Downloaded from GNOVELS.COM.NG This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG For feedback and support Facebook : https://facebook.com/gnovels Twitter : https://twitter.com/gnovels Telegram : https://t.me/gnovels [8/30/2022, 1:08 PM] Abk: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 🎄RAINON DAWA🎄 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free page 1/2 Bismillahir rahmanir Rahim. Ina farawa da sunan Allah,mai kowa mai komai,wanda ya bani ikon kammala littafin MACIJE NE lafiya,sannan yanzu na fara sabon book dina,RAINO DAWA.ina fatan Allah yasa yadda na fara lafiya ingama lafiya. Wannan littafin mallakina ne,banyarda wani ko wata ya juyamin shi ta ko wacce sigaba,saida izinina.dan haka akiyaye. Sannan ga masu bukatar biyan kudin wannan littafin zaku biya kamar haka. Normal group 300₦ Update biyar a sati. Special group 500₦ update bakwai asati, kuma zaku iya samun update biyu arana. Sannan akwai manyan mata,wadanda ke bukatar atura musu private,Ina sane daku hajiyoyina. Zaku biya 1000₦ Duka zaku turo kudinku ta wannan acc. Din. Saratu Kabir. U.b.a 2215749011. Saina jiku masoyana na Amana Ina sane daku. _____________Dajine mai cike da tarin bishiyu,dogaye masu yawan gaske,hakan yasa ta wani bangaren na dajin yake da duhu da sarkakiya,wani gurin kuma zaka ganshi akwai wadatar haske. Dajin yana da matukar girma,wanda ke dauke da halittu kala-kala.baka jin komai sai sautin kukan tsuntseye kala daban -daban. Kasancewar yanayine na damuna,hakan yasa dajin yayi lub-lub dashi,gaba ɗaya bishiyu dake cikin dajin sunyi ganye koraye shar dasu kwanin sha'awa. Wasu daga cikin ganyayyakin har ruwa zakaga yana diga daga jikinsu,alamun raba. Kai tsaye zamu iya cewa dajin yana da yanayi na ban tsoro,wanda bazaka taba tsammanin akwai wata halittar dan Adam dazata iya rayuwa cikinsa ba.saidai hakan bai hana dajin kyau da kawatuwa a idon duk wanda ya kalleshi ba. Akwai birrai da yawa cikin dajin,sannan ana tunanin akwai mugayen namun dawa dake rayuwa cikin dajin. Can gefe guda na hango wasu bishiyu kusan guda goma,acure guri ɗaya,kamar wanda aka hada kansu,suna da tsayi amma ba kamar sauran ba,da alama dai kamar yankesu akayi. Daga kaina nayi ɗan kallon iyakar tsayin bishiyun,saidai ga mamakina wata bukka na hango asaman bishiyun nan ɗonono,da alama kuma akwai mutum dake rayuwa cikin wanann bukkar. Dan kuwa kana iya hango abubuwa irinsu kwanuka,abin zuba ruwa,daga gefe kuma ga wani guri mai tudu wanda ke nuna alamun gurin kwanciyane. Daga can gefen bishiyun nan na hango wata yarinya tsugunne gaban wata yar korama dake dauke da ruwa mai kyau da haske,gefenta kuma zagaye da yan kananan shuke shuke,yarinyar ta juya bayanta,kuma ba kaya ajikinta,dan daga ita sai wani dan karamin towel data ɗaura shi asaman ƙirjinta,da alama dai wanka take,dan kuwa ruwa take diba tana watsawa ajikinta. Ahankali yarinyar ta mike tsaye tare da tattare uban gashin daya zubo gadon bayanta ta nannadeshi kamar gammo. sannan ta janyo wani dan zani ta daure kan nata dashi.juyowa tayi ta fara tafiya cike da kuzari atare da ita. Ta nufi jikin bishiyar nan. Masha Allah !!!shine abinda bakina ya iya faɗa,sakamakon arba da kyakykyawar fuskar yarinyar da akalla shekarunta zasu kai sha takwas,doguwace mai matsakaici jiki,bazamu iya kiranta da Siriya ba,sannan bazamu ce mata mai jiki ba kai tsaye.tana da kira mai kyau da ɗaukar hankali, daga kasanta abaje take sosai,tana da hips,sannan tana da albarkatun kirji,jikinta shar shar yake,ita ba bakaba kuma ba fara ba,irin choculate colour ɗin nance. Tana da rawn face,dauke da madaidaicin hanci mai kyau,idanunta dara dara ne farare tass dasu,bakinta dan karami,mai dauke da pink lips,ataƙaice dai zamu iya cewa kyakykyawar yarinyace ta gani afada. Hankali kwance take takawa cikin ɗan sauri ta nufi saman bishiyar nan, abin mamaki tana zuwa naga ta kama bishiyar cikin wani irin salo da kwarewa ta fara hayewa kamar wata biranya.kawai kama jikin bishiyar take tana ɗan tsalle sai kaga tayi sama. Cikin abinda bai wuce dakika biyar ba naga ta haye saman bishiyar nan. Zama tayi tare da janyo wani abu mai kama da akwati,saidai kuma da itace akayishi. Budewa tayi tare da ɗauko wani irin kaya masu kama da fatar damisa ta sanya ajikinta.riga ce doguwa,wacce duka duka bata wuce iyakar gwaurinta ba.sai wani wando irin skin tite dinnan shima iya gwuiwa,gashinta ta ware tare da ɗauko wani mataji mai ƙarfi dan da alama da katako akayi shi. Taje kan tayi sannan ta rabashi gida biyu ta daure.bayan ta kammala daure kan nata,saita dauko wani ƙaton zani ta lulluɓa ajikinta,ga mamakina saina ga ta tada sallah,saidai kuma haka tayi sallar nan gwauri a waje,kuma akwai kurakurai sosai cikin sallar.tana idarwa ta cire zanin sannan ta dauko wata ƙatuwar kwari da baka ta rataya awuyanta, sannan ta dauki wata yar karamar wuka,ta soke jikin rigarta,inda ta janyo wata jela jikin rigar ta daure ta abaya.kanta ba ko dan kwali haka ta kama bishiyar nan ta sauko kamar yadda ta hau. Tsayawa tayi tare da kallon gefen ta,kafin ta sanya hannu abakinta,harshen ta ta lankwasa sannna ta huri iska,nan take wani sauti mai kara ya fara fitowa daga bakin nata,kusan second biyar tana fidda wannan sautin, kafin ta dakata.saman wata bishiya naga tana kallo,fuskarta ɗauke da murmushi.cikin tsalle da gudu naga wani biri dan madaidaici yana sakkowa daga bishiyar.kai tsaye akafadunta yayi masauki bayan ya gama sakkowar. Dariya tayi tare da shafo jikinsa tace "janbu, zamu fita yau da wuri nake son muje mudawa,dan haka ka dage sosai yau kaji"ta fada cikin harshen Hausa tana shafa birin, Shikuwa birin wani dan ƙara yake yi,alamun yaji abinda ta fada kenan,kafin ya sauko daga kafaɗunta. Wani bakin abu mai kama da fata naga ta janyo daga jikin bishiyar da ta sauko,daurawa tayi akanta yayi kamar bandana,kafin ta fara tafiya,cikin azama birin yana Binta,suka nausa cikin dajin. Masu karatu ina zata da wannan kayan haka? Wacece wannan yarinyar. Muje zuwa . Anty mammy ce Mrs babi💘💘 Share as much as you can.fisabilillah. [8/31/2022, 10:47 AM] Abk: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 🎄🎄RAINON DAWA🎄🎄 Na mammy kabeer (Anty mammy) https://facebook.com/groups/943534712916776/ Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din👆🏽 Elegant online writers📚📚 Free page 3/4 Ga masu son karanta wannan littafi,zaku biya kamar haka. Normal group 300₦ Update biyar asati. Special group500₦ Update bakwai asati. Gareku manyan mata,masu so ta pc. 1000₦ Zaku turo kudin ku ta nan. Saratu kabir U.b.a 2215749011 Evidence of payment 08148360851. ______________Tafiya take cike da izza,sam ba wata alama dazata nuna maka cewar tana cikin yanayi na tsoro.domin kutsa kai kawai take cikin dajin,yayinda baka jin komai sai sautin kukan tsuntsaye da kwarina. Wannan birin da ta kira da jambu yana biye da ita,cikin dan gudunsa mai haɗe da tsalle. Suna cikin tafiyar ne,ta hango wasu zomaye guda biyu.da sauri ta dakata,tare da daga wa birin nan hannu, alamun shima ya dakata,aikuwa dakatawar yayi tare da kamewa guri ɗaya. Kwarinta ta dauko da baka,ta sanya kibiyar cikin bakar,sanan ta ɗameshi sosai ta saita daya daga cikin zomayen nan ta sakar masa kibiyar.aikuwa cikin sa'a kibiyar ta caku acikin wannan zomon, nan da nan zomon ya fadi yana burbuwa, yayin da guda ɗayan ya zura da mugun gudu,yayi cikin wani rami. Da gudu birin nan ya karasa gurin da zomon ke kwance yana burbuwa,daukowa yayi tare da dawowa gurin yarinyar.ita kuma yana zuwa ta karɓe zomon tare da yin Bismillah ta yanka wuyansa. Zomon katone sosai,dan haka suna kamashi tace da jambu cikin muryarta mai daɗin sauti"jambu mu koma gida kawai,wannan ma ya ishemu "tana faɗin haka ta juya cikin takunta mai cike da burgewa,kamar tarwaɗa haka jikinta ke rausayawa. Suna cikin tafiya ba zato ba tsammani wani ƙaton biri mai girma ya dira agabansu,birin baki ƙirin dashi,hakoransa jajaje, mai matukar muni. Da sauri jambu ya dare kan kafadarta yana ihu,da neman inda zai boye ajikinta. Ita kuwa cike da rashin tsoro ta ja ta tsaya,tare da kafe birin nan da ido,tana gyara tsayuwa. Wani ƙara birin yayi tare da girgiza,kafin ya nufota da gudu. Ja tayi da baya tare da zaro wukar data soke ajikinta itama ta nufi birin nan da gudu. Abin mamaki suna haduwa tayi tsalle tare da darewa bayan birin ta soka ma wukar nan akafaɗarsa. Wani ƙara birin ya sanya tare da yin wani juyi ya wurgar da ita can gefe. Faduwa tayi tare da buga kanta jikin wata bishiya,ƙara ta sanya tare da dafe goshinta wanda ya fashe, da gudu birin nan yayi kanta baki buɗe yana ihu shima. Saidai yana kusantowa gareta,wata irin bakar guguwa ta tashi,nan da nan gurin yayi duhu matuka,baka iya ganin komai sai karan birin nan dake tashi cikin guguwar nan,janbu ne ya garzayo gareta tare da tabata,yana ɗan kara,ganin har lokacin tana kwance dafe da kanta. Tashi tayi da sauri tana mai rungume janbu ajikinta,tare da zuba wa wannan guguwar ido,wacce ke kadawa aguri ɗaya tana ta juyi,yayinda karan birin nan ke kara tsananta cikin guguwar. Kusan minti biyu kafin guguwar ta lafa, sai kuma gurin yayi haske,can gefe suka hangi birin nan,cikin wani irin mugun yanayi,kwance yake gaba ɗaya jikinsa jini ke zuba. Tashi tayi tare da maida wukarta, tana bin wani farin haske da ido, sannan tayiwa janbu alamun su bar gurin. Cikin hanzari suka bargurin tare da komawa inda bukkarta take. Cikin salonta na kuzari ta haye saman bishiyar nan,tare da zama tana mai dafe kanta,dan kuwa ta bugu sosai. Janbu ne yazo jikinta yana kallonta tare da dan karansa. Kallonsa tayi kafin ta ɗanyi murmushi tace "karka damu janbu,ba wani zafi fa,zai warke,ka kwantar da hankalinka"ta fada tana shafa bayansa. Shikuma yana kara maƙalewa ajikinta. Kamar wacce akace ta duba gefenta, kawai tana juyawa taga wannan zomon da suka kamo dazu, ajiye kusa da ita. Sam batayi mamaki ba dan dama irin hakan tana faruwa,duk lokacin da wani abu yayi nufin cutar da ita,to wannan guguwa zatazo ta taimaketa, kuma bata taba barin Abunta awani gurin ba,kuma ta dawo makwancinta bataga abin nan ba.dan haka ta riga ta saba da irin hakan tun tasowarta cikin dajin nan. Murmushi ta sake yi akaro na biyu kafin tace "janbu kamar dai kullum yauma kaga zomon da muka bari agurin can, ankawo mana shi"ta fada tana janyo zomon gareta. Cikin kankanin lokaci ta fara gyara zomon nan da wukar da taje farauta, Ni dai bansan inda ta samo wuta ba,kawai naga wuta tana ci daga gefenta.murmushi naga tayi kafin taci gaba da aikinta, cike da rashin tsoro ko fargaba.haka ta gama hada naman nan taci wanda zata ci,ita da janbunta, sannan ta kwanta.kwanciyarta kenan barci yayi gaba da ita,yayinda janbu ma kwanta kusa da ita. Iskace mai sanyi ta fara kadawa cikin dakin na tsawon minti biyu,kafin wani haske ya bayyana gefen da yarinyar ke kwance.ahankali hasken ya rikiɗe ya koma wani kyakykyawan saurayi,fari mai matukar kyan idanu,kallon yarinyar fuskarsa ɗauke da murmushi,kafin ya buɗe rafin hannunsa,saiga wani dan karamin abu mai haske ya bayyana cikin hannun nasa,budewa yayi tare da lakuto wani jan abu adam yatsanshi,agishin yarinyar ya fara shafawa ahankali yana kallonta. Gama shafawarsa keda wuya,gurin ya koma yadda yake ba ciwon,kamar ma bata taɓa jin wani ciwoba. Haka wannan saurayin ya mike bayan ya gama shafa mata maganin,sannan ya zama farin haske yayi waje. Wannan kenan. Abuja birnin tarayya. Da misalin ƙarfe uku na rana,cikin anguwar maitama, wani rantsatstsen gida na hango,mai matukar kyau da ɗaukar hankali, kaida ganin gidan kasan cewa,ko cikin masu kudin ma,to ba kowaba.dan tsayawa fadar kyan da gidan kedashi ma bata lokacine. Kai tsaye na kutsa kaina cikin gidan domin dauko maku rahoto. Wata hamshaƙiyar Hajiya na hango,zaune kan daya daga cikin rantsatstsun kujerun da sukayiwa falon ƙawanya,tana zaune da waya akunnenta,cikin wata hadaɗɗiyar kwalliya mai cike da kyau da tsari,irin ta manyan mata masu ji da gayu dakuma Naira. Fara ce, amma ba irin can ɗin nan ba, kyakykyawar mace mai cikar haiba da zati,waya take, cike da nishadi,tana faɗin"yanzu Aslam ka kammala karatun ka,tun last week,Amma kaki dawowa gida,me yasa kake son zama cikin masu jan kunnen nan ne?ga kakarka nan kullum zancen ta daƴa Aslam. Gaskiya ya kamata ka dawo gida, muma muna bukatar ka kusa damu"ta kai ƙarshen zancen ta cike da nuna zallar son ganin wanda take wayar dashi. Daga can daya bangaren,naji wata murya mai cike da izza,wanda kana jin muryar nan kasan ma'abocinta zaiyi son girma da rashin don raini. "Ki kwantar da hankalinki,mommy zan dawo very soon,akwai Abinda Ya tsayar dani anan din amma dana kammala I will be back home soon kinji mommyna"ya ƙarasa cikin sigar rarrashi. Ajiyar zuciya matar tayi kafin tace "shikenan Aslam,Allah ya dawo da kai gida lafiya,kannanka ma suna kewarka sosai"ta fada tana canza tasha da remot din dake hannunta. Murmushi yayi kafin yace "ki sanar dasu,nakusa dawowa,saidai ina nan kamar yadda suka Sanni,dan haka saisu kula su nutsu,dan ba sassauci ga wanda yayi ba daidai ba"ya faɗa cike da salonsa na son girma. "Ai sun sani,Bama saina ƙara faɗa musuba, yaran da idan kana guri ko ƙwaƙwƙwaran motsi basa iyayi,basu ba ma, hatta Aman baya wargi idan kana guri"ta faɗa cike da son tunasar dashi,ƙannan nashi fa basu manta halinsa ba. Murmushi yayi yana kada kafa, haka yake so,ace duk iskancin mutum to yaji tsoron Aslam,Dan Aslam yana son raini ko kaɗan.sun jima suna hira ta waya da mahaifiyarsa,cike da nuna kulawa da kauna, har saida taji tsayuwar motar mijinta kafin sukayi sallama ta kashe wayar. "Alhaji yanzu goben zaka tafi can Niger ɗin, Kenan?"mommy ta fada,bayan mijin nata ya fito daga wanka,tana zaune abakin gado. "Ina sha Allahu Madam,gobe zan tafi,akwai bukatar zuwana Niger gobe,saboda in duba abubuwa yadda suke tafiya acan,kinga shi Aman makaranta yake zuwa,dama da ace Aslam ya dawo ne to shi zan tura,amma tunda baya nan dole in je da kaina"ya faɗa yana goge kansa da towel. "Shikenan, Allah ya kaimu,Amma dai ya kamata Ku tafi tare da Aman tunda kace amota zaka tafi,dan nikam ina tsoron wannan dajin dake tsaninmu da nijer,dan ance akwai abubuwan cutarwa cikin dajin"ta fada cike da nuna fargaba. Murmushi Alhaji yayi,kafin yace "banda abinki ai komai nufin Allah ne,duk abinda ya faru da mutum dama can Allah ya nufa,dan haka karki damu,zamu tafi tare da Aman ɗin,tunda gobe week end ne"ya faɗa lokacin da yake sanya kayansa. Murmushi Mommy tayi kafin tace "Allah ya tsare hanya Alhaji" "Ameen yace kafin ta zuba masa abinci yafara ci. Misalin ƙarfe biyar yaran sukan dawo gida.cike da tabara suka shigo falon, Cikin sakalci jannat ke kiran "Mommy mun dawo,wllh na gaji "ta fada tana jefar da jakarta aƙasan falon. Hanan ma cike da sakalci ta jefar da jakarta tana zama ragwab akan kujera"wash Mommy ruwa zansha"ta fada tana turo baki tare da jingina kanta jikin kujera. Mommy kuwa saukowarta kenan daga ɗakin ta,tajiyo hayaniyar yan shagwabar ta ta,girgiza kai tayi tana zama akan kujera kafin tace"nikam zanga randa zaku girma wllh,sakalcinku yayi yawa,yanzu duba kigani jannat anan kika jefar da school bag din ki,kuma bazaki daukeba, sai dai adauke miki. Ke kuma wai ruwa zaki sha,gaki ga fridge Amma jira kike adebo miki Kisha,Gaskiya lamarinku sai du'ai wllh"Mommy ta fada cike da jin takaicin sakalcin yaran nata. Turo baki jannat wacce ataƙaice zata kau shekara kusan ashirin aduniya tayi,kafin yace "haba Mommy ɗaga dawowarmy,zaki fara mana faɗa,shiyasa wllh nake son Daddy ba ruwansa da faɗa"ta fada tana barin gurin ba tare da ta dauki jakarba. Hanan ma tashi tayi tana kwalawa mai aikinsu kira"ramatu, maza ki kawomin ruwa dakina, bana son mai zafi "ta fada tana wajewa sama ita. Girgiza kai Mommy tayi kafin tace "Allah ya shirya minku" Aman ne ya shigo dakin da sallamarsa,yana kada keys ɗin mota,zama yayi kusa da Mommy yana faɗin"ji Mom ya gida" Murmushi tayi tare da shafa kan Aman tace "Aman ka dawo ?sannu"ta fada cikin murmushi. "Na dawo mom inna granny ?ko bata dawo ba"ya faɗa yana duba wayarsa. "Kasan ai bazata dawo ba,har sai kaje ka daukota,wai batason tuƙin driver bashi da sauri"ta fada tana dariya. Dariya shima Anan yayi kafin yace "granny case,Bari naje na daukota,Dan gidan baya dadi idan bata nan wllh"ya faɗa yana mikewa cike da nishadi yayi waje ... Wannan kenan. Masu karatu muje zuwa ,sannu kan hankali,zaku nishadantu,kudin👆🏽 a'azantu cikin wanna littafi. Bamu fara komai ba. Mene babi💘💘 Share as much as you can.fisabilillah. [9/1/2022, 10:53 AM] Abk: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 🎄🎄RAINON DAWA🎄🎄 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 https://facebook.com/groups/943534712916776/ Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din Free page 5/6 Ga masu son biyan kudin wannan littafin,zaku biya kamar haka. Normal group 300₦ Update biyar asati. Special group 500₦ Update bakwai,asati. Manyan mata masu son shi ta pc 1000₦ Zaku tura ta wannan acc.ɗin. Saratu kabir U.b.a 2215749011 Evidence of payment 08148360851. Saina jiku. ______________"Bari naje na dauko ta yanzu,dan gidan baya daɗi,idan bata nan.Aman ya faɗa tare da miƙewa,cike da nishaɗi yayi waje. Murmushi mommy tayi,dan tasan kiricin surukar Tata,idan tana guri,zaka sha dariya sosai.jannat ce ke saukowa daga matakalar benen, sanye take cikin wata riga mai yankakken hannu,wanda duka rigar Baza wuce gwuiwarta ba.kanta ko ɗan kwali babu,zama tayi kusa da mommy tana faɗin "mommy wai Ina granny?kodai bata nan ne?dan naji gidan shiru gwanin daɗi"ta faɗa tana lumshe ido. Hararar ta mommy tayi kafin tace"yanzu jannat dan grannyn bata nan, shine kikaji gidan yayi miki daɗi Ko?to ki kwantar da hankalinki,yanzun nan zata dawo "ta faɗa tana ci gaba da hararar jannat. Turo baki jannat tayi kafin tace"Ni wllh matar nan,takura Ni take agidan nan,yanzu zata fara kawo ma shirme kala-kala saikac... "Jannat, bana son rashin kunya fa!granny kike fadawa wannan maganar?wllh ki kiyaye Ni"Mommy ta fa ɗa, cikin faɗa. Shiru jannat tayi taci gaba da danna wayar ta. Tana turo baki,dan tasan halin Mommy yanzu saita ɓata mata rai,akan wannan tsohuwar. Aman ne ya shigo cikin falon,yana dariya.guri ya samu ya zauna tare da kafe ƙofar shigowa falon da ido. "Kai kuma lafiyar ka?ka shigo bako sallama kana dariya?ina grannyn take?kodai halin naka kayi mata?"Mommy ta fada tana kallon yadda Aman ke dariya. Kafin yayi magana akan buɗe ƙofar falon,garamm!!! Wata yar duma-dumar tsohuwa ce ta shigo cikin falon tana sababi"wllh Amanu akwai dan tijarar yaro, mutum sai ɓakar zuciya ta mugunta,yanzu daka rinƙa wujijjigani cikin wannan motar,so kayi ka kasheni, kai kuma ka zauna a duniyar kana ci gaba da jin daɗin ka ko?to wllh ta Allah ba takaba,dan bangama cin kaji da shan iyiskirin ba,kuma wllh zaka hadu dani"granny ke wannan maganar tana rike da kanta,dake juyawa.da sauri ta nemi guri ta zauna, dan Aman daya daukota amotar gudu yayi tayi da ita yana zagaye garin ,tsohuwace wacce zata kai kusan shekaru saba'in aduniya.saidai yanayin hutu da jin daɗi yasa tana nan garau da ita.taci adonta harda daurin dan kwali,ga wata uwar jaka saƙale ahannunta,da alama dai yar wankace. Banda dariya ba abinda Aman keyi.cike da ƙoƙarin danne dariyarta Mommy tace "subhanallah granny me ya faru kuma?" Cikin masifa granny tace "to ƴan sa ido,ina ruwanki?ko shishshigi?wllh bana son ana shiga tsakanina da Amanu,dan munfi kusa,bana son gulma"ta fada tana juyowa Mommy ƙeya. Shiru Mommy tayi,dan tasan dama za'ayi hakan.duk irin tsiyar da Aman zaiyiwa granny,da kayi magana zata gwasale ka. Jannat dai tana zaune bata ce komai ba,juyowa granny tayi ta kalleta cike da yatsina tace "to uwar mulki,bazakiyi min sannu da zuwa bama?saboda kin riƙa ko?"ta fada tana kallon jannat aɗage. Harararta jannat tayi kafin ta miƙa tsaye tace "banda lokacin ki granny bazaki samin ciwon kai ba"tana faɗin haka tayi wucewarta zuwa ɗakinta. "To tabbatacciya, ai idan bakiyi haka ba,ba za'ace miki marar mutunci ba,wllh idan kikayi wasa,zan zage mu dambatu dake agidan nan,dan ni da kikagani banyi ƙuruciyar tsoro ba,bare kice tsoronki nake ji, tass zan mutstsike miki wanna yan ƙirgan dangin da suke saki rashin mutunci" granny ta faɗa cike da masifa harda daure ƙugu da gyalen ta,alamun ta shiryawa danben. Dariya sosai Aman keyi yana kallon dramar granny da jannat,sam dama basa shiri atsakaninsu.har Gara ma Hanan, da yake ita tana da ɗan tsoro. Ganin granny ta zage sai masifa take,yasa Aman mikewa ta kamo hannunta yana cewa"haba matar,kiyi haƙuri mana,ki bar waccan blegger girl ɗin,karki biyeta ki ɓata wannan wankan naki,wllh baki ganki ba kamar wata minister"ya ƙarasa maganarsa cike da sigar kanbamawa. Dariya granny tayi tana kai masa dundu"ja'irin yaro,ai In faɗa maka lokacin da nayi yan matanci na,karkaso kaga irin samarin dake sona,dan kuwa ɗan gidan marigayi Malam jafaru mai jaki, idan ya ganni,har faduwa yake dan kallona, saboda yadda nake cin ado.ba budurwar da takaini awancan lokacin, inada shekara sha daya,amma haka nake kamar sarauniyar kyau"ta kai ƙarshen zancen ta cike da nishadi tana kallon Aman. Dariya Aman yayi yace "wai kice kinsha hawa kan jaki?lallai yan matan da kunfi na yanzu matsayi,harna haskoki akan jaki sarauniyar kyau"ya faɗa yana ƙara fashewa da dariya. Ganin irin dariyar da Aman keyi harda ta rainin hankali ne,yasa granny tsuke fuska tare da ƙanƙance ido tace "kai Amanu bana son tashanci fa,meye na wannan dariyar kamar wani mahaukaci? Bayan kasan akwai yan sa ido agurin,wllh idan ka ƙular dani,yanzu zan zage kaima mu dambatu da kai,kasan ba tsoronka nakeba ehe"cewar granny tana buga hannu acinya. Mommy dai na gefe tana ta ƙoƙarin danne dariyarta,dan gudun kartayi laifi,bakuma damar yin magana ,yanzu cibi yazama ƙari,dan haka tayi shiru abinta tana kallonsu,tare da yin dariya ƙasa ƙasa. "Kinga granny taho mutafi dakinki,muyi hirarmu acan ai dani dake bata baci,kinga mun huta da masu son jin kwakwafɗin"Aman ya faɗa yana kamo hannunta,tare da kallon Mommy Yana dariya. Girgiza kai kawai Mommy tayi,cikin dariya ganin yadda suka wani tafa da granny sannan suka wuce dakinta dake cikin falon. Ba jimawa hanan ta fito,kwanciya tayi akan cinyar Mommy sukaci gaba da hira. Ƙasar London,misalin ƙarfe hudu da rabi na yamma, Wani kyakykyawan matashine kwance kan wani lafiyayyen gado,wanda yake da matukar girma,daga shi sai boxers ajikinsa, dogone sosai, yana da faffaɗan ƙirji, dan ga dukkan alama irin mutanen nan ne masu motsa jiki,duba da yadda jikin nashi yake amummurɗe. Bakine amma ba irin can ɗin nan ba,fuskarsa mai cike da kwarjini da tarin haiba,yana da manyan idanu masu haske,da dogon hanci,bakinsa madaidaicine zagaye da gashin baki har zuwa gemunsa.lips dinsa jane mai duhu.atakaice zamu iya cewa kyakykyawa ne,mai kirar jaruman maza. Gefensa kuma wata kyakykyawar baturiya ce kwance tana barci,ba komai ajikinta,sai bargon dake lulluɓe da rabin jikinta.tayi matashi da damtsen hannun saurayin. Wayarsa ce tayi ƙara,hakan ya katse masa barcin daya fara daukarsa, bayan sun gama aikata alfasharsu, Cike da yatsine fuska kamar wata mace ya daga wayar ya kara akunnensa ba tare da yayi magana ba. "I will be there "kawai ya faɗa tare da kashe wayar.kallon yarinyar yayi dake barcinta hankali kwance, kafin ya zare hannunsa ya tashi zaune.wanka yaje yayi ya shirya cikin wasu riga da wando red and white, yayi kyau sosai cikin kayan.turare kawai ya fesa sannan yazo kan yarinyar yana kiran sunanta"Jennifer! Jennifer!!"ya kira sunanta da karfi fuskarsa ahade. Ahankali Jennifer tayi juyi tare da kallon Aslam dake tsaye yana muzurai.cikin barikanci tace "hi my man "tana ƙoƙarin tashi zaune. "Maza ki tashi ki gyara min gida,kuma ki shirya yanzu kificemin daga gida ,zan fitane karna dawo na tarar dake" fa fi hakan cikin harshen turanci,yana faɗin haka ya jefa mata kudi masu yawa sannan yayi waje. Binsa tayi da kallo cike da so da ƙauna,tana fatan Allah yasa watarana Aslam,yayi sex na gaskiya da ita,lallai data more,dan duk iya shegensa,baya yarda yayi sex da mace,saidai suyi romance ko wane irine,har su sami biyan bukata.duk yadda kikakai da nacinki kuwa,kuma bazai hada baki dake wajen yin kiss ba,saidai yayi miki akumatu ko goshi.wannan shine tsarinsa.rigarsa ta janyo ta rungume kafin tayi murmushi,ta koma ta kwanta. Cikin dawa kuwa bayan yarinyar nan ta tashi daga barci,gurin ciwon ta, ta shafa taji gurin sumul ba alamun ciwo ko kaɗan,murmushi tayi tare da tashi ta kama bishiyar nan ta sauko. Haka kawai taji tana son ta yawata cikin dajin,dan haka kai tsaye ta fara takawa cikin salon tafiyarta mai cike da jan hankali. Tafiya take cike da rashin tsoro,tayi tafiya mai matukar nisa,kafin ta sami kan wani dutse ta zauna. Zamanta keda wuya taji alamun tafiyar mutane,shiru tayi tare da kasa kunne,dan gurin da take zaunen yayi kusa da wani kauye,kuma bata cika zuwa ta wajen ba. Sukuwa matasan nan yan farauta ne,su kusan hudu.suka shigo jejin dama sun saba zuwa,amma basu taba gigin shiga cikin dajin sosai ba. Kafin tayi wani yunkuri kawai ta gansu tsaye agabanta. Kallonsu tayi cike da rashin tsoro kafin itama ta mike tsaye. Kallon juna matasan sukayi,tare da sakin murmushi,dayan yace "baba yaufa dawa tayi mai,kai ga wani kaya fa?lallai yau zamu huta"ya fada yana kallon sauran. Daya daga cikinsu yace "ai wllh yau saina more sosai agurin nan,dan dagani itama fa kamar yar hannu,dan haka kawai bari kugani,Ni zan fara wllh"ya faɗa tare da tunkarar yarinyar. Ja tayi da baya tare da zaro wuƙarta, ta tsaya cikin shirin ko ta kwana.ganin hakan datayi,suka tuntsire da dariya,dan gani suke ba'abinda zata iya musu. Kai tsaye dayan nan ya tunkareta,tare da mika hannu da nufin kamota, saidai kawai yaji kett!an yankeshi abayan hannu. Ihu ya kurma cike da jin azaba yana kallon hannun nashi. Cikin mamaki suke kallon yarinyar,ransu aɓace suka nufeta dukansu, suna masu fidda wuƙake. Ja tayi cike da jarumtata dame tana jiran ƙarasowarsu. Aikuwa suna zuwa suka fara kai mata duka da wuƙake,ita kuma tana tarewacike da jarumta,ganin zata basu wahala ne yasa suka yi kanta gaba ɗaya.kasancewar Sarkin yawa yafi Sarkin ƙarfi,suka samu nasarar rirriƙeta,ihu take tana ƙoƙarin kwacewa, amma ta kasa,cikin sauri dayan ke ƙoƙarin cire wando,kafin yayo kanta. Wani irin kara ta kwalla,wanda saida dajin ya amsa kuwwa, nan da nan idanunta sukayi jaaa, suka fara fidda hawayen jini,kafin kace meye,tuni wani bakin hayaƙi ya lulluɓe dajin gaba daya. Baka iya hango komai,sai wani irin ƙara mai amo da tada hankali. Cikin lokaci ƙalilan ihun matasan nan ya fara tashi,cikin sauti mai ƙarfi,wanda kanajin sautin kasan maiyin ihun yana cikin azaba. Masu karatu muje zuwa kubini sannu kan hankali. Mrs babi ce 💘💘 Share and comment fisabilillah. [9/3/2022, 12:35 PM] Abk: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 🎄🎄RAINON DAWA🎄🎄 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 https://facebook.com/groups/943534712916776/ Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din Free page 7/8 GA MASU SON BIYAN KUDIN WANNAN LITTAFIN,ZAKU BIYA KAMAR HAKA. NORMAL GROUP 300₦ UPDATE BIYAR SATI. SPECIAL GROUP 500 ₦ UPDATE BAKWAI ASATI. TA WANNAN ACC. ƊIN SARATU KABIR U.B.A 2215749011 EVIDENCE OF PAYMENT 08148360851. _______________Wani irin baƙin hayaƙine mai tsananin duhu ya turnuƙe dajin,baka iya ganin koda tafin hannun ka. Ba abinda ke tashi cikin dajin,sai wani irin ƙara mai fidda amon sauti mai firgitarwa. Sai kuma ihun da matasan suka fara kwalawa ya biyo baya,tare da wani irin sauti mai kama da ƙaran bulala. Ji kake fau-fau-fau.ihu suke,cikin azaba suna neman taimako,amma ko ganin su bakayi bare kasan ta ina zaka kaimusu ɗauki,tun suna ihun da iya karfinsu suna neman taimakon,har karfinsu ya kare suka daina ihun. Kusan minti biyu da daina jiyo ƙaran ihun nasu,gurin ya fara haske,wannan baƙin hayaƙin ya fara yayewa yanayin sama. Taruwa yayi guri ɗaya asararin samaniya yana juyawa,kafin yayi cikin dajin da gudu. Matasan nan ne kwance cikin mawuyacin hali,gaba ɗaya jikinsu yayi burɗi -burɗi da sawun bulala,sunyi kwance sharkaf sai nishi suke. Sai kuma wani abun mamaki,sam ba yarinyar agurin,cikin tashin hankali suka ƙara bude idanunsu suna neman inda zasu ga yarinyar,amma bata ba alamarta.hakan ya tabbatar musu cewar aljana ce, dan haka da mugun gudu suka tashi da gyar sukayi hanyar kauyensu aguje suna ihu da kiran "aljana!aljana!!. Nan suka bar duk wani kayan barautar da suka shigo jejin dashi. Ita kuwa wannan yarinyar koda iskar nan ta turnuke gurun, can gefe ta mayar da yarinyar,sannan ta fara cin uban matasan nan,saida ta gama zana su kafin tayi gurin yarinyar dake kwance kamar me barci ta ɗauke ta sukayi sama.bata ajiye ta ko ina ba sai cikin bukkarta. Ahankali kuma iskar ta rikide ta koma wannan matashin daya shafa mata magani agurin da taji ciwon nan. Kallonta yake fuskarsa amugun hade,yayin da take wani sauyawa kala -kala,baƙi,jaa,kore. Idanunsa yayi jajur kamar wuta. Kusan minti uku yana tsaye akanta,kafin ya murza hannunsa,saiga wani farin hayaƙi ya fito daga hannun ya nufi jikin yarinyar ya shige ta kafar hancinta.dan motsi tayi kadan kafin taci gaba da barcinta. Washe gari kamar yadda Daddy ya tsara cewar zasu tafi Niger shida Aman, hakan ce ta kasance,bayan sun kammala shirinsu suka fito falo,inda gaba ɗaya ahalin gidan ke zaune. Sallama Daddy yayi dasu kafin suka rakosu har farfajiyar gidan,inda granny ke fadin"to gadai Aman nan,ka kula dashi,kasan yarone,gashi daga shi sai kai zakuyi tafiya,sannan akwai shi da tuƙi irin na yan tasha,wllh kayi masa gargaɗi sosai ya kula,Allah ya tsare hanya ya kaiku lafiya ya dawo daku lafiya"granny ta fada cikin yanayi na sanyin jiki. Dariya Hanan tayi kafin tace "kai granny,wato tukin motar ma harda na yan tasha"ta fada cikin dariya. "To yar nan duk wanda yake irin tuƙin da wannan ja'irin yaron keyi,ai wllh bashi da maraba da na yan tasha,jiya saura kadan na mayar da ya'yan hanjina"ta fada cikin darura. Dariya sukayi gaba dayansu harda jannat da basa shiri da granny,Dan yanayin da granny rayi maganar abun dariya . Murmushi Daddy yayi kafin yace "In Sha Allahu zamu kula uwata,bazan bari yayi mana tuƙin ganganci ba"ya kai zancen sa yana kallon granny,fuskarsa ɗauke da murmushi. "Allah yasa dan nan,dan wllh Amanu ja'irin yarone mai wasa da rai,shikuwa rannan riritashi ake,idan ya tafi shikenan"granny ta fada tana watsa hannu da taɓe baki" Dariya kawai suke cike da nishaɗin abin dariyar granny. Mommy kuwa cewa tayi"yanzu Alhaji sai nan da kwana ukun kenan? "Eh In Sha Allah,saboda aikin da yawa,zamu zagaya sosai,sannan akwai muhimman abubuwan da zanyi acan, amma bazamu wuce kwana uku ba in Sha Allah"ya faɗa yana kallon matar tashi cike da soyayya. Sallama sukayi dai anan suka shige mota,mutanen gidan natajin kewarsu. Har sun shiga motar Aman ya fito yazo kusa da granny yana mata rada"granny kinsan wannan irin tuƙin danayi dake jiya? To yau shizanyi da ɗan ki koma fiye dashi,tunda har wani cewa kika wai yayi min gargadi,wato dashi kadai kika damu ko hmmmmm"Aman ya faɗa yana gwafa,sannan yayi saurin shigewa motar ya tada jin granny na faɗin"wllh Amanu ta Allah ba takaba,dan bakin ciki,kuma kasani idan wani abu ya sami dana,wllh hukuma ce zata rabani dakai,hatsabibin yaro kawai"ta fada cikin salon ta na masifa. Aman kuwa kwalo yayi mata kafin ya fice daga gidan. Gaba daya jikin granny yayi sanyi Allah sarki harta fara jin kewar Aman ɗin, dan mutum ne shi mai barkwanci sosai. Kallonsu tayi kafin tace "to ai sai a koma cikin gida ko,dan kuwa wllh ba mai fita daga gidan nan,da sunan yawo,har uwar taku"ta fada tana hararsu jannat,tsaki jannat tayi cike da rashin kunya kafin ta shige cikin gida abinda. "Kinyiwa uwarki tsaki,kinganta nan,to ita kikayiwa tsaki,marar kunya mai kafar alwala"granny ta fada tana bin bayan jannat kamar zata kamota. Girgiza kai kawai Mommy tayi kafin suna suka shige cikin gidan. Tunda suka dauki hanya tafiya kawai suke, cikin tuki na tsinaki Aman ke jan motar,suna dan taba Shira da Daddy,sunyi nisa sosai kawai Aman ya fahimci kamar ana binsu abaya,nutsuwa yayi yana son fahimtar shin da gaske bin nasu ake ko yaya?dan haka saiya dan rage gudun da yake,aikuwa motar dake bayansu ma saita rage gudun,gabansa ne ya fadi lokacin daya karawa motar su gudu,yaga wannan motar ma ta Gara gudu,nan fa aka fara tsere akan titin,Daddy ne yaga irin gudun da Aman keyi,dan haka yace "Aman, wanann gudun kamar zamu bar duniya haka ?" Cikin tsoro Aman yace "Daddy binmu ake abaya,tunda muka taho"ya faɗa yana ƙara take motar,ganin waccan motar har ta kusa cinmusu Gaban Daddy ne ya fadi cikin firgici yace "subhanallah meke faruwa haka?su waye ke binmu da wannan gudun haka?me suke nema agaremu?ya fada cikin firgici yana kallon bayansa. Ba zato ba tsammani suka farajin harbi yana sauka akan motar,Allah ma yasa motar harsashi baya hudata, nan suka ƙara gigicewa,lokacin sun kawo daidai dajin da yarinyar nan ke ciki.tsabar tsoro sitiyarin motar ya kwacewa Aman,suka nausa cikin dajin. Salati Daddy yake cike da tashin hankalin ganin yadda motar ke katantanwa cikin dajin,saida suka yi nisa kafin motar taje ta daki wata bishiya kafin ta tsaya. Gaba daya su Daddy sun shiga yanayi mai matukar wahala,dan kuwa tuni jini ya wanke musu jiki,dan Aman kam ya suma,can gefe guda motar ta cillashi cikin sarkakiya. Da gyar Daddy ya iya zaro kansa cikin motar nan,yafito ya na kiran "Aman!Aman!!Amma baiga inda Aman ɗin yake ba.daga zaune yake jan jiki yana neman Aman, kawai sai ganin mutanen nan yayi tsaitsaye akansa,kusan su bakwai,ko wanne riƙe da bindiga ahannunsa.kuma fuskokinsu arufe ruf da baƙin kyalle. Cikin tashin hankali da azabar ciwukan da Daddy yaji yake faɗin "dan Allah kuyi hakuri,kuyimin rai,me nayi muku?me kuke bukata wajensa?" Dariya