taɓani, meye haka?. Sadik yace "am sorry, na dena amma dan Allah kiyi haƙuri, zauna" Farhan ta nemi Guri ta zauna, yace "kiyi haƙuri bazan sake ba insha Allah" Ta zauna tana ɗan tura baki, taƙi kulashi, ya sake kashe murya yace "haba na face kiyi haƙuri" Tai murmushi tace  "Na haƙura ai" Suka cigaba da hira ita da Sadik, yama  manta da maganar wani Nazir. Har aka koma class Farhan bata sani ba, tana zaune tana hira da Sadik cike da nishaɗi, duk da mafi yawan hirar shi yake mata, ita murmushinta yafi yawa akan magana. "Ke Farhan!" Sukaji muryar Sir Nazir. A rikice Farhan ta waiga, dan ji tai an kira sunan nata tamakar saukar Aradu, Kamar yadda ta zata sir Nazir ne ba wani ba. "What are you doing here? Is this your class?" Ya tambayeta yana zazzaro ido. Cikin tsoro Farhan ta girgiza kai, alamar a'a  yayinda attention ɗin class gaba ɗaya ya dawo kansu, kowa ya zubo ido. "Me kikeyi a kusa da namiji a zaune? Ajin ku ne nan? Tashi ki bar ajin nan ki koma ajinku" Sadik ya fusata ze yi magana, Farhan ta girgiza masa kai, ta tashi da sauri ta fita, Sadik ya tsaya yana kallon kallo da Nazir. Naziru yai ƙwafa ya fice, yana fita Sadik ya daki benci yana muzurai, Nasir Yace  "easy Prince, kayi haƙuri" "Mutumin nan yana wuce gona da iri fa, zanyi masa kaca kaca a makarantar nan wallahi" "Kayi haƙuri, zamu san matakin da zamu ɗauka a kai" Farhan kam da Kusan gudu ta ƙarasa ajinsu, ai kuwa Nazir ya rufa mata baya, a gaban 'yan ajin ya shiga zazzaga mata bala'i. "Ke wace irin yarinya ce ne? Abunda kike kin kyautawa kanki ko iyayenki? Gurin wannan ɗan iskan yaron aka turoki? Me kike zuwa gurinsa yi?" Yai maganar yana tsatstsareta da ido. Farhan ta girgiza masa kai, alamar ba komai. "Wallahi idan baki shiga hankalin ki ba sena haɗa miki assembly, kuma in kira mahaifinki in gaya masa abunda kike aikatawa, gara tun wuri ki fita harkar wannan ɗan iskan yaron, tun be lalata Rayuwar ki ba" Farhan tana jin zafin cin mutuncin da Nazir yake mata, sedai jinsa kawai take dan bata tunanin zata iya rabuwa da Sadik,sum sum taje ta zauna a gurin zamanta tana sunkuyar da kai, Nazir na cigaba da zazzaga Mata cin mutunci. "Irinku ne masu komawa iyayensu da ciki ,ku lalace tunda ƙuruciyarku, saboda RUƊIN ƘURUCIYA na ɗibarku, sun turo ki kiyi karatu amma kina biyewa 'yan iska, a haka gaki kamar saliha amma baki da hankali, in sake ganin kinje inda yake, sena zaneki a makarantar nan" Farhan tai shiru, ta sunkuyar da Kai tana jin yadda maganganun nasa ke mata dirar mikiya a ƙirjinta, taji zafin yadda yake cin mutuncin ta a gaban 'yan ajinsu, dan seda tayi kuka, sedai sam maganganun nasa basuyi tasiri a zuciyarta ba, dan bata tunanin zata iya rabuwa da Sadik, tun da ita dai bata ga aibun Sadik ba, a barshii da zafin rai dai wasu lokutan da rashin son raini, amma yana da sauƙin kai sosai, sedai ta yanke shawarar zata yi duk me yuwuwa ta nesanta kanta da Sadik ko dan kaucewa cin mutuncin Sir Nazir da dizginsa da kuma gudun kar ya haɗa ta da mahaifinta, dan a duniya tana tsoron Allah, tana tsoron mahaifinta sosai. Nazir ya gama faɗansa san ransa sannan ya shiga gabatar da lesson ɗinsa. Har ya gama karatunsa Farhan kuka take yi, dan sam na ta fahimci komai ba har yai ya gama. Bayan ya fita wata daga cikin'yan ajinsu wadda ake cewa Lilly tazo ta dafa kafaɗar Farhan, Farhan ta ɗago kanta ta kalli Lilly. "Ki dena kuka ki rabu da wannan ɗan rainin hankalin kinji, ki dena kuka" Farhan ta jinjina mata kai alamar to. Koda aka tashi daga school, Farhan bata jira kowa ba ta silale ta tafi gida, Sadik yaita nemanta be ganta ba, haka ya haƙura ya tafi gida, yana mamakin yadda aka yi ta tafi basu haɗuba. ********** Gudu gudu sauri-sauri haka ta faɗo makeken tsakar gidan, hannunta ɗauke da jakar makaranta, tana zuwa ba tayi wata wata ba, tai jifa da jakar a tsakar gida, ta faɗa banɗaki. Dattijiwar dake zaune tana mulmula fura, ta kalli jakar makarantar da yarinyar ta jefar a tsakar gida, ta girgiza kai ta cigaba da aikinta, kusan mintuna biyar sannan ta fito daga banɗakin, ta tsaya a tsakar gida ta shafa cikinta tace  "wayyo Allah, fitsari idan ya matseka ba arziki, ina tafe a hanya kamar zanyi hauka, saboda yadda ya matseni" Dattijuwar ta kalleta tace "zaki zo ki ɗauke wannan jakar da kikayi jifa da ita a tsakar gida, ko kuwa se nayi yaƙi da bakina" Ɗan tura baki tayi, taje ta ɗauke jakar Tata, ta kai cikin  ɗaki ta ajiye, ta cire duk kayan jikinata, ya rage daga ita se dogon wandon makarantar ta, ta fito tsakar gida tana faɗin "Innarmu, wai yau me aka dafa ne?" Inna ta ɗago zata yi magana, amma taci karo da yadda yarinyar ta fito tsakar gida. "Nana waike wace irin sha3 ce ne haka? Kalli fa a yadda kika fito, kowane lokaci za'a iyayin sallama a shigo gidan nan, amma kika fito tsakar gida a haka" Ummi ta ya mutsa fuska ta kalli kanta tace "to ni innarmu me nayi?" "Dan ubanki baki san kin fara girma bane? Dubi ƙirjinki kin fara ƙigar dangi, amma kin fito a haka bako Kunya, ko 'yar shimi ba ki saka ba" "Meye kuma ƙirgar dangi?" Ummi ta tambaya cike da wauta. Inna tace "kin wuce kin nemi riga kin saka, ko sena taso na iskoki a gurin nan, gaɓuwa kawai ba kya ganin yadda ƙirjinki ya tasa? Amma kike yawo a haka? Karki adana su ki bari su fito a wulaƙance, naga alamar idan banyi dagaske ba, haka zakiyi budurci ba kintsi, 'yar butar uwa da kai kamar gwai gwai" Ummi ta faɗa ɗaki, tana kumbura baki, dan bata son wannan faɗace faɗacen na Inna, Gashi idan ta tashi yi bata rufe komai, haka za tai ta sakin bayani, ko a gaban waye kuwa haka za tai ta sakin zance da sunan faɗa. "Sarkin faɗa, ke da waye kuma da tsakar ranar nan kike faɗa haka?" Cewar dattijon da yake shigowa, jikinsa sanye da Alkyabba. "Dawa zanyi faɗa banda wannan yarinyar, duk gidan nan wake sani magana banda Nana, yarinya kamar ba'ace mata bari, taɓara da iya shege sinƙi sinƙi a cikinta" Dattijon yai murmushi Yace "haba ke kuwa, takwarar taki guda, Ki dinga haƙuri da ita, yarinyace har yanzu ke kike ganin girmanta, amma yarinya ce ƙarama" 'ko da yarinta, harda iskancinta wani lokacin, bata taɓa jin daɗi idan bata sani magana ba" Yai murmushi Yace  "to yanzu dai ba wannan ba, zuwa wani satin insha Allah, gidan Abdullahi  zasu kawo lefen Usman ɗin, ina fatan kina nan kina shiri?" Inna tace "eh ina shiri, naji yace bikin bada tsawo za'a saka ba, ina ga idan suka kawo Kayan, zan bisu se kuma anyi biki, dan bana son yawan tafiyar motar nan" But Nana dta fito daga ɗaki da ɗaurin ƙirji tace "Alhaji wai waye zeyi aure ne? Wai su wannan ɗin nan na birni?, wanda basa dariya sosai masu tara gashin nan kamar ƙabilu? 'ya'yan kawun nan?". Dattijon Ya buɗe baki Yace "yayyen naki ne baki san sunansu ba? Se masu tara gashi?" "Ni a ina zan san sunansu, bayan ba kula mutane suke ba, kuma ma ba zuwa gidan nan suke ba" Alhaji ya jinjina kai Yace  "ikon Allah, lallai wannan abu bemin daɗi ba, Dole a tafi da Nana, kuyi kwanakin Tare, dan ta ga 'yan uwanta sosai" Ummi tai tsalle tana faɗin "yee, zani birni inje asha bikin 'yan gayu dani" Inna tai tsaki tace "mara hankali, ai idan kikaje ma kallon kwantacciya zasu yi miki, musamman matar Abdullahi, me wa mutane kallon banza" Alhaji Yace "ai haka nan za'aje da Ita, rashin zumuncin yayi yawa, ace ba tama san sunayen su ba, shikenan ace yaran nan ko garin nan basa zuwa, balle su shaƙu da 'yar uwassu?" Inna tace  "to ya zamuyi tunda uwarsu bata so? Nace a kai maka furar turakarka ne idan an dama?". "Eh, a kawomin turaka, ina so idan na sha na ɗan huta, zanyi baƙi da yamma" Inna tace "to shikenan, Allah ya baka yawan rai, zan kawo insha Allah" Ya nufi hanyar ɗakinsa, Inna ta tashi, ta wanke hannunta, ta shiga ɗaki, ta tarar da Nana da ɗaurin ƙirji tana shirin Dutse" "Nana kinyi salla kuwa?" "Inna ai da sauran lokaci fa" "To kuma kafin kiyi wanka, ba lokaci yayi ba?" Nana ta zumɓura baki tace  "wai Inna ba nayi wankan nan da safe ba? Shikenan ni kullum cikin wanka kamar wata tarwaɗa?". Inna tace "kyaci ubanki, lokaci na nan zuwa da za kiyi medalili, wanka ba wataran da asubar fari, koman sanyi haka zakiyi shi" "Wankan?" Nana ta tambaya cike da mamaki. Inna tace  "ƙwarai kuwa wankan da ki ke gudu, kuma dole ki koyi wanka da tsafta tun Yanzu kina gida, gaba nake jiye miki, kuma Yanzu ki ke girma kina kan tashen balaga, warin jikinki daban ze dinga fita, kuma duk wanda ki ka bari yaji wari a jikinki kin faɗo, ze dena ganin mutuncin ki, kuma dan ubanki na sake ganinki da ɗaurin ƙirji Sena makeki, idan baki alkinta abubuwan nan ba haka zasu fito ba tsari, kiyi 'yan matanci amma nono a zube, kizo kiyi aure ba zasu dinga birge miji ba" "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, waike Innarmu kiyi ta faɗan magana ba kyajin kunya" Inna tace  "Naƙi inji kunyar, idan ban gayamiki ba wani a waje zan jira ya gaya miki?, kin tashi kin tafi wankan ko sena zo inda kike? Na watsar da ke" Nana ta tashi tana bubbuga ƙafa, da takaicin yadda Inna ke sata wanka ba gaura ba Dalili, ta ɗebi ruwa ta tafi banɗaki. Bayan shigar Nana banɗaki, Inna tace "A kula idan za'ayi wanka, a wanke hammata da kyau, wuya da duk wani lingu.... 'innalillahi Inna na haddace wallahi, na haddace ko karatune wannan na iya ke kullum sekin nanata min yadda ake wanka wai?" 'rufemin baki, gara in nanata miki ai, dan banƙi in zuba ruwa in wankeki da kaina ba,wani warin jikin yana faruwa ne daga rashin iya wanka tun a ƙuruciya, in kin gama wankan ga ruwan alumun nan da miski ki shafe jikinki dashi" Nana ta yiwa Inna banza, dan wannan karatuttukan na Inna basa ƙarewa. Inna ta damawa Hakimi furarsa, ta shiga kai masa, ta tarar dashi yana dariya, ta kalleshi tace  "lafiya naga kana dariya?" Yai murmushi yace  "dariya nake miki keda jikar taki, kina takura yarinyar nan da yawa fa" Inna tace  "a'a ba takura bace, gara in gaya mata ai, duk da Allah be taɓa bani 'ya mace ba, amma ni ban yadda se an sawa yarinya rana, sannan a dinga gaya mata ƙabali da ba'adi ba, tun tasowar yarinya ya kamata a dinga koya mata yadda zata kula da kanta, da yanayin Rayuwar Aure" Hakimi yai murmushi yace "eh to hakane, amma ai Nana tayi ƙarama da yawa, da wannan karatuttukan naki" "Taɓɗijan, kai kake ganin tayi ƙanƙanta, ba tayi ƙanƙanta ba, ba dan karatun boko ba, ai da yanzu idan ba'ayi aurenta ba, ana nan ana shirin hakan, kuma karkayi mamaki suna tattaunawa a junansu, yaran zamani ka kallesu kawai, gara in horata da nawa karatun, da wanda za'a karanta mata a waje ta ɗauka" Hakimi ya jinjina kai yace "hakane kam, naga zasu yi hutun makaranta, shiyasa nace ki tafi da Ita bikin nan, wallahi ina jin banƙin cikin rashin raɓata da jikokina basa yi" "Ka dena damun kanka fa, ita uwar yaran nata halin kenan, yaranta baza suzo ƙauye ba, dan haka ka haƙura ka bar mata yaranta, shi shine ɗanmu kuma yans zuwa inda muke, meye na damuwa dan yaransa basa zuwa?, Baga Ummi nan Allah ya baka ba" Ya ɗanyi shiru Yace  "na tabatta da baban Ummi na raye ba yadda ze hana yaransa zuwa inda muke, kin sanni da ƙawa zucin yara, Allah be bani su da yawa ba, duk ya karɓe abunsa, ina ƙaunar yaran nan, irin son da nakewa mahaifinsu, haka nake sansu" Inna tace "ni dai nace kayi haƙuri, ka maida komai ba komai ba, Ummin nan kawai in Allah ya bamu yawan rai, seka ga ta haysyyafa, ta cika mana gida da jikoki" Hakimi ya jinjina kai Yace "wai, idan ba wani ikon Allah ba, ina ni ina ganin 'ya'yan Ummi, 'ya'yan jika fa?" "Eh mana 'ya'yan jikan, ai abun na Allah ne, kai dai Allah ya baka tsawon kwana me amfani Saraki" Yai murnushi, yana jin daɗin yadda matar tasa take masa addu'a, ko kuma yi masa kirari. Inna na nan zaune tare da megari, seda ya kammala shan furarsa, ya kwanta sannan ta fito daga turakarsa, tana zuwa ɗaki ta tarar da mutuniyar tata, tana cin Abincin rana. "Yawwa ta Nana, gaki nan fes dake se ƙamshi kike, haka ake son mace a ganki kullum cikin gyara, ga kayanki can na islamiyya an goge miki, idan kin gama seki shirya ki tafi Makaranta" Nana tace 'to Hajiya Inna" Shirye shirye suna ta nisa, na bikin Usman, Sadik ma yana ta nasa shirin, dan yana son ya gwangwaje da bikin nan, zasu yi shagali sosai shida friend's ɗinsa. Yauma yaje school sedai har ya shiga aji be samu ganin abar ƙaunarsa ba, ana fitowa break ya tafi ajinsu Farhan, sedai ya tarar bata nan. Cikin takunsa na isa ya shiga cikin ajin, ya kallesu Yace "ina Farhan?" Lilly tace  "Ana fita break ta fita, bamu san inda ta tafi ba" Be kuma cewa komai ba ya fita, yana tunanin ina ta shiga haka? Tun jiya be sake ganinta ba. Ita kuwa bayan wani aji taje tai zamanta, dan karma su haɗu Sir Nazir yai mata faɗa, koya kira babanta, sedai sam itama zuciyarta a takure take, tana son ganin Sadik ɗin nata. Sadik yana zaune yayi shiru, Meenal ce ta zauna a kusa da shi, Tare da ɗan dukan cinyarsa tace  "Babban yaro, what's wrong ne? Ka wani yi shiru" Cikin damuwa ya ɗan lumshe idonsa ya buɗesu, sannan Yace  "Farhan na nema na rasa, naje har ajinsu bata nan, kuma ita bata zo nan ba" "Shine ka zauna kai wannan shirun haka? Lallai yarinyar nan ta kama zuciyarka fiye da yadda kake tunani" Yai murmushi Yace  "ke dai bari kawai, yarinyar ta musamman ce, komai nata abun burgewa ne, I can't do without her" Meenal tace  "Ranar daka bar makarantar fa?" "Zan bita har gida mana" "Hmm Sadik manya, banda abun so dai, banga me ka gani a jikin wannan Farhan ɗin ba, ita gata bata wani cika mace ba" Sadik yai murnushi sannan Yace  "Ni idona sun gane min abunda naku idon baya iya gani, ku kuke ganinta ƙarama, amma ni nasan me nake gani" Yai maganar yana lumshe idanunsa. Meenal ta kalleshi tace   "Allah me iko, kaga ni dai dan Allah yi mana ordern Abinci, yunwa nake ji wallahi" Sadik ya zaro wayarsa yana faɗin "bari inyi, kuma fa nima yunwar nan nakeji, amma banga zuciyata ba, ban sani ba itama taci ko bata ciba, ba zan iya ci ba" "Can ta nannaɗe muku kai da ita, ni dai dan Allah yi mana" Seda aka kunna jiniya, kowa ya koma aji, Sannan Farhan ta fito daga inda ta ɓuya zata koma aji, zuciyarta nata raya mata taje ajinsu Sadik ta ganshi, amma ta danne zuciyarta ta tafi ajinsu. A bayan wani aji ta hango wani malami, yana kissing ɗin Tasleem ta ajinsu Sadik, nan da nan mamaki ya cikata jikinta ya ɗau rawa, abun ya bata mamaki sosai, Malami da kansa yake haka shi da ɗalibarsa, ta shiga ajinsu cike da tunanin abunda ta gani. Ta zauna a gurin zamanta tana tunani, Lilly tace  'Farhan, ina kika shiga ne? Prince Sadik yazo nemanki fa' Maimakon ta bata amsa se dai murmushi kawai da tayi Mata. Koda aka tashi, cikin gaggawa Farhan ta ɗauki jakarta, dan ta gudu gida kafin Su haɗu da Sadik, sedai tana fita harabar makarantar tai karo dashi. Mazewa tayi niyyar yi ta fece, aikuwa ya riƙo hannunta cikin hanzari ya kalleta Yace "meye hakane Farhan? Kamar kina guduna ne 'yan kwanakin nan lafiya kuwa?" Farhan ta ɗan haɗe rai cikin shagwaɓa tace  "Nika cikani meye haka?" Sakin hannuta yayi, tare da shan gabanta  Yace  "tun jiya fa nake nemanki ban ganki ba, ko laifi nayi miki ne?" "Ni ba abunda kayi min, kawai ka dena bina". "Wace irin magana ce wannan haka?" "Ka dena bina ko zuwa inda nake kawai, Sir Nazir yace ya kuma ganinmu tare ze kira babana" Nan da nan annurin Fuskar Sadik ya ɗauke, ya canza fuska jikinsa har rawa yake ya kalli Farhan Yace  "dama shine dalilin da yasa kike guduna? Waye Nazir? Me akai akayi shi? Farhan wai so ƙaryane? Zaki fara wahal dani dan ina sonki? Ina ruwansa damu, meye nasa a cikin soyayyar mu, idan sonki yake ya fito Ya faɗa mana in bar masa ke, kuje kuyi dashi, nafi ƙarfin Wulaƙanci Farhan, karki sa zuciyata ta yanke hukuncin da zesa mu cikin dana sani nida ke". Nan da nan ido ya dawo kansu, babban abinda bata so kenan, wannan saurin zuciyar da zafin rai na Sadik, gashi ta kasa Magana, ga idon mutane da yai yawa a kansu. "Shikenan, tunda kin fifita decision ɗinsa aka abinda zukatanmu ke so, kije Nagode sosai da kika bari zuciyata tai zurfi a sonki, na sakankance kema kina sona, ashe nayi kuskure" Tasleem dake gefe tace  "shege Prince, akwai kalamai dole ya sace zuciyar yarinya ƙarama" Ganin yadda ransa ya ɓaci sosai, yasa Farhan sake dirircewa,  cikin muryarta me sanyi tace  "Ss..Sadik. wallahi" "Karki gayamin komai malama, kije na bar masa ke, ya kwaɗaki ya cinye" Fuuuu yai gaba, bebi ta kan jakarsa daya baro a aji ba, ya nufi inda motarsu take ya haye. Farhan kamar ta ɗora hannu a kai tayi ihu, dan a duniya bata son ɓatawa Sadik rai, dukda bata ta taɓa ɓata masa rai ba, amma taji ba daɗi yadda ransa ya ɓaci haka. "That's good, na gaya miki muddin na kuma ganinki da yaron nan, sena gayawa mahaifinki, wannan yaron dai ba aurenki zeba, ze ɓata miki lokacine kawai da rayuwa"....... Ayshercool 07063065680 [6/4, 4:21 PM] Jakadiyar Arewa: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ RUƊIN ƘURUCIYA PERFECT WRITERS ASSOCIATION (WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS) https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ P. W. A *Story and written by* AISHA ADAM (AYSHERCOOL) Writer of WATA KISSAR..(Sai mata) ABDUL JALAL AƘIDATA (paid book) WUTA A MASAƘA NOW RUƊIN ƘURUCIYA (paid book) _Labarin RUƊIN ƘURUCIYA, na iya zuwa da wani salo, wanda baku saba ganinsa a rubutuna ba, hakan ya biyo bayan akan abunda aka gina labarin, wani abun ze ɓoyu wani Abun baze ɓoyu ba sakamakon labari ne akan teenegers, yara masu tashen Balaga, but hakan ba ya na nufin na sauka daga kan tsarin yadda nake Rubutu bane, ƙofata a buɗe take dan karɓar ƙorafi, gayra ko shawara_ ⚠️⚠️⚠️ƘIRƘIRARREN LABARI NE, BAN YADDA A JUYAMIN SHI TA KOWACE SIGA BA SEDA IZININA ❌❌‼️                             Page 3&4 Waiga wa Farhan tayi ta kalli Sir Nazir, dake tsaye yana mata Magana, ji tayi tamkar ta shaƙeshi, saboda shine silar da yasa ta janye wa Sadik, kuma ga abunda tai yasa ran Sadik ɗin ya ɓaci. Abunda be taɓa zato ba, yaga Farhan ta galla masa harara, irin up anda down ɗin nan, tai gaba abunta, tsayawa yayi cak ya zuba mata ido harta ƙulewa ganinsa. Sadik kam a ɗakinsa na BQ ya tsaya, yana zuwa ya cire belt ɗinsa yai jifa dashi, ya cire neck tie ɗin wuyansa na makaranta ya jefar, ya cire rigar itama yai jifa da ita, ya faɗa kan gadonsa yai ruf da ciki, zuciyarsa na wani irin zugi, dan gaba ɗaya idonsa ya rufe, wata irin muguwar tsanar Nazir yaji tana ratsa shi, gefe guda yana ganin laifin Farhan da ta biyewa Nazir ɗin. Befi mintuna sha biyar da kwanciyar tasa ba, Yayansa Faruk ya shigo ɗakin Sadik, ya kalli Sadik yace  "Kai, Lafiya kuwa? Meke damunka kalli yadda kayi watsi da kayan makarantar taka fa, koba lafiya ne?" "Lafiya ta ƙalau" ya bawa Faruk amsa a taƙaice. 'ban yarda lafiyar ka ƙalau ba, kaga yadda idonka yayi ja kuwa?" "Budurwata ce ta ɓatamin rai" Zaro ido Faruk yayi Yace "What? Budurwa fa kace Sadik" Sadik ya tashi zaune Yace "eh, ko ban kai inyi ba?" "Ni na isa ince baka kai ba? Ka kai harka wuce ma Autan Mother, dama mates ɗinka ne suka zo, suna son ganin ka naga da alama ko gida basu je ba, dan jikinsu da uniform" Sadik Yace "kace musu su shigo" Faruk ya juya ze fita yana kallon Sadik, kamar yayi dariya wai ɗan wannan jaririn yaron ne yake da budurwa, harta kai ga ɓata rai, ko uwar me yake gaya mata oho?" Nasir ne da Aminu Manyan abokan nasa suka shigo bedroom ɗin. Nasir Yace "mazaaaaa, Yanzu ɓacin ran ne yasa ka tafi ka bar school bag ɗinka a school?" Sadik ya ɗanyi tsaki Yace "ƙyale ni kawai, ni bata jaka nake ba, raina ya ɓaci sosai, na rasa me nayi wa wannan banzan coper ya sani a Gaba, se kace ni kaɗaine ɗalibi, ko kuma nika ɗaine nake soyayya a makarantar nan?, duk ya samana ido, har yana wa Farhan barazanar ze kira mahaifinta, ita kuma ta fara guduna, to idan ya kira babanta ma me zece masa? Meye laifin zuciyata dan ta kamu da son Farhan? Ni nafi zargin anya ba sonta yake ba shima?" Aminu ne yai wata irin shewa Yace  "Oh my God, gayen nan kana burgeni Wallahi, dole ka tafi da zuciyar that innocent beb, ka iya kalamai, manyan yara a school suna crushing akan ka, amma ka dage kace kai se Farhan, that little baby, gashi ka koya mata son ka" "Bana tunanin Farhan na sona fa, bata taɓa gayamin tana sona ba fa" Nasir Yace "ka gane, yarinyar tana son ka, sedai kasan 'yar talakawa ce, and yaran talakawan nan some of them are not well civilised, shiyasa ita komai Kunya that's why ba zata iya gaya maka tana sonka ba" Sadik Yace "Karfa ka zageta, kuma ni kunyarta tana burgeni sosai, You don't know how much I love that girl" Nasir Yace  "Wai tsaya, dan Allah meyasa kake son yarinyar nan ne? Ba dai mummuna bace na sani, amma bata wani cika mace ba, she's still a Baby, you have to look for a hot and sexy Baby, but this one is too small for you, ƙwaya nawa wannan 'yar take?" Sadik ya kashingiɗa, ya shafa afro hair ɗinsa, sannan ya murmusa yace  "ina son Farhan sosai, ina son ta tashi da soyayyata ni kaɗai a ranta, ta fara so a kaina ta gama a kaina, kuma wallahi ni so nake na aure ta, dan banƙi a Auramin ita a Yanzu haka ba, saboda yadda nake ji akan ta" Wata shewa Aminu da Nasir sukayi, suka tafa, Aminu ya kalleshi Yace "Prince, kana wuta mutumina wato kai ko yanzu ka aure ta?" Sadik yace "Ku dena ɗauka da wasa nake fa, ina son yarinyar nan sosai" Aminu Yace "jika, kamar zaka iya wani abun arziki ne in kai Auren a yanzu, kana cika wa mutane baki" Sadik ya kalleshi yace "Nayi kama da nakashashshene? Nima cikakken namiji ne me lafiya, tsaf Zan iya zama da Mace nima a yanzu haka" Nasir Yace "we thought you don't have feelings na, even those movies you can't watch, I don't even thinks ka taɓa ko kissing Mace, shiyasa fa kallon soyayyar taka muke kawai shirirrita, babu wani armashi, You Are not romantic at all, your love is so bored, ɗan hugging ɗin nan ma kai bayi kake ba, a haka kake kiran kanka namiji, wai aka maka aure zaka zauna da mace? Malam if you can't do anything to a girl that will make her ehh... Ka gane ai You Are still a boy, ka jira lokacin da zaka zama cikakken namiji ba yanzu ba" Sadik ya jinjina kai, yana murmushin takaici dan yaji haushin abunda Nasir ɗin ya faɗa, Amma Yace "naji am still a boy, all I know is that, I love Farhan ina sonta sosai zan raini kayata harta zama yadda nake so in Aureta" Aminu yace 'Prince, that girl is not your type, taya zaka aureta? Kafin ka gama karatu ka tsaya da ƙafarka, ka aureta lokaci ya ƙure mata, dan haka shawarata a gareka koda ma Shi wancan wawan Nazir ɗin sonta yake, kawai ka bar masa empty, ka share hanyar kawai ka tsallak boda" Sadik Yace "ban gane me kake nufi ba?". Suka kwashe da Dariya, Nasir Yace "shiya sa muke ce maka You Are still a boy my friend, kawai ka more ƙuriciyarka da yarinyar nan, tana sonka sosai,  kawai ka huta, in yaso ka bar masa sauranka, kai da kana kallon B films ɗin nan da muke kallo da base ance maka ga yadda zaka yi ba, amma kai se Kaita abu kamar wani kidahumi" Aminu Yace "ka kawo System ɗinka, muna dasu kala kala, a tura maka kayi caji Yau, when you try it yarinyar nan ba zata sake jin maganar wani ba se Kai, saboda a yadda kake ɗin nan, You look so energetic, ba zata sake gangancin gudunka saboda wannan sakaran ba" Sadik ya girgiza kai yace  "Ina son Farhan ne ba dan in ɓata mata rayuwa ba, hasalima ni kamun kanta, sanyin halinta da kunyarta ne yasa na fara sonta, kuma ni sam bani da interest akan aikata abunda be dace ba, ni bazan kalli filma na batsa ba, bashi da wani amfani Sam, bayan ya toshewa me kallonsa ƙwaƙwalwa ga kuma zunubi, sannan nafi ƙarfin ku kirani yaro wallahi, cox i always have dreams, ina jin feelings kamar kowane lafiyayyen namiji, sedai ni ina son Farhan ne dan Allah ba dan wani abu ba" "Taɓɗijan, aikuwa in dai dagaske kana jin feelings, and you even have dreams ma, to tabbas a hankali watarana seka so kasancewa da mace,  kuma ga Farhan a kusa da kai, tunda ba aure za'a maka yanzu ba, Yawan kasancewarku tare komai na iya faruwa" Nasir yace "dalla bar ɗan rainin hankali, wai shi na Allah, se iskanci a baki amma baze gani ba koya aikata, my friend you better enjoy your life, that girl can do anything you ask her to do, gara ka gwada kanka kaji capacity ɗinka, ko ka ƙare a kame Kame, ƙishirwa ta addabeka, ga ruwa a kusa da Kai amma kaƙi maganin ƙishirwar" Aminu yace "rabu dashi, taso mu tafi Baba, duk ƙaryar banza ce ba namiji bane, har yanzu yarone". Suka kwashe da dariya, suka tafi suka bar Sadik cikin tunani. Nzarin maganganun sa ya dinga yi, gaba ɗaya yaji kansa yai dumm, yama rasa wane tunani zeyi? Su Nasir sun caza masa kai, suna ƙoƙarin cusa masa wani tunani, ga ɓacin ran Fargan kuma. Farhan kam harta je gida gaba ɗaya bata hayyacin ta, bata san ma daya taje gida ba, saboda tunanin ta ɓatawa Sadik rai, mussaman yadda ya dinga faɗan nan, ta san tabbas ransa ya ɓaci sosai, nan ta fara tuhumar kanta meyasa ma ta biye maganganun Sir Nazir, ta fara gujewa Sadik, ƙila ma barazana kawai yake Mata, ba wani Babanta daze kira ya gaya masa, dan gara ma a gayawa Babanta, ta san baze wuce ayi mata faɗa ba shikenan, amma idan Sadik ya dena kulata bata san ya zata yi ba. Jiki a sanyaye take yin komai, har seda mahaifiyarta ta lura da hakan, tace "Farhan meke damunki ne? Ko a makarantar ne akai miki wani abu?" Farhan ta girgiza kanta tace "A'a Umma, ba abunda akayimin" "To idan ma wani abun akayi miki, kiyi haƙuri, ki iya talaucin ki nasan duk makarantar babu ɗan talaka kamar ke, kema Allah ne yayi zakiyi wannan makarantar, saboda scholarship ɗin nan, dan haka sedai kiyi ta haƙuri" Har Umman Farhan tayi maganarta ta gama, sam Hankalin Farhan baya kanta, tunanin ta kawai yadda zata shawo kan Sadik, dan ta lura yana da kafiya wasu lokutan da zafin zuciya. Salla kawai tayi ta nemi Guri ta kwanta, Ummanta ta shiga ɗakinsu ta ganta a kwance "Islamiyyar ce ba zaki ba, ko kuma wani sabon salon wulaƙancin ne haka?" "A'a Umma, kaina ne yake ciwo" Daga nan Umma bata sake cewa komai ba, ta fita daga ɗakin, bin bayan Ummanta tayi da kallo taji ina ma Ummanta tana sauraren ta, kasancewar ta 'yarta ta fari sam bata wani shiga sabgarta, ko hirar kirki ba ta yi da ita, lokuta da yawa abu na damunta, amma ba zata taɓa iya tunakarar mahaifiyarta da maganar ba, duk da ƙanƙantar shekaru na Farhan, tana son hira da mahaifiyarta, amma sam mahaifiyarta bata bata lokaci,ba ta raɓar duk wani abu da ya shafi Farhan saboda kunyar ɗan fari. Ajiye wannan tunanin tayi, ta shiga neman mafita akan yadda zata shawo kan Sadik, shiru tayi ta shiga tuna haɗuwarta da Sadik, da yadda suka fara soyayya. Bayan an sanar da iyayen Farhan ta samu scholarship, a makarantar su Sadik saboda ƙwazonta, sunyi murna sosai dan makaranta ce ta 'ya'yan manya, kuna akwai karatu sosai a makarantar. Sedai Ranar farko da Farhan ta fara zuwa, ta tsorata da ganin yaran dake makarantar, saboda duk yadda ake zuzuta makarantar ta yaran masu kuɗi ce, bata zaci zata ganta haka ba, Yarane na alfarma a makarantar, 'ya'yan hutu rainon AC, gaba ɗaya tsarin rayuwarsu ya sha bamban da wanda ta taso taga anayi, kalar fatarsu kawai idan ka kalla ka ga yaran hutu, dan kaso mafi yawa na yaran farare ne ƙal. Suna da cikakken 'yancin aikata abinda suke so a makarantar, da ƙalubalantar duka' wani malami da yayi musu ba daidai ba, saɓanin makarantar data baro, Wadda ta kasance ta gwamnati, baka da wani kataɓus se Abinda malami yaga dama. A makarantar data baro ta saba da idan an fita tara, suje su kashe kuɗin makarantar su da idan yayi wuta naira hamsin, amma a wannan Makarantar idan aka fita tara masu zuwa da abinci zakaga Abinci ne na alfarma, kaji ko nama yanka zuƙu zuƙu akan abinci, ko kuma tarkacen kayan cake da chocolate da sauran kayan kwaɗayi, se kaga ɗalibi da sama da naira dubu guda. Ta saba a makarantar data baro, in an fita break, wasansu baya wuce 'yanta, 'yar gala gala da sauran wasannin yara, amma a wannan makarantar daga basket ball, football, volleyball irin wannan wasannin suke, sannan suna bawa birthday mahimmanci da sauran bidi'oi wanda bata saba dasu ba, suna da manyan gangaunan kiɗa da manyan speaku na disco, har clubs clubs ne na koyarda rawa ta zamani, da waƙe waƙe a makarantar. Ga uwa uba dressing, ita makarantar da ta baro dukda a Jss1 ta baro makarantar, amma hijjabinta ya wuce gwiwarta, manyan hijjabai suke sawa, amma a wannan makarantar, skirt ne gajere daidai jikin ka, ka rufe ƙwaurinka da safa idan kana buƙata, ga ɗan ƙaramin hijjabi, sam bata iya Ratsa unguwarsu da wannan ɗan guntun Hijjabin, seta saka babba a kai. Wannan banbance bambancen ne yasa Farhan ta sake takure kanta a makarantar, komai nasu ganinsa take daban takasa sabawa da abubuwan makarantar, saboda sun sha banban dana wadda ta baro, ta 'ya'yan talakawa. Sam bata da wasu ƙawaye a nan, dama dai bame kwashe kwashen ƙawayen bace. Gaba ɗaya yanayin makarantar da Al'adun makarantar se sukayi mata wani iri daban, babban abinda yake ƙara ɗaure mata kai be wuce yadda ɗaliban da wasu daga malaman ke mu'amalantar juna tamkar jinsinsu ɗaya ba, ta hanyar yin wasanni tare, kamar na ƙwallon ƙafa da sauransu, cin Abinci tare, gaisawa da juna ta hanyar musabiha tsakanin maza da mata, rungumar juna da dai sauransu, wanda a normal al'adar malam bahaushe hakan ya saɓawa tarbiyya da addininmi, dan haka gaba ɗaya Farhan take baya baya da lamuran makarantar nan dama ɗaliban, ta kama karatunta tunda shi tazo yi, suma ɗaliban ba kowa ke shiga harkarta ba saboda suna mata kallona wadda bata waye ba sam. Wataranar juma'a, lokacin kusan satinta uku a makarantar, Sadik ya dawo aka ce yaje Umra shida 'yan gidansu, anyi rabon kayan dabino bagaruwa, zam zam carbi agoguna, haka aka dinga rarrabawa, abunda Farhan ta lura shine, Ana matuƙar son Sadik, baga malamai ba baga ɗalibai ba, saboda barkwancinsa da yawan kyautarsa, dukda duk yaran masu kuɗine abokan nasa, amma yana musu ɓarnar kuɗi sosai. Gashi yana da ƙoƙari sosai, sedai ta lura bayan sonsa da akeyi kamar abun harda tsoronsa akeji, seniors ɗinsa na shakkarsa, haka juniors ɗinsa, ko gaban assembly ne ake surutu kafin a fara assembly malamai suzo, daya hau kan stage kowa yake yin shiru, Sadik akwai tsafta da gayu sosai da sosai, gashi baya son raini ko kaɗan, ko tahowa yayi Junior ya taho se an bashi hanya ba'a haɗa hanya dashi, koda kuwa 'yan SS1 ne, sedai Wasu lokutan yakan shiga cikinsu yayi Wasanni kamar ball da sauransu, sabida bayan kasancewar sa gwarzo a aji, ƙwararren ɗan wasa ne, dan ba dan mahaifinsa yaƙi bashi goyon baya ba, da ƙasar waje ze tafi makarantun koyan tamaula. Wata ranar juma'a, duk 'yan makarantar na gurin wasanni, wasu na wasa, wasu na gurin kaɗe kaɗe, Sadik ya shiga cikin makarantar ɗakko ATM card ɗinsa, ze fita cin Abinci, yazo wucewa ta ƙofar ajinsu Farhan, ya hango ta a zaune ita kaɗai a ajin, tunda ya dawo daga Umra ya ganta a makarantar, baƙuwar fusaka ce dan be santa ba kan ya tafi, sedai yana lura da yadda sam ba ruwanta da kowa, abinda ya dameta shi kawai take yi. Tura ƙofar ajin yayi, wanda hakan yasa ta ɗago da sauri, ya ɗan ƙura mata ido sannan Yace "ke bazaki gurin wasan bane?" Ta jinjina masa kai alamar eh. "To saboda me?" "Bakomai" ta faɗa a sanyaye. "Amma You Are new in this school ko?" Ta ɗaga kai alamar eh. Sadik yace "Yayi kyau, amma Yakamata ke ma ki fita gurin wasanni, ki dinga motsa jiki" Farhan ba tace masa komai ba se binsa da kallo da tayi, Sadik dogo ne chocolate color, kana ganinsa ka san ɗan hutu ne, yana tara suma a kansa, Afro style ko yaushe sumar tana ƙyallin mai, da wuya ka ga kansa a bushe babu mai, gashi da dogon hanci sosai, masha Allah ɗan kyakykyawan matashi ne Prince Sadik. Tun daga ranar da yai mata magana, duk in da suka haɗu se yai mata murmushi yace mata "Sannu" Wasu lokutan ta kan mayar masa da murmushin tace "Yawwa" Haka nan take burge Sadik, saboda shiru shirunta, kusan kullum se sun haɗu ko a hanya ko kuma a gurin assembly. Watarana ana birthday party na headgirl ɗin makarantar, gaba ɗaya an tare a gurin da ake raye rayen, Sadik ya duba duk gurin partyn amma be ga Farhan ba, ko a gurin assembly be ganta ba, haka nan yaji yana son ya ganta, dan haka ya tafi ajinsu. Ita kaɗaice a ajin, ta kifa kanta a kan benci, Sadik ya ƙwanƙwasa ƙofar clss ɗin, hakan ya sa tai saurin ɗagowa, kamar kullum yau ma musayar murmushi suka yi. Ya ƙarasa ya zauna a kusa da ita, zaman da Sadik yai a kusa da ita se taji tamkar wani babban zunubi ne, take fargaba ta shige ta da tunanin idan aka zo aka gansu a haka fa? Prince yace "meyasa baki je gurin birthday ɗin ba, Why do you always like to isolate yourself from the people?" A hankali tace "bakomai" "Ke kin fi son zama ke ka ɗai?" Ta jinjina masa kai. "Wai ni meye sunanki ne ma?" "Farhan" ta bashi amsa. "Wow, what a very nice Name, Farhan gaskiya baban ku ya iya zaɓen suna, kin dace da sunan naki, Farhan" Ɗan sunkuyar da kai Farhan tayi, taji daɗin yadda ya yabi sunanta, amma wannan zaman da yai a kusa da ita duk ya takurata. "Zo muje gurin party tare, kowa yana can yana walwala ke kuma kullum a takure, wai ke baki da ƙawaye ne?" Ta ɗaga masa kai alamar eh. "To shikenan, daga yau ni ne ƙawarki, kuma nine abokinki, ta so muje" "Ba se naje ba, ina hadda ne an jima idan naje islamiyya zan bada hadda" Sadik yace "wow, masha Allah yau kinyi doguwar magana, kina da murya me daɗi sosai, amma kullum nai miki Magana se ki amsamin a taƙaice, anyway ayi karatu lafiya se anjima" Yai maganar tare da miƙewa ya fice,haka kurum ta shiga yin murmushi, mussaman da ta tuna yadda yace muryarta na da daɗi. Har aka tashi  daga makaranra, da tayi mosti, se ta tuna Sadik, da ya faɗo mata rai kuma se ta kasa riƙe murmushin ta. Washegari an cika a gaban assembly, Sadik ne ke leading assembly ɗin, duk da kasancewar sa a Ss2, amma ƙwazonsa yasa ake sakar masa yin abubuwa da dama, ya kira wata kirista ta fito ta gabatar da addu'a a gaban assembly, ta koma yana ƙoƙarin kiran wanda ze Addu'a a cikin ɗalibai musulmai, kawai idonsa ya sauka akan Farhan yace "Farhan from Jss2, should come over and recite qur'an for us" Gaban Farhan ya faɗi jikinta ya shiga kyarma, tana zuwa competitions daban daban, amma ita gaba ɗaya wannan makarantar da mutan cikinta tsoro suke bata da kwarjini, seda ya maimaita abun da ya faɗa Sannan ta fito jiki a sanyaye. Aikuwa kowa ya bita da ido, cikin takunta da ta saba yi, kamar wadda ƙwai ya fashewa a ciki ta hau kan stape, takun da ke matuƙar burge Prince idan tana yinsa, ta kalli uban ɗaliban da suka zubo mata ido, ta waiga ta kalli inda Sadik shima ya kafe ta da nasa idanun. Ta daidaita nutsuwarta, ta sunkuyar da kanta ƙasa, ta fara rero karatun Alqur'ani cikin muryarta me daɗin sauraro, take gurin yai tsit kamar babu wata halitta a gurin, se muryar Farhan da ke tashi a gurin. Ayoyi goma ta karanta na farkon suratul Yusuf, sannan ta rufe da addu'a, tana idarwa akai mata kabbara, seda Sadik ya dinga wasata kafin ya miƙa ragamar assembly ga malamin da ke duty a ranar. Ta sha yabo ma daga gurin malamai, saboda yadda tai karatun cikin nutsuwa, bayan an watse daga Address, maimakon ya tafi ajinsu, se ya tafi ajinsu Farhan. Ya sameta a gurin zamanta yace "Weldon dear, gaskiya kin iya karatun Alqur'ani sosai Masha Allah, you have a nice voice" Se taji kalmar dear ɗin nan ta ɗan mata girma (😂😂 kun sanmu hausawa wasu lokutan) "Ya naji kinyi shiru, ba zaki ce komai bane?" Sunkuyar da kai ta kuma yi, kamar wata amarya, Sadik yace "shikenan, tunda ba zaki Magana ba, I love Your voice, in am fito break zan zo" Ai take gabanta ya faɗi, he loves her voice kuma? Allah yasa wani be ji me yace ba, love kuma? Wannan ya fiye rigimar tsiya. Sadik yana zuwa aji, Nasir yace "wai ina ka tafi ne?" "Na je Jss2 ne" Amin yace "wai uwar me kke a ajin nan da kake yawan zuwa,, kamar me zuwa neman wani abu?" yace "Wallahi gamo  nai a ajin" "Wane irin gamo kuma?" Prince yai wani ƙasaitaccen murmushi yace "a very beautiful Young beb, ban san meke damuna ba, se dai ina son kasancewa kusa da ita ko yaushe, in dinga kallon kyakykyawar fuskarta ɗauke da ƙasaitaccen murmushin ta" Nasir yai tsaki yace "ji banza, meye haka se kace wani a hausa film, malam ba fa acting ka ke ba, real life ne, kai ka fiye shirme wasu lokutan" "Ba shirme nake ba Nas, i think am in love with that beautiful creature" Amin ya kwashe da dariya yace "kaga wata asara, kuma da 'yar Jss2? Yaran da duk ƙwailaye ne,  maimakon ka samo wata zazzafa duk matan school ɗin nan ka rasa ina zaka samo budurwa se Jss2 dan ci baya, duk matan Senior classes ɗin nan, wanda suka amsa sunan su mata, dan tsuya se  a Jss2?" Prince yace "ba zaku gane ba ne" Nas yace "wait, wacece a cikin Jss2 ɗin?" "Farhan, Yarinyar da tai karatun Alqur'ani a assembly ground" A tare Amin da Nas suka ja tsaki. Amin yace "dan Allah meye abun so a wannan Yarinyar? Wannan kwata kwata yaushe aka yayeta daga shan Nono aka kawo ta makarantar?" Nasir yace "taɓɗijan, a part from sexy eyes banga meye abun burgewa a wannan Yarinyar ba, gata wata kidahuma, kullum tana aji da littafi kamar al huda huda, kullum kanta a ƙasa kamar munafuka, tana kallon Mutane ta ƙasan ido, da an tashi ta zumbula wani uban hijjabi kamar wata me da'awa ta ɗau jaka dunkum dunkum kamar 'yar 419, she don't even look romantic at all" A fusace Sadik yace "zanci ubanka Nasir, bana son wulaƙanci a haka nake sonta, ka sake faɗan wani rashin hankalin a kanta, zan fasa maka baki" "Allah ya baka haƙuri, Allah ya bar wannan ƙauna, ta shiga sahun tarihi fiye da Romeo and Juliet, ashe zaka iya yin budurwa Prince?" Tsaki Prince yai ya tashi ya bar ajin gaba ɗaya, saboda yadda suka sashi gaba da iya shege. Sadik ya sa Farhan a gaba, duk inda ya san ze ganta se yaje, shi babban abunda yake damunsa da Farhan rashin magana, gashi taƙi sakin jiki da shi sosai, ko abu ya bata ba zata karɓa ba. Wataran ya ritsata an tashi, ta  ɗau jakarta zata tafi gida, ta jiyo muryarsa yace "sweet heart" Da sauri ta waigo, dan tantance  da wa yake, kasancewar ba ita kaɗaice a gurin ba. "Da ke nake Farhan, yau ban ganki ba, Ina kika shiga ne?" Waige waige ta shiga yi taga ko su ake kallo, amma taga ba wanda ya damu da su, wannan kalma haka me nauyi da ba'a jinta se a bakin mayan samari da 'yan mata kuma masoya, amma ya kirata da ita a cikin jama'a. Ya ƙaraso inda take tsaye yace "Akwai abunda ki ke nema ne?" Ta girgiza masa kai, yai ajiyar zuciya yace "yau Friday shikenan ba zan sake ganin ki ba se Allah ya kaimu Monday?" Sunkuyar da kai tayi, tana wasa da yatsunta. "Farhan kalleni" Ta ɗago ta kalleshi ta mayar da kanta da sauri ta sunkuyar, saboda yadda yai mata kwarjini. "Farhan, ban taɓa budurwa ba, amma am feeling something different on you, ina sonki Farhan!" Se da ta de na ji na wasu ɗan lokuta, wannan gingimemiyar kalmar, wai yana sonta, taji kamar ƙasa ta tsage ta shige saboda yadda kalmar tai mata dirar mikiya. "Ya naga kamar kina tsoron wani abu ne? Ko dai ba kya sona ne"? Tai shiru ba tace Komai ba "shikenan, muje se mu sauke ki a gida" Da sauri ta girgiza kai tace "Za'amin faɗa a gida" "Ok, to mu fita gate ɗin tare" Ba zata iya yi masa musu ba, amma Jerowar da sukayi da Sadik ji take tamkar ta zura da gudu, wannan ai rashin kunya ne, yadda suka jero tare, amma shi ko a jikinsa. Har ta koma gida juya maganar Prince take, wai yana sonta, shi ko nauyin kalmar be ji ba, ta shiga fargabar kar a gida a gane, wani yace yana son ta dan ta san za ta sha faɗa, dan haka sai tai ta ƙoƙari ta manta da Sadik, amma bata cikakken mintuna ashirin kalmar Sadik na yana sonta be faɗo mata a rai ba. Tun da Sadik yace yana son Farhan, suke 'yar ɓuya, ba ta yadda su haɗu saboda nauyinsa da take ji, idan kuwa suka haɗu har ya gama surutunsa ba zata tanka ba. A hankali tun tana jin nauyinsa, saboda yawan haɗuwa da suke da zuwa gurinta da yake, yasa ta fara rage jin nauyinsa, take ɗan sakin jiki da shi. Gefe guda tana fuskantar tsangwama daga wasu ɗaliban, saboda yadda Prince ke ji da ita, ga kyawawan yara da suka fita komai suna crushing a kansa, amma ya je ya liƙewa Farhan. A hankali ɗalibai suka dinga gane alaƙar da ke tsakanin Prince da Farhan, kasancewar he is very popular a makarantar. Shaƙuwa ta fara shiga tsakani ta da Prince, ya zamana idan ma be zo inda take ba, da kanta za ta je ajinsu Sadik dan ta ganshi, Dawowa tai daga dogon tunanin da ta tafi, tana tunanin meye mafita akan yadda zata shawo kansa ya haƙura. Dan gaskiya she's ready to do anything dan taga Sadik ya dena fushi da ita, yanzu idan ya dena kula ta fa? Ko ya canza budurwa ya za tayi?! Ji tai gabanta ya faɗi, da tai tunanin Prince ya canza budurwa. YANZU AKA FARA, SALON NA DABANNE. DOMIN GYARA, SHARHI KO SHAWARA AYSHERCOOL 07063065680. [6/4, 4:21 PM] Jakadiyar Arewa: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ RUƊIN ƘURUCIYA PERFECT WRITERS ASSOCIATION (WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS) https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ P. W. A *Story and written by* AISHA ADAM (AYSHERCOOL) Writer of WATA KISSAR..(Sai mata) ABDUL JALAL AƘIDATA (paid book) WUTA A MASAƘA NOW RUƊIN ƘURUCIYA (paid book) _Labarin RUƊIN ƘURUCIYA, na iya zuwa da wani salo, wanda baku saba ganinsa a rubutuna ba, hakan ya biyo bayan akan abunda aka gina labarin, wani abun ze ɓoyu wani Abun baze ɓoyu ba sakamakon labari ne akan teenegers, yara masu tashen Balaga, but hakan ba ya na nufin na sauka daga kan tsarin yadda nake Rubutu bane, ƙofata a buɗe take dan karɓar ƙorafi, gayra ko shawara_ ⚠️⚠️⚠️ƘIRƘIRARREN LABARI NE, BAN YADDA A JUYAMIN SHI TA KOWACE SIGA BA SEDA IZININA ❌❌‼️                                5_6 Da sauri Farhan ta miƙe, ta kwaso Uniform ɗinta, taje ta wanke ta shanya. Ta na cigaba da tunanin, ya zata shawo kan Prince ɗin ta. Prince kam shima abun duniya ya ishe shi, ya rasa abunda yake masa daɗi, ya dinga jujjuya maganganun su Nasir, ɓangare guda yana jin yadda zuciyarsa ke ƙara jin son Farhan. Maganganun su Nas na kiransa Yaro, tabbas sun ɓata masa rai amma hanyar da suke ɗora shi a kai, ba me ɓullewa bace. Miƙewa yai zaune ya kalli agogo, har huɗu da rabi, tunda ya dawo be fita daga ɗakin ba. A hankali ya tashi ya shiga toilet yai wanka, ya fito yai sallar la'sar, sannan ya shiga cikin gida. Abun dai da baya so, mutane na ta shiga suna fita a gidan, saboda shriye shiryen bikin Yayansa. Yatsuna fusaka yai ya shiga falon, ya nufi ɗakin Mother. Yana shiga ta ɗago ta kalle shi tace "Autan, i have been looking for you since, where have you been ne?" "Mother ta ya zan shigo, duk an bi an cika mana gida, kamar an fara bikin, mutum da gidan su a hanashi sakewa" Tai murmushi tace "Ai Arziki ne abun farinciki ya samu brother ɗin ka, an zo taya mu murna, sedai kayi haƙuri, da anyi bikin an gama shikenan" Prince yace "Da anyi nasa se nawa kuma" Mother ta kalli Sadik ta ɗan buɗe baki tace "sannu, kai fa baka da kunya wasu lokutan, a beg go carry your food and eat" "Mother dagaske fa nake" "Zan make ka, tashi ka bani guri, ka ci Abinci ka ɗau litattafnka ka karanta, bana son shirme" Bin mahaifiyarsa yai da kallo, yana mamakin yadda suka ɗaukaki boko, ashe akwai daru a gaba, dan gaskiya baze iya zaman jiran wai se ya gama wata jami'a ba. Ya ɗau Abincinsa ya zauna yana ci a bedroom ɗin, amma tunanin sa na kan wani abu daban. "Auta, ya naga baka cin Abincin? Meke damunka ne?" "Bakomai" ya faɗa a taƙice, da ya kammala cin Abincin a nan ya bar kwanukan, da gurin yai gaba abunsa. BQ ya koma ya sake kwanciya, abun duniya duk ya dame shi, a gaskiya shi baze yadda da wanan aƙidar bokon ba, haka kurum wannan ai cutar mutum ne, ace wani seka yi master's tukuna. "Nana! Nana!" "Na'am Innar mu" "Au da kina jina nake ta faman kiranki  kika min banza?" "A'a, na amsa fa" "Ai kin san ni ɗin kurma ce da ban ji ba ko?" Ta girgiza kai alamr a'a. Inna ta ɗan ƙureta da ido sannan tace "Ni kin ma yi wanka tukuna yau?" Tura baki Nana tayi, jin Inna zata fara halin tace "nayi mana" "Amma kayan jikin ki masu datti ne ko?" "A'a jiya fa na sasu daf da magariba, kuma na cire na sa na bacci" 'wai ke wace irin yarinya ce me azababben taurin ka ne? Nace miki idan ki kai wanka ki ka sa kaya masu datti, da kinyi wanka da baki ba duk ɗaya jikin ki baze fasa wari ba, haka idan ki baki wanka ba ki ka sa kaya masu kyau shima ba zaki dena wari ba, amma kin kasa ganewa kinfi so kullum in ta yaƙi da ke ina maimaita miki abu ɗaya" "Haba Innarmu, wallahi bana wari, kayan fa ba datti su kai ba, kuma ko gumi ban ba" "Zaki wuce kije ki canza kayan ne, ko sena sa miki abun duka? Kije ki cire wannan kayan, ki ɗebi ruwa kije ki sake wanke hammatarki, ki kama ruwa ki wanke fusakarki, ki shafa mai ki canza wannan kayan bera ƙazama" Nana kamar ta ɗora hannu a kai ta ihu, Inna a duniya idan ba ta takura mata ba bata samun nutsuwa. Taje ta ɗebi ruwa tana kumbure kumbure, taje ta wanke jikinta, ta fito zata zira kaya, amma Inna ta kuma cewa "ba zaki bar ruwan jikin ki ya tsane ba, ki shafa ruwan alumun ba a haka zaki maka kaya a jikinki? Shiyasa nan da nan kike gumi, ki fara ƙari" Haka Nana ta shirya a gaban Inna, tace shafa kaza a nan, goga wancan a nan, su nayi Nana na zumɓura baki. Seda ta canza kaya ta shirya tsaf tai kyau, Inna tace  "yawwa ko ke fa, yanzu kije gidan Rabin kuka, ki ce ina gaisheta, ta baki saƙon nan ki kawomin, kuma ki sauri ina nan ina jiranki" Nana tace to, ta saka takaliminta ta fita, har taje ƙofar soro na farko, Inna ta ƙwala mata kira Nana ta dawo. Inna tace "na kira ki ne in sake jadad da miki, bake  ba Zuwa inda ban aike ki ba, kije ki karɓomin saƙo kawai ki dawo, ban da faɗi ba'a tambayeki ba, ko tsoma baki a abunda ba ruwanki, kinji na gaya miki ko?" "Eh naji" "Yawwa maza jeki" Nana ta juya, Inna tace "banda kula mazan da baki sani ba, wanda ki ka sanin ma tsakanin ki da su gaisuwa, kinji ba?" "To" Nana ta faɗa cikin ƙosawa. "To Allah ya kiyaye, ban da bi ta Majalisar maza, a tafi ana saka hannu a hijjabi, in ba haka ba, 'yan abubuwan nan da suka fara fitowa, wani ze taɓa ya gudu, kuma idan kika bari wani ya taɓa ba Aurarki yai ba, a haka zasu zauna, harki mutu ba zasu kuma fitowa ba, tun da ba kya alkinta su" Nana a ranta tace 'Allah ya kiyaye suƙi fitowa har in girma, shikenan ba zan zama 'yan mata ba taɓ" Inna na shirin kuma ɓaro wani abun, Nana tai waje abunta, dan ta gaji da wannan takarar ta Inna da bata ƙarewa se kace karatu. Ko da taje gidan da aka aiketa, ta shiga da sallama. Cikin wata siriryar murya wata ta amsa tace "waye?" Nana tace "Nice innarmu ce ta aiko ni" "To shigo mana" Nana ta shiga ɗakin da sallama, suka gaisa da wannan budurwar, ta girmewa Nana sosai, Nana tace "ina maman take?" "Ta shiga dubiya, nan maƙota yanzu zata shigo ki ɗan jira" Nan Nana ta zauna tana jiran dawowar wadda aka aiko ta gurinta. budurwar ta tashi ta ɗebi ruwa a bokiti ta tafi wanka. Tana shiga banɗaki Nana ta miƙe, taje gaban gadon dake ɗakin, ta ɗau wata brezia dake kan gadon, taje gaban mudubi, ta saƙala ta a haka ta kalli kanta a mudubi tace "Ohh ni Allah, Allah ka nuna min lokacin da zan fara saka wannan abar nima, wai da anga iyayi, ai ko a makaranta da ba kowa zan kula ba,taku ɗai ɗai zan dinga yi, in dinga yiwa kowa gani gani, Allah dai yasa nima nawa suyi girma, Innar mu ta saimin" Seda ta gama sakarcinta ita kaɗai, sannan ta ajiye ta nemi guri ta zauna. Tana zama babu daɗewa sega matar gidan ta dawo, tana shigowa taga Nana ta faɗaɗa murmushin ta, Nana ta durƙusa ra gaisheta, sannan ta faɗa mata saƙon Inna. Rabi ta ɗakko wata leda, ta bawa Nana tace "gashi nan ki riƙe da kyau, ko hanzarta ki koma, kar ta ga kin daɗe" Nana tace to, ta karɓi leda tai waje, tana daf da barin layin gidan, ta ga wata Budurwa tana ta zance a ƙofar gida, saurayin yana kan babur, ita kuma tana tsaye, yana mata magana tana murmushi haɗe da Rufe fuskarta. Cak Nana ta tsaya tana kallonsu, so take ta fahimci meyake gayamata haka da yake sata wannan nishaɗin, take murmushi haka. Nana ji take kamar ta janyo girma, abubuwa da yawa suna burgeta, a hakan nan ma a 'yan ajinsu akwai masu saurayi, amma tasan idan Hajiya Inna ta san tana da saurayi, se ta dafata ta sha romonta saboda terere da faɗa, gaba ɗaya se jama'ar ciki da wajen gidan sun san meyafaru, amma ita har ga Allah tana son jin me ake ji a tsakanin saurayi da budurwa. Haka ta tafi tana tunanin ko yaushe itama za tai saurayin nan taji me ake ji haka oho?. "Hajiya Nana 'yan mata!" Jin abunda aka faɗa yasa ta waiga da sauri, wani Jamilu ne ɗan me unguwa, ita ko magana bata haɗa ta dashi, saboda yawan kashedin Inna ba kowa take kulawa ba a maza, saboda gani take da taje gida Inna zata gane. Tsayawa tai sororo tana kallon Jamilu, ya ƙarasa inda Nana take yace "ba gaisuwa?" Nana tace "ina wuni?" "Lafiya ƙalau 'yar gidan Hakimi, daga ina haka?" "Inna ce ta aikeni" "Masha Allah,ya Innar da kowa da kowa?" "Lafiya ƙalau" Jamilu yace "muje, dama nima gurin unguwar taku zani" Cikin Zare ido tace "A'a, haka kurum aje a gaywa Hakimi ko Inna an ganmu a tare,amin faɗa gaskiya a'a" Jamilu yai murmushi yace "ba wanda ze gaya musu, ai gaisawa kawai muke" "A'a to ai na gaisheka ba shikenan ba?" "Nana manya, wai yanzu ajinki nawa ne?" "Ina ruwanka da ajina?" "Bakomai, kawai tambayarki nai" Ta ɗan murguɗa baki tace "ni gaskiya ka ƙyaleni, kar Inna ta gane na kula maza a waje" Yai murmushi yace"Shikenan na ƙyaleki, yadda ki ke so haka za'ai, kyakywar jikar Hakimi da duk garin nan babu Tamkar ta a gata ko kyau" Nana ji tai Jamilu ya wani Mugun fasa Mata kai, tace "dan Allah dagaske kake?" "Sosai, dagaske nake, ke me kyau ce Nana" "Amma Inna take cemin bani da kyau" "Wasa take miki, amma kyawunki ya wuce a misalta ma" "Kai amma naji daɗi, bari in sauri in tafi kar tace na daɗe" Ta rungume ledar ta, ta zumbuɗa da gudu, dan kar Inna tace ta daɗe. An fara kiraye kirayen sallar magariba, sannan Nana ta faɗo a guje, Inna ta kalleta tace "lafiya, kike wannan gudun haka?" Numfashi ta dinga saukewa sannan tace "Gudu nai dan karki ce na daɗe" "Au gudu Nana, haka kika ratso cikin mazan gidan nan da wannan uban gudun haka? Ke komai naki cikin hauka da hauma hauma ba nustuwa ba komai kamar rainon maza" "Allah ya baki haƙuri, ga kayanki nan" Ta ajiyewa Inna saƙon ta tai ɗaki abunta. Bayan sallar magariba, Nana tana cin tsiren da Hakimi kan sa a kawo mussaman saboda ita, tace "Innar mu, dan Allah dagaske na fi matan ƙauyen nan kyau?" Yatsina baki Inna tai tace "Wane maƙaryacin ne ya gaya miki haka?" "Ba fa maƙaryaci bane, Jamilun gidan me unguwa ne" "Me ya haɗa ki da Jamilun gidan me unguwar har ya gaya miki haka?" Gaban Nana ya faɗi tace "wallahi ba abun da ya haɗa mu, kawai gaisheshi nayi" "Daga gaishe shi ya fara ce miki kinfi kowa kyau? Dama idan na aike ki gurinsa ki ke tafiya ko?" "Na shiga uku, wallahi ni bana zuwa gurinsa kawai a hanya muka haɗu, yace ban gaisheshi ba, wallahi bana zuwa gurinsa, kuma wallahi ban tsaya  ma a kusa da shi, yace ze rako ni gida naƙi" Nan da nan hawaye ya wanke fuskar Nana. Inna tace "Naji ya isa haka, kin san me nake so dake?" Nana ta girgiza kai, "ban hana ki hulɗa da mutane ba, ko ki gaida mutane ba, ba haka bane, ina jiye miki sharrin mutanen zamanin nan, mussaman ke da RUƊIN ƘURUCIYA, Yake ɗibar ki. Komai lokaci ne da shi Nana, idan lokaci yayi dole ko ina so ko bana so in barki ki kula samari, a lokacin da nake sa ran ki mallaki hankalin kan ki, kin sai daidai kin san ba daidai ba. A wannan shekarun naki, za'a iya amfani da ƙanƙantar shekarunki, da rashin wayo gami da RUƊIN ƘURUCIYA a cutar da ke, su maza ba tabbas ne dasu ba, wataƙila ma abunda yasa ya tsaida ke wannan 'yan abubuwan na ƙirjinki yake kallo" A razane Nana ta kalli ƙirjinta, tai maza tasa hannu ta rufe ƙirjin ta, tare da gwalalo idanuwan ta waje. Inna tace "eh mana, kuma idan baki wasa ba wataran taɓawa zeyi, kuma ki ka bari ya taɓa ba ke ba Aure, ba haihuwa kuma ba zasu cigaba da fitowa ba" "Wayyo Allah na shiga uku, amma dai yanzu zasu cigaba da fitowa ko, ai be taɓa ba" "Eh to ba tabbas, amma dai ki kula, kuma kita istigfari ko zasu fito, maza ki ɗau carbi, ki shiga saƙo kiyi ta Astagfirullah". Jiki a saɓule, Nana ta cire hannunta daga ledar tsire ta koma gefe, ta ɗau carbi. Inna ji tai kamar ta tuntsure da dariya, Nana ta nutsu tana istigfari, Allah ya karɓi tuban ta. Farhan kuwa, ana kawo wuta ta tashi ta goge Uniform ɗinta, gaba ɗaya zuciyarta da tunaninta suna kan yadda za tai da Prince. Washegari da sassafe, Farhan ta shirya, ta shashafa turare, ta kints da wuri tai sallama da Ummanta, ta tafi makaranta. Ana buga jiniyar Assembly, Farhan tana cikin 'yan gaba gaba na fitowa gurin Assembly. Suka tsatstsaya a filin assembly, ta dinga rarraba ido amma ba ta hango Prince ɗin ta ba, ji tai kamar ta je ta tambayi abokansa ko ya zo?. Gaba ɗaya ta kasa samun nutsuwa, ba taga Prince ɗinta ba, Nazir ne yazo wucewa ta kusa da Farhan, se waige waige take, ya kalli Farhan yace "what are you looking for?" Kallon sir Nazir tai ta ɗauke kai, dan haushin Sir Nazir take ji. Yace "ba Magana nake miki ba?" Ɗan sunkuyar da kai tayi amma taƙi magana, tsaki Nazir yai ya wuce ta. Har aka kusa gama Assembly, ba Prince ba dalilinsa, hankalin ta duk yaƙi kwanciya, babban burinta shine tai tozali da Sadik. Har aka kammala assembly, aka fara tafiya classes, Sadik be shigo ba, jiki a sanyaye take ƙoƙarin barin assembly ground ɗin. Ba tsammani ta hango shi ya shigo, cikin bossy walk ɗin sa yake tahowa, hannunsa ɗaya goye da ƙatuwar jakarsa, ya cake comb a kansa, su Nasir ne suka je inda yake, suka fara gaisuwar su irin ta samari. Farhan kuwa tsayawa tayi ta zuba musu ido, karaf idon Prince ya sauka a na Farhan, amma cike da jarumta ya kauda idonsa kamar be ganta ba. Suka zo suka wuce ta gaban Farhan suna hira, Nas yace "Prince beb ɗin can fa saboda kai ta tsaya, kuma ka wani basar" "Na sani, amma dole in nuna mata mahimmancin soyayyata a tare da ita, zanga wa zata fifita tsakanina da wancan a jawon" Dariya suka kwashe gaba ɗaya su kai class. Farhan gaba ɗaya jikinta tai sanyi, shikenan Prince ya dena sonta, tun da har ze iya ganinta ya share ta haka? Kenan ya dena sonta?. Jiki a sanyaye ta tafi ajinsu, jinta take tamkar mara lafiya, wai yau ita Sadik ya gani amma ya share, ko meyasa ta biyewa maganganun Sir Nazir oho? Haka ta nufi ajin nasu, sedai tsayuwar da tai a hanya, tana zuwa ta tarar da Sir Nazir har ya shiga. Gabanta ya faɗi, amma ta dake ta shiga ajin, aikuwa ya ƙureta da ido. Hakan yasa ta ɗan dirirce, "from where are you?" "Assembly ground" ta bashi amsa. "Ni zaki wa ƙarya? Tun yaushe aka baro Assembly ground ɗin? Kin dai tafi gurin wancan banzan yaron mara tarbiyya ko?" Da sauri ta ɗago ta kalli Nazir, ta msida kanta ƙasa tana sake haɗe rai. "Wuce kije ki zauna, mara jin Magana kawai, ki cigaba da biye masa zan gauraya dake ne" Yana ɗauke kai ta murguɗa baki, taje ta nemi guri ta zauna. Ya ɗau marker, yaje kan White board ɗin, ya rubuta date da sunan subject ɗin, sannan ya zo ƙasa ya rubuta Adoloscent period, ya ja layi sannan ya juyo ya kalli 'yan ajin. "Today's lecture we are going to talk about adolescent period, but let me warn you guy's, if any body among you misbehave, i will mercilessly deal with that person, hope i made myself clear?" Suka amsa da yes sir. "Can anyone among you tells me a little he understand about this topic?" Gaba ɗaya ajin sukayi shiru, ba wanda yace komai. "So non of you ever heard this word before?" Nan ma shiru suka yi, Farhan ya kalla da ta ƙurawa guri ɗaya ido ko ƙyaftawa ba tayi. "Hey!" Ya daka mata tsawa. A razane ta dawo hayyacinta tana kallonsa. "Meke damun ki ne?" Ta girgiza masa kai tace "Nothing sir" "Oya stand up" Ba musu Farhan ta tashi tsaye, Nazir yace "what do you understand by Adoloscent period?" Sunkuyar da kai tayi, tai masa shiru. Yai maganar juyin duniya amma taƙi, magana. "Farhan, I don't know what you are turning to, you are gentle and so obedient before, amma yanzu gaba ɗaya kin canza, kin zama me taurin kai da rashin ji, a haka zaki lalata rayuwarki da tunanin iska da shirme, sit down senseless child" Farhan tana zama se hawaye, ta rasa me ta tsarewa sir Nazir da take damunta haka ya tsaneta, bayan yasa Sadik yana fushi da ita, amma ya gza dena binta da miyagun kalamai. "Kamar yadda ku ka gani a allo na rubuta, Adolescence is the period of transition between childhood and adulthood. Children who are entering adolescence are going through many changes (physical, intellectual, personality and social developmental). Adolescence begins at puberty, which now occurs earlier,than in the past, due to environmen and the kind of food we eat. Shi Adolescent period, lokaci ne na tashen balaga, lokacin da mutum ke canzawa da ga yarinta shiga mataki na girma. Yaran  da suka shiga matakin balaga, suna fuskantar sauye sauye a halittar jikinsu, yanayin mu'amalar su, tunaninsu da kuma hange. A baya a kan samu jinkiri, kan yara su shiga matakin tashen balaga, sedai a wannan zamanin yara na shiga matakin balaga ne a ƙananan shekaru, saboda yanayin Muhallinmu, Abincin da muke ci, kallace kallace da sauransu. Lokacin tashen balaga lokaci ne mafi hatsari a rayuwar ɗan Adam, idan mutum ya samu kyakyawar kulawa ya bar wannan stage ɗin lafiya, ans  sa masa ran yai kyakykyawar rayuwa, idan mutum ya bari ya lalace a wannan lokacin, to girman sa sedai wani ikon Allah, as how some of you are doing now, trying to be spoiled at their adolescent age, hanging around with stupid and spoiled guys. Sarai Farhan tasan da ita yake, amma ta basar. Ya cigaba da karatunsa. "Akwai sauye sauye da dama, da Yara maza da mata ke fuskanta a lokacin tashen balaga, da suke nuni da sun shiga wannan mataki na girma. A ɓangaren maza, akwai buɗewar murya, daga ƙaramar muryar su ta yarinta zuwa babbar murya, akwai fitowar gemu ko saje, akwai fitowar gashi a hammatar su da mararsu, manhood ɗin su ze ƙara girma, ba kamar da da suke yara ba, za su fara mafarki.. "Sir ai dama kullum ana mafarki" cewar wani yaro. "No is not a usual dream, mafarkin suna having sexual intercourse, wanda idan suka farka ta kan kai ga sun fidda maniyyi, akwai developing sexual feelings da opposite sex ɗinsu, saboda aiki da homones ɗin su sukeyi toward that, shiyasa in this period ba'a son yawan cakuɗeɗeniya da mu'amala a tsakanin opposite sex, saboda a  wannan lokacin ƙwaƙwalwa na negative thinking towards satisfaction of sexual feelings among the Adolescents. A ɓangaren mata kuwa, suma muryarsu na ƙara daɗi, daga muryar yarinta zuwa ta 'yan matanci, ta yadda muryar ta su kan iya atrackting opposite sex ɗinsu. Akwai development of breast, ƙirjinsu ze fara girma Yana tasawa, saɓanin da da yake a shafe Bakomai. Gashi ze fito a hamattar su, da kuma al'aurarsu. Zasu fara developing feelings towards opposite sex. Akwai fara jinin al'ada, zasu fara zubar da jinin al'ada duk wata. Any one of this signs is a sign of puberty, ba dole se mutum ya haɗa su gaba ɗaya ba lokaci ɗaya, wani na iya farawa da gashin hammata, wata za tai developing breasts amma ba ta da gashi a hammata, ko ta fara jin feelings amma ba ta fara al'da ba. Alamomin ba suna zuwa lokaci ɗaya bane, they are coming one after the order. The must dengerous part of it, is when a lady start seeing her menstrual period, and she's not able to maintain her sexual feelings, anything can happen at that time, she can easily get belle God Forbid. In our next class insha Allah, we will continue from where we stop, and we will discuss the other signs, and personal hygiene during puberty insha Allah, if anyone of you has a question he can ask, before i ask my own when ever I decide to do so, my question will be as assignment or test. Ya kammala ya tattare takaddunsa, ya fita, dan ba wanda yai tambaya. yana fita 'yan ajin suka sa shewa. Lilly tace "wai, yau zamu gane wanda suka reaching adolescent period, a mata zamu ga wadda ƙirjinta ya fara tasawa da wadda har Yanzu take Small Baby". Kwashewa su kai da dariya, wata yarinya tace "aikuwa maza kuma zamuji masu husky voice, da wanda suke da Baby voice har yanzu" Lilly tace "ke Hasina masu babbar murya wannan ai se daga ajin su Prince zuwa sama za ki ji wannan, sedai in layi za suyi a leƙa hanmatar mu gani" Hasina ta kwashe da dariya tace "ko muji in da wanda ya fara dreaming ba" "Hmm yau zamu tantance adults da Babies, ɗaya bayan ɗaya zamuyi screening, muji wadda ta fara saka brezia, da wadda har yanzu take sahun yara, maza kuma azo a bamu labari wanda suka fara dreams" Dariya suka kuma yi, Lilly tace "Yasmin ke fa 'yar iska ce wallahi, se su hau layi ki fara dubawa ai" Suka cigaba da taɗin su, Farhan kuwa tai shiru tana tunani, wasu daga singns ɗin nan na adolescent period, already ta fara Experiencing ɗin su, amma ita banda yau ba ta taɓa sanin wannan alamomin balga bane, babu wanda ya taɓa gaya mata. (Ƙalubale gareku iyaye) Tunani ta fara yi meye wannan sexual feelings ɗin, tasan shi ake nufi da sha'awa tun da sunyi a islamiyya, amma meye shi ɗin? Ya mutum ze gane that he has sexual feelings towards his opposite sex? Yanzu tarayyarta da Prince ze iya sa taji feelings akan sa kenan? Kuma hakan na nufin matsala ne kamar yadda Sir Nazir ya faɗa?. Kai koma me ze faru, ta san ba wani abu da za taji ko ya faru, dan tana tare da Prince, kuma ma ai shika ɗai ne namijin da take kulawa, ai ita ba shiga sabgar maza take ba. Da sauri ta tashi ta fita waje, ta nufi ajin su Prince. Tana zuwa ta tarar 'yan aji suna fitowa, da alama wani gurin za su. Mazan sun saka kayan sport wears, prince ya fito hannunsa ɗauke da ball, yana buga ta yana cafewa. Farhan ta zuba masa ido, ya ɗaga kai suka haɗa ido, ɗauke kai yai kamar be ganta ba ze wuce. "Sadik" ta faɗa a sanyaye. Ɗaga kai yai ya kalleta, be ce komai ba. Ganin ba za tai Magana ba, yasa shi yin gaba ze wuce, ba tare da shirya ba ta riƙe rigarsa. Ya waigo ya kalleta, yaga idonta ya cika da hawaye. Jiki a sanyaye tace "Am sorry please" "Sorry for what? You don't need to apologise, ki je ki biyewa wancan ajawon kiyi watsi da soyaya ta" "Dan Allah kayi haƙuri" Prince yai wani irin murmushi da ke sanya Farhan farinciki, yace "ok shikenan my Farhan, ai ba zan iyayin fushi da ke ba, na ma fasa zuwa gurin ball ɗin, hira zamuyi" A'a kar ka fasa zuwa, tun da kayi niyya" "No kin fiye min ball mahimmanci" Amin ne ya dawo yana mita yace "wai dalla me kake a gurin nan, tun ɗazu muna fili muna jiranka?" Prince ya jefa masa ball ɗin yace "ga shi nan kuje kuyi, ni na fasa zuwa" "Kamar yaya?" "Kamar yadda na gaya maka mana" "Amma wallahi ka cika mara mutunci, wannan ai wulaƙanci ne, ya za'ai an shirya abu kuma kace ba za kai ba?" Prince ya kalli Farhan yace "let's go inside my dear" Suka shiga ajinsu Prince, suka bar Amin a gurin. Amin ya juya ya tafi yana masifa, yana zuwa filin ƙwallon ya saki ball ɗin a ƙasa yana mita. Nas yace "ahh ya haka? Ina Prince ɗin?" "Waccan mayyar yarinyar ce taje gurinsa, Shine ya jefomin ball ɗin wai baze ba, ya tsaya a gurinta" Taslim tace "wai dan Allah meya sa Prince yake wa mutane hakane?" Meenat tace "ai shegiyar yarinyar ce mayya" Amin yace "maganin ta zamuyi, idan har zata cigaba da rayuwa da Prince to dole za ta shigo clique ɗin mu" Nas yace  "ƙwarai kuwa, rabu da shi za muyi maganinsu daga shi har ita" Daga nan suka fara ball ɗinsu a tsakanin maza da mata (😲🙄🤔). "Farhan, ko kina doubting akan son da nake miki ne?" Farhan ta girgiza masa kai. "To meyasa kike guduna Farhan? Wallahi i really love you" Shiru tai ta sunkuyar da kai, tana hawaye, Prince yace "ok I got you, is ok ki dena kukan" Yai maganar yana ƙoƙarin kai hannu ya share mata hawaye, amma ta jabda baya da sauri" Yace "ok sorry, karɓi hancky ki goge hawayen, ki dena zubarmin da su a banza" Ta karɓa ta goge hawayenta, tana cikin gogen hawayen aka kawowa Prince Abincin da yai order. Yaje ya karɓo ya dawo yace "My dear, me za'a kawo miki ne?" "Nothing" ta faɗa a taƙaice. "Why?" Tace "Na ƙoshi" "No baki ƙoshi ba, muci wannan tare" Farhan tace ba zata ci ba, Sadik yai ƙasa da murya ya ɗebo a spoon ya kai bakinta, yana mata wani irin kallo Yace "dan Allah kici ko nima in ƙi ci" Ji su kai an buɗe ƙofar ajin da ƙarfi, suka waiga gaba ɗaya..... Free pages are not much, hurry up and subscribe yours. Domin gyara, sharhi ko shawara Ayshercool 07063065680. [6/4, 4:21 PM] Jakadiyar Arewa: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ RUƊIN ƘURUCIYA PERFECT WRITERS ASSOCIATION (WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS) https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ P. W. A *Story and written by* AISHA ADAM (AYSHERCOOL) Writer of WATA KISSAR..(Sai mata) ABDUL JALAL AƘIDATA (paid book) WUTA A MASAƘA NOW RUƊIN ƘURUCIYA (paid book) _Labarin RUƊIN ƘURUCIYA, na iya zuwa da wani salo, wanda baku saba ganinsa a rubutuna ba, hakan ya biyo bayan akan abunda aka gina labarin, wani abun ze ɓoyu wani Abun baze ɓoyu ba sakamakon labari ne akan teenegers, yara masu tashen Balaga, but hakan ba ya na nufin na sauka daga kan tsarin yadda nake Rubutu bane, ƙofata a buɗe take dan karɓar ƙorafi, gayra ko shawara_ ⚠️⚠️⚠️ƘIRƘIRARREN LABARI NE, BAN YADDA A JUYAMIN SHI TA KOWACE SIGA BA SEDA IZININA ❌❌‼️                                7_8 Jikin Farhan har ya fara tsuma zaton ta Sir Nazir ne. Shi kansa Prince ya ɗauka Nazir ne, dan ya shirya tsaf dan maida martani ga duk wanda ya kuma kawowa soyayyarsa barazana koma waye. Se dai ba ba yadda suka zata bane, wani ɗan ss3 ne wanda ake cewa Babba. Ya shigo ya kalli Prince yace "wai kai Prince wane irin banza ne? Ya za'ai an shirya abu da kai kace ba za kai ba meye hakan?" Gyara zama Prince yai ya kalleshi Yace "an shirya yin abu dani, yanzu kuma nace ba zan ba, ba shikenan ba" "Dalla kar ka gayawa mutane Maganar banza mana, wannan ai wulaƙanci da rashin mutunci, wai kai meyasa kake haka a rayuwar ka ne?" Banza Prince yai masa, yaƙi ko kallonsa. Babba ya dinga zazzagawa Prince jaraba, amma ya mirsisi yaƙi sake tanka masa, seda Farhan ta fara jin haushin abun da Babban yake wa Sadik. Babba dai takaici ya isheshi, yai waje yana mita. Yana fita Sadik ya girgiza kai kawai yai murmushi. Farhan tace "Naga sun ji haushin abunda kayi, bari in tafi kawai kaje kai Ball ɗin" Sadik yace "No, ni kin fiye min ball ɗin nan, maza muci Abincin nan kar ya huce" Fafur Farhan taƙi cin Abincin nan, yai yai da ita amma ta ƙi yadda ta ci, se ƙyaleta yayi. Yana cin Abincin suna ɗan taɓa hira, duk da Mafi yawa daga hirar shi yake mata, can tace "wai meyasa ake ce maka Prince ne?" Wani kyakyawan murmushi Prince yai, da yai matuƙar birge Farhan, yace "Kinga ni ba sarki ba, ba ɗan sarki ba amma ana cemin Prince ko?" "A'a kawai tamabaya nayi?" "Kakana Hakimi ne, Kakata ma 'yar Hakimi ce, sannan babana yana da sarautu daban daban har a kudancin ƙasar nan, kwanan nan ma an masa wata Sarautar a Ghana, kuma ana ɗan cewa ina da jin kai, wanda ba hakan bane, kuma ni ne auta a gidanmu suna ji dani sosai wannan dalilin ne yasa ake cemin lil Prince" Murmushi Farhan tayi tace "Sannu Prince" "Yawwa matar Prince" ya faɗa yana kashe mata ido. Haka suka cigaba da hira ita da Prince, tana jin wani farinciki maara misaltuwa kasancewar ya dena fushi da ita. Da yake Friday ce, har aka tashi suna tare, ya raka ta har ajinsu ta ɗakko jakarta, suka fito harabar makarantar. Suna fitowa kuwa su kai arangama da Nazir, ya zubo musu ido yana musu kallon tuhuma, dan ba kowa a cikin makarantar se su, dan duk ana waje gurin wasa. Gaban Farhan yai mummunar faɗuwa, amma ta dake ta ƙi kallonsa. "Hey daga ina kuke!?" Ya faɗa cikin shouting, wani Mugun kallo Sadik yaiwa Nazir, yaja hannun Farhan da sauri, wanda se da hakan yasa ta firgita, be tsaya ko ina ba se bakin motarsu, ya buɗe mata yace "shiga" Ta waiga ta kalli Nazir ta kalli Prince, a hasale yace "shiga nace" Da sauri ta shiga, shima ya shiga motar ya cewa direba ya ja su tafi. Ta kalli Prince ta na so tayi magana amma taga ya wani haɗe rai, tilas ta ja bakinta ta tsuke, dan ko cikin kuskure ba tavsin sake aikata abunda zesa yai fushi. Har suka sauke Farhan be kuma ce mata uffan ba suka nufi gida. Shikuwa direban Sadik addu'a yake Allah yasa kar Sadik ya ɓata Yarinyar nan ganin yadda take masa biyayya kamar ubanta. Sadik suna zuwa gida, ya tarar da mahaifinsa a harabar gidan, shi da wasu baƙi, watanni biyu kenan mahaifin nasa baya gari, se Yau ya dawo. Da gudu Sadik ya sakko daga mota, ya nufi mahaifinsa da gudu, ga abokan mahaifinsa a gurin amma be bi takansu ba, ya rungume mahaifinsa yana faɗin "I miss You Daddy" "Miss you too Auta na, how are you and how was your studies?" "Fine Daddy, amma meyasa ba ka gayamin yau zaka dawo ba? Kawai se in dawo in ganka?" "Eh mana, i warn Your Mum kar ta gaya maka zan dawo yau" Murmushi Sadik yai, ya kuma kallon mahaifinsa yace "I really miss you" Mahaifinsa yai murmushi ya shafa sumar kan Sadik yace "maza kaje ka canza kaya ka huta, in zo muyi hira" Ɗaya daga abokan mahaifun nasa yace "Wai Sadik ne ya zama haka? Ya girma sosai, ko dan na daɗe ban ganshi ba?" Daddy yace "Shine gashi ya zama big boy ba" "Gaskiya girman ɗan mutum ba wuya, kwata kwata yaushe muka je da kai a kai masa kaciya, ai nasan ba ze manta dani ko dan wannan ba" Sadik a ransa yace "kutmar, ji ɗan rainin hankali wai suka kaini kaciya, abu ya wuce shekara goma sha, amma dan wulaƙanci wai an kaini kaciya dan cin zarafi, Allah yasa ma ba a gaban wanda zeji kunya ya faɗa ba, ya rasa dame ze tunani se sun kaini kaciya" Saidk ji yai kamar ya yi tsaki, amma ya maze ya wuce, ba tare da ko sannun ku ya cewa abokan mahaifinsa ba. Kuma hakan be damu mahaifinsa ba, dan yasan halin ɗan nasa na rashin son mutane, da kula jama'a. Da daddare bayan sallar isha'i, Sadik ya shiga cikin gida, dan gaba ɗaya ya bar ɗakinsa na cikin gida, saboda yawan mutane da suke zuwa gidan. Ya tarar da Daddynsa da Mother, da su Usman a falonsa, suna tattauna maganar bikin Usman. Prince yana zuwa ya haye kujerar da mahaifinsa yake zaun yace "bari in zauna ta nan inji ɗuminka sosai" Faruk yace "wai kaji ɗuminsa, kamar wani wanda za'a shayar" Daddy yai murmushi yace "kar ka damu ɗan auta mana, ƙyaleshi ya zauna kusa dani, nima ɗumin nasa zanji ai, nayi kewarsa sosai" Ango Usman kuwa ɗan taɓe baki yai, saboda taɓarar da Sadik yake yi tana yin yawa, yaiwa Daddy yaiwa Mother, kuma lailaya shi suke kamar wani ɗanyen ƙwai. "Auta na ga saƙonka kan in dawo, kuma shirye shirye sunyi nisa sosai, na tura kuɗin Neco da Waec ɗin ka, kamar yadda ka buƙata zaka kammala secondary this year ina sha Allah" Cike da farinciki yace "Wow, thank you so much Daddy, Nagode sosai Allah ya ƙara Arziki me Amfani" "Ameen My Son" Mother tace "wai dagaske jumping za kai masa kenan? A ss2 yake fa" "Ai ba laifi kin san yaron nawa ƙwaro ne, he can do it yace yana so, kinga ban san me yake hange da yace yana son ya kammala secondary School a wannan shekarar ba, may be he's planning something better for his future" Mother tace "to ai shikenan, Allah ya bada sa'a, shine ni ko a gayamin" Daddy yai murmushi yace "to ai gashi yanzu kin sani, kai kuma seka hanzarta gayamin jami'ar da kake so a waje, a fara processing tun da wuri" Nan da nan jikin Sadik yai sanyi, dan yasan tabbas da zarar ya kammala makarantar nan, ƙasar waje za'a ce ya tafi karatu, Farhan ɗinsa fa zata iya jiran sa? Ƙaddara ma zata jira shi, shi baze iya jiran tsayin wannan lokaci, yana bautar biro da takadda ba, bayan shi abunda zuciyar sa take so daban ba, gaskiya Aure yake so, dan yafi damuwa da Yayi Aure akan wannan bokon. "Ya naga kayi shiru? Ko baka son karatun ne?" Ji yayi kamar yace baya so, Aure yake so ai masa Kafin karatu, amma yace "A'a ina so, ina nazarin wace jami'a zan tafi ne, don't mind me zanje inyi tunanin wace jami'a ta dace da ni" Yai maganar yana miƙewa tsaye, Daddy yace "in wani abu ya shige maka duhu, ga yayyenka nan ko kazo ni ka sameni mu tattauna" "To Daddy, Good night" Yai maganar yana ficewa daga ɗakin. Da yaje nasa ɗakin ma kasa baccin yayi, ga ƙoshi ga kwanan yunwa. Da ƙyar bacci ɓarawo ya sace Prince Sadik, saboda damuwar da yake ciki. Washegari ya kama Asabar ranar da za'a kai kayan Auren Dr. Usman gidan Hakimi, wanda se an kai can sun kwana sannan za'a kai gidan su Yarinyar da ze Aura ɗin. Kaya sun kai kaya, akwatuna goma sha biyu ne na alfarma shaƙe da haɗaɗɗun kaya, masu tsadar gaske. Lefen ya haɗu ƙarshen haɗuwa, haka aka zuba kayan a mota, za'a tafi. Sadik yana saman bene, yana kallon yadda ake zuba kayan a Mota, ya ɗanyi ajiyar zuciya yace "Allah ka nunamin lokacin da zan haɗa kaya fiye dana Dr. a kaiwa Farhan ɗina, a ce yau gani zan Aure nima. Yana nan a tsaye aka ja motocin aka tafi dasu. Shima komawa yai ɗakinsa, ya shirya cikin ƙananan kaya ya fice nasa guri, dan a 'yan kwananin nan zaman Gidan nasu sam baya masa daɗi. Nana na tafe a hanya tana zura hannu a hijjabinta, tana rarraba ido kar taje wani ya kalleta a banza, Ta koma gida Inna ta gane, tana tafe tana ta sauri kamar wadda take da wani uzuri a gabanta. Tana zuwa ƙofar gida ta tarar da cincirindon motoci a ƙofar gidan, dama tun safe ta ga ana dafe dafe a gidan, ta tambayi Inna me ake haka amma ta gaya mata baƙar magana, taƙi gayamata meke faruwa. Fararan fararan ta shiga ratsa mutanen dake harabar gidan, ta shiga cikin gida. Ta tarar da mata a zazzaune ana ta rangaɗa guɗa, banda masu bushe bushe da ta baro a waje. Neman Inna ta shiga yi cikin lungu da saƙo na gidan, cikin sa'a ta hango Innan, ta sha Kwalliya. "Innarmu wai me akeyi ne haka?" "To tambaya, daga daowarki ko cire kayan makaranta baki ba, kin zo kin cikani da tambaya" "To Inna ni duk an zo a cika gidan a ina zanje in canza kayan ko ina mutane" "In kin gama fitsarar kya tafi kije ki canza kayan" Inna tai maganar tana cigaba da hada hadarta. Ɗakin Inna ta shiga ba kowa a ciki, ta cire kayan makarantar ta, ta zunduma uban hijjabi sannan ta shiga tai wanka, ta fito ta canza kaya. Inna ta shigo ɗakin zata ɗau abu, ta ga Nana na binta da kallo, Inna tace "kayan lefen Usman aka kawo mu gani, sati me zuwa za'a kai shikenan?" "Waye kuma Usman?" Nana ta tambayi Inna, tana ɗan tura baki. "Au Usaman ɗinma baki san shi ba? Iko se Allah to bari in miki yadda zaki gane, yaran nan masu tara gashi, na gidan Abdullahi" Murmushi Nana tayi tace "Au se yanzu na gane, to ina kayan lefen suke?" "Suna turakar Hakimi" Nana ta zabura tace "bari inje ina gani" "Ke bana son hauka, da baƙin a gurin zaki je? Kefa wani lokacin kwantacciya ce" Nana ta ɗan haɗe rai, dan taji haushin ce mata kwantacciya da Inna tayi. Se la'sar sannan masu kawo kayan suka tafi, Hakimi yace a bar kayan a nan, Ranar da za'a kai lefen, za'a tafi dasu daga nan. Haka kuwa akayi, aka tafi aka bar kayan a nan, akan se ranar da za'a kai sannan za'a tafi dasu. Ko da labari ya ishi Mother an baro kayan lefen nan a ƙauye Gidan Hakimi, abun ya baƙanta mata rai, ta dimga sababi akan me za'a baro mata kaya a can, salon a sace musu wani abun, haka tai ta sababin ta ta haƙura. Ranar Monday a school prince yai shirin ko ta kwana ko da Nazir ze gaya masa wata maganar banzan akan abunda ya faru Ranar Friday, amma yaga be kulashi ba. Ita kuwa Farhan faragaba ta dinga yi, dan kar ya cimata mutunci, dan ta fuskanci ya tsane ta sosai, ba ita kaɗai ke soyayya a makarantar nan ba amma yabi ya sa mata ido. Cikin ikon Allah kuwa be tanka mata ba daga ita har Prince ɗin. Ana fita break kamar jira take, ta tafi ajinsu Prince, sun barbaje suna ta hira ana kwasar dariya, suna tsara irin yadda zasu raƙashe a bikin Yayan Prince da za'ai nan da wata ɗaya, wanda ze kama a cikin hutun kirsimeti da kuma sabuwar shekara. Sallama tayi tana duba inda za ta ga Prince, yana kashingiɗe yana game a wayarsa, sedai in sunyi abun dariya shima yayi. Duk d rashin son kallo da Farhan ba tayi, da kwarjini da 'yan ajin nasu Prince ke mata, hakan baya hanata shiga ajin in dai za ta ganshi, kamar yasan ta shigo ya ɗago aikuwa su kai ido huɗu da Farhan. A tare sukayi murmushi yace "welcome my cwt" A hankali ta tako cikin tafiyarta me ɗaukar hankali. Taslim ta kalleta ta ɗan yatsuna fuska, dan yanzu haushi Farhan take bata tace "wai ke kam ba kya gajiya ne? Kullum cikin sintirin zuwa ajin nan ki ke?" Take jikin Farhan yai sanyi, ta ɗanyi sororo tana kallon Taslim, kuma Maganar Taslim tana kan gaskiya. Prince yace "Taslim wallahi zan tatala miki rashin mutunci da baki taɓa tsammani ba, ina ruwan ki da ita? Me tai miki ko ajin daga gidanku ki ka zo da shi? Bana son haka ban sawa kowa ido ba, dan haka nima kar a samin" Taslim tace "Allah ya baka haƙjri sarkin fushi, wasa nake mata" "To ba'a san wasan" ya faɗa yana harar  Taslim. Ya kalli Farhan yace "ƙaraso mana" A hankali ta ƙaraso tana ɗan wasa da yatsunta. Kan ta zauna ya ɗan tsaya yana kuma ƙare mata kallo, girma Farhan take ƙara yi, ƙara buɗwa take ga wani kyau da take ƙarawa. Ɗan lumshe ido yai yana murmushi, ta zauna a ɗan nesa da shi kaɗan. "To ya, kina lafiya my love?" Sunkuyar da kai tayi cike da jin kunya, tace "lafiya ƙalau" "Ai tun ɗazu naso in zo ajin ku, sedai nace bari in jira inga zaki zo?" Murmushi kawai tayi ba tace komai ba. "Nifa bana son wannan shirun, hira zaki min inji muryarki, kullum sedai ki zo ki kalleni kina murmushi, duk da murmushin naki burgeni yake, but say something" "I have nothing to say" ta faɗa a ɗan shagwaɓe. Dariya yai yace "muryarki da turancin kamar baturiyar England" Seda ta ɗan zare ido jin abunda Prince ɗin nata yace. "Farhan, an kusa bikin Yayana, zaki zo ko?" "Yaushe ne?" "Nan da 1month insha Allah, ai zaki zo ko?" "Ina tunanin ko za'a barni inje a gida" "Meyasa ba za'a barki ba?" "Baban mu yana da tsaro sosai, ba'a barina fita sedai in a 'yan ajinmu wasu zasu je, su zo mu tafi tare, kuma ka bani kati in kai gida" "Karki damu dan wannan ba Matsala, yama za'ai ai bikin bro tawa matar va taje ba, kin san daga bikinsu se namu fa" Zare ido tayi sosai kamar ya faɗi wani abun tsoro. "Meye naga kina zare ido haka?" "Ya za'ai amana Aure yanzu, mufa yara ne" Ƙasa ƙasa suke hirara ba wanda yake jina bunda suke faɗa, amma jin abunda Farhan ɗin tace yasa Prince cikin ɗaga murya cewa  "What!". Seda aka jiyo aka kallesu, Prince ya basar yai ƙasa da murya tare da ɗan haɗe rai yace "suwaye yaran?" Ɗan tura baki tayi tace "to ai naga ko makaranta ba mu gama ba, kuma base mutum ya girma yake Aure ba, waye ze mana Aure a haka?" Seda Prince yai murmushi, ya jinjina wauta da ƙuriciya irin ta Farhan, sannan yace "waye yace miki shi girma a fili yake, waye yace miki sharaɗin Aure ne se mutum ya girma sosai za'a masa Aure?" "Ai haka naga anayi" "Hmm Farhan kenan, yanzu idan Dad ɗina yazo nema min Aurenki baza'a bni ba?" Ya faɗa in a very serious tone. Kamar za tai kuka tace "wallahi ina ga se ya kusa ɓallani, cewa ze ya akai nai saurayi har na fara Maganar Aure?" "Hakane You Are still Baby, but looking so.... Se kuma yai shiru yana cigaba da ƙuara mata ido, har seda ta ɗan tsargu. "Amma ai kina sona ko?" Ɗaga ido tai ta kalleshi, ta mayar ta sunkuyar. "Hmm i understand" Babba ne na ss3 ya shigo ajin, yana shigowa Taslim ta miƙe da gudu ta rungumeshi, ya ɗagata yana juyi da ita a tsakiyar class ɗin. Mamaki ya cika Farhan, wannan wane irin rashin hankali ne da rashin ta ido. A shagwaɓe Taslim tace "I miss You Honey" "Miss you too dear, ai tunda na dawo tun lats week ba kya Zuwa bamu haɗu ba" "Bama gari, munje Abuja that's why, you are well dear, amma dai ka warke ko?" Babba yace "Alhamdilillah jiki yayi sauƙi sosai" Farhan kama gaba ɗaya seta tsargu, wata kunya ta mamayeta, ganin haryanzu sunƙi sakin juna Taslim da Mubarak wato Babba. Sadik yace "gaskiya Mubarak ku fita can waje kuyi, kun san Babyna jaririya ce kuna iskanci a gabanta karku ɓatamin mata ku sa mata wani tunanin daban" Taslim tace "ba wani jaririya, ta san komai, don't mind them my sugar" Tai maganar tana kissing Mubarak a kumatunsa. Nasir yace "kaga in da ake abu, ba irin soyayyarku ba, soyayya irin ta zamanin iyaye da kakanni" Farhan ta miƙe tace "Na tafi aji" Sadik yace "sun kore ki ko? Banzaye kawai muje in kaiki class" Ya miƙe suka jera suka fita, sedai Nas yabi bayan Farhan da kallo. Amin ya daki cinyarsa yace "kai lafiyarka kuwa?" "Lafiya ƙalau, ina kallon Yarinyar nan ne kawai, gaskiya ina ni zan sharewa Prince hanyar nan, kan uba ka ga abunda na gani kuwa?" "Aikuwa da yaci ubanka la'ada waje" "Kai dall ƙyaleshi, se wani abu yake waishi na Allah, this girl is looking so hot ka gane ai" "Karka kuskure ya gano ka wallahi, dan karonku baze maka daɗi ba, nasan akan yarinyar nan ba abunda baze iya ba" Nas yace "za'a cigaba da ɗora shi a layi, idan yaƙi ɗaukar haske zega aika aika" Suka cigaba da hiararsu ta rashin ɗa'a. Kwanci tashi asarar rai, satin kayan lefe guda cif, duk 'yan uwa dangin Alhaji Abdullahi duk suka zo suka ga kaya, sannan Inna ta shirya ita da Jikarta aka kawo motoci aka kwashe su su da kayan. Can gidan Alhaji Abdullahi suka tafi da kayan, Nana ta ware ido ta finga kallon gidaje kamar biscuit, kamar a ɗauka a ci dan kyau da tsaruwa. A ƙauye ana cewa ba gidan da ya kai na Hakimi ƙaruwa, amma yanzu idonta ya gane mata in da ake gidaje. Da ana zuwa da ita tsohon gidan, amma Inna ta daɗe bata taka ƙafarta gidan nan ba se yau. Hajiya Hauwa kuwa wato Mother, taji haushin yadda aka taho da 'yan ƙauye, wai za'a kai kayan lefe, abun nan ya baƙanta mata rai a nata faɗar zasu ɓata mata lamari dan ba hankali suka cika ba. Ba yadda ta iya tunda ga uwar mijinta, kuma shikansa maigidan yana gari balle tai rashin mutunci, tun asalin kai kayan ƙauye ma abun be mata ba, balle kai kayan lefen tare da su, ga ƙawayenta da 'yan uwanta 'yan gayu amma za'a haɗasu da tarkace. Aka kuma shishshsigo da Akwatuna, Inna tasa aka sassauke kaya aka sake buɗewa, Hakimi ya sa an ƙara atamfofi dozen a ciki, Inna kuma ta saka zobuna da sarƙoƙin azurfa. Nan aka dinga guɗa ana Allah ya sanya Alkhairi. Wata ƙawar Mother tace "kai Hauwa, dangin mijin nan naki duk da 'yan karkara ne, amma sun san abunda yakamata, wallahi da nawa dangin mijin ne, sedai a kaisu a haka inma basu saci abunda zasu sata ba, amma kalli aabun arziki kuma atamfofi masu tsadar gaske, su kansu azurfofin nan masu tsada ne sosai" Tsaki Mother tayi tace "nifa duk abunda za'a saka da mutanen nan ba sonake ba, inma bayarwar ne a aiko dasu mana, kawai an kwashi kaya an kai musu, an kuma kwasowa an dawo, za'a kuma kwasa a kai kaya dasu, ni Allah yasa ba wani abun sukai wa kayan ba, dan ni ba wani yarda nai dasu ba" "Ke Hauwa, meye aibun hakan? Taɓɗijan, a zaminin nan ki samu dangin miji suna son 'ya'yanka, ai wallahi banga aibun hakan ba" Tsaki Mother tai, ta cigaba da cika tana batsewa, tana wani basar da su kamar taga bola. Daddy ne ya shigo tare da Ango, wato Usman. Take 'yan ƙauyen nan suka kaure da guɗa ana shewa, Alhaji Abdullahi ya dinga murmushi, haka shima Usman ya dinga murmushi. Alhaji Abdullahi ne ya fara zubewa a gaban mahaifiyarsa wato Hajiya Inna, ya dinga mata kirari sannan ya gaisheta abun gwanin burgewa. Ya cire hular kansa ya durƙusa a gabanta yace 'barka da zuwa farar uwa me farar aniya, 'ya ga Hakimi mata ga Hakimi, katangar sukari kowa ya jingina dake se ya lasa, farar uwa abun alfahri 'ya'yanta, shalelen Hakimi barka da zuwa uwata ta kaina" Seda mutanen da ke falon suka saka shewa, saboda abun gwanin burgewa. Murmushi Inna  tayi, wanda se fararen haƙoranta suka bayyana sannan ta amsa masa "Sannunka ɗan gidan Innarsa, mun sameku lafiya" "Lafiya ƙalau Inna" "An shab turai, Usaman Allah ya kawo mu lokacin Aure, Ubangiji Allah ya Sanya Alkhairi" "Ameen Inna" Usaman yace "Inna ina wuni" "Ba zan amsa ba, bayan ba kwa zuwa inda nake" Usman yace "ba haka bane Inna, kin san ba zaman ƙasar muke sosai ba" "Eh kuna can kuna yiwa nasara bauta ba, ai shikenan ni gani nazo ai, ina nan har a yi biki ai, ga kaya nan Hakimi ya ƙara maka, yace yana maka murna, se kuma Allah ya kaimu Lokacin ɗauren Aure ze zo" Alhaji Abdullahi yace "Masha Allah, muna godiya ranki ya daɗe, Allah ya ƙara arziki yasa afi haka" Nana ce tace "Kawu ina wuni?" Ɗagowa Alhaji Abdullahi yai ya kalli Nana yai murmushi yace "ai ban kula dake ba, ni yakamata in gaisheki Uwata ta kaina, ina wuni Ummana" Rufe fuska Nana tayi cike da jin kunya ba tare da ta amsa ba. Inna ta nuna mata Usman tace "to kin san wannan? Ko kuma baki sanshi ba se me tara gashi?" Nana tace "Nasan shi mana" "To ya sunansa?" Shiru Nana tayi tana tunani, amma ta kasa tunawa. "Kaga abunda nake faɗa ko ko Abdullahi, bata san sunan 'yan uwanta ba, sedai tace 'ya'yan kawunmu masu tara gashi" Alhaji Abdullahi yace "Ayi haƙuri Inna, insha Allah za'a san abunyi" Nana gajiya tayi da zaman, ana ta hira ta tashi dan fitowa harabar gidan ta sake ganin abubuwa. Ta fito tana ƙarewa motocin dake harabar gidan kallo, bin motocin ta dingayi ɗaya bayan ɗaya tana shafawa, tana sake lelleƙawa. Ta gaji da wannan ta nufi wani ɓangaren daban. Leƙe leƙnta ta cigaba dayi, tana zazzagawa. Motar Prince na shiga gidan, ya fuskanci da yauma da mutane a gidan, tun daga cikin motar yake jan uban tsaki yana cewa aikin banza anzo an cikawa mutane gida, an hanasu sakewa. Ya saɓo jakarsa ya nufi BQ yana ƙwafa yana masifa, sedai yana shiga falo ya tarar da ita tana tattaɓa ƙatuwar plasma dake jikin bango. "Ke wace wannan? Uban me kike a nan?!" A razane ta waigo ta kalleshi tace "yi haƙuri ban san ba'a shigowa nan ba" Gani yai kamar ya santa amma ya manta inda a santa. 'ke wace irin banza ce, daga zuwa gidan mutane kawai kije inda ba'a aikeki ba, dama kinga mutane na zuwa nan ne?" Haɗe rai tayi tace "kar ka sake zagina ba nace kayi haƙuri ba" tai maganar tana tura baki. 'dalla zoki fita ki barmin ɗaki, mahaukaciya kawai" Nana tace "Kut, wallahi kaine mahaukaci bani ba" "Ni kike cewa Mahaukaci?" "To uban waye yace ka fara gayamin mahaukaciya?" "Ubanki ne" ya bata amsa. "Sedai ubanka bani ba" Aikuwa ya nufi inda take gadan gadan.... Free pages are not much, hurry up and subscribe yours. Ayshercool 07063065680. [6/4, 4:21 PM] Jakadiyar Arewa: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ RUƊIN ƘURUCIYA PERFECT WRITERS ASSOCIATION (WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS) https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ P. W. A *Story and written by* AISHA ADAM (AYSHERCOOL) Writer of WATA KISSAR..(Sai mata) ABDUL JALAL AƘIDATA (paid book) WUTA A MASAƘA NOW RUƊIN ƘURUCIYA (paid book) _Labarin RUƊIN ƘURUCIYA, na iya zuwa da wani salo, wanda baku saba ganinsa a rubutuna ba, hakan ya biyo bayan akan abunda aka gina labarin, wani abun ze ɓoyu wani Abun baze ɓoyu ba sakamakon labari ne akan teenegers, yara masu tashen Balaga, but hakan ba ya na nufin na sauka daga kan tsarin yadda nake Rubutu bane, ƙofata a buɗe take dan karɓar ƙorafi, gayra ko shawara_ ⚠️⚠️⚠️ƘIRƘIRARREN LABARI NE, BAN YADDA A JUYAMIN SHI TA KOWACE SIGA BA SEDA IZININA ❌❌‼️ 9_10 Kafin ya cinma ta tuni ta arta a na kare, kamar walƙiyya ta bar falon da gudu, ya bi bayanta sedai yana fitowa ya neme ta ya rasa kamar aljana, se kace iska ta kwashi takadda, ba ita ba alamarta. Ya ja tsaki ya koma ɗakin, yana ƙoƙarin tuna in da ya taɓa ganin fuskarta. Ganin hakan ba ze fushsheshi ba yasa ya shige bedroom ɗinsa yana tsaki, gami da jin haushin bikin nan na Yayansa, dalilin wannan bikin da yayime yayimen mutane ake a gidan, masu hankali, sekace akansa aka fara Aure. Haka yana ƙunƙuni yana mita, ya cire kayan makarantar sa ya shiga yai wanka, ya fito yai sallar azahar, yana son shiga cikin gidan cin Abinci, amma ganin taron jama'a da ke gidan ya hanashi shiga, dan baya son taro sam. Ya ɗakko tsaleliyar wayarsa ya nemo lambar Khairat ya kirata. Tana fara ringing ta ɗaga tace "ya akayi?" Seda ya ɗan yatsuna fuska sannan yace "kina gidanmu ne?" "Eh ina nan" "Suwaye a cikin falon nan?" Khairat tace "ji wata Magana, ta yaya zan iya lissafo maka wanda suke falon, mutane ne da yawa gasu nan a gidan" "Wani taimako nake son kiyi min" "Ok am all ears" "Abinci na zaki kawomin BQ" Kamar Sadik na gabanta ta ɗan murguɗa baki tace "meya hana kazo ka ɗauka da kanka?" "Nifa kin san taron mutanen nan ne bana so, in ba zaki kawomin ba shikenan" "Zan kawo maka ba dan halinka ba" "In dan halin nawane karki kawomin, bana son wulaƙanci fa" "Meye wani abun wulaƙanci kuma? Ina zaman zamana ka sani aiki" Tsaki yayi ya kashe wayar ya ajiye yace "Aikin banza ayi a gama wannan bikin ya tafi ya bawa mutane guri, ko ma huta da wannan jarabar, kullum gida a cike mutum baze huta ba, Aikin banza kawai" Se mita yake shikaɗai, haka nan ya tuno Nana da ta zage shi ɗazu a falo. Wani dogon tsakin ya kumayi, ya ji ina ma ya kama Nana, da se ya kusa karyata, seya tataka ta ya koya nata hankali, daƙiƙiyar yarinya fusaka kamar ta yaron aljani. Shikaɗai ya cigaba da soki burutsunsa, yana zage zage. Khairat tai sallama ta shigo bedroom ɗin, ta kalleshi tace "lafiya kake tsaki kai kaɗai, tun daga falo ana jiyoka kana masifa ciki ciki" "Bakomai" ya bata amsa. "Kai faɗan naka ya kai ka dinga yi kai ka ɗai ma a ɗaki, sekace me aljanu?" "Ke kika sani miƙomin Abinci na ni" "Au in maka abun arziki amma ba godiya, se gadara da isa ko, wallahi ka canza hali Sadik, wannan ba halin shiga jama'a bane" "Ina ruwana da wata jama'a, kawai an takurawa mutane, mutum da gidansu anzo an hanaka sakewa, wai ma dan Allah suwaye yau kuma a gidan nan, dan ni wata mahaukaciya ce ta shigo min ɗaki yau" Dariya Khairat tayi tace "wace irin mahaukaciya kuma? Gaskiya duk baƙin Gidan nan banga Mahaukaciya ba" "Ni na ganta ai" "Gaskiya ba wata mahaukaciya, Kakar ka ce fa tazo da 'yan ƙauyen ku za'akai lefen Dr." "What!" Sadik ya faɗa yana yatsuna fuska. " 'yan ƙauye kuma Farhan?" Cikin mamaki Khairat tace "Farhan kuma? Ka manta sunan nawa ne?" "Ohh sorry, Khairat nake so ince, meye haɗin 'yan ƙauye da kuma kai lefe? Kai Allah ya sa dai yau wannan tsohuwar zata tafi" Khairat tace "kakar taku?" "Ita ɗin mana, tsohuwar nan jarababbiya ce ta ƙarshe wallahi, faɗan tsiya ne da ita ga takurar masifa da sa ido, ni shiyasa ko ƙauyen nan bana zuwa, dama am allergic to the water of the village, ke nifa Even iskar garin nan is irritating me, Abincinsu ma ƙyama yake bani, sam bana zuwa garin nan" "Taɓ aikuwa tace tana gidan nan har ayi bikin dr." "Kut, wallahi Farhan barin gidan nan zanyi, ina zan iya da tashin hankali da takura?" "Farhan again?" "Ohh sorry, ke nifa Farhan ce a zuciyata da kuma harshena, shiyasa nake kiranki da sunanta" Ɗan haɗe fuska Khairat tayi tace "wace kuma Farhan?" "Sirikar mother ce, ana auren dr. Se nawa da Farhan Yarinya" "Aure kuma Sadik, waze maka Aure Yanzu?" "Ke dalla ban isa auren bane, ke tashi ki ban guri ma kin sani a gaba, zanci Abinci" "To ni meye haɗina da cin Abincin ka?" "Zaki tashi ki barmin ɗaki ko sena ji miki ciwo" Ta miƙe tace "kana cewa kakarka masifaffaiya, ai kaima masifaffaen ne da be san abun arziki ba, kuma gobe ma rana ce" Share Khairat yai ya zuba Abincinsa ya fara ci. Yaci ya ƙoshi ya miƙe tsam, ya haye gadonsa ya fara chatting, tunani yake ina ma Farhan ta na da waya, da ya kirata ya ji muryarta yaji daɗi. Faruku na shiga falo, ya tarar da Inna ga Daddy da Usman duk a zaune a falon, dam be san da zuwansu ba, ya ƙarasa gaban Inna yace "Sannu da zuwa" Ta ɗaga kai ta kalleshi tace "Sannunka, ba'a ganinku se anzo inda kuke ko Faruku?" Ya ɗan shafi sumarsa yace "ba haka bane Inna, ya Hakimi yana lafiya?" "Yana lafiya, sedai yana mitar baya ganinku" "Abubuwa ne suka ɗanyi yawa amma insha Allah muna nan tafe" Inna tace "yadda ka tara wannan gemun ai kyawunta ace kaima da naka auren za'a haɗa" Daddy yace "haba Inna, guda nawa Faruk ɗin yake? Dan ya tara gemu yarone ƙarami kawai abunsu ne na yaran zamani ya tara wannan uban gemun, amma haryanzu be kammala karatu ba" "Haka dai, boko boko boko, to boko yana hana Aure ne, in dai yaro yana da yadda zeyi, ku dena yiwa 'ya'yanku kallon yara fa, zamanin nan se addu'a kawai" Ran Mother ya fara ɓaci ds Inna, a ranta tace "da yake kowa irinku ne, Aure, Aure, da yaro ya fara tasawa besan komai ba se a hau Aure, se tara 'ya'ya nan da nan mutum yabi ya lalace ya tsofe da wuri, saboda ku dai Jima'i shikaɗai mutumin ƙauye ya sani" ta ja gajeren tsaki ta bar falon. Inna tace "Ni haryanzu banga ɗaya yaron naka ba Abdullahi" Daddy yace "ina ga be dawo daga makaranta bane" "Aikuwa dai ina son in ganshi dan rabona da shi na manta" Daddy yace "a daiyi haƙuri ranki ya daɗe" "Sadik! Sadik!" Ya jiyo muryar Faruk na kiransa tun daga falo, tsaki Sadik yayi yace "sekace be san in da nake ba yake min wannan kiran daga waje" Yai banza ya cigaba da danna wayarsa. Faruk ya shigo bedroom ɗin yace "kana ji ina kiranka amma kai min banza?" Sadik yace "na amsa ba ka ji bane kawai" "Kaje Inna tazo, tana neman ka kaje ka gaisheta" Yatsuna fuska yayi yace "tana nemana kuma? Me nayi?" "Se kayi wani abun tukuna? Kajeka gaisheta" "Nifa yanzu na dawo daga school gaskiya na gaji, Yanzu ina zuwa zata fara ƙaƙalen abunda za tai faɗa a kai, dama ni ba ta sona wannan tsohuwar, kawai ka ƙyaleni" "In baka je ba, kaga ta ji daɗin hucewa akan Mother, tace ita ke sangarta ka" Tura baki Sadik yayi ya juya baya, dan karma ya cigaba da jin abunda Faruk ze faɗa. Se bayan la'asar sannan aka kai kayan lefen nan gidansu Yarinyar da Usman ze aura, iyayenta duk da kasancewa suma masu abun hannu ne, amma sunyi murna sosai sunyi appreciating kayan da aka kawowa 'yar ta su na lefe. Daga nan gurin kai kayan 'yan uwan su Daddy na ƙauye aka maida su, aka dawo da Inna da sauran ƙawayen Mother gida. Sadik kuwa be fito ba se bayan la'asar, ya fita ya silale ya bar gidan, ya tafi nasa yawon. Ɗaki aka bawa Inna ita da Nana a falon ƙasa, ɗakin ba laifi babba ne, da banɗakin sa a ciki, ga gado da katifa a ɗakin, se ƙaramar sif ta kaya. Nana nata faman taka tsantsan akan abunda za tayi, dan kar tayi abunda Inna zata mata tijara a cikin mutane, dan ita Inna ba ruwanta koba gaban waye idan tai ba dai dai ba faɗa za tai mata. Sadik kuwa Be dawo ba se dare, lokacin kowa ya kwanta, sannan ya shiga falo ya wuce Kitchen, ya ɗakko Abincin sa ya koma BQ. Ita kanta Mother ba ta ji daɗin zaman Inna a gidan nan wai se biki ba, dan sam bata son sa ido irin na Inna. Mother na ta zuba ido taga ɗan auta, amma sam auta be shigo Gidan nan ba, tasan dama ba lallai ya shigo ba saboda mutane da ke gidan. Dan haka da safe tai niyyar zuwa ta ganshi kafin ya tafi Makaranta. Nana kuwa ba ta gajiya da ƙarewa gidan nan kallo, saboda tsaruwar gidan ba ƙaramin burgeta yake ba, tana sha'awar cigaba da zagawa da ganin in da ba ta shiga ba ta gani, sedai tana tuno arangamar da su kai da Sadik tai tsaki tace "Aikin banza kawai, Allah yasa kar in kuma haɗuwa da wannan sakaran, idan na kuma ganinsa kuwa nima sena masa rashin mutunci" Gari ya fara haske, Inna tana can tana laziminta, Nana ta lallaɓa ta fito, masu aiki se kaiwa suke suna komowa, suna ƙoƙarin tsaftace gidan, Suna ta ƙoƙarin gyara komai, Mother na fitowa suka fara ƙoƙarin gaisheta, amma se wani shan ƙamshi take tana amsawa da ƙyar tana cigaba da basu umarni. Ɓangaren Daddy ta nufa, tarara ya tashi, ya kalleta yace "good morning sweetie" "Morning dear, ka tashi lafiya?" Kamar ƙaramin yaro ya ɗan ɓata fuska yace "not that fine, kin gujeni mun dena kwana tare" "Mutane na kaiwa na komowa, kawai a ganni a ɗakinka ga mahaifiyar ka a gidan nan" "Ina ruwan Inna damu, ai ita ba ruwanta damu, yakamata kije ku gaisa, ni naje na gaisheta kuma tana mitar Sadik be zo ya gaida ita ba" Mother tace "ai kasan halin ɗan naka, shifa mutane ne ba ya so, ni kaina ban ganshi ba tun jiya, yanzu nake sa ran zuwa in dubi shi ma, zan sa yazo ya gaisheta" "Ai gara yazo su gaisa, kar ranta ya ɓaci" A ranta tace "jarababbiyar tsohuwa ba, yanzu se ta samu a gaba da ɗana da surutu" amma a zahiri tace "insha Allah zan tura shi, me zan dafa maka ne?" "Komai ma kika dafa ni ci zanyi, am missing Your food, komai kika bani zanci" Tai murmushi tace "shikenan ina zuwa" Ta jiya ta fito, Nana cikin masu aikin nan su talatu ta shiga, tana tai musu surutu da tambayoyi, tace su bata ta taya su mopping, amma suka hanata. Sedai surtun nata dariya yake basu, Nana Akwai baki, amma duk da dariyar da suke Mother na fitowa, suka nutsu suka cigaba da abunda suke. Nana ta kalli Mother tace "Ina kwana" "Lafiya" Mother ta amsa da ƙyar. Ba ƙaramin haushi Nana taji ba da yadda Mother ta amsa nata gaisuwa, Nana a ranta tace "aikuwa za'a daɗe ban kuma gaisheki ba" Ta jiya ta fita harabar gidan, abun sake burgeta yayi, duk yadda yake da hadimai a gidan Hakimi, amma wannan sun sha banban. Saboda an fito da wasu daga cikin motoci ana wankewa, ga masu gyara flowers, suna basu ruwa komai gwanin ban sha'awa. Nana ta ƙarasa gurin me wanke mota tace "Dan Allah ka bani abun zuba ruwan nan in wanke motar nima" Dariya yayi ya kalleta yace "kina mace zaki wanke Mota, ai wannan aikin maza ne" "To ai iya zuba maka ruwan kawai zanyi" "A'a ba ruwana, ai ba aikin mace bane" Nana tace "to me bawa bishiyoyin nan ruwa idan nace ya ban ze bani, ai naga mata ma zasu iya yi" 'je ki tanbaye shi kiji" Ba musu ta nufi inda dattijon kewa Flowers ban ruwa, tace "dan Allah nima zanyi" Waigowa yai ya kalli Nana yace "ke jikar Inna, wannan aikin ai ba naki bane" "Kai ya akai kasan ni jikar Inna ce?" Yai dariya yace "kai ai tun kina zanin goyo nasanki, kuma gaki nan kamar ki ɗaya da ita sak" Nan ta cigaba da zuba masa surutu kamar wadda aka ƙona a ka. Faruk ne ya fito da gajeren wando da vest, da gani motsa jiki yayi yace "Baba Ilu sannu da aiki" Baba yace "yawwa Faruku" Nana a ranta tace "ikon Allah, ji wanan ƙato ba kunya ƙwauri duk a waje yana yawo a cikin gida, duk tsiraicin sa a waje" Ya kalli Nana da ta ƙura masa ido yai murmushi yace "kin tashi lafiya?" Ɗaga masa kai tayi alamar eh, yace "Yama sunan naki?" Tace "Nana" Yace "Ohh yeah, Naana exactly, weldone Naana" Yai maganar yana tafiya, ita kuwa binsa tai da ido tace "iyayi, Nanan ma baza'a faɗa yadda kowa ke faɗa ba se anyi wani iyayi, maganar ma da wani iyayi ake yinta, waisu lallai turawa' Daga ƙarshe ta koma ƙirga motocin dake harabar gidan. Mother ta shiga ɗakin Sadik, ta tarar yana saka belt ɗin sa na Uniform. Yana ganin Mother yai murmushi yace "good morning mother" "Ba zan amsa ba, yaushe rabon da kaje inda nake?" "Hmm mother kenan, kema kin san bana son taron mutanen nan, kowa sekabi kana gaishehi ana wani kallon mutum, ana surutu that's why kawai naƙi shigowa, but am really missing you" Yai maganar tare da kissing ɗin hannun Mother. Ta kalleshi tace "naji, but kasan Granny ɗinku ta zo ko?" Yatsuna fuska yayi yace "na sani" "Amma ba kaje ka gaisheta ba? So kake tazo ta sani a gaba da masifa tace ni na hanaka zuwa ka gaisheta" Cikin shagwaɓa da sangarta yace "Mother kin san fa ni matar nan ta tsaneni wallahi" "Haka nan dai zakai haƙuri kaje" "To yanzu na saka Uniform, kar in makara zanje school, idan na dawo zanje" "Yawwa Son, safe journey ka kula da kanka" Ya jinjina kai ya cigaba da shirinsa, ita