babban cikinsu yayi kafin yace "baka da bukatar sanin komu su waye,domin sanin bazai amfanar da kai komai ba,dan kuwa mutuwa zakayi,zamu kasheka ne,sannan mu ɗauki abinda muka biyo ka danshi,wannan shine aikinmu"yana faɗin haka ya saita cikin Daddy ya sakar masa bullet,Kara Daddy yayi kafin ya koma ya kwanta idanunsa suna rufewa da budewa,har suka rufe ruf. Ganin haka wadandan mutanen suka nufi inda motar Daddy take kwatsa-kwatsa,suka fara dube -dube.saidai sunyi iyakar dubansu amma basu ga abinda suke nema ba. Cikin fushi babban ya dauko waya ya kira wata number"oga babu wannan takardun da kace mana acikin motar nan fa"ya faɗa cikin salon murya irin ta yan daba. Bansan me akace masa daga ɗayan bangaren ba, naji yace "mun duba ko ina,babu sannan dan nasama bamu ganshi cikin motar ba, kuma gaskiya kasan wannan dajin yana da hadari,kawai ,zamu fito"yana faɗin haka ya kashe wayar tare da umartar yaransa su bar gurin. Lokacin da suka sakarwa Daddy bindiga,dai-dai lokacin yarinyar ta farka daga barcin da take,zabura tayi cikin sauri ta sauƙo daga saman dakin nata.bayan ta rataya kwarinta da baka.cikin gudu take takowa zuwa inda tajiyo sautin bindigar nan. Tafiya mai dan nisa kadan tayi kafin ta ƙaraso gurin da taji karan bindigar,mota tagani jikin bishiya tayi raga-raga,alamun hadari akayi agurin. Da sauri ta karasa tana duba-dube.aikuwa kwance ta ga Daddy cikin jini,dan haka cikin hanzari ta durƙusa tare da kara kunnenta sautin zuciyarsa,"da ransa "ta fada cikin hanzari tana dagowa. Gaba daya jini ya bata farraren kayan dake jikin Daddy,sannan gefen cikinsa ga alamar harbi nan,juyawa ta farayi tana kalle -kalle.dan kuwa ta tabbata bayan hadarin ma akwai mugayen da suka biyo bawan Allahn. Cikin jarumta ta kama Daddy,da gyar ta miƙar dashi tsaye,hannunsa ta lankaya afadarta,ta fara tafiya dashi,duk da batafiyar yake iyayi ba,jansa kawai take, sunyi faduwa tafi nawa kafin ta kaishi bakin dakin nata,jikin bishiyar,ta kwantar da Daddy,kafin ta fara bashi taimakon gaggawa.abin mamaki,yarinyar nan yadda kukasanwata likita,haka tayi amfani da wukarta ta cirewa Daddy wannan harsashin daga jikinsa.ta daure gurin,sannan ta mike ta tattaro ganyayyaki,sukayi tudu,taja Daddy ta dorashi akai.sannan ta koma gefe tare da riƙe kugu tana kallon Daddy,sai uban nishi take gaba ɗaya ta haɗa zufa, tunani take wannan bawan Allah daga ina yake?kuma su waye suka harbeshi?me yayi musu?bata da amsar wannan tambayar,kuma gashi duk da ta ɗaurewa Daddy gurinn da aka harbeshi,amma jini zuba yake,akwai bukatar ta sanya masa magani,dan haka saitaje ta nemo ganyen dazai tsayar masa da jinin. Juyawa tayi ta koma cikin dajin da sauri,dan harhado ganyayyakin dazata sanyawa Daddy agurin ciwon. Cikin hanzari ta debi ganyayyakin da take buƙatar yin amfani dasu,sannan ta kamo hanya.tana cikin tafiya tazo saitin gurin nan,cikin sarkakiyar da Aman ya faɗa ta fara jiyo nishi kamar na mutum,dan dakatawa tayi tana kasa kunne,kafin ta zaro kwarinta da baka tayi ready,sannan ta fara takawa ahankali,har zuwa gurin,kwance ta iske Aman cikin jini,yana fidda numfashi da kyar,cikin hanzari ta maida kwarinta da baka sannan ta nufi inda yake kwance,dagoshi tayi da sauri tana jijjigashi. ahankali Aman ya bude idonsa da suka mugun kumbura ya sauke akan fuskar yarinyar,cikin sarkewar murya yace "D..aaddy na...ki...Taim..akeshi"yana faɗin haka jikinsa ya saki yana ƙoƙarin sake sumewa,miƙar dashi ta fara kokarinyi ,saidai kuma sam ta kasa,saima fahimta da tayi kamar ya karye akafarsa. Dan haka cike da dubara ta samo manyan ganyen bishiya ta dauresu akugun Aman,sannan ta sanya wata doguwar igiyar ta fara jansa har zuwa inda ta bar Daddy kwance. Tana ajiyeshi itama ta zube agurin tana maida numfashi,dan tayi mugun gajiya gaba ɗaya jikinta yayi tsami. Da gyar ta iya tashi zaune ta koma kusa da Daddy, da bakinta ta tauna ganyayyekin nan,sannan ta manna masa agurin da aka harbeshi,tsabar azaba saida Daddy yayi ƙara duk da yana cikin hali na suma.tashi tayi da ƙoƙarin hawa dakinta dan dauko abinda zata gyara musu ciwukan,amma saboda yadda ta gaji nan gurin ta zube itama tana nishi da gyar. Ahankali sanyi ya fara ratsa kasusuwanta gurin yayi wani haske sosai har saida ta lumshe idonta,daga nan bata kara sanin inda kanta yake ba. Hasken. Kuwa yana gama haduwa guri ɗaya, saiga wannan kyakykyawan matashin ya bayyana,cikin lokaci kankani yayi kansu Daddy, shafawa su Daddy magani yayi Aduk gurin da suka ji ciwon,sannan ya gyarawa Aman ƙafarsa inda ya karye. Gurin yarinyar ya koma ya bude bakinta ya tsiyaya mata wani ruwa cikin kwalba mai kama da ta zinare,kafin ya dan bubbuga kumatunta yace"ISLAM"cikin wani sauti mai matukar amo da dadin sauraro, Ahankali ta fara bude idonta tana kallon,saurayin daya kira sunan nata, saidai hasken dake gurin ya hanata ganin fuskar tasa,tunda take bata taɓa ganin,fuskarsa ba kullum cikin yanayin haske take iya ganinsa. Murmushi yake mata kafin ya bace.da sauri ta tashi zaune,babu alamun gajiya ko ciwon jiki atattare da ita. Kallonta takai inda su Daddy ke kwance,kamar yadda tayi tsammani ganinsu, a hakan ta gansu kuwa. Murmushi tayi tana kallonsu,kafin ta nufi gurin koramar nan ta dauro alwala,tana mikewa janbu yazo ta gabanta yana tsalle tare da dan ƙara,murmushi tayi tare da shafa kansa tace"janbu yau na samo wasu bayin Allah cikin mawuyacin hali,yanzu haka suna nan kwance agida,kasan menene,malamina ne yayi musu magani,ahalin yanzu ba wata damuwa,saidai mujira su farfaɗo"ta fada tana murmushi tare da nufar gidan nata,kamar yadda take fadi. Kai tsaye ta kama bishiyar ta hayetare da lulluɓa mayafinta ta fara sallarta .... Muje zuwa sannu kan hankali masu karatu. Mrs babi ce 💘💘 Share and comment as much as you can fisabilillah. [9/5/2022, 7:12 PM] Abk: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 🎄🎄RAINON DAWA🎄🎄 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free page 9/10 GAMASU SON BIYAN KUDIN WANNAN LITTAFIN,ZAKU BIYA KAMAR HAKA. NORMAL GROUP 300₦ UPDATE BIYAR ASATI. SPECIAL GROUP 500# UPDATE BAKWAI ASATI. ZAKU TURO KUDINKU TA WANNAN ACC. ƊIN. SAATU KABIR U.B.A 2215749011. SAINA JIKU. EVIDENCE OF PAYMENT 08148360851 _______________ Cikin dare Aman ya farfado, ahankali yake buɗe idon sa da su ka yi masa nauyi sosai.kasancewar dare ne hakan ya sa gurin yayi duhu, lumshe ido yayi cikin jin raɗaɗin da ƙafarsa keyi masa da ciwo. Yunkurawa yayi da nufin ya tashi zaune, saidai sam ya kasa tashi zaunen, sakamakon tsami da jikinsa yayi gaba ɗaya. Ahankali yake bin gurin da kallo, dan son gane inda yake, amma ya kasa gane War, ba abinda yake gani face alamun bishiyu dake tsaye agurin, sai kukan tsuntsaye,nan da nan tsoro ya kama shi,yayi saurin runtse idanunsa.tare da juyar da kansa,daga barin kallon dajin. Tunani yake cikin ransa,to inane nan kuma?waye ya kawo su nan?ina Daddyn sa yake ?waɗan nan tarin tambayoyin ne cikin zuciyarsa,amma ba amsa. Jin alamun kamar akwai mutum kusa dashi,yasa ahankali ya ɗan buɗe idonsa kadan,yana kallon Daddyn sa dake kwance,wani sanyin daɗi ne ya ratsa zuciyarsa,tabbas wannan, Daddy ne akwance.dan haka maida idonsa yayi tare da rufewa yana tunanin ƙila mutanen da suka biyo su ne suka kamasu. ahaka barci yayi gaba dashi cike da alhini. Washe gari da asuba Islam ta tashi tare da saukowa,saida ta dubasu kafin ta nufi ƙoramarta,alwala ta dauro sanann ta dawo, bayan tayi salla ƙasa ta sauko tare da wani kwano mai kama da akushi,an rufe shi da wani dan faifai. Ajiye wa tayi kusa da inda suke kwance kafin itama ta zauna,tare da kafesu da idanu. Sanyin asuba ne ya fara ratsasu,ahankali Aman ya buɗe idonsa, carab kuwa suka sauka akan Islam wacce ta zuba musu idanu,cike da tunani cikin ranta. Tsoro ne ya matukar kama Aman,Dan haka cikin hanzari ya yunƙura da nufin tashi zaune yana faɗin"A' uzubillah, wacece ke ? Me muka yi muku?me kuke bukata atare damu?" Ya faɗa adam razane yana kallon kyakykyawar fuskar Islam. Ita kuwa ganin yadda ya tsorota ne yasata matsowa da sauri tana faɗin"kayi ahankali,akwai karaya aƙafarka Ni ba komai zanyi muku ba,na taimake kune"ta fada tana mai kama kafadunsa ya tashi zaunen. Kallonta yake cikin dan hasken da bai gama mamaye gurin ba,mamaki sosai cikin ransa, wannan fa macece,to me takeyi agurin nan?dan gashinan ya gani daji ne gaba da baya, Kallon Aman tayi lokacin da ta koma ta zauna,sai kuma taga yana kallonta,harararsa tayi,tare da murguda baki sannan tace "kai ya haka ne kake ta kallona kamar zaka cinye Ni? ta fada cikin salon muryarta mai dadi,da nuna ba tsoro. Ajiyar zuciya Aman yayi kafin yace "mamaki nake, ta yadda yarinya mace kamar ke, ta kasance agurin nan? Sannan kuma ta yaya kika iya taimakon mu,?dan Allah ki fadamin kedin mutum ce ko aljan?sannan waye ya kawo mu nan gurin,nida Daddy na"ya kai karshen zancen sa yana dafe kansa dake masa ciwo. Banza Islam tayi dashi, tare da mikewa ta nufi ƙoramar nan,Binta Aman yayi da kallo,tare da kallon kayan dake jikinta,zuciyarsa cike da tunanin anya mutum ce kuwa?ba jimawa ta dawo da ruwa cikin wata yar gwarya, ajiye masa tayi tare da cewa"idan ka gama kallon nasa saikayi alwala kayi sallah"tana faɗin haka ta mike tare da kama bishiyar nan ta haye,Aman yana kallon ta baki buɗe,cike da zallar madarar mamaki,kalli yadda take hawa bishiya, kamar wata biri gaskiya shikam yana mamaki da tsoron wannan yarinyar. Aman yana cikin sallar Daddy ya farka,bakinsa dauke da salati.nan take abinda ya faru dasu,ya dawo cikin kwakwalwarsa tiryan tiyan. Ahankali ya buɗe idonsa yana mai kiran sunan,Aman tare da juyawa gefe da gefensa yana neman Aman din,ba karamin daɗi Daddyn yaji ba lokacin da idanunsa suka sauka kan Aman yana Sallah.hamdala yayi cike da godiyar Ubangiji kafin ya yunƙura ahankali ya tashi zaune.jingina yayi da jikin bishiyar yana mai runtse ido,tare da jin yadda gurin da aka harbeshi ke masa zafi. "Alhamdullah Daddy ka farka?sannu Daddy Ina ke maka ciwo yanzu?"Aman ya faɗa lokacin daya idar da sallar. Juyowa Daddy yayi shima yana mai yiwa aman din sannu,tare da kallon kafar Anan dake daure,alamun karaya. "Sannu Aman,kayi hakuri nina ja maka wannan kaddarar, dana Barka kayi zaman ka cikin yan uwanka, yanzu gashi an kama mu,an ajiye cikin wannan dajin"Daddy ya faɗa cike da damuwa. "A'a Daddy kadaina fadar haka Please,dama can Allah ya ƙaddara mana faruwar hakan,kuma ba kamu akayi ba,mun kubuta daddy" Jinjina kai Daddy yayi cike da jin jiki,yana mai lumshe idonsa. Kafin yace "Alhmdllh Aman ina ne ?waye ya kawo mu ? Kafin aman yayi magana sai ga Islam ta sauko,da sauri ta ƙaraso gurin Daddy ta durƙusa tana mai faɗin"sannu ya jikin naka"kallonta Daddy keyi cike da mamaki,wannan yarinyar fa?me takeyi anan?kodai iyayenta ne suka taimakesu? Cikin muryar dattako Daddy yace "sannu yarinya, jiki da sauki,muna godiya sosai da taimakon ku garemu,ina iyayen naki suke,muna bukatar barin gurin nan,dan ganin likita"Daddy ya faɗa cikin muryarsa wacce kana ji kasan yana shan wuya. Murmushi Islam tayi,kafin tace "bana da kowa,Ni kadai ke rayuwa anan,sannna saidai afita can bakin titi asami motar dazata kaiku asibiti"ta fada cikin nutsuwa tana kallon Daddy, Cike da mamaki Dukansu ke kallonta,kafin daddy yace "yarinya,ke kaɗai ke rayuwa cikin wannan hatsabibin dajin?jinjina kai Islam tayi tana mai ballawa Aman harara,Wanda ya kafeta da idanunsa,yana yaba tsarin halitta da kyau da Allah yayiwa yarinyar. Murmushi yayi ganin yadda take ta faman harararsa,kafin yace "Daddy ya kamata kayi sallah musan abinyi" Ruwan Islam ta mikowa Daddy sannan ta koma can nesa dasu,dan basu guri Daddyn yayi alwalar. Wannan akushin ta miko musu bayan Daddy yayi salla. Budewa Aman yayi, cikin mamaki yake kallon akushin dake dauke da gasasshen nama sai turiri yake, sannan ya kalli Daddy. Shima Daddy kallon Aman yayi jinjina kai,lallai akwai wani al'amari tattare da yarinyar nan,kuma ya ƙudiri niyyar bazai barta cikin wanan dajin ba yana bukatar sanin itaɗin ko wacece,zai tafi da ita gidansa,ya cigaba da riketa,domin tana bukatar taimako. "Yarinya ina kika samu wannan naman?Daddy ya faɗa yana kallon Islam. Murmushi tayi kafin tace" daga Allah "ta fada tana mai sunkuyar da kanta. Kallonta kawai suke cike da mamaki da al'ajabin ta. Sam Daddy baici Naman nan ba domin baya jin dadin jikinsa ko kaɗan,tunani yake cikin ransa,su waye waɗan nan mutane?me suke nema gurinsa?waye ya aikosu gareshi?yayi nisa cikin tunanin da yake yaji Muryar Aman yana faɗin"Daddy, zaman mu agurin nan fa akwai hatsari,ina tsoro kada mutanen nan su dawo, ko kuma wani abun ya samemu cikin wannan dajin" Jinjina kai Daddy yayi kafin yace "akwai bukatar mu bar gurin nan kam aman, amma ta yaya ?ka gani dai ba wayoyi atare damu,bare mu kira azo atafi damu,yarinya muna bukatar taimakon ki,muna son barin gurin nan,sannan kuma ina son ki bimu zuwa gidanmu,domin zamanki ke kaɗai cikin dajin nan babban hadari ne,duba da kasancewar ki mace" Daddy ya faɗa yana kallon Islam,wacce ke zaune daga can gefensu. Kallon Daddyn tayi kafin ta mike ta nufi bayan wata bishiya ta tsaya,tunani take shin ya kamata tabi su Daddy zuwa gidansu?ko kuma tayi zamanta cikin dajin ya fi mata kwanciyar hankali,tunda ta kwatanta zama cikin mutane,amma hakan yaƙi yiwuwa,saboda kowa burinsa ya keta mata haddi,jikinta kawai suke da bukata,kafin su taimaka mata,saidai tana ganin Daddyn kamar baya daya daga cikin mutanen da ta hadu dasu abaya,shidin kamilin mutum ne,kuma dagani yana da sanin ya kamata. harkene ya mamaye gurin da take tsaye,cikin murya mai cike da zaƙin sauti aka fara magana, "Islam, kada ki tsananta tunani,jini bawan Allah nan,domin kaddararki tana tare dasu,bazan taɓa bari acutar dake ba ,ina tare dake ako ina kike" Kallon hasken nan tayi,tare da lumshe ido,hakika tunda malaminta yayi magana,zata bishi,idan taga akwai matsala saitayi dawowarta nan ɗin.dan haka gurin su ta koma bayan hasken nan ya bace. Zama tayi tare da yin shiru kanta na kallon gefen ta. "Kinyi shiru yarinya baki ce komai ba,karki damu bazan taɓa barin wani abu ya cutar dake ba a zaman da zakiyi damu, sannan nima ina da yara dai -dai ke,ina son taimaka miki kamar yadda kika taimaka mana"ya faɗa cike da ƙarfafa mata gwuiwa. Ahankali ta ɗago ta kalli Daddy kafin tace "shikenan na amince zan bika, saidai idan nayi karo da abinda bai gamsar dani ba,zaku iya nemana ku rasa ako wane lokaci"ta fada kai tsaye tana kallon Daddy. Murmushi Daddy yayi yace "na gode da kika yarda zaki bini yata, dan kuwa jinki nake kamar yar cikina, Yanzu ta yaya zamu bar gurin nan" ya faɗa yana kallon fuskarta. Saidai muyi tafiya zuwa bakin titi, acan zamu samu mota zuwa cikin gari"ta fada tana mikewa tsaye tare da kallon Daddy, tace "Ina da abokin da bazan iya barinsa anan ba, wato janbu,idan ka amince zan tafi dashi " "Bakomai yata amma ina shi janbun Dan banganshi tare da ke ba"cewar Daddy yana kallon gurin. Hannunta ta sanya tare da danne harshen ta,tayi wani fito,nan da nan saiga janbu yana tsalle asaman bishi tare da nufota. Kan kafaɗarta ya sauka yana kallon su Daddy. "Ikon Allah ƴata wannan shine abokin naki kenan?to ba damuwa Allah yayi mana jagora. Ameen Aman yace wanda yayi shiru tun dazu yana sauraron su,yaji daɗi sosai dayaji cewar zasu tafi da Islam, dan shima bai goyi bayan zamanta agurin ba. Ba abinda Islam ta dauka aɗakin nata face kwarinta da baka,dan ta bar komai agurin ne saboda shirin ko ta kwana,dataga akwai matsala saita dawo gidanta. Haka Daddy ya yunƙura ya Mike yana dafa bishiya.wata sanda Islam ta mikawa Aman Dan ya dafa sandar su tafi. Ba ƙaramar wahala suka sha ba kafin suzo bakin titin, da gyar Daddy ya kai bakin titin duk da Saida Islam ta rikeshi. Suna fitowa suka ci Sa'a wani mai mota zai wuce Abuja da sassafe,ganinsu cikin wani hali na bukatar taimako yasa shi,tsayawa ya daukesu, yana ta kallon Islam tare da sakar mata murmushi. Kai tsaye asibiti ya nufa dasu,cike da mamaki Aman ke kallon drivern dan kuwa asibitin da suke zuwa, nan ya kawo su. Kasancewar Daddyn sananne nan da nan aka shiga dasu emergency,yayi da Islam ta zauna abakin ƙorar dakin da aka kwantar dasu, Mutumin nan day kawosu ne yazo gurin Islam yana mai kallonta,fuskarsa ɗauke da murmushi yace"Islam kada ki damu,kin shiga hannu na gari,kuma kamar yadda na faɗa miki, ina tare dake ako ina kike"ya faɗa yana mai kallon fuskarta . Sai lokacin Islam ta gane malaminta ne,dan haka murmushi tayi itama tana mai kallonsa,amma ba tace komai ba..... Can gidan Daddy kuwa hankalinsu ya tashi sosai,dan sunyi ta kiran wayoyin su Daddy amma, ba wacce ta shiga.hankalinsu yayi mugun tashi sosai. Suna zaune afalo mai gadi yazo yace ana sallama dasu, da sauri suka fito gaba dayansu,nan ake sanar dasu su Daddy na asibiti. Hankali tashe suka nufi asibitin gana dayansu cikin ruɗewa da tashin hankali,su jannat kam kuka suke..... Muje zuwa masu karatu. Yanzu zamu fara. Mrs babi ce💘💘 Kuyi hakurin jina shiru banjin daɗi ne. [9/6/2022, 9:26 PM] Abk: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 🎄🎄RAINON DAWA🎄🎄 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 https://facebook.com/groups/943534712916776/ Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din👆🏽 Free page 11/12 GAMASU SON BIYAN KUDIN WANNAN LITTAFIN,ZAKU BIYA KAMAR HAKA. NORMAL GROUP 300₦ UPDATE BIYAR ASATI. SPECIAL GROUP 500₦ UPDATE BAKWAI ASATI ZAKU TURO TA NAN. SARATU KABIR. U.B.A 2215749011 EVIDENCE OF PAYMENT 08148360851. SAINA JIKU *_Masu son Littafin MIJIN MALAMA suyi following Acct ɗin nan a Arewabooks👇🏾_* https://arewabooks.com/u/nimcyluv ____________Su Mommy ne zaune gaba dayansu, afalo. Hankalinsu gaba ɗaya atashe yake,dan sam Daddy bai saba irin wannan tafiyar ba,duk inda yaje daya sauka zai kira ya sanar dasu. Amma yau gashi tun jiya suke neman layinsa dana Aman,ba Wanda suka samu, hakan ba karamin abu bane gaskiya. Mai gadi ne ya shigo ya sanar da Mommy wani mutum yana sallama awaje, cikin sauri suka fito gaba dayansu,nan mutum wanda daga asibitin aka turo shi ,yake sanar dasu daga asibiti ne ake nemansu,ankai Daddy yayi accident. Cikin tashin hankali suka nufi asibitin,gaba daya,arude suke,dan su jannat ma tuni sun fara kuka. Lokacin da suka isa asibitin,tuni an gama ba su Daddy taimakon gaggawa suna dakin hutu,Aman ba'a sake masa wani daurin ba ,dan kuwa sunce wannan daurin da akayi masa yayi sosai,dan sunyi scanning kuna sunga komai yayi dai-dai. Daddy ma jini aka sanya masa,dan ya zubar da jini sosai. Dan haka su mommy na zuwa aka basu damar ganin su Daddy,Dan daki daya aka ajiye su. Tun aharabar asibitin granny ke kuka tana faɗin"wayyo Allah baban Asalam, jiya -jiya katafi, muka rabu da kai lafiya,ashe hadari zakayi?dana dan albarka, ku kaini na ganshi Ni fadimatu naga ta kaina"da gyar mommy ke rarrashin granny tana faɗin"granny kiyi shiru,inba haka ba bazasu bari ki gansu ba,zasu hanaki shiga" Cikin masifa granny ta ballawa mommy harara, kafin tace"to aniyarki ta biki har gadon barcinki,wllh banga dan tijarar da ya isa ya hanani ganin dana da jikana ba,dan ba wanda ya haifa min shi,yar shishshigi kawai"ta fada tana hararar mommy tare da kunna kanta cikin dakin. Girgiza kai kawai mommy tayi kafin tabi bayan grannyn,su jannat na take mata ba. Kuka sosai su jannat keyi,mommy kan sai hawaye,granny ma kuka take harda majina,lokacin da Aman ya gama basu labarin abinda ya faru,da yadda suka kuɓuta. Daddy haƙuri yake basu akan suyi shiru,ai an suna arziki,tunda suna raye. Fyace majina granny tayi da habar ,zaninta,kafin tace "Allah sarki ina yarinyar take yanzu?Allah yayi mata albarka har naji kaunarta cikin raina wllh" Daddy ne yace jannat ta duba waje zataga yarinyar ta shigo da ita. Lokacin kuwa Islam na zaune tare da malaminta, amma ba wanda yake ganinsa sai ita kadai,kallonta yayi da murmushi kafin yace "yanzu sabin ahalinki zasu zo su shiga dake,ki kwantar da hankalinki,duk lokacin da kikaso ganina,zan bayyana gareki,sannan ki riƙe aranki wadan nan mutanen alkairine agareki,kizama mai juriya Islam"ya karasa zancen sa yana mikewa tare da shafa kan Islam,wacce ke kallon sa cike da tarin tambayoyi abakinta,amma sam idan suna tare bata iya furta komai saidai kallo.haka tana kallo yazama haske ya bace bat. "Kece wacce kuka zo da daddyna yanzu"Islam ta tsinkayo Muryar jannat tana mata magana. Kallon jannat tayi kafin tace "Ni ce" Kallonta jannat keyi tunda ga sama har ƙasa kafin ta taɓe baki tace "zo muje"tana faɗin haka tayi gaba . Binta Islam tayi da kallo kafin tayi ƙwafa tace "wannan da gani bata ji,zan gyara miki zama wllh,Ni rainon dawa ce,bana ɗaukar raini"ta fada cikin haɗe rai kafin ta mike tabi bayan jannat. Suna shiga dakin,mommy ta kamo hannun Islam tana mai cewa"sannu yata, Allah yayi miki albarka,mun gode sosai kin taimakemu"murmushi Islam tayi tana kallon mommy,lokaci guda taji matar ta kwanta mata aranta. "To ai saiki barta tazo gurina nima inyi mata godiyar,mutum komai saiya nuna iyayi akai"granny ta fada tana janyo hannun Islam tare da hararar mommy. Murmushi mommy tayi tana mai kallon Daddy dake kusa da ita.lumshe mata ido yayi alamun tayi hakuri,itama idon ta lumshe masa alamun ba komai. "Sannu yar nan,kinyi abin kwarai,abin ayaba maki,kin ceci dana da jikana,dan haka zaki zauna tare da Ni, zan kula dake ba wanda zan bari yayi maki ba daidai ba agidan nan, kinji"granny ta fada tana shafa kan Islam, Jinjina kai Islam tayi kafin ta kalli jannat wacce ke ta faman yatsina. Aman kuwa sai bin Islam yake da kallo cike da ƙauna,shi komai nata burgeshi yake, kai tsaye take komai ba boye boye. Kallon granny Islam tayi kafin tace "kijawa wannan matar kunne, dan naga tana min wani kallon raini,Ni bana ɗaukar raini duk wanda ya takani, zan takashi, Ni rainon dawa ce bana ɗaukar raini"ta fada cike da haɗe rai tana kafe jannat da ido. Cike da mamaki jannat ke kallon Islam,sannan ta yunkuro cikin gadara zatayi magana mommy ta Banka mata wata uwar harara,hakan yasa ta maida fushinta ganin asibiti suke.amma zata nunawa wannan yar dajin ita ba kalarta bace. "Indai wannan marar kunyar ce muma hakuri mike da ita,kuma wllh na baki dama,idan tayi miki ba daidai ba ki rama dan nima ta isheni da rashin kunya"cewar granny tana hararar jannat. Ran jannat gaba ɗaya ya gama ɓaci.sai huci take tana hararar granny ta kasa -ƙasa. Daddy ne yayi gyaran murya kafin yace "ku tafi da Islam gida,tayi wanka abata abinci taci sannan ta huta,duk abinda take bukata atabbatar anyi mata shi"ya faɗa cikin muryar dattako yana kallon mommy. Haka mommy da yaran suka koma gida,akan ita zata dawo anjima,tunda granny tace Dole ita bazata koma gida ba,saidai mommy taje gidan yanzu. Ko acikin mota Mommy da Islam ne agaba, sai jannat da hannan abaya.hakan ba karamin ƙara kular da jannat yayi ba,tunda kowa yasan ita ke zama agaban mota idan zasu fita,amma an zo ansa wannan kucakar amazaunin ta. Koda sukaje gidan,ganin cewar Islam zatayi sa'ar hanan,dan haka sai mommy tace suje dakin hanan ɗin tayi wanka acan,hanan ta bata kaya ta sanya. To hanan tace sannan tace wa Islam"zo muje daki "tayi gaba abinta. Tsaye Islam tayi tana kallon inda hanan ɗin ta nufa,ita fa sam arayuwarta, bata son wulaƙanci,kuma yadda ta fahimci yaran gidan basu da mutunci ko kaɗan,kuma wllh bazata dauki sakarcinsu ba . Ganin bata bi hannan ɗin ba yasa mommy tace "ƴata kije dakin hannan kiyi wanka kinji?zan kawo miki abinci kici,saiki huta,ki saki jikinki,nan tamkar gidanku ne"mommy ta fada cikin muryar kwantar da hankali.murmushi Islam tayi kafin tace "to Hajiya" Hannunta mommy ta kamo tace "ba Hajiya ba,mommy kinji" Jinjina kai Islam tayi kafin tace "to mommy" Tana mai bin bayan hannan. Tsaki jannat ta ja mai ƙarfi kafin tayi sama itama,bakin ciki kamar ya kasheta. Aikuwa karaf akan kunnen Islam,dan haka da sauri itama tabi jannat din,taku biyu uku,ta cimma jannat,tana gab da shiga ɗakinta dake jikin na hanan,taji an fizgota tayo baya. Arazane ta yi dan ƙara tana rike wuyanta.cike da mamaki take kallon Islam dake tsaye cikin haɗe fuska,aikuwa cikin masifa tayi kan Islam"ke dan uwarki saboda baki da mutunci,Ni kike jawa riga ta baya?dan kut.... Dassss !!!jannat taji an bale mata lips,da mugun ƙarfi,hakan ya hanata karasa maganar da tayi niyya. "Idan kika sake zagina,wllh saina miki dukan tsiya agurin nan,banza marar hankali,karkiga nazo gidanku kiyi tunanin zan dauki raini ,wllh kikayi min ba dai-dai ba duka zaki sha,Ni rainon dawa ce bana daukar raini,ki kiyaye"Islam na gama faɗin haka tayi ɗakin hanan,abinta. Tsabar haushi da bakin ciki da ɓacin rai,jannat kuka ta sanya ta shige dakinta tare da banko kofar. "Wllh saina ci kan uwar yarinyar nan,har Ni zata bugewa baki?agidan ubana?wllh saina ci uwar yarinyar nan"ta fada cikin kuka tana jifa da fillows din kan gadonta. Mommy kuwa tana shiga ɗakinta ta dauko wayarta tare da kiran Aslam, Yana kwance kan kujera yayi dai-dai, da gashi sai gajeren wando da singlet,yana shafa kan wata baturiya dake kwance kan ƙirjinsa,wayarsa ta dauki ruri. Jin ringtone din mommynsa ne yasashi saurin dauka,saida ya dai-dai-ta nutsuwarsa kafin ya daga. "Mommy na, barka da gida"ya faɗa cikin muryarsa mai daɗin sauraro. "Aslam, daddynka yana asibiti,shida Aman, jiya aka taresu akan hanyarsu ta zuwa Niger,kuma an harbi daddynku acikinsa, Aman kuma ya karye,tare da manyan raunuka,Allah ne kawai ya kiyaye da tuni sun mutu. Dan haka duk abinda kake ka ajiye ka dawo gida"mommy na gama faɗin haka ta kashe wayarta, haka ne kawai zai sa Aslam ya dawo gida, ajiyar zuciya tayi tare da mikewa,sannan ta shiga kitchen da kanta. Aslam kuwa jin abinda mommynsa ke faɗi,tuni ya ture yarinyar dake kwance akan ƙirjinsa ya mike tsaye,"hello !hello!!mommy kina jina ?hello"yake ta fada cikin tashin hankali,amma ina mommy tuni ta kashe wayar ta. Hankali tashe ya fara hada kayansa,cikin gaggawa yake komai,yarinyar sai tambayar sa take lafiya amma ko takanta baibi ba. Waya ya dauka ya kira wata number yace yana son jirgin da zai tashi zuwa Nigeria yanzu. Cikin Sa'a ya samu wanda zai tashi nan da minti ashirin. Haka yayi ta kiran numbers din su Daddy da Aman, Amma basa shiga. Yana gama shirinsa ya fito riƙe da jakarsa da abubuwan da zai bukata.lokacin yarinyar na zaune kan kujera.mika mata keys din gidan yayi yace "ta kulle masa gida ta kaiwa mark mukullin, Yayi ficewarsa. Cikin ƙanƙanin lokaci da bazai gaza awannin uku zuwa hudu ba,Aslam ya sauƙa afilin saukar jirage da ke birnin tarayya Abuja. Kai tsaye ya dauki mai taxi,ya nufi gida. Lokacin daya isa gida mommy tuni ta koma asibiti ita da jannat suka koma, dan haka daga Islam sai hannan,agidan. Dan haka kulle ƙofar hanan tayi lokacin dazata shiga wanka,ta bar Islam afalo tana cin abinci,tana sanye da kayan da hanan ta bata ta sanya,riga da wando ne ajikinta,rigar ta sauko har gwuiwarta,sai wando wanda ya kasance three quarter ne, kanta ba dan kwali sai gashinta data daure, ko mai abata shafa ba,amma tayi kyau shar da ita,abinka da mai kyau. Norking din kofar ake tayi,tana zaune tana ji,amma batayi yunkurin tashi ta buɗe ba.saida ta kammala cin abincinta, sannan ta tashi cikin takunta mai cike da ɗaukar hankali ta nufi ƙofar,jin an Dada danna door bell din da ƙarfi kusan sau uku. Tsaki tayi tana faɗin"wai waye wannan haka?nifa gaskiya wannan tsirfar bazan iya da itaba,haka kawai ake kulle kofa sai mutum yana ta tashi budewa,"ta fada cike da ƙosawa tana jan tsaki,kafin ta buɗe kofar. Kallon- kallo ake tsakanin Aslam da kuma Islam,inda shi yake kallonta cike da ɓacin ran ba'a buɗe masa kofa da wuri ba, sannan yana mata kallon rashin sani,gashi sai wani yatsina fuska take tana kallonsa. Cikin rashin damuwa Islam ta gyara tsayuwar ta ,ba tare da ta kauce masa daga hanya ba, sannan ta wani karkata kai tana kallonsa tun daka sama har ƙasa kafin tace "malam daga ina?wa kake nema?masu gidan basa nan suna asibiti,saika bisu can"ta fada cikin wani salo irin mai kama da na yan daba tana juyawa da nufin komawa cikin falon. Kan uban nan,wannan ɗin wacece?wacce marar kunyar ce take min irin wannan tambayar agidan mu?lallai ,zan koya miki hankali,ya faɗa yana fizgo rigarta ta baya..... Masu karatu yanzu wasan zai fadra, Muje zuwa Mrs babi ce 💘💘 Share and comment fisabilillah. [9/8/2022, 11:54 AM] Abk: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 🎄🎄 RAINON DAWA🎄🎄 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free page 13/14 GAMASU SON BIYAN KUDIN WANNAN LITTAFIN, ZAKU BIYA KAMAR HAKA. NORMAL GROUP 300₦ UPDATE BIYAR ASATI. SPECIAL GROUP 500₦ UPDATE BAKWAI ASATI. GAREKU MANYAN MATA MASU BUƘATAR ATURA MUSU TA PC. ZAKU BIYA 1000₦. ZAKU TURA KUDIN TA WANNAN ACC. ƊIN. SARATU KABIR U.B.A. 2215749011 SAI KUNZO. https://facebook.com/groups/943534712916776/ Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din👆🏽 _______________"Kan ubancan,wannan ɗin wacece?wace marar kunyar ce take min wannan tambayar agidan mu?lallai zan koya mata hankali,zaki san waye Aslam yau"yana gama faɗin haka cikin zuciyarsa,ya wani fizgo Islam ta baya. Da mugun ƙarfi ya fizgota cikin salon sa na mugunta. Ba zato ba tsammani, kawai Islam taji an fizgota ta dawo baya,bugawa tayi da jikin bango,sosai ta buge kanta ta baya,dan lokacin da Aslam ya fizgota kaucewa yayi,maimakon ta fado jikinsa,sai ta bugu da bango.dan ƙara ta sanya tare da runtse idonta cike da azaba,dan ta bugu sosai.gashi ya damke mata gashi da ƙarfi cikin hannunsa. "WHO the hell are you?wacece ke?da har Kike iya kallon kwayar idona kina min wannan tambayar ta raini?kinsan waye Aslam kuwa?bana son raini ko nuna ban isaba, kishiga hankalinki,wannan gargadi na ne gareki,bansan koke wacece ba,amma yau kawai naji na Tsaneki,kada ki bari wani abu ya sake haɗani dake " Duk da irin azabar da Islam Ke sha,dan kuwa kallo ɗaya zakayi wa idanunta wanda ta buɗe su lokacin da Aslam ya fara magana,kasan cewa tana shan azaba ,tana karbar kida ahannun Aslam,Amma cikin nata kalar zafin ran,da mugun ɓacin rai,tayi wani yunkuri tare da juyar da hannun Aslam din,sai gata ta kwace kanta daga hannunsa. Gabansa ta matso sosai kamar zata rungumeshi,banda huci ba abinda takeyi, idonta yayi jajur,ta fara magana"lallai kayi gangancin yi min wannan kalar muguntar, wllh!wllh!!wllh!!!ka ajiye aranka,saina rama duk wani kalar cin kashi dazakayimin agidan nan,kamar yadda bansan ko kai waye ba ,Nima bakasan koni wacece ba,bazan taɓa daukar rainin hankali da wulaƙanci ba,dan Ni ba wulaƙantacciya bace,Ni rainon dawa ce bana ɗaukar raini"Islam ta fada cikin zazzare masa ido,kuma ba tare da nuna tsoro ko shayinsa ba,duk da yadda yake tsaye agabanta kamar Giwa,ita kuwa tana nan yar ɗull,akasansa. Cike da zallar mamaki Aslam ke kallon Islam,wai wannan wace yarinyar ce?me ta taka haka agidan nan?shidai yasan adangin mommy Ko na Daddy ba irin wannan yarinyar yar tijara,to a ina suka samota? Tambayar da Aslam keyiwa kansa kenan cikin mugunyar bacin rai,ji yake kamar ya shaƙeta ta mutu. Cilli yayi da jakar dake hannunsa,jikinsa har rawa yake tsabar ɓacin rai,kasancewarsa mutum mai matukar son girma,da son anuna shiɗin babbane gana ƙasa dashi,sai abinda Islam tayi masa yazo masa abazata,kannansa har wanda daga shi sai shi,ahaihuwa ma,tsoron sa yake ji,amma wannan abar da baifi yayi loma daya da ita ba ,itace take tsaye gabansa tana fada masa maganganu masu zafi haka?inaaaa!!!wllh bazai yiyuwa. Kallon ta yake cikin ɓacin rai,yana tunanin irin hukuncin da zai mata,itama kuma bata fasa kallon nashi ba,idonta ƙurr, akan kyakykyawar fuskarsa,wanda ɓacin rai ya mamayeta. "Zakiyi dana sanin haduwar nan tamu dake ta farko,zan nuna miki ke karamar yar iska ce,iyakar ki Nigeria,wllh saina san ya ki cikin tashin hankalin da saikin zabi mutuwar ki akan rayuwa"Aslam ya faɗa cikin wata irin zazzafar murya,har sarkewa muryarsa keyi,tsabar ɓacin rai. Wani shegen murmushi Islam tayi,kafin tace "nima ga nawa albishir din,ka sani,bazan taɓa gajiyawa da rama duk wani abu da bai gamsar dani ba,wanda zakayi min,zan zamo maka alaƙaƙai,zan zame maka ladangaren bakin tulu, Ni Islam rainon dawa ce bana ɗaukar raini"Islam ta fada cikin gadara tana karkada jiki. "Keeeeehhhh!!! Aslam ya daka mata tsawa tare da daga hannunsa ya sharara mata mari mai matukar zafi,ji kake tauuuu!!!har saida falon ya amsa. Hakan yayi dai-dai da fitowar Hanan daga wanka,zaro ido tayi sakamakon ganin ya Aslam ,kuma ya wanka wa Islam mari, da gudu ta ke saukowa daga matakalar Benin,harta ƙaraso garesu.jikinta banda rawa ba abinda yake.cikin rawar murya tace "yaya da...n ... Allah ...kayi hakuri bakuwar Daddy ce ...tare suka zo ,kuma itace ta ceci rayuwarsu"ta fada cikin tsantsar tsoro tana mai kamo Islam,wacce ta daskare atsaye riƙe da kumatunta,wanda Aslam ya kashe mata su da mari,tunda take arayuwarta,ba wani mahalukin daya taɓa daga hannu ya sharara mata mari haka,sai wannan mutum,lallai ya tsokano tsuliyar dodo,wllh tashin hankali yanzu suka fara. Kallon Hanan yayi tare da watsa mata wani shegen kallo na ki kiyaye,ko na dawo kanki. Da sauri ta koma bayan Islam ta buya,jikinta na rawa. "Wannan shine last warning da zan miki ki kiyayeni,bani da kyau,ba'a shiga gona ta afita lafiya"yana kaiwa nan yayi waje cikin fushi da ɓacin rai. Driver ya kira suka tafi asibitin,zuciyarsa kamar zata kama da wuta. Islam na tsaye bakin ƙofar nan riƙe da kumatunta dake mata zugi,idanunta sunyi jaaa sosai,ahankali Hanan ta zagayo gabanta ,cike da tausayawa tace "sannu,amma meye ya hadaku da yaya daga zuwansa?dan Allah kiyi nesa dashi,har zuwa lokacin da zai bar kasar nan,wllh yaya ya wuce duk yadda kike tunani,sam baya son rashin kunya,ke kuma naga alama kamar halinki ne rashin kunya,koda zakiyiwa wasu karki ce zakiyiwa yaya Aslam domin ya wuce tunaninki"Hanan ta kai aya tana kokarin kamo hannun Islam. Cikin masifa da jin haushi Islam ta fizge hannunta,tare da watsawa