kuma Mother ta fice daga ɗakin. Seda ya kammala shirinsa tsaf, ya fito Falo ya tarar Mother ta ajiye masa Abincin sa, ya zauna yai breakfast sannan ya fito dan tafiya makaranta. An fito da motar da ake kai Sadik makaranta, motar tayi fes se ƙyalli take kamar sabuwa. Tun daga nesa ya hango Nana a jikin motar, tana leƙawa tana zagaye motar tana shashshafa motar. Prince na hangota ya tunkaro inda take a fusace, "Ke meye haka! Ƙazama a wanke motar kizo kina taɓawa, wallahi kika sa min datti sekin wanke ta" Wata uwar harara tai masa tace "motar banza motar wofi, an shafa dattin, sedai ka mutu" "Ke ni kike gayawa haka? Wallahi zan tattka ki banza Mahaukaciya kawai" "Seka takanin in gani ai, kuma an shafa dattin, ta tofa miyau  a jikin motar ta zura da gudu tai cikin gidan. Sadik ya tsaya soror yana kallon motar, ba abun yabi Nana ba ya sake makara, yai ƙwafa ya buɗe motar ya shiga, ranasa a ɓace yana tunanin kalar rashin mutuncin da ze mata. Shikam Musa direban Sadik, kamar ya tuntsure da dariya, saboda abunda Nana tai masa, amma ya gimtse dariyar sa, kar yayi Sadik ya masa rashin Kunya. Sadik na zuwa makaranta ya samu guri ya tsaya a gurin Assembly, yana jin yadda su Nas suke masa Magana, amma yai shiru yaƙi kulasu. Farhan na ta leƙe ta hango abun ƙaunarta, sedai yadda ta ga fuskarsa tasan yana cikin damuwa, ransa a haɗa babu alamar fara'a sam a tare da shi. Jikinta se yai sanyi ta shiga tunanin meya sami Prince haka yai wannan mugun haɗe ran haka? Aka sallame su daga Assembly ground, suka tafi aji. Suna zuwa aji, malamin da suke da shi ya shiga ajin, dan haka abokan Sadik basu samu damar tambayar sa abunda ke damunsa ba. Har malamin ya koyar da abunda ze koyar ya fita, Prince yana tsaki lokaci zuwa lokaci, gaba ɗaya ransa a jagule yake. Taslim ce ta fara magana tace "Allah ya temaki Yarima, what's wrong with you know? You look somehow disturbed" Tsaki ya kuma yi tare da ɗan hura hanci, ya gyara zamansa. Amin yace "yeah, that's what I want ask since, kika rigani meke going ne?" Prince ya ɗan nisa sannan yace "wallahi mutane ne suka zo suka cika mana gida, harda wata mahaukaciyar yarinya, kidahuma 'yar ƙauye" Nas ya kwashe da dariya yace "kai Prince, wannan cin mutuncin fa? Ba relative ɗinka bace?" "Ni nama san wacece? Ni na manta in da nasan ta ma gaba ɗaya, kawai ganinta nai a gidan nan, wata fitsararriya 'yar ƙauye" Amin yace "kai harka kira wata 'yar ƙauye, ai budurwarka ce 'yar ƙauye" Sadik yaiwa Amin wani warning glance, ba shiri yace "Ohh am sorry i dont mean to hurt you" Sadik yace "Ai se nayi maganin yarinyar nan dan na tsane ta gaba ɗaya bana son ganinta" Taslim tace "to aini har Yanzu banji abunda tai maka ba" Nan Sadik ya basu labarin abunda Nana tai masa, daga jiya zuwa yau, sosai suka dinga dariya, hakan ya ƙara bawa Prince haushi, dan haka ya tashi ya bar ajin. Ajin su Farhan ya tafi, sedai suka haɗu a hanya, ya zuba mata idanunsa seda ta ƙaraso in da yake sannan ta tsaya, tare da sunkuyar da kanta. "Lovely meyasa ba ki zo ajinmu ba yau?" "Na ganka ɗazu a gurin assembly kamar ranka a ɓace, shiyasa ban zo ba" "Amma Farhan ki ganni a cikin damuwa amma ki ƙi zuwa in da nake, baki damu da halin da nake ciki ba kenan ko?" "A'a ba haka bane, naga idan kana fushi baka son aje in da kake ne" "Kuma se akace miki hadda ke? Da kinzo da tuni na manta da abunda ya faru, kin barni wancan Nasir ɗin sun sani a gaba suna sake bani haushi, dan dai ban biye musu bane" Farhan tace "am sorry, kayi haƙuri dan Allah" Yai murmushi yace "bakomai, ai matata bata laifi" Jin maganar tasa tayi wata uwar gundumemiya, wai matarsa ba ko kunya, shi baya jin kunyar wani yaji yana faɗar irin wannan maganganun sam. Suka jera suka tafi har ajinsu Farhan, a can ya zauna suka dinga hira, yana bata labarin kayan da aka kaiwa yayansa na lefe yace "ji nai kamar in ƙwace kayan nan a kai gidanku, ace na aurenmu ne Ni da ke Farhan" Shiruu tai ba tace Komai ba, kuma ba ta ɗago idonta ba. "Farhan, wai meyasa a duk lokacin da nai miki irin wannan zancen kike yin shiru ne, ko dai ba kya sona ne?" Ta girgiza masa kai alamar a'a. "To meyasa ba kya son in miki Wannan zancen? Tai shiru ba tace komai ba, ya gyara zama yace "Look Farhan, ina da kuɗin da zan iya yin Aure, kuma wallahi ni dagaske nake sonki Farhan, dan Allah ki dena doubting a kaina Please" Ta sake jinjina masa kai yace "Yawwa,  zaki ci wani abun ne?" Tace "A'a" Ya zira hannu a aljihunsa ya ɗakko dubu biyu ya ajiye mata. Zare ido tayi za tai Magana amma ya haɗe rai yace "shhhh" ya juya ya fita ta bi bayansa da kallo. A varrender ajinsu Farhan, ya haɗu da Sir Nazir, Nazir ya tsaya ya bishi da ido, Sadik ya haɗe rai sosai, ko kallon inda Nazir yake be ba ya wuce. Tunani Farhan ta shiga yi akan ya za tai da wannan kuɗin da ya bata? Ba tai aune ba taji mutum a kanta, tana ɗaga ido ta ga Sir Nazir, yace "wato ba ki rabu da wannan yarn ba ko?" Ɗan tura baki tai, ta sunkuyar da kai. "Wai ke dan Allah da ma haka kike da taurin kai ne? Waima meyake gaya miki da ya sa kika liƙe masa haka? Ko kuma me kuke yi da yasa kullum se yazo in da kike?" Ƙin ɗago kanta tayi da ga sunkuyar war da tayi. "Kije ki cigaba da biye masa karki fasa, nan gaba idan ya gama morar ki, ze watsar da ke ne, a lokacin ne zaki nadama mara amfani, wannan yaron sam ba tarbiyya ce da shi ba, ɓata miki lokaci ze a banza" Babban abunda yake ɓatawa Farhan rai be wuce duk wanda suke soyayya a makarantar nan ita kadai ya sawa  ido ba, kuma abun takaicin be wuce yadda yake dizgata a gaban kowa ba, saboda Prince. Nazir na fita Yasmeen ta ja tsaki tace "nifa wannan mutumin ya fara ɓata min rai akan abunda yake wa Farhan, ya fiye sa ido da takura wallahi" Lilly tace "ke bake kaɗai ba nima haka wallahi, ni yana burgeni yadda ya iya dressing ga shi kyakykyawa, sedai ya fiye shishshsigi, ni da ni yakewa haka wallahi da tuni nayi maganinsa dan ba zan ɗauka ba sam" Ita dai Farhan ba tace musu komai ba, can Yasmeen tace "ku akwai labari fa" Lilly tace "labarta mana muna jinki" "Wallahi Sister na naji suna hirar Wani book, so romantic ina son in samo Book ɗin nan" Hasina tace "haba dan Allah ki ɗakko mana mu karanta mana" Yasmeen tace "dalla a wayarta ne fa, kuma ni ban san sunan littafin ba, amma yadda naji suna hirar littafin na manyan kai ne" Lilly tace "ke dalla muma manyan kan ne, ki samo mana kawai" "Ku bari zan ɗau wayar tata in duba mana" Haseena tace "saura ki shanya mu, kiƙi nemo mana" "Dalla ni na gaya muku fa, zan nemo mana shi" Suka cigaba da taɗin su. Kamar wadda ƙwai ya fashewa a ciki, haka Farhan ta koma gida, zuciyarta fal tunanin Prince, dan lokacin da aka tashi daga school, akwai Malami a ajinsu Prince, dan haka ta samu ta tafi gida. A gidan ma kasa sukuni tayi, tana son samun wanda zata tatauna Maganar Prince da shi, amma babu ita ba me son yawan Magana bace, ba ta damu da yawan surutu ba, dan haka ko ƙawaye ba ta da su sedai 'yan makarantar su, suma ɗin ba kula su take ba, Ga mahaifiyarta ba ta sakar mata fuska sam, dan haka ba yadda za'ai ta tunkare ta da Maganar Sadik. Tana son tabattar da waye me gaskiya tsakanin Prince da Nazir, dagaske RUƊIN ƘURUCIYA ce soyayyar da suke? Ko kuma soyayyar da Prince ke nuna mata gaskiya ce? Gaba ɗaya ta rasa wane tunani ma Yakamata tayi, ta buɗe tsakiyar litattafan ta, ta saka 2k ɗin da Sadik ya bata, tana sake jin wani irin shauƙi yana fizgarta akan Sadik ɗin. Yauma a gajiye Sadik ɗin ya koma gida, ya kwaso gajiya matuƙa idonsa har lunshewa yake saboda gajiya, gashi yau ne ranar da ustaz ɗin dake masa lesson ze zo. Ya canza kaya kenan, sega kiran Mother a wayarsa, yana ɗaga wayar tace "Sadik wato seka janyo min zagi agurin wannan tsohuwar ko? Ba zaka zo ka gaisheta ba se raina ya ɓaci kenan?" Seda ya tura baki Sannan yace "Yi haƙuri gani nan" Ya ajiye wayar yana cigaba da kumbura baki. Ya fito ya nufi cikin gidan yana tura baki, ya haɗu da Khairat. Ya kalleta yace "ke wai kullum sekin zo mana gida ne?" "Lallai daɗinta ma muma muna da gidan ai" Murmushi yai ya janyota jikinsa yace "Sorry Sisto na, wasa nake miki fa" Nana dake hango su ta window ta buɗe baki tace "taɓ ga 'yan iska, Allah yasa Inna ta gani, kut ya taɓa ta taɓɗijan, dama wannan yai kalar 'yan iska" Inna na zaune a falon Sadik ya shigo, tun da ya shigo Inna ta ƙurawa Sadik ido, cikin majestic walk ɗinsa ya ƙaraso, ya ɗan durƙusa yace "Sannu ina wuni" Inna ko ƙyafta idonta ba tayi ta kafe shi da ido, dan seda ya fara tsarguwa tace "Sannu Abubakar" Ya shafi sumar kansa yace "yawaa an zo Lafiya?" "Ban sani ba, tun jiya ina gidan duk 'yan uwanka sun zo sun gaida ni amma banda kai, kuma ance min kana nan" "I was little bit busy that's why" "Ni ba gane wannan Yaren nasaran nake ba ai, wannan wane irin aski ne haka a kanka?" Ya shafi kan yace "suma ce kawai" "Wannan uban gashin kamar ɗan daudu? Kai ko damunka baya yi, ni yaushe ka girma har ka tara wannan gashin haka ma? Rabona da kai yafi shekaru uku, uwarku ba zata zo ba kuma ba zaku zo in damuke ba ko?" Mother tace "A'a ni bana hanansu zuwa, ya za'ai in hanasu Zuwa inda kuke?" "Idan ba ki hana su zuwa ba ai baki koya musu zuwa ba ko?" Sadik yace "wannan garin me uban sauro ga ruwan garin ɓata ciki yake ya za'ai mutum yazo" Inna tace "ba shakka ba yadda za'ai a zo kam, be kamata azo ba kar ruwan garin ya kashe mutum" Inna tai maganar cikin gatse. Sadik ya sake cusa baki, Mother tana ta masa signing akan ya kintsa bakinsa. Inna tace "kafin in bar garin nan ina son a rate wannan sumar ta kanka tunda kai ba mace bane, kuma ba kitso za kai ba" "Inna wanan sunar na asketa ai ba kanta, wallahi kuɗin da nake kashe mata yafi kuɗin dokunan gidan Hakimi" "Lallai kam naga alama, tashi kaje Allah ya shirya" Ya miƙe ya juya abunsa ze fita, sedai sukai karo da Nana tana ƙoƙarin shigowa falon, ta zuba masa miya a riga. Ya kalleta a Mugun fusace yace "ke! Wace irin dabba ce ke? Baki da hankali ne mahaukaciyar ina ce ke?" "Kar ka sake cemin Mahaukaciya, kai baka gani ne, kana tafe kana kallon sama" "Wai dan Allah wannan banzar 'yar waye, daga ina take? Waya kawo mana Mahaukaciya gida, wallahi na tsani ganin Yarinyar nan" "To kasheni ka huta, fitsararre" Inna na ƙoƙarin tashi ta ƙarasa inda suke, ya shaƙo hijjabin Nana! Don't Miss this book wooo, akwai damalamalin cakwakiya 😂😂😂 Domin Sharhi gyara Ko shawara Ayshercool 07063065680. [6/4, 4:21 PM] Jakadiyar Arewa:     🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ RUƊIN ƘURUCIYA PERFECT WRITERS ASSOCIATION (WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS) https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ P. W. A *Story and written by* AISHA ADAM (AYSHERCOOL) Writer of WATA KISSAR..(Sai mata) ABDUL JALAL AƘIDATA (paid book) WUTA A MASAƘA NOW RUƊIN ƘURUCIYA (paid book) _Labarin RUƊIN ƘURUCIYA, na iya zuwa da wani salo, wanda baku saba ganinsa a rubutuna ba, hakan ya biyo bayan akan abunda aka gina labarin, wani abun ze ɓoyu wani Abun baze ɓoyu ba sakamakon labari ne akan teenegers, yara masu tashen Balaga, but hakan ba ya na nufin na sauka daga kan tsarin yadda nake Rubutu bane, ƙofata a buɗe take dan karɓar ƙorafi, gayra ko shawara_ ⚠️⚠️⚠️ƘIRƘIRARREN LABARI NE, BAN YADDA A JUYAMIN SHI TA KOWACE SIGA BA SEDA IZININA ❌❌‼️                             11_12 Tuni Sadik ya shaƙe Nana da hijjabinta, dan da ƙyar take iya numfashi ma, ta ware maƙogwaro ta dinga rafsa uban ihu. Da hanzari Inna ta yo kansu, Mother ma ta taho da Sauri tana faɗin "Sadik meye haka? Baka da hankali ne?" Inna tace "saketa kar ka kashe ta" Zuciyar Sadik se tafasa take saboda takaici, ji yake kamar ya cigaba da shaƙeta seta suma tukuna. Da ƙyar Sadik ya saki Nana, Inna tace "ba shakka ka kyauta, 'yar uwakka ka shaƙe haka kake cewa ka tsaneta, jinin ka ce fa kuma dan rashin kunya da rashin ta ido, a gaban nawa kake iƙrarin ka tsani 'yar uwaka, lallai ga illar rashin zumunci ai" Saroro Sadik yai, se yanzu ya tuna in da yasan Nana ma, shi tun asali Nana ba tai masa ba, lokacin da ya santa tana yarinya sosai, tun tasowarta idan suka je ƙauye idan ya ganta haushi take bashi, mussaman yadda take shagwaɓaɓɓiya, ga tsiwar tsiya ga shegen ci, kuma ba'a isa a taɓata ba saboda son da Hakimi yake mata, amma yayi mamakin ganin girman da tai, tayi tsawo sedai halinta yana nan. Mother tace "dan Allah kiyi haƙuri, wallahi Halin Sadik se a hankali, in kika bibiya be ganeta bane shiyasa" "Eh ai dama baze ganeta ba, tunda tana ƙauye shikuma ba zuwa ƙauye yake ba, amma tabbas da dangin ki ce ba yadda za'ai yace be santa ba, yayi kyau" Mother taja hannun Sadik suka fice daga falon. Inna tace "ke kuma dan ubanki in rashin kunya abun yi ce gobe ma ki sake, se da nace ba zan taho da ke ba amma ya dage in taho da ke, kije ki cigaba da neman Magana da rashin nutsuwa ya illata ki a banza a wofi kan mu bar gidan nan" Gefe Nana ta koma ta zauna ta na kuka, dan taji shaƙar da Sadik yai mata ba kaɗan ba. Mother kuwa suna fitowa da Sadik tace  "Sadik meyasa ba ka gudun magana ne? Allah kaɗai yasan iya ɓacin ran da zaka jamin saboda abun da ka aikata, meyasa kake da baƙar zuciya ne kamar haka?" Cikin takaici Sadik yace "Mother, kalli jikina fa kalli yadda ta ɓatani da miya, tun jiya na ga Yarinyar nan, take zagina ni na manta ma in da na taɓa ganinta se yanzu, gaba ɗayan ta Mahaukaciya ce" Mother tace "Koma mece ce Ni dai ka lallaɓa mu rabu lafiya, karka jamin magana" Sadik be kuma cewa Komai ba, ya wuce ya nufi ɓangaren su kamar ya fashe da kuka dan takaici. Inna kuwa sosai ta cigaba da yiwa Nana faɗa, akan rashin nutsuwa da rashin zama guri ɗaya da ba tayi. Inna tai faɗanta son ranta, Nana kuma ta ƙule Sosai ta ƙuduri aniyar se ta yiwa Sadik rashin mutunci ta rama abun da yai mata. Khairat kuwa da akan idonta komai ya faru, ta fi jin haushin Nana, dan ta fuskanci Nanan ba dai rawar kai ba, ga iyayin tsiya. Nana tana nan a gefen ƙafafuwan Inna, tai zuru tana kallon tv amma ba tv take kallo ba, tana son ta fita ta sha iska, amma tasan tana fita Inna zata zageta tsaf, koma tace zata daketa. Har la'asar suna nan a Falo, Alhaji Abdullahi ya fito daga sashen sa, ya fito falon, yazo ya samun Inna cikin girmamawa yace "sannu da hutawa Inna" "Yawwa sannunka" Ya kalli Nana da tai tsuruu a bayan Inna yace "Mamana, ya na ganki a haka? Na ganki wani iri" Inna tace "eh nina hanata fita" 'amma Inna meyasa, ko bari tai walwala mana gidansu ne fa nan" "A'a ba dai gidan su ba, a gabana ba kunya ɗan autanka ya shaƙeta, wai shi be ma santa ba, Wannan rashin zumunci har ina Abdullahi, ace  'ya'yanka basu san ƙanwarsu ba, ko bayan ran mu wa take da su ban da kai da iyalinka?" Mother kuwa wani takaici ne ya ƙuleta, anyi abun nan ta bawa Inna haƙuri amma ta zaunar da Daddy tana maida yadda akayi. Daddy yace "subhanallah, Sadik ɗin ne yace be santa ba?" "Zan masa ƙarya ne? Haka yace be santa ba, amma na tabbatar da a dangin mahaifiyar sa take baze ce be santa ba, gaskiya Abdullahi yana da kyau ka sake sa ido sosai akan iyalinka, wannan halin na Sadik sam be min ba, kun sangarta shi da yawa ba shi da ɗa'a sam" "Ayi haƙuri Inna, insha Allah za'a gyara" Ya kalli Nana yace "Amma ayimin afuwa, an takura Mamana da yawa, bari mu ɗan fita tare da ita" Inna tace "sekun dawo" Yai murmushi yace "taso Mamana" Da murna Nana ta tashi, Daddy ya riƙo hannunta, suka fito harabar gidan. "Mamana ajinki nawa ne?" Nana tace "Ajina shida, daga wannan hutun zan shiga Sakandire" "Masha Allah, Yarinya ta girma, Allah ya temaka" "Ameen" ta amsa tana kalle kallenta. Alhaji Abdullahi ya ɗakko wayarsa ya nemo lambar Sadik. Sadik na ɗagawa Daddy yace "kana ina ne?" Sadik yace "Ina BQ" "Fito waje ina son ganinka" Mintuna kaɗan sega Sadik na tahowa, sedai yana hango Nana a kusa da Daddy ya haɗe rai hadda hura hanci. Ya ƙaraso yace "Daddy gani" "Sadik, wai baka san Nana ba?" Sadik ya galla mata harara yace "Eh amma na tuno ta daga baya" "A gaskiya banji daɗin abunda ya faru ba, Inna ta yi min complain da kai Sadik, gaskiya ban ji daɗi ba" "Daddy nifa ba abunda nayi, kawai kasan dama ni ta tsane ni, ba ta sona kawai, tana son Dr. Da Faruk amma ni ta tsaneni kuma wannan 'yar ai itama ba ta da kunya" Daddy yace "ba wannan na kiraka ka gayamin ba, na kiraka ne in ƙara jadadda maka, Nana ƙanwarka ce kamar Yadda Khairat take ƙanwar ka, bana son sake jin kunyi rigima ko ka gayamata wani abu mara daɗi ka ji ko?" Sadik fuska a cunkushe ya jinjina kai, sedai yana ɗago kai Nana tai masa gwalo, sannan a ɗan sanyaye tace "kuma ma da ya shaƙemin wuyan hijjabi na, seda na dena numfashi, wuyana ma Ni yanzu ciwo yake min, da ƙyar nake haɗiye miyau" Daddy yace "Ya Salam, kiyi haƙuri ze dena insha Allah, dan Allah ku dena faɗa 'yan uwa ne ku" Sadik A ransa yace "Allah ya kiyaye wannan me kama da cartoon ɗin ta zama 'yar uwata, shegen bakinta kamar ramin tsutsa' Daddy yace "bari mu fita shan icecream tare, ku ƙara sanin juna a dena faɗa" Sadik yace "Please Daddy, i scheduled to be with my friends by 5:00pm, if you don't mind i wanna be with them" "We must go together!" Shine amsar da Daddy ya bashi. Sadik kamar yai bindiga, haka yasa direba ya fito da mota suka fita tare, Sadik da Nana a baya, Daddy a gaban mota. Suna tafe a hanya da ya waigo ya kalli Farhan, se wani baƙin ciki ya mamaye zuciyarsa, Nana kuma suna haɗa ido zata murguɗa masa baki hadda fari da ido. Ji yake tamkar ya turata waje ta window kowa ma ya huta. Daddy yace "Mamana, idan kin girma me kike son zama ne?" Seda Nana tai wani ƙasaitaccen murmushi ta ɗanyi fari da ido sannan tace "Ina son in zama 'yar jarida, in din ga aiki a gidan Radio ina karanta labarai, ko in dinga hira da mutane, in dinga karanta labarai da turanci" Daddy yace "wow masha Allah, Allah ya cika miki burin ki Mamana, da kin kammala sakandare insha Allah za'a samo tsadajjiyar jami'a kije kiyi karatun insha Allah" Murmushi tayi tace "Kasan a wace gidan radion nake son in dinga karanta labaran?" Yace "A'a" "Ina wannan radion da Hakimi yake kaiwa yana ji da Asuba? Da kuma da rana rana haka" "BBC ko America?" Abba ya tambayeta yana murmushi, dan ya san Hakimi da son jin BBC. Tace "Yawwa BBC, kasan da Asuba suke hira da hausa, idan haka rana ta ɗanyi idan aka kunna sekaji suna turancin turawa, to irin wannan nake son nima in dingayi, in dinga labarai da turanci ina maƙale muryata" Sadik ya ja wani uban tsaki, dan gaba ɗaya Nana ba ta gajiya da surutu, bakinta ko ciwo ba ya yi, tai ta zuba kamar wadda aka kunnawa ashana a ka. A hankali Sadik yace "sedai aikin gidan radion jakai shi zaki, ba dai na masu hankali ba" "Ai kai ne jakin" ta faɗa tana hararar Sadik. Sadik yace "ke da wa kike?" "Da kai nake, waye yace kace min Jaka?" "Nike nace miki jakar?" Daddy yace "A'a ya faɗa kuma a gabana? Ba yanzu na gama yi muku nasiha ba akan faɗan nan?" Nana tace "cemin yai Jaka" Sadik a buɗe baki yana kallon Nana, wato bayan hauka hadda makirci ma Nana ta iya, in ba haka ba yauhse yace mata Jaka. Daddy yai ta musu faɗa, yayin da Nana ta cigaba da gallawa Prince harara hadda murguɗa baki. Suka je wani babban store, Daddy ya saiwa Nana kayan ciye ciye, sannan suka nufi komawa gida, Sadik be kuma cewa komai ba, Nana ne da Daddy suke ta hirar su tana masa shirme kala kala yana biye mata. Alhaji Abdullahi yana da son yara sosai, amma baya sha'awar ya tara su da yawa, sedai duk in da ya ga yaro ƙarami yana jansa a jiki ya kyautata masa. Se daf da magariba sukaje gida, Nana ta rungumi kayan da aka siyo mata ta kasa da gudu. Masaukin su ta nufa kasancewar ba ta ga Inna a falo ba, tun daga waje take ƙwalawa Innar kira, sedai tana shiga ɗakin kallon da Innar tai mata yasa ta nutsu. "Gudun me kike yi haka?" "Bakomai" "Ban hanaki wannan guje gujen ba, a Wannan sakarcin naki kika zubawa wancan yaron miya a jiki, shine yanzu ma kike maimaitawa ko? Bari in sa a kira Hakimin ya turo a ɗauke ki a maida ke gida" "Dan girman Allah kiyi haƙuri, na dena ba zan ƙara ba" Inna tace "da dai halinki ne ban sani ba, kiran me kike min?" Nana tace "kinga abunda aka saimin" Inna tace "kince masa kin gode dai ko?" "Eh na masa godiya" "To amma dai ki dena wannan guje gujen" "To na dena insha Allah" Da magariba ma Daddy yasa Sadik a gaba sukaje masallaci su kai salla, suna tafe yana masa Nasiha akan haƙuri da son zumunci, yai masa faɗa sosai yace masa Inna ba tsanarsa tai ba, amma ya dinga zuwa yana gaida Inna. Shi dai Sadik be ce komai ba, yai shiru yana sauraren Daddy, amma shi duk wani abu da ze haɗa shi da Inna ba so yake ba, saboda ta fiye ƙaƙalen abun da za tai faɗa. Da safe ya shirya tsaf ze tafi Makaranta, ya tuna kashedin Daddy, ɗan gajeren tsaki yai ya ɗau jakarsa ya kai mota, sannan ya tafi cikin gida. Ɗakin Mother ya fara zuwa, yaje ya gaisheta, ya zauna yai breakfast sannan ya fito, ya nufi ɗakin Inna. Yana zuwa ba Sallama ya shiga ɗakin, ya tarar Inna tana lazimi, Nana kuma nata bacci akan gado. "Ina kwana" shine abunda ya faɗa a taƙaice. Inna ta ƙare masa kallo sannan tace "lafiya ƙalau"  tana amsawa ya  miƙe ya bar ɗakin ba tare da ya kuma cewa komai ba. Yau ya makara sosai a makaranta, dan har an kammala assembly sannan yaje school ɗin, miƙewa yai da nufin ya tafi ajinsu, yaji an masa tsawa daga bayansa. Tsayawa yai ya waiwaya yaga wane ke masa wannan ihun haka. "Why are you always coming late ne?" Sadik ya watsa masa harar ya gyara jakarsa, ya cigaba da bin Nazir da kallon banza. "Am i talking to robot? Ba Magana nake maka ba?" "To me kake so ince maka, nifa gaskiya kana takuramin, ina ruwanka dani ka bi ka samun ido ka addabeni, kamar nikaɗai ne ɗalibi a makarantar nan, gaskiya bana son haka ka fita a sabgata na gaya maka" "Ni kake gayawa haka?" "To waye kai da baza'a gaya maka ba?" Yana gama maganar ya nufi ajinsu yana tsaki. Nazir yabi Sadik da kallo yana jinjina rashin tarbiyya na ɗaliban makarantar. Yana zuwa ajin nasu ya tarar ba malami a ajin, kowa se harkar gabansa yake, gaban aji kuwa Nas ne da wata 'yar SS3 suke wani dancing challenge ana musu video, se ihu ake ana musu tafi. Sadik ya ajiye jakarsa ya zauna, yana kallon su Nas, Nas ya kalleshi yace "Prince, ranar bikin Brother ɗinka Akwai casu wallahi, gaskiya yakamata ka shirya mana special party iya na 'yan school ɗin nan" Sadik yai murmushi yace "nayi wannan tunanin nima, dole ma ayi special party da za'a gyagije, kan kuzo Dinner bikin" Amin yace "idan hakane kuwa, na ga tallan wasu wanduna, Yakamata muyi order ɗinsu latest crazy jeans masu kyan gaske" Sadik yace "nunamin in gansu" Nan suka zauna, Amin ya nuna musu wandunan, Sadik yace "gaskiya sunyi kyau, ni blue ɗin nan nake so ɗan 15k ɗin nan, ku kuma zan muku order na 10k ɗin nan kuyi ankon su" Shewa suka ɗauka a gurin, Taslim tace "omo What do you mean? Mu ɗin kuma fa" Sadik yace "in dai zaku sa se ayi order da ku" Meena tace "mw ze hana? A siya damu" "Shikenan duk wanda ze je partyn, a saka order da shi, zan sa a bugo riguna polo, amma kowa siyan riga ze dan ubanku" Dariya su kai, Nas yace "nasan iya wuya ba tafi  5k ba, na saiwa mata goma riguna, amma fa se zafafa wanda suka cika mata, wadda idan ta saka kayan nan za'a ga kaya" Taslim ta buga wani uban ihu tace "yeee ina cikin wanda za'a saiwa riga ko ba'a so, dan na kai mace wallahi" Nas yace "ba ƙarya muma mun seda ai" Shewarsu suka cigaba da yi, suna ihu, suna cigaba da tsara rashin jin da za suyi a gurin party. Knocking ɗin ƙofar ajin akayi, Sannan aka shigo. Director ne ya shigo, shida wasu 'yan bautar ƙasa, maza uku mata biyu, sedai matan kiristoci ne, dan kansu ya sha ƙarin gashi. Tsit sukayi suka gayara zamansu, Director yace "my dearest And beloved student, can't you greet?" Seda yai Maganar, sannan suka gaishe su gaba ɗaya. Nan ya gabatar musu da 'yan bautar ƙasar nan, a matsayin sababbin malamai. Nan suka gabatar da kansu ɗaya bayan ɗaya ga 'yan ajin, bayan sun gama gabatar da kan nasu ne, Director da kansa ya dinga gabatar musu da ɗaliban da kansa, kowanne ya gabatar da shi da matsayin mahaifinsa. Seda suka kammala yai musu jawabin da ze musu, akan su bawa malaman haɗin kai, dan samun ilimin da ya dace. Meena ce cikin harshen turanci da iyayi, ta wakilci 'yan ajin ta yi musu barka da zuwa, da tabattar musu da za su basu Dukkan haɗin kan da suke buƙata, dan gudanar da aikinsu. Wani fari daga cikinsu wanda ya gabatar da kansa a matsayin Nura daga Kogi state, shima cikin harshen turanci ya wakilci 'yan uwansa, yai musu godiya da irin karɓar da a kai musu. Daga nan kuma suka bi Director suka fita suka nufi wani ajin. Suna fita Meena tai murmushi tace "Subhanallah" Taslim tace "ke lafiyarki kuwa?" Meena tai murmushi tace "Taslim kinga abunda na gani kuwa?" "Me kika gani?" "Wallahi I fall for that guy" "Wane guy kuma?" Taslim tai maganar tana kallon Meena. "That fair and tall Man, Nura looking very beautiful and energetic, wallahi yai min" "Ke bana son iskancin banza fa" "Ke wallahi ba ƙarya nake ba, before nafi ganin kyan corper Nazir, Amma yanzu naga abunda zuciyata ke so wallahi" Taslim tace "Nifa daɗina da ke 'yar bala'i ce ke, ki rage leƙe leƙe wallahi" "Ba wani leƙe leƙe ƙyaleni kawai" Nasir kuwa cigaba da batun bikin yayan Sadik sukayi. Yau Farhan ba ta zo gurin sa ba, dan haka da kansa ya kuma tafiya nemanta, sedai ya tarar ta kifa kanta akan benci, kamar me bacci. Ƙarasawa yai a hankali, ya ɗagota da ga kwanciyar da tayi. Hakan ya firgita ta sosai, ta shiga rarraba ido amma ba tace komai ba, yace "Am sorry na miki laifi, na firgita ki gashi na taɓa ki ko?" Ba ta masa ba, ya samu guri ya zauna daf da ita yace "Honey meke damunki ne? Naga idonki yai ja" Ji tai kamar Sadik ya taɓo mata inda yake mata ƙaiƙayi, tana da damuwa But she has no one to discuss with, she's developing some changes in her breast, suna mata zafi wasu lokutan, sedai ta kasa ganewa, is it the normal stage of puberty, ko kuma wata matsala ce daban, dan tana jin ana wayar da kai akan breast cancer, dan recently anyi taro a makarantar, na wayarwa da mata kai, akan ciwon sanƙaran mama, amma ita ta kasa gane a wani hali take? Gashi ba yadda za'ai taiwa Ummanta zancen, gashi ba wanda za ta iya gayawa damuwarta, a yanzu haka duk da ta na kwana guri ɗaya da Ummanta ta tashi, amma Babu wanda take da kusanci da shi a yanzu kamar Sadik, sedai shima ɗin Maganar tayi matuƙar nauyin da ba zata iya tambayarsa ba. "Lafiya naga kin yi shiru kina kallona? What's wrong ki gayamin please" Ajiyar zuciya tayi, cikin sassanyar muryarta tace "bakomai fa" Ya kwaikwayeta yace "ban yadda ba gaskiya" Hakan ya bata dariya da seda tai murmushi, yace "oya gayamin ina jinki" "Dagaske nake bakomai, bacci nake ji ne" 'ba kya bacci sosai ne a gida?" "Eh ina yin karatu da daddare" "Wow that's very good ai, amma ki dinga rangwantawa kanki kinji Hubby na, bikin yaya na ya kusa, za'ayi events da aka shirya a gidan mu, amma akwai party da zan organising, so akwai kalar outpit ɗin da za'a saka, ayi order dake zaki saka?" "A'a baza'a barni ba a gidanmu" "Ok ba damuwa, nasan dama ba lallai a barki b, but I just decided to tell you ne, amma dai ko sau ɗaya zaki zo ko?" "Eh Insha Allah" "Yawwa my wife" Sunkuyar da kai tayi ƙasa, dama yasan hakan ne ze faru, dan wannan kalaman nasa nauyi suke mata. "Farhan" ya kira sunan ta. "Na'am" ta amsa. "Next week zan karɓo exams card ɗina, na kusa Barin makarantar nan Insha Allah" Ai da sauri ta ɗago ta kalli Sadik tace "dan Allah dagaske ka ke?" "Am serious, zanyi Waec ne in kammala karatuna akan lokaci" Take jikin Farhan yai wani irin sanyi, ta kasa cewa uffan se dai damuwa ta bayyana ƙarara ta mamaye fuskarta. "Farhan" ya kira sunanta. A sanyaye ta kalle shi, yace "kin san meyasa nai haka? Duk cikin planing ɗina ne na in mallake ki, dan Allah Farhan kar ki kalli hakan da wata fuska daban, i really love you wlh, duk saboda nake wannan fighting ɗin, kimin addu'a samun nasara, bari in tafi aji kar Wannan jarababben mutumin yazo yai min masifa" Ya tashi ya kalleta yace "I love You baby" ya kashe mata ido ɗaya ya juya ya fita. Ai yana fita ta bawa hawayen da take ta kokawa da su damar zubowa, ta kifa kanta kawai ta fara kuka ƙasa ƙasa. "Yanzu idan Prince ya dena zuwa Makarantar nan ya za tayi, a duk ranar da ba ta ganshi ba, tana shiga mummunar damuwa, se gashi ze bar makarantar gaba ɗaya, nan hawaye suka cigaba da zarya a kuncinta, ta sa hanky tana gogewa, tun a lokacin taji ta fara kewar masoyin nata, take ta manta da damuwar ta ta farko dake damunta. Shi kansa Sadik tunda ya gaya mata yaga damuwa a fuskarsa, ya shiga damuwa shima, take yaji wani irin tausayinta ya kamashi sosai, shikansa ya san zeyi missing ɗinta, sedai barinsa makarantar ba yana nufin ya bar Farhan ba, akwai yiwuwar ya fara neman Hanyar cinma burinsa, na aurar wadda yake so a Wannan shekarun. "Idan ka aureta Yanzu tata rayuwar fa? Karatun ta fa?" Wata zuciyar ta tambayeshi. 'ta ƙarasa a gidana' ya bawa kansa amsa. Da gudu ta sheƙo ta kan varrender, tana ƙoƙarin ƙarasawa ajinsu "Lilly! Lilly" tsayawa Lilly tayi tana kallon Sir Nazir dake ta ƙwala mata kira kamar mafarauci. "Why are you running like this? Where is your jacket?" Ta kalli jikinta daga ita se inner shirt, da skirt ɗin ta iya gwiwa, ta cire jacket ɗin ta ajiye a aji, ta kalleshi tace "tana aji" "Meyasa kike yawo a haka? Baki san kin fara girma ba, kuma kina gudu a cikin yara haka? Ga hijjabin ki ƙarami, Why are you exhibiting childish behavior, don't you know you are at your Adolescents period, you have to maintain your body?" A ranta tace "ji ɗan iska, seka gayamin a Adolescents period nake, ai nima na sani" Ta tura baki cike da sangarta. Yace "idan na kuma ganin kin kuma cire jacket ɗinki kina gudu haka, sena zane ki, wuce ki ban guri" Tafiya tayi tana yatsuna fuska. Tana zuwa Ajinsu tace "hmm ƙawayen amana kun san abunda ya faru kuwa?" Haseena tace "ya za'ai mu sani se kin faɗa" Lilly tace "mhmm wannan sir Nazir ɗin ne na taho da gudu ya wani tsaida ni, wai meyasa nake yawo ba jacket nake gudu, wai ban san na fara girma bane na shiga Adolescents period, kuji min ɗan air mutum" Shewa suka yi Haseena tace "Ya ƙyasa ne yaseen, shine ya gaza shiruu seda ya tanka, ya tsaida ke ne kawai dan kawai ya sake kalla sosai" Ihu suka saka gaba ɗaya, tai wani juya tai girgiza tace "gani ba taɓawa ba asarar ido, nan gani nam bari ɗumamen mayya, kuma wallahi yawo ba jacket yanzu na fara, ke ni fa na kusa dena saka wannan ɗan hijjabin ma, haka zan dinga yawo, mutum ya kalla ko kuma ya runtse idonsa" Yasmin tace "to Allah ya temake ka abubuwa sun fara fitowa ace ba zakai gayu da abunka ba, wani abun ma se munje Final year lokacin sun gama fitowa, lokacin ne zega yadda ake abu, yadda zamu addabi makarantar nan, ai ya gani ya kasa shiru shine ya tanka miki, sun tsole masa ido" Lilly tace "aikuwa in hakane ya shiga tara mutumin nan, dan sena ganshi ma zan dinga kasawa da gud" Yasmin tace "ai base kinyi gudu ba, kya yiwa kan ki ɓarna ai, kina tafe kina ɗan bada style ma ya isa, ban gaya muku ba ma, na fa samo mana littafin nan, ku kunji abubuwa a ciki kuwa" Haseena tace "dan Allah dagaske ko da wasa?" "Wallahi dagaske nake, ke kunga yadda aka fayyace komai ban dai karanta ba, page ɗaya kawai na karanta, amma naji sena zo da wayata mu karanta tare, kai akwai tafasassun abubuwa a littafin nan" Lilly tace "shegiyar kaya, ai a kawo mana littafin nan, muji abubuwa kawai" Su kaita shewa, ita kam sam Farhan hankalinta baya kansu, hankalinta kacokan yana kan maganar da sukayi da Prince ɗinta. Shikansa Prince har aka tashi jikinsa a sanyaye yake, yaje ƙofar makarantar ya tsaya yana jiran fitowar Farhan. Aikuwa ya hangota ta fito daga cikin makarantar, idanunta sunyi jawur sosai, tana tafiya a hankali, daga inda yake tsaye yake kallonta, kullum ƙara girma take tana kyau abunta, sheɗan ne ya fara ƙawata masa ita, da ɗarsuwar wani abu daban a ransa, take yace "Subhanallah" ya dawo hayyacinsa. Tana ɗaga ido sukai ido huɗu da shi, murmushin dole tai masa, yace "ke muke jira taho mu tafi gida" "A'a zan tafi ai" "Bana son gaddama fa" Ba yadda ta iya haka ta bishi ta shiga motar, suna tafiya yace "Anya ba kuka ki kai ba, naga idonki ya ƙara ja" "Ba kuka nai ba, dama ina ciwon ido wani lokacin" "Ciwon ido, lallai ma ashe makauniya ce matar tawa, gaskiya sena rage sadakin da zan bayar" yai maganar yana murmushi. Direba ko a ransa yace 'ikon Allah, ji wani kwaɗo da fitsara wai ita game saurayi ta shiga motarsa yana mata kalaman banza na RUƊIN ƘURUCIYA, banda haka ina Sadik ina wata budurwa dan kawai yana ganin ya na da tsawon ƙafa!?" Seda suka kai Farhan gida sannan suka wuce gida, babban abunda yaiwa Sadii daɗi be wuce yadda yau gidansu ba mutane ba, hakan yai masa daɗi sosai. A ƙofar shiga BQ ɗin su ya haɗu da Dr. Ya kalleshi yace "Sadii yau kamar ba ka dawo da wuri ba, ina ka tsaya ne?" Sadik yace "mun sauke Farhan a gida ne, sannan muka taho?" "Wace kuma Farhan?" "My wife to be insha Allah" Sadik ya faɗa kansa tsaye. Usman yace "kasan me kace kuwa?" "Eh mana na sani, budurwata ce da nake burin Aure, kuma insha Allah daga bikinka se nawa" Usman ya jinjina kai yace "ba laifin ka bane, tashen balaga ne da RUƊIN ƘURUCIYA, ke ɗibar ka" Sadik yace "tashen balaga kuma? Oho koma dai menene, I mean what I say wallahi" Yana gama maganar ya wuce Usman, ya shige. Usman ya bishi da kallo, kawai ya girgiza kai, ya juya ya nufi in da motocin gidan suke. Sadik yai wanka yai salla, ya tafi ganin Mummynsa, sedai yana zuwa ya tarar ba ta nan wai ta fita. Haushi ne ya kama shi ya shiga Kitchen, ya tarar Khairat na dafa indomie, tana yi tana bin wata waƙa da ke tashi a wayarta. "Ss ke 'yar bainu" yai maganar da sigar tsokana. Waiwayowa tai ta kalli Sadik, tace "ka ga karka kuma cemin 'yar bainu" Yai murmushin yace "ke dallacan uwar fushi, ina Mother ta tafi ne?" "Nima ban sani ba, da Mummy ta ɗakkoni daga makaranta tazo ta ajiyeni suka fita tare" "To dafa indomie da ni, tunda Mother ba ta nan" "Baza'a dafa ɗin ba, 'yar bainu ta dafa maka" Dariya yayi yace "ke akwai zazzafan party da bikin dr. Fa, zamu shirya na 'yan school ɗin mu, kema za'a baki Card in da wanda zaki gayyata" Tsalle tai tace "wow, dole muje ai, kai za'a cashe fa Prince" "Ke dalla can, har wata rawa kika iya?" "Taɓ kaji ka, wace kalar rawa ce ban iya ba? Wallahi na iya rawa" Sadik yace "To yi mu gani, kuma in baki iya ba ba inda zaki" Yai maganar yana ciro wayar a aljihunsa, ya duba wayar ya saka mata waƙa, take Khairat ta fara rawa tana juyi, tana karairaya jikinta. Tafi ya fara yi mata yace "ba ƙarya kin iya, zaki je gurin partyn nan, let me join you" Nam suka shiga rawa shida Khairat a Kitchen, ya riƙe hannun Khairat yaana juaya ta suna rawa tare, kamar yaran turawa. "Lalalala! Innalillahi taɓɗijan, dama abunda kuke yi kenan? To wallahi sena gayawa Inna kuna abunda be dace ba, kuna taɓa juna bayan tace ba kyau. Ayshercool 07063065680. [6/4, 4:21 PM] Jakadiyar Arewa: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ RUƊIN ƘURUCIYA PERFECT WRITERS ASSOCIATION (WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS) https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ P. W. A *Story and written by* AISHA ADAM (AYSHERCOOL) Writer of WATA KISSAR..(Sai mata) ABDUL JALAL AƘIDATA (paid book) WUTA A MASAƘA NOW RUƊIN ƘURUCIYA (paid book) _Labarin RUƊIN ƘURUCIYA, na iya zuwa da wani salo, wanda baku saba ganinsa a rubutuna ba, hakan ya biyo bayan akan abunda aka gina labarin, wani abun ze ɓoyu wani Abun baze ɓoyu ba sakamakon labari ne akan teenegers, yara masu tashen Balaga, but hakan ba ya na nufin na sauka daga kan tsarin yadda nake Rubutu bane, ƙofata a buɗe take dan karɓar ƙorafi, gayra ko shawara_ ⚠️⚠️⚠️ƘIRƘIRARREN LABARI NE, BAN YADDA A JUYAMIN SHI TA KOWACE SIGA BA SEDA IZININA ❌❌‼️                                     13-14 A tare Khairat da Sadik suka juyo suna kallon Nana, dake tsaye tana musu kallon banza. Khairat tace "is this girl serious?" Sadik yace "A beg forget about her, she's mentally abnormal" "Nima na gani" Cikin tsiwa Nana tace "Wallahi Inna ta hana, tace babu kyau, kwata kwata babu kyau irin wannan abun, amma kai kuma kazo kana taɓata, tace marasa tarbiyya ne suke haka, kuma Allah ze fushi da mutum, Allah ya hana amma ka ke aikatawa, wallahi se na gaya mata" "Dan ubanki tsayuwar  me kike a gurin baki tafi gayamatan ba? Kifi ruwa gudu banza da baki kamar mazirari" "Kaine banza bani ba wallahi" Ta juya ta tafi ɗakinsu da sauri dan ta sanar da Inna. "Innarmu, Inna" ta shiga ƙwalawa Innan kira. Inna tace "Ya akayi meye kike kirana haka?" Se kuma Nana tayi saroro ta kasa Magana, kawai ta basar tace "kawai nemanki nake" "Dan kina nemana seki biyoni da wannan kiran Kamar wata sa'arki?" "To yi haƙuri" "Naƙi haƙurin" Nana ta ɗan sosa kai, ta nemi guri ta zauna. A yanzu Kusan duk lokacin da Sadik ze shiga gida ya haɗu da Inna, se tai masa faɗan wani abun, kodai na sumar kansa, ko rashin son mutane, ko kuma taɓara, saboda haka yana dawo wa daga makaranta, yake ficewa yawon sa baze dawo ba se dare, se ya tabbatar da Inna tai bacci, se ya shigo ya ɗau Abincin sa ya fice ya bar falon, in ma Mother ze gani ya ganta a lokacin. Wasu lokutan da ya fara ɓuruntu ze ɗau Abinci Nana ke farkawa daga bacci, ta fuskanci baya shigowa se kowa yai bacci, dan haka ta sa ido sosai ta lura be zo ɗaukar abinci da wuri ba, dan haka ta gane se daren ze zo ya ɗauka. Har sun kwanta bacci, Nana ta daidaici Inna tai bacci, ta miƙe cikin sanɗa ta fito falon, ta janyo ƙofar falon ta rufe, ta kulle da mukulli ta ciki, ta nemi guri ta kunna TV tai zamanta tana kallon cartoon. Wajen sha ɗaya da rabi na dare, Sadik yazo yana murɗa ƙofa ze shigo dan ya ɗau Abinci, amma yaji a rufe gam. Ya jinjina ƙofar yaji ta a kulle, nan ya shiga ƙwanƙwasawa, nan ma ba wani respond. Yayi mamakin yadda aka rufe ƙofar falon haka, dan ba'a cika rufeta ba, ko da yaushe tana buɗe, saboda ita ce babbar ƙofar da zata sada ka da kowane sashi na cikin gidan, amma abun mamaki yau an rufeta. Ya zaga ya ɗaga labulen window, yaga koda wani a falon, ya hango hijjabin ta akan 2 seater, yana ganin hijjabin yasan itace, saboda kullum haka take yawo cikin hijjabin nan kamar me takaba, be taɓa ganin ta cire shi ba, kullum da hijjabi take yawo. "Ke malama zo ki buɗe min ƙofar nan" Banza tai dashi taƙi ko waigo wa balle ta kalleshi. "Wai ba magana nake miki bane?" "Ka nemi ke ta zo ta buɗe maka" ta bashi amsa "Dalla ki buɗe zan ɗau Abinci" Tasowa Nana tai, ta nufi inda yake tsaye a window tace "ba za'a ɗakko ba ɗin, idan kana son cin Abincin ka dinga zuwa da wuri kana ɗauka, base ka gama gantalin ka ba sannan kazo kana ɓuruntu kamar ɓera ka tasheni daga bacci ba" Buɗe baki yai yana mamaki yace "tunda gidan ubanki ne ai dole ki samun doka" "Ai dama bance Gidan babana bane, gidan babana yana ƙuaye ya mutu, ya barni a gidan Hakimi" "Ke bana son iskanci, dalla ki buɗemin" "Wallahi ba zan buɗe ba taimako ɗaya zan iya yi maka" Ta juya ta nufi dining, ta ɗakko ragowar bredin safe, taje kitchen ta buɗe fridge ta ɗakko ruwan sanyi, Sadik ya zuba mata ido yaga me za tayi. Ba kunya taje ta zura masa bredi da satchet water tace "ga shi nan, amma kar ka sake zuwa ka damemu" Galala yabi bredin da kallo da tsananin baƙin ciki da takaici, Nana kuma ta kashe fitilar falon tai tafiyarta. Ji yai tamkar ya karya ƙofar ya shaƙe Nana, yai mata dukan da seta kasa motsi. Cike da ɓacin rai ya koma BQ, ya tarar dr. Na zaune yana waya, se wani kashe murya yake cike da tsantsar shauƙi da Soyayya. Sadik ya kalleshi ya ɗanyi guntun tsaki, ya wuce ya duba fridge ya samo cake, da lemo ya koma ya zauna akan 3seater, yana tura cake ɗin nan kamar ze fashe da kuka. Gefe guda kuma Usaman na sake ƙular da shi, yadda ya nannaɗe murya yana zuba taɓara a waya, duk haushi ya cika shi, se tsaki yake yana hararar Usman, wanda be san me Sadik ɗin yake ba. "Jeddaty, kamar in janyo Ranar Auren nan haka nake ji, zuciya ta ta kasa nutsuwa da samun sukuni, am about to loose control fa" "Na fika ƙaguwa Nurain, sedai kayi haƙuri mu jira lokaci, kamar yaune zaka ga yazo, duk abu in dai an sama sa lokaci yanzu zaka ga yazo" "Hakane Baby na, are you not sleepy?" "No am not, when am with you, i keep everything aside, kai kaɗai zuciyar take kallo" "Hmm Beb, yakamata ki kwanta dare ya fara yi fa, But are you on bed?" "Yeah" "Are you sure?" "Quite sure Dear" "So how do you dressed up, for today's night" "I just wear my night gound" "Ok am going to my room now, let me have a 1picture of you with the night dress, so that I can sleep well" "Ohhk my Baby, as you wish" Duk wannan wayar da Usman yake a gaban Sadik yake yin ta ba kunya ba Komai, Sadik ya dinga binsa da kallo, harya ta shi ya bar falon gaba ɗaya. Ji yai ya dena jin ɗanɗanon cake ɗin, dama cin da yake na dole ne, ya miƙe shima ya koma ɗakinsa, ya nemi guri ya kwanta, sedai ya shiga tunani me zurfi, da kwaɗaituwar son yaga hoton da za'a turawa Usman ɗin. Ina ma Farhan na da waya, da ko ba komai idan yaji muryarta ze ji daɗi a ransa, amma dai yasan ko kusa Farhan ba zata turo masa hotonta a kayan bacci ba, duk da ba mace a gidansu, amma yasan kayan Bacci na mata ba wasu kayan Kirki bane suke sawa, dan mafi akasari kayan baccin yana bayyanar da wani sashi na jikin su ne. Take zuciyarsa ta cigaba da azalzalar sa, da ƙawata masa abubuwa daban daban, mussaman Farhan ɗin sa, ina ma ko sau ɗaya shima yaga hoton ta a night gound, ko yaya yana son ganin wani sashi na jikinta, a cikin kyakykyawar fatarta me ɗaukar ido. Rumtse idonsa yai sosai yana sauke ajiyar zuciya, a hankali ya furta Farhan, yai ruf da ciki ya rirriƙe pillow ɗin da yake kai, a hankali ya dinga faɗin "Subhanallahi wabi hamdihi, subhanallahil azeem" A haka bacci yai awon gaba da shi, sedai kasancewar ya saka abun a ransa, se ga Farhan a cikin baccin sa, a yanayi me wuyar fassara. Yadda ya kwanta da wannan matsanancin tunanin, haka ya dinga mafarkai barkatai har Asuba, kiran farko ya buɗe idon sa, ya jiƙe sharkaf da gumi, duk da A.C da ke ɗakin nasa. Tashi yai yayi shiru yana tunanin mafarkin da yai, jinsa yai somehow abnormal. Tunani ya shiga yi yanzu se yayi wanka kenan? Amma ai mafarki ne kawai, shiru ya kuma yi yana tunani, ya ɗakko wayarsa ya shiga yai searching, tabbas wanka ya kama shi since he has a dreams. Tsaki ya ɗanyi, ya sakko daga kan gadon, a gurguje ya shiga banɗaki yai wanka yai alawala, ya fito ya zura rigarsa, sedai yana gamawa sega Faruk ya shigo ɗakin nasa, ya kalli Sadik yace "Au ashe ka tashi? Sarkin nauyin bacci, yau anyi abun arziki, dama Daddy ne yayo waya, amma ya nake ganin kanka kamar a jiƙe?" Tsaki Sadik yai yace "Alwala nayi fa" "Alwalar ce ka ke a jiƙe haka, kalli jallabiyar taka fa duk ruwa" Banza Sadik yai masa, ya ɗau turare ya fesa a jikinsa, ya saka hullar tashi ka fiye naci. Faruk ya kwashe da dariya yace "inyee, Su Auta an girma, iyee sekace wani magidanci wanka da Asuba haka, Lallai ka girma ka isa Aure, na yarda da batunka na cewa da kake ka isa Aure" Haɗe rai Sadik yai yaƙi cewa uffan, a falo suka haɗu da Usman shima ya fito, suka fito suka tafi masallaci, sedai suna tafe Faruk yana tsokanar Sadik, Sadik ya ƙulu matuƙar ƙulewa, amma yaƙi cewa komai dan kar Daddy ya fuskanci wani abu. Da suka dawo daga sallar ma Sadik be koma bacci ba, ya nemi guri ya zauna yana ta tunani kala kala daban daban a zuciyar sa. Haka ya zauna har gari yai haske, ya shirya ya fice dan tafiya makaranta, ba tare da ya shiga ko cikin gidan ba balle ya karya yai musu sallama, direbansa ya fara jan motar kenan ya hango Nana ta fito, se yanzu ya tuna abunda tai masa daren jiya, tabbas ba dan ya riga ya shiga mota ba da Allah kaɗai ze iya raba shi da ita yau, se kuma ya tuna yana taɓata ze sha tujara a gurin kakarsa, kuma Daddy ma ze masa faɗa, ƙwafa yayi dan ko me za'ai sedai ayi amma se yai maganin ta. Haka ya tafi makaranta yana ƙananun sambatu. Farhan ta shirya tsaf cikin Uniform ɗinta, sedai a jikinta tana jin tana ƙara ƙiba, dan skirt ɗin da ta sa tana jin yadda ya matse ta sosai, ta juya ta juya ta ƙarewa kanta kallo a madubi, ji take kamar ta cire shi ta canza wani, amma ɗaya skirt ɗin ba a goge yake va gashi ta makara sosai. Ta ɗakko ƙaton hijjabin ta ta ɗora akan Uniform ɗin sannan ta fito tsakar gida, ta kalli Ummanta da ke kaiwa tana komowa a tsakar gida tace "Umma na tafi" Ba ta kalli in da Farhan take ba tace "Allah ya kiyaye" cikin yanayin sanyin halin ta, ta wuce ɗakin mahaifinta, se da tai sallama akai mata izinin shiga sannan ta shiga. Tace "Abba ina kwana" "Lafiya ƙalau Farhan, za'a tafi makarantar ne?" "Eh Abba zan tafi" Ya saka hannu a aljihunsa ya ɗakko Naira ɗari ya bata yace "ga kuɗin makarantar ki, Allah ya tsare kin karya dai ko?" "Eh Abba na karya" "To shikenan, Allah ya kiyaye hanya, ki kula da kanki ki kula da addinin ki da mutuncinki kinji Farhan" "To Abba insha Allah, nagode Sosai" Ta miƙe ta fito, a soro ta tsaya ta buɗe jakarta ta ɗakko turaren da ta siya da kuɗin da Sadik ya bata, ta shashshafa a jikinta, dan tana matuƙar son ƙamshi a rayuwarta, sedai ummanta bata damu da ta ɗorata a hanya da yadda zatai amfani da kayan gyaran jiki ba, ko da yake yaushe ma ta kulata balle ta koya mata wani abu makamancin haka. Ta gama shafawa ta maida shi jakarta, sannan ta fita ta nufi titi. Gaba ɗaya Sadik yau kamar mara lafiya haka yake jinsa, yama rasa gaba ɗaya meke masa daɗi, duk yadda abokansa suka so jansa da surutu amma yaƙi magana, ƙyaleshi su kai, dan sun san haka yake yi wasu lokutan. Ana ta shirye shiryen fara jarrabawa a makarantar, wasu malaman duk sun ƙarƙare darususskan su, wasu sunyi teses ɗin da duka zasu yiwa ɗalibai, zasu fara jarrabawa. Farhan ta kasa fita daga ajinsu ma, gani take kamar ita za'a dinga kallo idan ta fita saboda yadda skirt ɗinta ya matse ta sosai, gashi bironta ya ƙare tana son siyan wani, haka ta daure ta fita siyan biron, sedai shop ɗin a kulle yake. Kawai ta yanke shawarar zuwa gurin Prince ta karɓi aron nasa. Ta ɗau littafinta ta fita, taje ajin nasu sedai tana shiga ta duba gurin zamansa ta ga baya nan, ita ba iya sakewa take da 'yan ajinsu ba, dan haka ta nemi guri kawai ta zauna tana jiran dawowar Prince ɗin. Gudu gudu sauru sauri take hawowa step ɗin benen, jacket ɗinta na riƙe a hannunta ɗaya, ɗaya hannun kuma na riƙe da jarkar youghurt, yana daga saman benen a cikin malamai yake hangota tana hawowa, ilahirin jikinta na rawa, kanta a ƙasa ba tsammani tai karo da shi a tsaye yana kallonta. Ƙoƙarin kaucewa tayi amma yaƙi ba ta hanya, yace "What did I told you last day?" Kallon hannunta tai da ta riƙe jacket ɗinta, ta kalli jikinta ta ɗan yatsuna fuska tace "sir zafi nake ji shine fa na cire ta" "Shut up! Bance karki sake cire jacket ɗinki ki tafi haka ba?" Ta yatsuna Fuska tace "kace" "Shine kika cire rigar kike yawo da ita a hannu dan rashin kunya ko?" Shiru tayi tana zumɓura baki taƙi Magana, yace "oya wear it back" Tana harararsa ta gefe haka ta maida rigar, sannan ya batta ta tafi. Tana barin gurin tace "ɗan rainin hankali kawai" ta sake cire rigar ta tafi aji. Corper Nura yace "Nayi matuƙar mamakin ganin irin wannan dress code ɗin na student, a garin Kano" Nazir yace "ai ba kai kaɗai ba, abun da mamaki kam kamar ba garin musulmi ba, kalli yadda suke yawo kamar ba musulmai ba, kuma babban abun takaicin an rasa me musu magana akan wannan shigar ta yaran, kuma su kansu iyayen suna kallo amma sun yi shiru" Nura yace "amma hakan be dace ba, ze iya buɗe ƙofar ɓarna a tsakanin malami da kuma ɗaliban kansu" Nazir yace "ai kai kaga haka, su ba wannan ne a gabansu ba, su makarantar burinsu yadda zasu samu kuɗi, su kuma iyayen burinsu ace yaransu na makaranta me tsada, amma ɓarna kam a makarantar nan sedai ai shiru kawai" "Subhanallah, Allah ya kyauta" Nazir ya amsa da "Ameen" Farhan kuwa gajiya tai da zaman jiran Prince, ga shi 'yan ajin se fitsara suke kala kala a gabanta, dan haka ta tashi zata bar ajin, harta fito taji yace "See me here" Ta waiga taga yana tahowa a hankali kamar mara lafiya, tai murmushi tace "ina ka tafi ne na daɗe ina jiranka fa" "Naje cin Abinci ne ina jin yunwa, kuma nasan idan nazo ma nace ki rakani ba zaki bini ba" Tai murmushi ta koma ajin nasu, tana gaba yana binta a baya, sedai shima ya lura da yadda take tafiya a kunyace saboda yadda skirt ɗin ya matseta sosai. Seda ta tsaya ya zauna sannan itama ta zauna, tace "dama pen nazo ka aramin, naje in siyo shop a rufe" Murmushi yai yace "in baki pen dai ba in baki aro ba" Ya zura hannu a aljihunsa ya ɗakko sabon biro ya bata ta karɓa tace "Nagode sosai Allah ya saka da Alkhairi" Be magana ba se jinjina mata kai da yayi, ta zauna tana ta 'yan rubuce rubucen ta, da alama tana solving maths ne, shikuma ya ƙura mata idanun sa, ko ƙiftawar kirki ba ya yi, se wata irin ajiyar zuciya yake. Ta kalleshi "baka da lafiya ne?" Ya girgiza masa alamar a'a. "Amma na ganka wani iri yau" "Am sick" ya bata amsa a hankali. "Meke damunka" Be magana ba ya lumshe idanunsa, ya kuma buɗe su a kanta. Cikin damuwa tace "dan Allah meke damunka?" "Nothing, cigaba da aikin ki" Jiki a sanyaye ta cigaba da rubuce rubucen ta, tana monitoring ɗin Sadik ɗin. Can aka jima ya tashi ya bar seat ɗin, ya koma baya ya kwanta akan wani benci. Gaba ɗaya Farhan ta damu, ta tashi ta bishi tace "Ko Clinic zan raka ka su dubaka?" "No zan ware insha Allah" "To kaƙi gayamin meke damunka" "Idan na gayamiki zaki min wani kallo na daban, just forget about it, kije class ɗinku kar Malami ya shiga" Taslim ta kalli in da suke tace "lallai yau ana jin soyaya, sedai naga fuskokin masoyan ɗauke da damuwa" Kallonta kawai Farhan tayi, ta tashi ta bar ajin cike da damuwa tana tunanin meya sa Prince a wannan mood ɗin haka?. A ƙofar ajinsu taga Dodon nata wato Sir Nazir, ya tsareta da ido ta maze tare da ƙi ɓoye tsoronta, "Allah ya shiryeki, ina tausayawa rayuwar ki a nan gaba" Farhan ba tace Komai ba ta wuce cikin ajin nasu, dan ita bata damuwa da duk surutun da Nazir ze mata akan Sadik. Seda duk aka koma aji sanna Meena ta kalli Taslim tace "Ke nifa na tafi in je inga ta ina zan fara kaiwa gayen nan hari" Taslim tai murmushi tace "jarababbiya idan me taurin kai ne kamar Naziru wahala zaki sha a banza a wofi" "Shi ya isa ma, shi ma Nazirun dan ban dage bane, amma da shi ɗin banza" "Hmm to ai shikenan maji ma gani" Meena ta miƙe ta gyagyara zaman Uniform ɗinta ta fice. Sadik ya rasa abunda yake masa daɗi, ya taso da niyyar ya koma gurin zamansa ya zauna, sedai idonsa ya sauka akan Taslim, da ta ɓalle botir ɗin sama na rigarta, wanda hakan ya bayyana wani sashi na ƙirjinta, dan kana iya ganin jar kalar brezia dake jikinta, ta nutsu tana danna waya. Wani uban tsaki Sadik yaja ya kauda kansa, wanda seda ya janyo hankalin wasu daga 'yan ajin kansa. Cikin muryarta me cike da iyayi Taslim tace "Prince what's going on ne? Gaba ɗaya yau ajin nan ba daɗi saboda mood ɗinka, what happens ne?" Be ce mata uffan ba ya ɗauke kansa daga kallonta, mafarkansa na jiya ne kawai suke dawo masa kansa, zuciyarsa na ta raya masa abubuwa daban daban, na arziki da na banza. Ganin Sadik ba shi da niyyar yin magana yasa Taslim ta ƙyaleshi, s cigaba da danna wayarta. Mubarak Babba ne ya shigo class ɗin, ya nufi inda Taslim take, yana zuwa ya kalleta yace "you look sexy today Beb, kinyi kyau sosai" Wani killer smile tayi, ta ɗan kashe masa ido, ta cigaba da danna wayar, zama yai kusada ita yasa hannu ya karɓe wayar yace "kalleni mana, ina Magana kina danna waya" Hararsa tai tace "dan bani wayata" "Sekin kalleni zan baki" Idonta cikin nasa ta kalleshi tace 'na kallka yanzu bani wayata" Wani irin kallo yake mata sanna yai murmushi yace "kinga abunda na turamiki jiya?" "Ban gani ba"ta bashi amsa. "Why?" "Z" ta faɗa tana hararsa. "Naga dai alama haryanzu fushi kike dani, duk da na baki haƙuri, shikenan in kin huce ma daidaita, But before ya kamata a rufe nan" Ya kai hannu ƙirjinta, ya rufe botir ɗin ta dake buɗe tare da kashe mata ido. Zumɓura baki tai taƙi kallonsa, ya gama surutansa ya fita. Meena kuwa safa da marwa ta dinga yi a sashen Office ɗin da Corper Nura yake, can cikin sa' se gashi ya fito da litattafai a hannunsa, da marker da alama aji ze shiga. Tace "good afternoon sir" waigowa yai ya kalleta yace "Afternoon how are you" "Fine sir"be jira abunda za tace ba yai gaba abunsa, haushi n ya kamata na tafiyar da yai b tare da ya sake kallonta ba. "Hey fine girl, what are you doing over there?" Ta juya ta a wake magana, ɗaya daga sababbin corpers ɗn da suka zo tare da Nura ne, me suna George. Ta ɗan haɗe rai tace "Nothing" "But you are suppose to be in your class now, Why are you here?" Yai maganar yana sake ƙare mata kallo kamar maye. Tsaki taja ta bar gurin, shikuma yabi bayanta da kallo yadda take tafiya, ƙwaurinta duk a waje ga matsatsen skirt da ɗan ƙaramin veil. Ya jinjina kai yace 'lallai makarantar nan akwai 'yanmata' Tana tafe tana tunanin ya zata ɓullowa Nura kuma. Ta koma ajinsu tana zancen zuci. Farhan ana tashi ta tafi ƙofar ajinsu Prince ta tsaya, tana nan tsaye se gashi ya fito, ta kalleshi tace "Sannu" Yace "yawwa" "Kawo jakar in riƙe maka" "No kar in ƙara miki nauyi mu tafi kawai" "A'a ka kawo tunda ba ka da lafiya" Ta karɓi jakarsa ta haɗa da tata, Nas yace "shege Prince, a ɓoye dai ka gama da zuciyar ƙwailar nan, ta gama faller maka wallahi" Wata uwar harara Farhan taiwa Nas, Nas yace "ke ni kike harara? Dan kina zuwa ajinmu ki zauna na ƙara ganinki a ajin sena ɓallaki" Prince yasa hannunsa ya kamo na Farhan, sedai yana yin hakan yaji zuciyarsa tana harbawa da sauri, ita ma nata ɓangaren hakan ne, bugun zuciyarta ya ƙaru sosai. Sadik ya dake yaja hannun ta, su kai gaba. Nas yace "Lallai Prince Mugun ɗan rainin hankali ne, yanzu har wannan 'yar ta fara wayewa ni zata harara" Mubarak babba ya shafa fuskarsa yace "Yarinyar nan ba ta taɓa burgeni ba sam, ni hasali ma haushinta nake ji, amma yau tunda na ɗora idona akan hips ɗinta raina ya biya, Uniform ɗinta na yau sunyi pitting ɗin ta sun mata kyau sosai" Amin yace "kaifa Babba wani lokacin Akuya ne, Kamar ya ranka ya biya?" "Kamar yadda na faɗa mana" Nas yace "Allah yasa Taslim ta jika" "To taji ɗin seme? Dole wannan yaron ya liƙe mata, shiyake ganin abunda ya gani, sedai na ga shi kamar soko ne" Wani wanda suke aji ɗaya da Mubarak me suna Ahmad yace "kai me kake nufi ne Babba?" "Zan kauda damuwata ne" ya faɗa yana murmushi. Nas yace "kai kamarya, wai kana nufin kai a yanzu haka kasan mata?" "Me za'a fasa? Kana tunanin kowane ke iya tsallake sweet sixteens ƙalau? Ga wannan mata muna shiga muna fita a cikinsu, suna dressing kamar a turai, mu zauna guri ɗaya da su, mu ci Abinci tare dasu, muyi raye raye da wasanni tare, kai this is not easy fa" Amin yace "taɓ ashe mu bamu san komai ba, ai mu iyakar mu romance da 'yan kallece kallace" Nas yace "baka san komai ba dai, dan nima kawai dai eh" Nan suka saka shewa, Amin yace "ashe ni kuka bari a tasha?" Nas yace "tunin ma, amma fa nima zuciyata na ƙawata min budurwar Prince ɗin nan sosai wallahi" Babba yace "What so ever, kan in graduation a school ɗin nan, Wannan Yarinyar sena san abunyi a kanta, she looks sexy in her every movement" AMIN AFUWA KWANA BIYU NAYI BUSY NE SOSAI, AMMA INSHA ALLAH ZAN ƘOƘARI IN CIGABA DA KAWO POSTING AKAI AKAI You can start subscribing now @₦300 only, Free pages are not much. DOMIN GYARA, SHARHI KO SHAWARA Ayshercool 07063065680. [6/4, 4:21 PM] Jakadiyar Arewa:          🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ RUƊIN ƘURUCIYA PERFECT WRITERS ASSOCIATION (WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS) https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ P. W. A *Story and written by* AISHA ADAM (AYSHERCOOL) Writer of WATA KISSAR..