Hanan kallon daya sata ta ja da baya. "Wllh ya dauki bashi,bazan taɓa yafe wannan cin mutuncin da yayi min ba,ba wanda ya taba marina sai shi,kuma yayi kuskure,sannan Ni bana tsoron uban kowa,bare wannan basamuden ya tsoratani,baki mai bakar aniya, zaisan ya taba Islam,ni rainon dawa ce bana ɗaukar raini"tana kaiwa nan tayi sama cikin sauri ta shige dakin Hanan. Zama tayi akan gado ta lankwashe kafafunta tare da kafe jikin bango da ido,zuciyarsa sai tafasa take.jikin tane ya kama rawa kamar mai farfadiya,nan da nan kwan dake haska dakin ya fara farfari,gaba ɗaya kayan dake cikin dakin hatta gadon da take kai girgiza yake,ji kake fasss!!! madubin dakin ya fado ya tarwatse. Da gudu hanan ta hawo saman,saidai abinda ta gani,yasata komawa falo da gudu tana ihu,jikinta sai rawa yake,anya kuwa wannan mutum ce?daga shiga daki gaba ɗaya kayan dake cikin dakin sun kama jijjiga? "na shiga ukuna "ta fada cikin tsoro tana kokarin kiran wayar mommy. Aslam kuwa kai tsaye asibitin suka nufa,har suka ƙara sa cikin asibitin zuciyarsa na masa zafi da suya. akan me wannan karamar yarinyar zata iya tsayawa agabansa tana masa rashin kunya?me ta taka ?wacece ita?daga ina take ?wllh saiya nuna mata shi ba sa'an yara ƙanana bane irinta.haka ya fito daga cikin motar zuciyarsa ba dadi,fuskar nan kamar hadari,ya wani hade ta sosai. Cikin izza da tsarin tafiya irin na sadaukan maza yake tafiya,duk inda ya keta ƙamshine kawai ke tashi.kai tsaye ya nufi dakin dayasan ana kwantar da ahalinsa idan sunzo asibitin, ahankali ya tura ƙofar bakinsa dauke da sallama. Gaba ɗaya suka juyo cikin hanzari,jin Muryar Aslam,granny ce ta mike da sauri tayo gurinsa,ɗauke da madaukakin farin ciki"Asalamu, kaine nake gani ko ido nane? Allah mun gode maka, shegun masu jan kunnen can sun gyale mini jika"Ta fada tana kamo hannunsa. Baice komai ba kawai kallonta yayi tare da danyin murmushin yake. "Wllh kuwa shine,sai dai har yanzu bakin halin yana nan,yaro saikace kafuran farko,kullum cikin ƙunci?ai wllh maganin wannan halin naka aure,shine kawai zai daidaitaka tunda ka koyi halin yahudawa"ta fada tana mai taɓe baki. Wani shegen kallo Aslam ya watsa mata kafin ahankali ya furta"ba saikiyi min auren ba,tunda akanki nake zaune"yana faɗin haka ya zare hannunsa ya nufi gadon da daddy ke kwance. "To dan tijara Ni kake fadawa haka?wllh zaka gane kai karamin tijararrene,banza basamuden wofi kawai,daga zuwanka ana murna zaka fara yiwa mutanen nonsi ,(wai tana nufin nonsense)lol. Ta fada tana komawa gurin data tashi tare da turo baki,wai adole tayi fushi. "Daddy sannu, hankalina yayi matuƙar tashi,lokacin da Mommy ke sanar dani abinda ya faru,amma Daddy an sanar da hukuma kuwa"?Aslam ya faɗa fuskarsa ɗauke da damuwa. Shafa kansa Daddy Yayi kafin yace"karka damu Aslam jikina da sauki,kuma yan sanda nata bincike akan al'amari,sannu kasha hanya "Daddy ya faɗa yana murmushi,dan yaji dadin ganin dan nasa. Gadon da Aman ke kwance Aslam ya koma,tare da shafa kan Aman ɗin yana mai faɗin"boy sannnu ya jikinka" Murmushi Aman yayi yace "da sauki yaya kasan am strong like you"murmushi Aslam yayi tare da kallon mommy,wacce ta kawar da kanta daga kallon Aslam,duk da irin dadin da taji lokacin daya shigo dakin,amma tana son nuna masa kuskurensa na kin dawowa gida. Lumshe ido yayi, da kokarin kawar da damuwarsa,kafin ya nufeta.yana zuwa ya rungumeta tare da ɗora kansa akafadunta. Cikin salon sa na barikanci yake faɗin"am sorry my love,nayi kuskure bazan ƙara ba kiyi hakuri,kinji?Please ki rungumeni, kona samu sassauci cikin zuciyata. I miss You alot"ya faɗa yana kara kwantar da kansa sosai tare da lumshe idonsa. Abinka da uwa da ɗa,tuni mommy taji zuciyarta tayi sanyi,ta rungume danta ajikinta sosai tana mai sauke ajiyar zuciya,sannan ta shafa kansa tace "i miss You too sweetie,fatan bazaka kara komawa London ba"ta fada tana ɗan kamo kunnensa. "Wayyo my love kunne na zai cire"Aslam ya faɗa cikin shagwaba,kamar ba shine ya gama horancewa yanzun ba. Dariya sukayi harda Daddy,Dan yasaba ganin wannan tabarar ta Aslam idan yana gaban mommynsa. Hararar Aman Aslam yayi yana mai faɗin"kai Ni kakewa dariya ?"ya faɗa cikin ɗaure fuska. Da sauri Aman ya tsaida dariyarsa ya fara dan tari yana faɗin "mommy ruwa!ruwa mommy na kware"yana faɗa yana kallon idon Aslam.Dariya Daddy Yayi yana mai fadin"ai fa horo ya dawo,yanzu kowa zai nutsu" "Ohh ni yar nan,naga abinda yafi karfina, na shiga uku na lalace,wannan wane irin zamani muke ciki,yanzu ke kuwa yar nan agabana,kike kama danki na fari kina runguma?kai wannan tijara tayi yawa,wllh kiji tsoron Allah,wannan ba halin kwarai bane ,dan fari kunyarsa akeji bawai kayi ta jansa ajikin kaba "granny ta fada tana hararar mommy. Jannat da tunda Aslam ya shigo dakin batace komai ba,sai sake nutsuwa da tayi dan gudun karta saba layi, yanzun nan taci na jaki,sai lokacin ta kalli granny tace "kuji granny,Ina ce nan kike ta ihun kuka kina anuna miki danki,kin shiga ukunki shi kadai gareki karya mutu,lokacin da aka kawo Daddy asibitin nan,amma yanzu zaki wani hana mommy nuna wa danta soyayya"jannat ta fada tana hararar granny. "Jannatu kaniyarki,kunji yarinya da salon munafurci da iya kulla sharri? wallahi idan baki fita harkata ba,zan zage mu muci uwar sabada dake aɗakin nan,kinsan ba tsoron ki nake jiba"granny ta fada cikin masifa tana gyara mayafinta. Daddy ne yayi ta ba granny haƙuri Dan ta day zafi sai masifa take,sannan yasa jannat ma ta bata hakuri,kafin granny tayi shiru da maganar,dan sai babatu take tana faɗin wllh sai su doku da yarinya. Sai da aka kira magrib sannan suka fara shirin tafiya gida,dan kuwa bakwai ake fitar da yan jinya,saboda tsarin asibitin mai zaman jinya baya kwana ,saidai kazo da safe ka tafi da yamma. Haka suka taho gida gaba dayansu,mommy da Aslam agaban mota,sai jannat da granny abaya,ana ta gwabzawa. Suna zuwa suka tarar da Hanan zaune afalo tayi gurum,cike da tsoro,tana ganinsu ta tashi da sauri ta rungume mommy sai kuka. "Mommy wllh waccan Islam ɗin ba mutum bace ,kuje kuga abinda tayiwa dakina dazun nan,da idona naga kayan dakin suna jijjiga da kansu. Cike da mamaki suke kallon ta,"jijjiga kuma kamar yaya"mommy ta fada tana dagota. "Muje ku gani kawai mommy"ta fada tana kamo hannun mommyn suka nufi sama. Dama tuni Aslam yayi shigewarsa ɗakinsa,dan ya gaji sosai,so yake yayi wanka sannan yaci abinci ya kwanta. Suna zuwa ƙofar dakin Hanan,mommy ta kama ƙofar ahankali ta turata "Ikon Allah "mommy ta fada cike da mamaki tana kallon dakin..... Masu karatu muje zuwa, Sannan mun kusan kammala free page,Dan haka mai buƙatar littafin nan yayi saurin biyan kudin sa,kar sai munyi kisa sannan mutum yace yana so,mun riga mun wucesa. Mrs babi ce💘💘 Share and comment fisabilillah. [9/9/2022, 12:08 PM] Abk: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 🎄🎄RAINON DAWA🎄🎄 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free page 15/16 https://facebook.com/groups/943534712916776/ Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din👆🏽 GAMASU SON BIYAN KUDIN WANNAN LITTAFIN ZAKU BIYA KAMAR HAKA. NORMAL GROUP 300₦ UPDATE BIYAR A SATI. SPECIAL GROUP 500₦ UPDATE BAKWAI ASATI. SAI KUMA MANYAN HAJIYOYI MASU SON ATURA MUSU PRIVATE ZAKU BIYA. 1000₦ DUK ZAKU BIYANE TA WANNAN ACCOUNT ƊIN. SARATU KABIR U.B.A 2215749011 Sai kun zo. _______________Da zuwan su bakin ƙofar dakin na Hanan,mommy ta sanya hannu ahankali, tare da murɗa handle ɗin ƙofar ta buɗe. "Ikon Allah"mommy ta faɗa cike da mamaki tana kallon cikin dakin. Cikin rawar murya Hanan ta ce"kin gani ko mommy?wllh dama na faɗa miki,da idona naga kayan daƙin suna rawa,har gadon da take zaune ma rawa yake"Hanan ta fada cike da tsoro tana ƙara buya abayan mommy. Turo ƙofar ɗakin mommy tayi, gaba ɗaya kofar ta wangale,ta yadda kowa zai hango abinda ke cikin ɗakin. Da sauri jannat da granny,suka leƙa ɗakin, dan ganewa idanunsu abinda Hanan ɗin ta fada. Sai dai cikin mamaki granny tace "a'a yau naga ikon Allah,hannatu me kike son nuna mana ne wai? Nidai banga komai cikin ɗakin nan ba,banda Islama dake ƙwance akan gadonki?" Granny ta faɗa tana nuna cikin ɗakin da hannunta. Da sauri Hanan ta bar bayan mommy tana mai leƙa dakin nata.ikon Allah dakin yana nan a yadda yake,hatta madubin daya fashe dazu,gashinan ƙalau ama'ajiyinsa,to me hakan ke nufi?ko dai idonta ne yayi mata gizo ɗazun? "Hanan kullum ina yawan faɗa miki,ki daina saurin adar da magana idan baki tabbatar da ita ba,bana son karya,ta yaya kayan daki zasu kama rawa? kamar wasu ƴan gidan gala?"mommy ta fada tana kallon Hanan. "Wllh mommy na gani,da idona na gani, lokaci. Da yaya yazo harya mareta shine ta dawo daki, nikuma na biyota dan In rarrasheta,kawai naga komai na dakin yana rawa"Hanan ta fada da iyakar gaskiyarta, tana marairaice fuska. Tsaki mommy tayi tace"saboda bashi da hankali,daga zuwa saiya kama marin ƴar mutane baisan ko wa ce ce ba?mtsss tayi tsaki tare da barin bakin ƙofar ta shige dakinta. Granny kuwa harara ta bankawa Hanan tace "banza wawiya marar hankali,inaga dai kin fara shaye-shaye ne, da ki ka sha shine take gaya miki ba dai-dai ba,yo Allah na tuba ko lokacin da muke yan mata da akayi yayin aljana yar caras,ai bantaba jin wai kayan daki suna rawa ba,bare yanzu. yara sai rashin hankali kawai da sangarta kuka iya"granny ta faɗa tana barin gurin itama. Kallon jannat tayi wacce ke tsaye ba tace komai ba tunda suka zo gurin. "Wllh anty jannat ba ƙarya nake ba,da idona naga tana kallon kayan dakin nan suna girgiza"Hanan ta fada tana kamo hannun jannat. Ajiyar zuciya jannat tayi,kafin tace "ki barta kawai,idan ma wani tsafin takeyi,wllh saina tona mata asiri,dan nikam wllh na tsaneta bana ƙaunarta ko kaɗan,dama wannan kyan nata ai ba irin na mutane bane"jannat ta fada tana hararar Islam dake kwance akan gado, kuma da alama barci ma take. "Kinsan me za'ayi? Jannat ta fada tana kallon ƙanwarta. Girgiza kai Hanan tayi,tana kallon jannat ɗin. "Kizo mu shiga ɗakin nan muyiwa shegiya dukan tsiya, ta yadda tana tashi zatace barin gidan zatayi,kinga mun kawo ƙarshen tsafin nata"jannat ta fada tana wani girgiza jiki. "Nifa anty jannat wllh tsoro nake ji,ba ruwana sai dai ke ki dake ta,amma Ni ba ruwana"jannat ta fada cike da tsoro tana gwabe fuska. Hararar ta jannat tayi, kafin tace "banza ƴar kut........uba, matsoraciya kawai,Ni bari ki ga abinda zanyiwa shegiya"tana faɗin haka ta kunna kanta cikin dakin,har bakin gadon taje ta tsaya akan Islam dake kwance. Ahankali Hanan ta shigo cikin daki,ta tsaya daga can jikin ƙofar bayan ta kulle. Wayar caji jannat ta ciro tare da dagawa da nufin zabgawa Islam,sai dai duk yadda tayi ƙoƙarin sauƙe hannun fir yaƙi sauka,cikin razana da tsoro ta daga kai tana kallon hannun nata dake tsaye kamar sanda,kawai ba zato ba tsammani,taga hannun nata ya fara zabga mata wayar cajin nan ajikinta. Ihu ta fara cikin razana da azaba,tana faɗin dukan kanta"wayyo Allah, na shiga ukuna,wayyo mommy kizo ki taimakeni, Hanan zoki taimakeni,wayyo bayana"abinda jannat ke faɗi kenan tana ihu,dan sosai dukan ke ratsa mata jiki. Hanan kuwa tana tsaye bakin ƙofa,amma ita a idonta ba abinda take gani,face yayarta tsaye bakin gado tana kallon Islam,sam bata jin wannan ihun da Neman taimakon da jannat keyi. Duka sosai jannat ta sha, kafin aka warɓar mata da hannun ya bugi, gefen gado. Ihu ta sake kwallawa cikin azaba ta nufi bakin ƙofa tana kuka.ai da gudu ta buɗe kofar dakin ta fice. Kallo Hanan ta bita dashi kafin itama tayi saurin ficewa daga ɗakin. Suna fita Islam ta buɗe idonta,tare da sakin murmushi. Tashi tayi ta zauna akan gadon tace "gobe ma ki ƙara tunanin zaki doke ni ki gani,da sannu duk saima gyara muku zama,har wancan basamuden yayan naku, marasa tarbiyyar kawai. Tana gama faɗin haka ta tashi ta nufi toilet. Jannat kuwa dakinta ta shiga da gudu ta buya alungun gado,kuka take sosai tana sosa jikin ta,wanda yayi burɗi -burɗi tsabar duka. Hanan ce ta ƙaraso kusa da ita tana faɗin"anty jannat lafiya kike kuka?me kuma ya faru?naga lafiya kika fito daga ɗakina ? Ta fada tana kallon jikin Hanan da yayi ruɗu-ruɗu da sawun bulala. "Ubanki ne ya faru,shegiya muguwa,lokacin da nake cewa ki kawomin ɗauki inace tsayawa kikayi kina min dariya?wllh gaba ɗaya saina ci kan ubanku keda matsafiyar can,ficemin daga ɗaki"jannat ta fada cikin tsawa tana zarewa Hanan ido. Da sauri Hanan ta bar ɗakin tana mamakin me yasa mu yayar ta ta haka?gaba ɗaya jikinta yayi burɗi-burɗin duka. Aslam kuwa yana shiga ɗakinsa,wanda yake gyare tsaf,dan kullum sai an gyara masa dakin,ko yana nan ko baya nan,kuma masu aiki basa shiga dakinsa,dan shi mutum ne mai tsantsani, sai dai mommy ko jannat. Kayan jikinsa ya cire daga shi sai single da boxer ya shiga toilet ɗin. Cire boxer da single yayi kafin ya tsaya jikin shaya,tare da sakawarwa kansa ruwa. Ba abinda idonsa ke hasko masa,sai fuskar Islam,da irin rashin kunyar data shuka masa,wani baƙin cikin ne ya turnuke masa zuciya sai huci yake yana dukan bango,wai wa ce ce wannan yarinyar? Me take taƙama dashi? Runtse ido yayi da ƙarfi yana sauƙe ajiyar zuciya, kawai yaji hannu ta bayansa ana goga masa soso,da sauri ya buɗe idonsa,yana kallon toilet din,Amma ba kowa,hakan yasa shi,ƙara rufe idonsa, saidai kuma da sauri ya sake buɗe idonsa,jin kamar ruwan wanka ya sauya yanayin da ya fara wanka dashi,aikuwa yana bude idan sa,yaga cewar,jini ne ke sauka daga jikin shayar,wato da jinin yake wanka, Cikin hanzari da zafin nama ya ja baya yana kallon shayar cike da mamaki, jini ya gani yana ta zuba daga jikin shayar,da sauri ya maida kallonsa jikinsa,nan ma jinin ya gani duk ya bata masa jiki. Runtse ido yayi gabansa na mugun faɗuwa,kusan minti biyu kafin ya buɗe idon nasa,kallon shayar yayi,sai kuma yaga ruwa ne normal yake sauƙa,da sauri ya kai kallonsa jikinsa,nan ma ba jinin sai ruwa dake ɗiga ajikinsa.ajiyar zuciya ya sauƙe,yana kallon ko ina na toilet ɗin, kafin ya koma jikin shayar, wankan kan sa ya karasa kafin ya janyo towel ya daura tare da yin alwala,sannan ya fito. Sai dai yana ta mamakin abinda idanunsa suka gane masa yanzu a toilet ɗin,to ko dai idonsa ke masa gizo?amma tabbas jini ya gani mai makon ruwa, yana zaune bakin gadonsa yanashafa mai, kamar wanda akace ya ɗago kansa, kawai kalli madubi,hoton mace ya gani zaune abayansa,ta jingina da jikin gadon, da sauri ya mike tsaye yana mai duba bayansa,amma baiga kowa ba,shiru yayi yana tunani cikin zuciyarsa,wai meke faruwa da shine? Kodai yayi gamo ne?amma koma dai mene ne Allah yafi karfinsa. Wayar mommy ce ta katse masa tunaninsa,dauka yayi tare da karawa akunnensa, Mommy ce ka sanar dashi ya fito suci abinci,to kawai yace kafin ya kashe wayar yayi waje. Duk suna zaune akan danning table,gaba dayansu,shi kadai suke jira,jannat na zaune ta kafe Islam da ido cike da tsana da tunanin ɗaukar fansa, ita kuwa Islam,wacce ke zaune itama kusa da granny fuskarta Sam ba alamun wasa,ta haɗe rai sosai kamar bata taɓa dariya ba,Hanan ma tana zaune kusa da jannat tayi tsumu,gaba ɗaya atsorace take. Ƙamshin turaren Aslam be ya saida musu zuwansa, dan shi idan yazo guri,to turaren sa ke fara muku sallama kafin shi. Yana zuwa yace "hi Mom barka da dare"ya fada yana mata side hug kafin ya zaune akan kujera. "Barka Aslam ka fito? dama kai muke jira tun dazu" "Ohhh Ni jikar dubure,idon da ranka kasha kallo,wai wannan gardin ke wani ƙwaƙumar uwarsa yana faɗin haye mam,gaba daya ka dauko al'adar yahudawa.wannan bakar tijara har ina"granny ta fada tana kama kumatu. Banza Aslam yayi da ita, sai harara daya watsa mata,ya fara cin abincinsa da aka zuba masa,sam hankalinsa bai kai kan Islam ba,baisan da ita agurin ba. Sai tsinkayo maganar ta da yayi tana faɗin"ke malama wai meye kika ƙura min ido kamar wata mayya?ko naci bashin kine? Nifa bana son kallo arayuwata,wllh idan baki daina kallona ba saina ƙwaƙule miki ido"Islam ta fada tana zazzarewa jannat ido.da sauri Aslam ya ɗago kai , Baki buɗe ya ke kallon Islam,wai wannan wa ce ce ne?me ye alaƙarta da gidansu?meyasa takewa kowa hawan ƙawara ne?me ta taka? Cikin ɓacin rai da jin haushi jannat tace "an kalleki dan uwarki,kiyi abinda zakiyi, shegiya gaki nan babbar mayya, ido kamar kwaruru, wllh saina rama abinda kikayi min, duk iya tsafin ki ,sai dai kiyi ki barni,banza ƴar tsintuwa yar bola,wayasani ma ko ke ɗin shegiya ce kizo mana gida zaki..... Tasss! Tasss!!kake jin saukar maruka akan kumatun jannat,ihu jannat ta kwala tare da dafe kumatunta "Wayyo mommy na shiga uku,ta ciremin haƙora"jannat ta fada cikin kuka tana rike da kumatun ta ga gefen bakinta yana zubda jini. "Wllh idan kika sake zagina ,saina miki wanda yafi wannan,dan Ni bana tsoron kowa, ki tambayi babanku kiji,da gyar suka lallabani na biyosu,dan haka baku isa ku wulaƙanta Ni ba,dan niba baiwarku bace, kuma Ni ba wulaƙantacciya bace, kuma ba ruwana da girman jikin mutum wllh saina rama abinda akayi min,dan Ni rainon dawa ce bana ɗaukar raini"Islam ta fada cikin huci tana hura hanci. Mamaki,al'ajabi gaba ɗaya sun rufe Aslam,yama kasa cewa komai,kawai kallon Islam yake cike da madarar mamaki, Granny kuwa dariya ta sanya harda tafi tace "ahayye wallahi isilama kinyi min dai dai,wannan ja'irar yarinyar dama ba abinda ta iya sai rashin kunya, bata ganin kowa da gashi,na baki dama duk wanda ya taka ki,ki takashi,wllh karki rage masa ehe"ta kai zancen ta tana sanya lomar tuwon shinkafa abakinta. Shiru mommy tayi kawai tana kallon Islam,abinda ta lura dashi,Islam yar rigima ce, bata yarda ayi mata ba dai-dai,kuma yanzu dai kam,jannat ce bata da gaskiya,dan haka cikin murya mai taushi,mommy tace "kinga Islam yi haƙuri zauna kici abincin ki,ke kuma jannat bana son irin wanann halin naki, mutum ba abin wulaƙantawa bane"mommy ta fada cikin muryar gargaɗi. Kallon mommy Jannat tayi cike da mamaki,tace "mommy kina gani fa marina tayi, kuma agidan ubana,Ni sa'arta ce" "Na gani masu uba,ai uban naki shine ya kawo ta,dan haka bana son fitina"mommy ta fada cikin haɗe rai.duk da har cikin zuciyarta,taji zafin marin da Islam tayiwa Jannat ɗin,amma bata son ta zamo marar adalci. Da gudu jannat ta bar gurin tana kuka tayi dakinta. Kallon mommy Aslam yayi cike da mamaki yace "mommy wannan shine hukuncin da zakiyi kawai?kina kallo wannan jakar yar ƙauyen ta zabgawa jannat mari,Wanda ahaife nasan jannat ta fita,amma rarrashinta ma ki ke yi mom ? Meke faruwa ne mom,wa ce ce wannan yarinyar agareku,?meye matsayinta agidan nan?WHO the hell is she"?ya fada cikin matsanancin ɓacin rai, yana ture flate ɗin abincin dake gabansa,tare da mikewa tsaye . "Ni zan faɗa maka ko Ni wa ce ce da kaina" Islam ta fada tana matsowa kusa da Aslam cikin yanayi na nuna rashin tsoro ta tsaya agabansa tana kallon cikin idonsa..... To fa Muje zuwa masu karatu,mun kusa gama free page, mai bukata yayi payment kafin mu Dora da paid page. Mrs babi ce 💘💘 Share as much as you can.[9/11/2022, 12:40 PM] Abk: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 🎄🎄RAINON DAWA🎄🎄 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers🎄🎄 Free page 17/18 https://facebook.com/groups/943534712916776/ Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din👆🏽 GA MASU BUƘATAR BIYAN KUDIN WANNAN LITTAFIN ZAKU BIYA KAMAR HAKA. NORMAL GROUP 300₦ UPDATE BIYAR A SATI. SPECIAL GROUP 500₦ UPDATE BAKWAI ASATI. SAI KUMA MANYAN MATA MASU BUƘATAR ATURA MUSU PRIVATE,ZA KU BIYA 1000₦ DUK ZAKU BIYANE TA WANNAN ACCOUNT ƊIN. SARATU KABIR U.B.A. 22 15749011 SAI KUN ZO. ______________Tsaye ta yi a gaban Aslam,tare da kafe shi da idanuwan ta,masu matuƙar ɗaukar hankali,ko kaɗan ba alamun tsoro ko shayinsa atare da ita.wani shegen kallo take watsa masa,tana ɗan jijjiga jikinta,kusan minti ɗaya tana kallonsa kafin ta buɗe baki ta fara magana. "Ni nan Islam,rainon dawa ce,bani da kowa sai malami na,sannan Ni ba kowa bace cikin gidan nan,sai dai fa,ba wanda yake da ikon hana ni yin abinda raina ke so,ko kuma ya hanani gyara abinda na ga ba dai-dai bane, zan gyara wa kowa kuskuren sa,koda kuwa gemunsa na jan ƙasa--tayi shiru tana sauƙi ajiyar zuciya kafin taci gaba ---wannan shine alaƙa ta da gidan nan,fatan ka gamsu Mrs arrogant"? Ta fada tana dage gira guda ɗaya. Shiru kawai Aslam Yayi, mamaki al'ajabi da kuma kallon iyakar ƙarfin hali,sun hanashi koda yin ƙwkwƙwaran motsi,she can't believe,ace wanann ƙaramar yar tsakuwar ke tsaye gabansa tana fada masa waɗan nan kalaman,a gaban mommy,kuma mommy tayi shiru. Kallon Islam yake cike da mamaki,kamar yadda itama ta kafeshi da ido. Jinjina kai yayi kafin yace cikin zazzafar murya"lallai ke ƙaramar karuwa ce yarinya,amma ki sani Ni Aslam bana ɗaukar raini,zan gyara miki zama,da sannu zaki sauke wannan rawar kan naki,kuma ki gane ,nan ba gidan ubanki bane,baki da ikon gyara kowa cikinsa,sai dai ke agyara miki zama,wllh badan ina tsoron abinda zai biyo baya ba,da saina tattaka ki agurin nan,sai dai nasan duka ɗaya idan na miki mutuwa zaki,amma da sannu zaki san waye Aslam"yana gama faɗin haka yayi hanyar ɗakinsa,ba tare da yaci abincin ba. Kiran sunan sa mommy tayi"Aslam! Aslam!!ka dawo kaci abincin mana"mommy ta faɗa cikin daga murya,dan har yayi nisa tsabar yadda yake sauri jikinsa na rawa. Cikin muryar fushi yace "No thank mom,tunda kin samu wannan abar,inaga idan ita taci baki buƙatar mu muci"ya faɗa cikin zafin rai yana juyawa yaci gaba da tafiya. "Kar yaci mana mommy,ki barshi,ai cikinsa ne,banza mai baƙin hali irin na kafuran da"cewar Islam kenan tana komawa inda ta tashi,tare da zama.haushin Aslam takeji sosai,ya cika girman kai da faɗin rai,kamar wani uban mutane. Karaf maganar Islam akan kunnen Aslam,runtse ido yayi cikin mugun jin zafi azuciyar sa,da hanzari ya kara sauri dan barin gurin,dan wllh idan yaci gaba da sauraron muryarta,tabbas zai shaƙe wuyanta,kuma bazai barta ba sai yaga bata numfashi. Yana shiga ɗakin sa,ya fara watsi da duk abinda yaci karo dashi,zuciyarsa kamar zata kama da wuta,ba abinda yake bukatar ahalin yanzu kamar ya kasance da wacce zata kore masa damuwa,gashi agida yake ya zaiyi kenan,haka yayi ta haukarsa yana fashe fashe,yayi alƙawarin saiya koyawa yarinyar nan hankali,ta yadda ko hanya baza ƙara bari ta haɗa su ba,gaba ɗaya ya yanke hannun sa,amma ko ajikinsa,ganin idan yaci gaba da zama zai je ya mutu da baƙin ciki ne adaki,hakan yasa yayi saurin zarar,mukullin mota yayi waje. Lokacin daya fito afusace,Islam na cin naman rago da akayi farfesun shi,hankalinta kwance. Granny na faɗin"ai Ni wllh jarumtar ki tana burgeni ƴar nan,kin iya koyawa mutum hankali,wllh halin mu ɗaya dake,Ni nan da kika gani,lokacin inada shekaru kamar naki,tsabar masifar faɗa yar dambe ake cemin,dan Ni in zage mu dambatu da mutum ba ƙaramin aikina bane,sam bana ɗaukar raini.amma dai kiyi ahankali ɗan kuwa Aslam yana da baƙar zuciya,duk sanda ya kamaki ahannun sa,wllh zaki daku"granny ta fada tana kai ƙatuwar tsoka bakin ta. "Tab ai wllh sai-dai mu doki juna,dan bai isa ya dakeni in gyale shi ba wllh,shida ba ubana ba,kuma bashi ya kawo Ni gidan ba"ta fada cike da rashin tsoro tana murguda baki. "Ai kuwa dai sai dai kiyi iyakar ƙoƙarin ki,dan Aslam mugune"cewar granny tana taɓe baki,tare da hararar mommy. Mommy dai tana zaune bata ce komai ba,tayi shiru tana tunanin ta yadda zata bullowa,al'amarin,dan bazata zuba ido Islam tana yiwa manya rashin kunya haka ba,koba komai,akwai buƙatar anuna mata matsayin wanda ya girmeta,tunda Ita dai bata fahimci ba'ayiwa babba rashin kunya ba,amma dole ta jata jikinta,ta nuna mata abinda ya dace. Hanan kuwa tsabar tsoro da fargaba sun hanata cin komai,ji take kamar tayi fitsari a wando,dan tasan Islam ta janyo musu cin uba. Kai tsaye Aslam ya nufi ƙofar fita daga gidan,banda rawa ba abinda jikinsa keyi,duk irin kiran da Mommy keyi masa,baiko juyo ba,bare ta sa ran zai kulata. Dafe kai kawai mommy tayi tana fatan Allah ya tsare mata shi. "Barshi,ya tafi ɗan tijara Ni dai bazan bari a cutar da ƴar nan ba wllh" cewar granny tana bin bayan Aslam da harara. Suna kammala cin abincin,granny ta kama hannun Islam tace "kinga taso mutafi can dakina,anan zaki zauna,dan In koya miki dabaru na zaman duniya ,da yadda mutum zai ƙwaci kansa ako ina ne"ta fada tana kama hannun Islam suka nufi ɗakinta dake ƙasa ,kusa dana Aslam.dan dakunan mazan a ƙasa yake. Da sauri mommy tace "Amma granny da an barta tare da Hanan,zata fi sakewa" "An ƙi abar tan,ke bana son shishshigi fa,ina ce ɗana ne ya kawo ta gidan?to ki barta ba ruwanki aguri na zata zauna"tana gama faɗin haka suka wuce ɗakin nata. Girgiza kai kawai mommy tayi, tana jin ba daɗi cikin ranta. Hanan ma tashi tayi tace "mommy Bari naje ɗaki, zanyi assignment ,ta fada ranta fess, Dan dama tsoron kwana take tare da Islam ɗin"jinjina kai mommy tayi ba tare da tace komai ba,hanan ta wuce ɗakinta. Ita kuwa zama tayi agurin tana jiran dawowar Aslam. Shikuwa Aslam yana fita daga gidan,yayi tafiya mai nisa cikin fushi,kafin ya sami gefen titi yayi fakking yana zaune shiru,kusan minti uku,kafin yayi saurin zaro wayarsa,wata number ya kira tare da karawa akunnen sa. "Ki na ina?ya faɗa cikin angry voice ɗinsa. Ita kuwa wacce ya kira ɗin,cikin rawar jiki take amsa masa"ina gida Aslam,saukar yaushe?"ta faɗa cike da ɗoki. "Ki sameni nan kusa da anguwar ku, bakin plaza yanzu "yana gama faɗin haka ya kashe wayar tare da runtse idonsa,tunani fal cikin ransa,na irin uƙubar da zai yiwa waccan yar tashar. Cikin zumuɗi yarinyar ta mike dama tana sanye cikin wata doguwar riga wacce bata wuce ƙwaurinta ba, gashi ta kamata damm, ajikinta,dan haka turare ta fesa ajikinta,sannan ta kara gyara fuskarta,ta janyo wani dan siririn mayafi ta fice daga gidan,bata ko sanar da mahaifiyar ta ba. Kai tsaye inda yace mata nan ta nufa da motar ta,yana hango ta ya kunna hasken motar,dan ta gane shine. Aikuwa da zumuɗi ta ƙaraso gareshi,fitowa tayi daga cikin motar ta,ta nufi tashi,cikin kwarkwasa,da tafiyar jan hankali. Shikuwa ya kafeta da ido kamar tsohon maye,tana shigowa cikin motar ƙamshin ta ya kara tunzurashi,ga ɓacin rai. Ba bata lokaci ya janyota jikinsa ya fara aika mata saƙonsa mai wuyar gogewa. Ita kuwa daɗi kamar ya kasheta,tana matukar kaunar Aslam,Amma shi sam baya ta Tata,lallai yau dama ce agareta.dan haka ta zage itama tana sauke masa hadda. Kusan awa guda suna romancing juna cikin motar,gaba ɗaya sun fice daga hayyacin su,burinta kawai Aslam Yayi sex da ita,sai dai duk yadda taso da hakan ya faru,sam Aslam yaki bata haɗin kai,daga ƙarshe ma ture ta yayi daga jikin sa tare da jingina kansa jikin kujera, yana sauƙe ajiyar zuciya da sauri da sauri. Cikin mutuwar jiki da buƙatuwa ta matso jikinsa tana shafa ƙirjinsa tare da ƙoƙarin zare belt ɗin wando jikinsa. Hannunta ya rike tare da cirewa daga jikinsa .sake maida hannun tayi tana mai faɗin"haba Aslam ya haka?kasan dai idan muka bar juna ahaka zamu cutu,Please ka bari miji daɗin mu mana"ta faɗa tana ƙara maida hankali wajen son cire belt din,sannan tana ƙoƙarin haɗe bakinsu guri ɗaya, "Stop !!!" Ya faɗa cikin daka mata tsawa, yana huci cikin zafin rai,dan shi maimakon yaji zuciyarsa tayi sanyi, sai wani ɓacin ran ne ma ya kara mamaye zuciyarsa. Da sauri ta zare hannun ta tana kallonsa cike da sha'awa.tana maida numfashi,gaskiya guy ɗin nan ya kwafsa mata,saida ya tada mata hankali,sannan zai wani gyaleta,gashi sam yaƙi bari ko ɗan tsotsar lips ɗin sa tayi, amma ba komai in Sha Allah saita Sami Abunda take so agareshi. "Fice min daga mota"ya faɗa cikin haɗe fuska ba tare da ya bude ido ba. Kallonsa tayi cike da ƙauna,kafin tace "Please Aslam,idan kana so ma Ni sai in bika can gidan mu kwana "ta fada cikin marairaicewar murya, Wani shegen kallo da ya watsa mata ne yasata sunkuyar da kai ba shiri. "Saboda ke daƙiƙiya ce ko?saina ɗauki karuwa na kai gidan mu,gaban iyayena ko?"ya faɗa yana mai kafeta da jajayen idanunsa,wanda jaraba da masifa ta sa suka rinar masa da su. Cikin rausayar da kai tace "Ayya Aslam ba haka nake nufi ba, dan Allah kayi hakuri,naga kamar ranka aɓace yake,shiyasa nake ƙoƙarin sanyaka farin ciki, amma kayi hakuri"ta fada cikin sanyin murya tana mai sunkuyar da kai. Tsaki yayi tare da cewa"ki tafi gida,zan nemeki, kuma wllh idan har naji labarin kina kula wani dan iskan,wllh saina ci uwarki kinsan halina"ya faɗa yana dage gira ɗaya. Jinjina kai kawai tayi,tana gyara rigarta, sannan ta fice daga cikin motar. Ya jima agurin bayan tafiyar ta,har lokacin ransa aɓace yake,zuciyarsa sai tafasa take,kallon wayarsa yayi yaga har ƙarfe sha ɗayan dare, ga miss calls ɗin mommy birjik,yasan zuwa yanzu mommy har ta gaji da zaman jiransa,ahankali ya kunna motar tare da juyawa gida.koda yaje gidan,mommy ɓata falon,ta gaji da zaman jiransa ta shiga ɗaki. Kai tsaye shima ya nufi ɗakinsa, dai-dai lokacin kuma ,Islam ta fito daga ɗakin kaka,wai zata je neman janbu ko yana lambun gidan. Tana fitowa shi kuma Aslam yana ƙoƙarin shiga ɗakinsa. Tsaki tayi lokacin data ganshi yana ƙoƙarin shiga ɗakin. "Dole ma asanya doka cikin gidan nan,dan bazamu laminci yawon dare ba, sai mutum yaje ya gama yawon karuwancinsa,sai lokacin da yaga dama sannan ya dawo gida,wllh bazan laminci ganin wannan ɓarnar ba ehe"Islam ta fada cikin daga murya tana buga cinya. Tsaye Aslam Yayi gyam!! abakin ƙofar dakin nashi, shi bai shiga ba kuma bai juyo ba,maganganun Islam ke masa yawo cikin kansa,lallai ya kamata ya nuna wa yarinyar nan asalin karuwan cin nashi,ko zata gane shi ba sa'anta bane. Afusace ya juyo tare da tunkarota kamar wani zaki. Ita kuwa tana tsaye ko motsi batayi ba, jira ma take ya ƙara so taga abinda zai iya mata. Shikuwa yana ƙarasowa ya saɓeta akafaɗarsa,tare da juyawa ya nufi ƙofar fita daga falon. Dukansa ta fara cike da masifa tana faɗin"kai malam meye hakan?wannan wane irin iskanci ne?zaka wani saɓeni akafada kamar yarka,?dalla ka saukeni,bana son iskanci banza bujimin sa kawai"ta fada tana dukansa da iya ƙarfinta.amma ko nuna alamun yana jinta ma baiyi ba.kai tsaye ya nufi boysquaters da ita. Bai direta ko ina ba sai cikin wani ɗaki,mai dauke da babban falo da ɗakunan kwana guda biyu.yana sauke ta ya kulle ƙofar da makulli,kallonsa take cikin rashin sanin me yake nufi da hakan,tace "kai wllh tun kafin raina ya gama ɓaci, ka buɗe min ƙofar nan, bana son iskanci "ta faɗa cikin masifa tana wani kashe ido. Murmushin mugunta yayi kafin ya fara takowa cikin ɗakin,yana tunkarota."me kike ci na baka na zuba,ai zan nuna miki irin nawa salon karuwancin ne,dan ki tabbatar da Ni nafi ƙarfin iya shegenki,dan uwarki "ya fada dai-dai lokacin daya ƙaraso kusa da ita. Ɗan ja baya tayi,dan kusancinsu yayi yawa,har saida taji gabanta na faduwa. "Dalla malam bani guri kaje can ka nemi yar iska irin ka amma Ni nafi ƙarfin ka "ta fada cikin rashin kunya tana ja baya. Runtse ido yayi cikin ɓacin rai,aduniya yana matukar jin ciwon yadda wannan yar yarinyar ke zagin sa,da fada masa baƙaƙen maganganu. Buɗe idonsa yayi da suka ƙara kaɗawa sukayi jaa, yayi kanta kamar zaki yana faɗin"wllh yau saina ci uwar ubanki,zan nuna miki Ni Aslam naci uwarki a iskanci.ya faɗa yana mai fizgota zuwa jikinsa. Baiyi wata wata ba ya fara ƙoƙarin ....... Masu karatu muje zuwa ,da alama Islam fa ta tsokano maza.koya zata kaya ? Ku biyoni sannu kan hankali. Maza kuyi payment ga duk mai bukatar ci gaba da karanta wannan littafin. Sannna ga masu buƙatar wannan littafin,iya maza kawai. Su tuntuɓi wannan number 08067072477. Iya maza kawai. Anty mammy Mrs babi 💘💘 Share as much as you can. [9/12/2022, 11:54 AM] Abk: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 🎄🎄 RAINON DAWA🎄🎄 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 https://facebook.com/groups/943534712916776/ Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din👆🏽 Free page 19/20 GAMASU SON BIYAN KUDIN WANNAN LITTAFIN ZAKU BIYA KAMAR HAKA. NORMAL GROUP 300₦ UPDATE BIYAR ASATI. SPECIAL GROUP 500# UPDATE BAKWAI ASATI. SAI KUMA MANYAN MATA MASU BUƘATAR ATURA MUSU TA PRIVATE ZA KU BIYA 1000₦ DUK ZAKU BIYA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN. SARATU KABIR U.B.A 2215749011 SAI KUN ZO. ______________Cikin zafin nama da ɓacin rai,Aslam ya tunkaro Islam,yana zuwa kusa da ita ya fizgota zuwa jikinsa,baiyi wata- wata ba,ya fara ƙoƙarin cire mata riga. Mamaki,tsoro da al'ajabine suka kama Islam,me kuma yake ƙoƙarin aikata mata haka?me zaiyi da rigarta da yake ƙoƙarin cire mata?cikin nata salon zafin naman ta damke hannunsa,tana mai kallon idonsa,wanda shima ya kafe nashi idon cikin nata, "Me kake ƙoƙarin aikatawa ne?meye nufin ka na cire min riga?ko dai bansani ba cewar da kuɗin ka aka haɗa aka siyi rigar?"ta faɗa cikin zazzaro manyan idanunta. Babban ɗan yatsan sa, ya sanya tare da dalle mata lips cikin salon mugunta,harda cije lips ɗin sa. Runtse ido Islam tayi sakamakon raɗadin azaba daya ziyarci kwakwalwarta. Buɗe ido tayi ta kafesa da su,cikin tsantsar haushi da tsanarsa tace "Allah ya isa na,bazan taɓa yafe maka ba,mugu azzalumi, baƙi mai baƙar aniya,wllh zaka san Ni kayiwa wannan abun"Islam ta fada cikin zafin zuciya da jin raɗaɗin da lips ɗin ta keyi. Shikuwa cikin salon mugunta ya kara sanya hannun sa ya matse mata baki sosai yana huci. Ubanwa kike wa Allah ya isa?Ni sa'anki ne?wllh idan kika ƙara min rashin kunya zakiga abinda zanyi miki,shegiya mai idon mujiya"Aslam ya faɗa yana mai kara matse bakin Islam kafin ya murde lips ɗin ta da ƙarfi,sannan ya saki. Da sauri Islam ta rike bakinta tana sauke ajiyar zuciya,dan shafo lips ɗin ta tayi,cike da mamaki take kallon jinin data gogo daga lips ɗin ta. Kallon sa tayi,kallo irin na tsana da kiyayya,tace "ka sani wllh wannan jinin daya fita daga jikina bai fita abanza ba,kuma wllh sai kaga Abinda zanyi maka akan hakan,banza ɗan iska kawai,Ni ka sakar min riga in fice wawa"ta fada cikin mugun ɓacin rai tana ƙoƙarin cire hannunsa daga kan rigarta,wanda ya damke rigar gan dasu. Kallonta yake,yana jinjina zallar rashin kunya da tsoro irin na wannan aljanar, anya kuwa wannan kanta ɗaya?kodai aljanu gare ta,ko iya kawo ta dakin nan da yayi,ya ci ace ta tsorata ,amma sai kara kaimin rashin kunya take,dole ya koya mata hankali.dan haka karfinsa ya saki tare da matse bakin nata ya buɗe shi,sannan ya tofa mata yawu acikin bakinta. Kuma yayi saurin matse hancin ta,bayan ya haɗata da jikin bango Ya matseta, ji kake ƙut!ta haɗiye yawun daya tofa mata abakin ta.zaro ido tayi cikin mugun tashin hankali tana kallonsa,shikuwa saida ya tabbatar ta haɗiye yawun sannan ya saki hancin nata. Wani irin kuka Islam ta sanya cike da ɓacin rai,ta cakumo shi da iya ƙarfi ta,ta fara kai masa duka ta ko ina,tana faɗin"Allah ya isana mugu azzalumi,ƙazami wllh yadda kasa na sha yawun wannan ƙazamin bakin naka,wllh saikayi nadama,banza bunsuro kawai ɗan iska mai.... Bata sami damar karasawa ba, sakamakon jin bakin Aslam da tayi cikin nata.ƙamewa tayi agurin cikin ruɗu da mafificin tashin hankali. Shikuwa cike da mugunta yake tsotsar lips ɗin ta yana cizon ta,tare da dura mata yawun bakinsa, Ƙut-ƙut, haka take haɗiye yawun cikin rashin sanin abinyi. Shikuwa Aslam da yayi nufin yi mata mugunta,sai yake neman rasa nutsuwarsa ,gaba ɗaya yaji yana ƙoƙarin shiga wani yanayi,hankalin sa gaba ɗaya ya tashi,sosai yake jin daɗin kissing ƙaramin bakin Islam,wanda har ya shagala.ba tare da yayi aune ba kawai yaji an damƙi wuyansa ta baya,da mugun ƙarfi,kamar za'a karya masa wuyan, nan take hankalin sa ya dawo jikin sa, sannan ya fahimci abinda yake aika tawa, da hanzari ya zare bakinsa daga cikin na Islam,wacce zuwa wannan lokacin gaba ɗaya jikinta banda rawa ba abinda yake,idanunta sunyi jajur dasu abin tsoro. Da sauri Aslam ya ture ta daga kusa dashi,yana jin wata irin juwa na ɗiban sa,ahankali,idanunsa ke rufewa da budewa, wani tsalle Islam tayi tare da cafko maƙogaran Aslam,Wanda ya fara fita daga hayyacinsa.saida taga yana neman sheƙawa sanan tayi cilli dashi can gefe guda ya fadi tare da buga kansa jikin bango,nan take idanunsa suka rufe ruff! alamun ya suma.can gefe itama ta fadi tare da runtse idanunta,banda azaba ba abinda lips ɗin ta keyi,gashi ya fashe daga gefe, ya kumbura sosai. Yunkurawa tayi cike da kasala ta nufi bakin ƙofar,tana budewa mai makon ta koma cikin gidan kai tsaye ta nufi garden,kallo ɗaya zaka mata kasan bata cikin hayyacinta. Tana zuwa cikin lambun, ta kama wata ƙatuwar bishiyar mangwaro ta haye samanta tare da kwantawa jikin wani reshe. Runtse ido tayi cikin zafin zuciya da takaici,tunda take ba wani mahalukin daya taɓa mata irin abinda Aslam Yayi mata,wllh ta tsane shi,bata ƙaunar ganinsa,kuma saita rama abinda yayi mata.hawayene ke zuba cikin idonta ba tare da ƙaƙƙautawa ba,shine mutum na farko,daya sata zubda hawaye tun tashin ta ,kuma zaiyi dana sanin yin hakan. Iskace ta fara kaɗawa mai sanyi,tare da wani haske daya mamaye kan bishiyar,hakan shiya tabbatar mata zuwan Malami ta. Cikin ƴan daƙiƙu kuwa saiga malamin nata ya bayyana, murmushi ɗauke akan kamilalliyar fuskarsa. Kallonsa take cikin kuka tana jiran taji me zaice. Ahankali ya sanya wani farin gyalle ya share mata hawayen,kafin ya fara magana"ki daina kuka Islam, kiyi haƙuri da duk wani halin da zaki tsinci kanki agidan nan,domin ƙaddarar ki tana ɗanfare ne da wannan gidan, anan zaki sami farin ciki,bayan haka game da Aslam kece wacce zata sanya shi ya daidaita rayuwarsa,kece zaki bawa rayuwar sa tallafi,komai zai dai-dai, kici gaba da ƙoƙarin faɗin gaskiya komai ɗacin ta,ki shiga rayuwar Aslam sosai,ta hakan ne zaki sami damar gyara masa duniyar sa,ki kwanta kiyi barci babu damuwa cikin ranki,ina tare dake"yana gama faɗin haka ya sanya hannunsa tare da shafar idanun Islam ,cikin abinda ba zai gaza daƙiƙa biyar ba ,Islam ta lumshe ido, nan da nan barci yayi gaba da ita. Washe gari da asubar fari,Aslam ya farka daga suman da yayi,ahankali ya buɗe idanunsa da sukayi masa nauyi,kanshi ya dafe tare da lumshe ido,sakamakon ji da yayi kan nashi na rasa masa. Ɗakin yabi da kallo,na dan lokaci,nan take duk abinda ya faru jiya ya fara dawo masa cikin kwakwalwar sa tirya-tiryan. Ohh shet!!me na aikata haka ne?me ya ruɗeni harna nayi kissing waccan ƙazamar? yanzu wane kallo zata rinƙa min,shikenan sabon raini zai shiga tsakani na da ita,amma bazan taɓa bari ta raina Ni ba,ko yanzu tayi min abinda bai min dai-dai ba,saina hukunta ta wllh.tashi yayi cikin jin ciwon jiki,sannna wuyansa na ɗan masa ciwo,barin dakin yayi ya nufi ɗakin sa. Wanka ya farayi kafin yayi Sallah,da kanshi ya tattare abubuwan daya fasa jiya,sannan ya sanya kayan motsa jiki ya nufi can garden. Islam kuwa koda tayi sallah,kan bishiyar ta sake hayewa tayi zamanta,bayan ta ciri mangoro tana sha.ba abinda take kitsawa,sai irin tijarar da zatayiwa Aslam,tana nan zaune ta hango shi ya nufi gurin da gudunsa yana motsa jiki. Wani sanyi ne ya ratsa zuciyarta,har da sauke ajiyar zuciya.kallon janbu tayi wanda ke kwance kan ruwan cikinta,tace "janbu so nake mu koyawa wancan wawan hankali, lallai karmu barshi har sai munga jini ya fita ajikin sa"ta fada tana kafe Aslam da ido,tana tuno yadda ya dure mata yawun bakinsa a cikinta ta shanye tass. Shikuwa Aslam zuciyar sa daya,yake motsa jikinsa,bayan ya ajiye gorar ruwa da towel ɗinsa ,kusan minti goma sha biyar,sannan yayo jikin bishiyar da Islam ke kai,zama yayi kan wani dutse da akayi masa siffar kujera,da alama,an ajiye shine dan hutawa.towel ɗin ya ɗauka yana goge zufar data jiƙa masa jiki. Ƙwal! Yaji saukar kwallon mangoro akansa.da sauri ya saki towel ɗin yana dafe kansa,dan sosai kwallon mangoron nan ya daki ƙeyarsa.dama gurin yana masa ciwo. Daga kansa yayi yana kallon bishiyar,amma baiga komai ba,dan tana da duhu.gashi kuma da alama ba'a jima da shan mangoron ba.komawa yayi ya zauna,tare da ɗaukar gorar ruwan ya buɗe yana sha.saitin gorar Islam ta saito wani ƙaton mangoro ta jefo masa.ai nan take ruwan cikin gorar ya fito da yawan gaske,sai hancin Aslam,gorar kuma ta faɗi,nan da nan ya ƙware, tari ya fara kamar zai mutu,idonsa ya firfito yayi jajur dashi,durƙushewa yayi agurin yana tari sosai.haba aikuwa nan Islam tayi ta jifansa da mangoro,timm!!timmmm!!!,gaba ɗaya Aslam ya gigice ga tari ga jifa,ya rasa inda zai sanya kansa,ya tashi ma ya bar gurin ya kasa. Cike da murmushin mugunta, Islam tace janbu hau kansa kayi ta yakushin dan banza,sai ka ga jini ajikinsa sannan zaka gyale shi. Aikuwa da gudu janbu ya sauko,bai dire ko inaba sai kan kafadar Aslam,nan yayi ta yakushin sa ajikinsa da fuskar sa. Iyakar ruɗewa Aslam ya ruɗe,sai ƙoƙarin korar birin yake daga jikinsa ya kasa hashi dama yana tsoron biri.janbu kuwa saida ya kai Aslam ƙasa,kuma yaga jini ajikinsa sosai kafin ya sauƙa daga jikin nashi,ya koma kan bishiyar da gudu. Dariya sosai Islam keyi,abun yayi mata daɗi sosai,farin ciki fall zuciyarta,take kallon Aslam,wanda ke sauƙe numfashi,da gyar,yana kwance. Kusan minti biyar ya kwashe kafin ya yunƙura da gyar ya tashi ya nufi gida,gaba ɗaya jikinsa ya kushin birin nan ne. Saukowa Islam tayi daga kan bishiyar tana dariya"kayi aiki mai kyau janbu haka nake so,kuma wllh ban gama ramawa ba, zai gane kurensa"ta faɗa tana murmushi,kafin tace "janbu maza je kaci ayaba son ranka,dan kuwa tunda suka kawo mu gidan nan,bazamu zauna da yunwa ba, duk abinda ranmu ke so shi zamu ci"da gudu janbu yayi kan bishiyar ayaba,ita kuwa ta nufi cikin gidan. Kai tsaye Aslam,ɗakinsa ya nufa,gaba ɗaya jikinsa ciwo yake,wani zazzaɓi ne ma ke ƙoƙarin rufeshi,tunani yake,wannan birin daga ina yake?waye ya kawo shi cikin gidan?ai kuwa Dole afitar dashi yau -yau ɗin nan.kwanciya yayi akan gado tare da lulluɓe jikin sa da bargo,dan kuwa tuni zazzaɓi yayi masa dirar mikiya. Islam kuwa tana shigowa cikin gidan ta wuce ɗakin granny,lokacin granny tana lazimi,taga shigowar ta ko ina ta shiga tun dazu oho? granny ta faɗa cikin zuciyar ta,kafin taci gaba da lazimin ta . Islam kuwa kwanciya tayi akan gadon granny,ba jimawa barci yayi gaba da ita. Misalin ƙarfe tara na safe, gaba ɗaya ahalin gidan suka hallara akan daining dan karyawa, kowa ya shirya,da sun kammala karin zasu wuce asibiti,dan akwai yiwuwar su taho da Aman gida,tunda ba ɗorin asibiti akayi masa ba. Mommy ce tace jannat taje ta kira yayan su,koda taje akwance ta sameshi ya lulluɓe jikin sa. Dan haka ta dawo ta sanar da mommy. Da kanta mommy taje ɗakin nashi,ta ganshi kwance jikinsa zafi sosai. Tambayar sa tayi me ya sameshi yace zazzabi ne ke samunsa,ganin baida lafiya ya sanya ta barshi,amma tace ya sha magani kuma yaci abinci, sannan ta fice,dan tasan jinya bata hana Aslam cin abinci. Koda ta nemi akira Islam,granny ce tace ,a'a barci take abarta ta huta idan ta tashi taci. Haka suka gama cin abincin su suka bar gidan,ya rage daga Aslam sai Islam cikin gidan. Jikin Daddy da sauki sosai dan sosai suka sha hira da ahalin sa,nan yake tambayar ina Islam da Aslam? aka ce masa barci take,Aslam kuma baya jin daɗi.nan suka ci gaba da jajanta abinda ya faru,abokai da yan uwa sai zuwa suke duba su Daddy,asibitin acike da mutane yan dubiya,abinka da mutum mai mutane. Sai kusan sha ɗaya zazzabin ya saki Aslam,Dan haka tashi yayi tare da yin wanka,ya shafa maganin radadi ajikinsa,gefen idon sa har ya kumbura.shiryawa yayi tsaf, cikin riga da wando na farin yaɗi mai kyau da tsada,yayi kyau abin sa. Kai tsaye danning ya nufa ya haɗa tea yana sha. Islam kuwa tana tashi itama wanka tayi,abin mamaki komai ta iya amfani dashi,bata tambayar komai,haka zaka ga tayi abinta kai tsaye,ko ina ta koyi amfani da irin waɗan nan abubuwan oho? Bayan tayi wanka kuma saita rasa wane kayan zata sanya,dan haka fitowa tayi ta nufi ɗakin Hanan dake sama,daga ita sai wani Dan towel Wanda bai karasa gwuiwar ta ba,tafiya take cikin takunta mai jan hankali,da sanya jaruman maza risinawa. Aslam ya kurbi shayi kenan,idonsa ya sauƙa akan ƙugun Islam,wani irin tarine ya taso masa,ba shiri ya watsar da tea ɗin bakinsa,yana ɗan bubbuga ƙirjinsa. Binta yayi da kallo kamar wani sakarai,masha Allah lallai Allah yayi kira agurin nan,kalli yadda take juya hips ɗin ta cikin salo na jan hankali,abinka da dan hannu, nan da nan Aslam yaji yanayi sa ya sauya,sosai jikinsa ya fara nuna alamun bukatar mace,yana nan zaune galau,harta shige dakin Hanan. Sam ya kasa cin abincin,surarta kawai idonsa ke haskowa,tsaki yayi yana mai jin haushin kansa,ya rasa wacce zai wani zauna yana tunanin surar ta sai wannan Shegiyar yarinyar mai kama da aljana,shifa yana zargin ma anya ba da gan-gan take wannan abun ba?dan kawai ta ja ra'ayinsa?aikuwa wllh tayi kaɗan,batakai matsayin da zata ja hankalinsa ba. Kusan minti biyar saiga Islam ta fito riƙe da wasu riga da wando ahannunta.har ta sauko ta nufi ɗakin granny, idonta bai nuna mata Aslam ba ,Wanda ya ƙara Binta da kallo kalauuu!! Saida ta kusan shiga ɗakin sannan taji ajikinta ana kallonta,juyowa tayi karaf idonsu ya haɗe dana juna. Da hanzari Aslam ya kawar da kansa yana jin faduwar gaba. Islam kuwa murmushi tayi tare da juyowa ta nufi inda yake.tsaye tayi akansa tana taɓe baki da kare masa kallo. Shikuwa duk da yadda gabansa ke faduwa, hakan bai hana shi ɗaure fuska ba kamar hadari,yi yayi kamar bai ganta ba ,yaci gaba da ƙoƙarin shan tea ɗinsa. Dariya sosai Islam ta sanya tana nuna shi,runtse ido yayi cikin jin zafi aransa, ya tsani dariya haka kawai ma bare kuma ace shi ake yiwa. "Kai Allah sarki sannnu amma kasha jiki,ai wllh so nayi birin nan ya ƙwaƙwale maka idanu,sannan ya gwagwuye wannan leben naka masu cin haram--ta ɗan dakata tana murmushin wulaƙanci,kafin taci gaba--nasan kana ta tunanin waye wannan wanda yayi maka irin wannan tijara?to albishirin,ka,ba kowa bace face Ni Islam rainon dawa,kuma wllh ban gama da kai ba, ina nan zan ci gaba da ƙuntata maka ,sai kayi dana sanin abinda kayi min"ta kai karshen maganar ta tana hararar sa. Afusace Aslam ya mike tsaye yana kallon Islam,tsabar bakin ciki da takaici,kawai ya dauki kofin tea ɗin nan ya watsa mata ajikinta. Wani irin zabura Islam tayi arazane sakamakon zafin daya ratsa jikinta,dan kuwa tea ɗin akwai zafi sosai,wanda saida yayi sanadiyyar zamewar towel ɗin dake jikinta,nan da nan,albarkatun ƙirjinta suka bayyana muraran,suna kallon Aslam, Dammmm! Dammmmm!! Dammmmm!!!ƙirjin Aslam Yayi wata muguwar bugawa,nan da nan jikinsa ya dauki rawa,yawun bakin da ya ƙame,sakamakon arba da manyan breast ɗin Islam da yayi,suna kallonsa, Azabure yayi kanta cikin gushewar tunani,da rashin madafa..... Wai shin wa ce ce Islam? Waye Kuma Aslma? Shin su waye iyayen Islam? Sannan me alaƙar Islam da malaminta? Hmmmmmmm. Masu karatu, laifin daɗi karewa,anan muka kawo ƙarshen,free page na wannan littafin, Dan haka ga mai buƙatar ci gaba da karantawa,sai yayi hanzarin biyan kudinsa kafin mu ɗoradinnda muka tsaya. Karku manta ,yanzu labarin zai fara. Akwai cakwakiya sosai cikinsa. Mrs babi ce💘💘 [9/19/2022, 2:35 PM] Abk: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 🎄🎄RAINON DAWA🎄🎄 Na mammy kabeer (Anty mammy) Paid page 21/22 Please kada wanda ya fitar min da littafi,dan Allah domin na kuɗine.duk mai so ta biya ta karanta.🙏🙏 _______________Azabure Aslam ya nufi Islam,cikin gushewar tunani da rashin madafa,kai tsaye ya cakumo Islam wacce ke yarfe hannu cikin azaba tana ɗan tsalle,gurin da ruwan shayin nan ya zubo ajikinta kuwa,har yayi jaa sosai kamar zai tashi. Ba ɓata lokaci Aslam ya rungumeta ajikinsa yana fidda wani irin numfashi mai kama da yana neman shiɗewa. Wani irin rawa jikinsa ya kama,sakamon yadda tsinin boobs dinta ke sukar ƙirjinsa, runtse ido yayi da ƙarfi yana mai tura fuskarsa dai-dai wuyanta tare da sakar mata hucin iska daga hancinsa. Itama Islam,wani irin yanayi ne mai matukar wahala agare ta taji yana ziyartar ta,wannan shine karo na farko arayuwar ta, da wani ɗa namiji ya taba rungumar ta ,kuma ba tare da kaya ajikinta ba, Da ƙarfi ta lumshe idon ta,tana sauke tagwayen ajiyar zuciya, abubuwa biyu ne suka tarar mata alokaci ɗaya,na farko raɗaɗin da ƙirjin ta keyi,na biyu rungumar da Aslam Yayi mata ba karamin daga mata hankali tayi ba,jin ta take kamar zata faɗi, jikinta rawa yake sosai,tsoro da fargaba suka baibaye ta, gashi ba ƙaramin dadin yanayin nasu take ji ba,idonta alumshe tana ƙoƙarin kwatar kanta daga gareshi,amma gangar jikinta ta ƙi bata wannan damar. Shikuwa Aslam,sai wani shafa soft fatar bayan ta yake,yana karajin shauƙi fiye da wanda yake ji, gaba ɗaya ya shagala,ji yake kamar bai taɓa jin jikin mace mai ɗumi irin na Islam ba.nan da nan jarabar sa ta motsa hankalinsa yayi ƙololuwar tashi ,sai nishi yake kamar mai zazzaɓi. Cikin ƙanƙanin lokaci,Islam ta dawo hayyacinta,ta fahimci halin da suke ciki ,lallai yau akwai bala'i, wannan azzalumi ne ya watsa mata ruwan zafi?kuma yaga jikin ta?sannan ya rungume ta? Ai kuwa ya taɓowa kansa bala'i wllh. Aslam yana cikin yanayin sa na gushewar tunani da saɓa lamba,kawai saiji yayi an tunkudeshi da mugun ƙarfi,har saida ya buga kansa da jikin bango,da sauri ya dafe kansa,yana mai runtse ido,lokaci guda kuma ya dawo hayyacin sa. Sannan ya fahimci irin ƙwafsin da yayi. Ahankali ya ɗago kansa yana kallon Islam,wacce ke huci kamar zakanya,tana riƙe da towel din bayan da ɗaure shi akirjin ta, ta rufe boobs ɗin ta. "Shikenan na kara kwafsawa,yanzu da wane idon zan kalli yarinyar nan?amma nasan me zanyi"Aslam ya faɗa cikin zuciyar sa yana mai kallon Islam cikin ɓacin rai ya fara magana"ke ƙaramar yar iskace,kina tunanin zuwan ki,gaba na da towel zai sa naji wani abu ne game da ke?hmmmmm,yarinya kinyi karya,domin bakya cikin tsarin matan da Aslam,zai iya jin yana sha'awar su ko ya shiga wani hali dalilin su,kuma wllh ina mai gargaɗin ki ki kiyaye zuwa inda nake,domin bana ƙaunar ki,bana son ganin wannan mummunar fuskar taki mai kama da an dama kashi,banza wawiya marar kamun kai"Aslam ya faɗa cikin ɓacin rai mabayya ni, wanda azahiri ƙoƙarin fidda kansa kawai yake. Yana gama faɗin haka yayi saurin nufar ƙofar barin falon,dan baya ma fatan jin abinda zata faɗa ,yasan ba abunda zai masa dadin ji zata faɗi ba. Cike da mamaki da al'ajabi Islam ke binsa da kallo,lallai mutumin nan,rainin hankalinsa yayi yawa, kan uba! Wato nice ma nake son ɗaukar hankalinsa?hmmmmm baisan wa ce ce Islam ba,wllh sai yayi dana sanin wannan iskancin da yayi min."baka taba jikin Islam abanza ba wllh saina koya maka hankali,banza ɗan iska kawai"ta fada cikin muryar jin haushi,da takaicin yadda ya faɗa mata magana kumaya fice ba tare da ta maida masa martani ba. Kayan data dauko ta zara cikin fushi ta koma dakin granny. Shikuwa Aslam,ko ganin gabansa bayayi sosai,haka ya fice daga falon,kai tsaye cikin motar sa ya nufa. Yana zuwa ya bude motar da sauri ya shige yana mai rige da malamar sa ,wacce tayi tsaye ƙyam kamar sanda. Kife kansa yayi akan sitiyarin motar,numfashi yake saukewa da sauri da sauri,idonsa alumshe,sosai yake jin wata irin matsananciyar sha'awa na taso masa,tunda yake bai taba shiga irin makamancin wannan yanayin ba,anya kuwa yarinyar nan mutum ce?ba abinda ke yawo cikin idon sa,banda cikakku kuma tsayayyun boobs ɗin Islam,tsaki yayi yana mai jin tsanar Islam na ratsa dukkan sassan jikinsa. Kusan minti talatin yayi cikin wannan yanayin,sai juya kansa yake yana lumshe ido da budewa,da gyar ya samu ya buɗe aljihun motar sa, ya ballo wasu ƙwayoyi ya watsa cikin bakinsa. Gumi ne ya fara tsatstsafo wa agoshin sa yana sauke ajiyar zuciya,kusan minti biyar kafin ya tada motar ya bar gidan,fuskarsa ba alamun walwala ko kaɗan ya nufi asibiti. Kamar yadda su mommy ke zato kuwa,hakan ce ta kasance,tare suka dawo gida da Aman,anan gida za'a ci gaba da kula dashi, Daddy ma nan da jibi suke sa ran zai dawo gida,dan ya ce bazai iya zaman asibiti ba,kuma jikinsa da sauƙi alhmdllh. Yau kwana biyu da faruwar wannan abun,sam Aslam yaki bari su hadu da Islam,dan baya fatan ganinta kusa dashi,haka kawai,zai zauna yayi ta tunanin manyan boobs ɗin ta,yana jin yadda suke sukar sa aƙirji. Hakan yasa ya yarda cewar Islam mayya ce ko kuma aljana. Itama bangaren Islam tana nan tana ƙulla irin yadda zata ɗau fansa akan abinda yayi mata.dan ta rantse baici bulus ba,saita rama abinda yayi mata. Yau ta kasance ranar juma'a,dan haka suna zaune gaba ɗayansu afalo, dan tuni an sallamo daddy, jiki alhmdllh yaji sauƙi yana yin komai da kansa yanzu haka yana part ɗinsa tare da babban amininsa ,da kuma yan dubiya. har su jannat da granny duk suna falon.Islam na zaune kusa da granny tana sanye cikin wata riga iyakar rigar gwuiwar ta,itama cikin kayan hanan taje ta zabo, ba ruwanta,idan tayi wanka dakin hanan kawai take nufa ta ɗauki kayan da ranta ke so ta sanya. Aman na zaune atsakiyar su, yana cin naman kaza.yayin da mommy ke yanka masa kayan fruit. Gaba ɗaya hankalinsa na Kan Islam,sosai take burgeshi,kuma yana jin kaunar ta cikin ransa,sosai. Kallonsu Islam keyi cike da jin kewar ahalinta, ko yaushe zata ga nata iyayen?ko suna wane hali yanzu?shin da ransu ma ko sun mutu? Tayi nisa cikin tunanin da take yi taji an dafa mata kafaɗa, juyowa tayi da sauri ta kalli granny. Cikin yanayi na damuwa tana,sauƙe ajiyar zuciya. "Yata me ne ne yake damun ki?ko wani yayi miki wani abu ne?fadamin yanzu inci mutuncin mutum wllh ko waye "granny ta kai ƙarshen maganar ta cikin masifa. Jannat ce cikin salon rashin kunyar ta tace "kuji dai grannyn nan,waye zai kula wannan abar harya bata lokacinsa, can dai tasan abinda ke damunta"ta fada tana murguda baki. Tsawa mommy ta dakawa jannat,tace "jannat bana son rashin kunya,grannyn kike fadawa wannan maganar?sa'arki ce?"ta fada cikin ɓacin rai. Turo baki jannat tayi tana ƙunƙuni. Yunkurawa Islam tayi dan ba,jannat amsa,sai dai Kafin tayi magana aka bude kofar falon,ƙamshin da suka ji ya cika falon ne ya tabbatar musu da cewar Aslam ne,dawowar sa kenan daga masallaci,yana sanye cikin farar shadda mai matukar kyau da ɗaukar ido,sallaya ce rataye akafaɗar sa, ta dama,sai hula baka da bakin takalmin,yayi kyau matuka kamar wani ango. Da sallama ya ƙara so cikin Falon,kusa da mommy yazo ya zauna.nan da nan su jannat suka shiga cikin taitayi su, Kallonsa mommy tayi cikin murmushi,tace "Aslam ka dawo? Lumshe ido yayi tare da jingina kansa akafadun mommy Yana wani yatsine fuska,kafin yace "Yes mommy am tired wllh,barci nake son nayi"ya faɗa yana wani narkewa jikin mommy kamar ɗan yaye. Kansa mommy ta shafa tace "kaci abinci saika kwanta ka huta. Ahankali ya ɗago da kansa yana shafa kan Aman,ya ce "boy ya jikinka?" Murmushi Aman yayi kafin yace "da sauki sosai yaya,nan da kwana kaɗan zan mike "ya faɗa cikin murmushi yana kallon yayan nashi. Jinjina kai Aslam yayi,kafin yace "in sha Allah. Duk abinda ke faruwa akan idon Islam,mamaki ,haushi, da takaici sun mamaye zuciyar ta,ji take kamar ta shaƙe wannan Aslam ɗin wllh,ji yadda yake wani kwanciya jikin mommy gidodo dashi. Tatsi tayi mai ƙarfi wanda saida ya ja hankalin kowa zuwa gare ta.cikin ɓacin rai ta fara magana"wllh wannan abun kunya da yawa yake,haka kawai mutum gundundun dashi yayi ta likewa mamar sa?yo wannan abun ban haushi har ina?dan Allah kai Aslam ko kunya bakaji?dubi ƴan ƙannan ka,suna zaune aguri daban,amma kai daga zuwa ka wani zo kana ɗora wannan rafkeken kan naka mai kama da kwallon kwakwa,akan baiwar Allah,wllh ka rinkayin abinda ƙuda zai bika"ta fada cikin salon rashin tsoronta tana kawar da kanta can gefe. Gaba daya ido suka zuba mata,cike da tsoro su jannat ke kallonta baki buɗe,jin irin kalaman da take faɗa wa yayan su,lallai wannan yarinyar rashin kunyar ta ya kai inda ya kai. Hanan kuwa tsabar tsoro sai kwabe fuska take tana ƙoƙarin yin kuka. Anan kuwa dariya ke son kama shi,wllh Islam ta ita yaba magana,wai rafkeken kai kamar kwakwa"ya faɗa cikin ransa yana danne dariyarsa. Gogan naku kuwa,saida ta fara magana ma ya san da ita agurin,kallon ta kawai yake cike da tsana da jin kamar ya shaƙeta ta mutu.lallai yarinyar nan,wai Ni take faɗa wa waɗan nan maganganun?agaban ƙannai na?kuma acikin gidan mu? Salon ta ja min raini gurin yara?kallon mommy Yayi,wacce itama take kallon Islam,da mamaki akan fuskar ta,ita tausayi. Islam take ji sosai,dan tasan rashin zama da babba shine babban dalilin da yasa bata girmama kowa. "Hummmm ƴar nan kema dai kya faɗa,wannan abin tsantsani har ina,ki dai gani,wannan uban wasu kakan wasun,shine ke kwanciya akan uwar sa, ko kunya baya ji, yayi aure amma yaƙi,wllh cikin sa'annin sa akwai masu yaya biyu,amma shi kullum ba abinda ya tsana sama da zancen aure,Allah yayi wadaran naka ya lalace"granny ta fada tana taɓe baki. Murmushi takaici Islam tayi kamar wata irin uwar nan tashi,kafin tace "to kema granny ta yaya zaiyi aure?bayan yana fita can yayi iskancinsa awaje,wllh dan baki san me yayi min bane rannan,amma wannan Aslam ɗin ba mutumin kirki bane wllh ɗan iska ne,bai gani ya gyal...... Tasss! Tasss!! Kake ji Aslam ya wanke fuskar Islam da wasu lafiyayyun maruka,wanda ya dauke ji da ganin Islam na wucin gadi, Zaro ido su hanan sukayi, cikin tsoro,da gudu hanan tayi bayan mommy ta buya idanunta na zubda hawaye,itama dai jannat bayan kujera ta koma ta tsaya,jikin ta na rawa. Nuna ta Aslam Yayi da ɗan yatsa cikin ɓaci rai yake faɗin"kinyi ƙarya,kice zaki tozar tani gaban ahalina, wllh baki haifu ba,ki sani Ni Aslam naci uwarki a iya shege, dan haka muzuba Ni dake shege ka fasa,daga ke har waƴan da ke daure miki gindi, kike iskancin da kika ga dama ina dai dai daku"Aslam ya faɗa cikin huci da tsantsar ɓacin rai,wllh badan yasan kashe mutum ba kyau ba ,da yau saiya kashe yarinyar nan kowa ya huta. Cikin masifa da ɓacin rai,granny tace "wato Ni kenan,da ubanka ko?to wllh nikam nafi ƙarfin rashin mutuncin ka, sai dai kayi wa ubanka,kuma wllh sai Allah ya sakawa yar mutane marin da kayi mata" cewar granny tana rike kafadar Islam kamar tayi kuka. Wani banzan kallo Aslam ya watsawa granny kafin yace "na mareta kuma zan sake marinta idan ta sake yimin rashin kunya" "Ni ka mara ? Islam ta fada cikin jin raɗaɗi da zafin marin da Aslam Yayi mata.idanunta sun ciki da hawaye. "Na mare ki kiyi duk abinda kike ganin zaki iya banza yar tasha wawiya jaka" Aslam ya faɗa cikin masifa. "Wllh kaine wawa jaki,kuma zaka san ka mareni, dama ina da ɗaukar fansa akan ka,to wllh ka ƙarawa kanka bala'i da masifa,kuma kaine dan tasha dan iska"Islam ta fada hawaye na zirarowa da idanunta. Daga hannu Aslam Yayi da nufin ƙara mata wasu marukan,mommy ta daka masa tsawa"Aslam meye hakan?dukan ta zaka ƙara yi?" Mommy ta fada cikin fushi,dan ba taji dadin marin da yayiwa Islam ɗin ba,ga sawun hannun sa nan ruɗu -ruɗu akan kyakykyawar fuskar ta. Afusace ya juyo yana kallon mommy"baki ji irin rashin kunyar da take min bane mommy?"ya faɗa kamar zaiyi ihu dan ɓacin rai. "Ko ma me tayi maka saika jira kaga irin hukuncin da zan ɗauka,amma agaba na kake marin ƴar mutane,wacce take matsayin amana agurin mu,ka bani mamaki Aslam,rai na ya ɓaci"mommy ta fada cikin haɗe rai. A duniya ba abinda Aslam ya tsana sama da ganin mahaifiyarsa cikin fushi,kuma ace shine silar fushin nata.dan haka sauke hannun sa yayi,yana mai aikawa Islam mugun kallo.kafin yayi ɗakin sa da sauri cikin fushi. Hawaye ne ke saukowa daga idanun Islam,bata taɓa jin kewa da son rungumar mahaifiyar ta irin na yau ba,amma wllh tayi alƙawarin Aslam bai ci banza ba,saita rama dukkan cin kashin da yayi mata. Cike da tausayi,granny ke shafa bayan islam"kiyi hakuri yataAllah zai saka miki,kinji"ta faɗa kamar zatayi kuka. Mommy ce tazo kusa da Islam ta kamo hannunta tare da zaunar da ita akan kujera,hannu ta sanya tana sharewa Islam hawaye,kafin cikin son kwantar mata da hankali tace "kiyi hakuri Islam,zanyiwa Aslam magana akan karya ƙara dukan ki, kuma ina son ki fita daga harkar sa,ki daina masa rashin kunya, dan babu kyau yiwa babba rashin kunya kinji"mommy ta faɗa tana rungume Islam tare da shafa bayan ta. Cikin muryar kuka Islam tace "mommy mari na yayi fa! Wllh ba zan yarda ba,saina rama abinda yayi min,rannan fa wani daki ya kaini,yayi ta dura min yawun bakinsa cikin bakina,ranar nan ma haka ya ganni ba riga,kuma ya rungumeni yana ƙoƙarin yi min iskanci, wllh ɗan iska ne shi,kuma bazan taɓa yarda ba"ta kai karshen maganar ta da sanya kuka,Islam zata iya rantse wa bata taba yin kuka na ɓaci rai ba, tun tasowarta sai yau.kuma akan wannan bijimin san,wllh zai gane kuren sa. Sosai gaban mommy ya fadi,salati kawai take cikin ranta,sun shiga uku,karfa Aslam ya jawo musu abin kunya?lallai dole ta sanar da daddy su san abinyi akan wannan matsalar. Salati granny ta dauka"laaaa ilaha'illallahu! mun shiga uku,Ni dama nasan akwai dalilin da ya hana wannan yaron aure,ashe ƴaƴan mutane yake lalubewa?shine zai fara akan yar amana wllh bazan yar da ba,dole asan abinyi. Shiyasa kullum zaka ganshi,da lumsassun idanuwa kamar mai jin barci,ashe Fitina ce acikinsu" Jannat da hanan kuwa sam basu yarda da abinda Islam ta fada ba,dan gani suke bata kai matsayin da yayansu zaiyi wani abu da ita ba,kawai ta fada ne dan tana son bata masa suna. Shikam Aman tausayin Islam ne ya gama mamaye zuciyar sa,sam yana ganin abinda yayan nashi yayi bai kyau ta ba,koma menene bai kamata ya mari Islam ba. "Meke faruwa ne?tun daga part ɗi na make jiyo hayaniya" gaba ɗaya juyawa sukayi suna kallon inda maganar ke fitowa. Ba kowa bane face daddy,Wanda ke tsaye riƙe da karfen hawa benen da zai kaika part ɗin sa.... Masu karatu, me zai faru idan ya kasance Daddy Yana jin abinda suke fadi? Muje zuwa Mrs babi ce 💘💘 [9/20/2022, 10:34 AM] Abk: ______________tsaye Daddy yake yana kallon su,kuma yaji duk abinda Islam ke faɗi, shi dama yana mamakin dalilin da ya sanya Aslam baya son ayi masa zancen aure,wato ashe akwai Abinda yake aikatawa,shine kuma yake son lalata ƴar daya dauko matsayin amana?lallai dole ya dau mataki akan wanna al'amarin. "Ba komai Alhaji, dama yanzu zan zo part ɗin naka,jira nake bakin su tafi,idan wani abun kake buƙata ka faɗa sai akawo maka yanzu"cewar mommy kenan tana kallon mijin nata,dan tafi son suyi maganar anutse. "Kuji min munafuncin banza? ya zaki ce ba komai?bayan kuma akwai komai ɗin,ai wllh ba batun rufa-rufa,haka kawai acuci yarinya kuma kice ba komai,saboda ɗan ki ne ko?"granny ta fada cikin masifar ta tana zarewa mommy ido. "Ba haka bane granny,Kinga wannan maganar bai kamata ayi ta anan gaban yara ba,kuma wllh niba ɓoye masa komai nake don yi ba,nafi son in sanar dashi a nutse Dan samun mafita"mommy ta fada kamar zatayi kuka. "Ƙyaji dashi wllh sai an faɗa masa maganar nan ehe" Cewar granny tana wani fari da ido kamar yarinya. Ahankali Daddy ke taka benen,har ya sauko ƙasan falon,zama yayi akan kujera yana mai kallon granny,kafin yace "Hajiya ki yi hakuri ki kwantar da hankalin ki,domin ba wanda ya isa ya cutar da yarinyar Nan agidan nan,kuma in gyale shi,duk abinda take faɗa ,naji akunne na,kuma zan ɗauki mataki kwakwkwar akan Aslam" Daddy ya faɗa cikin ɓacin rai,yana kallon mommy. Kafin yace "lallai -lallai Aslam ya sameni yanzu a part ɗina" Sannan ya juyo yana kallon Islam wacce ke zaune ta turo baki,cikin ɓacin rai ,zuwa lokacin kuma ta daina kuka. "Kiyi hakuri Islam,ban dauko ki zuwa gidan nan dan acutar dake ba,In Sha Allahu zanyiwa tubkar hanci"Daddy ya faɗa cikin yanayi na kwantar da hankali. Kallon Daddy Islam tayi kafin tace"ai wllh Alhaji,badan ina jin nauyin ka ba,da irin abinda zanyiwa wancan ɗan iskan ko,hmmmmm,amma duk da haka wllh saina rama ƙona Ni da yayi aƙirjina,sannan ya kalle min abinda ba wanda ya taba gani, Allah ya isa na wllh mugu kawai"Islam ta fada tana bin hanyar ɗakin Aslam da harara. "Kiyi hakuri Islam,kuma na gode da ya zamo kina ganin ƙimata har kike saurara masa "Daddy ya faɗa cikin ɗan murmushi,shikam karfin halin Islam na burgeshi,sannan yarinyar ta shiga ransa sosai,jinta yake kamar yar cikin sa. "Ato Gara dai ayiwa tubkar hanci, dan wannan yaron mai kama da na mamajo bamu san me zaiyi nan gaba ba. Mommy dai shiru tayi kanta a ƙasa,tana sauraron abinda granny ke faɗi,can cikin zuciyarta kuwa ,tsoro ne sosai maƙare,yaushe Aslam yazama haka?idan aure yake so ai Gara ya faɗa ayi masa,meye nashi na rungumar yar mutane,ita fa ta gane kissing ɗin Islam yayi baki da baki,shine ita kuma take tunanin yawun sa ya bata . " Madam ina son akira min Aslam yanzu,ya sameni a part ɗina"Daddy ya faɗa yana mikewa yace da granny"hajiyata Bari na koma na ɗan huta" "To ɗan nan Allah dai ya kara maka lafiya,ya kuma bayyana waɗan nan mugayen da suka so cutar da kai"ameen Daddy ya ce tare da wucewa part ɗin sa. Tashi mommy tayi ta nufi ɗakin Aslam,tana ta tunane -tunane. Ɗago kai Islam tayi,kawai suka haɗa ido da Aman ya na kallon ta.tsaki tayi tana hararar sa kafin tace"Ni wllh na tsani kallo arayuwa ta,kai kuwa Aman idan ka kama kallon mutum kamar tsohon maye haka kake,ina dalili kayi ta kallo na kamar zaka cinye Ni"Islam ta fada cikin fada tana hararar Aman. Shikuwa Aman murmushi yayi yana kara jin kaunar Islam cikin ransa,wllh komai tayi burgeshi take, haka yake son matar da zai aura ta kasance mai tsiwa. "Kai ƙanwata, yaushe na kalle ki?Ni da nake kallon jikin kujera"Aman ya fada cikin murmushin sa mai kyau. Kallon sa Islam tayi tare da taɓe baki tace "lallai kuwa ƙanwar ka,ta ina muka haɗa dangi?inba shishshigi irin naka ba?can dai ka nemi ƙannan ka,bani ba,Ni ba ƙanwar kowa bace"Islam ta faɗa tana turo baki. Dariya Aman Yayi kafin yace "koba komai,dai nasan yanzu baki da yan uwan da suka fimu, kuma idan ke baki ɗauke Ni matsayin yaya ba,Ni na ɗauke ki matsayin ƙanwa ehe"ya faɗa shima yana turo baki yadda takeyi. Kallon sa tayi,ganin yadda ya wani turo baki yaso baya dariya,dan haka ta ɗan kurmusa.ta buɗe baki zatayi magana,saidai Kafin tayi magana, jannat ta ja wani uban tsaki tana tace"aikin banza wai mutum ba kowan kowa ba,kuma ba dan kowa ba,amma shegen tsirfa da iyayi,ko me za'a kalla anan? Muma kuma bamu buƙatar ki matsayin dangin mu,dan kunci ƙarfin haɗa iri da kucakakamar ke"ta fada cikin yatsina tana nuna Islam kamar wata kashi. "Keee!! Jannat wllh ki kiyaye Ni, dan yanzun nan zan ɓaɓɓallaki in watsar agurin nan,banda asara.ina ruwanki da Ni?gidan naki ne ?ko ke kika kawoni gidan?banza mai zubin karuwai,wllh ki kula da kanki,duk ranar dana damƙeki sai jikinki ya fada miki,shi ai yayan naki yaga abin kallon,shiyasa yake kallo wawiya kawai"Islam ke faɗin wannan maganar azabure kamar zata doki jannat ɗin sai harara take banka mata. "Wllh kinyi ƙarya yar karoro,baki isa ki faɗa min magana agidan mu ba,gaki nan karuwa mai bin maza,zakiyiwa ɗan uwana sharri,wllh yaya Aslam ya wuce da ajikin ki,mai kama da mayya,gara tun wuri ki hada kayan ki ki bar mana gida. "Kee jannat meye hakan ?baki da hankali ne ?zaki rinka mata gori?ko baki san wanda ya kawo ta gidan ba?wllh idan na sake jin bakin ki sai na tattaka ki"Aman ya faɗa cikin zafin zuciya yana hararar jannat. "Barta tayi,ai idan batayi haka ba bazata nuna ita marar tarbiyya bace ,wllh nikuwa akan yarinyar nan ,zan iya dokuwa da uban kowa ehe" Cewar granny cikin masifa tana mikewa tsaye itama.dan duk abinda suke yi tana zaune . Mommy ce ta fito daga ɗakin Aslam bayan ta sameshi kwance akan gado ya ƙurawa silin ido,kallo ɗaya zakayi masa kasan ransa abace yake."maza kazo inji Daddyn ku"ta fada tare da barin dakin,ba tare da ta jira amsar saba ya fito. "Meye kuma ?me akeyi naga kun wani mimmƙe tsaye?ko faɗan ne? Mommy ta fada tana karasowa. "Mommy wannan yar karoron ce ke son raina min hankali,kuma wllh kan uwar uban shegiya zanci la'ada waje dan niba sa'arta bace... Tasss!! Jannat taji saukar mari akumatun ta, da sauri ta dafe kumatun tana kallon Islam,wacce ta wanke mata fuska da mari, "Kai -kai -kai!! Ni kika mara "jannat ta fada cikin mamaki. "An mareki, kuma idan kika sake