(Sai mata) ABDUL JALAL AƘIDATA (paid book) WUTA A MASAƘA NOW RUƊIN ƘURUCIYA (paid book) _Labarin RUƊIN ƘURUCIYA, na iya zuwa da wani salo, wanda baku saba ganinsa a rubutuna ba, hakan ya biyo bayan akan abunda aka gina labarin, wani abun ze ɓoyu wani Abun baze ɓoyu ba sakamakon labari ne akan teenegers, yara masu tashen Balaga, but hakan ba ya na nufin na sauka daga kan tsarin yadda nake Rubutu bane, ƙofata a buɗe take dan karɓar ƙorafi, gayra ko shawara_ ⚠️⚠️⚠️ƘIRƘIRARREN LABARI NE, BAN YADDA A JUYAMIN SHI TA KOWACE SIGA BA SEDA IZININA ❌❌‼️                                   15_16 Suka sake kwashewa da dariya gaba ɗaya. Farhan kuwa har gaban mota ta raka Sadik, ya kalleta yace "shigo mu tafi mana" Ta girgiza masa kai tace "A'a, na ga ba ka jin daɗi, gara ka tafi gida da wuri, Allah ya sawwake" Ta miƙa masa jakarsa tai gaba, Sadik ya bita da kallo yana lumshe ido, a hankali ya koma ya jingina da seat ya rufe idanunsa, babban burin sa be wuce ace ya mallaki Farhan ba, abunda yake ji game da ita yana neman yafi ƙarfin sa gaba ɗaya. Farhan ma harta tafi hanya tana tunanin Prince, ba ta san meya same shi haka wanda ya sa shi shiga wannan yanayin na damuwa sosai ba. Ko yana cikin damuwa idan ya ganta ya kan saki ransa, yai ƙoƙarin ɓoye damuwar ta sa, amma yau kam ya gaza ɓoye damuwar tasa gaba ɗaya. Da wannan tunanin taje gida, ta tarar da Umma suna cin Abinci tare da ƙannen ta, duk sun sanya Uniform ɗin islamiyya, suna hira Umma nata dariya, amma Farhan na sallama ta haɗe rai, ta dena dariyar da take. Ta kalli Umman tace "Umma na dawo" "Sannu" shine kawai abunda Umman tace. Farhan ta shiga ɗakin su ta ajiye jakar ta, ta canza kaya ta fito ta shiga wanka, bayan ta kammala tai salla ta shirya cikin Uniform ɗinta na Islamiyya itama, ta fito da niyyar cin Abinci, sedai tasan za'a kwashe wa kowa Abinci idan baya nan a adana masa, amma ita kuwa nata sedai ta tarar da shi a tukunya ya sandare. Haka ta zuba Abincin ta shiga ɗakin umman nata ta zauna tana cin abinci. Tana son tai hira da Umman, amma babu fuska sam. Umman Farhan cikakkiyar ba fulatana ce, gaba da baya, kuma Farhan ita ce 'yarta ta fari, bisa ga al'adar Hausa fulani kuwa, dama ɗan fari ba'a jansa a jiki saboda kunya, sedai idan uwa tana da wata yaya wannan 'yar fari ko ɗan fari ya riƙi 'yar uwar uwa a matsayin uwa. Sedai Umman Farhan ba ta da Yaya mace ko ƙanwa, duk se maza gashi ba'a gari ɗaya suke ba, dan haka abubuwa suna bawa Farhan wahala. Wasu lokutan ta kanji a ranta anya kuwa Umma ce ta haifeta? Saboda abun ya wuce alkunya, abunda take mata tamkar tsana ne, har gara kwanan nan ta kan yadda su zauna a guri ɗaya, amma a baya ko zama tai a guri Umma ba zata zauna ba. Dan haka babu wata shaƙuwa ta mussaman tsakanin Farhan da Umma, tsakanin ta da ita sedai kallo da ido, duk da Mahaifin Farhan kan yiwa Umman nasiha akan ta rage wannan alkunyar da take akan Farhan, sedai shima a nasa ɓangaren, ba wani sakin jiki yake sosai da Farhan ba, kasancewar ta mace kuma 'yar fari, yafi sakewa da ƙanenta maza, hakan ya ƙara saka Farhan ɗin zama mara kuzari ko a cikin yara 'yan uwanta. Dama a yanayin halittar ta ma ba Yarinya ce me hayaniya ba, ba ta iya sakin jiki da kowa, idan kaga walwalata to tare da ƙanenta ne, suma wasu lokutan Umma na musu faɗan be kamata ta girma ta dinga shiga  cikin ƙannenta maza ba. Shiyasa haɗuwarta da Prince ba ƙaramar Ni'ima ce a gareta ba, yadda yake janta a jiki da nuna mata kulawa ta hanyar kyautatawa, shiyasa take matuƙar jinsa a ranta, take jinsa tamkar wani gurbi me girma a tare da ita. Tana jin Sadik kamar ɗan uwanta duk da kasamcewar alaƙar dake tsakanin su ba ta 'yan uwanta ka bace, wasu lokutan har ƙaguwa take gari ya waye taje makaranta su haɗu, ko ba komai Sadik akwai iya tsara kalamai masu kwantar da hankali. Duk da irin wannan zama da take a gidan su, Farhan na matuƙar shakkar iyayenta, dan basu da sauƙi aguri tarbiyya sam, wani laifin idan tayi, da ido kawai za'a kalleta ta san tayi ba daidai ba ta hau tsma, dan a dunyta tsani ɓacin ran iyayenta dan kar ai mata faɗa, bata son faɗa dama rayuwarta. Cin Abincin kawai take ba dan tana jin daɗin sa ba, dan ya riga yayi sanyi sosai, gashi Umman ta tashi ta bar ɗakin gaba ɗaya, ga tarin Magana da zata so ta tattauna da Umman amma babu fuska, ga damuwar Sadik ta dameta. Haka ta tashi ta kai sauran Abincin Kitchen ta ajiye, ta ɗau jakar Islamiyyarta ta tafi. Shirye shiryen bikin dr. Nata nisa, ana ta faman shirin bikin su. Gefe guda kuma kullum cikin rigima da tashin hankali yake da Nana idan suka haɗu, ita tsiwa shi rashin haƙuri. A makaranta kuwa tuni sun fara jarrabawa, wasu suna maida hankali kan karatu, wasu kuma suna sharholiyar su kawai. Wasu lokutan Farhan ajinsu Sadik take tafiya, dan suyi karatu yana kusa da ita, yana tamaka mata a wasu abubuwan, dan Sadik ba ƙaramin gifted bane. Wasu lokutan kuma a Library suke zama, Farhan ba gifted ce kamar Sadik ba, she needs to read hard, amma 'yar dagiya ce sosai ga nacin karatu, ga son taga ta iya abunda ba ta iya ba. Ko a aji idan akai abu bata gane ba, da ta tambaya gara ta bari in malamin ya fita, ta tafi gurin Prince ya koya mata. Sedai a 'yan kwanakin nan, babban abunda yake ɓata mara rai be wuce yadda Mubarak Babba ke damun ta da kallo ba. Kusan kullum idan ta zo ajin, se ta ganshi ya zo gurin Taslim, amma se ya dinga mata wani irin kallon ƙurilla wanda ko Sadik baya mata, gashi kallon yana damun ta sosai, sedai ta lura sam Sadik be san Mubarak na mata wannan kallon ba, ita kuma bata gaya masa ba saboda gudun buyagin sa. Yanzu ma tana ajin, tana wani zane da Sadik ya koya mata, kasancewar za ta shiga jarrabawar basic technology bayan break, tafi gane karatun Sadik sosai akan wanda akai musu a aji. Tana ɗaga kai tai ido huɗu da Mubarak, ya kashe mata ido tare da lashe lips ɗinsa kamar wani maye, hakan ya ƙular da ita ta ɗauke kanta da sauri ta cigaba da abunda take. Sadik yace "Honey, waike a wani club zaki participating ne? Debate, quiz dancing competition ko kuma sport, kin san duk bayan exams Akwai wannan events ɗin da za'ayi, ga end of term party da za'ai, a me zaki participating ne?" "Ba kowanne" ta bashi amsa. "Ban gane ba kowanne ba, ko quiz ba zaki ba?" "Ai an ɗau sunan wanda za suyi tuntuni" "To meyasa ba'a saka da sunanki ba, naga You Are very brilliant" "Ni nace kar a saka, ni bama son duk abunda za'ace inyi performing a gaban mutane" "Ji ta dan Allah, kin fiye damuwa Farhan, I want you to be famous in this school, ya zaki dinga ɓoye baiwar da Allah yai miki? Yakamata ki dinga participating fa" "Ni bana son a dinga kallona" tai maganar a shagwaɓe. Be san lokacin da yace "wow" ba. "Ina son shagwaɓar nan taki Farhan, tana ƙayatar dani fa" Cikin wata shagwaɓa tace "Nifa ba shagwaɓa nai ba, kawai maganata ce a haka" Yace "Awwn so cute, ɗan sake inji" yai maganar zuciyarsa na ƙawata masa ya rungume Farhan yai kissing ɗin lips ɗinta. Ɗan rufe fuska tai tana murmushi. Yayin da shi kuma ya cigaba da bin ta da kallo, me ma'anoni daban daban. Bisa kuskure Farhan ta ɗaga kai, ta sauke akan su Mubarak da ke kissing ɗin juna, shi da Taslim. Wata mummunar faɗuwar gaba taji, take jikinta ya hau rawa dan abun ya bata mamaki, a makarantar nan ta fara ganin wannan watsewar muraran a zahiri. Bata manta ranar farko da ta gani ba, a wani aji ba kowa ta hangi wani malami da wata yarinya suna kissing, se kuma yau da ake zahiran a gabanta. Jiki na rawa ta miƙe ta kwashi litattafan ta, tace "Ni tafiya zanyi" Sadik yace "Lafiya kuwa? Lokacin shiga exam ɗin yayi ne?" Shiru tai masa tana ƙoƙarin raɓashi ta wuce, waiwaya yai dan yaga abunda ya ɗaga mata hankali haka. Take ya gano abunda ya jefata cikin wannan rawar jikin, se dai duk da ba yau su Taslim suka fara wannan ta'asar a gabansa ba, amma kawai yau se ya tsinci kansa a wani irin yanayi, mussaman da ga Farhan a daf da shi. Ya tattara nutsuwarsa yace "Farhan calm down, forget about them ina jin daɗin hirar nan da muke, ki zauna Please" Girgiza masa kai tayi tana son ficewa. Yana ƙoƙarin comforting ɗinta ta zauna, amma ina jikinta har tsuma yake ta bar ajin. Ganin Prince ba shi da niyyar bata hanya ta wuce, yasa kawai ta fita daga bencin, wanda garin fitar seda Jikinsu ya gogu da juna, wani shock suka ji a tare, wanda yasa Farhan saurin waigowa zaton ta ita kaɗai taji abunda taji. Sedai ta lura kamar shima yaji abunda ta ji, da sauri ta fice tana sassarfa. Mubarak kuwa a hankali ya cika Taslim yana murmushi, Sadik ya kallesu a fusace  yace "kai Babba, dan kutmar.... Kar ka sake zuwar mana aji kana mana Iskanci, ka tafi ajinku ku dinga yi a can" Mubarak yace "da can da muke a nan ɗin meyasa ba kai magana ba se yanzu?" "Saboda ba ze yuwu ku dinga takura nawa jin daɗin saboda iskancinku ba, Farhan Yarinya ce be kamata ta dinga kallon irin wannan abubuwan ba" Babba yace "A'a ka manta, a cikin mahaifa take ƙarewar yarinta, shikenan dan kana wannan soyayyar 'yan ƙauyen kowa ma irinta zeyi, yarinya se kidahumancin tsiya, wataƙila ma duk ƙaryar banza ce, dan yaran nan suma sun san komai" Sadik yace "what so ever dai, in ma zakuyi idan tana nan gaskiya ku dena, na gaya maka in ba haka ba za'aji kanmu da kai" Nas yai dariya yace "Allah ya temaki Prince, Your royal highness" Sadik yai tsaki yaƙi kulashi. Taslim tace "kaifa Prince ka fiye abun haushi, kai kaƙi bari Yarinya ta waye, kuma ka hana wasu jin daɗinsu akan me?" Wata uwar harara Prince yai mata, tai murmushi ta kalli Mubarak tace "one more time Dear" Suka kuma rungume juna suna kissing, Amin yace "shegu ai baku burgemu ba, tun da ba kuyi wancan aikin a gabanmu ba" Mubarak ya saki Taslim yace "ji shege, Allah ya shiryeka"  suka cigaba da dariya kamar ba suyi komai na damuwa ba. Prince kuwa sake jefa masa wani tunanin su kai a zuciyar sa, yana sake kwaɗaituwa da Farhan, shi duk iskancin sa ba ruwansa da kowace 'ya, banda ma yanzu da ya fara soyaya iyakar sa da mata, ayi hira ai ciye ciye, ayi party amma ba dai ya taɓa 'yar wani da sunan aikata alfasha ba. Da fari sam ba shi da feelings akan Farhan, yana dai sonta ne sosai, Amma zigar abokansa da RUƊIN ƘURUCIYA, sun fara ɗibarsa zuciyarsa na ƙawata masa ko sau ɗaya yai kissing ɗin mace. Shi da fari kiss ƙyama yake ba shi idan su Nas  sunayi, yaita ce musu ƙazamai, amma akan Farhan yana matuƙar son ko sau ɗaya yayi, yaji me suke ji ne, zuciyarsa na fara kissa masa abubuwa marasa kyau akan ta. Ita kam gaba ɗaya mamaki ya hanata sukuni da damuwa duk suka addabeta, ta godewa Allah da yasa masoyinta baya cikin irin wannan masu muguwar ɗabi'ar ta fitsara. Ta shiga ajinsu tana zancen zuci, sedai abun mamakin suda suke daf da shiga jarrabawa, se ta tarar da 'yan ajin nasu sunyi group sunyi tsit. Zaton ta karatu sukeyi, dan haka ta nemi guri ta zauna, sedai tana zama taji muryar Haseena, ba ta kai ga jin me take faɗa ba, taji sun kwashe da dariya suna shewa. Ba ta damu ba, ta cigaba da abunda ke gaban ta, sedai suna gama shewar da sharhin, suka sake yin tsit, Haseena ta ɗora da abun da take. Waya ce a hannun Haseenan, tana karanto musu wani abu, wanda da fari Farhan ba ta kai ga gane menene ba. Sedai da ta ƙara natsawa, ajin yai tsit ta fara fuskantar me Haseenan ke karantowa, wata irin narkakkiyar batsa Hassenan ke karanto musu, ba kunya ba tsoron Allah ba saye komai, yadda yake a rubuce haka take karanto musu. Lilly tai shewa tace "Kambu dama haka abubuwa ke wakana amma muna gefe? Dama akwai irin wannan zafafan Novels ɗin na hausa ban sani ba, ai ban taɓa zaton ana irin wannan abubuwa haka ba, kuma ban san ana karantawa a waya ba, na ɗauka se a bugaggen littafi ai" Haseena tace "inji wa, bugaggen littafi da kenan, ai yanzu an samu marubutan yanar gizo, littafi se wanda ki ke son karantawa, irin wannan litattafan zaki same su kala-kala. A gurin ƙawar yayata naji suna hirar, ina nan na bazama ina ta tara mana su, wasu marubutan kiji nasu littafin zallar nishaɗi ne, wasu hikima da iya rubutu kamar a gabanka akeyi, wata kuwa litattafan na ta zakiga wa'azi ne kawai" Yasmin tace "wayake ta wani littafin wa'azi, idan wa'azi ne ai kasan in da zakaji, amma ga irin wannan yadda ake fayyace komai, wanda idan tambaya za kai bame gaya maka, sedai ace maka kai yarone ba yanzu ba, amma ji yadda ake faɗar abubuwa, kai ni gaba ɗaya ma se naji kamar aimin Aure yanzu wallahi" Lilly tace "to shegiya zalamammiya, kema kar dai ace sex addict ɗin ce?" "To wa ya sani ma, tunda kai bawa ba gwadawa kai ba" Lilly tace "Ai na samo logics a littafin nan, ashe abubuwan attraction ɗin ma ba wuya, ba wuya ka tayarwa da maza hankali, shiyasa da ka ɗanyi abu kaɗan, se Sir Nazir ya hau masifa ahse abun ke damunshi jarababbe, ashe abar ke mintsinin sa, amma gaskiya i must try this seduction method fa" Haseena tace "try it on who? Ke ki rufa mana Asiri maza sukai mu ba mata ba" Lilly tace "on this guy Nazir man, wai shi man of God, komai ya dinga wani iyayi, kamar baya jin komai, ashe ga abunda yake damunsa yake sashi masifa dan mun cire jacket munyi yawo a haka, to wallahi akansa zan gwada pairing, in ga response ɗin shi" Yasmin tace "ki rufa mana asiri mana, idan ki ka zaƙe kika ɗaga masa hankali yayi yaya, shi ba aure ba" "Can ta mulmule masa, sauran malaman ma ai suna ji, amma suke ɓoyewa se shi baba suda uban masifa" Haseena tace "kuyi shiru mu ƙara ko page biyu ne kan a shigo exams" Su kai shiru, Haseena ta gyara zama ta ɗora da karanto wannan watsasten littafi. Tsam Farhan ta tashi, sumi sumi tai waje. Haseena tai tsaki tace "nifa na tsani yarinyar nan haushi take bani, wai ita ta Allah shine ta fita" "Bar 'yar ƙauye" cewar Yasmin. Lilly tace "A'a gaskiya karki zagi ƙawata, ni wallahi burgeni take ina son salihancin ta, dan bata magana ne, ni kuma ban iya ƙawance da mara magana, yadda Allah ya horemin maƙogwaron murya da harshe ba yadda zan iya zama da mara magana, amma wallahi ni ina sonta tana burgeni" Yasmin tace "ai seki tayi, wannan 'yar ƙauyen yarinyar, sam bata waye ba ta fiye abun haushi, amma ta iya wahsewa namiji baki tana masa dariya da surutu" Lilly tace "ke akwai Yarinyar da Prince ze toasting har taƙi saurararsa ne? Ku dena zaginta dan Allah bana jin daɗin hakan yaseen" Haseena tace "dalla ku manta da ita mu cigaba da karatun mu" Suka sake tattara hankalinsu akan baɗala. Farhan a ranta tace "wannan wace irin masifa ce? Shikenan kowa lalacewa a makarantar nan ba me cewa wani bari, banda fitsara ai gara abunda ta gani a ajin su Prince, akan wannan lukutayen bayanannun fitsara da ake karantowa suna saurara. Meenal ce ta shigo ajin tana tangaɗi, idanun ta duk sun kumbura alamar tana jin bacci, ko kuma tana cikin damuwa, ta nemi guri ta zauna a kusa da Taslim. Taslim tace "hey beb are you ok? Meke going ne?" Shiru Meenal tai ta kifa kanta akan benci tana ajiyar zuciya. Taslim tace "wai meye ne? Or do you need me?" Ta girgiza kai alamar a'a. "Kinje gurin mummynki ne ta ss3?" Meenal tace "malama, wata ƙwaya na sha tun jiya take wahal dani, na kasa baccin na kasa komai ga jikina duk a mace, taƙi sakina gaba ɗaya, kuma bana son in koma gida a gane" Taslim tace "calm down dear, nima farkon farawa ta haka naita fama wallahi, amma ki kwantar da hankalinki, ki matsa lemon tsami da yawa, ki zuba manja a kai ki sha, zan saka Mubarak ya kawo miki wadda zata dai-dai ta miki jikin naki, amma ki ƙwarara jikinki kiyi exams ɗin lafiya, kar a fuskanci wani abun" Ta jinjinawa Taslim kai alamar to. Haka invigilators suka shigo, suka fara arranging ɗinsu domin fara jarrabawa. Sadik kam kusan rabin jarrabawar nan be san meya rubuta baz tunaninsa da hankalinsa na can kan wani abu daban. Meenat kuwa duk da ta na cikin maye, amma taji daɗin ganin corper Nura a cikin invigilators ɗin nan. Da sun haɗa ido zata masa wani killer smile tana lumshe ido, tun yana basarwa har ya ɗan fara dirircewa. Murmushi tayi tace gayen nan ai dole ka shigo koma ta ko baka so. Da ya zaga ya zagayo se yaga tana kallonsa, ba ya son dizgata a gaban ɗalibai dan haka ya ƙarasa gaban seat ɗinta yace mata "gani me kike buƙata" Cikin kashe murya da magana ƙasa ƙasa tace "ni ba kiranka nai ba" "Amma ki ke kallona" "To sir dan kawai na kalleka, ni bani da lafiya ne" "Eyya sorry, can You write the exam?" "Yes am trying" "Ok sorry, in kin gama kije Clinic a dubaki" "Ok thank you sir" Har ze juya ya tafi tace "oushh" Ya juyo da sauri yace "ya dai cikin ne?" Ta jinjina masa kai alamar eh, "eyya ko dai zaki je a fara baki magani?" "No i will finish the exams first" "Ok sorry dear" Ta jinjina masa kai tana wani marairaice fuska. Yana wucewa tabi bayansa da wani irin shegen murmushi, a ranta tace "da Wannan raunanniyar zuciyar ta ka zan damƙe ka ta wuya" Ta sake sakin wani murmushi, tana cigaba da rubutu. Da wuri Farhan ta gama exams ɗinta, saboda tayi mata sauƙi sosai da sosai, duk da zare ido da muzurai da sir Nazir ya dinga yi, sam hakan be damu Farhan ba dan nan da nan ta kammala, dan abunda sukai bita tare da Prince mostly su suka fito musu. Tana gamawa ba ta jira Komai ba ta nufi hanyar fita, ta jiyo Sir Nazir yace "daga nan ki ɗau jakar ki ki tafi gida, idan kika kuskura na ganki a gurin yaron nan sena miki duka" Seda gaban Farhan ya ɗan faɗi, dsn tabbas yanzu Sir Nazir yana hukunta mutum idan yayi laifi, har duka yake, makaranta kuma sun kasa dakatar da shi, saboda jaki work da yake musu, he is very hard-working teacher, yana da jajircewa sosai suyi ta jibga masa jaki work, kuma hakan baya damunsa. Da akai masa Magana akan dukan da yake yace shi koyarwa ko duk Makarantar ne ze koyar, baze dameshi ba, amma baze dinga kashe energy ɗin sa yana koyar da yaran da basu san darajar Malami ba. Rashin Nazir ze sama musu babban giɓi a makarantar, dan haka suka ja masa kunne kome zeyi ya dinga yi sama sama, banda punishment me wahala ko duka, idan ba haka ba uban wani ɗan ze iya kulle shi. Ajiyar zuciya Farhan tayi da ta tuna da haka, tana fita wajen ajin taji maganar da yai ta shiga ta kunnen dama ta fita a na hagu, ajin su Prince taje ta tarar be fito ba, dan haka taje ta nemi guri ta zauna tana jiran fitowar tasa. Gajiya tai da zaman ta miƙe tsaye tana ɗan leƙewa cikin ajin. Ji tai an kama rigarta an janyota ta baya. Da sauri ta waiga amma taga Mubarak Babba ne da Wannan aikin haka. "Meye haka, me nai maka?" Ta faɗa a ɗan raunane. "Sekin min wani abu zan taɓa ki, i just feel like to do so, naga jiya kin bar ajinsu Sadik saboda nai kissing Taslim, shiyasa kema nake so in kissing ɗinki, in gwada miki yadda ake soyaya ba kamar wadda kuke ke da wancan wawan Sadik ɗin ba" Nema yake ya haɗata da jikinsa, kasancewar gurin ba kowa, kusan itace ɗaliba ta farko da fito daga ɗakin jarrabawa. Ƙoƙarin ƙwacewa take, ta hana shi ya haɗa jikinsa da nata, ga wani warin hammata da yake, take zuciyarta ta fara tashi. Abunda ko da wasa ba ta taɓa jin Prince ɗinta yana yi ba, abun mamaki ya bata ma, dama yaran masu kuɗi ma na warin jiki? Ga ƙamshin turare a jikinsa, amma warin daban ƙamshin daban. Ganin da tai bata da mafita yasa ta ware murya ta shiga kiran sunan "Sadik" Da sauri Babba ya ƙyaleta, dan yasan gamonsa da Sadik ba daɗi. Ta arta da gudu ta bar harabar gurin, tai waje. Sadik kuwa da Sauri yai submitting paper ɗin sa ya fito, dan tabbas yaji kururuwar Farhan. Sedai yana fitowa yaga be ganta ba, ya dudduba amma bata nan, ya nufi ajinsu ya tarar da wanda suka fito ya tambaye su Farhan, suka ce masa ai ta fita tun ɗazu. Haka yaita zaga makarantar ko ze ganta, amma be ganta ba nan ya dinga mamakin abunda ya sata wannan uban ihun haka, gashi ita ba waya ba balle ya kirata. Haka ya wuce ya tafi gida yana tunani. A gidanma abunda ba ya so, dan sati me kamawa za'a fara biki, masu rumfuna da kujeru duk sun kawo sun jibge a harabar gidan, wannan ya shiga wannan ya fita ita kanta Mother bata da lokaci, kusan kullum ba ta nan, ita ce nan ita ce can saboda hidima. Yana kwance a part ɗinsa da yamma, Nasir ya kira shi yace kayan da akai order sunzo, sedai nasa wandon ne se cikin satin bikin ze iso. Sadik yace "i hope dai za'a kawon kafin ranar partyn nan" "Za'a kawo insha Allah, ga sauran nan naje na karɓo rigunan ma, naso in biyo in kawo maka ka gani, amma ba mota a gidanmu duk an fita da su, a babur naje" "Ok shikenan, gobe in Allah ya kaimu seka zo dasu a bawa kowa nasa" "To shikenan Allah ya kaimu goben" "Ameen" ya katse wayar. Yanzu Nana ba ta haɗuwa da Sadik, sedai kuma abun ya koma rigima tsakanin ta da Khairat, haka kurum da ta motsa se Khairat ɗin ta fara hantarar ta, tana zaginta ko da kuwa a gaban Inna ne, Inna ba ta cewa komai dan ba ta shiga faɗan yara, in ba gani tai za su cutar da junan su ba, ita kuma Nana na gudun faɗan Inna. Amma Nana ta fara ƙuluwa da abunda Khairat ke mata, kuma babban abun takaicin ma shine, ba iya Khairat ke mata hakan ba, mahaifiyar Khairat ɗin itama haka take, matar gidan ma haka take mata mussaman idan ta ga babu idon Inna a gurin. Hakan ya fara damun Nana sosai, taji ita gaba ɗaya ma zaman Gidan ya isheta, gara su koma ƙauye dan a can matsalarta ɗaya faɗan Inna, amma kuma ba tsangwama da hantara, dan bata jin daɗin yadda ake hantararta a gidan. Duk gidan ba wanda take ɗasawa da shi sama da Daddy, se masu aikin gidan se kuma Faruk, yana da fara'a sosai yana da kirki, ba kamar dr. Ba, dan shima baya kula mutane ba ya Magana Sosai, shikuwa oga kwata kwata nasa yafi na kowa, ga rashin son mutane, ga wulaƙanci, ga zagi da hantara ga iya muzurai duk shi kaɗai, Faruk ne me halin Baban su ba ruwansa shi da wannan zafin kan. Yanzu ma Nana tana cikin 'yan aikin, ana girkin rana, Nana akwai son aiki sosai, sedai ko a gida Inna ba ta fiye sata aiki ba, Se su bata ɓarar maggi, ko jajjage ko shara, dan su huta da hayyatarta na lallai se taya su aiki. Aka kammala girki, aka zuzzubawa kowa nasa, Nana ta ɗauka ta dinga kaiwa kowa har inda yake. Ta kaiwa Inna nata, Ta ɗau na Mother ta nufi ɗakinta, da sallama ta shiga ɗakin, ta tarar da Mother da Maman Khairat se Faruk da yake riƙe da kuɗi a hannunsa da alama aikensa za'ai. Ta ajiye kulolin Abincin tace "wai ga Abinci" Mother ta kalli Nana tace "waye yace ki shigo nan?" "Ba kowa kawai kowa kai masa Abincin sa nake" "To daga yau kar in sake ganinki a nan ɗakin, ki dinga tsayawa a can in da aka sauke ku, baki da hurumin zuwar min sashe, idan kika kuma zuwar min nan sena saɓa miki" Turus Nana tai tana kallon Mother, tana tunanin meye a nan ɗin da dan ta shigo za'a dinga mata wannan kashedin haka, nan da nan ranta ya ɓaci. Maman Khairat tace "ba Magana ake miki ba kina jin mutane? Maza ki wuce ki bar gurin nan, da haka yaro ke koyar munafurci, yaran ƙauye dama ba kan gado suka cika ba, yanzu zaki ji ta haɗa wani abun ta gayawa kakarta ta kunno miki wata wutar" Jiki a sanyaye Faruk yace "haba Mother, meye a ciki dan ta shigo me aka ajiye a nan ɗin, naga Khairat ba ta da iyaka a shiga duk in da take so a gidan nan, hakan da kike mata ba zata ji daɗi ba, ba daɗi hantara" Mummy tace "to uban mu gayamana abunda yakamata" "Ba abunda yakamata zan gaya muku ba, amma idan bata zo ta ga abunda za ta je ta gayawa Inna ba, ai ta faɗa mata abunda a kai mata, na baƙaƙen maganganun da ku kai mata" Ya juya ya fita yana takaicin abunda sukai, dan shikansa baya jin daɗin wasu daga halayen mahaifiyarsu, Akwai ta da wulaƙanta ɗan Adam mussaman talaka, kuma Mummy ce ke zigata, kuma ko zata ƙyamaci kowa be kamata ta ƙyamaci dangin mahaifinsu ba. Yana fitowa harabar gidan ya hango Nana akan barands, tai shiru tana wasa da tsinke, da alama tana cikin damuwa akan abunda akai mata. Ya ƙarasa in da take yace "Naana What are you doing here?" Ɗaga kai tai ta kalleshi, ita ba ta fiye gane irin wannan turancin da suke ba, a dinga yin sa a wani harɗe, wata kalmar ma bata fita sosai, zuba mai ido kawai tai ba tace komai ba. Yace "ok, jeki gurin su Binta, su baki namu Abincin ki kawo mana BQ" "Ina ne BQ?" "Wancan sashen me farar ƙofa" Tura baki tayi tace "wannan ƙanin naka zagina yake, idan naje ze iya zagina" "No ba ze zageki ba, aini na aike ki" Ta tashi ta koma dan cika Umarnin sa. Yabi bayata da kallo, kawai yaji ta bashi tausayi, tsangwama bata da daɗi sam. Nana ta koma ciki, ta karɓo kwando ɗauke da kayan Abinci da plates, seda tai sallama sannan ta shiga, amma tana shiga taga Prince ya harɗe ƙafa yana video game. Kallon ta yai, ya tashi zaune yace "me kika zo yi nan? Ban hanaki zuwa ɓangaren nan ba?" "To ban hanu ba, se kai abunda za kai" AIMIN AFUWA FOR THE VERY LATE POST, ABUBUWA SUN SHA KAINA SOSAI DA SOSAI, AIMIN AFUWA. Gyara Sharhi ko shawara Ayshercool 07063065680. [6/4, 4:21 PM] Jakadiyar Arewa:     🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ RUƊIN ƘURUCIYA PERFECT WRITERS ASSOCIATION (WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS) https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ P. W. A *Story and written by* AISHA ADAM (AYSHERCOOL) Writer of WATA KISSAR..(Sai mata) ABDUL JALAL AƘIDATA (paid book) WUTA A MASAƘA NOW RUƊIN ƘURUCIYA (paid book) _Labarin RUƊIN ƘURUCIYA, na iya zuwa da wani salo, wanda baku saba ganinsa a rubutuna ba, hakan ya biyo bayan akan abunda aka gina labarin, wani abun ze ɓoyu wani Abun baze ɓoyu ba sakamakon labari ne akan teenegers, yara masu tashen Balaga, but hakan ba ya na nufin na sauka daga kan tsarin yadda nake Rubutu bane, ƙofata a buɗe take dan karɓar ƙorafi, gayra ko shawara_ ⚠️⚠️⚠️ƘIRƘIRARREN LABARI NE, BAN YADDA A JUYAMIN SHI TA KOWACE SIGA BA SEDA IZININA ❌❌‼️       TAƘABALLALAHU MINNA WA MINKUM, ALHAMDILILLAH ALA KULLI HALIN UBANGIJI ALLAH YA KARƁI IBADUNMU YA MAIMAITA MANA, INA 'YAN UWA MASOYA, MARUBUTA DA MAKARANTA MURNAR BARKA DA SALLA, UBANGIJI ALLAH YA MAIMAITA MANA. BAYAN HUTUN AZUMI ALHAMDILILLAH, GANI NA DAWO MUKU DA CIGABAN LITTAFIN RUƊIN ƘURUCIYA. INA FATAN ZAKU BINI SANNU, DAN JIK ƊUMBIN SAƘONNIN DA LITTAFIN YA ƊAKKO, WANDA SUKE TAMKAR BULALIYA GA IYAYE. SHIN KUNA DA LABARIN MANHAJAR AREWABOOKS KUWA? MANHAJA CE DA TAZO DA TSARIN DAN SAUƘAƘAWA MARUBUTA DA MAKARANTA SAUƘIN CINIKAYYAR LITATTAFAI. TA IN DA ZAKU IYA SIYAN KOWANE FEJI AKAN KUƊI ƘALILAN, DAI DAI DA ALJIHUNKU. INA FARINCIKIN SANAR DA KU CEWA, DA ZARAR NA KAMMALA FREE PAGES, ZAKU CIGABA DA SAMUN CIGABAN LITTAFIN RUƊIN ƘURUCIYA, AKAN MANHAJAR AREWABOOKS. KARKU BARI A BAKU LABARI, AKWAI TARIN DARASIN RAYUWA A CIKIN LITTAFIN.                            17_18 A fusace Sadik yace "ke ni kike gayawa haka?" Murguɗa masa baki tai tace "eh ɗin, na faɗa ɗin" Faruk ne ya fito hannun sa riƙe da wayarsa yace "Sadik meyasa kake hakane? Hantarar mutum ba daɗi, nine mace ta kawo mana Abinci nan" Sadik yace "Amma dai bani a Wannan Abincin da ta kawo?, dan ba zanci Abunda wannan ƙazamar ta taɓa ba" Aikuwa Nana ranta ya ɓaci sosai tace "wallahi ni ba ƙazama bace, kaje ka nemi ƙazama a can amma bani ba" Ta dire kwandon Abincin, zuciyarta na mata zafi, yace "in kinyi zuciya ki tattara ki bar mana gida yau, kun zo kun cika mana gida kun hana mutane sakewa" "Sadik meyasa kake hakane? She's lyk sister to you, be kamata ka dinga hantarar ta haka ba babu daɗi, yanzu ma fa daga gurin Mother take suna ta kyarar ta, ba bu daɗi hakan, kyarar ɗan Adam ba shi da wani Amfani ko rana" Yatsune baki Sadik yai ya koma ya kwanta yana cigaba da video game ɗin sa. Washegari a school kuwa, bayan fitowa daga exams aka kawo kayan nan da sukai order, wasu irin tsadaddun crazy jeans da riguna. Ana ta ɗaɗɗaga kayan ana bawa kowa nasa, ana shewa da lissafin in da ya kamata a kama na partyn, amma hankalin Prince yana kan rashin ganin Farhan da beyi a ajin nasu ba yau. Miƙewa yai tsaye yace musu yana Zuwa, ya fita da sauri ya tafi ajinsu Farhan, amma bata ajin, Library ya tafi ya tarar da ita a can tana karatu. Sadik ya ja kujera ya zauna yana kallonta, ta ɗaga ido ta kalleshi tace "good morning" "Naƙi in amsa gaisuwar taki, ba an gama exams ba, me ki ke a library kuma?" Cikin sanyin halinta tace "Ai clubs suna rehasals yau, dan haka ance ba me tafiya se lokacin tashi yayi, shiyasa na taho nan kawai" "Amma meyasa baki zo ajinmu ba?" "Bakomai" ta bashi amsa a taƙaice. Yace "yawwa, jiya ina exams kamar ihun ki naji kina kiran sunana" Ɗan kallonsa tai tana zare ido, ta dake tace "bani bace" "Kamar ya ba ke bace? Muryarki fa naji" "Am serious ba ni bace" "Ok shikenan, ta so muje class ɗin mu kiga kayan da zamu sa ranar bikin Brother na" Ɗan noƙe masa kafaɗa tayi alamar ba zata ba. "Baby meyasa?" "Bakomai" Sadik yace "kefa kin fiye mulki wasu lokutan, yau kuma ajin namu ne ba zaki ba?" Ta ɗaga masa kai alamar eh. "Nagane, saboda abunda su Taslim su kayi ne ranar ko? Na musu magana ba zasu sake ba" "Ni dai kawai yau ba zani ba" "Ko wani abun suke miki a ajin namu" Ta girgiza masa kai alamar a'a. Yace "shikenan ni na tafi" Ya miƙe ze tafi, da sauri tace "nace ba" Be juyo ba yace "ki ka ce me?" "I want to talk to you please" Juyowa yai ya kalleta, ya dawo ya zauna yace "am all ears" Cikin jin nauyi tace "dan Allah ka zauna a nan" Yace "Why?" "Kawai mu zauna a nan" Tai maganar kamar wadda take furta saɓo saboda jin nauyinsa. Wani ƙasaitaccen murmushi yai mata me cike da ma'anoni da yawa, yace "kina so in zauna?" Ta gyaɗa masa kai. Yace "Da sharaɗi gaskiya" "Sharaɗi kuma?" "Eh mana" ya faɗa yana kwaikwayon ta. Tai murmushi tace "meye sharaɗin"? Yace "Look up" ta ɗago ta kalleshi tai saurin sauke idonta, dan ji tai ba zata iya tsawaita kallon nasa ba. "Kice ki na sona dan Allah" Ba tare da ta kalleshi ba ta ɗan zaro ido tace 'taɓ' "Ba zaki iya ba kenan?" Shiru tai ba tace komai ba. Sadik yace "Farhan kenan, kedai wannan fulatancin naki yayi yawa, shikenan tun da kince in zauna yadda kika ce ai haka za'ayi gimbiyar mata" Yana zama kuma wata kunyar ta sake baibaiyeta tana mamakin kanta, wai ita ce ke cewa namiji ya zauna kar ya tafi, ta sauke nannauyar ajiyar zuciya, farin ciki na ratsata kasancewar ga Prince a kusa da ita" Haka shiru ya wanzu a tsakanin su, Prince ya katse shirun ta hanyar ɗakko mata hirarraki, a haka ta saki jiki suka cigaba da hirar tare. Seda aka kaɗa bell, sannan suka baro Library ɗin tare. Aka kammala jarabbawa, aka shiga shagulgula daban daban a makarantar, kullum akwai abunda za'ayi na nishaɗi, ko dai Quiz, Debate, inter House competitions, da dai games kala kala. Farhan ta so tai zamanta a gida ta dena zuwa tun da hutu za'ayi, amma idan ta zauna a gidan a takure take ga damuwa, dan haka take zuwa school ko ba komai tana ganin abun ƙaunarta tana jin daɗi. ************ "Meena, wai anya lafiyar ki ƙalau kuwa?" "Mum why are you asking? Me kika gani?" "Gaba ɗaya kin ɗashe, se wata uwar rama da kike yi, ga wani uban bacci wanda na kasa gane miki gaba ɗaya" "Am ok fa, kawai weather nan ce is not compostable to me, yau zafi gobe sanyi, and I have no appetite bana iya cin Abinci, shiyasa nake rama But i will be ok insha Allah" "To shikenan, idan kuma ba hali muje Asibiti a duba ki" "No don't mind Mum, sena dawo" "Ok safe journey" Meena ta amsa da "Thank you" sannan tai waje. An taru sosai a gurin hall ɗin makarantar, dan kallon fafatwar da za'ai na Debate, ɗalibai 'yan kallo suna cakuɗe maza da mata, ana kallon fafatawar. Farhan na kusa da Prince, ya bata wayarsa tana kallon pictures ɗin 'yan gidansu, yanayin hotunan nasu ya tabbatar mata da Lallai Prince ɗinta ɗan hutu ne, sannan da alamun akwai kyakkyawar alaƙa da shaƙuwa a tsakanin su. Farhan ta kalli hoton Mother tace "she's Your Mum ko?" "Eh mana, in law ɗinki ce, ai zaku haɗu agurin bikin Brother na, i will introduce you to my Family" Zare ido tai tace "ni dai a'a gaskiya, se ace munyi rashin kunya ai" "Meye wani rashin kunya, gara su sani tunda wuri ai, ko kin manta ina processing yadda zamuyi Aure ne? Gara su san da Maganar tunda wuri" Shiru tai jikinta yai sanyi, duk da maganar Auren da yai yasa jikinta yai sanyi, amma a wani ɓangaren tana fatan Allah ya amince, yasa ta Auri Prince, First love ɗinta kenan, ba ta jin daga kansa zata kuma son wani namiji haka. Ta cigaba da kallon hotunan ta, Sadik ya jiya yana magana da su Nas, yaji suna zancen wani Film. "Nas, kune sarakan kallon series Films, dan Allah in mun bar nan System ɗina na mota, zaku turamin fina finai masu kyau sosai" Amin yace "Allah mutumina, ka shigo layin kenan?" Sadik yace "wani layin kenan?" Nas yace "layin eh mana" Sadik yai tsaki yace "Malam ba wannan haukan nace ba, just normal films nake so na Soyayya, za'ai hutu bayan bikin nan ina so zan kalla, ina son wanda ake soyaya sosai a ciki" Amin yace "ji shi wai wani na Soyayya, se kace soyayyar suka iya, banda ƙauyanci da soyayyar yara ba abunda suke" Farhan ta ɗago ta kalli su Amin, ta ja ƙaramin tsaki wanda Sadik ne kawai yaji, yai murmushi yace "don't mind them Baby, kar su mayar min da ke mafaɗaciya, i love Your silent character" Farhan tace "ai ni ba faɗa zan ba" "Ai tunda kika fara tsaki, nasan faɗan ma zakiyi ne" Tai shiru ta cigaba da abunda take. Sadik yace "Nasir zaku turamin ko kuwa?" Nasir ya kashe ido ɗaya yace "meze hana a turamaka ranka ya daɗe, akwai korean, indian, American Chinese and many hot Love series, depending on which you wish to watch" Sadik yace "Kawai me kyau nake so" "Shikenan, bari a tashi daga nan ɗin, za'a tura maka Insha Allah" Suna cikin maganar sega Babba ya nufo su, yana tunkaro gurin Farhan ta haɗe rai, jikinta ya hau tsuma, saboda yanzu a Duniya ta tsani ko ganin Mubarak. Ya faki idon Sadik ya kashe mata ido, ta galla masa harara ta ɗauke kanta. Ya zauna kusa da su Sadik ya miƙa musu hannu, su kai musabiha, miƙewa Farhan tayi zata bar gurin, Sadik ya kalleta yace "ina zaki kuma?" Ɗan yatsuna fuska tayi tace "can zan koma" Sadik yace "ok as you wish my love" Tai masa guntun murmushi, ta koma cikin 'yan ajinsu mata, da suke ta zuba hira, gefen su kuma 'yan ajinsu Sadik ne, su Taslim da Meenal. Can kuma ana can ana ta faman Debate, amma hankalin su ba'a akan abunda ake yake ba. Su Lilly kam banda hirar litattafan da suke karantawa a Online ba abunda suke yi. Taslim ta dubi su Lilly tace "Lilly, me kuke Magana a kai ne?" Lilly tace "bakomai fa" "A'a naji kamar kuna hirar romantic book ne na hausa" A ɗan tsiwace Lilly tace "eh" "Dama akwai romantic books na Hausa?" Taslim ta tambaya Lilly tace "eh, akwai masu zafi ma kuwa" Nan Taslim ta dinga lallaɓa su Lilly, suna bata labarin litattafn da suke karantawa a Online. Gaba ɗaya hirar tasu ta gunduri Farhan, su gaba ɗaya makarantar daga mazan har matan tunanin su iri ɗaya ne, duk wata harka ta watsewa su ita suke so. Haushi ne ya kuma kama Farhan, ta Tashi ta bar hall ɗin gaba ɗaya ta fito, zagayen ta ta shiga yi a makarantar, tana 'yan leƙe leƙen ta, makarantar shiru kamar ba kowa duk suna hall ɗin da ake gabatar da Debate ɗin. Katsam idonta ya sauka akan corper George a cikin wani aji, abunda idanuwan ta su kai katarin gani ne ya kiɗimata, wanda har ya kusa awon gaba da nutsuwar ta na wani ɗan lokaci, a very deep Romance with his ss3 student, she don't even know the name of the lady, ta san dai shine class mastern finalist student ɗin. Jikinta ne ya hau wata irin tsuma, kuma ta kasa motsi daga gurin, se idanunta da take ta faman jujjuyawa kamar taiwa Sarki ƙarya. Ba tsammani George ya waigo ya ga Farhan tai musu ƙuri da ido, da sauri ya cika Nasreen, ɗalibar da suke watsewa taren, yana ƙoƙarin tattaro nutsuwarsa ya daidai ta. Ganin da Farhan tayi sun ganta Ya bata ƙwarin gwiwar, fizgo kuzarin da ta rasa na wani ɗan lokaci, cikin sassarfa ta ja da baya cikin hanzari ta nufi hanyar da ta sauka daga kan benen. Kana ganin ta kasan a firgice take, kamar wadda ke shirin zarewa, ba zato ba tsammani tai karo da Sir Nazir yana ƙoƙarin hawowa kan benan. Cak ta tsaya tana cigaba da rarraba ido, kamar mara gaskiya. Kallon tuhuma ya bi ta da shi, yana ƙare mata kallo yana son gano me ya razanata haka, fuskarta take bayyanar da alamun rashin gaskiya? Hanya ta bashi, dan ya wuce sannan ita ma ta wuce, amma ya tsyaa kyam yana cigaba da kallon ta. Ba tsammani taji muryarsa yace "me kike yi a nan?" Girgiza masa kai tayi tare da faɗin "Nothing sir" "Nothing as how? Ke da waye a saman gurin nan, bayan ba kowa duk ana hall ɗin da ake Debate?" Rasa amsar da zata ba shi tai, ta cigaba da tsatstasare shi da ido. "Ke da wannan shashashan yaron ne a saman ko?" A razane ta kalli Sir Nazir, tana son tabattar da abunda yake faɗa. Ganin Farham taƙi magana ta cigaba da bin sa da idanu ya sa ya ji zargin sa na neman zama gaskiya. "You Are Much more than stupid Farhan, ki cigaba da biyewa RUƊIN ƘURUCIYA, Kina rusa Rayuwar ki, nan gaba se kin yi kuka da idonki, a lokacin da kuskuren da ki kai ba ze gyaru ba, ki cigaba da ba shi damar keɓewa da ke, sheɗan na buga muku ganga, nan gaba zaki gane shayi ruwa ne stupid girl" Maimakon ya hau saman benen, se ya fasa ya juya ya sauka, zuciyarsa na ƙuna, ganin yadda rayuwar yara mata masu ƙananun shekaru, ke lalacewa saboda RUƊIN ƘURUCIYA. Farhan kuwa kasa matsawa ta yi daga in da take, maganganun sir Nazir suka cigaba da sukar zuciyarta, yana zarginta da wani abu, wanda ba shi da tabbas a kai, dan duk wannan masifar da yake a yanzu, bashi da wata hujja da ze kafa, akan ta, amma ya sa mata ido yana binta da miyagun maganganu, tabbas duk da ƙanƙantar shekarunta, tasan idan har aka zarge ka da keɓewa da wani namiji, to kuna aikata wani abune da be kamata ba, take ta tuno abunda ta gani yanzu a saman benen, kenan da irin abun Nazir yake zarginta kenan?. Hawayena ya shiga bin fuskarta, fan take ta ji ranta yai ƙololuwar ɓaci, haka ta sakko jikinta a sanyaye ta tafi hanyar gate ɗin fita ta zauna, ana kaɗa jiniya, tai gaba ba tare da ta jira kowa ba. Tun ranar da Nazir yai mata wannan zargin, gaba ɗaya se ta tsargu take ganin kamar kowama haka yake kallonta, dan haka kasancewar da ma sun kammala jarrabawa, ba ta sake zuwa makarantar ba har aka yi hutu. Hakan ya damu Sadik sosai, ganin ba ta zuwa har a kai hutu, ranar da za'ai hutu ya zo da system ɗin sa, aka tura masa fina finai, wanda ze dinga kallo kan a koma school. Satin da a kai hutu, a satin za'a fara bikin Ussy, ana ta shirye shirye, mussaman Sadik ya bugo nasa invitationsa ɗin, da ze rabawa abokan sa. Gefe ga son ganin Farhan da yake yi, gashi yasan gidan su Farhan Akwai tsaro sosai, dan mahaifinta malami ne, idan ya je gidan su Farham be san me zece ba. Shiryawa yai, ya tafi gidan su Khairat, a falo ya tarar da ita tana cin Abinci. Sadik yace "Ina Mama?" "Ba ta nan, lafiya na ganka kamar an jefo ka? Ka wani sha Manyan kaya kamar wani ango, ni na taɓa ganin ka a manyan kaya kuwa?" Sadik yace "Khairat gidan su Farhan na ke so ki rakani dan Allah" Yamutsa fuska Khairat ta yi tace "wace hakan?" "So nake na bata invitation, tace idan ban kai mata gida ba baza'a barta taje ba, ni kuma i dont know how to explain myself idan naje, shiyasa nace bari in zo muje tare" Khairat tace "to ai ita Farhan ɗin nake son jin wacece?" " 'yar ajinmu ce" ya bata amsa. "Gaskiya ban yadda ba, kana yawan kirana da Sunan ta, ko 'yar ajin ku ce akwai wani abu a tsakanin ku" "Eh budurwa ta ce" Yatsuna fuska Khairat tayi tace "kuma shine ni zan raka ka?" "Kinga idan ba zaki ba ba se kin rainamin hankali ba" ya faɗa a kausashe. "Naji zani" ta faɗa cike da ɓata rai. Ta tashi taje ta canza kaya, ta fito ta tarar da shi in da ta barshi. Yau Sadik da kan sa yake driving, suna tafe yana tsarawa Khairat abunda za su faɗa. A bakin layin su Farhan yai parking, gabansa se faɗuwa yake, ya hango mahaifin Farhan zaune a kan dadduma, yana tilawar Alƙur'ani. Khairat kuwa ganin gidan da Sadik ke dosa ya sa ta ɓata fuska, tun daga farkon unguwar kasan ta talakawa ce, ko ina kwata, se wari kwatocin ke yi, ga wasu gungu gungun awaki da tumaki da ke kaiwa suna komowa a tsakanin layukan. Ga kaji da ke ta sake haƙe kwatar da aka kwashe aka zubar a gefen hanya, gaba ɗaya haushin Sadik Yakamata, gasky Prince ya faɗo ya rasa in da ze samo budurwa se a wannan unguwar talakawan, sedai ba ta da ikon Magana, yanzu ze hayayyaƙo mata, haka tai shiru ta cigaba da bin sa. Suna zuwa in da Mahaifin Farhan yake, Sadik ya samu guri ya ɗan risuna. Mahaifin Farhan ya rufe Alƙur'anin gabansa ya kalli Sadik da Khairat, yace "Sannun ku da zuwa" Sadik ya ƙara nustuwa yace "Abba ina wuni" Baban Farhan yace  "Lafiya ƙalau Alhamdilillah, ya gida?" Sadik ya ƙara nutsuwa yace "Lafiya ƙalau Alhamdilillah, dama ni ɗan makarantar su Farhan ne, wannan ƙanwata ce ajinsu ɗaya da Farhan a Makaranta, Yayan mu ne ze Aure, shine muka kawo mata katin gayyata ko za'a barta taje" Sadik yai maganar tare da ɗakko katuna a aljihunsa ya miƙawa Baban Farhan. Ya sa hannu ya karɓa ya duba, ya kalli Sadik ya jinjina kai, dan sunan mahaifinsa d sananne ne, ya ƙara tabattar da Allah ne kawai ya yi Farhan za tai wannan Makaranta, ban da haka ina ita ina karatu da 'ya'yan Alhaji Abdullahi. A fili yai murmushi yace "Masha Allah, ai komai da sanarwa yana da daɗi, Allah ya sanya Alkhairi, shiga ki kai mata katin" Khairat ta karɓa, ta nufi gidan da mahaifin Farhan ya nuna mata, tana sake tsantsame jikinta, dan ita ƙyamar gurin take. Baban Farhan yana da kirki sosai, ya din ga jan Sadik da hira, tun Sadik na jin nauyin sa, harya saki jiki suka cigaba da hira sosai. Yadda Sadik ya zo cikin shiga ta mutunci da girmamawa, ba ƙaramin burge mahaifin Farhan yai ba. Khairat kuwa sallama ta yi tana ƙarewa gidan kallo. Gidan tsaf da shi, ko tsinke ba bu a tsakar gidan, se ƙamshin turaren wuta da ke tashi. (Dama ita tsafta ai ba se me kuɗi ba) Sallama Khairat ta yi, ta tsaya a tsakar gida, Umman Farhan ce ta amsa mata, sannan ta bata izinin shiga. Ta shiga ta gaida maman Farhan, ta amsa mata cikin kulawa. Khairat tace "dama gurin Farhan na zo, na kawo mata katin bikin yayan mu" Umman Farhan tace "Allah sarki, Allah ya sanya Alkhairi. Ta nunawa Khairat ɗakin da Farhan ke ciki. Ta shiga ta tarar da Farhan, sanye da dogon hijjabi ta na karatun Alqur'ani. Khairat ta samu guri ta zauna, Farhan ta dakata ta kalli Khairat, dan ba ta santa ba "Sannu da zuwa" Khairat tace "Yawwa, Farhan ko?" "Eh, sedai ban ganeki ba" "Ƙanwar Sadik ce" Kunya ce ta kama Farhan, tai murmushi tace "Allah sarki, sannu bari in kawo miki ruwa" Khairat tace "No, ba se kin kawo ba, dama katin gayyata ne na bikin Yayan sa, yace mu zo mu kawo miki yana waje, idan da hali yana san ya ganki" Shiru Farhan ta ɗanyi tace "ai ban san yadda zan fitan ba ne, ina jin tsoro Abba na yana nan" Khairat ta ɗan ƙare mata kallo a ranta tace 'taɓ, rayuwar yaran talakawa ba tai ba sam, wace irin jaraba ce wannan dan baban ka yana nana ace ba zaka fita ba?' A fili tace "ai ba daɗewa za ki ba, kice kawai zaki rakani ne, se muje ku gaisa kawai" Har ga Allah, Farham na son ganin Sadik, cikin sanyin jiki ta miƙe ta tafi ɗakin Umman ta, ta nemi iznin raka Khairat, ga mamakin ta se Umma ta amince, har da bawa Khairat ɗin kyautar turare, zaton ta ƙawar Farhan ce. Khairat kuwa a ranta mamakin irin wannan rayuwa take, saboda tsabar abu Yarinyar ko wayon yadda zata fita ba ta da shi, fita rakiyar ma seta tambaya, lallai 'ya'yan talakawa na rayuwar takura da rashin 'yanci. Cike da faragaba ta bi Khairat suka fita, cikin sa'a da suka fito baban Farhan ba ya ƙofar Gidan. Ta hangi Sadik zaune akan barandar da ke gefen gidan su, ya sha shadda dark blue, harda hula kai kace wani babban mutum ne, ba ta san lokacin da ta saki wani ƙasaitaccen murmushi ba, shima ɗagowa yayi ya kalleta yai mata murmushin, tare da sauke ajiyar zuciya a jejjere. Suna zuwa in da Sadik ke zaune ta sunkuyar da kai, tana wasa da yatsun hannunta. Sadik yace "Madam kawai se nemanki nai na rasa a makaranta, ki ka dena zuwa why? Ki ka bari ina ta cigiyar ki" Kasa Magana tayi, saboda fargabar kar wani ya ganta ko babanta ya dawo, ga Khairat a tsaye a gurin. Ganin yadda ta kasa sakewa, ya sa Sadik yace "zo muje daga bayan layin ku naga You are not comfortable here" Duk da Farhan na cikin fargaba, amma ba zata iya yiwa Sadik musu ba, ta bisu suka nufi in da sukai parking. Suna zuwa Khairat ta buɗe gaban mota ta shige, ta bar Sadik da Farhan. Ganin Khairat ta basu guri, yasa Farhan yin ajiyar zuciya tace "ina wuni?" "Se Yanzu zaki gaishe ni, kin ƙi ko kallona se wani ƙasa kike da ido kina kallo na, ki ɗago ki kalleni sosai" Murmushi tai, ta rufe fuskarta tace "kayan nan sun maka kyau" Sadik yace "dagaske?" Ta jinjina kai alamar eh. Yai murmushi yace "Alhamdilillah, Tunda sun burgeki, na haɗu da Abba a waje, munyi hira da shi sosai, Your father is very kind, Allah yasa idan aka zo nema min Auren ki ya bani, kar yace nayi yaro da yawa" Shiru tai ta sake sunkuyar da kanta tana murmushi. Shima murmushin yai yace "Anyway, meyasa ki ka dena zuwa school?" Gaban ta ne ya faɗi, da tuna abunda sir Nazir yake zarginta da shi, a zahiri ta basar tace "Nothing naga ba'a komai ne a school ɗin" "Shine, kika dena zuwa duk tunanin ki ya dameni, ga shi ba ki da waya balle in dinga kiran ki a waya" Tai shiru ba tace komai ba. Sadik yace "yanzu dai zaki zo bikin yayan nawa?" Farhan tace "Ai ka kawo katin gayyata, za'a barni insha Allah" Murmushi Sadik yai, wani farinciki ya kama shi, yace "Alhamdilillah, naji daɗi sosai" Farhan tace "meyasa kake murna dan zan zo?" Ya so ya gaya mata dalilin sa, amma se ya fasa dan yasan tsaf zata fasa zuwa,  ya gyara tsayuwar sa yace "My dan Allah ya zan dinga samunki a waya ne? Kin ga hutu za'ai ina son in dinga jin muryar ki, ko in dinga zuwa gida in ganki?" Zare ido Farhan tai, ta girgiza masa kai tace "A'a, Abba ze tambayi dalilin zuwanka" "To meye a ciki? Se mu faɗa masa gaskiya" "A'a dan Allah kar ka dinga zuwa" Sadik yace "to naji, yanzu ki bani lambar da zan dinga kiran ki in same ki a waya" Farhan ta ɗan yi shiru, dan tabbas ita ma tana son hanyar da zata dinga waya da shi, dan ko ba komai a yanzu bayan karatun ta ba wanda yake ɗebe mata kewa sama da Sadik. A hankali tace "ka bani lamabar wayar ta ka, idan na samu waya ni se in kira ka" Yace "ki min ko flashing ne, ni kuma zan kiraki insha Allah" Ya ɗakko jotter ya rubuta mata ya bata. Tace "Bari in koma gida, kar a fara nema na" "Ok to shikenan, amma tsaya muyi hotuna, wand zan din ga kalla ina jin daɗi" Ba tace komai ba se murmushin nan nata me ɗaukar hankali. Ya ciro wayarsa yai mata hotuna, sannan ya kalle ta yace "se Allah ya kaimu Lokacin bikin, i love You, take a good care of yourself" Juya tai tana murmushi ta na jin yadda kalaman nasa ke sake tasiri a zuciyar ta. Shi kuma ya koma motar su. Yana shiga Khairat tai tsaki. Ya kalleta yace "ke kuma lafiya?" Khairat ta yamutsa fuska tace "kai kam me ka gani a wannan bagidajiyar 'yar talakawa?" A hargitse Sadik ya kalleta yace "wallahi ki ka kuma zaginta sena miki rashin mutunci, a haka nake sonta" "Allah ya baka haƙuri, amma gaskiya ta fiye kidahumanci, ace dabarar da zatai ta fito ma se da na gaya mata, ta fiye tsoro gashi kamar ba wayayyiya ba, ga ta yarinya sosai" Sadik be ce mata uffana ba ya fara jan motar, jin yai mata banza ya sa ta ja bakinta ta tsuke, dan ta san idan ta matsa kuma, faɗa za suyi. Suna tafe lokaci lokaci, seya shafi sumar kansa yai murmushi, yana jin so da ƙaunar Farhan ɗin na ratsa shi. Kai tsaye gidansu suka wuce, suna zuwa yai parking a waje ya kalli Khairat yace "sauka, ni zani wani guri ne yanzu, maybe za'a kawomin wandon jeans, ki karɓa ki bawa Mother ta ajiyemin" Khairat ta ɗan taɓe baki tace "to" ta buɗe motar ta fice, shi kuma ya ja motar yai gaba. Khairat kuma ta shiga cikin gidan, sosai gida ya fara ɗaukar harami, saboda shirin shiga hada hadar biki. A falo Khairat tai karo da Nana, tana ta hira ita da talatu me aiki, ta kalli Nana tai tsaki. Nana ta kalli Khairat tace "Sannu tsaka" Ba ta kuma kula Nana ba, ta shiga Kitchen ta ɗakko madara a roba, ta dawo falo ta na sha. Dawowarta babu daɗewa, Sadik ya kirata a waya. Ta ɗaga tace "Yaya ina jin ka" "Kije gate ki karɓo min saƙon nan ki ajiyemin" Khairat tace "to" Ta ajiye robar hannunta ta fita, ba daɗewa ta dawo hannunta ɗauke da wata leda me kyan gaske. Ta zauna ta buɗe ledar ta fito da wani haɗaɗɗen wandon jeans, kai da gani kasan wandon me tsada ne sosai, sedai abun takaici duk an yayyaga wandon ta cinya zuwa gwiwa, kamar kare ya tattauna. Nana ta kalli wandon a ranta tace 'wannan wane irin wando ne?' Faruk da ke fitowa daga ɓangaren Mother yace "Khairiyya, wannan wandon fa?" Khairat tace "Wandon Prince ne, yace in karɓa in bawa Mother ta ajiye masa, kuma ban ganta ba" Faruk yace "wannan wandon na ganshi Online ana advertising ɗin sa, yafi dubu goma a kuɗin Nigeria" Khairat tace "Ai Sadik akwai rigima in yaso abu, amma wandon yayi kyau sosai" Faruk yace "hakane, ina ga dai Mother ba ta nan, amma ki ajiye masa shi a wani gurin" "Ko kuma in baka ka ajiye masa?" Faruk yace "No, ajiye masa, Mother yace ko bawa, akan wandon nan se ya ɗagamin hankali" Khairat tace "ok bari in Ajiye masa kawai" Nana kam jinjina lamarin ta cigaba da yi a zuciyar ta, yanzu wannan wandon me kama da tsumma ne wai yafi dubu goma, gaskiya mutan Gidan nan ba su san darajar kuɗi ba, wannan ai almubazzaranci ne" Faruk kuwa tuni ya bar falon, Wayar Khairat ce ta fara ringing, dan haka ta miƙe ta fita waje dan ta amsa wayar. Tana fita zuciyar Nana ta dinga raya mata abubuwa daban daban, dama a ƙule take da Sadik da Khairat ɗin gaba ɗaya, dan haka ta miƙe ta waiga falon taga babu wanda yake kallonta. A hankali ta ɗau ledar da wandon yake, ta ciro wandon ta zura a hijjabin ta, ta zaga kan baranda ta samu wani ruwan mopping da aka gama mopping da shi yai baƙiƙirin saboda datti, ta zura wandon a ciki. Seda ya naɗi ruwan dattin nan Sosai Sannan ta matse shi, ta yar a gurin ta ƙara gaba. A ranta tace "gobe ma ka sake zagina da kai da wannan shashashar Khairat ɗin, zaku gane kuren ku" Ita kam Khairat ko da ta koma, ta cigaba da sha'anin ta, ta manta da batun wandon Prince. WANDA SUKA RIGA SUKAI PAYMENT, IDAN FREE PAGES SUKA ƘARE SU KAWAI ZAN TURAWA TA WHAT'S APP, WANDA BE PAYMENT BA ZE IYA SA A MANHAJAR AREWABOOKS, DAN YAFI SAUƘI. DOMIN GYARA, SHARHI KO SHAWARA Ayshercool 07063065680. [6/4, 4:21 PM] Jakadiyar Arewa: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ RUƊIN ƘURUCIYA PERFECT WRITERS ASSOCIATION (WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS) https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ P. W. A *Story and written by* AISHA ADAM (AYSHERCOOL) Writer of WATA KISSAR..(Sai mata) ABDUL JALAL AƘIDATA (paid book) WUTA A MASAƘA NOW RUƊIN ƘURUCIYA (paid book) _Labarin RUƊIN ƘURUCIYA, na iya zuwa da wani salo, wanda baku saba ganinsa a rubutuna ba, hakan ya biyo bayan akan abunda aka gina labarin, wani abun ze ɓoyu wani Abun baze ɓoyu ba sakamakon labari ne akan teenegers, yara masu tashen Balaga, but hakan ba ya na nufin na sauka daga kan tsarin yadda nake Rubutu bane, ƙofata a buɗe take dan karɓar ƙorafi, gayra ko shawara_ ⚠️⚠️⚠️ƘIRƘIRARREN LABARI NE, BAN YADDA A JUYAMIN SHI TA KOWACE SIGA BA SEDA IZININA ❌❌‼️       SHIN KUNA DA LABARIN MANHAJAR AREWABOOKS KUWA? MANHAJA CE DA TAZO DA TSARIN DAN SAUƘAƘAWA MARUBUTA DA MAKARANTA SAUƘIN CINIKAYYAR LITATTAFAI. TA IN DA ZAKU IYA SIYAN KOWANE FEJI AKAN KUƊI ƘALILAN, DAI DAI DA ALJIHUNKU. INA FARINCIKIN SANAR DA KU CEWA, DA ZARAR NA KAMMALA FREE PAGES, ZAKU CIGABA DA SAMUN CIGABAN LITTAFIN RUƊIN ƘURUCIYA, AKAN MANHAJAR AREWABOOKS. KARKU BARI A BAKU LABARI, AKWAI TARIN DARASIN RAYUWA A CIKIN LITTAFIN. 19_20 Nana kam zuba ido ta yi ta ga yadda za'a kaya da wannan rigima. Wandon Prince kuwa tuni ya koma tsumman ƙarfi da yaji, saboda yadda aka dinga sauke tukwane da shi. Wandon yai baƙi ƙirin ya fita daga hayyacin sa. Sadik kuwa da ya tafi nasa yawo be dawo ba se wajen sha ɗaya na dare. Da takeaway ɗin sa ya dawo, dan karma ya shiga cikin gidan su, ya haɗu da Yarinyar da yafi tsanar gani wato Nana. Ya so ya shiga gidan ya ga wandonsa, amma ya fasa ganin dare yayi, ya wuce part ɗin su. Usman na kallon sa Sadik ya zo ya wuce, ya shige bed room ɗin sa, ya zauna yaci Abincin sa, yai wanka sannan ya nemi guri ya kwanta, sedai kwanciyar ta sa ke da wuya, yaji yanayin da ya saba ji ya fara bijiro masa, take bacci ya ƙauracewa idonsa, se tunanin Farhan da ya dinga masa yawo a ka. Duk yadda ya so ya rintsa amma abu ya gagara, se juyi kawai da yake akan gado, ya rintse idanun sa sosai amma ba abun da ya sauya daga yanayin da ya ke ji. Duk da yanayin da yake ciki, ba ya hana shi murmushi, lokaci lokaci idan ya tuna Wasu daga halayen Farhan, na tsoro da kuma tsananin Kunya. Abu kamar wasa Bacci ya gagari Sadik, maimakon ya tashi ya ɗau carbi, ko yai salla kawai se ya janyo laptop ɗin sa, ya kunna. Films ɗin da su Nasir suka tura masa, ya buɗe ya fara kallo da nufin ko ze manta da abunda ke damun sa. Sosai ya nutsu ya fara kallon film ɗin, kamar wasa film ɗin ya burgeshi yaji yana son ganin yadda za ta kaya. Da ya gama episode ɗaya idan yai niyyar kwanciya, se yaji lallai yana son ganin me ze faru a next episode. A hankali Film ɗin ya cigaba da burge shi, Soyayya ce me tsayawa a zuciya tsakanin Jarumin film ɗin da jarumar film ɗin, kasancewar film ne na masarauta, shi ɗan sarki ita kuma baiwa ce a gidan. A hankali kuma Film ɗin ya fara canza salo zuwa wani abu daban, yadda aka fara bayyanar da abunda ya zarce ƙa'ida. Da fari ya fara jure kallon cuddling da kisses da ake nunawa, ya dake ya cigaba da kallon, a hankali kuma aka fara zarce wannan matakin aka shiga nuna romance tsakanin jaruman, da yadda yake samar musu da meeting point, a cikin wani lambu, yaje suyi hirar su ta masoya ba tare da kowa ya sani ba, wanda a nan ne a hankali suka fara da kissing. Series ɗin yai matuƙar burge Sadik, sedai fa kansa ya soma cigaba da wuta, dan baze iya jure abunda yake cigaba da kallo a system ɗin ta shi ba. Kashe system ɗin yayi ya saketa ta faɗa ƙasan gado, ya dafe kansa tare da cije laɓɓansa na ƙasa, ya firzar da wata iska yace "Subhanallah, Nas why? Meyasa zaku turamin irin wannan Film ɗin?" A hankali ya tashi, ya tafi toilet yai wanka da ruwa me sanyi, ya dawo da ga shi se boxers ya kwanta. Wayar sa ya laluba, ya nemo hotunan Farhan da yai mata ɗazu. He Just stat zooming her beautiful face, seda hoton fuskar tata ya cika screen ɗin wayar ta sa. Ya ƙara zooming ɗin hoton, kyawawan leɓenta suka bayyana Sosai, da fararen haƙoranta kasancewar ta yi murmushi a hoton. He just start imagine himself kissing that her beautiful lips. Ya dinga sauke ajiyar zuciya a jejjere, a hankali ya ajiye wayar ta sa, yai ruf da ciki a kanta, tare da ƙanƙame pillow, yana jin yadda zuciyar sa ke harbawa da sauri, ga wani abu da ke masa yawo tun daga kan sa har ƙafafuwan sa. A haka bacci yai awon gaba da shi. Seda Sadik ya makara sallar Asuba, dan be kwanta da wuri ba, ga tarin mafarkai barkatai da yai tayi. Ya tashi yaje yai wanka yai sallar Asuba, ya koma bacci. Se wajen tara da rabi Sannan ya fito falon su dan yin break fast. A falon ya tarar da Faruk shima yana karyawa, ya nemi guri ya zauna yana ta wani ciccin magani, kamar wanda aka tursasa yai wani abu da baya so. Faruk ne yace "naga wani wando a gurin Khairat, tace min naka ne, wandon yai kyau sosai" Se yanzu wandon ya faɗowa Sadik a rai yace "Eh jiya aka kawo shi, se na shiga gidan yanzu zan nemota ta bani" Faruk yace "good" daga nan ba wanda ya kuma cewa komai, Sadik ya ɗebi Abincinsa ya koma gefe. Farhan kuwa da ta koma gida, kyakykyawar ajiya ta yiwa lambar Prince, ta na yi ta na murmushi idan ta tuna yadda ta ganshi cikin manyan kaya, ba ƙaramin kyau yai mata ba. Haka ta ƙarasa wunin ranar cikin annashuwa da farinciki, lokaci lokaci ta kan ɗakko takaddar da ya rubuta mata lambar sa, dan jin ƙamshin turarensa da ke jikin takaddar. Da safe kasancewar ba makaranta, yasa Farhan ta kammala ayyukanta na gida gaba ɗaya, ta koma ɗakinta tana karyawa. Umma ce da Abban ta zaune a tsakar gida suna karyawa, can Abban Farhan yace "jiya yaran nan da suka kawowa wannan Yarinyar katin gayyata, 'ya'yan Alhaji Abdullahi me turare ne fa" Umma tace "Ikon Allah, ina ta samo yaran wannan mutumin?" "Ahh makaranta mana, kin manta makarantar da take yi ne?" Umma tace "ban manta ba, ni dai ina fatan ta kammala Makarantar nan Lafiya a aurar da ita, dan ina jin tsoron cuɗanyar su ita da yaran masu kuɗi" "Haba ki zama me kyautata mata zato mana, mun san tarbiyyar da muka bata ai, kuma ni yaran na gansu a nutse, ba rawar kai shiyasa na bar yarinyar ma ta shigo, kuma ni da ki kai zancen ta gama Makaranta a aurar da ita se ki ka tunanin da batun Yaron nan Sunusi" Umma tace "Wane Sunusin kenan?" "Sirikin ki mana, Wannan ba barbaren yaron, babban Almajirin malam Abbas. Na yaba da hankalin Yaron sosai, Malam Abbas ɗin ne da kansa ya zo min da zancen ya na son in bawa Sunusin Auren ta, ni kuma na gamsu da nustuwar yaron, nace masa ba damuwa amma ya bari ta ɗan ƙara girma kan ayi Magana" Umma tace "Alhamdilillah, Allah ya tabattar da Alkhairi, tana gama wannan Makarantar se ayi Magana, Allah ya tabattar da Alkhairi" Ƙosan da Farhan ke taunawa a bakinta, tafi ƙarfin mintuna tana kokawa da shi amma yaƙi haɗiyuwa, ji tai gaba ɗaya test ɗin bakinta ya ɗauke. Gaskiya Sunusi be mata adalci ba, gaisawa ce da girmamawa tsakaninta da shi, dan me za'ai mata haka? Gaba ɗaya, ba ya cikin tsarin ra'ayinta, ba ta san me ake ji a so ba, se akan Prince ɗinta, gashi ɗan gaye me aji, gashi me kyau, ina zata kai Sunusi, ga baƙi kamar an rina shi, ga tsagu a fuskarsa kamar ƙwarya, seya shafe sati yana saka yadi ɗaya, dama batun gayu babu shi, sedai Sunusi akwai haddar Alqur'ani me girma, dan gwani ma ake cema sa, da ka yake Rubutun Alqur'ani. Ya san Alqur'ani sosai da sosai, sedai bayan ilimin Alqur'anin nan babu na hadisi, babu na fiqihu, amma idan ya zauna ze iya gaya maka adadin ayoyi na kowacce sura a cikin Alqur'ani, sau nawa Allah ya ambaci kowane Annabi, sau nawa sunayen Allah suka zo a Alkur'ani, adadin sunan Allah nawa ne a Alqur'ani da in da aka ambace su, duk da ka yake irin wannan abubuwan. Duk da fankar ɗakinta na ta uban gudu ta na bada iska, Amma ita wata irin zufa takeyi, sam ta kasa samun nutsuwa. Ummanta kuwa cigaba su kayi da hirarsu, yayin da Farhan kuwa ta shiga cikin zullumi da damuwa, dan ita a duniya yadda take ji a zuciyar ta, idan har ba Sadik ba, ba zata iya auren kowa ba. Duk da ana yawan faɗa mata Soyayyar su RUƊIN ƘURUCIYA ce kawai, kuma babu lallai ya Aureta, amma ita yadda Sadik ɗin ke nuna mata ba ta jin ze kasa Aurenta, Amma idan aka haɗa ta Aure da Sunusi an gama cutarta, yanzu ta san ciwon kanta, ta gane menene so meye daɗin sa, sam zuciyarta ba zata iya karɓar Sunusi a matsayin mijin Aure ba!. Sadik kam cikin gida ya shiga, yana zuwa ya tarar da Inna a falo Nana na kusa da ita, da sauran ma'aikatan gidan da ke ta shige da fice, da fara shirin karɓar baƙi, dan saura kwana biyu a fara biki, gidan a cike yake da mutane. Sadik na ganin Inna ya ɗan ɓata fuska dan baya son damuwar tsohuwar nan, amma ya basar ya ɗan risina yace "Ina kwana?" Inna ta ɗaga kai ta kalli Sadik, ta ɗan yi murmushi me cike da ma'anoni tace "lafiya ƙalau ka tashi lafiya?" "Lafy ƙalau" ya amsa tare da miƙewa ze tafi. "Su sauran jama'ar ɗakin ba zaka gaishe su bane?" Haushi ne ya kama Sadik, ita dai tsohuwar nan ba ta san zaman lafiya kwata kwata, tun da dai ya gaisheta meye na wani seya gaida sauran mutanen ɗakin?" Juyowa yai ya tsurawa Innan ido amma yaƙi magana. Nana kuwa zuciyarta se dukan bakwai bakwai take, tana fargabar kar ya gano waitar da tai masa. Ana haka sega Mother ta fito, akan Sadik ta fara sauke idonta tace "Sadik har ka tashi da safen nan haka?" Inna ta kalli Mother, kusan ƙarfe goma na safe, amma tana kiran har ya tashi da safen nan. Sadik cikin shagwaɓa yace "Mother, ina wandona?" "Wane wandon?" Ta tambayeshi cikin rashin fahimta. "Wanda Khairat ta baki ko ajiyemin" ya bata amsa. Mother tace "A'a ba ta bani komai in ajiye maka ba, ni yaushe rabon da in sa Khairat a idona ma?" Sadik yace "jiya fa nace za'a kawomin saƙo ta karɓa ta baki ko ajiyemin" "To ni ba ta bani ba, kuje can ku ƙarata" Sadik ya ɗan fesar da iska daga bakinsa yace "yau a nan gidan ta kwana?" "A'a a gidansu ta kwana, amma nasan anjima kaɗan zasu zo" Be ce komai ba ya jinjina kai ya bar falon. Inna ta ɗago ta kallesu kawai ta girgiza kai. Nana kam cikinta ya fara ɗurar ruwa, dan idan Asirinta ya tonu ta shiga uku. Nan ta ga sam ba ta kyauta abun da tayi ɗin, be kamata ace tayi haka ba, duk da a ƙule take da Sadik da Khairat tayi hakan ne dan huce takaicin wulaƙancin da suke mata, amma kuma se taji gaba ɗaya ba ta kyauta ba. Wajen ƙarfe sha ɗaya Khairat suka zo gidan, ita da 'yan gidansu, se iyayin yawon karɓar ɗinki da zuwa gurin Saloon take yi, gaba ɗaya ta manta da batun ajiyar Sadik. Kamar an jefo shi se ga shi ya kuma dawowa, ya tarar da Khairat ɗin a falo, ita da wasu 'yan uwansu zasu koma gurin tela, Mother na musu sautu. "Malama ina kayana?" Shine abunda yace da Khairat ba tare da ya kula kowa ba. Tana ganinsa gabanta ya faɗi, dan gaba ɗaya ta manta, se kuma ta ga kamar ta bawa Mother ai. "Na bawa Mother tun jiya" "Na tambayi Mother ai, tace baki ba ta ba, ina kika ajiyemin kayana?" Mother tace "Ni baki bani komai ba" Nan Khairat ta shiga wulƙita idanu, dan gaba ɗaya ta manta da batun wandon nan ta shiga sabgar ta. Cikin zafin rai Sadik ya daka mata tsawa "ina wandona malama?, ina miki magana amma kin tsaya kallo na" "Am..wallahi Sadik ni kamar Mother na.." "Dalla rufemin baki, wallahi sekin nemo min abuna, daga cewa ki karɓi abun ki bawa Mother ta ajiyemin seki ɓatarmin, a haraba fa naga ledar kamfanin wandon tana yawo, duk in da yake ki nemo min abuna na gaya miki" Duk Wannan bala'in a gaban babar Khairat ɗin Sadik ke zazzaga mata, ba ta ido ba Komai haka ya rintse ido yana masifa. Mother tace "Kai dai ka cika rashin haƙuri, Khairat kiyi tunani ina kika ajiye masa?" Khairat da idonta ya cika da ƙwalla tace "I can't remember, na zata na baki ne, kuma yan... "Wallahi sekin nemo min, na gaya miki gobe in Allah ya kaimu zanyi amfani da shi, ki nemomin kayana kawai, careless girl" Nana kam se hailala da salati take, kar a ɗago wannan ɓarnar da tayi. Sadik kam yana uban huci, haka ya bar falon. Mother tace "ohh ni Hauwa'u Allah ya shirya min Auta, Khairat kiyi ƙoƙarin tuna in da kika ajiye masa wandon nan dan Allah kar ya zo ya kuma ɗaga mana hankali. Jiki a sanyaye Khairat tace "wallahi Mother na zaci na baki ne, wallahi na manta yadda nai da wandon" Sadik na fita yaci karo da abu akan baranda, abunda ya ɗau hankalin sa shine tambarin kamfanin wandon fa yai siyayya. Tsayawa yai, yasa hannu ya ɗago wandon, aikuwa Tabbas shine, ya yi duƙun duƙun, da alama anyi goge goge da shi ha baƙin tukunya a jiki. Wani abune ya soki ƙirjin sa, nan da nan jikinsa ya ɗau rawa. A fusace ya koma falon yana wani irin huci, yana shiga ya jefawa Khairat wandon a jikinta. Da sauri ta kauce, kasancewar yadda wandon ya koma tsumma, ya fita da ga hayyacin sa. "Wannan shine abun da na baki ajiya, aka mayar da shi haka ko?" Mother tace "ba dai wannan ne wandon ba?" Tabbas shine, amma ya akai haka ta faru ya koma haka. Cikin kuka Khairat tace "wallahi ban san yadda akayi ya zama haka ba, nasan a cikin ledar sa yake. Mother ta ɗaga wandon, ba shi da maraba da tsumma. Inna da tun ɗazu ba ta tanka ba se yanzu tace "Wannan ai tsumma ne, shine wandon da ake ta rigima a kai?" Talatu me aiki tace "Ai wandon sabone" Inna tace "wannan ɗin, amma na ganshi duk a yayyage? Ya za'ai sabon Wando a yage haka kamar na mahaukaci" Duk da halin da Nana ke ciki na regeretin, se da tai dariya jin abunda Inna tace, duk yadda ta so riƙe dariyar ta kasa, ta miƙe ta bar falon tana darawa. Sadik kuwa ji yai tamkar zuciyarsa ta tsaga ƙirjinsa ta fito. Mummy tace "Khairat baki kyauta ba gasky, careless ɗin ki yayi yawa, nawane wandon Ni se in biya kuɗin wandon?" Wata uwar harara ya gallawa ƙanwar mahaifiyar tasa yai waje yana fidda numfashi. Inna ta girgiza kai, ganin yadda suke ta wani lallaɓa shi yana fizgar kai, sam ba ɗa'a. Ita kuwa Khairat fashewa ta sake yi da kuka. Mother ta janyota tana rarrashin ta, suna mamakin yadda a lamarin ya faru. Farhan kam abun duniya ya hanata sukuni. Tunda taji zancen Sunusi ko Abincin kirki ba ta iya ci, bacci ma gagararta yake yi, saboda tsabar damuwa. Ba ta san meyasa iyayenta haryanzu suke rayuwar mutanen da ba, meze sa kawai ai mata miji ba tare da neman yardatta ba, shikenan an mata shamaki da kawo kowa tace ta na so. "Yaya tunanin me kike ne?" Muryar cousin ɗinta Huzaifa taji, wanda ya dawo da ita daga dogon tunanin da ta tafi. Murmushi ta yi tace "ba abunda nake tunani" Ya kalleta yace "ba wani nan, kin san tun yaushe na shigo, ina ta magana kinyi shiru, na shigo Umma ma bata nan" Farhan tace "Kaga ni ba wannan ba, dan Allah wayarka da kuɗi a ciki?" "Eh da kuɗi, amma ba yawa me zaki da ita?" "Waya zanyi yanzu zan baka" Ya sa hannu a aljihunsa, ya ciro wayar duk screen ɗin wayar ya tsatsage, wayar ta sha jiki, ya miƙa mata yace "kuma ki ka cinyemin kuɗi sekin biyani, minti ɗaya da rabi na baki" Murmushi tai tace "godiya nake gwani Huzaifa" Abba na son a kirashi gwani, saboda a duniya ba shi da burin da ya wuce haddace Alqur'ani. Yace "kai kin sa naji daɗi sosai, in Allah ya yadda se na wuce ki a hadda" Farhan tace "bari fa, na riga na wuce ka" Murmushi yai ya fita yana faɗin, 'aikuwa zan baki mamaki" Bayan ya fita, ta fito tsakar gida ta duba, ta ga Umma bata nan ta fita. A hankali take tafiya kamar mara gaskiya, ta je ta duba ɗakin Abba ta tarar yana bacci, ta koma ɗakinta ta kulle ta saka sakata. Litattafanta ta zazzage, ta ɗakko lambar Sadik, jikinta na rawa saboda rashin sabo, gani take kamar ana kallonta. Jiki na rawa ta kwafi lambar ta sa, ta danna kira. Sadik na kwance ya yi ruf da ciki, zuciyarsa na ta tafasa akan asarar da Khairat tai masa, wayarsa ta hau ringing. Wani dogon tsaki ya ja ya ɗauke kansa da ga kallon wayar. Tai ringing harta katse be ɗauka ba, gaba ɗaya se taji ba daɗi, amma se tai masa uzurin ko yana wani abun ne. Ta tattare litattafan, ta mayar cikin jakarta, ta maida jakar ma'ajiyarta. Taita dakon ko Prince ze biyo wayara, amma shiru. Ba ta gaza ba ta sake kiran layin nasa, a fusace ya fizgo wayar ya ɗaga cikin masifa yace "Wai waye ne?" Cikin sanyin muryarta, me sigar shagwaɓa tace "nice fa" Wata irin ajiyar zuciya ya ja, tare da lumshe idanunsa, ba tare da yace komai ba. "Ka na ji na kuwa?" "Ina jinki Princess, ina tattaro kalaman ban haƙuri ne, na rashin ɗaga wayarki da farko, sannan kuma nai miki shouting, bari in kira ki" Ya katse kiran, sannan ya kirata, seda ta kuma leƙawa tsakar gida ta ga ba kowa, sannan ta koma ta zauna ta ɗaga wayar. "Ina fatan an karɓi ban haƙurina" yai maganar cike da kasala. Ɗan tura baki tai tace "naji muryarka wani iri, meke damunka?" A shagwaɓe yace "Princess ɓatamin rai akayi zanyi kuka" Dariya Sadik ya bata tace "Subhanallah, kuka kuma?" "Eh mana" "No, sorry kar kayi kuka, kaifa namiji ne kuka ai se mata" "Khairat ce ta ɓatamin rai" Tace "am sorry ni ban tambayeka ya kuka je gida ba?" "Lafiya ƙalau, wandon nan da na siya, aka kawo nace ta ajiyemin ta bari akai mopping da shi, wai an zata tsumma ne" Kwashewa da dariya Farhan tayi, dan sosai ya bata dariya. Cikin dariya tace "to ai ba kowane yasan wannan wandon gayu bane, abu duk a yayyage" "Au haka zakice ko? Shikenan" "A'a kayi haƙuri kasa wani" "Ai raina ya gama ɓaci, sena hukunta ta akan abunda tayi" "A'a dan Allah kayi haƙuri, tsautsayi ne" "A'a wannan ba tsautsayi bane, za ta gane kurenta" "Dan Allah kayi haƙuri mana" Sadik yace "ko zan haƙura se nayi tunani, duk da ita ma ina sonta, duk wadda Allah ya bani a cikin ku ina so, sedai na fi son ki, da ke ki kai laifin da tayi ba abunda zan iya" Ɗif Farhan tayi taƙi magana, Sadik yace "ya dai Baby Princess, naji kinyi shiru" "Ba ka cemin ƙanwarka ce ba?" "Ai cousin ɗina ce, akwai Aure a tsakanin mu" Take Farhan taji zuciyarta na tafasa, jiki a sanyaye tace "se anjima" Sadik yace "Malama kar ki kashemin waya, ban gama Magana ba" A ɗan hasale tace "to ai aiki zanyi" Rungume pillow yayi yace "na so ace am with you right now, in ga kishi na a kyakykyawar fuskar nan taki Baby, da wasa nake miki wallahi, tsokanar ki kawai nake" Tura baki tai kamar yana ganin ta tace "to ni ina ruwana in ma dagaske kake" "Ke ko kike da ruwa Yarinya, ba zaki tabattar da hakan ba, se kin ganni da wata, amma bana fatan hakan, ke kaɗai kin ishi Prince, am sorry kinji Babyna wasa nake miki" Motsi ta jiyo a tsakar gida, dan haka da sauri tace "se anjima" Ta kashe wayar, kallon wayar yayi, tare da yin murmushi, ji yai duk damuwarsa ta gushe, ya ji daɗin yadda yanzu take sakin jiki harta faɗa masa abunda yake ranta, a hankali yana sake gane halayenta. Sauka yai daga kan gadon yana murmushi, da jin daɗin yadda kishinta ya kasa ɓoyuwa. Ita kam Farhan shiru tayi, tana sauraren wanda ke motsi a tsakar gida, Huzaifa ya leƙo ɗakinta yace "kin gama wayar?" Tace "eh na gama, ga ta Nagode sosai" Ya sa hannu ya karɓi wayar yace "ba batun godiya, kuɗin kati kawai zaki kawo" Ba tace komai ba se murmushi da tai masa. Shiru tai ta na nazarin maganganun Prince, yanzu idan dagaske yake mata fa, Khairat ma budurwarsa ce!. Da ma ana ta masa gorin yana Soyayya da ita, tana abu kamar 'yar ƙauye, amma da gani dama Khairat wayayyiace kamar Prince, dan yakan yi mata hirar Khairat ɗin, amma ba ta taɓa kawo komai a ranta ba, saboda cewa yake ƙanwarsa ce. Gefe guda kuma ga batun Sunusi, da ta tuno zancen Sunusin nan, se taji gabanta ya faɗi gaba ɗaya se ta rasa sukuni. Ba ta san da wani idon zata fara kallon tsabar idon Abbanta, idan lokaci yayi tace masa ba ta son Sunusi ba ita da wanda take so. A hankali ta zame jikinta ta kwanta, ta lumshe idanunta tana sauraron yadda bugun zuciyarta ya ƙaru saboda damuwa. Shikam Prince zuwa yamma tuni ya manta da batun wandon sa da Khairat tai masa asara, sema nemanta da yake suje taga gurin da ya kama, za suyi party da abokan sa. Sedai ya nemi Khairat ya rasa, Mother ta sanar masa, ko ɗinkin ba taje ta karɓo ba, tunda yai mata tijara da safen nan, ba ta kuma fitowa ba. Ɗan girgiza kai yai yace "lallai ma yarinyar nan ba ta da kunya, tai min laifi kuma ta hau fushi, Allah ya temaketa Princess ta bani haƙuri, fa sena tattaka ta" Mother tace "wacece kuma Princess" Ba kunya Sadik yace "sirikar ki ce" yai maganar yana nufar part ɗin Mother. Ɗan girgiza kai tayi ta cigaba da sabgoginta, dan bata ɗaukar maganganun Sadik ɗin da mahimmanci, tana barinsu ne a mazaunin ƙuruciya, Ina Sadik ina wata budurwa. Duk wani shirye shirye Sadik ya kammala, daga kama guri kuɗin Abincin da zasu ci shi da abokansa duk ya kammala biya. Ranar Laraba ya kama ranar da Sadik ɗin zeyi tasa walimar, shida abokansa saboda ranar Alhamis za'a fara bikin. Ɗan maidaidacin hall ne ya kama, yayi kyau sosai gurin, ƙarfe biyar motoci suka fara parking a harabar gurin. Kallo ɗaya za kaiwa matasan yaran, masu ji da tashen balaga kasan 'ya'yan gata ne. 'yan secondary, Mazansu da matan suna sanye cikin crazy jeans, da riguna me ɗauke da sunan Amarya da Ango a gaba, baya kuma sunan mamammalakin rigar. 'yan makarantar sun wa Sadik kara, dan harda 'yan primary a cikin wanda suka zo partyn. Shikansa uban gayyar duk da Asarar da Khairat tai masa, amma ya saka wani wandon, yayi kyau ya fito a ainihin ajebon sa, sumar nan tasa afro style ta sha wanki da mayuka, se wani irin ƙyalli take. 'yan mata sangan sangan se yawo suke a cikin maza da matsastun riguna da wanduna, duk sun matse halittun Jikinsu. Tamkar jinsi ɗaya suke, haka suke shiga suna fita a cikin mazan nan, ba ruwansu da wannan namiji ne waccan mace ce. Ita kanta Khairat da taje gurin, seda ta sarawa rashin ji irin na 'yan makarantar su Sadik, duk itama ta su makarantar suna nasu rashin jin, amma su Sadik sun damesu sun shanye. Nan aka fara raye-raye, da ɗaukar hotuna, su Nas suna ta zuba rashin mutunci, da tanka 'yan matan in anjima su rungumo waccan, ko su kamo waccan suna rawa. Shikansa uban gayyar haka 'yan mata suka baibaye shi, da sunan ɗaukar hoto suna rungumarsa, dan duk taƙadirancin Sadik a school, ba ruwansa da rungume rumgumen mata. Kan stage suka janyo shi, suka dinga juyashi da sunan rawa. Mubarak ne yace "mutumin nifa banga Farhan ba" Haɗe rai Sadik yai yace "in ka ganta me za tai maka?" "A'a bakomai, ai gani nai Yakamata ace tana gurin nan dan tayaka murna" A taƙaice Sadik yace "ba ta zo ba" Ba'a tashi daga gurin nan ba se goma na dare, amma anci an sha yadda yakamata, wanda aka gayyata da wanda ba'a gayyata ba duk sunci sun ƙoshi. Wasu sukaiwa Sadik keyholders da Manyan kofuna na cas, da sunan couple's ɗin a jiki, kowa da abunda ya bayar na gudunmawa saboda shima Sadik ɗin meyi ne. Seda aka watse za su taho gida sannan hankalin Sadik ya dawo jikinsa, Mother tai masa missed calls ba adadi. Haka ma Khairat, itama wayarta kira ne rututu a ciki. Khairat tace "Sadik kaga kiran wayar Mother, ga na Mummy bari in kira su inji ko lafiya?" "No ƙyalesu in muje Gidan ayi duk wadda za'ayi" Haka ya cigaba da driving, suka tafi gida. Sedai suna zuwa gidan, a harabar gidan suka tarar da su Mother a tsaitsaye suna kiran layinsu, dan babu wanda yasan in da suka tafi, Sadik be gaywa kowa party ya shirya ba, dan karma asa wasu su bisu suje su hana su rawar gaban hantsi. Ganin su Mother harda shi kansa angon a harabar gidan be dameshi ba, dan ko a jikinsa, amma idonsa na sauka a na Inna yaji gabansa yai wata irin mummunar faɗuwa! Domin sauke manhajar AREWA BOOKS, Danna wannan link ɗin. https://arewabooks.com/book?id=6220842688e1ec3a0410329f Domin gyara, Sharhi ko shawara Ayshercool 07063065680 [6/4, 4:21 PM] Jakadiyar Arewa: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ RUƊIN ƘURUCIYA PERFECT WRITERS ASSOCIATION (WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS) https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ P. W. A *Story and written by* AISHA ADAM (AYSHERCOOL) Writer of WATA KISSAR..(Sai mata) ABDUL JALAL AƘIDATA (paid book) WUTA A MASAƘA NOW RUƊIN ƘURUCIYA (paid book) _Labarin RUƊIN ƘURUCIYA, na iya zuwa da wani salo, wanda baku saba ganinsa a rubutuna ba, hakan ya biyo bayan akan abunda aka gina labarin, wani abun ze ɓoyu wani Abun baze ɓoyu ba sakamakon labari ne akan teenegers, yara masu tashen Balaga, but hakan ba ya na nufin na sauka daga kan tsarin yadda nake Rubutu bane, ƙofata a buɗe take dan karɓar ƙorafi, gayra ko shawara_ ⚠️⚠️⚠️ƘIRƘIRARREN LABARI NE, BAN YADDA A JUYAMIN SHI TA KOWACE SIGA BA SEDA IZININA ❌❌‼️       SHIN KUNA DA LABARIN MANHAJAR AREWABOOKS KUWA? MANHAJA CE DA TAZO DA TSARIN DAN SAUƘAƘAWA MARUBUTA DA MAKARANTA SAUƘIN CINIKAYYAR LITATTAFAI. TA IN DA ZAKU IYA SIYAN KOWANE FEJI AKAN KUƊI ƘALILAN, DAI DAI DA ALJIHUNKU. INA FARINCIKIN SANAR DA KU CEWA, DA ZARAR NA KAMMALA FREE PAGES, ZAKU CIGABA DA SAMUN CIGABAN LITTAFIN RUƊIN ƘURUCIYA, AKAN MANHAJAR AREWABOOKS. KARKU BARI A BAKU LABARI, AKWAI TARIN DARASIN RAYUWA A CIKIN LITTAFIN. https://arewabooks.com/book?id=6220842688e1ec3a0410329f 21-22 Jikin Sadik yai sanyi da kallon da Inna take masa, wani irin kallo take ƙare musu tun daga sama har ƙasa. Mother tace "Auta ina kuka tafi haka? Tun wajen goma na safe rabonku da gidan nan, ba irin kiran wayar da ba'ai muku ba amma ba kwa ɗauka, ina kuka shiga ne?" Tsuke fuska Sadik yai yace "mun shirya party ne da abokaina, 'yan makarantar mu, shine muka je da Khairat" Usman yace "Amm ai seka sanar, duk ka ɗaga mana hankali kun sa mutane a damuwa" Khairat dai tai tsit tana rarraba ido. Sadik kam ƙara haɗe rai ya fara takawa, ze nufi sashin su. "Kai zo nan" Inna ta kira shi cikin bada umarni. Ɗan tsayawa yai yayi jim, se kuma ya juyo ya tako in da suke ya tsaya. Inna ta kalli Khairat ta kalli Sadik, sannan ta kalli in da Mother ke tsaye tace "yanzu ke Hauwa tsakanin ki da Allah, Laifin da yaran nan sukai ba su isa hukunci me tsauri ba? Kalli shigar jikinsu, kalli jikin wannan Yarinyar, ta bishi cikin maza, tun safe ba sa gida se ƙarfe goma na dare suka dawo, maimakon ku tsananta bincikar su, ku san matakin da zaku ɗauka, kawai iya abunda zaku ce musu kenan? Kalli wandon jikinsa kamar mahaukaci duk a yayyage kamar wanda ya zare, kalli uwar sumar kansa kamar ɗan daudu, ita wannan Yarinyar kalli suturar jikinta. Wannan wane irin riƙo kuke wa yaran nan? 'ya'yayenku fa se Allah ya tambayeku akan rainon su, suna shekarun su ne na RUƊIN ƘURUCIYA, Komai ze iya faruwa, amma har suje su shirya abu isu isu babu sa idonku a kai, wannan wace irin rayuwa ce, a tunanin ku wannan wayewa ce? Babu sa ido akan yaranku kun bar su suyi abunda suke so? Wallahi idan baku kiyaye kun kula da tarbiyyar yaranku ba watarn za kuga abun da ba kwa so" Cike da ƙosawa Mother tace "Allah ya kiyaye ya tsare, dan Allah kima dena wannan maganar, kar ki musu baki yara idan ba'a bar su sun huta ba ya za'ai, a kirshe su, shima  yawan takura yana lalata yara, kuma naga yaran nan sun saba da rayuwa da turawa ne, in Allah ya yadda ba abunda ze faru, yawan yi musu faɗa ma raini yake kawowa, kuma party a tsakanin su yara ba yanzu suka fara ba, kuma ba abunda ya taɓa faruwa, sunyi ne kawai dan taya ɗan uwan su murnar Auren da ze" Inna ta jinjina kai tace "ba shakka, 'ya'yan turawa ko, shikenan Allah ya temaki turawa, Allah ya shirya" Tana gama faɗin haka ta juya ta koma cikin gidan. Shi kam Sadik kamar ya fashe, saboda yadda ya kumbura baki yana wani irin huci. Mother tace "kaga abunda ka janyo min ko? Na gayamaka tunda Allah yasa tsohuwar nan ta tare a gidan nan kayi komai a hankali, in ba haka ba ido zata samana komai ta gani taita masifa" Usman yace "Mother, dan Allah duk kuyi haƙuri dan Allah komai ya wuce, karki kuma yin wani lafin, kuma dan Allah idan ta ɗau zafi ki dena tanka mata, hakan yana tunzurata, Yanzu dai duk kuyi haƙuri" Sadik bece komai ba ya wuce ɓangaren su, Khairat ma ta shiga cikin gidan tana sunkuyar da kai kamar munafuka. Mother kuwa tana zuwa ɗakinta, cikin 'yan uwanta ta hau masifa tana mitar Wai Inna tana ja wa 'ya'yansu masifa tana musu baki, ita Alla alla takema ayi bikin nan tabar mata gida duk tabi ta isheta. Suka haɗu suka dinga yi da Inna suna zagin ta. Ita kam Inna tunda ta koma ɗakin da suke, tai shiru tana tunani al'amuran Sadik na bata tsoro da mamaki, tabbas idan aka cigaba da tafiya a haka da wannan sakacin ko sakarcin na uwarsa tabbas Yaron ze lalace. Dan ta lura halayyar sa daban da ta sauran yayyen sa, tarbiyyar Sadik na buƙatar jajircewa da kuma sa ido, saboda kansa yana rawa fiye da shekarun sa. Sadik kuwa gaba ɗaya ransa a ɓace yake, Alla Alla yake a gama bikin nan wannan tsohuwar ta bar musu gida, ya rasa me ya tare mata take masa wannan abubuwan, ba damar ya motsa se ta haushi da masifa. Haka yana kumbure kumburen baki, yai wanka ya kwanta, amma bacci yaƙi zuwa. Can kuma se partyn da su kai suka dinga dawowa kansa, take surorin 'yan matan nan suka dinga dawo masa kansa. Ƙoƙarin banzatar da tunanin yayi, amma abu ya faskara, zuciyarsa ta dinga raya masa cigaba da kallon series film ɗin nan, amma wata zuciyar ta shiga gargaɗin sa. Series ɗin yana ƙayatar da shi, amma kusan kaso arba'in na film ɗin yana bayyanar da very hot Romance ne tsakanin masoya. Runtse idanunsa yai, amma se ya dinga Ganin Farhan a idonsa, da wannan kyakykyawan murmushin nata. A hankali ya furta "Oh God" Ya ɗakko wayarsa, ya dinga kallon lambar da ta kirashi da ita, se kuma ya kalli agogo yaga kusan sha ɗaya na dare, jiki a sanyaye ya ajiye wayar, ya nemi guri ya kwanta. Da tunani barkatai cikin ransa da haka bacci yai awon gaba da shi. Washegari Alhaji Abdullahi ya dawo daga tafiyar da yayi, wanda ya kasance ranar fara bikin ɗansa Usman. Da yamma ya shiga gaida Inna, lokacin kusan duk jama'ar gidan sun yo ye sun tafi gurin biki. Cike da girmamawa suke hira shi da Mahaifiyar sa. Can Inna ta nisa ta kalli ɗan nata tace "Abdullahi!" Wani banbarakwai yaji, dan Inna ba ta sba kiransa kai tsaye da sunan sa haka ba, se idan ta na da wata mahimmiyar magana. Hakan yasa shi tattara nutsuwarsa da hankalinsa akan ta, yana sauraren me zata ce masa. Cike da damuwa tace "Kamar yadda ka sani, ni mace ce me son haihuwa, Allah ya bani haihuwa, sedai duk sun koma, kaine ɗana na huɗu, bayanka na hayayyafa amma duk ba su rayu ba, ɗan uwanka Abubakar ya taso ina murna Allah ya barmin, se bayan yayi Aure ya haifi wannan Yarinyar ya karɓe shi ya karɓi mahaifiyarta" Mamakin maimaita wannan tarihi da ta ɗakko yake yi, wanda duk wannan abun da take faɗa ya riga ya san da shi. Ta cigaba da cewa "Ni macece me son iyali na, fiye da tunani, duk da irin son da nake maka, Allah ya ɗaga ka, kayi Aure ka dawo birni da zama, sedai ƙawa zucina akan 'ya'ya ya ragu, tun bayan da Kai Aure, nasan dama namiji wataran mijin wata ne, mace ce duk inda take hankalinta na kan mahaifiyarta. Na ɗora rai akan jikokina, saboda ganin suma duk tsastona ne, na ƙallafa rai akan su, sedai shima sena fuskanci matarka ba ta buƙatar hakan, ba ta son 'ya'yanta su raɓi ƙauyawa jahilai. Sena maida hankalina kan Abubakar, ba dan zuciya ta ta dena sonka da 'ya'yanka ba, sedan bana son shiga cikin lamarin iyalan ka, saboda gudun matsala da zubewar mutunci. Ashe Habu ma bame tsawon kwana ba ne, bayan yayi aure, an haifi wannan 'yar, matar tazo sake wata haihuwar Allah ya karɓeta, bayan rasuwarta nai ta fama da shi yai aure, amma be ba, har shima yai hatsari a hanyar dawowa daga gidanka zuwa ƙauye shima Allah ya karɓe shi. Nasan za kayi mamakin sake maimaita maka abunda ka riga kasan shi, kuma ya wuce ban yi haka dan Komai ba, sedan sake jaddada maka irin so da ƙaunar da nake maka da 'ya'yanka, saboda dukkanin ku tsatsona ne, ba zan so inga wani mummunan abu ya sami zuriyata ba. Ja da baya da nayi na zura maka ido kai da iyalan ka, baya na nufin na sallamaku bane bana kishinku. Ka sani na sani, ni mace ce me zafi kuma da haka nai tarbiyyar ku, ba dan na dage da addu'a da jajircewa ba, da baka taso a haka har wani yai sha'awar Aura maka 'yarsa ba. Abdullahi, kai da yaranka ba turawa bane ba, 'ya'yanka da kai Hausa Fulani ne masu kamala da tarbiyya, dan kayi boko, ko kun zuwa ƙasashen turawa ba shi ke nufin kuma turawa bane ba. Bari in fito maka a mutum, yaranka ba su da tarbiyya!" Da sauri Alhaji Abdullahi ya ɗago ya kalli Inna yace "Inna ba su da tarbiyya kuma?" Cikin ƙwarin gwiwa, da nuna isa Inna tace "Ƙwarai kuwa, 'ya'yanka ba su da tarbiyya, mussaman me sunan Ƙarami ɗan Autan ka. Allah ya sani ina ƙaunar yaranka fiye da yadda nake sonka, ka san yadda nake son jikokina duk da ba sa zuwa in da nake, amma hakan ba ze hanani faɗin gaskiya akan su ba. Abdullahi ka sanya idanu akan tarbiyyar yaranka, kuɗi ba hauka bane ba, kafin kai dubun ka sunyi arziki kuma sun shuɗe babu su a duniyar nan, yana daga cikin sadaka me gudana bayan ran bawa, ya haifi ɗa na gari da ze dinga aikata aikin Alkhairi. Kana tunanin wannan? Ko kuma neman kuɗin kawai ka saka a gaba, yau kana Habuja, gobe kana gurin wancan gwamana, jibi ka na waccan ƙasar, ka bar mace da tarbiyyar gidanka matar da ita kanta tana buƙatar tarbiyya, wannan ganganci ne haihuwa da damuna. Ba ina kushe maka iyali bane, ko ƙoƙarin haddasa maka husuma a cikin gida ba, bulaliya nake maka, naga shekaranjiya, naga jiya gashi ana damawa da mu a yau, ko kai da kai boko ka zaga duniya, ba zaka gayamin sanin duniya da zamantakewa ba, bar ganina bagidajiya bafullatanar ƙauye, shekarun da nayi a duniya naga abubuwa da dama, kuma ina iya fahimtar abubuwa da dama. Dan haka ka kula da iyalinka, ka sa ido akansu sosai ka kula da tarbiyyar su, ka barsu da ingantacciyar tarbiyya da kyakykyawar rayuwa yafi wannan kuɗin da kake tara musu, da basu san ciwonsu ba, sedai su ɗiba suyi ta bushasha" Tun da Inna ta fara faɗan nan, ya sunkuyar da kai, bece uffan ba seda ta kammala, ya ja nannauyar ajiyar zuciya yace "Insha Allah Inna za'a kiyaye, in Allah ya yadda zan kula kamar yadda ki ka ce" Inna tace "to Allah ya wuce mana gaba, ya kare dukkan zuriyar Annabi daga taɓarɓarewa da sharrin ƙarshen zamani" Yace "Ameen ya Allah, Inna nagode Sosai" Har ya miƙe ze fita tace "fita za kayi ne?" Yace "eh Inna" Tace "to zo in fesa maka turare" Yai murmushi yazo gabanta ya durƙusa, ta ɗakko turare ta feffesa masa tace "yawwa duk da naji kana ƙamshin turare ai gara ka ƙara, ai ƙamshi rahama ne" Yai murmushi yace "hakane Inna nagode" Tai murmushi ta cigaba da laziminta. Maganganun Inna sun damu Alhaji Abdullahi Sosai, duk d aba ta fito ta gayamasa ƙarara meyafaru ba, amma maganganun nata sun tsaye masa a rai sosai. Se dare sannan aka din ga dawowa daga gurin kamun da aka tafi, wanda zasu kwana a gidan duk suka taho nan gidan, dan a tare motocin suka dinga dawowa. Wajen ƙarfe sha ɗaya na dare, Mother tayi wanka ta canza kaya, ta nufi sashin Megidanta da coffee. Tun da taje take zuba masa hira, tana nuna masa hotunan biki, sedai ta lura kamar yana tunanin wani abun ne. "Yallaɓai ya na ganka wani iri ne? Kai da Yakamata ace kana farinciki zaka aurar da ɗanka na fari" Kallonta yayi sannan yace "Akwai wani abu da Sadik yaiwa Inna ne na rashin kyautawa" Haushi ne yakama Mother, wannan takurarraiyar tsohuwar ta isheta. A fili tace "wani abun tace ya mata ne?" "No, ba tace min yamata Komai ba, sedai tamin hannunka me sanda a cikin Magana, dan haka dan Allah idan ma da wani abu na rashin ɗa'a ko kyautawa da yake, ki ja masa kunne, nima zan masa magana bana son ranta ya dinga ɓaci akan wani abu" Ajiyar zuciya Mother tai tace "ni dai iya sani na ba abunda yai mata, sedai kasan ba su fiye jituwa ba, amma zan masa magana insha Allah" Yace "yayi" Yana ɗauke kai ta dalla masa harara, gaba ɗaya haushin Inna take ji, ta fiye sa ido da son hanasu rawar gaban hantsi ita da 'ya'yanta. Aka cigaba da gudanar da biki cikin bajinta, da kuma wadata. Ranar Dinner Inna tace ba in da Nana za taje, wani irin bikine baza'a fara shi ba se dare dan watsewa, waye ze sa mata ido akanta. Nana hadda kuka, tana son zuwa amma Inna ta hana. Faruk ne ya shigo cikin shadda coffee colour, se sheƙi take kamar shine ango yayi kyau sosai. Part ɗin Mother ze nufa, amma yaga Nana a zaune kusa da Inna tana kuka. Ya dawo da baya yace "lafiya kuwa? Nana ana ta shirin tafiya gurin biki amma kina zaune kina kuka?" Duk da tana shakkar Inna amma tace "Inna ce tace ba zani ba" Ya kalli Inna yace "Inna meyasa ba zata ba?" Inna tace "bana son abunda baza'ayi shi ido na ganin ido ba, wane irin biki ne za'a tafi wata uwa duniya ayi shi da daddare" Faruk yace "haba Inna, aina lokaci ɗaya ne, yanzu kowa seya tafi a barta a gida, ai za taji ba daɗi, tashi ki sako kayanki mu tafi tare" Inna tace "ki tashi daga nan kiga yadda zanyi dake" Faruk ya ɗan marairaice yace "dan Allah Inna ki ƙyaleta, kinga kuka take fa" "Ni bani da idon ganin kukan take ai, tayi kukan jini ma" "Dan Allah Inna ki bari taje, kuka fa takeyi" Inna tace "A'a yau naga ikon Allah, ka ƙyaleta tai ta kukan mana" Faruk yace "wallahi Inna bana son inga mata suna kuka, kinga nan gidan bamu da ƙanwa mace, shiyasa idan naga yarinya ƙarama mace nake jin tausayin ta, dan Allah ki bari taje ko ta dena kukan nan" Ɗan tsura masa ido Inna tayi, ta tuna haka mahaifinsa ma yake, ba ya son yaga mace a damuwa ko ta na kuka, da irin wannan damar Matarsa tai amfani se yadda tai da shi, ta lura Faruk shine me sanyin hali a cikin su, duk da ga irin sunansa amma ba shi da zafi sosai. Inna tace "Naji, amma sedai muje tare, in sa ido akan ta" Faruk yai dariya yace "Hajiya Inna agurin dinner" "Bana wasa da yara, ka sani ƙaniyar ka zanci ni" Yai murmushi tare da miƙewa tsaye. Ba'a tafi gurin bikin nan ba se kusan ƙarfe tara na dare, Faruk ya ɗau Inna da Nana zuwa gurin bikin nan. Inna ta sha mamakin irin tsukewar da 'yan mata da iyayensu sukai, ba bu batun mayafai dama, kowa sabgar gabansa kawai yake yi. Ga zabga zabagan baligan samari, wanda suka kasance dangin Amarya da na Ango, suna shiga suna fita. Inna ba ta ƙara tsinkewa da al'amarin ba, seda aka fara cashewa, ba iyaye ba 'ya'ya, ana ta liƙa kuɗi ana raye raye. matashiyar 'yar galar nan me suna Gimbiya Ameeea ta nishaɗantar da su agurin, da kala kala samfur daban daban na rawa, cike da ƙwarewa da burge al'umma (Wanda be san labarin Amira ba, ya hanzarta neman littafin WUTA A MASAƘA) Daga bisani dj Sultan, ya sanar da zuwan, Maman Ango da Amarya. Zuwansu ba daɗewa sega Amarya da Ango suma sun hallara. Masha Allah, sunyi kyau matuƙa shi ya Sanya light blue ɗin shadda, ita kuma ta saka dark blue ɗin less. Nan fa biki ya fara ɗaukar harama wajen ƙarfe goma saura na dare, gaba ɗaya zaman gurin ya ishi Inna, gashi ba ta san in da zata gano Faruku ba balle tace ya maida su gida ba, dan ba dan ya matasa ba ba abunda ze kawota gurin nan, dama ta zo ne saboda Nana, dan ba zata iya sakinta haka tazo wannan guri, ita kuma tana gida a zaune ba. Tana cikin tunanin ne, taji ana wata shewa, ta ɗaga kai ta hango wasu gungun samari da 'yan mata sun shigo, suna ta faman iface iface. Zuba ido tai sosai, ta hango Sadik a tsakiyar su, sanye da coffee ɗin shadda irin ta Faruk. Mother da ke tsakiyar fili ta nawa Usman liƙi ta hango shigowar Sadik, tsayawa tai tana murmushi, yayin da Dj ya shiga koɗa Sadik ɗin yana masa kirari. Da hanzari Sadik ɗin ya ƙaraso in da Mother ke tsaye, ya zura hannu a aljihun Rigar sa ya zaro bandir na kuɗi yana liƙa mata. Juyi Mother ta dinga yi shima tana zuba masa kuɗin, ya rungumeta ana masa hotuna. Inna kam tagumi tai tana kallon ikon Allah, can kuma aka sanar da cewa ana neman abokan Autan Hajiya Hauwwa,  akan stage dan yiwa abokinsu kara na zuwa bikin Yayansa. Aikuwa nan da nan suka cika stage ɗin mazan su da matansu. Ba kunyar iyaye ko manya da ke gurin, suka dinga tiƙa rawa ta fitsara a gurin nan, Taslim ta riƙo hannun Prince tana juya shi shikuma yana murmushi. Rai a ɓace Inna ta kalli Nana da ta zubawa stage ɗin ido tana kallon ikon Allah, wanda ita kanta Nana a ranta abun da su Sadik ɗin keyi haushi yake bata, gaba ɗaya ba taga tsari ko dacewar Abun ba. Inna tace "ke dan ubanki kin zura musu ido kina naɗar abunda suke ko? Wallahi ko da wasa naga makamancin wannan a tare da ke, se na shaƙe ki, ki mutu kowa ya huta" Ɗan tura baki Nana  tayi tace "To Inna ni me nayi?" "Rufen baki, tashi mu bar gurin nan" Nana tace "mu bar nan Inna muje ina? Ba mu san hanya ba fa" "Zaki ta shi ko se na make ki" Nana ta miƙe suka fita daga cikin hall ɗin, Inna na cigaba da banbami kamar Nana ce tai mata laifin. Ko fa suka fito sha ɗaya saura na dare, babu ababen hawa ma, nan Inna ta shiga rarraba ido, ta ga ta ina za ta hango Faruk, dan da ya shiga hall ɗin se ta neme shi ta rasa, saboda da alama shike ƙoƙarin sallamar abokan sa da na Usman. Suna nan tsaye a in da akai parking ɗin motoci, sega Sadik ya fito shida abokan sa, suna hawa motocin da aka kawo su a ciki. A hakan ma se rashin albarka suke. Inna se girgiza kai kawai take, cikin sa'a kamar an jefo Faruku, se gashi ya nufo in da Su Inna suke. Yace "Inna ba dai tafiya za kuyi ba?" Inna tace "Aikam dan tun ɗazu kai nake nema, ka maida mu gida" Faruk yace "to shikenan, bari in ɗakko motar" Suna tafe a hanya, tunanin da Inna take daban har suka je gida. Sadik kam kwana yai da ɗokin washegari Mother's evening, Farhan za ta zo, ze gabatar da ita a gurin Mother, sedai ayi duk wadda za'ayi. Da safe yana ta ɗoki, yana son tabattar da zata samu zuwa ko kuwa? Kasa haƙuri yai, ya ɗakko wayarsa ya kira lambar da Farhan ta kira shi da ita. A daidai lokacin kuwa Huzaifa yana gidan su Farhan, kasamcewar cousin ɗin ta ne,  ɗan wan Abbanta ne. Ɗaga wayar yayi tare da yin sallama. Dumm Sadik yai jin muryar namiji, amma ya basar ya amsa sallamar yace "Amm Farhan nake nema ko tana kusa ka haɗani da ita?" Huzaifa yace "wace Farhan ɗin?" "Ta kirani da wannan layin shekaranjiya" Umma tsurawa Huzaifa ido tayi, tana sauraran abunda yake faɗa a wayar, ta ƙara saita nutsuwarta ne jin an ambaci Farhan ake nema. Huzaifa yace "ok na tuna tayi waya kam, bari in kirata" Huzaifa ya katse wayar, Umma ta kalleshi tace "ya akai ta karɓi wayarka ta kira wani?" Huzaifa yace "Ai ban san wanda ta kira ba, kawai ta cemin za tai waya ne?" Umma ta jinjina kai tace "kirawo ta" Huzaifa ya miƙe ya kirawo Farhan, wadda ta duƙufa tana bitar Alƙur'ani. Ta taso ta zo gaban Umma tace "gani" "Waye yake kiranki a waya?" Umma ta tambayeta ta na kallon idon ta. Farhan tace "Ni kuma?" Huzaifa yace "wani ne ya kira wayata yace yana nemanki, wai kin kirashi a layina shekaranjiya" Gaban Farhan ya faɗi amma ta dake tace "Yayan ƙawata ne, na kirata munyi magana ne, akan bikin da zamu anjima, ban san lambar