rashin tarbiyya agaba na,wllh saina ƙara miki wani,banza yar tasha agaban mahaifiyar ki kike zagi dan baki da ɗa'a,wllh da sannu zan saita miki kwakwalwarki"Islam na gama faɗin haka ta juya tare da barin falon ta fice waje. "Yawwa ƴar albarka kinyi dai-dai Allah ya baki ikon gyara wannan fitsararriyar yarinyar "cewar granny tana barin gurin,ranta fess.dan dama haushin jannat take ji ta raina ta sosai. "Kuka jannat ta fashe da shi tana faɗin"mommy kina gani?agabanki wannan yarinyar ta mare ni?wllh bazan yar daba,saina rama" Jannat ta fada cikin kuka tana buga ƙafa aƙasa, irin na tabararrun yara. "Na gani, kuma tayi dai -dai jannat yau she zakiyi hankali ne?kullum kina girma kina da ɗa cin kashi?Indai rashin tarbiyya ne kije kiyi tayi,Ni kuma bazan hana yarinya ƙarama koya miki darasi akan rashin dacewar zagi ba"mommy na faɗin haka tayi wucewar ta ɓangaren Daddy. Zaman yan bori Jannat tayi tana kuka harda shura ƙafa,wllh saita ci kaza-kazan Islam,hanan ce tazo kusa da ita tana rarrashinta,kamar zatayi kuka. Shikuwa Aman tsabar haushi wayarsa kawai ya dauko yana latsawa. "Keeee!!!! Uban me aka miki kike wa mutane wannan haukan kamar karamar yarinya?" Aka dakawa Jannat tsawar da tayi silar haɗiye kukanta. Aslam ne ya fito daga ɗakinsa, fuskar nan kamar hadari . Cikin rawar jiki Hanan ta ce"yaya wannan Islam ɗin ce ta mare ta" Wani malolon baƙin ciki ne ya tokare maƙogaron Aslam,wai wannan yarinyar wace irin annoba ce haka agaresu?ta takurawa kowa agidan,tsabar baƙin ciki bai san sanda ya kaiwa jannat duka da ƙafar sa ba,da sauri jannat ta kauce dukan ya bi iska. "Shegiya a sararriya,yanzu ki rasa wacce zaki zauna kinawa kuka sai waccan yarinyar?sa'ar ƙanwar ki?wllh kin ji kunya,ba abinda kika iya sai tara samari da iya shege acikin gida ko?ki zauna tayi ta saki kuka,wata rana ma kakkarya miki ƙasusuwa zatayi ta watsar banza sha sha sha"ya na kaiwa nan azance sa yayi wucewar sa ɓangaren Daddy.cike da jin haushin jannat "Wllh saina illa ta yarinyar can "cewar jannat ta na ci gaba da kukan ta. Hararar ta Aman Yayi kafin yace "ko ita ta illa taki ba,banza ba karfin kirki sai rashin kunya,Ni wllh tayi min dai-dai ma"ya faɗa yana mai da kansa kan waya. "To baƙin mugu dama haka zaka ce mana,kasa ido zaka ga abinda zanyi mata"Jannat ta fada tana tashi afusa ce,fuuuu!!! Tayi ɗakin ta.Hanan kuwa kan kujera ta koma ta zauna cike da tsoro,sai rarraba ido take. Faɗa sosai Daddy ya rufe Aslam dashi,lokacin daya shiga ɗakin,ko amsa gaisuwar da Aslam keyi masa ma bai yi ba.ta inda ya shiga ba ta nan yake fita ba,sai da Aslam ya Raina kansa,yaji kamar zuciyarsa zata kama da wuta,hakuri yake ta bawa Daddy Amma ko sauraronsa baya yi.sannan ya ɗora da cewa"kuma wllh Aslam,na baka nan da sati biyu ka kawo min matar da zaka aura,idan ba haka ba,Ni da kaina zan zaɓa maka,tashi ka bani guri mutumin banza kawai"Daddy ya faɗa cikin fushi. Sosai fargaba ta kama Aslam,aure kuma ?to shi wama zai kawo matsayin matar da zai aura?bayan ba shi da budurwa,sai dai abokan harka? impact ma shi bai shiryawa aure yanzu ba.haka kawai ya ɗorawa kansa damuwa.haka ya koma ɗakinsa jiki ba kwari,yana ta tunane tunane,shi gashi ba aboki gare shi ba,bare ya nemi shawara.itama mommyn da yake ɗan shawarar da ita,tayi fushi,dan ko kallon sa bata ma yi. Hakuri sosai mommy ke bawa Daddy tana kwantar masa da hankali akan lamarin Aslam,har ta samu ya sauko daga fushin da yake. Kai tsaye garden Islam ta wuce ,kan bishiyar goba ta hau tayi zamanta,bayan ta kira janbun ta,lumshe ido tayi kamar mai barci,sai dai sam ba barcin take ba ,tana tunanin rayuwarta,da kuma iyayen ta, ko suna wane halin yanzu?ko sun mutu ma waya sani.ahankali ta kai hannun ta tare da shafo ƙirjin ta,inda Aslam ya watsa mata ruwan zafi,ƙwafa tayi tare da furta"wllh saina rama,zaka san nika gona,gaba ɗaya yaran gidan nan basu da mutunci,kuma wllh saina koya musu hankali"ta fada kamar wata shugaba. Aslam kuwa ji yayi dakin yayi masa ƙunci,yana buƙatar shan iska mai sanyi,dan haka tashi yayi kai tsaye bayan ya sauya kaya,daga manyan zuwa ƙanana,garden ya nufa,zuciyar sa sam ba daɗi.yana zuwa ya sami guri abakin swimming pool Yayi zamansa bayan ya zura kafafunsa cikin ruwan.ba abinda ke yawo cikin zuciyar sa,face kalaman Daddy,ya Nemo mata nan da sati biyu,to a ina zai nemo?wa yake da ita?amma yasan yadda zaiyi,zaiyi ta bawa Daddy haƙuri,idan lokacin yayi,akan zai nemo yana kan bincika wa ne,da haka zaiyi ta jan ran Daddy har ya hakura da zancen. Kamar daga sama Islam ta hango Aslam,zaune bakin ruwa,murmushi tayi tare da radawa janbu magana a kunne"maza janbu jeka ciro min ayaba guda biyu,ka dawo yanzun nan. Aikuwa cikin gudu da tsalle janbu ya nufi kan bishiyar ayaba,ba jimawa sai gashi ya dawo dauke da ayabar guda biyu ahannunsa. Karba tayi tana murmushi,kafin ta bare ta cinye guda ɗaya,ta rike ɓawon,janbu ma bashi dayar tayi ya cinye.bawon ta karba sannan ta sauƙo daga kan bishiyar ahankali,dan basu da wata tazara da gurin wankan. Ahankali ta lallaɓa, ta bayan Aslam,cikin sanɗa. Tana zuwa bata jira komai ba kawai ta ingiza shi cikin ruwan nan,ji kake tinjimm!! Aslam ya faɗa cikin swimming pool ɗin nan,aikuwa kansa ya bugu da jikin mariƙar shiga ruwan. Runtse ido Aslam Yayi da mugun ƙarfi,sakamakon raɗaɗin azaba daya ziyarci kwakwalwar sa.nan da nan gurin ya fashe ,jini ya fara tsatstsafowa.dariya Islam ta sanya da karfi tana nuna Aslam da hannun ta. Cikin sauri ya buɗe idon sa afusace jin Muryar Islam na masa dariya.hakan na nuna ita ta turashi cikin ruwan kenan? "Wai wayaga tinjimi, ka ganka kuwa?wllh kamar wani barawon kaza,irin an kamashi ɗin nan yaci duka,hahhhhh"ta ƙyalƙyale da dariya. Cikin fushi da ɓacin rai Aslam ya kama karfen shiga ruwan ya fara fitowa da mugun sauri,yau kam idan ya kama yarinyar nan,sai dai shima akashe shi,amma sai ya shaƙeta ta mutu. Ganin ya fito cikin fusata ya nufota gadan -gadan ,yasa Islam saurin watsa wannan bawon ayabar dake hannunta,ai kuwa ba tare da lura ba Aslam ya taka bawon nan,ya kwashe shi,suuuuu yayi baya ƙafarsa ta lankwashe,sannan ya faɗa kan ƙafar. "Wayyo Allah ƙafa ta"Aslam ya faɗa yana runtse ido,jin yadda ƙafar ta dauka wani duuummmm. Dafe kansa yayi wanda ya ci gaba da sarawa kamar zai rabe gida biyu.sai juya kansa yake cikin azaba. Islam kuwa takowa tayi zuwa inda yake kwance, tana masa kallon uku saura kwata. Kafin ta sanya dariyar mugunta tace "kaɗan ma ka gani,In dai nice wllh sai zaman gidanku ya gagare ka,ba dai Ni kake rainawa ba,kayi kuskure taɓa Islam,kuma wllh waɗan na abubuwan da ka kalla,baka gani abanza ba,saina ɗau fansar hakan,Ni rainon dawa ce bana ɗaukar raini"tana faɗin haka ta juya ta bar gurin ta nufi cikin gidan. Aslam kwance yayi agurin cikin azaba,yana juya kansa,tabbas zuwa yanzu ya gama yarda, wannan yarinyar aljana ce. Cikin dabara ya yunƙura tare da mikewa zaune,ƙafarsa tayi wani ƙaran da saida ya kwalla dan ihu yana runtse idon sa.... Masu karatu karfa islam ta ballawa Aslam kafa🤣🤣 Hohoho muje zuwa masoya, Lamarin na gaba. Mrs babi ce 💘💘 [9/21/2022, 1:11 PM] Abk: _______________Da ƙyar, Aslam ya yunƙura ya miƙe tsaye yana cije leɓe,dan sosai ƙafarsa ke masa wani irin zugi da raɗaɗi. Ga jikinsa duk ajiƙe,yanzu idan ya shiga gida mai zai ce musu? sai kawai yace Islam ce ta jefeshi cikin ruwa?kuma ta kayar dashi?ina! Hakan bazai yiwu ba.dole dai ya nemo mafita. Ahankali ya fara ɗingisawa, ya nufi jikin bishiyar da Islam ta sauko,zama yayi aƙasan bishiyar yana mai runtse idon sa,me ya kamata yayi wa yarinyar nan ne ya huce?ya fuskanci,sam bata da cikakken hankali,tsaf zata iya kashe mutum,ya zama dole yasan matakin dauka akanta. Kusan minti biyar yana zaune,ya ga dai zaman baida wani amfani,dan haka ya yunƙura da gyar yana runtse ido,ya tashi tsaye,sai huci yake tsabar ciwon da ƙafar sa keyi,gani yake kamar ma gociyar ƙashi ya samu. Cikin gidan ya nufa ahankali yana dafa bango,ga jiki duk ajiƙe.yana buɗe ƙofar falon yayi arba da Islam ta ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya tana cin apple,Aman Yana ta mata surutu,ita kuma sai murmushi take. Ahankali yake takawa zuwa cikin falon,saida yazo tsakiyar falon,Islam ta tuntsire da dariya,tana faɗin "ɗaya! biyu !! Uku!!!"tana dariyar ta alamun takunsa take ƙirgawa. Cak Aslam ya ja ya tsaya tare da runtse idanun sa,zuciyar sa na masa zafi,yana kara jin tsanar Islam cikin ransa. Da sauri Aman ya kalli inda Islam ke kallo tana dariya,ɗan uwansa ya hango da jiƙaƙƙun kaya ajikinsa, ga shi ya ɗage ƙafa ɗaya,kuma da alama ciwo yaji. "Yaya me ya same ka haka?me yasa naga jikin ka ajiƙe ?ƙafar ka ma yaya kamar ciwo kaji fa"Aman ya faɗa cikin yanayi na nuna tsantsar damuwa. Ɗan satar kallon Islam Aslam Yayi,aikuwa shi take kallo ta dage gira ɗaya tana jiran jin abinda zai faɗa. Kawar da kai yayi yana kallon Aman kafin yace "am ok bro,I just fall down,and I think I get injury in my leg"Aslam ya faɗa cikin harshen turanci,dan kar Islam taji me yace ta ƙarya ta shi. Aikuwa saiji yayi ta sanya dariya tana faɗin"Lear !wllh he's telling you lear,is better ma ka sanar dashi gaskiya,dan ba Yaren da zakayi Islam bata ji me kace ba"ta faɗa tana kallon Aslam da murmushi. Mamaki sosai ya kama Aman,yarinyar dake rayuwa cikin jeji ina ta koyi Turanci?dan shikam iya tunaninsa kamar tun ƙuruciya take cikin wanan hatsabibin jejin. Shikuwa Aslam da bai san inda take rayuwa ba,kawai dai yayi mamakin ashe ta je school,dan baiyi expecting tana jin turanci ba. Ci gaba yayi da nufar ɗakinsa,ba tare da ya kara furta komai ba,yana jinta tana faɗa wa Aman cewar"wllh ƙarya yake maka,nice nan na cillashi cikin ruwa,sannan na sanya masa ɓawon ayaba ya taka ya faɗi"ta ƙarasa maganar da dariya. Marairaice fuska Aman yayi yana kallon Islam yace "haba ƙanwata, baki kyauta ba gaskiya,yaya fa is like second father to us,shine babban yayan mu,dan Allah ki daina masa rashin kunya bana jin daɗi,and..... "Kai dalla malam ya isheka haka, saboda yayan ka ne shine kake son kareshi?Ni baka ga irin rashin mutumcin da yake min ba ko?to wllh yanzu na fara bashi wahala,dan saina ɗau fansar duk abinda yayi min, dan kuwa bana yafiya"Islam ta fada cikin salon masifar ta tana hararar Aman. Shiru Aman Yayi yana kallonta, yasan halin ta da masifa,kuma shi baya son ranta ya baci, amma sam baya jin daɗin yadda take yiwa yayan nashi sam,cikin sanyi murya yace "kiyi hakuri Islam bawai dan ya na matsayin yaya na nake faɗin haka ba,kawai dai naga gaba yake da ke,kuma koba komai ance bin naga bin Allah"ya ƙarasa cikin sanyin murya kamar wanda ke tsoronta. Harara ta watsa masa fuskarta ahaɗe, sannan tace "wato Ni kafura ce bana bin Allah ko?kai wllh fa kaima ka kiyaye ni, kar kaga ina kula ka nuna ɗan mutunci kace zaka ringa faɗa min baƙar magana,idan na dawo ta kanka,wllh ba za kaji daɗi,dan sai na hana wannan karyayyar ƙafar taka warke wa"ta fada tana nuna ƙafar tasa da ke ɗaure. Murmushi yayi tare da girgiza kai,lamarin Islam kam,sai du'ai sam bata da gwani."to nikam kiyi hakuri karki ƙarasamin ƴar ƙafar tawa in zama gurgu,kinsan ƴan mata bazasu aureni ahaka ba"ya faɗa cikin murmushi. "To dole ne sai kayi auren?ba sai kayi zaman ka agida ba,dama waya ke son wani aure ana zaune ƙalau ?kaga Ni bari na tashi barci ma nake ji ka ishe Ni da surutu"Islam ta fada tana mikewa tsaye,da yar rigarta iya kwauri. Kallo aman ya bita dashi,yana jin wani irin abu na ɗarsuwa cikin zuciya da jikinsa,shi wllh da zata taimaka ta daina sanya kayan nan da ta taimakeshi,dan sosai take sanya shi cikin wani hali idan ya ganta da wannan shigar. "To kallamu,ka fara ko?kai kam Aman bakaji daɗi ba wllh,kallo sai kace maye"Islam ta fada tana watsa masa harara. Ajiyar zuciya yayi kafin yace "Please ƙanwata dan Allah ki daina sanya irin waɗan nan kayan,domin suna bayyana surar ki sosai awaje,kuma kinsan akwai matsala idan har ina kallon ki ahaka"Aman ya faɗa cikin marairaita kamar zaiyi kuka. "Kuttt!!! Lallai ma Aman,yanzu kayan da nake sawa ma,sai an zaba min?to ina ruwan ka da shiga ta?wllh ba wanda ya isa ya hanani yin shigar dana ga dama,kuma ai bance ka kalle Ni ba,bare kaga akwai matsalar,banza kawai mai hanci zororo kamar karas"tana faɗin haka ta jefa masa guntun apple ɗin dake hannunta,tare da murguɗa baki ta juya zuwa dakin granny Jikin ta ko ina na girgiza. Lumshe ido Aman yayi tare da sauke ajiyar zuciya mai ƙarfi,Allah ya gani shikam wllh duk lokacin daya ganta da irin wannan shigar,mafi yawan lokaci yana tsintar kansa cikin felling sosai,dan ba ƙarya ko makaho yasan akwai ƙira agurin. "Allah ka mallaka min Islam matsayin mata ta"ya faɗa ahankali yana Binta da kallo har ta shige ɗakin granny. Aslam Yana shiga ɗakinsa da gyar ya cire riga da wandon sa ya kwanta akan gado,kansa ciwo yake ga ƙafar sa,sai zogi take masa.tsabar bakin ciki da takaici,ko maganin rage radadi bai shafawa ƙafar ba. Haka yayi kwance aɗakin har dare, Dan ko abincin rana ƙin fitowa yayi yaci,mommy kuwa kasancewar tana fushi dashi,ko neman akirashi batayi ba. Aikuwa kafin dare kafa ta kumbura suntum, nan da nan,har ta zuba masa zazzaɓi,amma saboda taurin rai irin na aman yaƙi fitowa aduba masa ƙafar haka ya kwana bai ko runtsa ba. Koda suka kammala breakfast,school su jannat suka wuce ita da hanan. Aman ne ya kalli mommy yace "mommy Yaya fa tun jiya banga fitowar sa ba,kuma da alama baida lafiya,dan yaji ciwo akafar sa jiya,ya kamata adubo sa" jinjina kai mommy tayi kafin tace,nima tunanin da nake yi kenan,gaskiya ba lafiya ba,bari naje na duba da kaina"ta fada tana mikewa ta nufi dakin Aslam ɗin,dan dama dauriya kawai take,amma tun daren jiya take son sanin wane hali yake ciki,ta sanshi sarai da ɗacin rai,sai yayiwa kansa horon yunwa,gashi ba shi da juriya akan yunwa. Yana kwance cikin bargo sai rawar sanyi yake,haƙoran sa har haduwa suke da juna.da sauri mommy ta karasa cikin dakin,ta yaye bargon daya rufe jikinsa dashi,daga shi sai single da boxers. "Subhanallah! Aslam, baka da lafiya?meke damunka?ta fada tana kai hannunta tare da taɓa jikinsa,zafi ƙau jikin nashi kamar wuta, Ahankali ya buɗe idanunsa da sukayi jajur dasu,ya kalli mommy dake shafa kansa. Cikin rawar murya yace "mommy ƙafa na ciwo take sosai, sanyi nake ji mommy"ya faɗa jikin sa na rawar sanyi. Kallon ƙafar tasa mommy tayi,zaro ido tayi ganin yadda ƙafar ta kumbura sosai"Aslam Ina kaji wannan ciwon haka?garin yaya?me yasa ka bari har gurin yayi tsami haka? innalillahi bari na sanar da Daddyn ku,anemo mai gyara"tana faɗin haka ta fice da sauri. Lokacin Islam na zaune kusa da Aman,tana shafa masa wani magani agefen ƙafar sa, shikuma sai kallonta yake,mommy ta fito da sauri ta nufi saman Daddy.kallon juna Islam da Aman sukayi,kafin Aman yace "da alama yaya bai da lafiya,dama tun jiya bai fito,kin gani ko Islam,kuma wllh yaya bai iya ciwo ba"taɓe baki Islam tayi kafin ta ce "ina ruwana karya iya ciwon mana,In yaso ma ya shekara yana ciwon bai dame Ni ba"ta fada tana ci gaba da shafa masa maganin. "Amma fa kece silar ciwon nashi Islam,yanzu ko kaɗan bakiyi nadama ba?" Aman ya faɗa yana kallon ta. Aikuwa matse gurin da take shafawa maganin tayi da karfi,har saida Aman Yayi ƙara yana riƙe hannun ta"wayyo Allah Islam zaki karya min kafa,yi hakuri na tuba bazan ƙara magana ba"Aman ya faɗa cikin sigar rarrashi Yana kif-kif ta ido,dan yaji zafi sosai. Sakin ƙafar tayi tana mai faɗin"wllh da saina ƙara karya maka nan gurin ma,dan naga surutun ka yayi yawa,shikenan kuma Allah bazai jarrabi bawan sa ba,sai ka ɗora min kace Ni ce?shi ragon ina ne da ɗan wannan abin da nayi masa zai sashi jinya?" Kafin Aman yayi magana,saiga mommy da daddy suna saukowa, "Daddy barka da fitowa"aman ya faɗa cikin girmamawa. "Yawwa aman sannu ya kafar taka?fatan dai kana jin sauƙin?"cewar Daddy Yana shafa kan Aman . "Alhamdullah Daddy Ina jin sauƙi sosai" "Masha Allah haka akeso,Islam sannu ko,fatan dai ba wata matsala?"Daddy ya faɗa yana kallon Islam, fuskar sa dauke da murmushi. Murmushi tayi itama kafin tace "ba komai Alhaji ya jikin naka?" "Jiki kam Alhmdllh ai na warke,ina ƙara godiya sosai agareki yata Allah yayi miki albarka"Daddy ya fada yana kallon Islam,murmushi tayi bata ce komai ba. "Alhaji da kayiwa mai gyaran waya kawai yazo,dan sosai ƙafar tashi ta kunbura,ina ga dai ko targaɗe ko kuma tsagewar ƙashi ya samu"mommy ta fada cikin yanayi na damuwa. "Eh hakan za'ayi bari na kira malam haru in yaso saiya zo ya duba ƙafar tashi"Daddy ya faɗa yana ƙoƙarin cire wayar sa daga aljihu. "Daddy Nima na iya gyaran targaɗe da gocewar ƙashi ko tsagewa " Islam ta fada da sauri tana kallon Daddy. Fasa ɗauko wayar yayi yace"af !aini na manta ma wllh,muna da mai gyara agida,Hajiya ga Islam,dan kinsan ita ta ɗaurewa Aman karayar sa" "Wllh nima na manta Alhaji,hankali na ne duk atashe,ganin yadda ƙafar tasa ta kunbura sosai, Yanzu muje Islam ki ga yadda ƙafar tayi"cewar mommy tana kama hannun Islam. Dakin suka nufa Daddy na binsu abaya. Aman kuwa zaro ido yayi yana jin faduwar gaba ,Allah yasa Islam karta ƙara wa yaya Aslam wani targaɗe. Kai tsaye suka shiga ɗakin na Aslam,ba kowa cikin Falon sai ƙamshi da sanyin ac. Sosai ɗakin yayi wa Islam mugun kyau,har taji cewar dama dakin tane. Shiga sukayi cikin uwar ɗakan, inda Aslam ke kwance kan luntsumemen gadonsa, ya rufe jikinsa da bargo. Kallon dakin kawai Islam keyi cike da sha'awar dakin,dan sosai taji tana son dakin cikin ranta.komai neet an ajiye shi gurin daya dace,sai ƙamshi ke tashi ta ko ina. "Lallai na samu gurin huta wa wllh"Islam ta fada cikin ranta. "Islam duba masa kafar ki gani"cewar mommy tana yaye bargon daga jikin Aslam. Waral!Aslam ya bude idon sa,jin sunan da aka ambata ,matsayin wacce zata duba masa ƙafar,tab Islam kuma?itace mai duba masa kafar?ina bazai yiwu ba,haka kawai ta zai miƙa kafa wannan ƴar dabar fara ta murde masa ƙafar,bayan itace silar shigar sa cikin wannan halin da yake ciki, Yunkurawa yayi da gyar ya tashi zaune fuskarsa hade yace "mommy waye zai gyara min kafar ? Badai wannan yarinyar?wllh Indai itace Gara ƙafar ta lalace da na yarda ta taɓa min ƙafa" Aslam ya faɗa cikin mugun ɓacin rai yana huci...... Masu karatu ya kuke gani? Anya Aslam zai yarda Islam ta duba masa ƙafar sa kuwa? Kun ji dai Islam tace ta sami gurin hutawa,ya kuke ganin zata kaya tsakaninsu da Aslam? Muje zuwa taku ce dai, Anty mammy Mrs babi💘💘 [9/22/2022, 10:33 AM] Abk: _____________"Kai Aslam meye kake faɗi haka?akan lafiyar taka ma saika nuna taurin kai?ko anfaɗa maka ana wasa da lafiya ne?to kayi hanzarin tsayawa ta duba maka ƙafar tun kafin raina ya gama ɓaci gaba ɗaya" Daddy ke faɗin wannan magana cikin ɓacin rai,dan yasan halin Aslam da kafiya,idan ba zabu-zabu yayi masa ba,to bazai tsaya ta duba masa kafar ba. Cikin jujjuya kai irin na shiga halin ƙaƙa nikayi Aslam ya kalli Daddy ya fara magana cikin marairaita"Daddy please Dan Allah ka kira koma waye yazo ya duba min ƙafar,amma banda wannan yarinyar wllh Daddy idan ta duba min ƙafata zafin da zanji cikin zuciyata saiya fi na raɗaɗin da ciwon nan kemin,Please mommy kisa baki"Aslam ya faɗa yana kamo hannun mommy, jikinsa zafi ƙau. "Kai Aslam,bana son Shashanci fa,Ina faɗin magana kana musani?ranka zai matukar ɓaci wllh, kasan ba na son shirme ,ke Islam maza zo ki taimaka masa"Daddy ya faɗa ba alamun wasa akan fuskar sa. Kallon mommy Aslam Yayi kamar wani Maraya yana karya wuya.lumshe ido mommy tayi alamun yayi hakuri Islam ta duba masa ƙafar. "Daddy naga kamar baya son na duba masa,kawai ka nemo wani mai gyaran ya duba masa,dama Ni tausayin sa ne yasa na ce zan duba masa kafar,amma tunda baya so kawai bari na tafi"Islam ta faɗa cikin muryar tausayi tana juyawa da nufin barin ɗakin. "Kinga Islam karki tafi, zoki duba masa ƙafar kinyi niyyar aikin lada karki fasa"cewar Daddy kenan ganin Islam na ƙoƙarin barin ɗakin. Saida Islam tayi murmushin mugunta kafin ta juyo ta dawo cikin dakin. "Maza Islam duba masa kinji"cewar mommy tana janyo Islam zuwa bakin gadon. Zama Islam tayi agefen gadon tace "Miƙo ƙafar taka muga"ta faɗa cikin dakiya kamar wata uwarsa. Tsabar haushi da bakin ciki yasa Aslam ya manta da ciwon da ƙafar ke masa ya wani turo ta bakin gadon da karfi, da hanzari ya runtse idonsa tare da damƙe zanin gadon,sakamakon azabar daya ji ƙafar nayi masa. Islam kuwa ahankali ta sanya tattausan hannunta tana ɗan shafa ƙafar tasa sannu kan hankali,kamar tana masa waiwayi, Wani yuuummm!!! yaji tsikar jikin sa na tashi,ahankali ya lumshe idon sa tare da sakin wani ɗan nishi,da bai shiryawa fitowar shiba.ji yake kamar sosa masa gurin take,wanda hakan yaso sanya shi cikin wani yanayi,ga lallausar fatar hannunta mai dumi dake ratsa kashin ƙarar tasa.sai wani lumshe ido yake yana ɓudewa. Duk abinda yake idon Islam na kansa,tana kallon sa,ɗan jijjiga kai tayi tare da dan ne lips ɗin ta na kasa.cikin zuciyar ta tana mai cewa"zakayi bayani ne kwarton banza,wato kana jin daɗi ina shafa maka ƙafa cikin salon iskanci ko?yanzu zaka dawo hayyacin ka" ta kai ƙarshen zancen zucinta, tana mai cafke ƙafar tashi da ƙarfi. Aslam Yana can ya fara lulawa duniyar jin daɗin sa,dan tuni zuciya da gangar jikinsa sun fara amsar tayin Islam,kawai ba sani ba sabo yaji wani ramtsatstse zafi ya ratsa kwakwalwar sa,sannan ya watsu cikin sassan jikin sa. Da sauri ya buɗe jajayen idanun sa,ya sauƙe su kan fuskar islam.wacce ke kallonsa cikin wani salo na ɗaukar hankali,da murmushin ƙeta. Saurin kawar da kansa yayi tare da haɗe rai. Ƙara matsa kafar Islam tayi da karfin Daya fi na farko. "Washhhhh mommy "ya furta ahankali yana mai kamo hannun mommy idonsa arufe. Sannu aslma,ai laifin ka ne,kabar ƙafar tayi maka tsami da yawa,dole kaji zafi sosai."cewar Daddy kenan cikin tausayawa. Mommy kuwa kansa kawai take shafawa cike da tausayi. Haka Islam ta dage tana ta matsa kafar Aslam cikin mugunta,saida ta tabbatar ya azabtu dan gaba ɗaya gumi ya gama wanke masa jiki,tuni zazzaɓi yayi nashi gurin. Kafin tace "dadddy ya sami gocewar ƙashi ne,kuma ya bari har saida gurin ya kumbura,yanzu ma da gyar na gano hakan,dan haka yanzu zan gyara masa ƙashin, amma saiya ɗaure dan naga kamar rago ne"Islam ta fada tana nuna alamun tausayi akan fuskarta. "Wani matsiyacin kallo Aslam ya bi ta dashi,wato shine ma rago?yanzu duk wannan iskancin data gama yi masa da ƙafa bata gama gyarawa ba kenan? Wllh yasan da nufi tayi masa hakan,amma ba komai akwai ranar ƙin dillanci,duk ranar daya shigo hannunsa wllh saita raina kanta. "Karki damu Islam ki gyara masa,ai dole ya daure inba haka ba sai kafar ta sami matsala"cewar Daddy kenan. Haka Aslam yana ji yana gani Islam ta kama ƙafarsa taci gaba da gana masa azaba,aganinsa, amma wannan karon kam gyara tayi masa na tsakani da Allah,dama kuma tana kallon ƙafar ta gane gociyar kashin ne ,kawai taso bashi wahala ne. Idan kuka ga Aslam awannan lokacin saikun tausaya masa,dan ba ƙaramin wahala ya sha ba,sai cizon lips kawai yake yana juya kai.gumi kuwa kamar yayi wanka. Su mommy sai sannu suke masa. "Daddy na kammala,yanzu sai ya kula sosai banda garajen tashi idan zaiyi wani abu akwai buƙatar ya sanar dani,dan In nuna masa yadda zai motsa kafar" "Sannu Islam Allah yayi miki albarka "Daddy ya faɗa cikin jin daɗin yadda take taimakon ahalinsa. Murmushi tayi kawai tana kallon Aslam Wanda yayi lamo akwance,kansa akan cinyar mommy Yana maida numfashi. cikin zuciyarsa kuwa tunanin hanyar ɗaukar fansa yake. "Mommy yanzu aɗan kawo masa farfesu mai yaji sosai ya samu yaci" Islam ta fada tana kallon mommy. "To Islam Bari na haɗo masa yanzu mun gode ƴata"cewar mommy tana shafa kan Islam. Murmushi tayi tana mai cewa,ba komai mommy zan ma jira ki kawo dan naji yanayin yajin da ake buƙata idan yayi kuma in dan kula dashi karya motsa kafar,tunda yanzu zai ji tana masa zugi "Islam ta faɗa tana kallon mommy fuskarta ɗauke da murmushi. Murmushi mommy tayi kafin ta fice daga ɗakin ta nufi kitchen Dan haɗawa Aslam farfesun. Tana ganin mommy ta fice ta kalli Daddy tace "daddy Ina buƙatar man zafi dan yin addu'a aciki, sai a rinƙa shafa masa"to Daddy ya ce sannan ya nufi ƙofar barin ɗakin,bashi da wata damuwa tunda yasan Aslam baida lafiya,bare yayi yunkurin yiwa Aslam wani abu,kuma yaji gargaɗin da yayi masa,dan haka hankali kwance ya fita dan kawo man zafin. Daddy na fita Islam ta sanya dariya har da riƙe ciki.kallonta kawai Aslam ya tsaya yi ba tare da yace komai ba,to me zaice ya fuskanci abun na iso sai godiyar Allah kawai,amma tabbas tana da matsalar ƙwaƙwalwa. Zagayawa tayi kusa da inda kansa yake, rungume hannu tayi tana kallon sa da fuskar tausayi kafin ta fara girgiza kai tana faɗin"Allah sarki malam tinjimi, kaɗan bani tausayi kaɗan,dubeka akwance shirim kamar kayan wanki,amma duk kai ka jawa kanka,taurin kai da rashin kunya sune matsalar ka,Ni kuma bana ɗaukar raini haka Allah yayi ni,shiyasa duk wanda ya shiga gona ta yake shan wahala,kai kuma abubuwan sunyi maka yawa,gaka ɗan iska mai shegen son mata,kai da fa ka zata da farko ina taɓa maka ƙafa ne dan kaji daɗi,shine har da wani lumshe ido,kai ga jarababbe, daga mace ta rabeka saika fara layi kamar ɗan giya ko?ai da gangan nayi maka hakan,sannan na ƙara tada ciwon yadda zamani zafi sosai kafin na gyara maka.kaga nan gaba saika ƙara yimin abun da ba daidai ba next time ƙarya ƙafar zanyi"ta faɗa tana nuna yadda zata karya ƙafar tashi da hannunta. Bakin ciki,ta kaici,tsana ,haushi sune suka taru suka cunkushe zuciyar Aslam,ji yake kamar ya kurma ihu ko zai samu sassauci cikin zuciyar sa, shi mutum ne da bai fiye son doguwar magana ba,amma yarinyar nan ƙarfi da yaji nema take ta sanya shi yazama mafadaci,amma bazai kula ta ba,sai dai taga sakamako aƙasa.dan haka yayi shiru bai ce mata komai ba,sai zuciyar sa dake masa zafi kamar wuta. Islam kuwa jin baice mata komai ba yasa taji haushi cikin ranta. Cikin masifa tace "wato ka maida ni mahaukaciya, ina ta magana kayi shiru ko?ta faɗa tana bugar ƙafar sa mai ciwon. Runtse ido yayi da ƙarfi yace "washhh,kafin ya buɗe idon ya sauke akan Islam --to meye marabar ki da mahaukatan aike bayan hauka ma jahilci da rashin sanin girman na gaba dake,sannan da rashin tarbiyya sune babbar damuwarki, ga dukkan alamu iyayen ki basu baki tarbiyyar mai kyau ba,sam baki da kamun kai,sannna da ganin ki riƙaƙƙiyar karuwa ce, kin gama yawon iskancin ki shine kikazo nan kike cutar da rayuwar mu, I hate you with all my heart,sannna ki saurari sakamakon abinda kika yi min sai kinyi dana sani Kum....." Da ƙarfi Islam ta toshe kunnen ta, tare da sanya wani irin ƙara mai firgitarwa,wanda sai da yayi sanadin da turarukan dake kan madubin Aslam suka faɗi ƙasa tare da tarwatsewa. Banda rawa ba abinda jikin Islam keyi,tunda take arayuwa ba wanda ya taɓa gasa mata maganganu makaman tan irin wanda Aslam ya yaba mata yanzu,hakan yayi matuƙar ƙona mata zuciya,yadda ya ke jifan iyayen ta da munanan kalamai, lallai Aslam baida tarbiyya ko kaɗan, yana buƙatar gyara. Cikin wani irin yanayi na rinewar kwayar idon ta,daga fari zuwa jaa sosai,ta buɗe idon tare da saukesu akan fuskar Aslam,Wanda yayi kasaƙe yana kallon ta cikin mamaki,anya yarinyar nan mutum ce?daga yin ihu kalli yadda kwalaben turare suka farfashe?gaskiya koda ta kasance mutum akwai shafin aljanu tare da ita. Ƙurrr ta kafe Aslam da idanun ta,wanda suka koma masu ban tsoro, magana ta fara cikin wani irin sauti mai kama da tsawa"kayi kuskuren shiga gona ta Aslam,baka isa kaci mutuncin iyaye na ka zauna lafiya ba,zan gwada maka irin tarbiyyar banzar da suka bani ka kuka da kanka"Islam ta fada cikin zubda wani irin hawaye mai kama da jini.tana kaiwa nan ta juya cikin takun sauri ta bar ɗakin,inda sukaci karo da mommy ta taho daga kitchen da gudu,dan taji ihun da Islam ɗin kwalla. "Lafiya kuwa islam? Me ya faru?ko dai yayi miki wani abun ne?"cewar mommy tana riƙe kafaɗun Islam ɗin. Kallon mommy Islam tayi, kafin ta girgiza kanta ahankali tana sakin murmushin yaƙe,wanda kallo ɗaya zakayi mata kasan bai kai har zuciya ba."ikon Allah meye wannan kuma yake zuba daga idanun ki kamar jini?"cewar mommy tana kai hannu kan fuskar Islam. Kafin hannun nata ya ƙara sa kan fuskar, Islam tayi saurin barin gurin.kai tsaye kitchen ta wuce inda mommy ke dafawa Aslam farfesu.robar dakakken yaji ta ɗauka ta zazzafar cikin tukunyar sosai,sannan ta juyyuya yadda baza'a gane ba ta rufe tare da ficewa daga kitchen ɗin Binta kawai mommy tayi da kallo tana mamaki abinda idanunta suka gani,to kodai kukan jini yarinyar take yi ne?amma meye zai sa ta yi kukan jini ita da ba aljana ba?cikin dakin na Aslam ta shiga,dan tambayar sa abinda ya faru. Yana nan kwance,ba alamun damuwa akan fuskar sa,saima murmushi data ga kamar yanayi,dan ba karamin daɗi Aslam yaji ba,yau ya ɓatawa Islam rai ,dan haka zai ci gaba da faɗa mata maganganu masu zafin da zasu iya fasa mata zuciya kowa ma ya huta. "Aslam me kuma kayi wa Islam naga ta fita ranta abace?sannna kamar ma kuka take har da jini"cewar mommy bayan ta shigo cikin dakin. Ahankali Aslam ya buɗe idonsa yana kallon mommy"mommy nikuma da nake kwance me zan mata?kinga barci ma ya fara ɗauka na,bansan bata cikin ɗakin bama"ya faɗa cikin halin ko inkula yana mai da idonsa ya kulle. Shiru mommy tayi na ɗan wani lokaci kafin ta fice,farfesun ta zubo masa cikin kula,ta hado da flate da cokali ta dawo dakin. Dai-dai lokacin Daddy ya kawo maganin zafin.sai dai mommy tace Islam ɗin ta fita,sai dai ya ajiye idan ta dawo tayi addu'ar ta shafa masa. Koda mommy ta zubawa Aslam farfesun nan,ai yanayin cokali ɗaya ya fara zare ido,dan yaji sosai ne aciki.gashi shi kwata kwata baya ƙaunar yaji."mommy bazan iya cin wannan naman ba,yaji yayi yawa"Aslam ya faɗa yana gwabe fuska. "Na san baka don yaji Aslam,Amma Dole ka daure kaci,ko dan samun lafiyar ka"mommy ta fada tana dibo naman cikin cokali. Haka mommy ta tusashi gaba,yana cin naman,duk loma ɗaya saiya sha ruwa,da gyar yayi loma biyar yace ya koshi.ji yake harshen sa kamar zai zazzago dan zafin yajin. Mommy kuwa ficewa tayi daga ɗakin ta kai flate ɗin kitchen. Gaba ɗaya Aslam ya rasa inda zai tsoma rayuwar sa,idonsa yayi jajur banda azaba ba abinda bakinsa keyi,ahankali ya dauko daga kan gadon ya nufi toilet cikin ɗingisawa,yana ɗan runtse ido,kan sink kawai yake ya tsaya tare da bude bakin sa yana kwara ruwa aciki.amma kamar ƙara zafin yake. Cikin gigita ya zame tare da zama agurin yana mai runtse ido. Islam kuwa har ta bar falon tayi wani tunani dan haka kai tsaye ta juyo cikin gidan bayan ta kira janbu.dakin Aslam suka shiga yana hannunta.lokaci Aman yana barci afalo,dan shi yafi Zama sosai afalon saboda masu zuwa duba shi. Suna shiga ɗakin tace "janbu daga yau anan zamu rinka hutawa, akan wannan gadon, dan haka maza hau mu kwanta"ta fada tana sakin janbu,shikuwa ya ɗare kan gadon aman. Itama hawa tayi tare da yin miƙa kafin ta janyo filo ta kwanta. Kusan minti biyar kuwa barci ya fara daukarta, dan sosai taji daɗin gadon. Saida Aslam ya kwashe kusan minti goma cikin wannan mawuyacin hali kafin ya yunƙura ya mike,wanka yayi tare da sanya rigar wanka ajikinsa,sannan ya fito .zuciyarsa daya Yaga shiryawa cikin wasu riga da wando,marasa nauyi,wandon iya gwuiwa ne,sai rigar mai yankakken hannu ce.turare ya feshe jikinsa dashi,kafin ya nufi gadon. Kasancewar barci yake ji sosai kuma ɗakin nashi ba haske sosai ya kashe kwan mai haske ,hakan ya hanashi ganin Islam da janbun ta. Kai tsaye ya haye kan gadon tare da kwanciya.miƙa hannunsa yayi dan ɗauki wayarsa kawai yaji ya kai hannun sa kan abu mai matukar laushi. Azabure ya tashi zaune tare da danna Madannin hasken dakin.nan da nan ɗakin ya gauraye da haske. Cikin firgici ya zaro ido sakamakon abinda idanunsa suka gane masa...... Ko me ya gani? Muje zuwa. Anty mammy. [9/23/2022, 10:58 AM] Abk: _______________Zaro ido sosai Aslam Yayi cikin mamaki da tsoro,mamakin nashi ba komai bane face,ganin Islam kwance maɗe-maɗe akan gadon sa. sannan abinda ya bashi tsoro kuma,ganin biri shima kwance akan gadon nashi,da sauri ya ja baya yana dafe ƙirji.lallai yarinyar nan ta cika hatsabibiya tama rasa inda zata kwanta,sai kan gadon sa?kuma bayan haka harda biri? Cikin ɓacin rai ya nufi inda Islam ke kwance,yana zuwa baiyi wata wata ba ya sanya hannunsa ya finciko ta tare da jefar da ita aƙasan dakin. Cikin huci yake kallon Islam,wacce tayi firgigit ta tashi aɗan tsorace,dan barci ya fara kamata kawai ta jita aƙasa. "Har ke wace ce?da zaki hau min kan gado,da wannan ƙazamin jikin naki?how dare you?ya faɗa cikin tsawa, dan zuwa wannnan lokacin Aslam ya gama ƙufula sosai da Islam,baya kuma tsoron duk abinda zai faru,dole ya koya mata hankali. Kallon sa Islam keyi cike da tsantsar haushin yadda ya wani cillar da ita a ƙasa kamar kayan wanki, "akan me zaka cillar dani haka kamar wata dabba? Dan kawai na hau wannan banzan gadon naka?"Islam ta fada cikin jin haushinsa . "Saboda baki da mara ba da dabbar agareni,ke shaiɗaniya ce marar hankali,jaka kuma mahaukaciya,kisani duk abubuwan da kike min bawai ina tsoron ki bane,ina gudun ɓacin ran mahaifa na ne,wllh da tuni na gama da ke, dan ke ba komai bace face ƙaramar alhaki,na tsane ki! Bana ƙaunar ganin ki,ahalin yanzu kaf duniya bani da wanda na tsana sama dake ahate you ƴar bariki wacce bata sami tarbiyya ba"Aslam ya kai ƙarshen maganar sa da tsawa, kamar zai fasa mata kunne. Kallon sa kawai Islam keyi,idanun ta sunyi jaaa sosai,haƙiƙa maganganun Aslam sun shiga zuciyar ta,sun matukar dukan ta,zafin da take ji cikin ranta kuwa,Allah ne kadai ya san iyakar sa. Kallon kallon suke tsakanin su,ko wannen su,zuciyar sa cike da tsanar dan uwansa. Ahankali Islam ta daga kafar ta ta fara tahowa zuwa gareshi ,sai da tazo gab dashi kafin ta tsaya.idanunta har lokacin yana kan kyakykyawar fuskar Aslam,ajiyar zuciya ta sauƙe mai zafi tare da huro iska daga bakinta,kafin ta fara