wa ta bani ba" Ba tare da ta kalli in da Farhan take ba Umm tace "tashi ki je" Farhan ta tashi ta koma ɗaki, tana jin yadda wani irin gumi yake bin cinyoyin ta na Rashin gaskiya. Ita kanta tayi mamakin yadda wannan idea tai saurin zuwa kanta. Seda Farhan ta bari Umma ta tafi ɗakin Abba, sannan ta fito cikin sanɗa ta shiga ɗakin Umman ta ɗau wayar Umma, ta saka lambar Sadik ta kirashi. Tai sa'a ya ɗauka, yana ɗagawa tace "call me" Ba musu ya katse kiran, ya kirata ta ɗaga tare da yi masa sallama. Ya amsa yace "Princess, kewarki ta dameni, na ƙagu in anjima, fatan dai zaki zo ɗin" Tai ƙasa da muryarta sannan tace "Ka dena kirana se idan nice na kiraka, lambar da na kiraka ta Yayana ce, wannan kuma ta Umma ce, ka bari sena kira ka seka dinga kirana" Sadik yace "ok i understand, yaya zaki zo ɗin?" "Eh zan zo insha Allah, se anjima" Tai maza ta kashe wayar, ta ajiye ta fita daga ɗakin da sauri. Da ƙarfe huɗu da rabi na yamma, Farhan ta shirya cikin wani leshinta maroon me sauƙin kuɗi, ba wata kwalliya a fuskarta amma tayi kyau sosai. Ta ɗakko ƙaton mayafi ta rufe jikinta, ta tafi ɗakin mahaifinta. Ta tsaya a bakin ƙofa tai sallama, ya amsa mata sannan ta shiga, Umma ma na cikin ɗakin a zaune. Tace "Abba na shirya zani gurin bikin nan" Abba yace "Masha Allah, bari in baki kudin mota, sannan dan Allah kar ayi dare, ki kula da kanki kinji, kinga ban taɓa barinki zuwa guri irin wannan ba, ina jin nauyin yaran ne, sunzo hargida sun gayyaceki, kuma ko a Addinan ce babu kyau a gayyaceka walima kaƙi zuwa babu wani ƙwaƙwaran dalili, ki kiyaye kinji" Farhan tace "to Abba, Insha Allah" Ya bata ɗari biyu ta sa hannu biyu ta karɓa, ta kalli Umma tace "Umma na tafi" Umma ba ta kalleta ba balle ta amsa mata, haka Farhan ta miƙe ta fita. Abun takaicin ta na zuwa ƙarshen layinsu, se ga Sunusi da wani yadinsa, milk ne amma ya koma brown saboda ya dafe. Yana ganinta ya washe baki yace "unguwa za'ane 'yar Malam" Kamar tai masa banza amma tace "eh" "To adawo lafiya" A ciki tace "Allah yasa" Ta miƙe ta nufi titi,tana addu'a akan Allah ya bata Sadik, in dai da Sadik kome za'ai ba abunda zatai da Sunusi. Ko da taje gurin bikin babu wanda ta sani, duk se 'yan uwansu Sadik, ta samu guri gefe ɗaya ta zauna. Tana nan zaune aka fara cika gurin, kasancewar wuni ne, tun huɗu ake ta zuwa  gurin bikin. Yauma Inna tare da Nana Faruk ya kawo su. Gaba ɗaya Farhan ta fara takura kasancewar ba ta san kowa agurin ba, gashi biyar ta wuce ta fara tunanin tafiya gida. Khairat ce ta shigo hall ɗin, se rawar kai take tana kaiwa tana komowa. Babu tsammani suka haɗa ido da Farhan, take ƙirjin Farhan ya buga da ƙarfin gaske, dan tuno da abunda ya gaya mata akan Khairat. Khairat kam murmushi tai mata ta ƙarasa in da Farhan take, cikin iyayi tace "ashe za'a barki ki zo ɗin?" Farhan ba tai Magana ba se murmushi da tayi. Khairat tace "yana hanya ya kusa ƙarasowa, ya raka Mother gurin makeup ne" tana gama maganar tai gaba Mamaki ya kama Farhan, jin wai ya raka mamansa gurin Kwalliya. A lokaci ɗaya 'yan makarantar su suka shigo, sedai babu Sadik a cikin su, su Nasir ne da Taslim suka shigo. Farhan ta shiga rarraba idanu dan ganin ta ina za ta ganshi. Aminu ne ya fara taɓa Nasir yace "Baaba kalli mutuniyar Prince can" Yana ɗaga kai ya hango Farhan zaune akan kujera. Ya kwashe da dariya yace "dalla kalleta kamar wata ladaniya, se kace wata babba ga wani uban mayafi" Suka kuma saka dariya, ka tsaye suka nufi in da Farhan ke zaune, suma suka zauna, suka sakata a tsakiyar su. Ji tai kamar ƙasa ta tsage ta nutse, Amin yace "Matarmu kinyi kyau fa sosai, ya hutun?" "Lafy ƙalau" ta faɗa tana sunkuyar da kai. Miƙewa tsaye tayi, suka kalleta sukace "ina kuma zaki?" "Gida zan tafi" ta faɗa cikin raunin murya. Nasir yace "ai yanzu ze zo, ya faɗa yana wani ƙare mata kallo. Ba ta kuma bi ta maganarsa ba, ta janye kujera ta nufi hanyar tafiya. Hakan yai daidai da ƙarasowar Motar da Mother ke ciki ita da Sadik. Ta cikin motar Sadik ya hangi Farhan, cikin hanzari yace "bari in sauka" Mother tace "meyasa? Ka bari mu shiga mana" Ai kan ta kuma Magana ya buɗe motar, wanda ya tilastawa direban tsayawa,yai waje da sauri. "Farhan!" Ya kira sunan ta da ƙarfi, tsayawa tai ta waigo ta kalli in da yake. Da sauri ya ƙaraso in da take yace "ya zaki tafi da wuri haka?" Kamar za tai kuka tace "na fa daɗe a nan, kuma za'aimin faɗa a gida" Yace "ok am sorry, bari in maida ke gidan, muje ku gaisa da Mother tukuna" Zaro ido tayi tace "ince me?" "Ki gaisheta mana" "Wallahi kunya nake ji" ta faɗa cikin tsoro. Yai murmushi yace "karki damu, zan gabatar da ke ne a matsayin 'yar makarantar mu" Ta amince da hakan suka koma hall ɗin, can ya hango Mother harta shiga cikin yamar jama'a, anata gaisawa ga sautin kiɗa da ke tashi. Hannun Farhan Sadik ya riƙo ya shiga ratsawa da ita cikin mutane, gaba ɗaya se ta ɗan dirirce shikam ko a jikinsa. Se da ya kaita gaban Mother tukuna, Yace "Mother ga sirikar ki na kawo miki" Mother ba taji me Sadik ɗin yace ba, kasancewar hankalinta ya rarrabu ana mata Magana. Cikin jin nauyi Farhan ta gaisheta, Mother ta sa hannu ta kamo na Farhan tace "Sannu 'yan mata, ya gida?" "Lafy ƙalau" Farhan ta amsa cikin sunkuyar da kai. Mother tace "mungode sosai kinji, Sadik ka duba motar Mummy ka bata kayan bikin" Daɗi ne ya lulluɓe Sadik yadda Mother ta mutunta Farhan, nan da nan ya fara wani tunanin dabam, dan a zaton sa ta ji me yace mata. Har zasu wuce Farhan ta ga Inna, wanda ko ba a gaya maka ba, kasan kakar su Sadik ce, saboda ta san hoton baban Sadik, kuma ta ga suna kamanni. Durƙusawa tai tana gaida Inna, wadda sam shi Sadik be ma lura da Innar ba. Inna ta amsa mata cikin sakin fuska, yayin da Nana kuma ta zuba mata ido. Sadik be so Farhan ta kula Inna ba, dan yasanta da sharhi ƙil se ta tofa wani abun. A kai sa'a dai Innar ba tace komai ba, su Amin ne suka fara ɗagowa Sadik hannu, amma yai musu alama yana zuwa, Sadik ya dinga nunawa familyn su Farhan. Seda Farhan taji dama ba ta zo ba, dan wata kunya da ta mamayeta. Ya je in da aka ajiye kayan biki, ya ɗebo mata fal, ya karɓi mukullin motar Mother a hannun direba, ya tafi maida ita gida. Suna tafe a hanya, yana tai mata surutu da yadda yai missing ɗinta amma tai banza taƙi masa Magana. Shima shiru yayi seda sukaje unguwar su, in da suka saba ajiyeta, ta sa hannu za ta buɗe motar, amma taji a rufe. "Wai fushin me kike?" "Ba kaine ba, kawai ka dinga nunawa mutane ni, kuma bayan ba haka mu kai da kai ba" Dariya yai yace "to maza yi kuka, na iya rarrashi ai" Zumɓura baki tayi tace "buɗe min, kar a ga na daɗe" Maimakon ya buɗe mata se cewa yai "You look so beautiful" yai Maganar yana tsura mata idanun sa. Nan ya fara gwagwarmaya da zuciyarsa da ke ta kissa masa wasu abubuwa, a hankali ya miƙa hannunsa da gargasa ta fara lulluɓewa, yatsunsa biyu ɗauke da manyan azurfa ga agogonsa me kyau, ya miƙa hannu ya riƙo na Farhan . haka nan taji jikinta yai sanyi ta rasa dalilin hakan, kuma ta kasa yi masa magana, ta kasa zame hannunta, ga lokaci yana ƙurewa, kar a ga ta daɗe, amma ta kasa Magana saboda yadda yake binta da kallo, ga wani sihirtaccen ƙamshin druma da na kayan jikinsa ya gauraye motar, hakanan taji hannun nasa ya mata kyau!. Me so daga farko ya duba AREWABOOKS KO KUMA WATPAD PLEASE. Ayshercool 07963065680. [6/4, 4:21 PM] Jakadiyar Arewa: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ RUƊIN ƘURUCIYA PERFECT WRITERS ASSOCIATION (WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS) https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ P. W. A *Story and written by* AISHA ADAM (AYSHERCOOL) Writer of WATA KISSAR..(Sai mata) ABDUL JALAL AƘIDATA (paid book) WUTA A MASAƘA NOW RUƊIN ƘURUCIYA (paid book) _Labarin RUƊIN ƘURUCIYA, na iya zuwa da wani salo, wanda baku saba ganinsa a rubutuna ba, hakan ya biyo bayan akan abunda aka gina labarin, wani abun ze ɓoyu wani Abun baze ɓoyu ba sakamakon labari ne akan teenegers, yara masu tashen Balaga, but hakan ba ya na nufin na sauka daga kan tsarin yadda nake Rubutu bane, ƙofata a buɗe take dan karɓar ƙorafi, gayra ko shawara_ ⚠️⚠️⚠️ƘIRƘIRARREN LABARI NE, BAN YADDA A JUYAMIN SHI TA KOWACE SIGA BA SEDA IZININA ❌❌‼️       SHIN KUNA DA LABARIN MANHAJAR AREWABOOKS KUWA? MANHAJA CE DA TAZO DA TSARIN DAN SAUƘAƘAWA MARUBUTA DA MAKARANTA SAUƘIN CINIKAYYAR LITATTAFAI. TA IN DA ZAKU IYA SIYAN KOWANE FEJI AKAN KUƊI ƘALILAN, DAI DAI DA ALJIHUNKU. INA FARINCIKIN SANAR DA KU CEWA, DA ZARAR NA KAMMALA FREE PAGES, ZAKU CIGABA DA SAMUN CIGABAN LITTAFIN RUƊIN ƘURUCIYA, AKAN MANHAJAR AREWABOOKS. KARKU BARI A BAKU LABARI, AKWAI TARIN DARASIN RAYUWA A CIKIN LITTAFIN.                           23_24 A hankali Sadik ya sauke ajiyar zuciya, ya saki hannuanta  yace "Farhan" A hankali ta ɗago ido ta kalleshi, yai unlocking Motar yace "nagode Sosai da halartar bikin yayana, ki gaisarmin da Abba" Ba tace masa komai ba, ta ɗau kayan da ya bata ta fita daga Motar, sedai gaba ɗaya taji jikinta yai sanyi. Haka ta nufi layinsu dan kama hanyar gida. Se da ta ƙule sannan Sadik ya kunna motar ya koma gurin taron bikin. Yana komawa su Nas suka cigaba da tsokanar sa akan Farhan, su kai ta iya shegen su san ran su. Sedai gaba ɗaya jikin Prince ɗin a sanyaye yake, ya dake ya ɓoye halin da ke damunsa, ya dinga biye musu. Nas yace "Prince, wai ya batun movies ɗin da aka tura maka ne, ka kalla kuwa, kaga yadda ake madarar Love, ba irin wanda ku keyi ba, sekace masu wasan yara, dan Allah kai ba ka ji kunyar ka dinga nuna wannan Yarinyar kace budurwarka ce ba? Kalli kayan jikinta ta jibga uban mayafi kamar wadda zata ja salla.... Wani irin warning glance Prince yaiwa Nas, hakan ya sa Nas ɗin yin shiru. Daf da magariba amma har a lokacin zuwa ake, har 'yan ajin su Farhan ma sun halarci taron bikin. Sedai gaba ɗaya Haseena ta kasa sukuni, saboda kyan da Sadik yai a idonta, babban abunda yasa ta tsani Farhan bakomai bane illa kishi, gashi Sadik ɗin ba shi da fuskar da za tai masa shishshsigi, amma harga Allah yana matuƙar burgeta. Yau ta ƙara tabattar da Sadik ƙyakyawa ne na gaske, dan ba ƙaramin cika ido da kwarjini yai a cikin manyan kaya ba, duk da ƙarancin shekarunsa, Allah yai masa ƙirar manya, dogo ne ga shi da jiki, wannan jikin ne ke ɓoye ainihin ƙuruciyar sa. Yauma Inna ta ga taɓara kala kala, da rashin ta ido, wanda suka ƙara tsaye mata a zuciya. Se wajen ƙarfe goma na dare, Sannan aka watse daga gurin bikin. Farhan da ta koma gida, tayi zaton Umma za tai mata faɗan ta daɗe, amma ga mamakin ta ba abunda Umman tace mata. Nan ta baje uban kayan da Sadik ya bata, ta bawa Umma, amma Umman taƙi ko kallon in da kayan yake, ƙarshe se bari tai da Abba ya dawo, ta kai masa ya sa albarka, yace suje su raba ita da ƙanen ta. Ta rasa yadda za tai da ranta da wannan halin ko in kula da mahaifiyarta ke mata, kawai saboda tana 'yar fari, ita tafi danganta wannan abun da kawai ba ta santa ne, dan wannan abun ya wuce kawaici. Tun da suka taho da Sadik, ta kasa gane me ke damunta, gaba ɗaya jinta take wani iri kamar ba ta da lafiya, ta rasa takaimeme meke damunta, ga Wani yanayi da ta tsinci kanta, tun shigarta motar Sadik duk da ba yau ta fara hawa ba, amma ta kasa tantance yanayin da ta shiga. Ga shi ƙasan cikinta yana mata ciwo kaɗan kaɗan, amma babu wanda ta gayawa, to wa ma zata gayawa? Ummanta da ba ta son taje in da take? Ko kuma ƙannenta maza?. Jin ciwon be takura mata bane, yasa ta cigaba da sabgogin ta. Tun bayan sallar isha'i da tai, ta samu guri ta zauna ta shiga tunani daban daban, a baya ko bisa kuskure Sadik ya taɓa jikinta, se ta nuna masa taji haushi, amma haka nan yau ba ta ji haushin hakan ba, sema kasa manta hannun sa da tayi, da irin ƙamshin turarensa. Nan ta lalace a gurin da Tunanin Sadik,ba ta taɓa sanin haka akeji a soyaya ba, Sadik ya koya mata son sa. Ji tai tana son yi masa bangajiya, amma da wace wayar? Nan ta shiga tunani, can wata dabar ta faɗo mata, ta tashi ta tafi ɗakin Umma, ta tarar da Umman na shirin kwanciya. Cikin sanyin jiki tace "Umma, dan Allah aron waya nake so ki bani, zan duba wani abu a internet" Nuni tai mata da in da wayar take, ta juya ta kwanta. Cikin farinciki taje ta ɗau wayar Umman, ta koma ɗakinta zuciyarta cike da farinciki. A gajiye sosai Sadik ya koma gida, sallar isha'i kawai yai, ya haye gadon sa, dan ya gaji sosai. Cikin sa'a bacci yai awon gaba da shi. Cikin baccin yaji wayarsa na ringing, a fusace ya ɗago wayar, amma yaga Farhan ke kiransa da layin. Murmushi yai, ya katse kiran ya kirata. "Assalamu alaikum" ta faɗa cikin sassanyar muryarta. Shiru yai yaƙi amsawa, ta sake maimaita sallamar amma yai shiru. "Hello ba ka ji na?" Murmushi yai cikin muryar bacci yace "Ina jinki fa" Dariya tayi tace "ji shi kamar wani Baby" "Ummmm ai Babyn ne, dan na tashi daga Babyn Mother Babyn Princess ne" Wata kunya ce ta lulluɓe ta, har mamakin Sadik take idan yana wani abun, ta rasa ina yake koyo manyance, da iya soyayya. "Ya naji kinyi shiru? Ina fatan ba ai miki faɗan kin daɗe ba?" Tai ajiyar zuciya tace "ba aimin ba" "To Alhamdilillah, a ina kika samu waya?" "Wayar Umma ce, nace mata zanyi abu a internet ne" Wani murmushi Sadik yai wanda shikaɗai yasan ma'anarsa. "Ya naji kana dariya?" "Dole inyi dariya mana, 'yar budurwata ta faller sona sosai, tunda zata iya ƙarya ta karɓi waya dan taji muryata" "Nice nake ƙarya ko?" "No, ba haka nake nufi ba, sorry bugun zuciyata, the only Moon in the sky, My little angel, my diamond Baby" Dariya tayi tace "to ya isa haka, wai a ina kake koyo wannan abubuwan?" Gyara kwanciyarsa yai yace "to ta ya bazan koya ba? A gabana Yayana ke ta sa soyayyar, lokacin muna tsohon gidanmu a ɗaki ɗaya muke kwana, a gabana yake soyayya, ga fina finai da nake kallo, ƙarewa ma Daddy da Mother ba sa ɓoye yadda suke son junansu ko a gabanmu ne, to meyasa ba zan iya soyayya ba" Zare ido Farhan tai tace "kai! Mother kuma?" Sadik yace "eh mana Mother, a gabanmu suke cewa suna son juna, basa ɓoye soyayyar su duk da sun tsufa maimakon su barmana" ya ƙarasa Maganar yana murmushi. Shiru Farhan tai, ta ɗan tafi tunani anya tunda take ta taɓa ganin wani abu makamancin soyayya a tsakanin iyayenta? Iya abunda take gani shine law and order, biyayya da hidima amma ba ta ganin wani abu makamancin na so a tsakanin su. "Kin tasheni daga bacci, kin ƙimin hira kinyi shiru" Dawowa tai daga tunanin tace "au ka fara bacci ne?" "Eh, na fara bacci wayarki ta shigo" "To ba yanzu zaka koma baccin ba, cigaba da yi min hira" Yanzu Sadik ke ƙara tabattar da Farhan ta iya hira, samun wanda za tai hirar ne babu. A shagwaɓe yace "ni bacci nakeji" "Ni kuma bana jin baccin" "Ke gobe in Allah Ya kaimu za'a ɗaura Aure, da wuri zan tashi ki ƙyaleni" "Aushhh" ta faɗa a raunane. Da sauri yace "lafiya kuwa?" "Cikina ne yake ciwo" Sadik yace "ya salam, ko kinci wani abun ne?" "A'a seda safe kawai" Cikin damuwa yace "wait, ki sha magani karki kwanta kina jin ciwo kinji Babyna" Da hmmm kawai ta amsa masa. Ta katse kiran, cikin sanɗa ta je ɗakin Umma, ta tarar tuni Umman tayi bacci ta ajiye mata wayarta ta fito. Haka cikinta ya cigaba da yi mata ciwo, wanda ta rasa ina ne ma yake ciwon. Sadik yai rigingine, a hankali ya furta ya rabbil izzati ka tsareni faɗawa halaka, Allah kasa iyayenmu su yadda su Auran yarinyar nan, ina sonta Sosai, Allah ka aurar dani da wuri. Ya ƙarasa yana lumshe idon sa. Inna kuwa bacci ɓarawo ne ya ɗauke ta, ƙarshe cikin dare ta tashi tai Alwala tai salla, ta dinga addu'oi tana nemawa zuriyarta da al'ummar Musulmi shiriya, amma ta girgiza da yanayin rashin tarbiyyar da ta gani a tsakanin yaran ƙarshen zamani, masu ji da RUƊIN ƘURUCIYA! Sadik ya kwana da begen Masoyiyyarsa, cike da mafarkai masu tabattar da lafiya da nuna alamun girma ga ɗan Autan na Alhaji Abdullahi. Farhan kuwa da ƙyar tai bacci, gefe guda ciki na ciwo ga kuma tunanin soyayya. Bayan sallar Asuba, Sadik ya koma bacci, kaɗe kaɗe da bushe bushen da suka cika gidan ne, suka sa ya farka. Windown ɗakin sa ya buɗe ya leƙa, yaga manyan motoci anyi parking ɗinsu, ga maroƙa da manyan mutane sun cika harabar gidan, alamar ana shirin tafiya gurin ɗaurin Aure, kuma masu bushe bushen ya tabattar masa da Hakimi ya ƙara so. Cikin hanzari ya shiga ya watsa ruwa ya fara nasa shirin shima, dan tuni hayaniya ta cika BQ ɗin, abokan Dr. Sun cika part ɗin suna shiryawa. Rufe ɗakinsa Sadik yai, ya cigaba da shirinsa cikin nutsuwa. A babban falon gidan Hakimi ya zauna, ya sha kayan sarauta se zuwa ake ana kwasar gaisuwa, ana ta gaggaisawa cikin girmamawa kasancewar sa mutum me barkwanci. Nana kam ta dinga murna, fa zuwan Hakimi taje ta maƙalƙale shi, ta zauna a inda yake, tana nuna yadda tai kewarsa. Ƙarfe goma shaɗaya aka kammala haɗuwa, aka nufi babban masallacin unguwarsu Amarya Jidda in da za'a ɗaura Auren. Nan ma Mother ta sha ado, tai kyau kamar itace Amarya se zuba ƙamshi take, ta sha shadda hannunta da wuyanta duk gwal, da ka ganta ka ga matar manya. Ƙarfe ɗaya aka dawo daga ɗaurin Aure, aka dinga shigowa ana Allah ya Sanya Alkhairi ana ɗaukar hotuna. Hakimi ne ya fara shiga falon, se Alhaji Abdullahi da 'ya'yansa, abun da yafi ƙayatarwa shine, duk sun ɗora farar Alkyabba me aikin blue, akan fararen shaddojin su, ga naɗi da akayi musu, sunyi kyau matuƙa gaya. Inna ta kalle su tai murmushi tace "Allah ya shirya mana zuri'a" dan ganin su cikin wannan kamalar ba ƙaramin burgeta yai ba. Nan aka zauna Hakimi ya dinga addu'oi, tare da Nasiha ga angon da kuma iyayensa, tare da yi musu gargaɗi akan shiga sabgar ɗan da matarsa idan ba aka abunda ya zama dole ba. Daga ƙarshe yace "Nagode Allah, sannan nai farinciki da Allah ya aramin rai na ga Auran jikana na fari, idan ina da rabo Allah ya nunan na sauran, na Faruku da na wannan abokin nawa, mara son mutane" Yai maganar yana kallon Sadik, ba kunya Sadik ya gyara Alkyabbarsa yace "zama ka gani insha Allah, dan nawa za'a fara wata shekarar sannan nan wannan" yai maganar yana nuna Faruk. Hakimi yai murmushi yace "Allah yasa" Abba kuwa daƙuwa yaiwa Sadik yace "Ƙaniyar ka, mara kunya wayake ta taka, kaida ko sakandiren baka gama ba, next year by now insha Allah kana Amurka ko jamus kana karatu" Ɗan tura baki Sadik yayi, yayin da Inna take bin su da ido tana nazartar, duk wani motsi na Sadik ɗin. Da Yamma Hakimi ya ja tawagar sa ya koma, yayin da Inna tace ba zata bisu ba, za ta koma daga baya akwai abunda za tayi kan ta taho, ƙila se bayan sati da bikin. Nana tace ita kuma za ta bi Hakimi ta koma ƙauye, Inna tace ba in da zata yadda suka zo tare za su koma. Nana ba taji daɗin hakan ba, dan harga Allah ta gaji da zaman Gidan nan dan ba ta ga zaman me zasu yi ba bayan an gama biki. Bayan sallar isha'i, 'yan uwan Amarya suka kawota gidan su ango gaida surikai, kan a kaita nata gidan. Aka dinga mata Nasiha da Addu'oi, sedai kana kallonta kasan itama 'yar boko ce, ba wani kuka da take yi, gashi a ƙalla ta kai shekaru ashirin da bakwai. Inna ba tace komai ba, se mamakin yadda ake ajiye 'ya'ya sukai mizani kamar wannan ba aure da sunan boko, bayan mutane ne su ba ƙarafa ba, a haka ake lalacewa Garin zurfafa bokon nam, dan Akwai lokacin da tilas jiki na buƙatar abokin rayuwa, kuma ga uwa uba gurin yin bokon a cakuɗe ake maza da mata, dan itama dangin amaryar da 'yan makarantar ta su ba ƙananan shakiyayyai bane, irin abunda suka dinga yi a gurin bikin. Da gani baza'ace Jidda miji ta rasa shi yasa ba tai Aure da wuri ba, saboda ta na da kyau sosai, ra'ayin Auren ne kawai ba'aiba se an gama bokon da suka ɗauketa kamar wani tikitun jin daɗin duniya, ba 'a taɓa cewa ba za'a aurar da 'ya se ta sauke Alqur'ani ba, da wasu litattafan addini ba sedai ace se ta gama boko. Haka Inna tai ta zancen zuci ita kaɗai, aka gama yi wa amarya nasiha aka tafi rakata ɗakin miji. Shikam Sadik ji yake dama shine yai wannan Auren haka, amma ace ba za'ai wa mutum Aure ba se bayan ya gama boko, idan kuma mutum ya mutu be gama bokon ba kuma beyi Auren ba fa? Shikenan Allah ya yayewa Dr. An bar shi shida Faruk a wannan wahalar. Ya dinga tsaki yana juyi, yai ta zuba ido ko Farhan za ta kirashi, amma shiru ba ta kira shi ba, kuma gashi tace idan ba ita ta kira ba karya kirata, gashi tace masa cikin ta na ciwo yana son yaji halinda take ciki. Ƙarshe dai se haƙura yayi ya kwanta bacci. Akai biki aka watse, amma Mother ta ga Inna taƙi tafiya, ta na so tai magana ta na jin tsoro, amma ita har ga Allah ta gaji da zaman Inna, dan wajen watan ta guda a gidan, tun da su kai Aure da Alhaji Abdullahi Inna ba ta taɓa zuwa ta kwana a gidan ba, se a wannan karon, kuma ita har ga Allah zaman na Inna ya isheta. Alhaji Abdullahi na shan cofee ɗinsa da daddare kamar yadda ya saba, Mother na sake gyara masa shimfiɗa, tana saka turaruka tace "D mace ba kuyi magana da Inna yaushe zata tafi bane?" Ya ajiye kofin hannunsa yace "kina da damuwa da hakane?" "A'a, naga ba ta taɓa zuwa ta daɗe haka bane" Yace "to se a kai yaya? Ba ta da ikon yin hakan ne? Ko kin manta gidan ɗanta ne?" "A'a ban manta ba, kawai na tambaya ne" Be kuma ce mata komai ba ya cigaba da shan cofee ɗin sa. Bayan sallar Asuba, gari yai haske sannan Inna ta koma bacci, Nana na ganin Inna ta kwanta bacci ta tashi ta fito, ita gaba ɗaya kamar akan ƙaya take, ta gaji da zaman Gidan nan, ta rasa zaman me suke a gidan suka ƙi tafiya. Zuwa yanzu ta saba da masu gadi da ma'aikatan gidan, saboda shegen surutun Nana da san gwaninta, gata da shiga rai dan haka duk sun santa. Faruku ya fito hannunsa riƙe da kwando, da manyan flask na Abinci a kai. Da sauri ta ƙarasa in da yake tace "ina kwana" Yai murmushi yace "lafiya ƙalau, kina lafiya" Maimakon ta amsa seta jinjina masa kai. Tace "kawo in tayaka ɗauka" Yace "No ya miki nauyi, gidan amarya zanje kai musu Abinci, ko zaki rakani?" Da sauri Nana tace "eh zan raka ka, dama banje ba" Yace "ok let's go" Ta bishi zuwa mota, ya buɗe mata gaba ta shiga, ya ajiye Abincin a bayan motar, ya kunna suka tafi. Sun ɗanyi tafiya, kan su ƙarasa gidan Usman, suna tafe suna hira da Nana ta na zuba masa shirme kala kala. Gidan babba ne, sedai be ka gidan su Girma, buzun da ke gadin gidan yana ganin Motar Faruk ya buɗe musu, suka gaisa da Faruk, ya shiga da motar. Ta ƙarewa harabar gidan kallo, sannan ta kalli Faruk tace "gaskiya gidan nan me kyau ne, yayi kyau sosai" Yace "dagaske?" "Allah yayi kya masha Allah" "Zan gayawa dr. Ince kin yaba gidansa, kimce yayi kyau" Ɗan kwaɓe baki Nana tai, dan da Dr. Da Sadik ba suyi mata ba, Dr. Ba shi da fara'a Sadik kuma bashi da mutunci. Ƙofar falon Faruk yai knocking, sun ɗan jira, 'yan mintuna sannan aka buɗe. Dr. ne ya buɗe, da alama bacci suke, Faruk yace "wai haryanzu baku tashi ba?" Uasman ya ɗan yamutsa fuska yace "kai kullum seka dinga mana sammako haka, ka dena kawo Abincin nan haka Please" Faruk yace "Ai nima Umarnin Mother nake cikawa, ita zaka cewa a dena kawo muku Abinci" Usman yasa hannu ze karɓi flasan Abincin, amma Faruk yace "meye haka? Wallahi semun shiga, Nana wants to see your bride, semun shiga" Ya ture Ussy ya shige, Nana tabi bayansa tana leƙa fuskar Usman, ko zeyi Magana, amma taga beba, se yamutsa fuska da yake alamar an takurashi. A Falo suka zauna, Usman ya wuce bedroom ya barsu, Faruk ya kunna musu kallo yace "muna nan, ka gama kumburin ka, se Nana ta ga amarya" Nana tace "naga kamar yaji haushi fa, ko mu tashi mu tafi ai naga gidan, kuma naga amaryar ranar biki" Faruk yace "ba haushi yaji ba" "Amma ai naga ya sha kunu fa" "Ai shi haka yake, ba ya dariya sosai shiyasa ba'a fiye gane ɓacin ransa ba, koma yaji haushin ƙyaleshi kawa, a nan ma zamu karya muci har na rana sedai su fashe shi da amaryar" Dariya Nana tayi tace "idan zasu fashe semu tafi" Ya biye mata suka cigaba da hirarsu, kusan mintunansu talatin, sega Jidda ta fito ita da Usman, tana sanye da doguwar riga da hula akanta. Tana ganin su Faruk, tai murmushi tace "Afuwan uncle, mun barku a falo ban san kunzo ba, be tasheni ba" Faruk yace "ai dama nasan baze tashe ki ba, nikuma nace muna nan se kin tashi" Tai murmushi tace "ya gida ya Mother na" "Tana lafiya ƙalau, tana gaisheku, ima bacci na ta kirani a waya, wai inje Kitchen in ɗakko Abinci in kawo muku, mun kawo kuma mijinki se wani haɗe rai yake yi" Banza Dr. Yai musu, ya zauna ya ɗau remote yana canza chanel. Nana ta kalli Jidda tace "Ina kwana" Jidda tace "Lafiya ƙalau, ya kike?" Nana a ranta tace "wai su wannan suyi hausa ma se sun mata iyayi" a fili tace "lafiya ƙalau" Jidda tace "Uncle ina kuka sami wannan ne? Naga dai ba Khairat bace, Khairat ta girmi wannan, kuma gashi tana kama da ku" "She's our little sister" "Haba dai, dama Mother na da 'ya mace ne?" "Cousin sister ɗinmu ce, tana gidan Hakimi ne ita" Jidda tace "Allah sarki, sannunki kinji" Nana tai murmushi kawai, Usman yana ta canza tashoshi, ya kamo MBC3 ana film ɗin up, Nana tai farat tace "laaaa cartoon dan Allah a bar mana" Camzawa yai ba tare da ya kula Nana ba, Jidda cikin shagwaɓa tace "haba Baby, dan Allah ka bar mata mana" Ba shiri Nana tace "subhanallahi Baby kuma" Take dariya ta ƙwace mata, ta kalli girman Usman fuska duk gashi, amma ana ce masa Baby. Dariya Jidda tai tace "it sounds strange to you ne? Yayi girma ince masa baby ko?" Nana dai dariyarta ta cigaba da yi, dan babyn nan ya bata dariya sosai. Faruk yace "mu fa gaskiya ba mu karya ba, dan haka a haɗa Abinci mu ci" Jidda tace "eyya sorry, kar ace ina da rowa ban san ba ku ci Abinci ba ai, bari in ɗakko plates se mu karya tare. Ta ɗakko kwanuka a Kitchen, ta zuzzuba Abincin ta haɗawa kowa tea ta bashi, suka fara  ci, sedai Nana ta kasa sakin jiki taci Abincin se ɗan tsakurar sa da take saboda su Faruk da ke gurin. Maimakon da suka gama cin Abincin su tashi su tafi, se suka shantake a gidan dan Jidda ba ƙaramin dariya surutun Nana yake bata ba. Inna kuwa tun bayan farkawarra ba ta ga Nana ba, ta zaci ɗan fita falo tai zuwa harab zata dawo, amma taji shiru ba taga motsinta ba, Nan da nan ta fita nemanta da kanta, sedai ba Nana ba alamarta a gidan nan. Hankalin Inna ya ɗaga ta shiga tanbayr masu gadi, da masu aikin gidan amma suka ce ba su ga Nana ba. Da hanzari Inna ta koma babban falo, wanda yai daidai da fitowar Alhaji Abdullahi, kallo ɗaya yaiwa mahaifiyar ta sa ya fuskanci akwai matsala. Cikin damuwa yace "Hajiya Inna, lafiya kuwa?" "Yarinyar nan ce ban gani ba, tunda na farka ban ganta ba, bata gidan nan" Yace "Subhanallah, garin yaya babu kuma wanda ya aiketa?" "Bana tunanin hakan, dan ba in da ta sani" Mother ce ta fito ita da Sadik, daga sashen ta, tai tozali fa su a tsaye cirko cirko. "Lafiya kuwa?" Mother ta tanbaya. Alhaji Abdullahi yace "Nana ce ba'a gani ba, tun ɗazu ba ta gidan nan an tambayi masu gadi sunce ba su ganta ba, ka ga Sadik ka fita ka ɗan zazzaga layu kan nan ko wani gurin ta fita. Ɗan buɗe baki Sadik yai yace "Abba ni ta ina zan fara neman ta? Ina zan nufa?" "Koma ina ne ka nufa, kaje ka zazzaga ko Allah ze sa ka ganta" Ran Sadik yai matuƙar ɓaci, ya bar falon yana ƙunƙuni, wai ya fita nemanta se kace wata Akuya. Mother kamar za tai magana, amma ta fasa dan ta kula kamar kwanan nan Inna zuga Alhaji Abdullahi ta ke, da ta ɗanyi masa kuskure kaɗan se ya fara mata masifa. Nana kuwa tare suka shiga Kitchen da Jidda su kai girkin rana, suna yi Jidda na cin dariyar Nana, babban abunda ke ƙara bata mamaki da burgeta game da Nana be wuce yadda Nanan ke magana da manyance ba, a shekarunta wasu abubuwan tayi ƙanƙanta da faɗinsu, amma ba abun mamaki bane, tunda a hannun tsofaffi take. Yayin da ita kuma Nanan ke manakin yadda Gaba ɗaya suke magana da iyayi, magana ɗaya biyu se anyi turanci, turancin ma me wuyar ganewa irin na turawa, ga yadda Jiddan ke zubawa Dr. Shagwaɓa a gabansu ba kunya. Se bayan azahar, sanan Faruk yace Nana ta tashi su tafi. Jidda tace "gaskiya uncle ka barmin Nana, idan zasu koma se ka zo ka tafi da ita" Faruk yace "taɓ, ai wallahi kakarta ba zata yadda ba, ki bari in kin tambayi izinin Hajiya Inna, shikenan" Nana ta shiga ran Jidda sosai, ta haɗa mata sha tara ta arziki, su kai hotuna sannan suka nufi komawa gida. Sadik kuwa yana tafe yana masifa ya koma gida yace shi be ga Nana ba, gaba ɗaya aka dinga jimamin in da Nana ta shiga, hankalin Inna ya gama tashi, Alhaji Abdullahi yana ko report za'a kai gun 'yan sanda. Turo ƙofar ɗakin Nana tayi, hannunta rungume da kaya ta shigo da Sallama, gaba suka waigo suna kallonta. Se yanzu ta sha jinin jikinta, ta tuna ba ta sanarwa da Inna zata fita ba. A fusace Inna tace "daga ina kike?" Kafin ta amsa, sega Faruk ya shigo falon shima. Ya kalli su Abba yace "Abba lafiya na ganku a nan?" Abba yace "Nana ake ta nema, kuma se gaku tare" Faruk yace "ai ni ne nace ta rakani gidan dr. Mu ka kai musu Abinci, daga nan kuma muka zauna se yanzu, laifina ne ayi haƙuri please". Wani uban tsaki Sadik ya ja yace "wallahi wannan Yarinyar ba tayi ba, ta sa aka wahal da ni ina zaga layuka nemanta kamar ɓarawo" Murguɗa baki tai tana hararar Sadik, ya ƙara harzuƙa yace "wallahi nazo gurin nan sena tataka ki, na tsani yarinyar nan tunda ta zo gidan nan take wahalar da mutane' "Seka kasheni ai tunda ka tsaneni, masu gida na ga ma kunkuru da yake yawo da gidansa a ka, se ka naɗa gammi ka ɗau gidan naku a bayan ka ai" Inna tace "rufemin baki kan in zo in gurza wannan shegen bakin naki, kai kuma kayi haƙuri kaji zamu bar muku gida, ba kai kaɗai ba naga alamar matar gidan kanta mun isheta, zamu tafi Insha Allah, gara mu tafi ka dena ganinta kana ƙara tsanarta" Mother tace "to ni kuma meye nawa a ciki?" Faruk yace "dan Allah kuyi haƙuri, dul laifina ne wallahi" Abba kam ya fusata sosai da abunda Sadik yayi, ya tabatta abunda Inna ke faɗa yaransa ba su da tarbiyya, dan haka yace "Sadik faɗan da nai maka ta dama ya shiga ya fita ta hagu ko? A gabana ka ke cewa ka tsani Nana ko, duk da matsayin ta a gurina, Nagode amma ka sani nafi ƙaunarta fiye da kai ɗan da na haifa a cikina, shashasha mara ɗa'a" Da sauri Sadik ya ɗaga kai ya kalli Abba, jin Abba yace wai ya fi son Nana da shi. Nana kam sumsusm ta wuce masaukin su, Inna ma ba ta sake cewa komai ba ta bi bayan Nana, taje ta sameta a ɗaki, ta dinga mata faɗa ta inda ta shiga ba ta nan take fita ba, dan seda Nana tai kuka. A lokacin Inna ta saka Nana ta fara haɗa musu kaya, dan ta ƙudirce a gobe in Allah ya kaimu zasu bar gidan. Da daddare Sadik ya buɗe ɗakinsa na cikin ƙaton falon da ke daf da ƙofar sashin Mother, saboda yanzu gidan ba kowa. Ƙofar ɗakinsu Inna a buɗe tana jiyo hirar da Mother take da Sadik. Sadik yace "Mother, nifa banji kin yaba sirikar taki ba" Mother tace "ai sirikata son kowace ƙin wanda ya rasa, ga ilimi ga kyau ga gayu, ai Jidda tayi ta ko ina" Sadik yace "Mother ba wannan ba, yarinyar da na kawo ku gaisa da ita Ranar Mother's evening fa" Mother ta ɗanyi shiru tace "wace yarinyar ce? Namanta wallahi" "Mother, wata Fulani girl da na kawo miki, har kuka gaisa kina magana da su Anty Naja lokacin" Mother tace "to ai Mutanen da yawa ba lallai in tuna ba" "Please Mother ki tuna ta mana" "Kai ka ƙyaleni, ni ban tuna ba, ya ma akai ta zama surikata?" Ɗan sosa kai yai yace "eh, in law ɗinki ce to be in the next couple's of year's, not year's ma in next year Insha Allah" "Wai tsaya, ba dai budurwar Faruk bace, aikuwa zeci ƙaniyarsa ze gamu dani, he better concentrate in his studies, karma ya ɓatawa 'yar mutane lokaci, shine y turoka da ita?" Sadik yace "Ohhh my God, Mother she's my fiance, budurwata ce fa" "What! Me kace?" "Mother you heard me fa, and you are still asking me" "Ai dole in sake tambaya, wace irin maganar banza ce wannan? Ina kai ina wata budurwa, ko secondary School ba ka gama ba" Ɗan kwaɓe fuska yai yace "Mother, am finishing secondary School this year insha Allah, zan kammala secondary School a wannan shekarar, Abba yace in zaɓi kowace school nake so a duniya ze kaini, kan in gama degree ta kammala secondary ita, ni da ze yuwu ma, da se mu tafi can in da zanyi karatun ni da ita" Wani banzan kallo Mother ta watsawa Sadik, ta ja tsaki ta maida hankali kan TV. "Mother i meant what I said, Aure nake so inyi please, ki sa baki dan Allah, kinga ko da kuɗin plazar mu zan iya riƙeta, se Abba ya suponsoring karatunmu, ina son Yarinyar ne Please Mother ki sa baki, dan... "Shut up Sadik!" Mother ta faɗa a tsawace. "Kasan me kake faɗa kuwa, haryanzu ba ka cika shekaru goma sha takwas ba, uban waye ze maka Aure, me kai achiveing a rayuwar ka da har zaka fara tunanin wani Aure? Get out from my side, kaje ka kama litattafanka, kayi karatu ka zama wani abu kafin ka fara wata maganar aure, Allah ya ƙara nunamin kayi Wannan zancen" Sadik ya ƙulu da jin zancen Mother, dan gani yake kamar kalaman nata na nisanta shi da mallakar Farhan ɗin. Fuuuuu ya tashi ya bar falon a fusace, ya fasa kwana a ɗakinsa na cikin gida da yai niyya. Inna kam duk da taji hirar ta su girgiza kai tayi, da jinjina gaɓunta irin na wasu iyayen na wannan zamani,kamata yai yadda yaran suka zama na zamani, iyaye ma su zama na zamani a gurin tarbiyya. Suna ta ihun ilimi ilimin zamani, amma takasa amfani da hikima da ilimin akan ɗanta. A fakaice yana wa mahaifiyarsa nuni da waye shi ne? Da kuma abunda yake so amma ta kasa ganewa, hakan yana faruwa a farkon a ƙuruciya, wanda wasu yaran kan zo musu da RUƊANI, idan ba su samu kyakykyawar kulawa da shawarwari ba se a samu matsala. Yanayin Sadik, da abunda suka dinga yi shida abokansa a gurin bikin nan kawai, ya isa ya nuna maka waye shi, a ɗan zaman nan nata tana ankare da halayyar yaron. Ba dan gudun shiga abunda be shafe ta ba, da tayi abunda ya dace akan Sadik, amma tayi alƙawarin fita daga sabgar su gaba ɗaya, idan lokaci yayi iyayen Sadik zasu hankalta, da maida hankali akan yaransu, sedai zata taya su da addu'a Allah ya shirya mata zuriya ya tsaresu da taɓarɓarewar ƙarshen zamani da RUƊIN ƘURUCIYA! Domin gyara Sharhi ko shawara Ayshercool 07063065680. Kar a manta a garzaya shafin Arewabooks, domin cigaba da samun littafai na, kuyi following ɗina @Ayshercool. https://arewabooks.com/book?id=6220842688e1ec3a0410329f. [6/4, 4:21 PM] Jakadiyar Arewa: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ RUƊIN ƘURUCIYA PERFECT WRITERS ASSOCIATION (WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS) https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ P. W. A *Story and written by* AISHA ADAM (AYSHERCOOL) Writer of WATA KISSAR..(Sai mata) ABDUL JALAL AƘIDATA (paid book) WUTA A MASAƘA NOW RUƊIN ƘURUCIYA (paid book) _Labarin RUƊIN ƘURUCIYA, na iya zuwa da wani salo, wanda baku saba ganinsa a rubutuna ba, hakan ya biyo bayan akan abunda aka gina labarin, wani abun ze ɓoyu wani Abun baze ɓoyu ba sakamakon labari ne akan teenegers, yara masu tashen Balaga, but hakan ba ya na nufin na sauka daga kan tsarin yadda nake Rubutu bane, ƙofata a buɗe take dan karɓar ƙorafi, gayra ko shawara_ ⚠️⚠️⚠️ƘIRƘIRARREN LABARI NE, BAN YADDA A JUYAMIN SHI TA KOWACE SIGA BA SEDA IZININA ❌❌‼️       SHIN KUNA DA LABARIN MANHAJAR AREWABOOKS KUWA? MANHAJA CE DA TAZO DA TSARIN DAN SAUƘAƘAWA MARUBUTA DA MAKARANTA SAUƘIN CINIKAYYAR LITATTAFAI. TA IN DA ZAKU IYA SIYAN KOWANE FEJI AKAN KUƊI ƘALILAN, DAI DAI DA ALJIHUNKU. INA FARINCIKIN SANAR DA KU CEWA, DA ZARAR NA KAMMALA FREE PAGES, ZAKU CIGABA DA SAMUN CIGABAN LITTAFIN RUƊIN ƘURUCIYA, AKAN MANHAJAR AREWABOOKS. KARKU BARI A BAKU LABARI, AKWAI TARIN DARASIN RAYUWA A CIKIN LITTAFIN. Sadik a fusace ya koma BQ, ya shiga ɗakinsa ransa na masa ƙuna. "Wannan wace irin rayuwa ce? Boko boko boko! Kamar bokon nan ce tikitin jin daɗin duniya, shikenan dan mutum zeyi boko baze aure ba?" Wani tsakin ya kuma yi, tare da fesar da iska daga bakinsa. Meyasa Mother taƙi goya masa baya a wannan karon? Meyasa ita kullum take kallon shekarunsa da ƙanƙantarsa? Ɗan gajeren tsaki ya kuma ja, ya haye gadonsa ya kwanta yai rigingine, take Farhan ta kuma faɗo masa, wani irin shauƙin sonta na ƙara ratsa shi sannu a hankali tabbas son da yake mata ba RUƊIN ƘURUCIYA ba ne, soyayya ce da ba ruwanta da girma ko yarinta. Wayarsa ya ɗakko yana kallon hotunan ta da yake wayarsa, she's cool and Beautiful, uwa uba ta na da tarbiyya da ɗa'a a nutse take. Ya shafi screen ɗin wayar ta sa, ya lumshe ido yace "I love You Farhan" yai Maganar a hankali, yana sauke ajiyar zuciya. Kamar wanda aka tsikara, ya tashi zaune, ya janyo system ɗin sa, ya kunna, Series ɗin nan da yake kallo ya nemo, ya kunna ya cigaba da kallon sa ba tare da fargabar Komai ba, a tunaninsa hakan ze ɗauke masa hankali da rage masa damuwa. Ya cigaba da kallo, daga episode ɗin da ya tsaya a baya, Film ɗin yana cigaba da nuni da tsantsar soyaya me tsuma zuciya, sedai ba ta sauya zani ba, akwai adult content a cikin Film ɗin, kusa kaso arba'in ɗari na film ɗin in da yafi karkata kenan. Rikicin film ɗin na ƙayatar da shi, rikicin masarauta da na Soyayya. Amma maimakon hakan ya ɗebe masa kewa daga damuwarsa, sema sake faɗawa wata damuwar da yayi. Kamar wanda aka mintsuna, haka ya kashe socket ɗin da system ɗin ke jone, ya rufe System ɗin ya ja wani uban tsaki, ya kife akan gadonsa yana sauke numfashi sama sama. Haka yai ta juyi, tare da jera tsaki ba adadi, kan bacci yayi awon gaba da shi. Da sassafe Inna ta fito falo, ta tarar da Mother ta fito ta na bada umarni ga masu aikinta, akan abunda za a girka. Mother ta kalli Inna tace "Ina kwana" Inna tace "lafiya ƙalau, nace Bawan Allah  ya tashi ne?" "A'a be tashi ba" Mother ta bata amsa. "Ta so min shi" Inna ta faɗa ta na zama. Mother tace "ba ya son a tashe shi idan yana bacci, ya hana tashin sa idan ba shine ya tashi ba" Inna tace "umarni na ne, a tasomin shi" Mother ta juya tana ɗan hura hanci, dan takurar Inna tayi yawa. Kusan 10minutes se ga Mother ta fito, ita da Alhaji Abdullahi. Sedai Inna ba ta falon, Alhaji Abdullahi yace "bari in duba ɗakin su" Ya nufi ɗakin Inna, yana zuwa ya tarar da ita a gefen katifa a zaune. Ya rusina yace "barka da safiya" Inna tace "Yawwa, ka tashi lafiya?" "Alhamdilillah, amma yana ga Kamar kin tattare komai?" Inna tace "Ehh, dama nace ai maka magana ne da azahar kasa a maida mu gida, zaman ya isa haka na gama abun da ya zaunar da ni" Alhaji Abdullahi yace "Amma Inna da wuri haka cikin gaggawa? Ko dai wani abun akai miki a gidan?" "Babu ɗaya, kawai ina son tafiya ne kawai" "Amma Inna, ba ki gayan da wuri ba ba'a shirya muku komai na komawa ba" "Ni ba wani abu da nake buƙata daga gurinka, abu ɗaya ne zan sake maimaitawa shine ka kula da tarbiyyar yaran ka, ka saka ido sosai ka gane meye damuwarsu sannan meye mafita ga damuwar ta su ba wai abunda kai kake so ba" Shi dai Alhaji Abdullahi be gama fuskantar in da maganganun na Inna suka sa gaba ba, amma yace "Insha Allah za'ai yadda kika ce" Tace "Yawwa da azahar zamu tafi Insha Allah" Ya tashi ya fita jikinsa a sanyaye. Yau sam Sadik yaƙi shiga cikin gidan, ko gurin Mother be je ba, saboda ransa a ɓace yake gaba ɗaya. Yana zaune a falo yana video game, Faruk ya fito daga ɗakin sa yace "kai Muje Abba yana neman mu" Sadik ya kalleshi yace "ina fatan dai ba wani abun nai ba?" Faruk yace "nima ban sani ba, kawai dai ya kirani a waya ne Yanzu". Sadik yace "ina zuwa" "Karfa ka ƙi zuwa ace ban gaya maka ba" "Kayi gaba kawai, zan zo" Faruk ya fice daga falon nsau. Yana isa harabar Gidan yaga Alhaji Abdullahi ya yo wa Su Inna rakiya, an saka Akwatin su a Mota. Da sauri ya ƙaraso yana faɗin "ya naga haka kuma?" Abba yace "eh za su koma ne, shiyasa na kiraku kuzo kuyi sallama" Cikin damuwa Faruk yace "tafiya ba sanarwa haka? Inna meyasa zaku tafi?" "Gidanmu zamu koma, ai mun zaunu a gidan nan, kuma gashi za'a koma makaranta" Faruk yace "Inna banji daɗi ba, ke ki tafi ki bar mana Nana a nan" Inna tai murmushi tace "Inaa ai baze yuwu ba, tana katara ta" Wani Mugun kallo Mother ta watsawa Faruk, wanda ya sashi mamakin me yai ake masa Wannan kallon. Sadik ne ya ƙaraso in da suke ya gansu a tsaye, ya kalli Abba yace "Abba gani". "Dama Inna ce za su koma, na kiraku kuzo kuyi musu sallama" Sadik ji yai kamar yayi tsaki, amma ya maze ya kalli Inna yace "ku gaida gida" Maimakon Inna ta amsa se kallon sa da take, Tun daga sama har ƙasa. Ɗan tsuke fuska yai yana basarwa, dan ya rasa dalilin da yasa Inna take masa irin wannan kallon a duk sanda suka haɗu. Yana ɗaga ido, sukai ido huɗu da Nana aikuwa ta galla masa harara. Wani Mugun kallo yai mata, ya tsani Yarinyar nan kamar ya shaƙeta. Kan su gama sallama Faruk yai sauri ya koma BQ, har sun shiga mota da sauri ya ƙaraso, ya sa hannu a Aljihunsa ya ɗakko kuɗi da wata leda, ya miƙawa Nana. Nana ta kalli Inna sannan ta kalli Faruk. Yace "karɓi mana" Inna tace "ta karɓi ledar dai, amma banda kuɗin" Faruk yace "Inna wai meyasa kike min hakane, ina ruwanki da mu ba zan bawa ƙanwata abu ba?" Inna tai murmushi tace "Allah ya baka haƙuri me ƙanwa" Nana ta sa hannu ta karɓa tace "Nagode". Yace "yawwa Allah ya kai ku lafiya, ban san zaku tafi yau ba da na muku rakiya ai" Nan suka cigaba da Sallama aka fara jan motar a hankali, Sadik yace "Allah raka taki gona" hakan ya sauka a kunnuwan Inna, amma tai kamar ba taji ba, aka ja motar suna ɗago musu hannu. Mother ji tai kamar an yaye mata damuwar ta gaba ɗaya, dan tafiyar su Inna ze sa ta sake a gidan ta, dan zaman su ba ƙaramin takura ne a gareta ba. Sedai ta ƙwafe Faruk a ranta, fan ba ta gane kan wannan rawar kan da yake ba. Sadik be shiga gidan ba, ya nufi BQ Faruk ya bi bayansa, suna shiga Sadik ya koma kan game ɗinsa, Faruk ya zauna a ɗaya daga kujerun falon Yace "Kai Allah sarki, ɗan zaman su a gidan nan na saba da Yarinyar nan wallahi, zanyi missing jokes ɗin ta, she's so Funny" "She's crazy dai, yarinya kamar Mahaukaciya bazar bazar ba nustuwa, ga surutu kamar wata parrot, ni wallahi gara da suka tafi, dama ga tsohuwar nan kullum cikin samun ido take, tai ta min wani irin kallo wanda na kasa gane kansa" Faruk yace "shut up Sadik, mahaifiyar babanmu ce kar ka faɗi abunda be dace akanta b, kome za tai ba dan ta takura mana take ba, yaushe rabonta da gidan ba zuwa take ba fa, kuma batun Nana, she's our blood sister like Khairat ban san meyasa ka tsaneta ba" "Ni yarinyar ce ba tai min ba sam, ta fiye rawar kai da fitsara" "Ni kam ba abunda tai min, ina jinta a matsayin ƙanwata" "Lallai ƙanwa manya" Sadik yai maganar yana ajiye remote ɗin hannunsa ya bar falon. Yana shiga ɗakin sa, ya cire wayarsa dake caji, ya ga message ya buɗe message ɗin ya duba. "Assalam Alaikum, ina fatan kana lafiya, am missing You, kar kai min reply wayar Umma ce, idan na samu dama zan kiraka Farhan" Jujjuya message ɗin ya dinga yi yana murmushi kamar yana gabanta yace "am missing You too Princess" Ya cigaba da kallon saƙon, mussaman kalmar am missing You, ba ta taɓa furta masa haka ba, ji yai tamkar ya shirya ya tafi gidan su. Murmushi ya sake yi yana jin yadda shima yake kewarta. Yana tuna yadda su kai da Mother jiya da yai nata zancen Farhan yaji ransa ya ɓaci, take yaji ze iya ɗaukar kowane risk dan ganin ya samu abunda zuciyar sa ke so. Se Yamma sannan su Inna suka isa gida, duk da a motar gida suke, Inna ta gaji duba da yanayin jikin girma. Nana kamar ta zuba ruwa a ƙasa ta sha, saboda sun koma gida ga Hakimi se taraiyar ta yake yi. Tabbas Nana ta yi missing ɗin Kakanta, me sonta da kuma ji da ita sosai. Duk da ta wani fannin ta ɗan ji daɗin zaman birni, amma ta kasa mantawa da baƙin halin Mother da na ɗanta Sadik, mussaman Sadik da ke nuna mata tsana a fili. Duk surutun Nana da wuri tai bacci, saboda ta kwaso gajiya sosai da sosai. "Inna wuro kun sha birni, kun barni kamar maraya ba jikata ba ke" "Hmm mun sha birni kam, Alhamdilillah gashi kuma mun dawo ai" "Hakane, ya kuka baro min su?" "Lafiya ƙalau, sedai akwai ƙura fa" Hakimi ya sake nutsuwa yace "kamar yaya kenan?" "Ranka ya daɗe, nifa sedai kace na cika ƙorafi, amma maganar gaskiya akwai gyara a gidan Bawan Allah, mussaman Ƙaramin ɗan sa, na rasa wace irin macece Hauwa" Hakimi yai murmushi yace "ba zaki dena damun kanki akan yaron nan da iyalan sa ba ko?" Inna ta girgiza kai tacee "ba damun kai bane, ina jiyewa bawan Allah abunda ka iya zuwa ya zo, akan wannan taƙadarin yaron nasa" "To wai me yai miki ne? Ni kuma kinga nutsuwarsa nake gani, lokacin da naje ɗaurin Aure mota ɗaya muka shiga da shi muka dawo, banga wani abuba tare da shi ba" "Hmm ni na gani ai, Allah ya kyauta kawai" Washegari da Safe Sadik ya shiga ɗakinsa da ke cikin babban falo, ya fito daga ɗakin kenan se ga Mother ta fito hannunta ɗauke da wata leda, ta kalli Sadik tace "wai kai uban me a kai maka ne? Ko zuwa gaisheni yau ba kai ba, tun ɗazu Abba yake ta cigiyarka? Meye hakan ka ne, kullum ba ka da aiki se yin abunda zaka jamin laifi gun mahaifinka ko danginsa" Mamaki ne ya kama Sadik, wato har Mother ta manta abunda ya faru, amma ya basar yace "Mother ba Komai fa, am not in mood ne kawai, amma ba wani abu" Faruk ne ya shigo da sallama, hannunsa ɗauke da key Yace "Mother gani na shirya, kawo saƙon in kai" Mother ta ƙarewa Faruk kallo sannan tace "Yawwa dama ba iya kai saƙo ne yasa na kiraka ba, ɗazu da ka shigo mahaifinka na nan, ba damar in maka magana a gaban sa kar yaji haushi" Faruk cikin rashin fahimta yace "Mother wani abun ne ya faru ne?" Mother tace "eh wani abu me ya faru, zaman kakarku a gidan nan, da wannan fitsarariyar yarinyar naga kana wani rawar kai, kana wani shishshsigi da neman suna, to let me tell you something, wallahi idan ma wani abu kake tunani game da Yarinyar nan gara ka cire shi daga ranka, ka maida hankali akan karatunka kar ma du fara tunanin wani abu ne a tsakanin ku suyi tunanin liƙa maka ita, ba zan amince da 'yar ƙauye a matsayin sirikata ba, dan naga su ba abunda suka saka a gaba banda Aure Aure, ko Aure za kai kafi ƙarfin wannan 'yar ƙauyen" "Ohh my God Mother, what are you trying to say? Me nayi da ya nuna ina son Nana, idan alaƙata da Khairat be sa an kirata da Soyayya ba me ze sa alaƙata da Nana ya zama soyaya, wannan 'yar ƙaramar yarinyar, You know i just love female sister that's all, ban san meyasa kike zargin wani abu ba, she's a sister to me ina sonta saboda ita kaɗaice 'yar uwamu a ɓangaren Abba that's all, amma in kinji haushi ne am sorry for that, amma ba abunda kike Tunanin bane" Duk haƙurin Faruk da alama yaji haushin maganganun Mother, Yain da Sadik shi abunda ya dame shi be wuce yadda Faruk ma me shekara kusan Ashirin da biyar ake cewa ya maida hankali akan karatu ba, balle shi da be ma cika shatakwas ba. Gajeren tsaki ya ja ya bar Mother da Faruk a falon. Mother ta dafa kafaɗar Faruk tace "am sorry my Faruk, ba na faɗa ne dan in ɓata maka rai ba, na faɗa ne dan in saka a hanya, ka maida hankali akan karatun ka ka zama wani abu a rayuwa, duk harkar matan nan shirme ne kawai, mutanen ƙauye da sunga kana nan nan da ita se suce zasu haɗa ku Aure da ita, But don't mind, zo ka kaiwa Mummy kayan nan" Faruk be kuma cewa komai ba, ya karɓi ledar hannun ta, yai waje ba tare da ya kuma cewa komai ba. Farhan duk damuwa ta isheta, duk a takure take sosai, tana son sake ganin Sadik ko ta kirashi a waya, amma ta rasa yadda za tai ta kuma samun waya ta kirashi, haka nan take jin kamar zuciyarta a takure take rashin Sadik ɗinta, saura 1 week a koma school, amma ji take tamkar Shekara guda ya rage a koma makarantar. Sadik yawonsa ya tafi, amma wajen tara na dare ya dawo gida, a falo ya tarar da Mother da Abba ga kuma Faruk suna kallo. Abba ya kalli Sadik yace "kai daga ina haka?" Sadik yace "na raka Salman ne gidan kakar su an aike shi" "Mamanka ta san ka je rakiyar?" Mother tace "A'a Abba ai naga abokinsa ne, kuma suna fita tare dama meyasa kake tambaya?" Abba yace "bana son yawan yawon nan ne, gara ya zauna a gida yai karatu" Sadik be ce Komai ba ya wuce ɗakinsa da ke cikin falon yana mita aƙasan ransa boko boko boko, an kasa fahimtar halin da mutum ke ciki se batun wata boko" Ya ƙarasa Maganar yana rufe ƙofar ɗakin, ya jingina bayansa a jikin ƙofar yana sauke ajiyar zuciya. A hankali ya taka ya zauna a gefen tangamemen gadonsa, wanda yafi na BQ girma da kyau, ya ƙurawa system ɗin sa ido, yana jin kunnawa ya ci-gaba da kallonsa, amma yana tuna halin da ze iya shiga a dalilin cigaba da kallon. Miƙa hannu yai ya ɗakko remote ɗin TV dake kan fridge ya kunna, canza tashoshi yake yana neman wadda ze kalla. Ya daɗe yana caccanza Channels, miƙewa yai da niyyar rufe tagar ɗakinsa, ya hango Mother kwance a jikin Abba, suna kallo yana bata popcorn a baki, su dai sam basa girma suna bawa junansu kulawa duk da shekaru sun fara ja, amma Mother ta kan maida Abban kamar ɗan shekaru talatin, basa ɓoye Soyayyar su ko a gaban yaran su ne. Sakin labule kawai Sadik yai a hankali ya furta "When, When will you understand that am also human being?" Ya koma ya zauna yana cije lips ɗin sa na ƙasa. Farhan a hankali ta lallaɓa ta shiga ɗakin Umma, ta tarar Umman tuni tayi bacci, cikin sanɗa ta ɗau wayar Umma ta fito daga ɗakin. Ta sa wayar a silent ta tafi ɗakinta. Ta turawa Sadik message kamar haka "Barka da dare, kwana da yawa ina fatan kana lafiya" Wayarsa tai ƙara alamar saƙo ya shigo, ya kai idonsa kan wayar, yai ajiyar zuciya sannan ya janyo wayar, ya duba yai tozali da saƙon Farhan. Hannu yasa a sumarsa yai murmushi, ya kwanta sannan ya kirata a waya. "Dama idonka biyu ba kai bacci ba?" Sadik yace "ke zan tambaya ba ki bacci ba?" Farhan tace "eh nayi tilawa ne, na ɗakko wayar Umma na kiraka" Yai murmushi yace "gaba ɗaya na koma kamar mara lafiya, saboda bana samun ganinki da jin muryarki" "Nima haka ai" "Dagaske kinyi missing ɗina" "Umm" ta bashi amsa. "Ok i understand, ya jikin naki?" "Ni meya sameni?" "Ba kince min kina ciwon ciki ba?" Farhan tace "wallahi har yanzu yana min kaɗan kaɗan, wasu lokutan idan ya far sena dena duk abunda nake sedai in kwanta" "Amma baki je Asibiti ba?" "No ai ya dena" "Karki min wasa da lafiyar ki Farhan please" ya ƙarasa Maganar muryarsa da rauni. Farhan tace "lafiya kuwa, naji muryar ka na rawa?" "Farhan Aure nake so" ya faɗa mata kai tsaye ba wata kunya ko shakka. Jin maganar tai a bazata, wai Aure yake so se taji abun wani banbarakwai. Shiru tai ta kasa Magana, Sadik yace "is sound somehow to you ko? Ban san a ya zan miki bayani ki gane ba, Farhan zanyi duk me yuwuwa in ga na Aureki nan kusa ba a nesa ba Insha Allah, ki kwanta kiyi bacci, dare yayi have a nice dreams Cwthrt" A hankali ya ajiye Wayar ba tare da ya katse kiran ba, wayar Farhan ta bi da kallo, ta na maimaita abunda ya faɗa a ranta, cikin sanɗa ta tashi ta maida wa Umma wayarta, ta ajiye ta dawo ta kwanta, tana cigaba da jujjuya maganar Prince. Kwanci tashi asarar rai, sati ya zagayo aka koma Makaranta, domin cigaba da gwagwarmaya ta neman ilimi, wanda ba'a samunsa da sauƙi, amma duk da haka a gurin neman ilimin Akwai bambanci me tazara tsakanin yaran talaka da na me kuɗi. Farhan uniform ɗinta a goge suke tsaf, se murna take za'a koma Makaranta, wanda a zahiri ba komawa makarantar ce ta sata farinciki ba, haɗuwa da Sadik take ta ɗoki. Shima nasa ɓangaren yana cike da shauƙin son ganinta, da kuma abokan karatunsa. Ɗaliban sunji daɗin sake haɗuwarsu a zangon karatu na gaba, saboda akwai shaƙuwa ta mussaman a tsakanin ɗaliban. Yana tsaye a cikin abokansa a gurin Assmebly tun daga nesa ya hangota ta shigo makarantar, ta cire ƙaton hijjabin jikinta, ta bar na makarantar da suka kasance tsangalallu. Ta ƙara ƙiba tai fresh da ita, ta ƙara cika kayan makarantar nata, sosai alamun girma ke sake bayyana a tare da Farhan ɗin. Be san lokacin da murmushi ya suɓuce masa ba, tare da lumshe idanunsa. Guri ta samu ta tsaya a cikin 'yan ajinsu, ba wanda ya kulata se Lilly da ta miƙa mata hannu su gaisa. Farhan ta miƙa mata suka gaisa, Lilly tace "An dawo lafiya" Farhan tai murmushi tace "Lafiya ƙalau Alhamdilillah" Nasir ne ya taɓa Sadik yace "dan Allah karka cimye Yarinyar nan da wannan idanun haba, wannan kallo haka" Be ce Komai ba se cigaba da murmushi da yayi. Har aka kammala Assembly ba ta gano shi ba sam, tai ta rarraba ido amma ba ta ganshi ba. Haka aka gama ta tafi aji tana tunanin ko ya dawo yau oho. A timetable period ɗin farko, Sir Nazir suke da shi. Ya shigo ajin suka miƙe tsaye suka gaishe shi, kan ya basu iznin zama ya dinga bin su ɗaya bayan ɗaya da kallo, ya ɗan tsurawa Farhan da ta sunkuyar da kanta ido, kan daga bisani ya janye idonsa zuwa kan Lilly. Ta ɓalle botiran jacket ɗin ta, ana ganin ta cikin, gashi Masha Allah ta zama budurwa ita ma, duba da yanayin girman jiki na yaran masu kuɗi, ita ma ta fara cika. A kausashe yace "Fatima, Allah ya dawo damu ko, close your jacket my friend" Ɗan tura baki Lilly tayi, sannan ta sa hannu ta rufe botir ɗin rigar ta ta. Haseena ta waigo ta kalli Lilly, ta sunkuyar da kai tana dariya ƙasa ƙasa, yai musu umarni suka zauna. Daga bisani yai musu maraba da dawowa sabon zango, yai musu Nasiha sannan ya ɗora musu da lectures na ranar. Kasancewar double period ne be fita daga ajin ba, se break yana fita Haseena ta kalli Lilly tace "to ƙarama 'yar air, daga dawowa zaki fara sa bawan Allah a gaba" Lilly tai murmushi tace "gani ba taɓawa ba asarar ido" Haseena ta ƙara samata da "taɓawa ba tafiya da shi ba asarar hannu" Lilly tace "dan ubanki hauka nake zan tsaya a taɓa, ba wannan maganar sedai in ta gwara kan mutum" Yasmin da ke ƙarasa kwafar note tace "za kiga ba me taɓawa, naga kin ƙaro wulaƙanci har wani chestout ki ke yanzu" Lilly tace "to ke ya kika gani?" Farhan na jinsu, amma ba ta ko motsa ba, ta cigba da danna carbin hannunta. Ƙamshin turarensa ne ya mamaye mata hanci, tana ɗaga kai ya zauna daf da ita a hankali yace "shine ko ki neme ni ko? Anya kinyi missing ɗina kuwa?" Murmushi tai tace "Ai na duba a gurin Assembly ban ganka ba, nayi zaton baka dawo ba" "Meze hanani dawowa inga amaryata, ni tun lokacin da kika shigo na ganki ai, Kinyi ƙiba sosai, me Ummana take baki ne haka?" Wani daɗi ne ya cikata jin yace Ummansa, ko ba komai yai mata kara ya girmama Ummanta. "Tuwo take bani" "Nima zan zo ta dinga bani gaskiya, karki fini ƙiba" Ƙaramin tsaki Haseena ta ja tace "ban taɓa ganin munafukin mutum kamar wannan Farhan ɗin ba, ba wanda ta kula amma ga yadda take wata dariya" Lilly tace "to ke da shi ɗaya ne, abunda ke jikinki shike jikinta akan me zata sakar miki fuska? Dalla ku tashi mu tafi muyi order Abinci" Wani irin baƙin ciki ne ya cika zuciyar Haseeena, da ƙara tsanar Farhan fiye da baya. " 'yar me kyau na, nayi kewarki sosai fa" Sunkuyar da kai Farhan tai tana murmushi, tana jin daɗin hirar da yake mata. "Tashi muje ki rakani wani guri" Ba musu ta tashi suka fita daga ajin tare, sedai kamar tsautsayi suna fita sun fara sakkowa daga bene, sega Nazir na hawowa ya dinga bin su da wani irin kallo, kamar haɗin baki suka basar da shi suka wuce. Shop ta raka shi, ya sai mata kayan ciye ciye kala kala, se dai da farko ƙin karɓa tayi, seda ya ɓata rai, sanna ta karɓa. Seda ya rakata har ajinsu, sannan ya tafi nasu ajin, ta zauna ba daɗewa taji tana jin fitsari, dan haka ta miƙe ta tafi banɗakin mata da benen, dan ba ta son sake sauka daga benen. Tana shiga ta ga was 'yan ss3 a ciki, da alama kamar ba su da gaskiya, ɗaya ta mata tsawa tace "ke me kike a nan!" "I want ease myself" Farhan ta faɗa fuskarta ɗauke da tsoro. Wata daga cikin su tace "dena mata tsawa, budurwar Prince ce fa, a kanta yanzu ze tayar miki da jijiyar wuya, dan ban manta zagin da yai min akanta ba" "To ina ruwana, yi abunda zakiyi ki fita, tana Magana da wata maƙalalliyar muryata, tana turanci kamar baturiya, saboda iyayi" Ɗayar tace "don't you see she's Fulani girl, i just like her she's beautiful and innocent, I want her to be my lover" Farhan ba ta gane me suke tattaunawa ba, taga Anshigo da Nasreen toilet ɗin, an rirriƙeta tana ta uban gumi. Tabbas ba zata taɓa manta fuskar Nasreen ba, dan a duk lokacin da ta ganta ba abunda take tunawa se yadda ta gansu ita da George. Farhan ba ta son su kuma yi mata Magana, dan haka ta shiga ɗaya daga toilet ɗin tai abunda za tai ta fice. "Wayyo Allah na zan mutu! Na shiga uku zan mutu, ku taimaka min dan Allah!!!" THIS IS JUST THE BEGINNING!!! DOMIN GYARA SHARHI KO SHAWARA Ayshercool. 