magana. "Kayi munanan kalamai akaina,ba tare da sanin ko niɗin wace ce ba,ka zage ni, ka kirani da karuwa marar kamun kai,sannan ka zagi iyayen na,kace basu bani tarbiyya mai kyau ba,ina so kasani,kamar yadda kake kallon iyayen ka matsayin waɗan da suka raine ka da tarbiyya haka nima nake kallon nawa iyayen,domin tarbiyyar da suka bani itace ta sanya na kawo har wannan lokacin cikin mutunci,abu guda dana sani shine,ba wani mahaluƙin da zai cutar dani in gyale shi,sannan wannan gidan naku bani na nuna ina da ra'ayin zuwa ba,baban ka shine wanda ya takura Ni akan saina biyo shi,bana son shiga cikin mutane ,saboda marasa adalci irinka,baku da wani buri daya wuce tozarta mutum,da son cutar da rayuwar sa.ka sani Aslam na tsane ka,kamar yadda ka tsane ni, bana ƙaunar ganin ka, i hate everything about you,Kaine mutum na farko daya fara sanya Ni kuka,kuma zakayi dana sanin aikata hakan,kuma kasani nasan duk halin da kake ciki,da sannu zan tona maka asiri gurin iyayenka da kake yaudara,janbu zo mu tafi"Islam ta kai ƙarshen zancen ta tana share guntun hawayen daya zubo mata tare da nufar ƙofar dakin. Harara Aslam ya bita dashi yana faɗin"wllh duk ranar da kika ƙara zuwa dakina saina illata ki,banza useless kawai marar hankali" Juyowa Islam tayi ta kafa masa idanu,kafin tace "wannan na saka shi cikin raina,duk lokacin dana bukaci zama cikin ɗakin nan naka,to tabbas zan zo kuma zan huta cikin sa, ba ɗan iskan daya isa ya hana ni"tana kaiwa nan azancen ta tayi waje da sauri. Duka Aslam ya kaiwa bango cikin ɓacin rai yake faɗin."I hate you na tsane ki bana son ganin ki"ya faɗa da ƙarfi yana ƙara kaiwa bango duka . Islam tana fida daga ɗakin ta nufi dakin granny,bayi ta shige da sauri,tana zuwa ta kunna shaya tare da zamewa gefe guda ta zauna tana mai sakin kuka.kuka take sosai tana mai tuna iyayen ta sosai yau ɗin nan take jin mugun kewar su,ƙaddara ta raba ta da su ta kawo ta inda ake zagin su da faɗa mata munanan kalamai. "Wllh bazan Barka ba Aslam,saina ƙuntata rayuwar ka,saina hanaka farin ciki,kamar yadda ka sanya Ni kuka"Islam ta faɗa da ƙarfi cikin kuka. Ta jima tana kuka atoilet,kukan da zata iya rantse wa bata taɓa yin irin sa ba,tun da take arayuwar ta.amma yau silar Aslam ta zubda hawayen ta,ta yaya zata gyale shi? Aslam kuwa gaba ɗaya tsantsanin gadon da ɗakin ma gaba ɗaya yaji yanayi,dan haka cikin takun dingishi ya bar ɗakinsa zuwa dakin mommy. Tun daga wannan rana kuma ya fita harkar Islam,ko da wasa baya barin wata damar da zata haɗa su da Islam,baya ma zaman gidan,tun yana dingisa ƙafar sa har ya zo ya take ta,idan yana gida ma,to zaka sameshi part ɗin daddy, Dan baya son abinda zai haɗashi da Islam,sosai yake jin tsanar ta cikin ransa,baya ƙaunar ganin ta. Bangaren Islam ma sam bata son ganin Aslam ahalin yanzu,bata zama cikin gidan ma,rai da rai tana garden,ita da janbu,suna kan bishiya.damuwa tayi mata yawa,tana matuƙar son ganin malamin ta,amma shiru tun daga ranar nan,bai ƙara zuwa gare ta ba. Yau sati biyun da daddy ya ɗibarwa Aslam suka cika,dan haka suna zaune shida mommy apart ɗin sa yace"Madam,yau ne adadin kwanakin dana ɗibarwa ɗan ki ya cika,dan haka akira min shi ɗan jin inda zancen mu ya kwana"ya kai zancen sa yana canja tashar labarai. Shiru mommy tayi bata ce komai ba,sai wayar ta kawai data ɗauko tare da kiran wayar Aslam,tana tunanin da wuya idan Aslam ya samo matar da zai aura kam,dan tasan halin Aslam Sarai . Lokacin da mommy ta kira Aslam Yana ɗakinsa, wanda shigar sa kenan,yayi wanka.yana sanye da jallabiya kasancewar magrib ne lokacin,turare kawai ya feshe jikinsa da shi,ya fito. Yaran gidan duka suna falo,banda Islam,shi wllh yanzu har mantawa yake da wata Islam,dan tun ranar da wannan abun ya faru bai kara sanya ta cikin idanun sa ba.dan ko abinci baya fitowa falo yaci,Gara ya ci abin sa aɗakin sa. Haka ya wuce yaran suna ta masa sannu da fitowa. Yana shiga ɗaki kuma saiga Islam sun fito ita da granny. Da sallama ya karasa dakin Daddyn nashi,zama yayi bayan an amsa masa sallar. "Daddy barka da gida "ya faɗa cikin ladabi. "Yawwa Aslam,ya ƙafar taka ?fatan dai ba wata matsala yanzu"cewar Daddy Yana kallon Aslam. "Babu daddy ai tuni ƙafar ta warke sosai ma,bana jin ciwo ko kaɗan"cewar Aslam,Yana son jin abinda ya sanya daddy neman sa,dan shi sam ya ma manta da umarnin da daddy ya bashi na neman mata. Jinjina kai daddy Yayi kafin yace "Alhmdllh,yanzu saika faɗa min inda ka samo yarinyar da zaka aura ko?dan yau adadin kwanakin dana ɗibar maka suka cika,dan haka ina sauraron ka"daddy ya faɗa fuska ba wasa. Darammmm !!! Gaban Aslam ya faɗi,Dan shi wllh yama manta da wannan batun,kuma yana ganin tunda yayi rashin lafiyar nan,ai Daddy zai dan jinkirta akan batun,ashe Daddyn yana sane kuma bai manta ba. Shiru yayi kansa a ƙasa,dan baisan me zai faɗa wa Daddyn ba. "Ina sauraron ka Aslam,bana son shirme fa,kayi shiru kana wani sunkuyar da kanka ƙasa,kai nake jira"cewar daddy cikin dan ɗaga murya,dan yaga aslma na son kawo masa wargi. Ɗago da kai Aslam Yayi yana kallon mommy,fuskar sa tayi kalar tausayi,mommy kuwa kawar da nata kan tayi dan kuwa bata goyon bayan Aslam awannan karon,itama tana so da ƙaunar ganin yayi aure. Cikin sanyin murya Aslam ke faɗin"daddy kayi haƙuri Dan Allah aƙara min lokaci,wllh ban samu damar tsayawa na kalli yan matan Bama ,bare na zaɓi matar da zan aura,saboda wannan ciwon ƙafar da nayi,amma in sha Allahu zan kawo matar da zan aura very soon daddy"Aslam ya faɗa yana fatan amincewar daddy akan abinda ya faɗa. "Zancen banza kenan,Aslam saboda ka raina Ni kuma baka da burin yin auren,shine zaka kawo min wannan maganar anan?to wllh na kara maka kwana uku,idan baka kawo min matar da zaka aura ba,zan ɗauki mataki mai zafi akan ka,dan haka zaɓi ya rage naka"cewar daddy kenan yana maida hankalinsa kan labaran da ake haskawa. Kallon mommy Aslam Yayi tare da ɗan turo baki yana mai kamo hannunta,cikin ƙasa da murya yace "mommy please kisa baki ya ɗan ƙaramin lokaci mana" "A'a Aslam,wannna karon ba ruwana wllh,duk hukuncin da Daddyn ku ya yanke shikenan,dan na fahimci ba son yin auren kake ba,haka kawai ka zauna sai jawa mutane rai kake,wllh ka samo matar kamar yadda ya faɗa"cewar mommy tana zare hannun ta daga cikin na Aslam. Haka nan Aslam ya tashi jiki ba kwari ya bar ɗakin na daddy,tunani yake yanzu shi wa zai kawo matsayin matar da zai aura nan da kwana uku?shi fa sam har yanzu baiga dai-dai dashi agarin nan ba,duk wayewar su tayi yawa,shikuma mace yake so ya aura mai tarbiyya yar mutunci.yana wannan tunanin har ya kawo tsakiyar falon bai sani ba.saida yaji granny na faɗin"yoo ikon Allah,yau naga sabuwar tijara gangariya,yanzu kai Asalamu, kamar wani Giwa ka taho sanƙan-sanƙan kana neman take Ni?kalli yadda kake wani tafiya kamar bijimin sa ,wllh idan ka mangareni da wannan ƙafar taka kamar shebur saina rama,Dan zagewa zanyi mu doku da kai,ba tsoronka nake ji ba"cewar granny cikin masifa,tana matsawa gefe dan aƙasa take zaune,shikuma Aslam ya biyo ta jikinta sosai kamar zai bi ta kanta,wanda shi baima luraba ko kaɗan. Tsayawa yayi tare da kallon granny yadda ta haƙikance tana bala'i girgiza kai yayi kafin yace "to sarkin faɗa amma dai banbi ta kan naki ba ko?saiki sarara da wannan surutun naki kamar aku" "Wllh uwarka ce Aku bani ba ,yaron banza kawai,ai Gara kayi kayi auren ka bar gidan nan kowa ya huta mai baƙin hali" Harara ya bankawa granny kafin yace "ba saiki yimin auren ba,cikin garin nan banga macen da zan iya aura ba,gaba ɗayan su basu da tarbiyya,yan iskane lalatattu. ba wacce zan aura " Ya kai zancen sa yana yatsine fuska.kuma har lokacin idonsa bai sauƙa kan Islam ba. Ita kuwa Islam jin abinda yake fadi,saitayi tunanin da ita yake,dan haka ranta yayi mugun ɓaci sosai,ita da ta fita harkar sa shine yake yaɓa mata maganganu haka? Cikin zafin zuciya ta kalli granny tace "granny kinsan duk wanda yake watse wa atiti baya son yayi aure,sannan yana kallon kowa ne kamar halin su ɗaya,kuma da yawa masu cewar yaran mutane watsatstsu ne ,to sune manyan watsatstsu dake bata tarbiyyar yaran,daga baya kuma suce bazasu aure su ba da sunan basu da tarbiyya" tayi shiru tana huci da hararar Aslam,kana jin yanayin yadda take maganar ta kasan ranta abace yake,kuma kai tsaye take aika saƙo zuwa ga wani. Sai lokacin Aslam ya San da ita agurin,kallon ta yayi fuskar sa ahade sosai,rabon da ya ganta kusan sati kenan,ashe mayyar tana gidan har yanzu? "Kwarai kuwa Islama zancen ki haka yake,sune masu sanya yaran mutane suna latsewa a lungu,wllh tun wuri Gara kayi aure kafin mu nemo maka da kanmu" "Allah ya kiyaye Ni Aslam ,anemo min matar da zan aura,ai wannan sai ya'yan da basu da galihu, masu bin gidajen mutane suna laɓewa,waɗan da suka gama yawon barikin su sukaga ba ci, sune akewa irin wannan, amma Ni cikakken ɗa ne wanda ke gaban iyayen sa,dan haka ina da cikakkiyar damar da zan zabi matar da nake son aure ba kowacce kara biti ba "Aslam na kawo wa nan azancen sa yayi wucewar sa zuwa ɗakinsa. Nan ya bar Islam da tarin damuwa cikin ranta,wato itace marar galihu agidan?sannan wacce ta gama yawon iskancin ta?hmmmmm Aslam kenan zan nuna maka kalar nawa karuwan ci,zaka sha mamaki na Ni Islam.ta faɗa cikin ranta tana murmushi tuno da irin makircin da zata kullawa Aslam. Washe gari da yamma,jannat tayi baƙo, dan haka ansha ƙwalliya cikin riga da siket na atamfa,wanda suka matse jikinta,shima sai da mommy tayi da gaske kafin ta sanya kayan,dan ita ƙananan kaya take son sanyawa.suna ɗakin baki suna hirar su ita da saurayinta, wanda hira ce wacce bata dace ba sam,dan jannat tana jikin saurayin sai shafa ta yake da taɓe-taɓe ajikinta,su aganinsu wannan itace soyayya. Sunyi nisa sosai da shafe shafe su,wanda har basu sani ba,suke ta sauke nishi na jin dadi,dai dai lokacin kuma Islam ta taho dan zuwa garden,kawai take jiyo nishi sosai aɗakin,tunani tayi ko menene cikin dakin haka?dan bata san jannat na cikin dakin ita da saurayin ta ba,kawai ta sanya kanta cikin dakin, Abinda idanunta suka gane mata ne yayi silar kwalla karanta,cikin tsoro. Jannat ce kwance kan kujera yayi da saurayin ke kanta yana lashe duk wani sannan na jikinta,dan tuni anyi wurgi da rigar jikin jannat. Ihun Islam kuma yayi dai dai da karasowar Aslam gurin,dan haka da sauri ya kunna kansa cikin dakin da yajiyo ihun,yana shiga idon sa yayi arba da jannat kwance maɗe -maɗe wani gardin yana sarrafata. Tsabar tsoron abinda Islam ta gani jikinta rawa kawai yake da sauri ta nufi Aslam Wanda shima yayi mutuwar tsaye cike da mamakin jannat ɗin.... Muje zuwa anty mammy ce. Mrs babi [9/26/2022, 12:35 PM] Abk: _____________Tsabar tsoron abinda idanun Islam suka gani,jikinta rawa yake ta nufi inda Aslam ke tsaye kamar gunki,cikin shocking.tana zuwa gareshi ta kama gefen rigar sa tace,"Aslam ka gani ko?kaga halin da ƙanwar ka ke ciki,kalli abinda jannat keyi acikin gidan ku,tare da wannan shegen mai kama da talo-talo"Islam ta fada cikin ɓacin rai da tsoro. Kallon ta Aslam Yayi,zuciyar sa na wani irin bugawa kamar zata fito,haƙiƙa abinda idanunsa suka gani yau,yayi matuƙar girgiza shi,mamaki da al'ajabi sun hana shi yin koda ƙwaƙwƙwaran motsi.kallon jannat kawai yake wacce ta gama kiciniyar maida rigarta, jikin ta sai rawa yake tana kallon yayan nata. Shima saurayin yana tsaye ya kasa motsi sai zare ido yake. Girgiza Aslam da karfi islam tayi ,da ƙarfi tace "tsaya wa zakayi kana kallon wannan shegen fitinnan ne daya zo har gida yana ƙoƙarin bata maka ƙanwa?wallahi yau bazaka bar gidan nan salin alin ba,saika ci ubanka,nan gaba bazaka ƙara zuwa gidan mutane kayiwa ƴaƴansu iskanci ba"Islam na kaiwa nan maganar ta tayi kan saurayin jannat gadan gadan,tana zuwa ta wanke shi da maruka har uku masu zafi da shiga jiki.dafe kuncin sa saurayin yayi yana kallon Islam,dan sosai marin ya shige sa. "Bar kallo na annamimi dan iska,wllh kaima kana zaune agabanka za'a lalata ƙanwar ka,maha'inci mugu azzalumi yau zaka yabawa aya zaƙin ta"Islam ta fada tana kaiwa saurayin nan duka ,tun yana kallon abun kamar wasa, ya 'na kare kasan har ya kasa kare kannasar,dan irin dukan da Islam ke masa,abin zai baka mamaki,naushinsa kawai take da bashi ƙafa.abinka da yayan masu kudi,dama jiki ba kwari nan da nan ya galabaita ahannun Islam sai jini ke zuba ahancin sa da bakin sa. Kuka sosai jannat keyi hannun ta aka,ganin yadda jini ke fita ta baki da hancin saurayin nata. Cikin mutuwar jiki da tarin damuwa Aslam ya tako zuwa inda saurayin nan ke kwance Islam na jibgarsa,hannu ya sanya cikin sanyin jiki ya kamo hannun Islam, cilak! ya miƙar da ita tsaye tare da riƙe kafadar ta yana kallon ta,idanunsa sunyi jaaa,sosai.girgiza mata kai yake alamun ta daina dukan saurayin. Cikin huci da fushi ta fizge kafaɗar ta tana faɗin"ka barni na hukunta wannan shegen yaron,domin sune suke lalata yayan mutane. "shegiya kema mai kama da muciya, ana. Kallo ki haka ashe shaiɗaniya ce ke,yanzu idan mommy taji wannan labarin me kike tsammanin zai faru da ita?wane halin damuwa kike tunanin zata shiga? Jannat kin cuci kanki,kin ɓata tunanin ki,wllh ban taba tunanin wayonki na banza bane sha sha sha kawai" Cikin kuka jannat tace "wllh ba laifi na bane shine yace wai.... Tass Islam ta dauke ta da mari tana huci."rufemin baki,wawiya idan yace kiyi abu sai kiyi?uban ki ne shi?ko shi Aslam ne ?banza marar wayo kawai" Durƙushewa jannat tayi agurin tana kuka sosai,tare da kamo ƙafar yayan ta, "Dan Allah yaya kayi haƙuri,wllh sharrin shaidan ne,kayi min duk hukuncin da zakayi min,amma karsu mommy suji wanan maganar,nayi nadama yaya "jannat ta fada cikin kuka sosai harda shashsheƙa. Kallonta kawai Aslam keyi,zuciyar sa na masa zafi sosai,ashe haka iyayen waɗan da ake lalatawa rayuwa suke jin zafi aransu?bai taba jin nadamar abinda ya ke aikatawa ba arayuwar sa sai yau,shi gani ma yake kamar shine ya jawa jannat faruwar wannan al'amarin. Hannunsa ya sanya tare da kamo kafaɗun jannat ya miƙar da ita tsaye.kallonta yake ba tare da yace komai ba. Fuskar sa ba walwala ko kaɗan. Ita kuwa sai kuka take jikinta na rawa. Saurayin nan haka ya ja jiki ya zauna a ƙasa tare da jingina bayansa jikin kujera sai maida numfashi yake. Cikin rawar murya yace "dan Allah kuyi hakuri,wllh sharrin shaidan ne,In shaa Allahu hakan bazata ƙara faruwa ba,na tuba yaya Aslam ka ya femin" ya faɗa cikin zubda hawaye. Kallonsa Aslam yayi bayan ya zaunar da jannat kan kujera shikuma ya jingina da jikin bango. "Yanzu kai wannan abunda kukeyi aganin ka shine soyayya?meye ribar ka idan ka lalata rayuwar wacce kake so?shin da gaske kake ƙaunar jannat?" Aslam ya faɗa da Muryar sa da tayi mugun sanyi. "Wllh da gaske nake ƙaunar jannat,kuma auren ta nake son yi "saurayin ya faɗa da sauri yana kallon Aslam. Ajiyar zuciya yayi kafin yace shikenan,ina son ka turo magabatan ka domin ayi magana adaura muku aure,amma ka kula kada ka sake yunƙurin aikata irin wanan abun da kuka yi yanzu tashi ka tafi gida" Aslam ya faɗa yana ƙarasowa kusa da saurayin ya miƙar dashi tsaye tare da gyara masa kwalar rigar sa. "Na gode yayanmu in sha Allah zan sanar da iyayyena kuma duk yadda ake ciki zan sanar da jannat ta faɗa maka"cewar saurayin yana sunkuyar da kansa ƙasa. "A'a daga yau bazaku sake yin waya da jannat ba,sannan bazaka ƙara zuwa hira ba,har sai an gama maganar auren ku,dan wllh Ni har yanzu Ban wani yar da da tuban ka ba ja'iri fitinanne"cewar Islam kenan cikin tarar numfashin sa. Jinjina kai Aslam Yayi yace "tabbas wannan maganar haka take,ba waya ba hira har sai mun gama magana da iyayenka, kaje kawai" Sumi -sumi ya kama hanyar barin falon yana ɗan ɗingisa ƙafa,har ya kai bakin ƙofa,juyowa yake son yi dan ya kalli jannat Islam ta daka masa tsawa"kul!! Karka sake ka waigo wllh maza ka fice daga ɗakin nan "ta fada cikin tsawa. Da sauri kuwa ya ƙarasa ficewa daga ɗakin,yana mamakin wannan wace yarinya ce mai shegen ƙarfi da iya subirbuɗar mutum haka? "Ke kuma jannat yanzu irin tarbiyyar da mommy ta baki kenan?yanzu irin rayuwar da kike yi acikin gidan ku kenan?meye ribar ki akan aikata irin wannan?meyasa baki sanar damu cewa aure kike so ba?da tuni mun aurar dake ba sai kinzo kina zubar mana da mutunci ba" Kuka sosai jannat keyi kamar ranta zai fita,bata taɓa jin kunya da nadama irin ta yau ba,"dan Allah yaya kayi hakuri wllh sharrin shaidan ne da son zuciya,amma wllh bazan sake ba,kayi min duk hukuncin daya dace,amma dan Allah karufa min asiri kar su mommy suji wannan maganar "jannat ta fada cikin sarƙewar murya tsabar kuka. "Dole su mommy su san halin da kike ciki jannat,domin kinci amanarsu ,kuma keda kika saɓawa Allah meye naki na jin tsoron bayin sa su sani,shiɗin fa yana kallon ki ko kin manta?tashi ki shiga ciki kafin nan ki bani wayar ki "Aslam ya faɗa cikin haɗe rai. Hannu na karkarwa jannat ta mika masa wayar tana kuka,kafin ta tashi jiki ba kwari ta nufi cikin gida,tana fatan Allah yasa ba kowa cikin Falon. Tana fita ɗakin ya rage daga Aslam sai Islam,sosai taji tausayin kukan da jannat keyi,tasan dole taji tsoron iyayensu su san wannan maganar,kallon aslam tayi wanda ya dafe kansa yayi shiru tare da lumshe idonsa,istigfari kawai yake cikin ransa yana tuba ga Allah,yanzu haka watarana za'ayiwa yarsa kenan idan bai daina ba?tun yanzu ga abin ya fara biyar ƙanwar sa, Ƙarasowa kusa dashi Islam tayi tare da zama,ajiyar zuciya ta sauke tare da kallon sa ta fara magana"kaga ka kwantar da hankalin ka,abinda ya faru ya riga ya faru,saidai Allah ya kiyaye gaba,sannan ya kamata kasanya ido akan ƙannan ka sosai,kasan yadda suke rayuwa,Ni dama na jima ina zargin jannat,dan kuwa ina jin yanayin yadda take waya,wani lokacin ma shike haɗamu faɗa da ita,kuma kayi shiru da maganar nan iya tsakanin mu,amma karka sanar da su mommy Dan gudun tashin hankalin su,tunda jannat ɗin tayi nadama,Ni dai nayi alƙawarin riƙe mata sirri ,kaima Please karka sanar da kowa"Islam ta faɗa tana kallon idonsa. Shima kallon ta yake cike da mamaki,dama tana da hankali haka?ta iya magana mai daɗi da bada shawara. "Shikenan na gode sosai da rufawa ƙanwa ta asiri da zakiyi,sannna in sha Allahu bazan sanar da su mommy ba,kawai abin ne yake damun zuciya ta,da baki zo kin gansu ba me zai faru?sannan tsawon wane lokaci suka ɗauka suna aikata wannan lalata?" "Allah shiga barwa kansa sani,kayi ƙoƙarin manta wa da komai shine yafi,Ni bari na tafi dama lambu zanje neman janbu"Islam ta fada tana mikewa tsaye tare da fara tafiyar ta cikin salo . "Na gode "Aslam ya faɗa ahankali yana bin bayan ta da kallo. Juyowa tayi tare da balla masa harara tace "kaga malam ba dan ka gode min nayi ba,ra'ayi na ne kawai ,ka riƙe godiyar ka kagane"ta fada tana murguda masa baki tare da ficewa. Kawai Aslam ya tsinci kansa da sakin murmushi,wato dai mai hali baya sauya wa,amma koba komai dai yau daya tayi abin ayaba mata,kuma yaji daɗi sosai.yana nan zaune ya fara duba wayar jannat,abubuwan da ya gani sosai suka tsorata shi,videos ne kala kala na sex da saurayin ke turo mata,sannan ga hotunan su Nan marasa kyan gani,chat ɗin su kuwa kasa karantawa yayi. Haka ya tashi jiki asanyaye ya nufi ɗakinsa da wayar,ya ajiye bayan ya goge komai dake ciki. Gaba ɗaya kwana biyu jannat ta sauya ta zama shiru-shiru yanzu ba rashin kunya ba surutu,kullum da hijabi da casbi ahannun ta,kuma Indai Mommy zata shiga kitchen tare suke shiga ,sosai takeyi yiwa kowa ladabi da biyayya agidan, mommy ba karamin daɗin hakan taji ba.tana kuma mamakin abinda ya kawowa ƴar Tata sauti lokaci ɗaya haka. Aslam aranar ya Sami daddy da batun jannat,cewar saurayin ta yayi masa magana akan iyayensa zasu turo,kuma ya tambayi jannat ɗin tace da amincewar ta,dan haka Gara kawai su aurar da ita,inyaso ta kammala karatun ta agidan mijinta.tunda level 2 zata shiga yanzu. Ba musu kuwa daddy ya amince,ba tare da yace wa Aslam komai ba game da nashi auran. Yau kwana ki ukun da daddy ya ɗibarwa Aslam suka cika,kuma yau iyayen saurayin jannat suka zo,an tsaida magana akan nan da wata biyu za'ayi bikin,bayan kowa ya watse har baƙin da suka taya daddy karbar iyayen saurayin jannat,daga Daddyn sai mommy da Aslam,Aman kam tun da ya fara taka ƙafar sa ,kullum suna tafe zuwa garden shida Islam,tana koya masa tafiya a cewar ta,amma ko yaya yayi kuskure yanzu za'a matse kafar ace za'a maidata gidan jiya.haka zaiyi ta bata haƙuri yana taka tsantsan,wani lokacin harda su jannat ake taya shi tafiyar. "To Aslam, Alhmdllh an gama batun neman auren jannat,nan da wata biyu za'ayi bikin,wanda kaine da kanka ka yanke haka,to dama na bari ka zabi lokacin ne da kanka,dan ahaɗa da naka.dan haka,saika yi mana bayani in yaso nan da gobe kaima sai muje neman naka auren ko" Daddy ya faɗa yana kafe aslam da ido. Shiru Aslam Yayi kansa a ƙasa,yana kasa magana dan baida abin cewa. "Kai nake sauraro kayi shiru"cewar daddy. "Am daddy adan ƙara hakuri dai a kammala bikin jannat ɗin in Sha Allahu kafin lokacin zan kawo matar da zan aura nima,ina nan ina bincike ne"aslma ya faɗa cikin sunkuyar da kai. "Yanzun ma baka samo ba kenan ko?to shikenan na baka damar daya kamata in baka,kayi wasa da ita,dan haka sai ka saurari nawa hukuncin da zan zartar nan da lokacin"daddy ya faɗa ba tare da nuna ɓacin ransa ba. "Na gode daddy"Aslam ya faɗa cikin murnar samun nasara,Dan atunaninsa daddy ya amince da batun sa ne.nan kuwa baisan me daddy ke shiryawa ba. Washe gari daddy yace yana neman kowa aɗakin sa, bayan sun gama zama shida granny, da mommy,kome suka tattauna oho. har da Islam, yace tazo dan zaman nata ne.aikuwa gaba ɗaya suka hallara afalon daddy, Kowa yayi shiru yana sauraron abinda daddy zai faɗa, Ahankali daddy ya bude taron da addu'a kafin ya fara magana..... Bari mu jira me daddy zai ce . Mrs babi ce Anty mammy. [9/27/2022, 4:15 PM] Abk: ____________Gaba ɗaya sunyi shiru,suna jiran abinda daddy zai faɗa. Ahankali daddy ya buɗe baki tare da yin addu'a,bayan sun shafa ne kuma ya fara magana kamar haka. "Alhamdullah nasan zakuyi mamakin abinda yasa na tara ku anan,to ba komai bane sai dan yau ina buƙatar sanin tarihin Islam,domin aiwatar da wani ƙudiri nawa akanta,dan haka Islam,muna bukatar jin abinda kika sani game da rayuwar ki"daddy ya faɗa yana kallon Islam. Ɗago kai Islam tayi tare da kallon daddy na wasu ƴan sakwanni, kafin ta sauƙe ajiyar zuciya tare da gyara zama ta fara magana. "Ni dai sunana khadeeja amma Islam ake kira na dashi,kamar yadda malami na ya sanar dani.na taso cikin gata da kulawa gurin iyayena,mahaifina babban ɗan kwangila ne sosai,ba abinda na nema na rasa arayuwata. Bazan iya cewa ga asalin garin mu ba,sai dai zan iya tuna abu guda game da rabuwata da iyayena. Lokacin inada shekara takwas a duniya. Wata rana da daddare muna kwance ,kawai sai muka far jin harbi ta ko ina,lokacin Ni kadai ce agurin iyayena sai kanina wanda ahalin yanzu na manta sunan sa. Tashi nayi ina kuka dan na tsorata sosai,ina zaune cikin dakina,saiga mama na,da babana sun shigo agigice,nan naji babana yana cewa mamana yan fashine suka shigo cikin gidan namu,kuma suna gab da ƙarasowa cikin bangaren da muke,dan haka maza-maza muzo mu gudu.haka babana ya sanya wata doguwar igiya ya fitar dani ta window mai nisa sosai,dan asama muke,ina ta kuka ina cewa suma su sauƙo mu tafi tare sai dai ,yana saukeni naji ihun mamana lokacin barayin sun ƙara so cikin dakin.kuka na ƙara sanya wa ina kiran sunan mama na da baba. Duk abinda suke faɗi ina iya jiyowa, dan da ƙarfi suke maganar,naji suna tambayar babana,ina takardun kwangilar da aka bashi,dana sauran kadarorinsa. Bansan ya akayi ba,kawai naji ihun mama na da baba na,kuma naji baba na Yana fadin"Islam ki gudu karki tsaya. Ina nan tsaye cikin tsoro da firgici,kawai naga wani daga cikin yan fashi ya leƙo ta windown yana faɗin akamoni ahaɗa Dani akona mu gaba ɗaya. Jin abinda ya faɗa yasa nayi saurin bin ƙofar baya na fice daga gidan ,ina gudu ina kuka.sosai na shiga cikin daji,wanda tsabar gudu kafata gaba ɗaya ta fashe sai jini ke zuba cikinta. Ban daina gudu ba saida ƙarfi na ya ƙare na faɗi atsakiyar jeji. Koda na farfaɗo na ganni kwance cikin wata bukka ansaka min magani cikin ƙafata. Tashi nayi na fara kuka ina kiran suna iyayena,awannan lokacin ne na fara haɗuwa da malamina, ina cikin kuka naji an daga kafaɗunta cikin rarrashi yake bani hakuri tare da faɗin zai kaini gurin iyayena idan na warke. Haka nayi ta zama cikin jejin nan,daga Ni sai malamina,wani lokacin ingan shi wani lokacin kuma ina rasashi. Ahaka muka shaƙu dashi sosai.sai dai tunda nake zaune dashi ban taba ganin wani mahaluƙi yazo gurin ba ,kullum mu biyu ne muke rayuwa. Ranar dana cika sati biyu agurinsa nace ya kaini gurin iyayena. Ba musu kuwa yace In rufe idona.cike da ƙuruciya na rufe idona ina murnar zanga ahalina,koda yace inbude idona,aikuwa gaban gidan mu na gannu tsaye.sai dai ga dukkan alamu gidan gobara yayi dan gaba ɗaya ya kone yayi baki.nan take na fara kuka ina tambayar ina iyayena suke.wani makocin mu ne yake sanar da malamina cewar ai barayi ne suka shiga gidan suka kunna wuta da iyalan gidan gaba ɗaya,sai dai ansmi tabbacin dama bana cikin gidan,kuma suma iyayena an duba ko ina ba alamar sun kone acikin gidan,anfi zargin wutar bata rutsa dasu ba suka gudu. Nidai iya sanina bansan wani dangi na mamata ba,sai dai lokaci lokaci muna zuwa wani gari inda yan uwan babana suke kuma Ni bansan ya sunan garin ba.dan haka koda aka bukaci kaini gurin yan uwan iyayena ,ba wanda yasan idan za'a nufa dani,dan haka wannan makocin namu yace zai rikeni. Da farko ina zaune lafiya agidan,sai daga baya na fara fuskantar baranaza kala-kala.duka,zagi aikace -aikacen gidan duk Ni keyi,gashi niba wata babba ba,amma haka ake tulamin aiki,cikin ƙanƙanin lokaci na rame nayi baki sosai,ga yunwa makaranta kuwa tuni na daina zuwa. Wata rana matar gidan ta kamani ta zaneni da daddare kuma ta kora ni waje. Ina kuka cikin tsoro na duƙunkune jikina,sai naji Muryar malami yana cewa"Islam kiyi haƙuri haka taki ƙaddarar take,daga yau kin bar zama agidan nan,tashi mutafi. Cikin farin ciki na mike nabi malamina ,muka koma can gidansa na daji,daga nan ya fara koya min karatu da yaruka iri-iri,bayan yan shekara guda ba irin Yaren da bana ji,nan yake kaini wata makaranta cikin ya'yan turawa,anan nayi firamare da sacondary .ya koya min duk wani abu na yan gayu,hakan yasa koda nazo gidan na ba abinda ban iya amfani dashi ba.shine ya koya min yadda zan kare kaina idan an zo cutar dani,abu guda ne bai sanar da Ni daba,inda iyayena suke,yace wannan ƙaddara ce zata haɗani dasu,bashi ne zai sanar dani ba. Lokacin da matasa suka farga dani cikin dajin ,sun sha kawo min hari da burin cutar da rayuwa ta,amma Allah bai basu nasara akaina na,duk lokacin da wani yayi nufin cutar dani,malamina yana zuwa ya kawo min ɗauki.sannan shine ya ƙarfafamin gwuiwar zama cikin gidan nan,yace anan cikon ƙaddarata yake. Wannan shine iya abin da zan iya fada muku game da rayuwa ta cikin dawa na girma ,nan ne gida na birrai datsuntssye sune suka zamo dangina bani da kowa sai malamina.bansan inda iyayena suke ba,kullum ina addu'ar Allah ya haɗani dasu"ta kai karshen zancen ta tana mai share hawayen dake zuba cikin idonta. Shiru falon yayi kowa yana tausayin Islam da iri. Gwagwarmayar da tasha,lallai dole ayiwa Islam uzuri game da rayuwar ta. Granny ne ce ta fashe da kuka tana mai kamo Islam zuwa jikinta. "Allah sarki Islam, kinga rayuwa Allah ya bayyana iyayenki,ya saka muku abinda waɗan nan mugayen sukayi muku,amma da alama malamin nan naki ba mutum bane,wani bawan Allah ne cikin aljanu yake taimaka miki Allah yasa ma Ni dai ina ƙaunar ki,dan kar watarana ya maidani kunkuru" cewar grannay tana dafe ƙirji da yarfe hannu.saida ta sanya kowa yayi murmushi agurin,wai karya maidata kunkuru. "Haƙiƙi Islam rayuwar ki abar tausayi ce,amma in sha Allahu komai yazo ƙarshe,zamu kula dake cikin aminci,sannan zamu ci gaba da addu'ar Allah ya bayyana iyayenki,sannan zamuyi ta cigiyarsu har Allah ya bayyana mana su.ki ɗauke mu ahalin yanzu mune ahalinki,kuma yan uwanki, domin kin zamo daya daga cikin mu. Bayan haka kuma,nasan zaki so sanin namu tarihin dan haka zan sanar dake asalinmu,sannan zan nemi alfarma guda daya agareki,ina fatan zan samu?cewar Daddy Yana kallon Islam. "Ina sha Allah daddy nayi maka alƙawarin zan yi maka duk abinda ka nema agurina in har ina dashi,zan baka"inji Islam cikin sanyin murya. Ajiyar zuciya daddy Yayi kafin yace "alhmdllh Nagode ƴata.da farko dai kamar yadda kika gani yara na hudu Aslam,Aman ,jannat sai auta hanan,Ni dan asalin garin gumel ne dake cikin jahar Jigawa,zama da kasuwanci ya kawo Ni Abuja,matata daya Hajiya sadiya,ga mahaifiyata Hajiya Khadijah,mu biyu ta haifa ,amma ahalin yanzu saura Ni kadai,mahaifina ya rasu tun kafin ahaifi Aslam,sannan Hajiya sadiya yar Kano ce ,ta kasance ya ga aminin mahaifina,yan uwanta gaba ɗaya suna can kano.wannan shine taƙaitaccen tarihin ahalina. Sai kuma taimakon da nake son kiyi min-yay shiru yana kallon yanayin Islam,wacce ta maida hankalin ta gaba ɗaya kan daddy. Kafin yaci gaba. Ina son ki taimaka ki auri ɗana Aslam,nan da watan biyu masu kamawa" Ɗif!!kake ji duk wani motsi dake cikin dakin ya dauke,sakamakon daina bugawar numfashin su na wasu yan dakikai. Gurum Aslam yayi yana kallon daddy,so yake ya kara tabbatar da abin da kunnensa yaji masa,kai sharrin iska ne ma ,ta dauko masa wata shirmen magana zuwa kunnen sa,hakan ba mai taba yiwuwa bane har abada.dan haka sai yayi ɗan murmushi tare da dafe ƙirjinsa dake wata irin bugawa kamar zai fashe.cikin zuciyarsa yace "kai zuciya ma bata da ƙashi,ko menene ya kawo min wannan shirmen mai kama da wasan yara?" Aman kuwa baki buɗe cikin bugawar ƙirji yake kallon daddy da mommy tare da granny,ko kaɗan ba wata alamar damuwa ko mamaki akan fuskar su,alamu dai sun nuna cewar sun san da maganar, shike nan,ya rasa Islam,yayi dakon soyayyar ta abazan, innalillahi yanzu yaya Aslam ne zai auri Islam ba Ni ba?ya Allah ka cire min soyayyar ta daga zuciyata"Aman ya faɗa cikin zuciyar sa ,yana jin idon sa na kawo kwalla,da sauri ya sanya bayan hannunsa cikin dubara ya goge ba tare da kowa ya gani ba. Jannat kuwa da hanann,kallon juna sukayi cike da mamakin daddy,ta yaya zai hada aure tsakanin ya Aslam da Islam,bayan kowa yasan rashin jituwar dake tsakanin su,impact ma sam Islam ba ajin sa bace,ya Aslam da yan mata ke rububi akan sa,shine za'a haɗashi da wacce tayi rayuwa cikin jeji tare da dabbobi?tan,lallai akwai drama. Islam kuwa shiru tayi tana kallon daddy,zuciyar ta cike da wani tunani,ita dai bata shiryawa aure yanzu ba,kuma tana jin nauyin ƙin amsar maganar da daddy yazo mata da ita,amma dole zata bashi hakuri,badan komai ba,sai dan bazata iya zama da Aslam matsayin miji ba,tab me ma zatayi da wannan baƙin mai kama da buhun hatsi,dama dai ace Aman ne to koba komai zata amince saboda shi yana da kyakykyawar zuciya,amma wannna !ƙila ma yabi dare ya danne mata hanci da filo ta mutu. "Karki damu Islam,bazan takura miki cewar saikin bani amsa yanzu ba,zan baki cikakkiyar dama kiyi nazari akan magana ta ,sannan ina so kiyi min kyakykyawar fahimta,banyi hakan da nufin cutar dake ko wani abu ba,nayi hakan ne bayan dogon nazari da tunani,sannan saida na shawarci mommyn ku da Hajiya ta,dan haka ki kwantar da hankalin ki,duk amsar da kika bani bazata ɓata min rai ba. Kai kuma aslam,wannan umarni ne, agareka,muddin Islam ta amince da batun auren nan,to baka da wata mata sama da ita,wannan shine hukuncin dana yanke,zaku iya tafiya dukan ku"daddy ya faɗa yana jingina da jikin kujera. Kallonsa kawai Aslam keyi,wai shin da gaske ne abinda kunnen sa suka jiye masa?aure daddy ke son hada shi da wannan yarinyar yar jeji?waya sani ma ko karya take labarin data faɗa musu, yawon duniyar ta kawai ta fito,lallai kuwa akwai tashin hankali mai girma cikin gidan nan,kuma wllh shidai bazai amince da wannan haɗin gambizar ba,haba yana za'a ce kamar shi Aslam Mahmud kabir,ya rasa wacce zai aura sai wannan kidahumar? impossible " "Ko kana da magana ne Asalamu naga ka kasa tashi,bayan kowa ya watse?ko ja'ircin zaka mana,ai wllh ka godewa Allah ma,daya baka wannan zankadediyar yarinya son kowa ƙin wanda bai samu ba,yo iya binciken ka ai baka isa ka samo ya ita ba,ai wllh naso ace Amanu ne ya samu yar nan,yaro mai nutsuwa da hankali"cewar granny tana ballawa Aslam harara tare da turo dan kwali. Shidai Aslam kallon ta kawai yake ,ba tare da ya fahimci me take faɗi na,dan zuwa wannan lokacin hankali da tunanin sa sam basa jikinsa. Kallon sa ya maida kan mommyn sa,kallo yake mata na neman karin bayani,amma saita yi saurin kawar da kanta gefe guda. Dan haka ya kara tabbatar da abin da kunnen sa yajiye masa gaskiya ne,lallai dole ya samo mafita tun wuri kafin lokaci ya kure masa.tashi yayi cikin zafin nama kamar zai tashi sama ,haka yake tafiya ya bar ɗakin na daddy.kallo daddy yabi sa dashi kafin ya girgiza kai,yana faɗin yaro gata nayi maka,bazaka gane hakan ba sai nan gaba. Ba kowa afalon lokacin da ya fito,tsayawa yayi yana tunanin inda zai gano Islam,sai huci yake kamar zaki,dai-dai lokacin ita kuma ta fito daga kitchen dauke da robar ruwa mai sanyi. Batayi aune ba kawai taji an fizgota tare da yin waje da ita. Janta kawai Aslam keyi da mugun sauri,ita kuwa binsa take har da ɗan gudu,dan yafita saurin sosai. Bai zame da ita ko ina ba sai garden.yana zuwa ya hankaɗota zuwa gabansa,saura kaɗan ta fadi kasa tayi saurin dafe bishiyar dake bayan ta. Ɗago kai tayi tana kallon sa cikin haɗe rai da jin haushin abinda yayi mata. Aslam kuwa saida ya ƙare mata kallo cikin ƙasƙanci kafin ya jinjina kai tare da nuna ta da hannu kamar kashi. "Ba doguwar magana zanyi dake ba,kawai zan gargadeki ne,sannna in baki umarni,akan kada ki sake ki amince da wannan auren tatsuniyar,domin Ni Aslam ba sa'an auren ki bane,how comes ma?za'a haɗani aure da ke,ke wacece?me kike dashi?me zan aura ajikin ki?jaka kidahuma wawiya marar aji irin ki,Ni Aslam ace zan aura?wllh ko mata sun ƙare nafi ƙarfin ki,so kema nasan kinsan da hakan,dan haka ki hanzarta dakatar dasu,da wannan shirmen da suke son haɗawa Aslam is not your type"Yana gama faɗin. Haka ya tofa mata yawu tare da barin gurin. Wani irin hucin bakin ciki Islam keyi,zuciyar ta kamar zata fashe,tsabar takaici da haushi kawai ta kama dukan bishiyar dake gefen ta tana kuka, "zakaga irin hukuncin da zan ɗauka akan ka,nima bana sonka me zanyi da kai mugu kawai ƙaton banza,wllh saikayi dana sanin fadamin wannan baƙaƙen maganganun,zaka gani"ta faɗa da ƙarfi tare da nufar cikin gidan kamar zata tashi sama,kai tsaye part ɗin daddy ta nufa... Mezatayi a part din daddy,karfa tace bata son Aslam? Hmmmm muje zuwa masoya. Mrs babi ce Anty mammy. [9/28/2022, 9:28 PM] Abk: ___________"Wllh sai kayi dana sanin faɗa min wannan baƙaƙen maganganun,zaka gani sainayi maganin ka,zaka gane Islam bata ɗaukar raini"tana gama faɗin haka cikin kuka da ɗaga murya ta nufi cikin gida cike da ɓacin rai. Kai tsaye ta nufi part ɗin Daddy. Nocking tayi tare da sallama,daga mommyn har granny suna ɗakin,dan suna tattaunawa ne akan maganar auren tare da daddy. "Shigo mana Islam,fatan dai ba wata damuwa?"cewar daddy bayan yaji muryar Islam. Ahankali ta tako zuwa cikin ɗakin,guri ta samu tare da zama tace "ba wata matsala daddy,har na yanke shawara ne,naga ba bukatar daukar dogon lokaci shine nazo sanar daku"tayi shiru tana sauke ajiyar zuciya. Dukkan su fata suka rinkayi, Allah yasa ta amince da batun auren,karta ce bata yar da ba. "Yi magana ƴar, nan muna sauraron ki,wllh har na fara jin cikina yana ƙara ƙulululu karki ƙi amincewa"cewar granny tana dafe cikin ta da zubawa Islam ido. "A'a granny nazo ne in sanar daku cewar na aminci,zan auri Aslam,domin kuwa dama ya sanar dani cewar yana son aure na,nice dai ban bashi haɗin kai ba,saboda alokacin naga kamar shekaruna sunyi ƙanƙanta da yin aure,amma ahalin yanzu na amince dan nima ina sonshi mun dai dai ta kan mu,shine ma ya aiko Ni yanzu in sanar daku,wai shi yana jin nauyi"Islam ta faɗa har da sunkuyar da kai ƙasa" "Alhamdullah wannna abu yayi min daɗi sosai,Hajiya ! Kiji fa dan Allah,dama yaron nan yasan yana son Islam ɗin maimakon ya nasar damu tun wuri shine ya tsaya kunbiya-kunbiya.ko meye na jin nauyin? Na gode Islam Allah yayi miki albarka da wannan alfarmar da kikayi mana Nagode sosai"cewar daddy cikin farin ciki. Mommy ma abin yayi mata daɗi sai murmushi take tana godiya ga Allah cikin ranta. Granny kuwa guda ta sanya tare da faɗin"kai wannna al'amari yayi daɗi,to ko shiyasa dazun Asalamu ya tsaya ya kasa fita? so yake ya sanar damu suna son juna shida Islama! Ja'irin yaro ashe yana jin kunya, sannu Islam Allah ya yi miki albarka mun gode sosai wllh " Murmushi yaƙe Islam tayi kafin ta mike tare da barin dakin.tana fita kai tsaye ta wuce garden,Kan bishiya ta haye tare da sanya kuka.Allah ya gani wllh bata son Aslam,tayi haka ne kawai,dan ta ƙunsa masa baƙin ciki,ta nuna masa bai isa yace batakai matsayin da zai aureta ba,kuma zatayi amfani da wannan damar ta gasa masa aya ahannun sa.zatayi duk mai yiwuwa Dan ganin anyi auren. Nan Tana nan zaune kan bishiyar tana zubda hawaye,taji andafa kafaɗun ta ,da sauri ta ɗaga kai sukayi arba da malamin ta,cike da kewa da ɗokin ganin sa ta riƙe hannunsa tana ƙara ƙarfin kukan ta. Murmushi yayi tare da shafa kan Islam,yana girgiza mata kai."ki daina kuka Islam,wannan itace ƙaddarar ki,zaki zama tauraruwa cikin gidan nan,zaki taimaka musu ta hanyoyi da ban -daban kuma kinyi dai-dai da kika amince da batun auren,karki ɗauki ƙiyayyar dake tsakanin ku abakin komai,wata rana zata gushe,farin ciki zai mamaye zuciyar ku,daga yau karki ƙara kuka,kizama jaruma kamar yadda na sanki, kina da aiki gagrumi nan gaba "yana kaiwa nan azancen sa,ya share mata hawaye tare da yin addu'a cikin tafin hannun sa ya shafa mata agoshinta. Sannan yayi mata murmushi ya bace bat!.ajiyar zuciya Islam ta sauke,lokaci guda ta nemi damuwar ta ta rasa,dan haka sauƙowa tayi daga kan bishiyar ta nufi bakin swimming pool ta zauna tare da zura ƙafafun ta ciki. Aslam kuwa yana can cikin dakin sa,baƙin ciki kamar ya kashe shi,duk da yasan cewar baza ta amince da batun auren ba,amma shi haɗata ma da akayi da shi,abin ba ƙaramin ƙona masa rai yayi ba,shi Gara ma kawai yayi auren kowa ya huta,dan haka zai nemi yarinya yar mutunci kawai ya aura. Kwanciya yayi akan gadon sa yana mai tunanin ta ina zai fara neman auren?wa ya kamata ya aura,wayar sa ce tayi ƙara alamun ana kiran sa,dan haka dauka yayi tare da kangawa akunnen sa. "Hello daddy,ok gani nan zuwa"ya faɗa yana mikewa tsaye,murmushi yayi tare da faɗin,harta sanar dasu kenan,hmmmm yarinya da kin yabawa aya zaƙin ta wllh"da sallamar sa ya shiga falon na daddy ya zauna. "Daddy gani"ya fada kansa asunkuye. "Yawwa Aslam,munji saƙon ka daga bakin Islam,amma meye na ƙin sanar damu gaskiyar abinda ke cikin ranka sai kace muba iyayen ka bane?ai babu hijabi tsakanin mu da kai" "Ayi hakuri daddy,Ina gudun ɓacin ran kune shiyasa ban faɗa ba,amma tunda Ita ta faɗa shikenan Allah ya zaɓa mana abinda yafi alkairi"Aslam ya fada cikin sanyin murya kansa a ƙasa ,farin ciki fal zuciyar sa. "Ba komai Allah yayi maka albarka ya shirya ku,yanzu Abinda nake so dakai shine,ka ɗauki Islam kuje store dan ta zabi kayan da take buƙatar yin amfani dasu,tun dadewa nake son yin hakan,amma azuri yayi min yawa,to kaga yanzu aiki ya koma kan ka,sannan akwai buƙatar asanya ta amakaran ta ,duk da dai cewar tayi karatu,amma ya kamata ta koma,idan da hali sai ahaɗasu da hanan su kammala tare"daddy ya kai ƙarshen maganar sa yana kallon Aslam. "To daddy za'ayi kamar yadda kace Allah ya ƙara girma"Aslam ya fada cikin farin ciki da tunanin komai yazo ƙarshe cikin sauƙi. "Ohh!! Kinibabben yaro ana so ana kaiwa kasuwa ai wllh ka gode Allah ma dan samun wannna damar sai ɗan baiwa"cewar granny tana hararar Aslam. Banza yayi da ita yana mai ficewa,shidai koma me za'ace bashi da matsala tunda an yakice masa auren wannan kucakar . Washe gari da safe gaba ɗaya sun hadu wajen cin abinci,daddy ne kawai baya gurin dan yayi asubancin barin ƙasar ,kowa da abinda yake ci,Aslam yana zaune cikin shiga ta ƙananan kaya,sunyi matukar karbar jikinsa,fuskar sa kamar kullum aɗaure baya dariya. Yayin da mutuniyar ke kusa da Aman, Wanda damuwa da alhinin rabuwa da Islam suka hana masa cin abincin sai juya cokali yake, Granny kuwa an zage ana ba naman kaza hakkin sa, Mommy dai tea kawai take kurba. Jannat na gefe sanye da hijabinta tana cin jallof ɗin taliya data sha kayan lambu da naman ƙaramar dabba,sai hanan dake shan romo. Ahankali Islam ta ɗago kanta tare da kallon Aslam,Wanda ya zage Yana cin kwai da dankalin turawa. Harara ta banka masa kafin ta ɗan yi murmushi tace "kai Aslam,ka wani zage sai cin dankali kake,Please ka ɗanci taliyar nan mana,kasan bana son yunwa ta kama ka,Gara kana ɗan ci abu mai nauyi,duk da ma taliyar ba nauyi gareta ba"ta faɗa cikin maƙale murya tana murmushi. Cikin mamaki Aslam ke kallon ta,wato wani sabon barikin ne wanna ta tsiro dashi,salon yayi mata wani abu ace shine marar gaskiya,hmmm yarinya Indai bariki ne kin tarar dashi,nidai tunda ba batun auren nan ai nafi kowa farin ciki,dan haka cikin ɗan murmushin da bai kai zuciya ba yace "A'a Islam banaso na cika cikina sosai,wannan ɗin ma ya ishe Ni,ke dai kiyi hanzari ki kammala,dan zamuje ki zabo kayan da kike ɓukata,sannan ranar monday zaki fara zuwa school"ya kai zancen sa yana murmushin yaƙe wanda yafi kuka ciwo. Ba haka Islam taso ba,so tayi ta bata masa rai yayi kurarin sa ta yadda idan anyi auren ma zatayi ta ɗora masa sharrin da zaiyi ta shiga matsala,amma duk da hakan ma zai zo hannu.kuma tana mamakin ta yadda akayi bai nuna damuwar sa ba ahalin yanzu kamar yadda yayi da farko. Cikin ɗoki tace "kai amma ka burgeni,yau zan ga gari akaro na farko,Please idan mun fita ka biya dani guraren masu kyau, musha lemo tare irin yadda masoya keyi,bari naje na shirya"Islam ta fada tare da kashe masa ido ɗaya kafin ta nufi dakin hanan. Binta yayi da kallo,yama kasa gane kan bayanin nata,wai susha lemo tare,irin na masoya,banza wawiya,can dai ƙyaje ki samo masoyin ki ba Aslam ba. "Kai wllh Asalamu kayi sa'a,domin samun wannan yarinyar alkhairi ne agare ka,ji yadda take nuna maka soyayya gaban kowa,inaga anyi auren?wllh harna matsu ayi bikin nan,wai ranar nan za'aga yadda ake ado da taka rawar sabada"cewar granny tana wani juya kafada. Dariya su jannat suka sanya,hanan tace "granny kiyi dai ahankali kar garin rawa kije ki karya kafaɗa"ta ƙara sa da dariya ƙasa-ƙasa. "To muguwa mai baƙin hali,fatan ki ya sari ɗanyen kashi,ai lokacin ina budurwa,kaf garinmu ba wacce ta kaini iya rawar kalangu ta gani -kani gwalelen ka"granny ta faɗa tana ɗan karya baya.dariya sosai suka sanya sakamakon yadda granny tayi rawar,hatta mommy saida ta dara , Aman yace "woo matar gaskiya kinyi zamani kice haka kuke karya ƙugu alokacin yan matanci?"ya fada cikin dariya da ƙoƙarin kawar da damuwar dake cikin ransa. "Sosai ma ai ina ,zuwa gurin mai kalangu zakaji an ɗauki ihu da sowa,ana gwanar rawa tazo hatta kidan kalangun sauya wa yake"ta faɗa cike da alfahari tana dariya. Shidai Aslam kallon su yake yana kuma son fahimtar inda zancen su ya dosa,kamar fa granny na son cewa har yanzu shine wanda zai auri Islam,kuma yadda yaga Islam na masa wasu abubuwa kamar har yanzu zancen yana nan. Kallon mommy Yayi cike da son ƙarin bayani yace "mommy wai me granny ke son faɗa min ne?nifa ban gane ba?"ya fada cikin yanayi na damuwa. Kallonsa mommy tayi tare da ɗaure fuska tace "kamar ya baka gane ba?bayan kaine ka aiko Islam ta sanar damu alaƙar dake tsakanin ku da ita,kuma ta bayyana mana amincewar ta da taka akan auren,kuma dama Daddyn ku ya sanar dakai tare za'a hada bikin ka dana jannat,shine dalilin fitar dazakuyi yanzu,dan ta zabo kayan da take buƙatar amfani dashi kafin ahaɗa mata lefe. "What !!!mommy me kike son faɗa min?yaushe mukayi wannan maganar da yarinyar nan?mommy ta yaya zan so wannan yarinyar?dama ba magana kuke min akan fasa haɗin auren ba?kenan ba zuwa tayi ta sanar daku bata sona ba?"Aslam ya fada cikin tashin hankali da tarin damuwa. "Kai aslam karka maidamu wasu shashashai mana ! Wllh tun wuri karma ka kawo wani zancen banza,domin ranka zai mugun ɓaci agurin Daddyn ku kaji na faɗa maka"mommy ta faɗa cikin faɗa tana nuna Aslam. Runtse ido Aslam Yayi da mugun ƙarfi,kenan wannan shine dalilin da yasa Islam ke masa wannan karuwanci?lallai yarinyar nan ta jawa kanta bala'i wllh sai tayi dana sanin yarda da wannan auren da tayi,haba wllh angama cutar sa, Indai aka aura masa Islam. Dai-dai lokacin kuma Islam ta fito sanye da doguwar rigar hanan,ta atamfa,tayi matukar yi mata kyau sosai ,rigar a shape ce mai dogon hannu,sai stones da akabi rigar dashi gaba ɗaya,bata sanya mayafi ba ,kawai ɗan kwalin kayan ta ɗora akanta ba tare da ta ɗaura ba. "Na shirya,ya kaga kayan fatan dai sunyi mini kyau?"Islam ta fada tana ɗan juyawa kamar mai tallar kaya. Wani malolon baƙin ciki ne ya turnuƙe Aslam ,cikin masifa da ɓaci rai yayi kan Islam, "Uban waye yace kije ki sanar dasu mommy nace ina sonki?yaushe mukayi haka dake Ni Aslam nace ina sonki?me zanyi dake ke wacece da zan yarda in haɗa soyayya dake ?meyasa kikayi min haka ?meyasa?"Aslam ya fada cikin ƙara ji da masifa. Murmushi Islam tayi cikin barikan ci tace "saboda ina sonka ina ƙaunar ka,kaine rayuwata bazan taɓa iya rayuwa ba kai ba,dan Allah mommy ki bashi hakuri wllh nidai na amince ina sonshi,yana fushi ne dan abaya na nuna rashin amincewa ta"Islaman ta fada cikin marairaitar murya tana kamo hannun mommy. Muje zuwa masu karatu . Mrs babi ce Anty mammy.[9/28/2022, 10:36 PM] Abk: ___________"Dan Allah mommy ki bawa Aslam haƙuri,karya ce baya sona,dan bazan iya rayuwa bashi ba,shi nake so na aura mommy"Islam ta faɗa cikin marairaice murya tana rike hannun mommy. Galala Aslam Yayi Yana kallon karuwanci irin an Islam,lallai yarinyar nan,saboda yace bazai aureta ba ,shine taje ta haɗa masa ƙaryar cewa shine ya aikota ta sanar dasu mommy amincewar su akan auren?wai ma to menene nufin ta na amince wa da wannan haɗin?me take nufi da yin hakan?kodai turo ta akayi ta shiga cikin rayuwar sa ne ?yana cikin wannan tunanin ya tsinkayo Muryar mommy tana faɗin"ki kwantar da hankalin ki Islam,badai kin amince da auren ba?kuma ki na son Aslam? Gyada kai Islam tayi kamar ƙadangaruwa. Cigaba mommy tayi da cewa-ki kwantar da hankali ki baki da wani mijin daya wuce Aslam,inhar mune muka haifeshi, kamar anyi auren nan angama" Mommy ta faɗa tana mai shafa kan Islam. "Nagode mommy idan har kuka aura min Aslam kungama min komai arayuwa"Islam ta faɗa tana ɗora kanta akafaɗar mommy,ɗago idonta tayi tare da kallon Islam,aikuwa carab suka haɗa ido,kashe masa ido ɗaya tayi tare da dage gira ɗaya tana murmushin kazo hannu. Kamar Aslam zai ƙwalla ihu yace "mommy Kinga abinda take min ko?wllh wannan amincewar ba har zuciya tayi ba,akwai manufar ta tayin hakan,mommy please ki saurare ni wllh bana son yarinyar nan har cikin zuciya ta,kuma itama ba sona take ba kawai tana son baƙanta min ne"ya ƙarasa kamar zaiyi kuka yana riƙe hannun mommy. Kuka mai ƙarfi Islam ta sanya tana faɗin "wllh ina sonka mommy wllh ina sonshi,shine rayuwata mommy kitaimaka min granny kiyi wani abu karna rasa rayuwata"Islam ta fada tana komawa jikin granny. Kuka granny ma ta sanya harda rinji tana mai riƙe Islam ajikinta sosai"Allah sarki ƴata kiyi haƙuri Indai ina raye saikin auri Aslam,Indai ni ce na haifi ubansa,wllh saiya aureki,shashashan banza,to idan har ka samu ma ka auri wannan yarinyar ai wllh kayi sa'a arayuwar ka,dubeta fa son kowa ƙin wanda ya rasa,kaima borin banza kake yi, dan kasamu za'a haɗaka da ita banza mai kama da ƴan dambe"granny ta fada cikin masifa kamar zatayi dambe da Aslam, Runtse ido Aslam Yayi,ganin gaba ɗaya sun kasa fahimtar sa,dan kuwa cikin fushi mommy tayi ɗakinta. Da sauri Aslam ya rufa mata baya yana kiran sunan ta. Islam na ganin haka ta yi wani kayataccen murmushi,shikenan burin ta ya cika,koba komai yanzu Aslam ya shiga cikin matsala sosai. Hannu ta sanya ta sharewa granny hawayen idonta kafin ta ce"granny ki daina kuka,ba dai kin yarda da soyayyar da nakewa jikan ki ba?to insha Allah saina aureshi ya zama mijina,karki wani damu kanki"cewar Islam ta na sharewa granny hawaye. "Wllh na yarda ƴata,kuma idan ya ce zai kawo wani shirme wllh sai in zage mu daku da shi in kakkarya masa ƙasusuwa in watsar da banza,inyaso daga baya a gyara shi"granny ta faɗa tana gwada yadda zata karya masa ƙashi. "Wayyo granny idan kika karya shi kuma wazan aura "ta faɗa cikin shagwaba. "Kuma haka ne,wllh zan ɗaga masa ƙafa ne kawai saboda ke yaron banza kawai"granny ta faɗa tana hararar hanyar dakin mommy. "Lallai ma granny ya Aslam ɗin zaki kakkarya har ki watsar? Idan ke baki karya shina shiya karya miki tsofaffin ƙasusuwa ki ya watsar" cewar hanan tana turo baki. "Saidai ya karya na uwarki,kinji ko?ja'ira mai maka da takanɗa wllh ki bar ganin ina tausaya miki,duk randa na juyo kanki Allah ne kawai zai ƙwaceki"cewar granny tana hararar hanan. "Yanzu dai granny ki gyale wannan shashahar ,kije ki kwanta ki huta,idan mun fita zan siyo miki tsaraba"cewar Islam cikin murmushi. "Yawwa ɗiyata ki siyomin iyisikirim mai sanyin tsiya "granny ta faɗa tana nufar ɗakinta bayan ta ballawa jannat da hanan harara. Murmushi Islam tayi tana zama akan kujera tare da ɗora kafa ɗaya kan ɗaya,kallon hanan tayi kafin tace "Ki shiga taitayi ki hanan,manyan kima sunyi sun barni bare ke ƙaramar alhaki" Shiru hanan tayi bata ce komai ba sai turo baki da tayi. Aman ne ya matso kusan da ita ya zauna shima jiki ba kwari,yace "islam me yasa kikayi wa yaya haka? Me yasa kikayi haka? Bakya tunanin akwai masoyan ki da dama dake jiran ki?Please ki janye wannan maganar Islam"Aman ya fada kamar zaiyi kuka " Murmushi kawai Islam keyi tana kallon sa, saida ya kammala maganar sa kafin tace "nayi haka ne dan In nuna masa Islam tafi ƙarfin wulaƙancin sa,cewa yayi fa bazai aureni ba,harshi waye dazai ce baya sona ko yayi tunanin nima ina son shi ne? Zan aure shine kawai dan na koya masa hankali yasan Islam rainon dawa ce bata ɗaukar raini"ta faɗa tana wani girgiza ƙafa kamar boss. Dafe kai Aman Yayi cikin damuwa yabar falon,hanan ma da jannat jiki sabule suka bar falon.ya rage saura Islam kadai . Aslam kuwa bin mommy Yayi cikin ɗakin ta Yana kiran sunanta "Please mommy ki saurareni wllh yarinyar nan ba da gaske take ba,tana da wani ƙudiri ne akaina shiyasa,amma ba wani sona da take,mommy Dan Allah ki saurare ni"ya fada dai-dai lokacin sun iso dakin na mommy. Cikin fada da daga murya mommy ta daka masa tsawa, "Kai Aslam wllh ka kiyayeni!dan bana son shirmen banza,me kake son mai damu ne?ƙananan mutane ko me?to wllh tun wuri kama bar wannan maganar,tun kafin Daddyn ku yaji"ta kai karshen maganar cikin faɗa. Shiru Aslam Yayi ganin yadda ran mommy ya ɓaci sosai,dan haka ya tausasa muryar sa yace "kiyi hakuri mommy,ba nufina in bata muku rai ba,kawai bana son ayi abinda zai zo ya zame mana matsala ne nan gaba,ko kuma ranku yazo yana ɓaci shiyasa,amma dan Allah kiyi hakuri"Aslam ya fada cikin ladabi. "Ai yanzu ne kake son ran namu ya ɓaci Aslam,Dan me zaka rinka mai damu kamar wasu sa'anninka,ayi magana kuma daga baya kace ba haka ba" "Mommy kiyi haƙuri please,kada ranki ya baci,yanzu ki faɗa min abinda kike son nayi"ya fada cikin ladabi da son kwantar mata da hankali. "Kaje ka ɗauki Islam,ka kaita store ta zabo duk abinda ranta ke so,kuma bana son wannan halin da kake nuna mata,bana son takura Dan wllh inhar kace zaka ci gaba da ɓata ran yarinyar nan to zamu saba da kai" "Kiyi hakuri mommy In Sha Allah zan kiyaye"Aslam ya fada cikin sanyin murya, tare da barin ɗakin, zuciyar sa kamar ana kunna masa wuta haka yake ji. Afalo ya tarar da oganninyar ta ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya.kallon tsana yake mata,yana jin kamar yaje ya shaƙeta ta mutu kowa ya huta. Islam kuwa tana ganin sa ta tashi cikin takun ta mai ɗaukar hankali ta nufi inda yake tsaye yana watsa mata wani mummunan kallo. "Masoyi! Ka fito kenan ?zamu iya tafiya?"ta faɗa cikin wani salo tana kashe masa ido. Ji Aslam Yayi kamar ta soka masa nashi cikin zuciyar sa,afusace yace"kije can dai ki nemi masoyin ki,dan Ni har abada bazan taɓa sonki ba, wllh dana soki Gara In dawwama bani da zuciya aƙirjina ,bare harta darsa min sonki,dan wlllh na Tsaneki bana ƙaunar ganin ki"ya faɗa cikin huci kamar wani zaki. Wani shu'umin murmushi Islam tayi tana kaɗa jikinta , kafin ta kalli Aslam sama da ƙasa tace "wayaga bijimi, wllh Ni yanzu dariya ma kake bani,saboda idan kayi wani abun kamar taɓaɓɓe haka kake,kuma da kake iƙirarin baka sona,Ni waya faɗa maka ina sonka?ƙila ma yadda nake jin tsanar ka cikin raina, kai baka jin koda rabin ta akaina.kuma ka sani zanyi amfani da wannan damar ne dan In ƙuntata maka in zame maka ƙarfen ƙafa,sannan ka gane cewar Islam ba kanwar kasa bace, na wuce ajin tsageranci irin naka"Islam ta fada cikin nutsatstsiyar murya tana murmushi,ta yadda bawanda zai gane maganganu masu zafi take fadawa Aslam. Shiru Aslam Yayi,yana sauraron ta.dan sai yanzu ya gane cewar, tana zurmashi yayi ta nuna ɓaci rai gaban kowa, yayin da ita kuma take ƙuntata masa cikin ruwan sanyi,daga yau shima zai sauya kalar nashi salon zai nuna mata shima ɗan barikine. Dan haka matsowa yayi sosai daf da ita tare da rangwafowa saitin fuskarta,har suna iya jiyo saukar numfashin juna akan fuskokin su. "Na gode da nuna min hanya da kikayi,daga yau zan nuna miki nima cikakken ɗan tasha ne kuma taɓaɓɓe,sannan good player,zamu fara wasan ne daga yau,zamu gani nidake waye zaiyi nasara,matar Aslam Mahmud kabeer"ya kai ƙarshen maganar sa yana mai shafa gefen fuskar ta cikin salon sa da yake narkar da zuciyar yan mata. Wani yarrrrr Islam taji tun daga tafin ƙafarta har zuwa babban ɗan yatsan ta, da sauri ta ja baya tana Banka masa harara gabanta na bugawa da sauri-da sauri. Murmushi Aslam yayi tare da kamo hannunta cikin nashi ya ce"muje amaryar Aslam ko?"ya fada yana wani matsa mata hannu cikin salon mai tada hankali tare da kashe mata ido.... Manage please wayata ba caji ne. Mrs babi ce Anty mammy. [9/30/2022, 12:05 PM] Abk: _____________Murmushi Aslam yayi,tare da kamo hannunta cikin nashi yace "muje ko amarya Aslam"ya fada yana wani matsa mata hannu cikin salon sa mai tada hankali tare da kashe mata ido. Sosai Islam ta runtse idanunta,sakamakon yadda yake matsa hannun nata,cikin salo mai wuyar fassara wa,wani irin yanayi take ji ajikinta,dan haka da sauri ta fizge hannun ta,tare da balla masa harara tace "malam karka ƙara taɓani bana son iskanci"ta fada cikin ɗaure fuska tana nufar ƙofar fita daga falon. Murmushin mugunta yayi tare da bin bayanta yana mai faɗin"da gaske bakya son iskanci?lallai aiki ya ganki dan kuwa niɗin cikakken dan iskane,kuma zakiga salo-salo na iskanci iri-iri,dama ai saboda kina son iskancin kika ce saikin aureni,kuma Indai iskanci ne kinsamu yarinya"ya fada dai-dai lokacin sun kawo wajen motar sa,mai shegen kyau da tsada. Tsaki Islam tayi tare da tsayawa jikin motar ta na masa kallon sama da ƙasa"ai dama ba sai ka faɗa ba,nasan kai ɗin riƙaƙƙen dan iska ne,sai dai wallahi ka sani,zan aure ka ne badan wannann tunanin ba,dan kuwa koda wasa kace zaka taɓani,wllh zakaga yadda ake bala'i"ta faɗa cikin tsiwa tana murguda baki. Murmushin gefen baki Aslam Yayi,tare da cije lips ɗin sa na ƙasa,cikin ransa yace "yarinya aiko mutuwa zanyi baki isa in nemi wani abu ajikin ki ba,bare kiyi tunanin zanyi sex dake,Allah ya tsareni"amma azahiri buɗe motar yayi ya shiga tare da faɗin"Allah ya kaimu lokacin zanga abinda zakiyi innazo hawa kanki "ya fada kai tsaye ko ajikinsa. Kallon sa Islam tayi baki buɗe,dan ita kam kalmar tashi tayi mata nauyi,wai inyazo hawa kanta?sai kace wata doki. Banza tayi dashi tare da buɗe gaban motar ta shiga.wani sanyi ne haɗe da ƙamshi mai daɗi suka ratsa hancin ta,har saida ta lumshe idon ta,kafin ta buɗe tare da jingina bayan ta da jikin kujerar. Kunna motar Aslam yayi,tare da barin harabar gidan,fuskar sa aɗaure sosai,wllh shi har kunya ma yake ji agansa da wannan yarinyar, Ai ajinsa sai ya zube,adaina ganin girman sa,haka kawai yana zaman sa lafiya za'a ƙaƙaba masa wannan alaƙaƙai ɗin,wacce basu san daga ina ta fito ba,shi Daddy ma ba ruwansa da sanin asalin ta,kawai burin sa yayi aure,shine yake son hada zuri'a da ita. ɗan juyowa yayi ya kalli Islam,wani bakin ciki ne ya ƙara turnuƙe masa zuciya,ganin yadda take wani hura hanci kamar wata tsiya, ji yake kamar ya shaƙeta ya huta. "A'a wai ya haka ne?meye kuma zaka wani rinka satar kallo na?wllh kurwa ta kurr,inkai maye ne kaci kan ka,haka kawai da wanne zanji?ga wannan marin da motar keyi na gardawa, duk ya dameni, ji nake kamar nayi amai,kuma bazaka barni da wannan bala'in haka ba,saika kafamin wannan idanun naka,masu kama da kana jin barci?to bana son kallo ehe,ni..... Bata sami damar ƙara sa wa ba,sakamakon buge mata baki da Aslam yayi cikin fushi. "Wllh idan ki ka ce zakimin rashin kunya anan zane ki zanyi in cillar dake agurin nan,banza fitsararriyar yarinya kawai"Aslam ya fada cikin fushi yana jifan Islam da mugun kallo. Islam kuwa kallon sa kawai take tare da riƙe bakin ta,ranta yayi mugun ɓaci. "Wllh bazan yafe maka ba,mugu kawai,haka kawai kasanya wannan hannun naka mai kama da shebur ka kwaɗamin abakina? Allah saiya saka min wllh"ta faɗa cike da jin haushin sa. Shima cikin jin haushin yadda take masa rashin kunya,ko tsoron sa bata ji yace "wllh idan baki rufemin baki ba zan yi maganin ki ne agurin nan,wawiya daƙiƙiya marar hankali kawai uban waye yace da kishigo motar?tunda qarin gardawa take?saidai inkece gardiyar da tasanya motar wari,dan kuwa ke kin ma fi bunsuru wari"ya fada cikin mugun fushi yana figar motar da mugun gudu. Ji kake ƙummm!! Kan Islam ya bugu da jikin kujerar,da sauri ta dafe kan nata tare da runtse ido. "Wllh duk baƙin cikin ka sai dai kayi ka barni amma nidai nan gani nan bari,kuma bazan fasa faɗin kai mugu bane,dan ba tsoron ka nake ji ba wllh sai Allah ya saka min kuma wllh ni bana wari koda ban sanya turare ba,dan Ni bana amfani da banzan turare na ƙasar nan ma "Islam ta fada afusace idanun ta na kawo ruwa,Amma tsabar taurin rai irin na Islam tayi saurin maida hawayen . Hannu Aslam ya sanya akaro na biyu ya ƙara buge mata baki har saida lips ɗin ta ya fashe. Kuka Islam ta sanya tana mai kallon jinin data gogo daga lips dinta,cikin kuka da jin haushi ta kama dukan Aslam tana faɗin "Allah ya isana mugu,kalli yadda ka fasamin baki?wllh sai na rama,bashi ka ɗauka azzalumi kawai"Islam ta fada cikin kuka tana dukan gefen kafadar Aslam. Tsayar da motar Aslam Yayi dai-dai sun kawo bakin store ɗin,wanda yake mallakina Aslam ɗin ne,dan haka haɗe hannayen ta yayi guri ɗaya tare da zaro manyan idanunsa da sukayi jaaa,saboda ɓacin rai yace "wllh idan baki nutsu ba zan miki dukan tsiya cikin motar nan,kuma in jefar dake anan gurin bani da asarar komai,banza maƙarya ciya,gidan uban wa kike shafa turaren kasar wajen ? Gara ki min shiru ,ki nutsu,dan nan ba gida bane,inkin ga dama ki fito "yana faɗin haka ya warɓar da hannayen nata tare da ɓude motar yayi ficewar sa. Bakin ciki kamar ya kashe Islam,wllh bashi ya ɗauka,saita baƙanta masa kamar yadda ya baƙanta mata itama,kuma wllh duk baƙin cikin sa, saiya siya mata ƙayan nan,kuma wllh lodar kayan zatayi dan yayi asarar kudin sa.tana gama wannan tunanin tayi saurin fitowa tare da bin bayan sa, tana share hawayen da ya maƙale gefen idon ta,dama kukan nata ba wani hawayen kirki. Lokacin data fito harya kusan shigewa cikin store ɗin,dan haka da sauri ta cimma sa, tana balla masa harara. Juyowa yayi ya kalle ta cikin yatsina yace "ashe dai zaki fito ƙaramar tsagera" "Ai badan kai na fito ba,ra'ayin kaina ne yasa na fito"ta faɗa cikin tsiwa tana murguda masa baki. Banza yayi da ita suka shiga cikin store ɗin,aikuwa nan da nan ma'aikatan gurin suka fara gaida Aslam,cikin girmamawa da nuna farin cikin su,dan ya jima baizo gurin ba,komai ta online yake gudanar wa. Taɓe baki Islam tayi ganin yadda suke ta wani girmama Aslam, Cikin jin haushin su tace "aikin banza wahalallu marasa aikin yi,ku rasa wanda zaku girmama haka sai wannan saƙaƙon,mtssss"ta buga uban tsaki tana riƙe ƙugu. Sukan basu fahimci inda zancen nata ya dosa ba,amma shikam oga Aslam, Sarai ya gane da shi take,banza yayi da ita gudun karta tsinkashi gaban ma'aikatansa, Ɗaya daga cikin ma'aikatan gurin mata ya umarta akan ta raka Islam ta zabi abinda take bukata. Shi kuma ya shige wani ɗaki. Aikuwa cikin girmamawa matar wacce zatayi sa'ar jannat tace "to ƙanwata muje ko"ta faɗa cikin sanabe tana kallon Islam da murmushi. Wani banzan kallo Islam ta wurga mata kafin tace "ke dalla Malama bana son iyayi,wacece ƙanwar taki?kinga nayi kama da ƙanwar ki?kije can ki nemi ƙanwar ki ba Islam ba,bana son shishshigi,ki wuce kawai kiyi abinda aka saki"Islam ta fada cikin yarfi. Aikuwa sosai budurwar nan taji kunya tare da haushin Islam, dan ma ba mutane agurin, ita tunanin ta Islam ƙanwar Aslam ce,ita kuma aduniya tana bala'in son Aslam, shine take son kama ƙafa da Islam ɗin,saidai taga wannan yarinyar bata da kunya.dan haka simi-simi ta ja babban kwando tare da yin gaba Islam tabi bayan ta. Ba ƙaramin kaya Islam ta debo ba, dan kwandon ma saida yayi kaɗan ta riƙo wasu ahannun ta. Budurwar nan sai hararar Islam take ,ba damar yin magana dan tana tsoron rasa aikin ta. Haka suka zo gurin biyan kudi aka lissafa, kuɗi sun doshi dubu dari uku da hamsin,dan kaya masu tsada Islam ta zabo,wasu ma ba amfani zatayi da suba,kawai ɗiba take tana zubawa cikin keken,banda gayyar ƙananan kaya data lubgo,da kayan cinye -ciye. Koda aka fadawa Aslam kuɗin kayan mamaki yayi sosai,amma bai nuna damuwa ba,ya basu atm yace su cira, duk da sun nuna ba sai an karbi kudin ba,amma yace a'a su cire kawai. Haka aka loda kayan cikin Boot ɗin motar Aslam. Ta jima zaune cikin motar tana ta cin chocolate ɗinta,data ɗauka cikin waɗanda ta lubgo,kafin Aslam ya shigo cikin motar. Kallon ta yayi yadda ta ke cin chocolate ɗin ta hankali kwance. Kafin ya jinjina kai ya tada motar.haushi fal cikin ransa. Maimakon suyi hanyar gida sai kawai Aslam ya wuce gurin shagunan sa,da ake dinka zallar hulunan sawa, masu kyau da tsada,suna tafiya ta buga wani uban tsaki wanda yasan ya Aslam saurin juyowa ya kalle ta. Cikin haɗe rai tace "kaga malam dan juya kamaidani wancan shagon,dan nayi mantuwa,naga wata alawa kuma ban ɗauko ba" ta faɗa kamar tana bashi umarni. "Saboda ubanki ne ya bani kuɗin ko?baki san zafin neman su ba kika kashemin kudi wajen kwata million sannan yanzu kice in koma zaki ɗauko alawa,ai ko da kuɗin babanki na gina store ɗin baki isa ki sani na koma baya ba"ya fada cikin ɓacin rai. Sai lokacin Islam ta san wai ashe gurin ma nashi ne.duk da zagin uban ta da yayi, ya matukar ƙona mata rai amma saita haɗiye ɓacin ran tace "kash!! Wai kana nufin gurin ma namu ne?amma me yasa baka faɗa min ba? Ai wllh da yau duk wanda taje siyayya gurin bazai biya ko sile ba,amma ba komai za'a tara gaba, abu namu maganin akwabemu,bari nayi saurin shanye waɗan nan uban alawowin dana ɗebo in yaso saina sake sabon shiri"ta fada cikin murmushi idon ta akan Aslam,Wanda yayi galala yana kallon ikon AllahWato ma ita abinda tayi bai dame ta ba,wata barnar take ƙoƙarin sake yi masa?hmmm,ya ga da uban da zata dawo store ɗin. Ƙyale ta yayi baice mata komai ba,dan gani yake magana ma da ita ɓata lokaci ne,dan haka yayi mata banza,tana ta neman maganar ta,har ta gaji tayi shiru ganin bazai kula ta ba,haka tayi ta shan chocolate ɗin nan,data shanye zata ɗauki wata. Har suka zo gaban manyan shagunan nashi,buɗe motar yayi tare da ficewa,kuma ya kulle motar,koda Islam tayi yunkurin fitowa ,akulle taji ƙofar,tsaki tayi tace "aikin banza ya kulle motar,ko nufin sa inyi zaman jiran sa anan?kamar wata baiwar sa?to uban me ma zaiyi agurin nan,maimakon ya kaini gida shine ya wuce yawon karuwancin sa dani,dan gurin nan da da gurin karuwai yayi min kama,gashi nasan janbu yana can yana nema na"ta fáda tana wani taɓa baki tare da gutsirar chocolate ɗin ta. Shikuwa Aslam,Yana zuwa shagon suka gaisa da ma'aikatan sa ,cikin mutunta wa da girmamawa,kai tsaye ya wuce babban office ɗin da yake zama idan yazo. Office ne haɗaɗɗe mai kyau,harda ƙatuwar katifa ta huta wa,dan haka,bayan sun kama lissafin kuɗi da managern sa na gurin,kan karifar ya haura tare da kwanta wa, tunani kala-kala cikin ransa,yanzu idan ya auri yarinyar nan,ya makomar auren nasu zata kasance?shin akwai ƙa'idajjen lokacine da zai sake ta ko kuma zama zasuyi tayi har abada?amma ta yaya zama zaiyi ahaka?bata sonshi,shima baya sonta?Allah yasa anayin auren suga iyayen ta, sukuma suce basu yarda da aurar musu da yarinya da akayi ba,dan haka dole ya sake ta,shikenan komai zai zo masa cikin sauƙi, ya zama dole gareshi ma ya fara neman iyayen nata cikin sirri,ta yadda zasu bayyana cikin sauri koma kafin ayi auren,amma ta yaya zai zauna da mace kuma ba tare da yana samun nutsuwa da ita ba?shidai bazai taba zubar da girmansa yazo gurin wannan abar da sunan neman hakkin sa ba,tabb!! ALLAH ma ya kiyaye wannna ranar. gashi yayi alƙawarin bazai ƙara ƙetare gonar da bata saba,duk da shi iyakarsa romance ne,amma yaga illar yin hakan,kuma ya tuba, Wanda Yayi abayama Allah ya yafe masa. Haka Aslam yayi ta saka da warwara cikin ransa,yana cikin haka barci ɓarawo yayi gaba dashi. Islam kuwa tun tana cin chocolate ɗin nan cikin marmari, har tazo ta fara gundurar ta, gaba ɗaya ta zubar masa da bawon chocolate har Kan seat din da yake zama,kuma duk dan neman magana tayi,ta ɗora ƙafar ta akan gaban motar. Tsaki ta farayi ganin har lokacin bai dawo ba,sai masifa take ita kaɗai cikin mota,Bama wanda yasan da mutum cikin motar,tunda irin baƙin glass ɗin nan ne ajikin motar. "Aikin banza kawai,yazo ya shanya mutane cikin wannan akwalar motar tasa ya tafi yawon karuwan cin sa,wllh zai dawo ya sameni,saiya bani bayanin inda ya tafi ya barni cikin wannan gwangwani nasa,anfaɗa masa Ni mai gadi ce?mugu kawai "Islam ta faɗa cikin jin haushi kamar ta kwalla ihu,dan kusan awarta ɗaya cikin motar bai dawo ba. Wasa-wasa Islam fa tayi awa kusan uku cikin motar,ga yunwa da ciwon ciki dake damun ta, dan ba shan wasa tayiwa wannan chocolate ɗin ba,gashi dama ƙarshen wata ne,riƙe take da cikin ta tana juya kai,dama irin wannan lokacin tana shan wahala idan zatayi period,bare kuma yanzu ta haɗa da zaƙi. Sai murƙususu take rike da cikin ta,tun tana daure wa,har ta fara kuka tana ambaton sunan Allah"innalillahi wayyo Allah cikina,zan mutu! wayyo baya na la'ilaha'illallahu muhammadar rasulullu, Wayyo Allah na, cikina !ciki!!abinda Islam ke ta faɗa kenan tana rike da marar ta dake azabar ciwo kamar zata balle tana kuka. Gashi wannan lokacin ba malamin ta,dama shike bata magani da ta fara wannan ciwon. Yanzu kuma ba mataimaki sai Allah,inka ganta saita baka tausayi,nan da nan lokaci ɗaya tayi ramar dole kamar marar lafiya Aslam kuwa bai farka daga wannan nannauyan barci ba,saida aka fara kiran sallah,ahankali yayi miƙa tare da karanta addu'ar tashi daga barci tare da buɗe idonsa. "barci nayi kenan?"ya fada cikin cool voice,kafin ya mike ahankali,ya shiga toilet,alwala yayi bayan ya kama ruwa,ya fito,saida ya gabatar da salla yana zaune kafin ya tuno da Islam cikin mota.dafe kai yayi da sauri yana runtse ido,harga Allah ya manta da ita, da sauri ya duba agogon Rolex dake hannunsa,kusan awa huɗu yayi yana barci, subhanallah,idan