07063065680. [6/4, 4:21 PM] Jakadiyar Arewa:   🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ RUƊIN ƘURUCIYA PERFECT WRITERS ASSOCIATION (WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS) https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ P. W. A *Story and written by* AISHA ADAM (AYSHERCOOL) Writer of WATA KISSAR..(Sai mata) ABDUL JALAL AƘIDATA (paid book) WUTA A MASAƘA NOW RUƊIN ƘURUCIYA (paid book) _Labarin RUƊIN ƘURUCIYA, na iya zuwa da wani salo, wanda baku saba ganinsa a rubutuna ba, hakan ya biyo bayan akan abunda aka gina labarin, wani abun ze ɓoyu wani Abun baze ɓoyu ba sakamakon labari ne akan teenegers, yara masu tashen Balaga, but hakan ba ya na nufin na sauka daga kan tsarin yadda nake Rubutu bane, ƙofata a buɗe take dan karɓar ƙorafi, gayra ko shawara_ ⚠️⚠️⚠️ƘIRƘIRARREN LABARI NE, BAN YADDA A JUYAMIN SHI TA KOWACE SIGA BA SEDA IZININA ❌❌‼️       SHIN KUNA DA LABARIN MANHAJAR AREWABOOKS KUWA? MANHAJA CE DA TAZO DA TSARIN DAN SAUƘAƘAWA MARUBUTA DA MAKARANTA SAUƘIN CINIKAYYAR LITATTAFAI. TA IN DA ZAKU IYA SIYAN KOWANE FEJI AKAN KUƊI ƘALILAN, DAI DAI DA ALJIHUNKU. INA FARINCIKIN SANAR DA KU CEWA, DA ZARAR NA KAMMALA FREE PAGES, ZAKU CIGABA DA SAMUN CIGABAN LITTAFIN RUƊIN ƘURUCIYA, AKAN MANHAJAR AREWABOOKS. KARKU BARI A BAKU LABARI, AKWAI TARIN DARASIN RAYUWA A CIKIN LITTAFIN.                           27_28 Tsoro ne da fargaba suka ziyarci Farhan, jin wannan ihun haka, ba tare da tayi fitsarin ba a razane ta leƙo, aikuwa ta ga jini na zuba sosai a jikin Nasreen, wadda ta riga ta haɗa uban gumi kamar tayi gudu. Take Farhan ta sake birkicewa, ta tsorata ainun ganin wannan uban jini, kamar an yanka rago. "Ke da kin san baki iya abun ba kika je kika fara, gobe ma kya kuma ai, se ki shiga taitayinki, in kin san zaki yawon ki, seki ɗau mataki ba ki bari abu ya faru haka ba" Suka cigaba da caccakarta suna mata mita, ita kuwa Nasreen se jujjuya kai kawai take, ita kaɗai ta san azabar da take sha. Can wata tace "seki gode Allah, tunda Allah ya rabaki da wahala cikin ya faɗi" Gaban Farhan yai mummunar faɗuwa,  Suf Farhan ta silale ta bar banɗakin jikinta yana tsuma, gaba ɗaya ta birkice, ba ta taɓa ganin jini me yawan haka ba. Abunda ya sake ɗaure mata kai, be wuce yadda taji ana cikin ya faɗi ba, to ciki ya faɗi kamar yaya? Ta yaya cikin mutum ze faɗi?. Jikinta se tsuma yake ta tafi ajinsu, ta nemi guri ta zauna ta kifa kanta a benci, tana jin yadda zuciyarta ke wani irin lugude kamar zata faso ƙirjinta ta fito. Haseena ta kalli in da Farhan take ta ja uban tsaki, tace "Idan za'ai taro na 'yan makarantar nan be kamata a dinga gayyato 'yan alfarma ba, ga bikin yayan Prince da mukaje, yadda wata taje yarkace yarkace kamar wata 'yar ƙauye, taɓɗijan Ni wallahi da bikin gidanmu ne ta zo korarta zanyi wallahi" Gaban Farhan farhan ta ji wani dumm a ƙirjinta, dan ta san tabbas da ita Haseena take, taji zafin Abinda Haseena ta faɗa amma ba ta damu ba sosai, sakamakon tasan eh dagaske ita ɗin ba 'yar kowa bace akan su. Ita abunda ta gani yau yafi komai ɗaga mata hankali nesa ba kusa ba. Yauma Meena lesson kawai ake, amma ba wani ganewa take ba, dan tunda ta zo take maye, ƙwayar da ta sha daren jiya ba ta gama sakinta ba. Taslim ta kalleta tace "Ke Meena, ki dena shan abun nan in zaki zo school, so kike se an fara ganewa tukuna? Kinga abunda kike yi kuwa? Idonki duk ya juye" "Taslim ya zanyi, idan ba sha nai ba sam ba na jina yadda nake so, idan na sha nafi jin daɗi" "Aikuwa za'a ganoki a gida da wuri, ki dinga bari se dare in ba haka ba kuma Asirin ki ya tonu ba ruwana" Meena tace "Insha Allah baze tonu ba ba, kuma ma fa daddaren nake sha, kawai sakina ne ba tayi fa wuri" Jakar Taslim Meena ta ɗauka, tana dubawa ko zata samu chewangum, ta samu ta ɗan tauna amma da mamakimta se ta ga maganin planing a jakar ta ta. Ta kalli Taslim tace "beb what is this?" Taslim tace "meye na tambaya, maganina ne" "Amma wannan ai maganin hana ɗaukar ciki ne" Taslim ta kalleta tace "ke a gidan ubanwa kika sani?" "Naga Yaya Amra na sha ne, tace na planing ne kullum tana sha" Taslim tace "ni ban san yadda akai ma na sa shi a jakata ba, ɓare shi nake daga satchet ɗin, in bar shi a haka ba wanda yasan meye" Meena tace "Amma Taslim me kike da maganin hana ɗaukar ciki ke ba Aure ba?" "Naga kamar baki fahimci amfanin maganin nan ba, bature beyi wannan maganin dan masu Aure kawai ba, yayi shi ne dan mabuƙata" "Kenan kema kina cikin mabuƙatan?" Taslim tace "ƙwarai, ina amfani da shi ne dan hana ɗaukar ciki" Zare ido Meeena tayi tace "Taslim, it means you are not virgin fa" "Yes of course, amma ai ba abun mamaki bane" "Kamar ya ba abun mamaki bane? Kenan fa ke ba budurwa bace kina bin maza kenan" Taslim tace "Ina ke shaye shaye kike yi? Shike ba ki nustuwa da kwanciyar hankali?" "Amma Taslim shaye shaye daban, wannan da kike Magana daban, maganin hana ɗaukar ciki fa" Taslim tace "to ke da da kike ƙoƙarin jan hankalin sir Nuradeen, me kike so yai miki?" Meena tace "kawai ina son muyi soyaya ne na school, kuma ni iya abuna ba na wuce Romance, amma naga ke naki babba ne" Taslim tai wani murmushi tace "Meena, ni dake kusan abu ɗaya ne, ke da ni budurwa ce ta ya zan dinga duk wani rashin mutunci da Mubarak Babba, ko dayake virgins ɗin ma nayi, amma yadda kike romancing da namiji, wataran zaki abunda nayin nima, nima da fari ba'a san raina ba, soyayya ce ta jani ta kaini ga wannan matakin, ina ƙoƙarin in dena, amma na riga na saba ba yadda na iya, ki manta kawai kiyi kamar ba kiga komai ba" Taslim ta ƙare maganar tana kallon idon Meena ta na mata murmushi. Galala Meena ta cigaba da bin Taslim da kallo, Taslim tace "Meena ki dena kallo na a haka, kamar kinga wata baƙuwar halitta mana, nifa mutum ce, kuma kema mutum ce kin san me ake ji a irin wannan shekarun, so stop pretending" Duk iya shegen Meena, Taslim ta dameta, dan bata taɓa tunanin gawurtar Taslim ta kai haka ba. Sadik kam a gurin zamansa ya zauna, yana duba wani Keypoint na Physics, sega su Nas sun shigo ajin, sedai tun shigowar su yaji suna ƙauri. Nas yace "Baba yane, zamu fita muka nemeka muka rasa ina kayi ne?" Amin yace "kai seka tambaye shi ma? Yana cam gurin waccan ƙwailar da ba ta san ta tsinana masa komai ba sedai shi yai mata" Nas yace "bar wannan batun kar yaji haushin ka, kasan shi baya son gaskiya" Sadik be ce mus uffan ba ya cigaba da duba abunda ke hannun sa, Nasir ya zauna a kusa da Sadik amma Sadik ya dube shi yace "malam leave my place please" Nas yace "meyasa kake korata?" "Kai ba ka jin yadda kuke warin sigari ne, banzaye dalla tashi kar ka sani amai" "Amma wallahi Sadik ka ɗan wahala ne, yau ka fara jin warin sigari da kake batun zata saka amai, naga har shisha kana sha ai" "Shisha sigari ce? Dalla ku barmin seat" Amin yace "Wallahi Shisha da sigari ba wani banbanci, tunda duk hayaƙi muke sha" ya ƙarasa Maganar yana miƙewa daga seat ɗin Sadik ɗin. Farhan abun duniya ya isheta, gashi haka nan tun da taga wannan jinin ta tsorata taji cikinta ya ƙara tsananta mata ciwo, tun tana basarwa harta kasa jurewa ta fara zubar da hawaye,ba tare da kowa ya gane halin da take ciki ba. Ganin an tashi kowa na fita, amma ita tana zaune yasa Lilly ƙarasawa gurinta, ta taɓa ta tace "Farhan an tashi fa" Shiru Farhan tayi ba ta ɗago ba, kuma ba tace komai ba. Sadik yana fitowa daga ajinsu ya tafi gurin Farhan, sedai ya tarar da ita ta kifa kanta, ba ta da alamar tashi daga gurin zamanta, ga Lilly a tsaye a kanta. Sadik ya ƙaraso da sauri yace "lafiya kuwa?" Lilly tace "wallahi ban san meya sameta ba, na mata magana amma taƙi tashi" "Princess menene? What's wrong with you?" Ɗago kai tayi a hankali, hawaye ya wanke mata fuska. Yace "Ya Salam, menene?" "cikina ne kemin ciwo". A hankali ya durƙuso yace "Baki je Asibitin da nace ba ko? Tashi muje Clinic a duba ki" "Um um ni bazanje ba, gida zan tafi" ta haɗa gumi sosai, ga hawaye na bin fuskarta. He just wish he can hug her and wipe her tears. Yace "ba zaki A dubamin ke ɗin ba kenan?" "Ni gida kawai" tai maganar tana jujjuya kai saboda ciwo. Yace "ok tashi muje mota" ita kam Lilly gaba ɗaya burgeta sukayi, yadda yake nuna damuwarsa akan ta. Sadik ya miƙa hannu ya riƙo hannunta, Lilly ta kama ɗaya hannun suna tafe tana durƙushewa, Sadik yace "Farhan, bari in ɗauke ki kawai in kaiki mota, tunda tafiyar ta gagara" Da sauri ta sake fashewa da kuka tace ba ta yadda ba. Da ƙyar suka ƙarasa mota, makaranta duk an watse. Nazir yana bene na biyu, a Office yana ƙoƙarin tashi, ta window ya hango Lilly da Sadik sun riƙo Farhan, tana durƙushewa, ya girgiza kai ya nemi guri ya zauna, dan abunda tunanin sa ke kawo masa akan su daban ne" Tare da Lilly Sadik suka tafi kai Farhan gida, Lilly na rungume da Farhan. Da sukaje gidan ma, Sadik na mota Lilly ce ta kama Farhan Zuwa cikin layinsu. Hakan yai daidai da fitowar Abban Farhan ze tafi masallaci, a kiɗime ya ƙarasa in da Su Lilly suke yace "lafiya kuwa? Meya sameta?" Lilly tace "ba ta da lafiya ciwon ciki take" Da Sauri Abba ya riƙota yana mata Sannu, Lilly ta juya zata tafi yace "Yarinya zo muje ko ruwa ki sha a gidan" Lilly tace "A'a Nagode, zan tafi gida kar a ga na daɗe" Abba yaita mata godiya yana sa mata albarka. Sadik na bakin layin yana kallonsu, sedai be ƙarasa ba, da Lilly ta dawo seda suka kaita har gida sannan suka tafi. Umma ma ta tsorata da ganin Farhan a haka, amma ta kasa nuna damuwarta sosai, Abba ya ɗebo ruwa yai tai mata tofi, ya bata ta sha. Da ƙyar aka samu bacci ya ɗauke ta. Sadik kam tunda ya koma gida kasa sukuni yai, yana ta tunanin halin da Farhan ke ciki, dan ya tsorata da halin da ya ganta a ciki. Tunda Farhan ta fara bacci ba ta tashi ba, se la'asar kuma ta tashi da sauƙi da sosai, ƙannenta suka dinga jera mata Sannu. Umma anyi abun kai ta kaiwa Farhan ruwa tace taje ta watsa, Farhan taji daɗin hakan sosai. Sedai bayan tayi fitsari taga kamar jini a cikin fitsarin, basarwa tai dan bata kawo daga jikinta bane, dan haryanzu ta kasa manta abunda ta gani, lokaci lokaci ta kanji gabanta ya faɗi idan ta tuna. Wankanta ta cigaba dayi, ta kammala tai Alwala ta miƙe kawai taga jini na bin ƙafarta. Ihu ta buɗe baki zatai, tai saurin saka hannu ta tsohe bakinta, nan ta shiga zazzare idanu a banɗakin. Kawai ta hasko abunda ya faru da Nasreen ta ss3 shine itama ya sameta, ta dinga rusa kuka a banɗaki. Se da tai me isarta sannan ta sake wanke jikinta ta fito. Ta dinga ƙoƙarin ɓoye hawayen da takeyi, ta shiga ɗakinta, ta tarar Umma ta ajiye mata shayi a ɗakin nata. Kasa sha tai ta nemi Guri ta zauna ta cigaba da kukanta, can ta kalli ƙafarta ta ga yadda wani jinin ke cigaba da binta, nan ta sake rikicewa ta cigaba da kuka ta koma banɗaki da sauri ta sake wankewa. Umma ta biyo ta ɗaki da magani a hannunta tace "ga magani nan, Na aika gidan Nurse ɗin nan, tace ki sha wannan"   Sedai Umma taga kamar Farhan hankalinta baya kanta, nan ta lura da hawayen dake kwance a idonta. "Ke lafiya kuwa?" Cikin kuka Farhan tace "Umma mutuwa zanyi" Cikin rashin fahimta Umma tace "ke bana son shirme, cikin ne yake miki ciwo haryanzu?" "A'a fitsarin jini nake yi, kuma ko banje nayi fitsarin ba se inga ya zubo" Gaban Umma me yai mummunar faɗuwa, ba ta taɓa kawowa Farhan yin Al'ada a Yanzu ba, saboda ƙananan shekarunta" Jiki a sanyaye Umma ta bar ɗakin, ba ta daɗe ba ta dawo ta miƙawa Farhan pad tace "ki dena wannan kukan, jinin al'ada ne, ga wannan da shi ake amfani" Umma tai maganar ko haɗa ido ba ta san yi da Farhan, tana bata tai waje. Mamaki ne ya kama Farhan, menstruation fa kenan, shikenan ta shiga uku itama za'a fara rubuta mata zunubi. Jin tana ƙoƙarin sake ɓaci ne yasa, tabi direction ɗin yadda ake amfani da pad ɗin da ke rubuce a jiki ta saka, dan ba wani bayani da Umma tai mata, akan yadda zata dinga kula da kanta, da abunda ba'a so tayi. Ita Umma hankalinta ne yai ƙololuwar tashi, duk wasu alamu na girma sun gama bayyana a jikin Farhan ɗin. Duk da ƙanƙantar shekarunta, alamun girma kam yanzu babu wanda babu a tare da ita. Farhan kuwa kukanta ta cigaba da rerawa, kamar wata ƙaramar yarinya, ko wadda wani bala'i ya faru da ita. Bayan sallar magariba Abba ya dawo gida, ya siyowa Farhan kayan marmari, ko zata iya ci. Yace Umma ta kira masa Farhan. Ba jimawa sega Farhan ta zo, fuskarta duk ta kumbura saboda kuka, da ƙyar take tafiya, ko ƙwaƙwƙwaran motsi ba ta son tayi. Abba ya kalli Farhan, Sannan ya kalli Umma yace "yarinyar nan ko dai mu tafi Asibiti ne?" Umma tace "A'a base munje Asibiti ba" "To ai naganta haryanzu wani iri ne" Farhan tace "A'a Abba ai na samu sauƙi" Abba yai ajiyar zuciya yace "shikenan, ga wannan ledar ki ɗauka kije ki samu kici, Allah ya sawwake" Tace "Ameen Abba Nagode sosai" Ta tashi ta bar ɗakin, Umma ta kalli Abba tace "Yarinyar nan fa, Al'ada ta fara" Abba yace "to ciwon cikin kenan dama, lallai Farhan an girma, to Allah ya sawwake" Cikin damuwa Umma tace "Nifa ina cikin damuwa, Farhan tayi ƙanƙanta, haryanzu fa ba shekarunta goma sha uku, tayi ƙanƙanta" Abba yace "to banda abunki zamu hana Allah ikonsa ne akanta?" "A'a, amma a tsorace nake, yarinya ce ƙarama amma kalli yanayin jikinta, anya ba za'a haƙura da bokon nan ba a Aurar da ita, ina jin tsoron wannan zamanin da muke ciki" "A'a ki kwantar da hankalinki, ai Allah shi ke ds zamani, kuma kowacce yarinya da irin halittar da Allah yai mata, kiyi haƙuri ki yi mata Addu'a kawai" Jiki a sanyaye Umma tace "to Allah ya tsare" Har Dare yayi Sadik ya kasa bacci, yana son sanin halin da Farhan ke ciki amma ba damar sanin hakan. Da safe da wuri Ya shirya ya tafi Makaranta, amma har aka tashi Farhan ba ta zo ba. Abun ya sake ɗaga masa hankali, da aka tashi ya koma gida da yamma, yaje ya ɗakko Khairat yace mata zata rakashi gidan su Farhan ya duba ta. Ba ta musa masa ba ta bishi, ya biya yai siyayya, suka tafi gidan su Farhan ɗin. da sukaje layin ya bata kayan dubiyar yace in ta shiga ze kirata ta haɗa shi da Farhan. Khairat har Mamaki take akan yadda Sadik rawar jiki akan wannan 'yar mistilar Yarinyar. Yauma Umma ta karrama Khairat sosai, Farhan na ganin Khairat ta san tare suke da Sadik. Suka shiga ɗakin Farhan suka gaisa, Khairat ta kalleta tace "ya jiki?" "Alhamdilillah na samu sauƙi" "Bari in kira shi a waya, yace in haɗaku ku ze miki ya jiki" Farhan ta jinjina kai, Khairat ta kira Sadik a waya ta bawa Farhan. Sedai kowannen su ya kasa Magana, can Sadii ya katse shirun ta hanyar cewa "ya jikin naki?" "Naji sauƙi Alhamdilillah" "Kunje Asibitin ne?" "Eh munje" ta bashi amsa. "To shikenan, ki kula sosai dan Allah ki sha magungunan da aka baki kinji Babyna" Murmushi tai tace "to insha Allah" Su kai sallama ta katse wayar, Khairat ta miƙe tace "to shikenan Allah ya ƙara sauƙi, zan tafi" Iya tsakar gida kawai Farhan ta iya raka Khairat, saboda gani take da tayi kyakyawan motsi, za'a gane halin da take ciki. Wasa wasa seda Farhan ta shafe kwana biyar cif, sannan ta koma makaranta lokacin ta koma normal. Lokacin da ta gama period ɗin ma tayi amfani da karatun Islamiyyar ta ne gurin yin wanka, da gane ɗaukewar jinin, dan in ta Umman ta ne sedai ta zauna a haka ba zata gaya mata ba, dan tunda Farhan ta fara period ma kamar sake janye mata tayi. Ranar da ta koma makaranta Sadik ji yai kamar ya rungumeta saboda farinciki, tayi haske gau, amma fuskarta ta faɗa sosai. "Princess, kin rame da yawa fa" Murmushi kawai tai ta ɗauke kai ba tace masa komai ba. "Da kuka je Asibitin ba suce miki komai akan ciwon cikin naki ba?" Gabanta ne ya faɗi, ta maze tace "kawai ciwon ciki ne kuma na warke ai" Yace "to Alhamdilillah, Allah ya ƙara mana lafiya" Ta Amsa da "Ameen" Tun dawowarta makaranta, kullum idan aka fita break su Lilly ba su da aiki se karanta litattatafai masu ɗauke da zunzurutun batsa, wadda ta kasance barazana ga ƙwaƙwalwar ƙanan yaran. Da an fita break, Farhan ke tattara kayanta ta tafi ajin su Sadik, sedai can ɗin ma da nasu kalar watsewar, ga Mubarak Babba da ke cigaba da takura mata, wani rashin mutuncin ma se sunga tazo ajin suke fara yin sa. Haka nan take jin zaman makarantar ya isheta, mutum ɗaya ke bata farinciki a makarantar Shine Sadik. Kasancewar ta tare da shi ne kawai ke bata nishaɗi da ɗebe mata kewa, amma duk lamuran ɗaliban har malaman sun ishe ta. Nana ke zaune a gefen Hakimi ta na ta zuba masa surutu kala kala, yayin da yake kashingiɗe yana sauraronta, fuskarsa na bayyanar da tarin murmushi. "Kaga Baba Alaji, da mukaje bikin nan kawuna ya tambaye ni me nake son na zama idan na girma" "To ke me kika ce masa?" "Ai ni kasan 'yar jarida nake son zama, me karatu da turanci, irin na turawan nan ina son inga na iya turanci sosai da sosai fa" Hakimi yai murmushi yace "Ai Yanzun ma kin iya, tunda in anyi kina ji" "Taɓ me na iya, ai idan ina ƙauyen nan na fi iya turanci, da mukaje birni duk se naji ba turancin, kaji irin turancin da suke kuwa kamar Turawa, ni bama na gane irin nasu turancin wallahi" Hakimi yai murmushi yace "to Allah ya ida nufi, ya nuna mana kammala karatun naki" Nana ta gyara zama tace "ina ga fa nima ƙasar wajen ze kaini, inyi karatun fa" "Ba Gidan uban da zaki, kina gama Sakandire Aure za'ai miki, kya yi karatun a can, dama ba Jamilin Gidan me unguwa bane yake biyo ki idan na aike ki ba, da kin gama makaranta za'a ace ya fito"  Inna ce take wannan bayanin a ƙofar ɗakinta. Kwaɓe fuska Nana tayi tace "ni wallahi ba saurayina bane, dan Allah ki barni in karatu, wallahi ban isa Aure ba, kefa kike cewa Ni yarinya ce" "Eh ke yarinya ce a yanzu ba, amma kan lokacin ai kin ƙara girma" Nana ta kalli Hakimi tace "dan Allah ka sa baki, nima a barni inje inga ƙasar wajen nan inyi karatu" Inna tace "idan kika je ƙasar waje karatu, ba bu me Aurenki za'ace idonki ya buɗe" "Wallahi za'a samu me Aure na, kinga lokacin na zama 'yar gayu sosai, dama ni ba zan Auri ɗan ƙauyen nan ba, se ɗan gayu, ɗan birni wanda ya iya turanci" Hakimi yace "Banda abunki, shi wannan turancin in kinyi Auren shi zaki ci ne, ai mutum Nagari ake nema" "Eh to nagarin, kamar dai Farukun Gidan kawu" Hakimi yace "shi kike so kenan" Kamar wadda ake ce tayi zunubi tai farat tace "A'a ba haka ba, taɓ kawai dai ya iya turanci, kuma yana da kirki sosai, ba kamar wannan dogon mara kunya ba" "Waye kuma dogo mara kunya" Nana ta ɗan keɓe baki tace "wannan Sadik mana, wallahi na tsane shi ba shi da kirki kwata kwata, kaga yadda ya shaƙeni zemin duk ranar dan na zuba masa miya ban sani ba, ni kuwa na ɗau wandonsa me tsada na sa a ruwan datti" Hakimi ya ɗaga kai ya kalli Inna su kai ido huɗu, ya jinjina kai yace "Kar ki sake cewa kin tsani mutum, kuma kinga ai shi yayanki ne, karki sake" "Baba Alhaji, yaro ne fa shi, tsawo kawai ya fini, dan haka ba wana bane,  Faruk ne Yayana, me Kirki yaita saimin abubuwa da muna gidan" "To uwar son abun duniya, dama saboda yana sai miki abubuwa shiyasa kike ta rawar kai a kansa, tashi ki bar nan uwar surutu, ko gajiya ba kya yi, kamar an kwance ruwa ki ta zuba" Nana ta tashi, sum sum ta bar tsakar gidan, Hakimi yace "da kin ƙyaleta, a hirar ta ta nake fuskantar wasu abubuwan" Inna tace "Na sani, nima a haka nake bugun cikin ta nake jin abunda ke ranta, amma wasu lokutan surutunta yai yawa, idan ba'a taka mata birki, a waje ma zata iya zuwa tai hakan" Prince ya riga yai registration ɗin jarrabawar ƙarshe da wanda zasu gama a shekarar, zeyi tsallaken aji guda, duk a ƙoƙarin cinma burinsa na ganin ya shiga jami'a da wuri, dan ya samu ya mallaki abunda zuciyar sa ke so. Sedai ɓangare guda idan ya tuna da ze bar makarantar, yai nesa da Farhan gaba ɗaya se ya ji damuwa ta mamaye shi, yana matuƙar jin Farhan a ransa. Kamar kullum, Nazir ya kammala koyarwar sa a ajin su Farhan na ranar, ya bawa Class rep Umarnin ya tattara masa litattafan 'yan ajin ya kai masa ze duba notes. Yana fita Lilly tace "kan bala'i, wai dagaske gayen nan yake checking note zeyi? Aikuwa kashi na ya bushe dan ba na wani note wallahi" Haseena tace "Ubanki ze ci la'ada waje wallahi, kin raina mutumin nan kowa na tsoron sa amma banda ke" Lilly tace "ke bari kawai, wallahi nima ina tsoron sa, ko kallona ya fiye yi se inji hantar cikina ta kaɗa wallahi, ni yanzu ya zanyi?" Yasmin tace "to ki sauri ki ksrɓa kiyi mana" "Ke wallahi ba zan ba, note ɗin fa fa yawa, ba yi nake na Assignments ɗin sa ma bayi nake ba, sedai ya kashe ni ya huta kawai" Class rep ɗin su yace "ba shakka kin shahara Lilly, mitumin nan ba raga miki ze ba" "Aikuwa sedai ya kashe ni, ni bari ma in tattar maka litattafan, idan ka tashi sedai ka kai masa kawai" "Aikuwa da kin kyauta" Lilly ta tashi ta na karɓar litattafan 'yan aji, ta zo kan Farhan, ko littafin ba ta ɗakko ba. Lilly tai murmushi tace "Sannu basarakiya matar Prince, a dole se an nuna mana sarauta, kina kallo ina haɗa litattatafai amma ko ɗakkowa baki ba" Kunya ce ta kama Farhan, tai murmushi tace "Yi haƙuri, ba wata sarauta wallahi, hankalina ne yana wani gurin" "Eh hankalinki na kan tunanin sa ko?" Murmushi Farhan ta cigaba da yi, ta ɗakko littafin ta bawa Lilly. Lilly ta karɓ ta fara buɗe littafin tace "Masha Allah, ke komai naki abun burgewa, kalli handwriting ɗinki me kyau kamar ke" Murmushi ta cigaba da yai tana sunkuyar da kai, Lilly na cikin buɗe littafin ta tsinci takaddar haihuwar Farhan a ciki. Farahn ba ta san takaddar ta na ciki ba, Lilly ta tsaya tana duba takaddar. "Wow Masha Allah, Ashe akwai birthday me yaji a school ɗin nan, saura sati ɗaya birthday ɗin ki Ashe?" Da sauri Farhan tace "A'a ni ba na wani birthday, ban ma san takaddar na ciki ba, bani in ajiye" Lilly tace "ke kin isa, budurwar Prince guda ace ba za'ai celebrating birthday ɗin ta ba, wallahi dole ayi let me go and show him in case be sani ba" Lilly tai waje da sauri da takaddar a hannunta, gaba ɗaya Farhan ta rasa abunyi, sam ba ta so abunda Lillyn ke shirin yi ba, meyasa za tai mata haka. Cikin sa'a Lillyn na fita, ta hango squad ɗin su Sadik ɗin, suna tahowa da alama zasu fita ne, Sadik na maga duk sun bashi attention ɗin su. Tun lokacin da Lilly ta bi Sadik, suka kai Farhan gida idan ya ganta ya kan ɗan sakar mata fuska, saɓanin da da ba ruwansa da su, hasali ma Juniors suna tsoron sa, kuma ta fanni guda ana son sa saboda yawan kyautarsa. Ta ƙarasa in da suke, Sadik ya ɗan kalli Lilly, amma be ce komai ba. Miƙa masa birth certificate ɗin tayi, ya karɓa yace "wannan na menene?" Tai murmushi tace "nasan wataƙila ba ka sani ba, birth certificate ɗin Farhan ne, on 8th ne birthday ɗin ta, nasan maybe ka shirya wani abun" Murmushi yai ya fara duba takaddar, yana bawa duk wani abu da ya shafi Farhan mahimmanci. Ya shafi sumar kansa yace "Wow, naji daɗin wannan Albishir ɗin, nasan ba dan kin gayamin ba ba zata faɗan ba, dole ai celebrating, kina da kyautar wannan Albishir ɗin" Lilly tace "godiya nake Allah ya raya mana Farhan, ya kaimu lokacin abun" Sosai Sadik yai murmushi har seda haƙoransa suka fito yace "Ameen" Ya kalli su Nas yace "guys kuyi gaba, let me go and see her first" Aminu ne ya fara jan uban tsaki yace "what a shit! Wallahi tun fa Yarinyar nan ta zo school ɗin nan ka zama wani bita zai zai, ni na rasa uwar me kale bi a Yarinyar nan, ni banga wani abun burgewa a tare da ita ba, amma kai ta wani ɓare ɓare a kanta" Wani ɗan fito Sadik ya ja, me cike da rainin hankali yai gaba abunsa ya nufi ajinsu Farhan" Nas yace "ƙyale shi, nasan abunyi, nasan dole ze haɗa mata birthday ai, tunda kuɗin banza gareshi be san cuwon su ba, da wannan damar zamuyi amfani musa shi a hanya" Amin yace "what a good idea, shi banda wawanci ma, wannan 'yar talakwan kawai ya sarara ya watsar da ita, ko wani abun yai mata ba mataki zasu iya ɗauka ba, amma ya kankane ya hana kowa wai shi Aurenta zeyi" "Bar banza za muyi maganinsa ne" Ya na zuwa ya tarar da Farhan ta cika tai fam tana zumɓura baki, Lilly na mata dariya. Yana zuwa ya kaɗa paper a fuskarta, ta miƙa hannu zata karɓa amma ya ɗauke yana murmushi. Yace "ke yanzu birthday ɗin naki ya kusa, amma baki gayamin mu fara shiri ba" "Ni ba wani shiri, ni bana wani birthday fa" "Wannan karon zaki fara, hall zamu kama ƙarami ai shagali kamar ana bikinmu" "Dan Allah ka bari, base anyi ba fa, ni a gida baza'a barni ba ma" Tsuke fuska Sadik yai yace "in dan gida ne, ba matsala zan san yadda za'ai a fitomin da ke, amma sekin zo gurin nan, in kuma ba kya so ne ki gayamin" Ɗago fararen idanunta tai ta sa a nasa, amma ta kasa sake musa masa se shiru da tai ta sunkuyar da kai. "Idan ina Magana, ko ince ayi abu kina mun gaddama, I will....." Se kuma yai shiru, ya juya ya fita. DOMIN GYARA, SHARHI KO SHAWARA 07063065680. [6/4, 4:21 PM] Jakadiyar Arewa:   🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ RUƊIN ƘURUCIYA PERFECT WRITERS ASSOCIATION (WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS) https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ P. W. A *Story and written by* AISHA ADAM (AYSHERCOOL) Writer of WATA KISSAR..(Sai mata) ABDUL JALAL AƘIDATA (paid book) WUTA A MASAƘA NOW RUƊIN ƘURUCIYA (paid book) _Labarin RUƊIN ƘURUCIYA, na iya zuwa da wani salo, wanda baku saba ganinsa a rubutuna ba, hakan ya biyo bayan akan abunda aka gina labarin, wani abun ze ɓoyu wani Abun baze ɓoyu ba sakamakon labari ne akan teenegers, yara masu tashen Balaga, but hakan ba ya na nufin na sauka daga kan tsarin yadda nake Rubutu bane, ƙofata a buɗe take dan karɓar ƙorafi, gayra ko shawara_ ⚠️⚠️⚠️ƘIRƘIRARREN LABARI NE, BAN YADDA A JUYAMIN SHI TA KOWACE SIGA BA SEDA IZININA ❌❌‼️       SHIN KUNA DA LABARIN MANHAJAR AREWABOOKS KUWA? MANHAJA CE DA TAZO DA TSARIN DAN SAUƘAƘAWA MARUBUTA DA MAKARANTA SAUƘIN CINIKAYYAR LITATTAFAI. TA IN DA ZAKU IYA SIYAN KOWANE FEJI AKAN KUƊI ƘALILAN, DAI DAI DA ALJIHUNKU. INA FARINCIKIN SANAR DA KU CEWA, DA ZARAR NA KAMMALA FREE PAGES, ZAKU CIGABA DA SAMUN CIGABAN LITTAFIN RUƊIN ƘURUCIYA, AKAN MANHAJAR AREWABOOKS. KARKU BARI A BAKU LABARI, AKWAI TARIN DARASIN RAYUWA A CIKIN LITTAFIN.                               29 Bayansa Farhan ta bi da kallo, ta na shakkar bijirewa abunda ya ke so, da kuma hatsarin aikata wani abu ba da izini ko sanin iyayenta ba. Muryar Lilly ce ta dawo da ita hankalinta. "Haka kurum, zaki mana sagegeduwa, ai nasan in dai ya sani akwai shagali na gasken gaske, dan Prince akwai son harkar girma" Ita dai Farhan ba tace uffan ba, se tsunduma kogin tunani da tai. Haseena kam tsaki ta ja, dan ta tsani duk wani abu da ya danganci Farhan, haushin ta take ji nesa ba kusa ba. "Fatima Hakeem Yola, lambarki ta fito" cewar class captain ɗin su Farhan. Lilly tace "lambata ta fito a ina? Me nayi?" "Sir Nazir ke nemanki" "Innalillahi wa innalillahi raji'un, kashina ya bushe nasani" Kwashewa da dariya Yasmin tai tace "kaga 'yar iskar ƙarya, ke da kike cewa zaki dinga abun da zaki ɗaga masaa hankali, se kuma gashi kin tsure dan ance yana kiran ki" Hararta Lilly tai tace "ke dalla ƙyaleni, ni mutumin nan wasu lokutan tsoro yake bani wallahi, gashi jarababbe" Class rep yace "to yanzu zaki je ne ko kuwa?" Murguɗa baki tai tace "wallahi ba zani ba" "Au ba zaki ba, idan ya zo ya ritsaki fa?" "Wallahi ba zanje ba, fecewa zan gida, sedai komai za'ayi ayi, haka kurum" Suka dinga yiwa Lilly dariya, ta ɗauki jakarta ta bar ajin gaba ɗaya. Ko da aka tashi daga Makaranta, ba wanda ya nemi wani a tsakanin Sadik da Farhan, sedai ta tafi gida tana ta zullumin abunda Sadik ɗin ke shirin yi, tana tsoron iyayenta su gano, bata san wani irin hukunci zata iya fuskanta ba. "Nana wai shirin me kike yi ne haka?" "Inna kin manta ne, babar 'yar ajinmu ce fa ta haihu yau suna, nace miki zamuje, bana tambayeki ba kika ce kin barni ba?" Inna tace "ai na manta ne, kuma baki tunamin ba, se ganin ki nai kina shiri kawai dole in tambaya ai" "Ai na gayamiki kin manta ne" Inna tace "Allah ya taimaka" Nana ta cigaba da shafe shafen hodarta tana shiryawa. Inna na aiki a tsakar gida, sega ƙawayen Nana sunyi sallama. Inna ta amsa musu tana ƙare musu kallo ɗaya bayan ɗaya. Daga bisani tai musu nuni da ɗakin da Nana take. Kai tsaye suka nufi ɗakin suka shiga. "Ahh su Nana 'yan mata irin wannan ado haka?" Nana tai fari da ido tace "to a garin nan idan ban ado ba waze yi?" "A'a ba wanda zeyi ta Jamilu ba da kanki a sare, ai idan muka wuce ta hanyar gidan me unguwa ya ganki seya rikirkice" "Wallahi kuwa, dan mun haɗu ɗazu na kai niƙa yace min ina Nana? Nace masa kina gida amma da yamma ta layinsu zamu wuce zamu suna, ina ga ma yana nan a bakin layin yana jiran mu" Nana tace "ke Hannatu, kama kanki, ni ba sa'ar wannan yaron bace" Hannatu tace "ke! Jamilun ne yaro?" "Eh mana ban da ya rainawa kansa hankali ni zece yana so?" "Ke Nana shikenan kowa yana da saurayi amma banda ke?" Nana tace "To Alawiyya meye dan bani da saurayi? Ke nifa wallahi ɗan Birni zan aura insha Allah, amma se nayi karatu me yawa, in auri saurayi ɗan gayu ɗan birni" Hannatu tace "eh lallai kin ɗakko da zafi, ko da yake kuna da 'yan uwa a Birni ai" Alawiyya tace "Amma ki tsaya ku gaisa da shi, kinga ba daɗi wulaƙanci" Ɗan shiru Nana tai tana tunani, dan harga Allah ta na son taji ance ita ma ta na da suarayi, ta na son sanin me ake ji a soyayyar idan ana zance me ake cewa?" Ba ta kuma cewa komai ba ta tashi, ta ƙarasa shirinta suka fito tsakar gida. Nana tace "Inna zamu tafi?" Inna ta kalleta tace "zaku tafi ina kenan?" "Haba Inna, ɗazu fa nace miki ga inda zamu" Inna ta ƙare musu kallo tace "ba inda zaki" Saroro Nana tai tana kallon Inna, Cikin rawar murya Nana tace "Inna meyasa? Na tambayeki fa kince kin barni" "Yanzu kuma nace ba zaki ba" Ƙwalla ta taru a idon Nana tace "Inna meyasa ba zani ba?" "Saboda na isa, kin wuce kin ban guri ko senai fatali da ke a gurin nan? Ku kuma maza ku kama hanya ku tafi" Sumi sumi suka nufi hanyar fita daga gidan. Nana kam da gudu ta bar tsakar gidan tana kuka, ta rasa wace irin rayuwar takura ce haka, wasu lokutan gani take kamar Inna ba ta ƙaunarta Saboda yadda take takuramata, da hanata sakewa. Su Alawiyya na fita suka fara gulmar Inna. "Taɓ Hannatu, dama haka kakar Nanan take, wannan mata anyi jarababbiya, ji yadda ta koremu" "Hmm kedai bari, shiyasa Nanan ma gata nan jarababbiya, wallahi idan nice ba zan yadda da wannan abun ba, ai kakata ce ba uwata ba" "Wallahi kuwa balle kuma ni" Suka tafi suna cigaba da tattauna maganganun su. Nana da mayafinta, da jakarta da takalmin ta duk a tsakar ɗakin ta watsar da su tana kuka. Inna ta shigo ɗakin, ta kalli kayan da ta watsar ɗin, ta kalli in da Nana ta dunƙule ta na kuka tace "dan ubanki zaki tashi ki kwashe wannan kayan da kika zubar ko sena saɓa miki? Ni zan miki Magana ki min zuciya ki zubarmin da kaya a tsakar ɗaki, kiyi kukan jini ma tashi daga gurin nan ko in haɗa miki jikinki yanzun nan, mara ɗa'a kawai" Nana tana share hawaye, ta miƙe ta shiga tattare kayan da ta zubar ta maida su mahallin su, ta cire kayan jikinta, ta ɗakko masu datti ta saka dan ita ma ta ɓatawa Inna rai, ta ɗakko hijjabi ta saka, ta tafi turakar Hakimi tai kwanciyarta. Inna tai banza da ita bata tanka mata ba, ta cigaba da hidimomin ta. Ko Abinci dare Nana ta ƙi ci, Inna kuma ba ta takurata taci ba. A haka Hakimi ya dawo ya tarar da Nana, taci kukanta ta godewa Allah, tana kwance tai shiru a ɗakinsa. "Subhanallah shalelen ba lafiya ne?" Yai Maganar yana taɓa goshinta. Girgiza masa kai tayi alamar a'a. "To meyafaru?" "Inna ce" tai maganar tana fashewa da kuka. "Me Innar tai miki?" Kasa Magana Nana tayi, se cigaba da kukanta da tai" Hakimi yace "shikenan, ya isa dena kukan haka share hawayen. Suna cikin haka Inna ta shigo ɗakin, ɗauke da kwanukan kayan Abinci. Kallo ɗaya tai musu, ba tace komai ba ta ajiye ta cigaba da harkokin ta, yasa Nana a gaba suka ci Abincin su tare. Seda ya tabattar ta ƙoshi, sannan yai mata umarnin taje tai sallar isha'i ta kwanta. Hakimi ya saba da irin wannan rigimar ta Nana da kakarta, dan haka be takura akan se ya san meya haɗa su ba. Har washegari Nana ta shirya za ta tafi makaranta, amma ba ta wani shiga sabgar Inna, saboda a ganin ta ta gama dizga ta a gaban ƙawayenta. Tun da Lilly tai ido huɗu da Sir Nazir a gurin Assmebly gabanta yai mummunar faɗuwa, dan tasan tai masa laifi gagarumi, Allah kaɗai yasan yadda ze da ita. Ga mamakinta ko kallonta be sake yi ba, balle yai mata Magana ya shareta. Ita ma share shin tayi, sedai ƙirjinta na ta dukan uku uku. Aka watse daga gurin Assembly, suka nufi classes ɗin su. Farhan na tafe sannu a hankali, taji an riƙo hannunta ta baya, cikin hanzari ta waiwaya zaton ta Sadik ne, se dai ba kamar yadda tai tsammani bane. Salma ce ƙawar Nasreen wanda suke a Ss3, wanda ta gansu tare da su Nasreen ɗin ranar da Nasreen ɗin tai ɓari. Murmushi taiwa Farhan tace "Farhan ko?" Farhan ta jinjina mata kai alamar eh. "Dan Allah in ba zaki damu ba, ina son ki zama sister na a school ɗin nan,  if you won't mind" Saroro Farhan tai tana kallon Salma. "Anyway, idan an fita break ki zo Class ɗin mu ina son ganinki please" Farhan ta jinjina mata kai, ta juya ta tafi tana tunanin ita kuma wannan meye haɗinsu, da zata wani ce ta na so ta zama sister ɗin ta?. A ɗarare Farhan take gudanar da al'amuranta na yau, kasancewar ta na cikin period ne, wanda wannan shine karonta na biyu da farawa, gaba ɗaya ta kasa sakin jikinta, ga shi ƙasan cikin ta na ɗan mata ciwo kaɗan kaɗan, wani lokacin kuma ya ɗan tsananta takura mata. Ga wata uwar kasala da ke damunta, babban abunda yake ɗaga mata hankali be wuce yadda take jin ƙirjinta wani iri ba, zafi zafi ciwo ciwo, ba ta san wa zata gayawa ba, tafi tunanin ko Cancer ce ta kamata, gaba ɗaya ta kasa gane kanta. Ana musu lesson amma zuciyarta fal tunani daban daban, a ranta take addu'a idan mutuwa za tai Allah ya nuna mata ta auri Sadik kan ta mutu. Har aka fita break tana wannan tunane tunanen. "Yau kuma tunanin me kike yi?" Firgigit ta dawo hayyacinta, ta kalli Sadik dake kusa da ita a zaune. "Bakomai" "Bakomai kamar yaya? Kin san lokacin da na shigo?" Girgiza masa kai tayi alamar a'a. "Ke kin ma yi min laifi ko ki neme ni balle ki bani haƙuri ko?" "Lefi kuma?" Ta faɗa a ɗan shagwaɓe kamar za tai kuka. "Eh laifi mana, na yimin gaddama" "Ba fa haka bane, ni tsoro nake ji a gida kar ai min faɗa" "Zam bi hanyar duk da ta dace, ba wanda ze san anyi, kawai za'a ɗan yanka cake ne aci a sha, mu tayaki murna shikenan fa" Sunkuyar da kai tai ba tace komai ba. "Ko dai haryanzu ba kya so ɗin" Ta girgiza masa kai alamar a'a. "Yarinya kin taimaki kanki, da faɗa za muyi" Ɗan murmushin gefen baki tai, dan ita yanzu halin da take ciki ne yafi damunta, na wannan ciwace ciwacen da take fama" Idanunta ne suka kuma sauka a hannun Sadik, a ido kawai fatarsa abun sha'awa ga wannan gargasar ta jikinsa da take burgeta. A hankali ta ɗauke idonta daga kallon hannun nasa ta ɗaga kai ta kalleshi, karaf sukai ido huɗu yace "me kike kallo a hannuna?" Mamaki ne ya kamata, dama yaga hannunsa take kallo. "Ni ba hannunka nake kallo ba fa" "Yanzu kuma ƙarya nake kenan?" "Wai kai komai nayi lefi ne" tai maganar kamar ta rushe masa da kuka. Cikin kwaikwayon muryarta yace "kawai ina son in dinga tsokanar ki ne" Littafin gabanta ta ɗauka ta kwaɗa masa a hannu, ya cigaba dai mata dariya yace "naga hannun nan kamar wani abun kike kallo a jiki, bari in ciro miki shi sosai ki gani" ya kama botir ɗin gabar rigarasa ze fara ɓallewa. Zaro ido tai ta ja da baya daga kusa da shi, tana kallonsa dariya yai yace "ke da shagwaɓar ki, da tsoron ki, duk ba sa ɓuya, tashi muje ki rakani shop" "Ni ba zani ba banda lafiya" "Ke kullum ba ki da lafiya ne? To sekin rakani" "Ni bana son bi ta wajen SS3 ɗin nan" Yace "meyasa?" A ɗan marairaice tace "Kasan wani abu kuwa?" Sadik yace a'a sekin faɗa. "Kasan wannan Salma ɗin ta SS3?" Yace "eh na santa" "Ita ce wai tace wai tana so in zama ƙanwarta, idan aka fita break wai inje" Take ta ga annurin fuskar Sadik ya ɗauke, wani gumi ya tsatstsafo a goshinsa, cikin kaushin murya yace "meya haɗa ki da ita?" "Ni ba abunda ya haɗani da ita, kawai ranar na gansu a toilet ne, wai wata ba ta da lafiya, Nasreen wai cikinta ya faɗi, naji tace ina burgeta shine yau tai min Magana" "Cikin waye ya faɗin?" Ya tambayeta yana tsareta da idanunsa. "Wai cikin Nasreen ɗin" ta faɗa cike da rashin wayo. "I hope ba abunda sukai miki?" Ta girgiza kai "ba suyi min Komai ba" Be jirata ba ya tashi fuuu yai waje, hakan ba ƙaramin ɗaure mata kai yayi ba. Kai tsaye SS3 ya nufa, hakan yai daidai da fitar malami daga ajinsu. Ba shakka, ba komai ya kutsa kai ya nufi gurin zaman Salma. Kallo ɗaya tai masa tace "lafiya ka zo ka tsaya min a ka haka kamar wani ɗan sanda?" Dukan benci yai da ƙarfin gaske, sannan ya nunata da yatsa yace "kashedi na zo nai miki, nasan kin san Farhan, to idan kuna rashin mutuncin ku da ɓata yaran mutane, ku kiyayi abunda yake nawa, Farhan is my Asset, don't Cross your limit, kince kina son ta zama ƙanwarki, to ta gayamin, wallahi da wasan wasa kika kuskura wani abu ya sameta, wallahi tallahi I will show you what am capable of doing na gaya miki" Miƙewa tsaye tayi tace "kai ɗan saurara, kar ka gayan maganar banza, idan kana wa saura hura hanci da tunƙaho karka kuskura kaimin, ni ba sa'ar yinka bace, shekara nawa na baka kamarni zaka zo kace za kaiwa warning?" Nasreen cikin sauri tace "ke Salma, namiji ne fa wallahi akan 'yar nan ze iya yi miki illa, akan kuɗin vanacula ɗinta ranar ba kiga tijarar da yai min ba" Mubarak babba ne yace "calm down Sadik, dan Allah kayi haƙuri ka manta da ita kawai, insha Allah ba abunds ze samu beb ɗinka" "Na rantse da Allah, da wasa ita da gangs ɗin ta sukaiwa Farhan wani abu senai musu illa wallahi, Ita ɗin tawace nikaɗai, nasan suwaye ku nasan abunda kuke aikatawa, kar ku kuskura shashancin ku yazo kan yarinyar nan, ba ruwana da 'yar kowa a makarantar nan, nima ban yadda a taɓa abunda yake nawa ba" Da ƙyar Mubarak ya fidda Sadik daga ajin nan, sannan ya dawo ya kalli Salma yace "ke baki da hankali, wannan yaron kamar ta masa Asiri haka yake wannan zafin kan akanta kamar matarsa, babansa yana da ɗaurin gindi a ƙasar nan, zaki iya jawa kanki masifa" "To shine se ya zo kaina yana min hauka?" "Kibi komai a sannu, bake kaɗai ba ni kaina Yarinyar nan tarko zan mata, dan wallahi ta burgeni, shi ba ya tsaya sokonci ba, ze ga tsiya sena watsa rayuwar yarinyar uban kowa ya huta" Tace "Aikuwa sedai ya mutu, dan nima zan cigaba da bibiyarta. Ita kam Farhan sam bata san ma wace wainar aka toya ba tana fama da kanta. Ba tsammani sega Sir Nazir ya shigo ajinsu, kuma alhalin a ranar kwata kwata ba su da lesson ɗin sa. Gashi kowa yana tsoro balle suyi Magana, dan da wani malamin ne bore za suyi suce su ba zasu saurari lesson ɗin ba. Lilly tai ɗaiɗai ta cire jacket ɗin ta, ta ɗora ƙafafuwan ta akan benci, tana cin shawarma, hatta ɗan ƙaramin hijjabin jikinta ta naɗe shi baya, tana ciye ciyenta. Yana shigowa ta sauke ƙafafuwan ta tana raraba ido, yayin da cikinta ya dinga wata uwar ƙara kamar ya ɓaci. Ya shigo hannunsa ɗauke da litattatafai, ya juya ya fara rubutu akan board, ita kuma tai maza ta cigaba da cin shawarmar ta, yana juyowa sukai ido huɗu. Bece mata komai ba, ya cigaba da abunda yake, ɗaya bayan ɗaya ya dinga raba musu litattafan su, da yazo kan Farhan har seat ɗinta yaje ya ajiye mata, ya kalleta yace "Congratulations, you got the highest score in my Assignment, And your note and digrams are well drawn And label, clap for her please" Raf raf raf. Suka tafa mata. Ya kalleta yace "yadda kike brilliant ɗin nan Allah ya shirye ki, yasa ki dena biyewa wancan ɗan iskan yaron kuna lalacewa" Dumm haka ƙirjinta yai mata, dan maganar ta daketa, ta rasa meyasa yake son dizgata haka a gaban 'yan ajinsu. Shi kam ko a jikinsa kamar beyi Komai ba. "Fatima Hakeem, stand up and explain the assignment i gave you" Gaban Lilly ya faɗi, ta miƙe tsaye tana zazzare idanu, dan ita ta manta sam akan me ma ya bada Assignment ɗin. Ta kai mintuna uku ba tare da tace komai ba. Cikin tsawa yace "Am talking to you my friend" Ba ta san lokacin da tace "Ni i have no idea on it" tai maganar tana hararsa ta gefen ido. "Wow you have no idea on it, na bada Assignment ba kiyi ba, ba ki submitting littafin ba, nace ki zo kin ƙi zuwa, na shigo class kin cire riga, kina ciye ciye, bagidajiyar ina ce ke?" Shiru tai ta sunkuyar da kai. "Oya bring out your notebook let me check" Tana zumɓura baki ta ɗakko littafin ta miƙa masa. Sannu a hankali ya dinga buɗewa yana dubawa, ba uwar da takeyi a littafin ba ta note ba ta Assignment. Ya ajiye littafin ya kalleta yace "Follow me to my Office, daƙiƙiyar banza da ta wofi, ba abunda kika iya, sedai ku dinga burga kuna hura hanci iyayenku n kashe maƙudan kuɗi, ana kawoku a manyan motoci amma kanku bakomai, hopeless girl" Ƙunƙuni ta shiga yi, tana ƙoƙarin ɗaukar jacket ɗin ta, amma yai mata wata razananniyar tsawa, ba shiri tai waje da gudu. Class rep yace "taɓ she kashin wata ze bushe yau" Yasmin tace "Wallahi kuwa dan babu alamar imani a idonsa" Yana fita Sadik ya shigo ajin su Farhan, tai mamakin sake ganinsa, yai mata alamar ta biyo shi. Ba musu ta tashi ta bishi, kan barandar ajin su Farhan suka tsaya, ya kalleta yace "Farhan" Ta amsa da "Na'am" "Ba ke babu wannan 'yan SS3 ɗin, duk wadda ta kuma samunki da zancen wai ki zama sister ɗin ta ko makamancin haka, ki sanar dani Please" Farhan tace "to ni dama ba saninsu nai ba, wai amma meyasa kace haka?" "Babu wani abun kirki da ke tattare da su, galibinsu 'yan lesbian ne" "Meye lesbian?" Ta tambaye shi tana kallonsa. Lallai Farhan Yarinya ce, ba ta san ma'anar kalmar lesbian ba. "No karki damu, ba ta da wata ma'ana kawai dai ki kiyaye kinji Babyna, ke tawace nika ɗai Please Farhan watch your self in this school, ni I thinks you are quiting this school as soon as possible, da na samu admission, insha Allah zamuyi Aure mu tafi tare, ba zan iya barin ki a makarantar nan ba" Ajiyar zuciya ta sauke tana ɗan kallonsa. "Anjima da yamma zanje in duba hall ɗin da za'ai birthday ɗin nan, ko kina da wani zaɓi ko ra'ayi?" Ta girgiza kai alamar a'a. "Ni bana son wannan girgiza kan, talk to me" "I have no choice, duk abunda kai shikenan" "Ok to shikenan, I love you Baby" Murmushi tai tana jin yadda zuciyar ta ta karɓi kalmar da ya faɗa ɗin, ta juya ta koma Class. Nana kam da taje makaranta kasa haɗa ido tai da su Alawiyya, saboda yadda aka dizgata a gabansu, suka dinga yar mata da ƙananun maganganu, sedai duk iya faɗan Nana ba ta kulasu ba ta share su, ta cigaba da sabgarta. Inna tana ankare da ita harta dawo daga Makaranta, ba ta sakin jiki ta kula Inna. Har ɗaki Inna taje ta tarar da ita, ta ƙare mata kallo sannan tace "Nana gaba kike dani dan na hanaki bin ƙawaye ko?" Ta girgiza kai alamar a'a. "Ƙarya nai miki kenan? Ke 'yar ƙanƙanuwar ki dake har kin san ki fifita ƙawayenki a kaina? Wato ƙawayen ki sunfi mahimmanci a kaina ko? To wallahi duk ranar da suka kuma zuwa gidan nan gurinki, dogari zan saka yai musu dukan tsiya, daga ke har su ɗin, shashasha mara hankali kawai" Wani malolon takaici ne ya tsayewa Nana a rai, ta rasa wannan wane irin abu ne haka, amma tai shiru tana kumbura wuya. Lilly kuwa Suna zuwa Office ɗin Sir Nazir ta tsaya kyam a tsaye, a hasale yai mata tsawa "On your knees" Ta kalleshi sororo "Sir knees kuma?" "You Are asking me? Ba ki ji me nace ba ne?" Abun da ba ta taɓayi a makarantar ba, haka ta durƙusa akan gwiwowinta, tana cuna baki. Ya samu guri ya zauna, ya kunna System ya shiga sabgogin sa. Tun tana tunanin abun na ƙare ne har ta sare, ƙafafunta suka dinga rawa, duk da AC dake Office ɗin amma ta haɗa gumi, farar fatarta tai jawur, gwiwowinta suka dinga mata wani irin raɗaɗi. Cikin rauni tace "Please Sir am sorry" Banza yai mata ya cigaba da aikinsa. Maimaita abunda tace tayi, Amma ya ɗago ya kalleta yace "kika kuma yin Magana, sena sa bulala na zane miki jikinki" Yadda yai maganar ba alamar wasa, yasa ta karaya ta fashe da kuka. Amma babu alamar mutumin nan ze ƙyaleta, ta dinga kuka tana shesheƙa, amma yai banza da ita. Haka nan yaji zuciyarsa na bugawa da Sauri sauri, tana ƙara sautin kukan bugun zuciyarsa na ƙaruwa, amma ya dake. Ji yai kamar numfashi yana neman gagararsa saboda tsanantar bugun zuciyar, ya kalleta yace "for now ki tashi ki tafi aji, amma kullum idan aka fito break, ba ki da break, nan zaki zo ki kwafe note ɗin nan gaba ɗaya, kuma kiyi Assignment da duk diagrams ɗin fa baki ba, tashi ki ban guri fitsarariya kawai. Miƙewa tai a hankali ta shiga jan ƙafarta, saboda yadda su kai mata tsami sosai, jin su take kamar ba'a jikinta ba. Da ƙyar ta sauka daga kan benen, ta na ta shesheƙar kuka, tamkar za ta shiɗe. Sedai tana tafe a hankali tana jan ƙafar, kan ta kai ga ajin nasu ta faɗi a hanya!. A garzaya a buɗe AREWABOOKS, Ai following Ayshercool, RUƊIN ƘURUCIYA ya kusa komawa kan manhajar AREWA BOOKS. Domin gyara Sharhi ko shawara Ayshercool 07063065680. [6/4, 4:21 PM] Jakadiyar Arewa:       🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ RUƊIN ƘURUCIYA PERFECT WRITERS ASSOCIATION (WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS) https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ P. W. A *Story and written by* AISHA ADAM (AYSHERCOOL) Writer of WATA KISSAR..(Sai mata) ABDUL JALAL AƘIDATA (paid book) WUTA A MASAƘA NOW RUƊIN ƘURUCIYA (paid book) _Labarin RUƊIN ƘURUCIYA, na iya zuwa da wani salo, wanda baku saba ganinsa a rubutuna ba, hakan ya biyo bayan akan abunda aka gina labarin, wani abun ze ɓoyu wani Abun baze ɓoyu ba sakamakon labari ne akan teenegers, yara masu tashen Balaga, but hakan ba ya na nufin na sauka daga kan tsarin yadda nake Rubutu bane, ƙofata a buɗe take dan karɓar ƙorafi, gayra ko shawara_ ⚠️⚠️⚠️ƘIRƘIRARREN LABARI NE, BAN YADDA A JUYAMIN SHI TA KOWACE SIGA BA SEDA IZININA ❌❌‼️       SHIN KUNA DA LABARIN MANHAJAR AREWABOOKS KUWA? MANHAJA CE DA TAZO DA TSARIN DAN SAUƘAƘAWA MARUBUTA DA MAKARANTA SAUƘIN CINIKAYYAR LITATTAFAI. TA IN DA ZAKU IYA SIYAN KOWANE FEJI AKAN KUƊI ƘALILAN, DAI DAI DA ALJIHUNKU. INA FARINCIKIN SANAR DA KU CEWA, DA ZARAR NA KAMMALA FREE PAGES, ZAKU CIGABA DA SAMUN CIGABAN LITTAFIN RUƊIN ƘURUCIYA, AKAN MANHAJAR AREWABOOKS. KARKU BARI A BAKU LABARI, AKWAI TARIN DARASIN RAYUWA A CIKIN LITTAFIN.                                                    30 Sosai Lilly take kokawa da numfashinta, dan ya dinga sauka cikin huhunta da sassan jikinta, amma abu ya gagara. Sadik da ya taho daga ajinsu ne yai karo da ita a hanya a ƙasa. "Subhanallah, ke meyafaru meya sameki haka?" Ya tsaya yana tambayar ta. Ba ta iya magana, se numfashinta da ke tayin sama yana ƙasa. Rasa abunyi Sadik yayi, ana haka sega su Nas, sun dawo daga inda suke zuwa shaye shayensu. Nas yace "lafiya ita kuma wannan meya sameta take kwance a ƙasa?" Sadik yace "nima ban sani ba, na taho ne kawai na ganta a kwance a nan" Amin yace "to ai kamata yai ka ɗagata da ga ƙasan nan, ko Clinic ka kaita" Sadik ya kalleshi yace "waye ze ɗagatan?" "Kai mana" Nas y faɗa yana nunashi. "Bana taɓa abunda ba nawa ba" Sadik ya basu amsa. "Dallacan banza, ji wata ƙaryar wofi wai baya taɓa abunda ba nasa ba" Sir Nazir ne ya sakko daga kan bene, hannunsa riƙe da litattafai alamar aji za shi, har ze tafi ya hangi su Sadik a tsaye a guri ɗaya. Takawa yai ya ƙarasa in da suke tsaye, yaga Lilly a baje a gurin. "Yasalam, meya sameta haka?" Sadik ya ɗage kafaɗa alamar i don't know, ya ja da baya a hankali ya bar gurin. Nazir yace "this is an emergency case, you are not supposed to stand just watching at her, what if her breath seize. Be saurari me za suce ba, yasa hannu ya ɗagata yace suje ajinsu Lilly su kira masa mutum biyu a ƙawayenta, daga nan ya nufi Clinic da ita. Ya samu gado ya kwantar da ita, sedai me kula da Clinic ɗin baya nan, yana kwantar da ita sega Haseena da Yasmin. Suna zuwa suka zubawa Lilly ido, duk ta ɓata Uniform ɗinta, se ƙoƙarin tashi zaune take, amma Nazir ya riƙeta. Ya kalle su Yace "maza ku zo ku riƙeta karta tashi, Sannan ku cire mata hijjabin jikinta" Haka kuwa akayi, suka cire mata hijjabin jikinta, suka barta daga ita se long slip ɗin ta, ta ɓalle botir ɗin saman rigar, dan haka idonsa ya sauka fatar wuyanta zuwa ƙirjinta me matuƙar haske. "Astagfirullah" yaita maimaitawa a zuciyar sa, ya kalli su Yasmeen yace "dama ta na da wani special case ne?" Haseena tace "Eh dama tana da Asma, amma ba ta fiye tashi ba" Yace "ke Haseena, jeki staff room, ki kiramin Madam Joy" Da Sauri Haseenan ta fita daga ɗakin dan aiwatar da abunda yace. Sedai numfashin Lilly ya cigaba da sarƙewa, Dan she's unconscious ba ta san meke faruwa ba. Yace "ko a jakarta Babu inhaler, ko maganin da take sha?" Yasmin tace "gasky babu, dan tana daɗewa sosai ba ta tashi ba, sedai idan tayi kuka sosai take tashi, dan har cewa take ta warke daga Asma" Kasancewar Microbiology ya karanta, yasa yasan wasu daga cikin clinical skills ya kalli Yasmin yace "can You resustate her?" Yasmin tace "Sir meke nan?" "Ki bata artificial respiration" "Wallahi sir ban iya ba" Tsaki yayi, ya durƙusa daf da fuskar Lillyn da ƙirjinta ke ɗagawa yana sauka, numfashinta na fita da Wani irin sauti, wani lokacin ma ya ɗauke gaba ɗaya seta ɗan ɗau lokaci kan ya dawo. Sedai yana kai fuskarsa yaji zuciyarsa tana bugawa da sauri da sauri, addu'a yai tayi sannan ya kai bakinsa na ta, yasa hannunsa ya matse hancinta, ya ɗaga haɓarta ta kalli sama sosai yasa bakinsa a nata ya shiga hura mata iskar bakinsa. Sama ƙirjinta ya ɗaga amma ta kasa karɓar iskar, se hawaye dake bin gefen fuskarta. Ya cigaba da ƙoƙarin ba ta artificial respiration, a hankali huhunta ya fara karɓar iskar, Yasmin kuwa ta zuba musu ido tana kallonshi. Haseena ta shigo ita da Madam Joy, sedai ɗan turus Haseenan tai tana kallon ikon Allah, dan ba ta taɓa gani ba. Madam joy ta ƙarasa da sauri tana tambayarsa meyafaru. Nan yai mata bayani, tace to bari  Director magana, a aika a siyo inhaler ai mata amfani da shi. Madam Joy duk tace su Haseena su koma aji. Suna fitowa daga Clinic ɗin Haseena tace "ke Yasmin, kinga abunda na gani ko nika ɗai na gani?" Yasmin tace "taɓ, ni da kika bari a gurin, ai ni yace in mata nace ban iya ba, shine yai mata da kansa" Haseena tace "taɓ to Allah ya kyauta, kinga yadda ya wani naniƙeta?" "Na gani mana, Allah ɗai yasan me yai mata ai daga Office ɗinsa take, tunda muke da ita sau ɗaya na taɓa ganin Asmarta ta tashi se yau" Haseena tace "baiwar Allah, ga wahalar ciwo ga yawun ƙato, kai Allah ya bata lafiya akwai buduri yaseen" Suka tafi ajinsu suna dariya. Da aka tashi daga school, A harabar makarantar Farhan ta tsaya tana jiran fitowar Sadik. Tana nan tsaye se gashi ya taho, yana tafiya a hankali, sedai shikaɗai ne ba abokan nasa. "Yana ganka wani iri kamar mara lafiya?" "Am ok, just tired" "To Sannu" ta faɗa cike da kulawa. "Yawwa matar, kinga da munyi Aure muna zuwa gida ki ban Abinci, ki rarrasheni inyi bacci" Banza tai masa kamar ba ta ji ba. Matsawa yai kusa da ita yace "kina jina fa, shine ki kaimin shiru?" Sunkuyar da kai tayi taƙi kallonsa, kuma taƙi Magana" "Hmm, lalallai Yarinyar nan kin raina ni, shikenan mu tafi" "Ni ba binku zan ba Napep zan hau" Yace "Akan wani dalilin?" "Ni tsoro nake ji, kar a gayawa Abbana kawoni ake gida a mota" Sadik ya fuskanci yau rigima take ji, hannu yasa ya ƙwace jakarta da take ƙoƙarin goyawa yace "in kinga dama kizo mu tafi, in ba haka ba wallahi na tafi da jakar nan sedai ki bini gidanmu ki karɓa" Zare ido tai jin yace wallahi, ta ina zata fara zuwa gidansu karɓar jaka? Ba shiri ta bishi da sauri zuwa motarsu. Sedai se cika take tana batsewa, tana hura hanci, suna tafe a Motar taƙi kulashi. Shima ya shareta sedai yana satar kallonta. "Wash Allah" ta faɗa a marairaice. Ya kalleta yace "lafiya kuwa" "Lafiayata ƙalau" ta bashi amsa. "Ok na gane, so kike dama in kulaki dan kinji nai miki shiru" "Ni cikina ne yake ciwo" "Waike wannan wane irin ciwon ciki ne?" Shiru tai masa ta kashingiɗa a jikin seat ɗin motar, tana jin yadda mararta ke ɗan takura mata da ciwo. Sadik yaita mata magana amma tai masa shiru, seda suka zo in da take sauka, sannan ta ɗau jakarta tacewa direban  "Baba nagode" Direban yace "Yawwa bakomai" Sadik yace "Nifa?" Murguɗa masa baki tai ta sauka, sedai tana sauka yaga inda ta tashi yai staining na jini, ga shi ƙasan baban hijjabin da take sawa ma ya ɗan ɓaci. Kwanciya yai a jikin seat ɗin motar, ya ɗan shafi sumar kansa yace "Babyna ta girma ba labari, sedai yana ganin kamar tayi yarinta sosai da farawar" Murmushi ya cigaba da yi, wanda shi kansa be san dalilin yin sa ba. Suna zuwa gida ya kalli direbansa yace"A wanken motar nan" Be jira amsar da ze bashi ba yai gaba abunsa ya nufi BQ. Lilly kuwa seda aka haɗa mata da ƙarin ruwa da allurai sannan ta dawo hayyacinta gaba ɗaya, Sir Nazir yayi regrating Punishing ɗinta da yai har yai leading ɗinta ga Wannan condition ɗin. Amma a zahiri ya dake ya nuna ko a jikinsa, seda ta gama farfaɗowa sannan aka ɗakko mata jakarta daga aji, Madam Joy ta riƙota ta kaita motar Makaranta, ta shiga dan raka Lillyn gida. Seda Nazir ya tabattar komai ya daidaita, sannan ya koma ya tattara kayansa shima ya tafi gidan da yake zaune. Sedai lokaci lokaci da ya tuna yadda ya kasance da Lillyn a ɗazu dan ceto ranta, se yaji wata irin mummunar faɗuwar gaba, ƙirjinsa kuma na bugawa da ƙarfin gaske. Ya dinga maimaita 'Innalillahi, wa innalillahi raji'un" A ƙauye kuwa Nana ce zaune a can ƙuryar ɗakin Inna, ta samu ƙatuwar 'yar tsanarta tana ta taje mata gashi, dan sam taƙi kula Inna, hakan ya kasance ɗabi'ar Nana, duk da shegen surutunta, amma lokuta da dama idan aka ɓata mata rai, se tai shiri ta dena maganar se abunda ya zama dole. Sedai kan tai irin wannan fushin tana daɗewa. "Nana" Inna ta kira sunanta, ba ta amsa ba sedai ta ɗago ta kalli Innan "Ba zaki dena wannan fushin ba ko? Dani kike fushi ko Nana?" Nana tace "A'a ni ba fushi nake ba fa" "Ƙarya nai miki kenan, to dan ubanki wannan ba halin zuwa gidan miji bane, ba Namijin da ze ɗauki wannan iskancin da rashin mutuncin naki" Nana tai shiru taƙi magana, can Innan ta kuma cewa "Nasan zakiga kamar ina takura miki akan wasu abubuwan, ba ina yine da cuzgunawa rayuwarki ba, ina yi ne dan ganin Rayuwar ki ta inganta. Jiya duk hirar da ku kai da waɗanda suka zo gurin naki ina jinku. Da sauri Nana ta kalli Inna, dan sam ba ta zaci taji hirar tasu ba. "Ƙwarai kuwa, ko dan kinga na ƙyaleki? Naji suna gaya miki wani yana bakin layi yana jiranki, Nana ita rayuwa ba'a mata gaggawa, duk saurayin kirki da yake sonki saboda Allah, gidanku ze zo ya nemi izini, ba wai ya dinga laɓewa a bakin hanya yana tsare ki ba. Nana ke yarinya ce, kina kan ganiyarki ta RUƊIN ƘURUCIYA, Shiyasa abubuwa da dama kike ganin kamar ina takuramiki. Ba takura miki nake ba, so nake rayuwarki ta inganta, ki guji ƙawaye barkatai, idan kika fiye ƙawaye da yawa zaki zama baki da sirri, sannan ba kamun kai, dan zaki suffantu da ɗabi'u daban daban daga gurin su, masu kyau da marasa kyau. Dan haka duk abunda ya shige miki duhu, wanda kike buƙatar ƙarin haske ni zaki samu ki gayawa, duk wata shawara da ƙawa zata baki, in dai zaki iya ɓoyewa ba zaki faɗa ba to ba shawarar Allah da Annabi bace, dan haka ki kiyaye kinji abunda nace miki?" Nana ta jinjina kai alamar eh. Inna tace "Yawwa". Koda Madam Joy ta raka Lilly gida, ta gaya musu kawai ciwonta ne ya tashi, sun bata taimakon da ya dace a Clinic ɗin Makaranta. Maman Lilly ta karɓe ta cikin girmamawa tare da yi mata godiya. Mamanta se jera mata sannu take, yayinda zuciyar Lillyn fal take da jin haushin Sir Nazir, babban abunda ya ƙara ƙular da ita be wuce yadda tana buɗe ido ta kalleshi, ya wani haɗe rai ya bar Clinic ɗin ba. Ba ta san lokacin da tai ƙwafa a fili ba. Mamanta ta kalleta tace "Lillyna meke faruwa ne? Nifa nayi mamakin yadda a kai ciwon nan naki ya tashi, ko dai an miki wani abun ne kinyi kuka?" Cikin taɓara Lilly tace "please Mamma allow me to rest, am still feeling pain in my chest" "Ohh God, ko a kira Doctor Kaseem ne?" "No am ok, i just need rest" "Ok rest my dear, amma zuwa magariba insha Allah zamuje Asibiti, bana son mahaifinki yaji ciwon nan ya tashi, ban kaiki Asibiti ba yaita sababi" Lilly ba ta sake Magana ba se gyara kwanciyarta da tai. (Cikakken sunan Lilly Fatima, itace 'yar Auta a gidan su, su huɗu ne a gidansu, babanta Babban General ne na Sojoji, yana matuƙar ji da ita, kasancewar sunan mahaifiyarsa ya samata, shine suke ce mata little daga baya kuma suka koma cewa Lilly, hakan yasa ba kowa yasan sunanta na gaskiya ba). Da magariba ba yadda maman Lilly ba tai da ita ba akan suje Asibiti amma taƙi, se ƙyaleta tai. Sadik kam Kamar yadda ya saba duk dare, hotonta yake ta zooming yana ƙare mata kallo, kamar a lokacin ya fara ganinta, yana jin wani abu yana cigaba da shigarsa a kanta. Ajiyar zuciya ya sauke lokacin da ya kalli agogon wayarsa, ƙarfe ɗaya da rabi na dare, a hankali yai juyi tare da ƙanƙame wayar a jikinsa yana sauke numfashi. "Allah ka amince min na mallaki Farhan" Wani irin gumi ne yake tsatsafowa a goshinsa, a hankali ya ajiye wayar ya miƙe ya fito falon su. Faruk ya tarar yana kallon wani Nigerian Film, kusancin jarumin da jarumar Film ɗin na nuna wani abu na shirin faruwa. Tsakin da Sadik yai ne yasa Faruk ɗagowa ya kalli in da Sadik yake yace "kai kuma kai da waye?" "Wannan shirmen da kake kallo mana Sadik ya bashi amsa yana buɗe fridge, ya ɗakko ruwa me sanyi. "Ai seka tsaya ka gani kan ka yanke hukunci, tunda ba wani abun a kai ba" Ɗan taɓe baki Sadik yai yace "Ni wannan ɗin ma shirme ne, mutum na zaman zamansa ya kallowa kansa damuwa" Dariya Faruk yai yace "Allah nawan?" Sadik ya zauna akan kujera one seater ya ɗora ƙafarsa, a kan ƙaramin teburin dake falon ya kalli Faruk yace "bro, am telling you the truth, wallahi bana iya jure kallon wannan fina finan, a simple Romance can put me in trouble, you understand what I mean" Faruk yai murmushi yace "So, seka dena kallon Film gaba ɗaya ka koma cartoon" "Ba zaka gane bane" Sadik ya faɗa yana shan ruwan da ya zuba a kofi. "Ya zakace ba zan gane ba, i went through same situation as you, kawai Lokaci ne da jiki ke girma, da alamu na zama cikakken mutum shine kawai, amma nan da wani lokaci zaka koma normal" Ɗan guntun tsaki Sadik yai yace "ni bana tunanin wannan yanayi ne da zan iya fita daga gareshi lokaci guda, duk kallace kallacen fina finai da nayi a baya, bana jin komai se haɗuwata da Wata yarinya a makarantar mu, i really fall for her, gaba ɗaya na kasa gane kaina, nayi ƙoƙarin nusar da Mother ni Aure nake so, amma se ta shareni koma taimin faɗa" "Hmm ai dole tai maka faɗa, Sadik dudu guda nawa kake ne? Shekarun ka nawa a duniya da har zaka fara zancen Aure? Ni ban yi wannan zancen ba se kai, kasan Aƙidar Gidan nan ko? Boko first before anything" "Aƙidar banza, ai ba dokar Allah bace, ni wallahi idan aka cigaba da tafiya a haka, ba zan iya wani karatu ba" yai maganar yana tsuke fuska. Faruk ya tashi daga in da yake zaune, ya dawo kusa da Sadik ya zauna ya dafa kafaɗarsa yace "Sadik, ita yarinyar da kace sanadinta ne ka shiga wannan halin, ba wani abu bane face RUƊIN ƘURUCIYA, wanda yake faruwa a lokacin tashen balaga, wani abune na ɗan lokaci, kuma abun da kake ji kowa ma yaji, amma dannewa ake, kar ka sake wannan feelings ɗin yasa ka rusa Rayuwar ka, kayi ƙanƙanta dafara ɗaukar stress na marital life, just forget about her, focus on your life, da zarar ka samu abunda kake so zaka dena jin wannan son, dan haka ka kula" Shiru Sadik yai yana sauraron Faruk, a hankali ya sauke ajiyar zuciya, ya ajiye kofin hannunsa, ya miƙe tafi bedroom ɗinsa ba tare da ya kuma cewa komai ba. Safa da marwa ya shigayi, yana son tabattar da dagaske son da yakewa Farhan RUƊIN ƘURUCIYA ne? Ya rasa dalilin da yasa kowa yake ce masa ai Soyayyar su RUƊIN ƘURUCIYA ce kawai. Sedai abunda yake ji akan Farhan ya wuce a kirashi RUƊIN ƘURUCIYA kawai, shikaɗai yasan meyake ji a kanta. Da wannan tunanin ya kwanta, har bacci ya ɗauke shi. Kwana biyu Lilly ba ta Zuwa school, se ana uku taje, lokacin ta warware sosai, aikuwa tana zuwa su Haseena suka dinga ihu suna rungumeta. Ture su Lilly tai tace "dalla can marasa mutunci, ba wadda taje dubani a cikin ku" Yasmin tace "Wallahi yau muke cewa zamuje dubaki, jiya mutumin ki yazo yana tambayar ko kin zo?" Lilly tace "waye mutumina?" "Sir Nazir mana" Haseena ta bata amsa. "Uwar mutumina, ai gayen nan Allah ya sakamin kneel down fa ya sani, na dinga kuka ina roƙonsa amma yaƙi saurarata, seda ya ga dama yace in tafi aji, kawai na faɗi a hanya" "Dama ya za'ai ya saurareki, ai shi wannan ciwon naki gaba ta kaishi, ya samu abunda yake so" Da mamaki ta kallesu tace "kamar yaya?" Yasmin tace "ai ni zan labarta miki, da aka kai ki Clinic ɗin nan, kin kasa numfashi bakinsa yasa a naki yana hura miki iska" "What, dalla bana son ƙarya" Haseena tace "to ubanwaye ze miki ƙaryar, Wallahi dagaske ne, ya sa aka cire miki hijjabi daga ke se Long sleep, yaita hura miki iska, a wayance kuma dai kamar dai ba iya hura iskar yake ba" ta ƙarasa maganar suna kwashewa da dariya, banda Lilly da ta haɗe rai kamar zata fashe. "Allah ya isa na" ta faɗa tana jan tsaki. Suka sata  a gaba suka ding tsokanar ta suna dariya. Sunan zaune malamin da suke da shi ya shigo, yai lesson ɗinsa ya gama ya fita, yana fita sega ɗan aiken Sir Nazir yana kiran Fatima Hakeem. Tsaki tayi, dan a lokacin saura mintuna bakwai a fita break, su Haseena kuwa dariya suka cigaba da yi mata, wanda hakan ba ƙaramin ƙular da ita yai ba. Haka ta tashi ta tafi Office ɗinsa, sedai ko da taje kallo ɗaya yai mata ya ɗauke kansa. Wani haushi ne ya sake mamayeta, ta tsaya a tsaye ƙiƙam taƙi Magana, shima ya cigaba da sabgar gabansa. Jin ƙafafuwan ta na rawa ta gaji da tsaiwar ne yasa tace "Sir gani" "Gaki, baki iya gaisuwa ba kenan ko?" Kamar tayi masa tsaki, amma ta dake ta gaishe shi, be amsa yace "me nace miki ranar a Office ɗin nan?" "Ai bani da lafiya" "Will you shut up? Maza kije aji ki ɗakko littafinki kizo, in kin ga dama karki dawo" Juyawa tai ta fita a matuƙar hasale, harda ƙwallar baƙin ciki. Tana zuwa Class ta tarar da su suna karatun littafin watsewa da suka saba. Tace "ke Yasmin shine kuka cigaba bana nan?" "Ba dole mu cigaba ba, yaushe zamu tsaya jiranki?" Suka cigaba da karatunsu, ta ɗauki littafinta tai waje, dan bata son dalilin da zesa Nazir ya kuma yi mata wulaƙanci. Babban abunda ya bata haushi, be wuce yadda takasa faɗar abunda yai mata harta shiga halin rashin lafiya ba, da ko ba komai babanta yasa azo ai masa warning koma yasa a haɗa masa jikinsa. Haka ta cigaba da Tunani, harta je Office ɗin. Kujerar da ke facing ɗinsa ya nuna mata, ta nemi guri ta zauna. Ya ɗakko wani littafi ya miƙa mata yace "maza ki duba daga in da kika tsaya da kwafar note ki fara kwafa yanzu Yanzu. Kamar ta fasa kuka haka ta karɓa, tana jin haushin ajinsu ana can ana karatun Novel ɗin nan ba ita, ya kashe mata break ɗin ta. Note ɗin da ake binta ba kaɗan bane, dan haka tasan ƙaryarta ta kammala shi a yau ɗin nan. A hankali ta fara kwafa, sedai tun ba'aje ko ina ba ta gaji, ta fara tunanin me zatayi wanda zesa ya ƙyaleta ta tafi. Ɗagowa tai ta kalleshi, shirt ce baƙa me gajeren hannu a jikinsa, damatsensa sun cika hannun rigar, sumar kansa zuwa sajensa se shining suke, ta kalli faffaɗan ƙirjinsa ta fara kamanta shi da jaruman da ake siffantawa a cikin book. A ƙalla yana da kaso sittin cikin ɗari na yadda ake fasalta ƙirar jaruman littafi, ba shi da ƙaton baki ga gashi yaiwa haɓarsa ado. ƙirjinsa zuwa dantsensa ta cigaba da bi da kallo, she just imagine how will she feels if he hugs her? Ta tuna yadda aka bata labarin yadda ya ɗauke ta da ta suma, da yadda ya bata artificial respiration, nan da nan ƙwaƙwalwarta ta shiga bata wasu lissafe lissafe da hasaso abunda suke karantawa a littafi game da malamin nata. "Note ɗin zaki kwafa ko kallona zaki cigaba da yi?" A ɗan kunyace ta dawo hankalinta, amma ta kwaɓe fuska cikin shagwaɓa tace "Am starve' Ya ɗago ya kalleta yace "oya die here" Kwaɓe fuska ta kumayi tace "Allah sir am hungry, let me go and eat food" Drower gabansa ya janyo, ya ɗakko donut da drink, ya ajiye mata yace "oya kina ci kina rubutu" Ta janyo donut ɗinta ta fara ci, sedai ƙwaƙwalwarta na mata saƙa a Mugun zare game da malamin nata. A nasa ɓangaren shima yana basarwa ne, amma haka kurum yanzu da yaga yarinyar ƙirjinsa ke tsananta bugawa. Seda aka koma class, Sannan ya bata damar tafiya, ta ɗau littafinta ta juya ta fara wata irin tafiya, wadda seda ya bita da ido harta fita. Nannauyar ajiyar zuciya ya sauke, ya cigaba da aikin da yake. Ko da ta koma aji har wani malamin ya shiga, dan haka kawai ta nemi Guri ta zauna, tana cigaba da tunanin Sir Nazir ɗin. Sadik har yaje ya biya kuɗin ɗan maidaidacin hall ɗin da za'ai partyn, duk wani abu da za'a buƙata ya tanada, hatta rigar da Farhan zata saka ya siya. Sedai Farhan na ta fargabar yadda za'ai wannan lamari iyayenta basu sani ba, tana fargabar Idan Asirinta ya tonu da wani idon zata kalle su?.       Har ƙanan invitation card ya bugo, ya bawa mutane ƙalilan, dan ba gayya yayi ba yadda za'ai komai a tsari ayi a gama. Ya bawa Farhan invitations yace koda wanda zata gayyata, amma tace baby duk wanda ya gayyata shikenan. Yau juma'a ta kama ranar da za'a gudanar da murnar zagayowar haihuwar Farhan, sedai gabanta nata faɗuwa ƙirjinta na ta bugawa, tabbas ba dan Sadii bane bijirewa wannan partyn za tai, dan haka nan taji ƙirjinta na bugawa da sauri da sauri da zarar ta tuna. In da suka saba ajiye Farhan su kai parking, ya kalleta yace "Anjima su Taslim da Khairat zasu zo su ɗakkomin ke, kin riƙe abunda nace ki faɗa a gida ko?" Farhan ta jinjina masa kai jiki a sanyaye. Yace "good, see you later" A hankali tasa hannu ta buɗe motar ta fita, ta nufi layinsu tana ta saƙawa tana warwarewa. Bayan an sakko daga masallaci, Abban Farhan ya dawo gida, taje ta same shi a ɗakinsa suka gaisa Sannan tace "Abba dama..dama maman malamin mu aka kwantar a Asibiti, anjima za'aje dubata shine nake son ka barni" Abba yace "Farhan bana san yawan fitar nan da kike fa, kiyi masa Addu'a kawai ya isa" "Ammm...Abba ai ba ni kaɗai zanje ba, a motar gidansu 'yar ajinmu za'aje su zasu zo mu tafi, su dawo dani gida" "Nifa bana son yawan shishshsigewa 'yan ajin nan naku, kin san dai ba ƙarfinku ɗaya da iyayensu ba, shikenan Allah ya bashi lafiya, ki kula da kanki Allah ya tsare" "To Abba nagode" ta tashi ta fito daga ɗakin nasa, sedai jikinta a matuƙar sanyaye saboda ƙaryar da tai Masa. Shi ya sanar da Ummanta anjima za suje dubiya, ta gaya masa. Ƙarfe uku da 'yan mintuna sega Taslim da Khairat ƙanwar Sadik, sun sha dogayen hijjabai, Taslim nata ƙarewa gidan kallo. Farhan tai sallama da Umma cikin dogon hijjabi, tabi su Taslim suka fita daga gidan. Kai tsaye in da za'ai partyn suka nufa, maimakon su shiga hall ɗin partyn, wani ɗaki suka nufa da ita a cikin gurin, Taslim ce take ƙoƙarin shiryata, ta ba ta wata doguwar gown dark blue tace ta shiga toilet ta saka. Farhan ta dinga juya rigar nan kan ta saka, dan da gani rigar me tsada ce, rigar ta rufe mata ko ina na jikinta, sedai ta kamata tsam a jikinta. Ta fito daga banɗakin tana kakkare jikinta, Taslim tasa comb ta taje mata gashin ta, ta kawo ribboms ta ɗaure mata shi, su kai mata simple make up, aka samata wata hula nan da nan Farhan ta sake haskawa, kamar ba ita ba tai kyau matuƙa, sedai ita duk a tsorace take. Seda suka gama shiryata tsaf sannan suka nufi main hall ɗin da za'ai birthday. Abun mamaki suna zuwa duk an gama hallara, an ƙawata gurin matuƙa, idonta ya sauka akan Mubarak Babba da yake binta da wani irin mayen kallo, take wani Mugun haushin sa da tsanarsa ya sake baibaye ta. Haɗa ido sukai da Sadik yana waya, ya kashe mata ido ɗaya, ta sunkuyar da kai tana murmushi. Duk kunya ta isheta, saboda kayan dake jikinta. Kan a fara Komai Sadik yasa duk wanda ze shigo seya ajiye wayarsa a waje, dan yace be yadda ayi video ko ɗaukar hoto ba, se Camera ɗinsa da ya kawo. Nan aka shiga shagalin ciye ciye da shaye shaye, amma banda Farhan da ta takure kamar ace ket ta zura da gudu dan fargaba da Zullumi. Nas shine yake MC a gurin, ya ɗau mic yace  "Kafin mu cigaba da abunda ya taramu, wato taya abokiyar karatu, kuma wife to be ɗin abokin mu shagalin birthday ɗin ta, akwai wani game da za muyi Yanzu a gurin nan, Prince Sadik zan ajiye wasu papers, zaka fito kai da ita zaka zaɓi paper ɗaya, duk abunda ka ɗauka will be the birthday gift for your Beb" Sadik yace "I already bought the birthday gifts for her" "Wannan ai kai da ita ne, wannan kuma game ne kawai" Sadik yace shikenan ya taso shi da Farhan, Zuwa tsakiyar hall ɗin. Aka zube takaddu da aka ninke a kan tebur akace Sadik ya zaɓa. Yasa hannu ya ɗakko takadda ɗaya, Nas ya karɓi takaddar ya buɗe, take yai shouting "wow, this is an amazing Love game, Prince takaddar da ka ɗakko tace :you will kiss her for good 3minutes as her special lovely, birthday gift" Ƙuuuu cikin Farhan ya kaɗa, ta fara gumi ta zubawa Sadik ido taga reaction ɗin sa. Girgiza kai Sadik yai zeyi Magana, amma suka ƙi bashi dama, suka kaure da shewa da ihu. Nas yace "zamu gani, as a young man abokin namu ya cika namiji ze iya kokuwa ragone haryanzu yaro ne? Ita ma beb ɗin zamuga can she sacrifice to make him happy, zata yadda dan ganin ba ta bashi kunya ba? Ko kuma zata sa yaji kunya a gaban abikansa, Yau dai zamu tabattar namijine ko kuma maza ya rako? Ya kai mutum ko kuwa haryanzu be wuce goyon Mother ba yaro ne" Ire iren wannan maganganun na Nas, suka shiga tunzura Sadik, dan sosai yake jin haushin kalmar yaro da suke kiransa da shi wasu lokutan. Dan haka kai tsaye ya fara takawa a hankali yana tunkarar in da Farhan take. Nan da nan suka ɗau tafi da shewa a gurin. Yayin da ita kuma ta shiga zazzare ido, tana jan numfashi da ƙyar! Kome ze faru? Akwai cakwakiya da tarin darussa me yawan gaske, gefe ga Lilly da Sir Nazir, ga Nana da kakarta RUƊIN ƘURUCIYA karku bari a baku labari yanzu aka fara. Da fari book1 naso in baku free kamar yadda mukai a AƘIDATA se ku sai 2, amma an maida ni gantalallliya, ina posting ba kwa Comment kuma kuna karantawa, dan haka zan cigaba da sawa a Arewabooks, me son cigaba ya siya a can, me buƙatar ƙarin bayani yai min magana ta lambata. Iya wanda sukai payment tunda fari su zan cigaba da turawa ta what's app, nagode ina Alfahari da ku masoya a duk inda kuke. Taku har kullum Ayshercool. Domin gyara Sharhi ko shawara 07063065680. Share please 🙏 [6/4, 9:58 PM] Jakadiyar Arewa: SHIN KUNA DA LABARIN MANHAJAR AREWABOOKS KUWA? MANHAJA CE DA TAZO DA TSARIN DAN SAUƘAƘAWA MARUBUTA DA MAKARANTA SAUƘIN CINIKAYYAR LITATTAFAI. TA IN DA ZAKU IYA SIYAN KOWANE FEJI AKAN KUƊI ƘALILAN, DAI DAI DA ALJIHUNKU. INA FARINCIKIN SANAR DA KU CEWA, DA ZARAR NA KAMMALA FREE PAGES, ZAKU CIGABA DA SAMUN CIGABAN LITTAFIN RUƊIN ƘURUCIYA, AKAN MANHAJAR AREWABOOKS. KARKU BARI A BAKU LABARI, AKWAI TARIN DARASIN RAYUWA A CIKIN LITTAFIN.                                                  31 A hankali ya ƙaraso in da Farhan ke tsaye, yasa tattausan hannunsa ya riƙo nata, ya matse a hannunsa ya kalli cikin idonta. Hakan ya saukar mata da kasala ta sunkuyar da kai daga kallonsa saboda kwarjinin da yai mata. A hankali cikin wata irin murya da ita kaɗai take jin meyake cewa yace "A karo na biyu bayan neman soyayyar ki, zan nemi Alfarma a gurinki Farhan, dan Allah ki amince na gaji da abunda suke min akanki Please Farhan" Shiru tayi tana jin yadda zuciyarta ke wani irin bugawa, gumi keta keto mata kota ina, ba ta gama yanke hukunci ba, taji Sadik ya haɗata da jikinsa, ya haɗe bakinsa da nata. Wata irin tsuma jikinta yake yi, ta rasa gane a wani yanayi take, tsoro ko kuma haushin Sadik, duk da yadda Sadik ɗin ya riƙeta gam, amma ji take tamkar zata faɗi ƙasa, dan haka ta sa hannu ta rirriƙe shi karta faɗi. Wani irin ihu da shewa suka ɗauka a gurin nan Gaba ɗaya, seda mintuna uku suka cika cif sannan Sadik ya cika Farhan. Idanunta sunyi rau rau kamar za tai kuka, se ajiyar zuciya take kamar wadda tai gudu. Nan akaita tafa musu, Nas yace "Weldon gaskiya abokinmu da his wife to be, kun burge kun ƙayatar kuma ka tabattar mana da cewa kai....." Se kuma yaƙi ƙarasawa. Aka yanka cake amma sam Farhan hankalinta baya jikinta, ji take tamkar ta aikata wani gagarumin zunubi da Allah baze yafe mata ba, take taji nadamar zuwa gurin partyn ta baibaye ta. Da sauri ta silale ta tafi in da aka shiryata, ta cire rigar jikinta ta ɗau kayanta ta saka, wasu irin hawayen nadama suka shiga zarya a fuskarta. Ta fito harabar gurin tana ƙoƙarin fita Sadik ya biyota yana ƙwala mata kira, amma taƙi tsayawa, cikin hanzari ya koma ya ɗakko mota, yaja ta da gudu yabi bayanta. Su Nas kuwa dariyar mugunta suka dinga yi, Amin yace "wannan ne karonsa na farko da yayi, amma kamar ƙwararre dama can a matse yake, da haka da haka dai" Babba yace "Aiku kuka ɓata abun da kuka hana ai amfani da ƙwayar nan wallahi" "Dan ubanka idan anyi amfani da ƙwaya muyi yaya da su a gurin nan? Kuma ka san ba komai ake bashi ya karɓa ya ci ba, amma sannu a hankali se mun sa shi a layi" Amin yace "hakane, Amma a hakan ma muny nasara ai" Suka cigaba da dariyar mugunta. Wani wawan parking Sadik yai a gaban Farhan, ya sakko yana faɗin "Farhan meye hakane kikeyi? Ki tsaya in maida ke gida mana" Cikin kuka ta kalleshi tace "ba zan tsaya ɗin ba nika ƙyaleni" "Ba zan ƙyalekin ba, ki wuce mu tafi" "Bazan wuce ɗin ba" Fizgota yai da ƙarfin gaske ya dannata a mota, yaja motar da gudun tsiya ya bar gurin. Sosai Farhan take masa kuka iya ƙarfin ta, amma be saurareta ba, seda ya dangana da unguwarsu, sannaan yai parking. Ya kalleta yace "Farhan me nai miki hakane?" Wani irin mugun kallo tai masa, ta fara ƙoƙarin buɗe motar, amma yai saurin cewa "ok i understand, dan Allah kiyi haƙuri nayi kuskure amma hakan shine mafita kawai a gareni" Buɗe motar tayi ta sauka, ta nufi lungun gidansu da sauri. Sadik ya dafe kai ya jingina da motar yana dana sanin biyewa su Nas. Ta samu guri ta zauna ta sha kukanta, kafin daga bisani ta goge hawayenta, ta tashi ta nufi gida, tan daf da shiga gidan sega Sunusi, yana ganinta ya washe baki yace "me sunan larabawa, daga ina haka?" Ko saurararsa ba tayi ba, ta shige gida sedai tun a soro ƙirjinta ke bugawa, gani take tana shiga Asirinta ze tonu. Ta daɗe a soron a tsaye sannan tayi sallama ta shiga, Umma na tsakar gida tana tankaɗe, ta ɗaga kai ta kalli Farhan, ta amsa sallamar ta maida kai ta cigaba da abunda take yi. Dama hakan umman take mata tun a baya, amma wannan karon se ta tsargu ta ga kamar Umman na san karantar wani abu a tare da ita. Ta daɗe a tsaye sannan ta shiga ɗakinta, tana shiga ta nemi Guri ta zauna ta cigaba da kuka, wai yau ita Sadik yasa bakinsa a nata a gaban jama'a ba kunya bakomai, shikenan ya zama ɗan iska itama yana son ya maida ita. Duk da ta cire wancan kayan, amma natan ma da ta mayar ƙamshin turarensa suke, cikin hanzari ta tashi ta cire kayan, amma ta fuskanci ba iya kayan ne keyi ba, jikinta ne yake ƙamshin turaren nasa. Addu'a ta dinga yi akan Allah yasa kar Asirin ta ya tonu, a gane in da taje da abunda ya faru. Har zuwa dare, amma taƙi sakin jikinta ta kasa sukuni, ga damuwa da fargaba duk sun cikata. Ko yunwa ba taji balle taci Abincin dare, haka taje ta kwanta, hakan be damu Ummanta ba balle taji ba'asin dalilin ƙin cin Abincin nata. Sosai Sadik ya damu da yadda Farhan tai ta kuka, nadama duk ta bi ta lulluɓe shi da dana sanin biyewa abokai, ya dinga tunanin ko a wane hali take? Ko ta dena kukan Allah masani. Sedai wani ɓangare na zuciyarsa ya kasa tantance nishaɗi yake ji ko kuwa? Abunda ya faru tsakanin su yai matuƙar tsaye masa a rai, he really enjoys it, abunda ya daɗe yana kwaɗayi ne dama, sedai damuwar da ya ganta a ciki ya hana shi sakewa yaji nishaɗin yadda yakamata. 'Auta yau ina ka shiga ne, for the whole day ban ganka ba, ba ka zo inda nake ba, rabona da kai tunda ka tafi school" Beji shigowar Mother ba sam, se maganar ta da ya ji, a hankali ya ɗan gyara kwanciyarsa yace "bakomai Mother" "But it seems like something is going wrong somewhere, na ganka wani iri" "Bakomai kaina ne yake ɗan min ciwo, kuma na sha magani" "Naga Abincin ku a falo, kaɗan aka taɓa kaci kuwa?" "No, naje gurin friend ɗina bayan sallar juma'a a can nai lunch" "Anyway shikenan, idan kan be dena ciwo ba se a tafi Asibiti" Ya jinjina mata kai tare da lumshe idanunsa, ina ma ba weekend za'a shiga ba ya samu ya kuma ganin Farhan, ya rarrasheta. A ɓangaren gidan dr. Kuwa wato ango sha guɗa Usman, Amarya ta fara fuskantar ƙalubale daga gareshi, duk da irin tarin soyaya da sukai a waje, ta kasa gane kansa yadda yakamata. Usman wani irin mutum ne me murɗaɗɗen hali, gani take kamar ta dena burgeshi gaba ɗaya, da yawa wasu halayen bata san yana da su ba se yanzu, miskili ne na gasken gaske, idan har tai masa laifi ko zata mutu baze ce mata kin min laifi kaza ba, sedai tagavya canza gaba ɗaya ga zuciyar tsiya, nan da nan damuwa ta isheta, taga tamkar canza mata Ussyn a kai ba shine wanda sukai soyayya ba. Wayarta ta ɗakko ta fito falo ta zauna, ta buɗe ta shiga contact ɗinta ta fara duba lambobi, tana zuwa kan wata lamba da aka saka my other half tai ajiyar zuciya da alama, lambar take nema. Nan take ta dannan kira ta shiga sauraren a ɗau wayar. "Salamu Alaikum" Jidda tace "wa'laikum salam, ba dai bacci kike ba?" "Wallahi ba bacci nake ba, nayi aikin gida ne na gaji, ya akayi ne Amarya?" Jiki a sanyaye Jidda tace "Besty dama haka auren yake? "Kai Jidds, yaushe a kai Auren da kike wannan zancen?" "Besty na kasa gane kan dr. Gani nake kamar an canzamin shi, gaba ɗaya na dena burgeshi, duk rawar kan nan da yake a kaina babu, in yi kwalliya in tsuke, amma ko kallo ban isheshi ba na rasa meye matsalar" ta ƙarasa maganar cikin damuwa. Wadda ta ke kira da besty ta gyara zama tace "Jidda kenan, lokacin da nake miki gargaɗi ina ɗoraki a hanya gani kuke Kamar ban waye ba, ban iya soyaya ba, ta yaya ba zaki gundure shi ba, bayan tun kuna waje kan kuyi Aure kin saba tura masa hotunan ki da ƙananan kaya, har video Call kuke da sleeping gown a jikinki, to me zaki da zako burgeshi kuma? Muna school idan yazo hugging ɗin sa kike, you even kisses his cheeks, idan nai Magana se kuce ni 'yar ustazai ce, to ga abunda nake gaya miki nan, abunda zeyi ɗokin kin gama nuna masa a waje, to what next kuma?" Cikin sanyin jiki Jidda tace "hakane besty, wallna gani, kuskure dai na riga nayi shi, amma yanzu meye mafita, ke kaɗai na gayawa halin da nake ciki" "Mafita ɗaya ce, ke dama ɗabi'arki ce zama da English wears kullum kamar 'yar turawa, tunda he's no more appropriating ita, ki koma masa ƙabilarki ta Hausa Fulani, ki duba kayan lefenki ki dinga masa wankan atamfa da leshi, idan yaso ki dinga saka English wears ɗin lokaci zuwa lokaci, Sannan shaƙuwar da ku kai a waje kar ta sa ki dinga kallonsa kamar mate ɗinki, ko ki dinga masa magana ba wani respect, no matter how close you are to each other, he deserves a respect from you shi namiji namji ne, ki dena wannan maganar taki cikin gadara, ki fara da jarraba wannan mu gani, se muga meye next abun yi" "Ka besty i love You lodi lodi, ina yinki Sisyna, insha Allah zan jarraba Allah yasa a dace" "Ameen Allah ya daidaita, kice ina gaishe shi" "To zeji insha Allah" Jidda ta fara tunanin maganganun bestyn ta, wato duk abun nan da suke a school suna ganin wayewa ce ashe yana da negative impact a gaba? Dama duk abun nan da take dan burge Usman kuma a kirata wayayyiya ze zo ya dena burgeshi? In Kuwa hakane Lallai a rayuwar ƙuruciya ana tafka shiirmen da ze zo ya zamewa mutum abun dana sani a gaba. Daga Sadik har Farhan sukuku su kai Weekends ɗin, damuwar Sadik ɗaya kukan da suka rabu tana yi, ya dimga fatan Allah yasa karta rabu da shi a dalilin abunda ya faru. Sedai baze iya misalta zallar nishaɗin da tsananin shauƙin soyayyar da ya shiga ba, a lokacin da yake sumbutar Farhan, wani abu ya dinga ji from no where yana ratsa ilahirin jikinsa, dan gaba ɗaya mantawa yai da batun wani ƙyanƙyami ko wani abu me kama da haka, hakan ya ƙara kwaɗaita masa son Auren Farhan, sabida wani irin sonta da ya ƙara shigarsa. Amma ba ya jin ze kuma yadda ya aikata makamancin wannan kuskuren, dan shi kansa yayi nadamar biyewa su Nas ya aikata abunda be taɓa aikatawa ba a rayuwar sa. Duk yadda ta so jin tsanar Sadik a ranta saboda abunda yai mata amma abu ya gagara, sam ba taji ta tsane shi a zuciyarta ba, mussaman idan tai la'akari da shima be san abunda su Nas suka shirya ba, sedai a jikinta tana jin abunda suka aikata ɗin ba daidai bane, kuma kasancewar sun aikata a gaban mutane, ba za'a taɓa dena kallon su da abun ba. Ba zata iya misalta yanayin da ta shiga a lokacin da abun ya faru ba, dan Tamkar a mafarki haka ta dinga ganin lamarin, kuma ta kasa tantance halinda ta shiga, saboda taji wani abu da jikinta be taɓa bata ba a tsawon rayuwarta se a wannan karon da abunda ya faru ya faru, lokaci lokaci idan ta tuna abunda ya farun ta kanji ta tsani komai, sedai ƙarƙashin zuciyarta na hasaso mata wani yanayi ne me wuyar mantawa. Ranar Monday kuwa Sadik shirin Makaranta yake, amma cike da zullumin yadda ze tunkari Farhan ta saurare shi. Itama nata ɓangaren tunanin yadda zata shiga makarantar take tayi ido huɗu da wanda akai abun a gabansu, dan tana ji a jikinta ta rasa wata kima da daraja da take da ita a idon wasu daga cikin abokan karatun nata. Jibtaka tamkar ta fasa zuwa makarantar, amma idan ta fasa tasan se a tambayi ba'asin hakan, dan haka jiki a sanyaye take aiwatar da shirin makarantar. Seda aka gama Assembly sannan ta shiga makarantar, ta wuce ajinsu tana sussunkuyar da kai, duk wanda suka je gurin tsirarun mutane ne, dan a 'yan ajinsu Lilly ce kawai taje se wasu daga 'yan ajinsu Sadik se Khairat, du du du ba su fi su goma ba, amma gaba ɗaya ta rasa sukuni. Sadik na shiga ajinsu suka hau yi masa ihu da shewa. Be kula su ba yaje ya nemi guri ya zauna a mazauninsa, Nas da Amin sukaje suka zauna kusa da shi, Nas yace "Mazaa, ya ake ciki ne? Munyi ta kiran wayarka ba ta shiga, kuma ka barmu a gurin partyn ba ka dawo ba, ya kaji abun?" Sadik ya ɗago idanunsa ya kalli Nas, kallon da Nas ɗin ya kasa tantance kallon meye. Amin yace "wallahi you did it in the most passionate way, naji haushi da ka hana ɗaukar hotuna ku bada kala fa" Nas yace "ai mun tabattar da namiji ne yanzu, yanzu zaka fara soyayyar morewa ba irin wadda kake yi ba da, ta ƙauyanci, nasan ko yanzu ka samu chance you want do it again ko ba haka ba?" "Shut up!" Sadik ya faɗa da ƙarfi yana dukan benci. "Dan Allah ku ƙyaleni inji fa abunda ya dameni, ku tashi ku ban guri" Binsa su kai da kallon mamaki, meke damunsa hakane? Kasa jurewa yayi, ya tashi ya nufi ajinsu Farhan amma ya tarar Madam Joy na ciki na musu lesson dan haka ya koma ajinsu. Bayan fitar Madam Joy, Lilly taje in da Farhan ke zama ta zauna a kusa da ita tace "mutuniyar ya gajiyar taro?" Wata ƙwalla ce ta zowa Farhan, da tuna a gaban Lilly Sadik yai kissing ɗinta, ta san maybe Zuwa yanzu duk ta gama bawa 'yan ajin labari. Lilly tace "yana ga kamar zaki kuka? Meyafaru?" Aikuwa maganar Lillyn tasa hawayen da Farhan ke maƙalewa ya gangaro kan kuncinta. "Yasalam, Farhan menene?" Cikin kuka Farhan tace "bakomai" "Bakomai amma kike kuka?" Farhan ta jinjina mata kai. Lilly tace "anyway shikenan, bari in ƙyaleki kar in takura miki" Har Lilly ta miƙe Farhan ta riƙo hannunta, ta dawo ta zauna tace "ya akayi?" "Fatima dan Allah kin gayawa wani abunda ya faru agurin nan?" Lilly ta riƙe hannun Farhan tace "i understand you ƙawata, karki damu ni ba wanda na gaywa, ni ba haka nake ba, and is something common in this school, no one will cares, amma duk da haka ni ban gayawa kowa ba, in abunda ya saki kuka kenan ki kwantar da hankalinki" Farhan ta jinjina kai tace "Nagode sosai" "Bakomai karki damu" Ana haka, aka kaɗa jiniyar fita break, Lilly ba ta jira kowa ba ta ɗau littafinta, da kayan ciye ciyenta ta tafi ofishin malam Nazir, fan wata irin ƙishirwar ganinsa ke damunta, tun incident ɗin nan da yafaru, idan har bata sa shi a idonta ba, ba ta jin daɗi. Kan tai sallama yaji ƙamshin turaren ta "Assalam Alaikum" tai Sallama. Be ɗago ya kalleta ba ya amsa. "Good morning Sir" "Morning how are you?" "Fine Alhamdilillah" Ta ja kujerar da ta saba zama ta zauna, ta fara ƙoƙarin kwafar note ɗin ta, so take ko sau ɗaya su haɗa ido, amma yaƙi kallonta aikinsa kawai yake, wanda seda hakan ya ɗan bata haushi. Sir Nazir kam yana sane yaƙi kallonta, saboda ya kasa gane kansa akan 'yar ƙaramar yarinyar nan. Yayi rayuwar University cikin manya manyan 'yan manta, yai yawace ywacensa, amma be taɓa cin karo da wadda yake jin wannan bugun zuciyar akanta ba se wannan yarinyar me shegen iyayin tsiya. Yayi mata kyau sosai, ji take tamkar ta gaya masa yayi kyau, amma tai shiri da bakinta tana tunanin me za tai wanda zesa ya kulata? Can tai gyaran murya, tare da miƙa hannunta kusa da inda hannunsa yake ta ɗau biro. Ɗagowa yai suka haɗa ido, ta ɗanyi luuu da nata idanun cikin wata irin murya tace masa "Nawa biron ya tsaya, shine na ɗauka aron naka" A hankali ya jane idonsa daga nata, ya cigaba da abunda yake yi. Wayarsa ce ta fara ringing, ya kalli wayar sannan yasa hannu ya ɗauka ya kai kunnensa. "Assalam Alaikum" yai Sallama. Lilly ba ta iya jiyo me ake cewa a wayar amma taji yace "like serious, congratulations my dear, am missing you, very soon zan shigo nima insha Allah" Ya ɗanyi shiru Sannan yace "yadda kike so, idan ta idar ki bata wayar in kwashi gaisuwa" Tunda ya fara wayar Lilly ta ƙura masa ido harya ƙare, gaba ɗaya Annurin fuskar ta ya ɗauke bata san lokacin da tace "Sir fa wa kake waya?" "Da ƙaniyarki" ya bata amsa. Sunkuyar da kai tayi ta cigaba da rubutunta, haka nan taji haushi ya kamata. Mintuna kaɗan aka sake kiransa ya kuma ɗagawa, cikin wata nustuwa da girmamawa yace "Ina kwana Umma, duk kuna lafiya, ai insha Allah na kusa shigowa, Auta tace min ba ta da carryover a exam ɗinta, baki yaƙi rufuwa" Murmushnsa ya faɗaɗa yana shafar gashin kansa yana wayar, wata nustuwa Lilly taji da ta fuskanci da 'yan gidansu yake waya. Babban abunda ya bata mamaki da kusan dariya be wuce yadda yakewa Mamansa shagwaɓa a wayar ba, se taji ya wani ƙara burgeta sosai da sosai, ta dinga kallon sa tana murmushi. Yana Ajiye wayar ta kalle shi tace "Sir is she your Mum?" Ya jinjina mata kai alanar eh. Tai murmushi tace "Amma Babba da kai kake shagwaɓa" Murmushi ne ya ƙwace masa ya shafi gemunsa yace "Ai su iyaye ba a girma a gurinsu" "Eh hakane, amma kai kayi girma da shagwaɓa" Yace "Allah ko?" "Eh mana, ai mata ne kawai suke shagwaɓa" Murmushi yai ya cigaba da dannan System. "Sir kana da ƙanne mata ne?" "Eh ina da ƙanne mana, shiyasa bana don inga kuna rashin ji, idan na tuna da ƙanne na, bana jin daɗin ganinku kuja rashin ji, sedai ku kuma ba kwa son ace muku bari" "Sir ba haka bane ba fa?" "To yane Fati, ke kanki na san kina jin haushi na saboda hukunta ki da nayi ko?" Lilly ba zata iya misalta farin cikin da ta shiga ba, kasancewar Sir Nazir yana mata Magana cikin nutsuwa ba hargowa da zare ido. Ta ɗago idonta ta kalleshi, ta ga shima kallonta yake, ga wani cikar zati da kwarjini da ya sake yi masa ado. A hankali ta sauke ajiyar zuciya, a ranta tace "ohhh God" ta fara tunanin ko ba duka ba za'a samu Sir Nazir da Mafi rinjayen siffofi da ake kamanta mazan littafi da shi, ba abunda yake tsole mata ido irin sajensa da wannan faffaɗan ƙirjin da yake da shi, she wish to hugs him even once, ta shafa wannan sajensa kamar yadda take karantawa a littafi. "Fatima ya kira sunanta" "Wani irin ɗagowa tai da idanunta, wanda sukai mata nauyi saboda jinta da take a gajimare, sheɗan na ta buga mata gangarsa a kwanyarta. Kallon da tai masa ne yasa jin jikinsa yai wani irin sanyi, yaji gumi na karyo masa. Kuma ta tsatsare shi da idanunta taƙi ɗaukewa. Jin halin da yake shirin shiga ne yasa ya aro jarumta, ya haɗe rai yace "concentrate on what you are doing" A hankali ta janye idanunta ta cigaba da note ɗin, amma lokaci lokaci idan ya ɗago ido se su haɗa ido tana masa wani irin shu'umin kallo da be san dame ze fassara kallon ba. (Ƙalubale gareku iyaye da malamai, Annabi Sallallahu alaihi Wasallam ya hana keɓancewa da mace wadda ba muharramarka ba, a yanzu muharraman ma se ana sa ido sosai, saboda muna zamani ne computer age, wannan kallace kallacen fina finan wanda ya dace da wanda be dace dui matasan mu kallo suke, ga uwa uba litattafai wanda wasu suke taka muhimmiyar rawa, gurin gurɓata tunanin Young adults ɗin mu. Sannan mace duk in da take komai girmanta ko ƙanƙartarta duk girmanka duk ƙanƙantarka zata iya jefaka a bala'i, 'ya mace tana da hatsarin gaske, Allah yasa mu dace" Farhan tai zuruu da ido, kamar agola a rabon gado, gaba ɗaya ta kasa sakewa. Gefe ga su Haseen suna ta karatun littafin su, da fari hankalinta baya kansu, tayi zurfi a cikin tunani, sedai jefi jefi kunnuwanta na ɗaukar wasu abubuwan. Tana nan zaune aka tashi, kowa ya bar ajin amma ita tana zaune ba ta tashi ba. "Farhan" taji muryar Sadik ta daki dodon kunnenta. Haɗe rai tayi sosai ta ƙi kallonsa. Matsawa yai kusa da Ita, tai saurin matsawa daga in da yake. "Farhan meyasa kike guduna kuma? Fushin kike dani haryanzu?" "Dan Allah ni ka ƙyaleni" "Bazan iya ba Farhan, dan Allah kiyi haƙuri" "Dan Allah ka ƙyaleni" "Kema kin san ba abune me yuwuwa ba, tsautsayi ne baze sake faruwa ba insha Allah, ki tashi mu tafi gida Please kiyi haƙuri" "Bazan haƙurin ba, kawai kasa nayi abunda ban taɓa yi ba" "Nima ban taɓa yi ba, amma ai nace ba zan sake ba" Tsaki tai masa ta ɗakko jakarta, ta raɓa shi zata wuce. Riƙota yayi ya haɗata a bango yana kallonta, kamar yadda yaga anayi a Bollywood 🙄🙄🙄. "Farhan nike baki haƙuri kina min wulaƙanci, nasan nayi miki laifi but am sorry, dan Allah kiyi haƙuri" ya ƙarasa maganar a sanyaye. Kawai idanunta suka fara zubar da hawaye. Hannu ya kai ze share mata hawayen, amma ta riƙe hannunsa. "Shikenan na gane ba zan taɓaki ba, zo mu tafi" "Ni ba zan bika ba" "Baki haƙura ba kenan?" Ya tambayeta a marairaice. Gaba ɗaya ta rasa dalilin da yasa ta kasa jin haushin Sadik, yadda yake marairaicewa ne yasa wani irin tausayinsa ya shige ta, kuma tasan idan ta dena kulashi, bata da wanda zata cigaba da raɓarsa tana jin daɗi, babu wanda zata dinga raha da shi tana jin daɗi. Yasa hannu ya karɓi jakarta, yace "muje ko" Tabi bayansa suka fito, a harabar in da ake parking ɗin motoci, suka haɗu da Mubarak Babba, ya kalli Farhan yana wani kashe ido yace "A'a yarinya ta zama 'yar hannu, delay ɗin na meye haka baku fito ba, ko dai ana tisa wancan karatun ne da a kai ran Friday". A take Farhan taji wasu hawayen na silalowa daga idanunta. Sadik ya kalli Babba yace "Mubarak, ka sanni na sanka, ni da kai kar ta san kar ne, ko da wasa ba ruwanka dani da kuma Farhan, abunda ya faru ma tsautsayi ne, kar ka kuma na gaya maka" Mubark yace "hmm to shikenan, na dena" Yaja Farhan suka shiga mota suka tafi. Seda suka kaita har inda take sauka Sannan Sadik yace "dan Allah ina ƙara baki haƙuri Farhan, kiyi haƙuri" Ba tace Komai ba, tasa hannu zata buɗe motar ta fita. Ya kuma riƙo hannunta, ta waigo ta kalleshi yace "baki cemin kin haƙura ba" "Bakomai ya wuce" tai maganar tare da zare hannunta ta fice. Shikam direba a ransa yace "Allah yasa yaron nan ba wata watsewar sukai da Yarinyar nan ba, naji yana bata haƙuri. Sam Farhan ba taji wani abu ya ragu game da son da takewa Sadik ba, sema wani ƙara jinsa da take a ranta. Idan ta kwanta bacci ba abunda yake yawo a ƙwaƙwalwarta se tunanin Sadik ɗin. Tana cikin tunanin Ba tsammani taji wani irin yanayi yana bijiro mata, wanda ba ta san menene ba balle ta tantance baƙon yanayin da ke ji a jikinta! Faɗin cakwakiyar da ke cikin littafin nan ba ta faɗuwa, hanzarta zuwa AREWABOOKS dan samun naku. Or subscribe it at affordable price of ₦300 only. (Saura acemin mara kunya, labarin ne yazo a haka🙄) Mum Amnash ina godiya da sharhinki da kuma shawara, Nagode Allah ya bar zumunci 🙏 Domin gyara Sharhi ko shawara 07063065680. Downloaded from GNOVELS.COM.NG This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG For feedback and support Facebook : https://facebook.com/gnovels Twitter : https://twitter.com/gnovels Telegram : https://t.me/gnovels