wani abu ya same ta cikin mota fa?ko kuma tana buƙatar yin wani uzurin? Wayyo sam baiji daɗi ba,dan bashi da nufin cutar da ita irin haka.da sauri ya mike ya zari wayar sa da car key Yayi waje cikin hanzari. Yana zuwa ya buɗe motar yana kallon inda take zaune, Cikin tsoro da firgici ya shiga cikin motar tare da zaro ido ya kallon islam cikin tsoro. Dan zuwa wannnan lokacin tuni Islam ta sume tsabar zafin ciwo,hannun ta rike da marar ta,ta ɗora kanta akan seat ƙafafun ta dire aƙasan motar. Cikin tsoro da hanzari Aslam.ya dagota yana jijjiga ta, cikin tashin hankali ya fara kiran sunan ta karon farko arayuwarsa" ke ISLAM !buɗe idonki mana,menene ya sameki?Islam !Islam!!ya faɗa cikin ruɗu yana jijjigata, innalillahi karfa yarinyar nan ta mutu?me zai cewa su mommy? "ya salam" ya faɗa yana haɗata da jikin sa ya rungumeta tsam yana jin wani irin zafi cikin ransa..... Muje zuwa masu karatu Mrs babi ce Anty mammy. [10/1/2022, 9:03 PM] Abk: ____________"Ya Salam,ke !Islam tashi mana,menene ya sameki?am sorry I don't mean to do that,barci ne ya ɗauke ni, Islam Please wake up"Aslam ya faɗa cikin damuwa yana kallon fuskar ta,wacce hawaye ya gama bushewa. Ko motsi Islam batayi,sai yadda ya juya ta kawai take binsa,cikin hanzari ya maidata kan kujera tare da ɗaura mata seat belt ya kunna motar tare da janta aguje yayi asibiti da ita. Yana zuwa asibitin ya kira family doctorn su cewar yana tafe da petient. Doctorn yace masa ya shigo da ita office ɗin sa kawai. Aikuwa yana facking ɗin motar, ya buɗe ya fito,sannan ya zagayo inda Islam take ya ɗauke ta cak! Kamar yar tsana ,dan sam Islam bata da nauyi. Kai tsaye ya nufi office ɗin doctorn da ita. Kwantar da ita likitan yace yayi akan wani gado dake office ɗin,kwantar da ita yayi tare da tsayawa yana kallon ta,bai taɓa jin tausayin ta irin na yau ba,kuma sam bai ji daɗin abinda ya same ta ba. Tambayar sa likitan yayi mai ya sameta har ta suma, "Doctor I have no idea kawai na ganta asume bansan menene yayi silar suman ta ba,kawai ka duba ta"cewar Aslam Yana kallon likitan. Ruwa likita ya fara ɗaura mata,kafin ya fara ƙoƙarin ganin numfashin ta ya dai dai ta. Cikin nasara kuwa ta farfaɗo,saidai tana farkawa ta tashi da ciwon marar.dafe marar ta tayi tana kuka."wayyo Allah marata zan mutu,Aslam kazo ka kaini gida,wayyo Allah na"abinda ta tashi dashi kenan tana murƙususu,jikin ta har rawa yake. Da sauri Aslam ya riƙe hannun ta yana faɗin"sorry Islam yanzu zamu tafi gida,kuma maran naki zai daina ciwo kinji"ya fada cikin tausayawa ganin yadda take ta haɗa zufa jikinta na rawa. Allura likitan yayi mata,dan ya gane meke damun ta,kuma yana tunanin ko tasha kayan zaƙi ne.yana mata allurar kuwa cikin ƙanƙanin lokaci marar ta lafa mata sosai,ta daina murƙususun.tayi lamo kan gadon idonta arufe,ba abinda take rayawa cikin ranta,sai irin matakin da zata ɗauka kan Aslam. Can suka koma kan kujera shida likitan yana faɗa masa,ai period ne zai zo mata,kuma da alama ta sha zaƙi, sannan irin hakan tana kasancewa ga ƴan matan da basu san maza ba,wasu magani yana musu aiki,wasu kuma dole sai idan anyi musu aure sun tara da namiji,kafin suke daina wannan ciwon marar. Shiru Aslam Yayi Yana sauraron likitan har ya kammala bayanin sa,ahankali ya sauƙe ajiyar zuciya tare da yiwa likitan godiya,sannan ya buƙaci arubuta musu magani su tafi gida,tunda jikin nata da sauki,gashi tun safe suka fito yanzu kuma yamma tayi. Haka likita ya rubuta musu magunguna,dai -dai lokacin kuwa,tuni ruwan da aka sa mata ya ƙare,likitan ya cire mata. Cikin sanyin murya da tausayi Aslam yace "zaki iya tashi ne,ko ina taimaka miki? Banza tayi dashi kamar bataji me yace ba,dan mugun haushinsa take ji matuka,wato tasan da gangan ya barta cikin mota,kuma ya kulle,dan kawai ya tsane ta, yana kuma son ta mutu,badan Allah yasa da kwanan ta agaba ba aida tuni ta sheƙa,zaiyi bayani ne wllh"ta faɗa cikin zuciyar ta tana mai ci gaba da kwanciyar ta. Ba irin maganar da Aslam baiyi mata ba,amma tayi biris kamar batajin sa,ƙoƙarin ɗaga ta yayi ganin bazata tashi su tafi ba, Amma sam taƙi yarda ya taba ta,ɗaya kawo hannu zata buge hannun .yasan haushin sa take ji,amma ai shima bada son ransa yayi mata hakan ba,shine take wani neman raina masa hankali dan taga yana lallaɓata,nan take shima ransa ya ɓaci,cikin tsawa yace "ke dalla malama ki tashi mutafi,In kuma anan zaki kwana sai nayi tafiya,dan ina da abubuwa masu muhimmanci agabana" Aslam ya fada cikin fushi yana hararar ta. Ko ci kanka Islam batace masa ba,kuma batayi yunƙurin tashi ba.hakan ya karasa hasala Aslam,sai huci yake ransa ya gama ɓaci. "Kayi mata ahankali Aslam,kasan yarinya ce kuma bata da lafiya , bari nayi mata magana "cewar likitan yana dafa kafadar Aslam tare da kallon Islam ,wacce ke kwance ko motsi batayi. Murmushi likitan yayi yana mai cigaba da kallon Islam dan lokaci guda yaji ta kwanta masa cikin ransa, kyakykyawa da ita mai saurin shiga rai. Ahankali ya matsa kusa da gadon da take kwance, ɗan leƙa fuskarta yayi,dan ta basu baya.cikin taushin murya da sigar rarrashi ya fara mata magana" " Sannu ko, Ƙanwa ta,yi hakuri ki daure ki tashi,In kuma kina jin ciwo ne saiki faɗa min, In baki magani kinji?yi haƙuri daure ƙanwa ta"likitan ya fada cikin taushin murya sosai. Hararar likitan Aslam Yayi,aransa yana cewa "ji banza yadda yake wani maƙale murya kamar wani mace,wawa kawai"Ya fada cikin zuciyar sa yana harara likitan da yaji haushinsa ya kamashi lokaci guda,ganin yadda yake yiwa Islam magana kamar wani saurayin ta. Aikuwa ahankali Islam ta yunƙura tare da zama akan gadon kafin ta sauƙo daga kan gadon ahankali,fuskar nan Tata amatuƙar ɗaure.ta nufi ƙofar fita daga office ɗin ta fice. Binta sukayi da kallo dukan su,Aslam wani bakin ciki ne yake nuƙurƙusar zuciyar sa,wato shida yayi mata magana tayi banza dashi, saboda ta maidashi ɗan iska,amma wannan garan yana mata magana ɗaya, tabi umarnin sa, lallai ta raina shi,ko gidan uban wa ma tasan wannna banzan da har zataji maganar sa sama da tashi.rai bace shima ya nufi ƙofar office ɗin da takardar maganin ahannunsa. "To Aslam Allah ya sawake agaida gida,Please akula da petient sosai saina zo dubiya"likitan ya fada cikin murmushi yana kallon Aslam dake barin office din. Ko ci kanka Aslam baice masa ba yayi waje da sauri,tare da buga ƙofar da ƙarfi,ji kake buumm ! Ƙofar tayi ƙara. Saƙare likitan yayi yana bin ƙofar da kallo,meye kuma ya ɓatawa Aslam Rai haka?ko dai ɓacin ran yarinyar ne yasashi wannan fushin?any way,koma dai menene shiya shafa,shikam yaga mata,kuma zaibi sawu,dan yarinyar ta tafi da imanin sa, masha Allah ga diri. Aslam kuwa cikin ransa yake faɗin"shege, gidan ubanka zaka zo?wllh duk randa naga wannan shegen agidan mu da sunan yazo gurin Islam,saina ci uwarsa,daga zuwa ya duba ta shine yake wani shishshige mata. koda ya ƙarasa Islam bata cikin motar,mamaki ne ya kamashi,to ina kuma ta tafi?ko wane gurin tayi kuma?kamar wanda akace ya duba hanyar fita daga asibitin,aikuwa ya hango Islam har ta kusan ficewa daga asibitin. Dafe kai yayi tare da lumshe idonsa,to gidan uwar wa zata?wa tasani anan?wannan yarinyar nema take ta zame masa matsala arayuwa,salon tayi wani gurin ta ɓata,ace da gangan ya batar da ita,ta ja masa damuwa. Shiga yayi cikin motar tare da bin bayanta,lokacin har ta fice daga asibitin,ƙafar ta ko takalmi babu,ta miƙe kwaltar tana tafiya abinta. Gabanta yasha da motar tare da tsaya ya buɗe mata ƙofar motar, alamun wai ta shigo. Ko inda motar take Islam bata kalla ba,ta zagaye motar taci gaba da tafiyar ta.ƙara tarar gabanta yayi tare da buɗe motar yace "bazaki shigo bane ko yaya"ya fada cikin faɗa da ɗan tsawa. Sake kaucewa tayi tare da ci gaba da tafiyar ta duk da yadda takejin jikin ta ba kwari,gashi marar ta na mata ciwo kaɗan -kadan, amma ta gwammace tafi aƙasa,akanta shiga motar sa .cikin haushi da ɓacin rai Aslam ya fito yayi kanta,yana zuwa bai jira wata-wata ba ya sure ta ya juya gurin motar da ita. Dukan sa Islam keyi cikin haushi da kunar rai tana zille wa,tare da faɗin. "Dalla malam ka sake ni, bana son iskanci,Wanda kaje kayi bai isheka ba shine zaka rinƙa tabamin jiki,dalla saukeni bazan shiga motar taka ba,banza mugu kawai" abinda take fadi kenan cikin ɓaci rai tana dukan sa da son kwacewa.amma riƙon da yayi mata bazata iya kwacewa ba,har ya sanyata cikin motar ya kulle tare da zagayawa mazaunin driver ya shiga shima. kuka mai tsanani Islam ta sanya tana tureshi tare da dukan ƙirjinsa. "Ka budemin na fita bana so !bana so" abinda take fadi kenan Muryar har sarƙewa take.kana jin yadda sautin kukan ke fita kasan taji zafin abinda Aslam Yayi mata matuka.duk yadda yaso riƙe hannayen dan ta daina ƙoƙarin dukansa, kin yarda tayi,bori kawai take masa cikin mota tana kuka da kai masa duka,ganin haka yasashi kawai ya janyo ta jikinsa ya rungume ta tsam-tsam.ta yadda dole ta haƙura da dukan nasa tayi lamo kan faffaɗan ƙirjinsa tana kuka mai sosa zuciya. Lumshe ido Aslam Yayi Yana sauraron kukan tana,yana jin ba daɗi cikin zuciyar sa.duk da irin yadda yake jin ya tsane ta,amma dole yaji ba daɗi cikin ransa,tunda shine silar wannan kukan Nata. Islam kuwa ta riƙe gefen rigar sa ƙam _ƙam tana kuka sosai harda shashsheƙa..... Hmmmmm masu karu anya kuwa waɗan nan mutane ? Muje zuwa dai. Mrs babi ce Anty mammy. [10/2/2022, 10:02 PM] Abk: _____________Islam kuwa riƙe take da gefen rigarsa tana kuka mai shiga zuciya.kusan minti goma suka ɗauka cikin wannan halin,kafin ta fara ƙoƙarin tashi daga jikinsa,jingina bayanta tayi jikin kujera tana share hawayen dake zubowa daga idanunta. Kallonta Aslam yayi fuskar sa ba yabo ba fallasa,kafin ya tada motar suka nufi gida. Kafin su ƙara sa gida ya tsaya ya sai magungun da likita ya rubuta masa, tana zaune cikin motar bata uhmm,bare uhm -uhm. Sai zuciyar ta dake ƙara cika da tsanar Aslam.da tunanin ɗaukar fansa. Haka ya dawo da ledar magungunan ahannun sa,ya ja motar suka tafi. Saida Yayi facking ɗin motar sannan ya ga wayarsa dake ta kawo haske,dan a silent ya saka ta.kira rututu yawanci na mommy ne, dan haka kiranta yayi tare da karawa akunnen sa bayan ya gama facking.yana tsayawa Islam ta fito daga motar tare da nufar cikin gidan. "Hello mommy "Aslam ya faɗa bayan ta ɗaga wayar. "Ina ka kai yarinyar nan ne tun safe?maza ka dawo min da ita,kuma bana buƙatar ganin wani abu da ban yarda dashi ba atare da ita"tana gama faɗin haka ta kashe wayar. Shiru Aslam Yayi Yana bin wayar da kallo,me mommy ke nufi kenan?kodai tana zargin ya tafi da yarinyar ne wani wajen dan yayi mata wani abu?yanzu kuma idan ta shiga ta sanar da mommy wata maganar ta daban fa?anya kuwa mommy zata yarda cewar daga asibiti suke? Ya Salam"ya faɗa yana dafe kansa ,sai kuma yayi saurin fita daga motar tare da nufar cikin gidan. Gaba ɗaya suna falo,dan lokacin anyi sallar magrib,kowa da abinda yake,Mommy na zaune tana kallon ƙofa,zuciyar ta cike da tsoro,dan bata san abinda ke faruwa ba,fatan ta ɗaya shine Allah yasa abinda zuciyar ta ke raya mata ba shi bane.tana nan zaune gurum,taji ƙaran buɗe ƙofar,Islam ce ta shigo cikin Falon da sallama abakinta. Da sauri mommy ta miƙe tana nufar inda Islam take"Islam ina ya kaiku?me ya faru?me yasa kuka daɗe?"mommy ta faɗa tana riƙe hannun Islam tare da kallon jikinta. Murmushi Islam tayi da ƙoƙarin kawar da damuwar ta tace"kai mommy da Aslam muka fita fa, me kike tsammanin zai faru,yawo kawai mukayi tayi da kai ziyara gurare, mommy kar ranki ya ɓaci"Islam ta faɗa dai-dai lokacin Aslam Yana shigo.sosai yayi mamakin yadda Islam ta rufa masa asiri,ko da wasa bai tsammaci hakan ba,ahankali ya sauke ajiyar zuciya tare da godewa Allah da Islam bata yi masa wani sharrin Ba,amma yana mamakin dalilin ta na ƙin sanar da mommy abinda ya faru. "Har naji daɗi hanaklina ya kwanta Islam,bakiji yadda tsoro ya kamani ba,ganin tun safe kuka fita amma baku dawo ba,yanzu kije kiyi wanka da sallah kici abinci ko,granny na can tana cigiyar ki"mommy ta faɗa cikin murmushi tana dafa kafadar Islam, Murmushi itama Islam tayi,kafin tace "aikuwa nima nayi kewar granny sosai,mommy kice ya kawo min kayana kalli yadda ya shigo ba kayan"Islam ta faɗa cikin shagwaba.tana shigewa dakin granny. Shikuwa Aslam Binta yayi da kallo cikin mamakin ta,shifa atunanin sa zata sanar da mommy abinda yayi mata,amma madadin haka ma kareshi tayi,lallai yasan ba banza tayi hakan ba tana da dalili. "Me kuma ka tsaya tunani Aslam?ka kawo mata kayan mana may be tana da buƙatar su yanzu"cewar mommy kenan tana kallon Aslam. Kallon mommy Yayi tare da jinjina kai ya fice,kayan ya dauko ya shigo dashi falon. Hanan da jannat waɗanda suke zaune afalon tun dazu ,ya umarta dasu kaimata kayan dakin granny. Haka suka ɗauka kuwa suka kai mata.lokacin har ta shiga wanka,sai granny dake zaune bakin gado tana magana ita kaɗai"to Ni gani nayi idonki kamar wanda kikayi kuka,wllh ƴar nan ki fadamin gaskiya idan wani abu Asalamu yayi miki na rantse da Allah zage zanyi daga Ni sai ɗan tofi da shima,mu daku iya dakuwa dashi,dan wllh bana tsoron sa" "Wai ke granny baki da wani aiki saina dakuwa, sai kace gidan ƴan dambe?ai wllh ko dani aka barki baki isa darawa ba,bare yaya Aslam,kindai ga yadda Allah yayi masa halittar ƙarfafa"hanan ta faɗa tana ajiye ledojin hannun ta. "Hananu ungo taki,granny ta faɗa tana mata dakuwa,kafin taci gaba,yo girman jikin sa na banza,ai gaɓa gaɓa bashi bane,abin azuciya yake,lokacin ina budurwa samari ma tsorona suke wanda sukafi Asalamu girman jiki ma bare shi.wllh. Duka zan masa,bare wata ke da kike tsaye kamar muciya zororo"granny ta faɗa tana nuna Islam,ita dai jannat bata ce komai ba,tana ajiye wa tayi waje. Turo baki hanan tayi tana mai faɗin "gaskiya granny ki daina ɓata min suna wani hananu?kuma ki daina cemin kamar muciya,kina nufin fa atsaye na tafi bani da shape ko hips?ta faɗa tana turo baki. "To ina kika ganshi?ai wannan sai Islama,yarinya son kowa,ga diri abuɗe ƙasan ta yake kamar turmi, ba irin naku ke da jannat ba,kamar na tsuntsuwa "granny ta faɗa tana cuno baki. Haushi ne sosai ya kama hanan,na yadda kullum granny ke kushe su tana yabon Islam,tsaki tayi tare da barin dakin itama. Nan granny ta fara ɓude kayan cikin ledar . "Kai amma Islama kin iya zabe kalli kiga kayan nan?irin na turawa,kinga da anyi auren saiki yi ta sa abinki,dan zasu miki kyau wllh"granny ta faɗa tana bare wata chocolate mai daɗin gaske. Lokacin Islam ta fito daga wanka,zuwa Wannan lokacin tuni jinin yazo mata,kuma marar ta daina ciwon,dan haka shiryawa tayi tsaf sannan ta zauna bakin gado suna ɗan hira da granny,tana Shan tea ɗin da aka kawowa granny,Dan kullum saita sha tea da dare. Bayan sati guda da faruwar wannan abun,sam Islam ta fita daga harkar Aslam,bawai Dan ta hakura ba,sai dan ta samu ya saki jiki ta yadda zata rama abinda yayi mata cikin ruwan sanyi. Shikuwa Aslam sai yake jin haushin yadda take share shi,idan yana guri saita nuna kamar bata ganshi ba,ko in tana zaune yazo gurin saita tashi.hakan yana sosa masa rai,gani yake kamar raini ne hakan. Yau ma suna zaune afalo ita da Aman,Aslam ya shigo riƙe da uniform,Yana zuwa falon ta fara ƙoƙarin barin falon,bata son zama inda yake,dan tasan muddin suka zauna saita takale shi,kuma bata son hakan yanzu,so take saita hukun tashi tunkunna. "Ke tsaya ki karbi wannan,gobe zaki fara zuwa school,zasu miki interview inkin cancanci shiga ajin su hanan zasu sakaki, in kuma kan ba komai dole kije js 3"ya fada da son takalota. Juyowa tayi ba tare da ta lalle shi,ta miƙa hannu ta karbi kayan da yake miƙo mata tare da ƙoƙarin tafiya. "Ke wai Ni sa'an kine?ya zaki rinƙa min abu kamar wani dan aiken ki ne?bazaki ce min kin gode ba,ahaka zaki karbi kayan kiyi gaba,kinsa da yadda na samo wannan school ɗin"Aslam ya fada azafafe yana huci. Kallonsa Islam tayi sama da ƙasa,kafin ta taɓe baki tace "Ni na saka nemo min makaranta?nace maka bani da ilimi ne?kona bukaci neman ilimi ta hannunka?kai kasa kanka,dan haka bani da lokacin yi maka godiya Malam "ta faɗa cikin tsiwa tana barin gurin. Binta Aslam Yayi da kallo cikin jin haushi,duk fafutukar da yayi wajen nemo mata makarantar amma da irin wannan iskancin zata saka masa kenan? "Yaya kayi hakuri kasan halin Islam,bai kamata kana damun kanka akan lamarin ta ba"Aman ya faɗa yana kallon yayan nasa dake huci kamar kububuwa. Lumshe ido yayi tare da fadin" aman bansan me yarinyar can ke nufi dani ba,yanzu ahaka za'ayi mana auren tana rainani?wane irin zama kake tunanin zamuyi?gashi sam su mommy sun kasa fahimta ta"da ya fada cikin damuwa yana kallon Aman. "Kayi haƙiri yaya ahankali zata gyara,idan kunyi auren kai da kanka zaka koya mata yadda zata girmama ka"ya fada yana kallon Aslam. "Hmmm wannan mai taurin kan ce kake tsammanin zata girmama Ni?yarinyar da bata tsorona ko kaɗan,inaga ma ba wanda ta raina arayuwar ta sama dani,kuma wallh zata sha wahala ne koda anyi auren" ya faɗi hakan tare da barin falon,baisan me yasa ba,ahalin yanzu baya son yadda take share shi,take nuna shi ba komai bane,yafi so koda faɗa ne ta kulashi suyi.inyaso yayi mata masifa itama ta rama . Shiru Aman yayi yana tunanin dama shine ya samu damar da yayan sa ya samu mana,da ba abinda zai hanashi koyawa Islam sonshi,kuma zai kula da ita fiye da tunani,amma kash!! Daddy Yayi sauri. Yanke hukunci wanda dolen sa ya hakura da soyayyar Islam cikin ransa. Washe gari kuwa kamar yadda Aslam ya fada,haka Islam ta shirya cikin uniform din, doguwar riga ce iya ƙwauri sai dan hijabi iya kafaɗa,rigar fara ce sai kasanta blue, haka hijabin ma ya kasance fari ne,sai kanbas fari da safa.ba ƙaramin kyau kayan sukayi wa Islam ba,ta sanya turare ajikinta mai kamshin daɗi.cikin takun ta na izza ta fito daga dakin granny,Dan mutanen gidan duk suna kan danning, ta fito tana tafe tana rangwada wanda zakayi tunanin da gangan takeyi,amma haka tafiyar ta take ,gaba ɗaya saida suka juyo suna kallon ta.banda Aslam,Wanda yayi ƙoƙarin sosai wajen hana kansa kallon ta. "Masha Allah ƴata,kayan nan sun karɓeki sosai "mommy ta faɗa cikin murmushi. Murmushi tayi itama tana zama kusa da granny tace "na gode mommy" Kallonta granny tayi tana mai sakin dariya harda gudakafin tace "Wllh kamar wata yar kasar waje,wannan kayan sunfi miki kyau akan kowa Islama,Allah ya bada Sa'a,kuma ban yarda ki ragawa kowa ba,duk wanda ya taɓaki ki maida masa martani cikin makarantar nan, bana son ki tsaya su raina ki"cewar granny tana buga cinya da cuno baki. Dariya Aman Yayi yace "to ke granny da ake wa mutum faɗa yayi karatu,amma ke kina mata huɗubar tayi faɗa anya karatun kike so tayi?ya fada yana dariya . "To saita tsaya araina ta? Kai kaji banzan,wllh kar naji karna gani, kiyi karatu kuma ki kwatar wa kanki ƴanci" "Mu Bama a faɗa amakarantar mu "hanan ta faɗa tana shan tea. Jannat dai bata ce komai ba dan yanzu haka ta koma bata cika surutu ba sam. "Karki damu granny,kinsan ni ai bazan dauki tsageranci ba, wllh duk wanda yayi min kan kara saina yi masa na itace"cewar islam kenan tana cin soyayyen dankali.tare da hararar saitin da Aslam yake zaune. Ahankali Aslam,Wanda tun fitowar ta bai ɗago kai ya kalle ta ba,duk da yadda yaji suna fadin kayan sunyi mata kyau,sai yanzu ahankali ya sauke idonsa akan fuskar Islam,wacce take nan fayau ba ko kwalli,amma tayi matukar yin kyau,fatar ta har wani sheƙi take. Yasan kuma dashi take wannan maganar Tata,dan yana ɗagowa suka haɗa ido tana hararar sa. ajiye kofin hannun sa yayi tare da mikewa yace "mommy ya kamata mu tafi yanzu,dan lokaci yana ja,idan ta shirya ta sameni cikin mota"yana faɗin haka koyayi waje abinsa. "Islam maza ki kammala ku tafi karki makara" "To mommy "Islam ta faɗa tana mikewa.sallama tayi musu kafin ta fice. Maimakon ta nufi motar ta Aslam, Wanda yake ciki yana jiran ta,kawai saita nufi garden,cikin mamaki yake kallon ta ,mekuma zatayi agarden da sassafen nan? yana nan zaune cikin mota yana tunani yaji tana buɗe bayan mota, baisan me ta saka ciki ba,kawai taji ta rufe ta zagayo ta shiga gaba. Kunna motar yayi tare da nufar makarantar. Ba wanda yayiwa wani magana cikin su, sai kira'ar sudies dake tashi cikin motar,har suka iso makarantar. Ƙoƙarin buɗe motar aslam keyi idonsa ya sauƙa kan janbu dake kokarin dawowa gaban motar kusa da Islam,zaro ido Aslam Yayi tare da saurin matsawa jikin window yana rarraba idanu,ganin yadda birin ke ƙoƙarin ƙetarowa gurinsa... Muje zuwa Mrs babi ce. [10/4/2022, 7:58 PM] Abk: 45/46 _____________Matsawa Aslam Yayi jikin windown motar yana rarraba ido,ganin yadda birin ke ƙoƙarin ƙetarowa gaban motar,sosai yaji tsoron birin dan bazai manta yadda birin ya yayyage masa fuska ba. Cikin murya mai cike da rashin son birin yace "ke meye wannan ɗin?yaushe ya shigo min mota?uban waye ya kawo shi?"ya fada yana nuna birin . Harara Islam ta banka masa kafin tace "idan baka san ko menene wannan ba to nima bansan ko menene ba,sannan nice nan na kawo shi,dan bazan barshi agida ba Ni natafi wata makaranta aji daɗin cin zalin sa,taho maza janbu yau munzo makaranta zamuyi karatu kuma muci uban wanda ya takura mana"islam ta faɗa tana janyo janbu zuwa kan cinyar ta, "Ke wai meye hakan? Baki da hankali ne?nan fa makaranta ce ba gida ba,ubanwa kika ga yana zuwa makaranta da biri?ko an kaya miki makarantar mahaukata ce nan?"Aslam ya fada akufule. Juyawa Islam tayi ta fara kallon makarantar tana taɓe baki,ba ƙarya makarantar tayi mugun kyau sosai,kamar aturai, Juyowa tayi tana kallon Aslam kafin tace"ahaka dai kamar akwai masu hankali acikin ta,amma karka damu idan na shiga ciki,zan bincika maka koda mahaukata cikin ta bamu sani ba"tana faɗin haka ta fara kiciniyar buɗe motar ta fito waje. Dafe kai Aslam Yayi cikin damuwa da ɓacin rai,ta yaya wanda yazo makaranta zai zo da biri?wane karatu zatayi banda ta razana ya'yan mutane?da sauri ya fito daga motar ya zagayo inda take cikin faɗa da ɓacin rai ya fara magana"ke bana son hauka fa,ki san yadda zakiyi da wannan birin,dan bata yadda za'ayi ki shiga musu da wannan birin ,so kike ki razana musu dalibai ko me?"Aslam ya fada cikin haɗe rai. Shafa bayan birin kawai Islam keyi cikin halin ko in Kula tace "ina ruwana da ɗaliban su?wanda yaga zai kalli birina ya kalla,wanda zaiyi karatu yayi amma tunda na taho dashi ba inda zai koma"ta faɗa tana turo baki. Shiru Aslam Yayi Yana jin kamar ya kwada mata mari, wannan yarinyar tana bashi ciwon kai,wllh baisan ya zaiyi da ita ba,idan anyi auren ƙila wataran saidai su dauki mushen sa,baƙin cikin ta ya kashe shi. Haka ba yadda ya iya ya nufi office din principal cikin ɓacin rai,Islam tana tsaye jikin mota bata bishi ba,saida ya kai baƙin kofar office ɗin sannan ya ga bata binsa.kamar ya kwala ihu haka ya juyo yana kallon ta.itama kallonsa tayi tana wani dan iskan murmushi na rainin hankali. "Bazaki taho bane ko? daukan ki zanyi akaina?"ya fada ahasale. Murmushin taci gaba dayi kafin tace "au jirana kake kenan,ashe biyoka zanyi?ai baka ce min in taho ba shiyasa "ta faɗa tana ƙara rungume janbu sannan ta taho gurin Aslam,Wanda yayi saurin shigewa office ɗin principal ɗin. Da sallama ya shiga,cikin girmamawa suka gaisa da principal ɗin ,dan akwai sanayya mai ƙarfi tsakanin principal da daddy. Nan yake sanar dashi ga yarinyar nan ya kawo. Sai lokacin principal ya kalli Islam wacce ke zaune kan wata kujera, janbu kwance kan cinyar ta yana rarraba ido . Cikin mamaki principal yace "subhanallah meye wannan kuma malam Aslam?kamar biri fa nagani ahannun ta? principal ya faɗa yana mikewa tsaye. Dafe kai Aslam Yayi kafin yace "wllh yallaɓai bansan ta taho da wannan abun ba,saida mukazo nan kafin na gani,kasan ba cikakken hankali gareta ba,sannan ba cikin mutane ta tashiba, waɗan nan sune abokan ta shiyasa,amma kayi hakuri"Aslam ya fada cikin baƙin ciki da takaici. "Gaskiya Aslam bazai yiwu mu karɓeta da wannan birin ba,saboda zata razana mana ɗalibai,ko birin ya janye hankalinsu, suƙi maida hankali suyi karatu,saidai ku koma gida yanzu ta ajiye wannan birin zuwa gobe saiku dawo"principal ya fada yana kallo Islam data kafeshi da ido tana hararar sa. "Am yallaɓai ayi haƙuri dai inyaso saina koma da birin ita ta zauna"Aslam ya fada cikin sanyin murya. "Wllh bazan baka janbu na ka koma dashi gida ba,haka kawai kaida ba imani gareka ba,kaje ka kashemin janbu na ?a'a wllh to karatun dole ne?tunda dai wannan mai ƙaton cikin yace bai yarda ba kawai mu koma gida,dan naga shima ɗan bakin cikine" Islam ta faɗa tana hararar principal. Da sauri Aslam ya buge mata baki cikin fushi,yace "wllh idan baki yi shiru ba zan zaneni agurin nan,marar kunyar banza"ya fada kamar zai rufe ta da duka. Buɗe baki principal Yayi Yana kallon Islam,lallai bata da kunya,anya ma zai karɓeta kuwa? "Please yallaɓai kayi hakuri ,zamu dawo goben in Sha Allah"Aslam ya fada yana jan hannun Islam cikin fushi suka bar office ɗin. Zama principal Yayi yana faɗin"wannan yarinyar bata da kunya dole In haɗata da sajan ya koya mata hankali" Janta kawai Aslam keyi cikin fushi da mugun ɓacin rai,ita kuwa sai binsa take kamar zata faɗi. "Malam ka daina jana haka mana kamar wacce nayi maka sata,dalla ka sakemin hannu"ta faɗa cikin salon ta na rashin kunya.bude motar yayi tare da cillata da ƙarfi,har saida kanta ya buge da gaban motar.dafe kai tayi tana faɗin"kai-kai-kai wllh bazan yafe ba mugun mutum kawai,bazanyi karatun Bama na fasa tunda ba dole bane abarni nayi zamana haka kawai wata banzar makaranta ace bazaka zo da abinda kake so ba? wllh ba'a isa hanani yin abinda raina ke so ba ehe"ta faɗa cikin faɗa tana murguda baki da juya ido. tsabar takaici ko kulata Aslam baiyi ba yaja motar da gudun gaske,ya nufi gida. Sai surutu take amotar cike da tsiwa. yayi banza da ita dan idan ya kulata wllh zai iya balla cikin motar nan,dan ba ƙaramin haushi ta bashi ba yau ɗin nan. Da ƙarfi ya taka burki lokacin da suka iso gida,ji kake kan Islam gumm,ya bugu da kujera. "Wai meye hakan kake ta bugemin kai?ko so kake kwakwalwata ta hadu da jini in haukace ?to wllh ta Allah ba taka ba"ta faɗa tana hura hanci. Bayan hannunsa ya sanya ya buge bakinta da ƙarfi,har saida lips ɗin ta ya fashe. Da sauri ta dafe lips ɗin nata tana kallon Aslam. Shima kallon ta yake da wani irin ɓacin rai"wllh kikayi min rashin kunyar nan taki,saina koya miki hankali,daga yau na daina gyale ki,jikin ki ne zai gaya miki wawiya marar hankali kawai"Aslam ya fada cikin fushi yana ficewa daga motar. Kallonsa kawai Islam keyi,batace komai ba,koba komai taga yadda ransa yayi matuƙar ɓaci yau ɗin nan,kuma haka take so dama. Tana ƙoƙarin fitowa daga motar taji an fizgota da ƙarfi anyi cikin gida da ita. Cikin Sa'a kuwa mommy da granny suna falon,yana zuwa ya direta gaban mommy,cikin huci yace "mommy wllh na faɗa miki wannan yarinyar bata da hankali" "A'a me ya faru kuma?ya naga kun dawo kuda kuka tafi makaranta?mommy ta fada cike da mamakin ganin dawowar su yanzu. Cikin muryar bacin rai Aslam yace "mommy can You emagine?wai yarinyar nan da birin nan ta tafi school! Bayan haka take ƙoƙarin yiwa principal rashin kunya"ya fada afusace yana nuna Islam. "Kai Aslamu kaji tsoron Allah,ta yaya zatayiwa furuncipal rashin kunya?saidai idan tabota yayi,zo nan Islama fadamin me ya faru"cewar granny kenan tana janyo Islam. Cikin damuwa mommy ta kalli Islam wacce ke riƙe da birin ta tace "ƴata waya faɗa miki ana zuwa makaranta da biri?haba ƴata kefa mai hankali ce,bai kamata kina irin wannan abubuwan na yara ba,ba kyau kinji Islam?kinga kin ɓatawa yayanki rai,maza ki bashi hakuri "mommy ta faɗa cikin taushin murya da sigar rarrashi. Kallonsa Islam tayi yadda yake ta faman huci idonsa yayi jaa,saida ta faki idon mommy ta murguda masa baki kafin cikin kissa tace "kayi hakuri Aslam,bazan sake ba kuma ai kana gani shine yace min mahaukaci jaka mai yawo da biri,sannan yace wai da gani ba karatun zanyi ba ƙila ma yar ta'adda ce ni ,kai kuma baka ce masa komai ba,shine nace ya daina fadamin haka,kawai ya sanya hannunsa mai kama da katako ya bugemin baki,mommy kalli fa saida gurin ya fashe kuma nace suyi hakuri zan maida janbu gida,amma aslam yaƙi tahowa dashi,wai ba ai bawan bane shi "Islam ta faɗa cikin ƙaƙalo kwalla tana nunawa mommy lips ɗin ta.sosai mommy da granny suka ji tausayin Islam,granny kuwa fadi take Allah ya isanki wllh,mugun furuncipal mai baki jaba. Muje daki in goge miki gurin kai kuma kaci baƙin halin ka"granny ta faɗa tana kama hannun Islam suka nufi daki. Juyowa Islam tayi tare da kashewa Aslam ido ɗaya tana murmushi. Shikuwa Binta kawai yayi da kallo cikin mamakin irin ƙaryar data shirgawa principal da sharrin da tayi masa.lallai Islam sai addu'a. "Me yasa ne Aslam kake son takura yarinyar nan?yanzu kana gani agaban ka ayi mata wannan raunin ? Maimakon kayi wani abu sai kaima kayi ta ɓata mata rai?ita fa macece ba abar duka ba,gaskiya idan ba hali kawai asauya mata wata makarantar"cewar mommy kenan cikin damuwa. Zama yayi kusa da mommy ganin yadda ranta ya ɓaci ,cikin saisaita kansa yace "wllh mommy yadda ta faɗa muku ba haka abin ya faruba, nan ya fada mata yadda sukayi tun farko har zuwan su gida,ya dora da cewa-mommy yarinyar nan inaga zama da dabbobin da tayi ya taɓa mata ƙwaƙwalwa,akwai buƙatar akaita taga likita"ya fada yana kallon mommy. Girgiza kai mommy tayi tana kallon Aslam kafin tace"Ko daya aslam,kalau take,yara irin Islam daban Allah ke halittar su,saidai ayi ta musu addu'a dakuma jansu ajiki ana nusar dasu menene dai dai menene ba dai dai ba,Gara ka koyi yadda zaka rinka nuna mata dai dai,saura kwanaki ya rage auren ku,nauyin ta ya kusan rataya ayuwan ka, sai kana hakuri da ita"mommy ta faɗa cikin rarrashi. Ajiyar zuciya Aslam Yayi ,tare da jingina kansa da jikin kujera,tunowa da yayi an kusa bikinsa da Islam,lallai aiki ya ganshi. Da la'asar Aslam ya fito da nufin zuwa store ɗinsa, dan yana son duba yadda abubuwan ke tafiya, mommy kuma dama tun azabar ta fita wajen biki dasu hanan,Aman baya gida,granny kuwa tana dakin ta tana barci,ba yadda mommy batayi ba akan Islam ta shirya su tafi amma tace suje kawai tafi so ta zauna agida dan haka suka tafi. da sauri aslam ya fito daga dakin sa ya nufi farfajiyar gidan,harya buɗe motar sa ya tuna ya manta wayar sa adaki,dan haka cikin hanzari ya koma,ba tare da ya rufe motar tashi ba. Yana shiga ɗakin ya dauko wayar sannan ya fito. Shiga cikin motar yayi tare da zama yana ƙoƙarin rufewa,kawai yaji an bango kofar tare da zare makullin motar. Da sauri ya ɗago kansa yana kallon window, Islam ce tsaye da keys ɗin motar tana kaɗa masa su cikin murmushi. Sannan tayi masa nuni ya kalli tayoyin motar sa. Tacikin motar ya duba tayoyin gaba ɗaya an sace su ba iska jikin ko wacce.... Hahhhhh Islam manya Muje zuwa Mrs babi ce Anty mammy. [10/6/2022, 12:59 PM] Abk: ______________Ta cikin motar Aslam ya kalli tayoyin motar tashi,cike da mamiki yake kallon tayoyin dake asace. Da sauri ya ɗago kansa yana kallon Islam dake tsaye tana kaɗa masa car keys ɗin dake hannun ta,fuskarta ɗauke da murmushi. Duk da aslam yasan cewa dama Dole Islam sai ta ɗauki fansar abinda ya faru,dan bazata taɓa barinsa ya tafi amatsayin tsautsayi ba,amma bai taɓa tsammanin zata rama ta wannan hanyar ba,wato ta kulleshi cikin mota,bayan kuma ta sace tayoyin motar gaba ɗaya. Islam kuwa murmushi take ta yi tana tsaye gaban motar ta yadda Aslam zai hangota sosai. kissing ɗin tafin hannun ta tayi tare da hura masa iskar alamun kiss.sannan ta kashe idon ɗaya tare da juyawa tabar gurin tana murmushi ga car keys ɗin ahannun ta. Yana kallo ta bar gurin ba yadda ya iya. Da ƙarfi ya daki sitiyarin motar tare da lumshe ido ya jingina kansa jikin kujerar motar. Bai taba tsammanin Islam zata yi masa wannan ɗanyen aikin ba,kuma ai ya bata hakuri,sannna bada niyya yayi mata ba.yanzu ya zaiyi gida ba kowa?gashi baba mai gadi yana can bakin get kuma akwai tazarar da ko yayi wani yunƙuri,sam baba mai gadi bazai jishi ba. Cikin sauri ya zaro wayarsa daya ɗauko adaki. Zaro manyan idanun sa yayi tare da kafe wayar da ido,sakamakon yadda yaganta tayi kwatsa-kwatsa,gaba ɗaya an fasa creen ɗin wayar. Waya mai matuƙar kyau da tsada,wacce ta kasance sabuwar shigowa dan dai-dai kun mutane ke da irin ta.sannan akwai abubuwan sa masu matuƙar muhimmanci aciki.amma yanzu kalli wayar yadda ta tashi daga aiki?dan ko kunnuwa taƙiyi, Lokacin daya ɗauko ta sam baiga wannan aikin da akayi mata ba,dan yana zarowa ya cusa cikin aljihunsa. Waye yayi masa wannan aikin?shiru yayi yana tuno abubuwan da suka faru daga safe zuwa yanzu. Tabbas Islam ce,dan yaganta dazu aɗakin sa,ashe ba mafarki yake ba da gaskene? Lokacin yana barci,ya ganta cikin dakin,sam bai kawo aransa Itan bace yayi tunanin mafarki yake,dan barcine sosai cikin idonsa. to lallai awannan lokacin tayi masa wannan danyan aikin. Shiru Aslam Yayi zuciyar sa na bugawa da ƙarfi cikin ɓacin rai,ahankali ya lumshe idonsa tare da sakin ajiyar zuciya akaro ka barkatai.kawai saiya kwantar da kujerar da yake kai yayi kwanciyar sa aciki motar. bayan ya ƙara gudun ac. Duk yadda yayi ƙoƙarin kawar da ɓacin ransa, ya kasa.nan da nan idanun sa sukayi jaaa sosai,tunanin irin hukuncin daya kamata yayi wa Islam yake,amma duk hukuncin daya yanke,sai yaga yayi mata kaɗan. Haka Aslam yayi ta zama cikin motar nan,zuciyar sa kamar ta kama da wuta,gashi har magrib ba wanda ya dawo gidan. Islam kuwa tana can gurin granny Suna ta hira da dariya.amma bata shigo dakin granny da key ɗin motar ba, saitayi saurin shiga ɗakin Aslam ta ajiye makullin akan madubi tana dariya sosai.kafin ta tafi ɗakin grannyn. Saida ana kiran sallar ishsha sannna su mommy suka dawo.can nesa da Aslam motar su tayi facking suka fito,da sauri Aslam ya tashi yana ɗaga musu hannu,amma kasancewa glass ɗin baƙi ne, sam basu kula dashiba suka wuce cikin gida suna labarin bikin. Dukan sitiyarin motar Aslam yayi da ƙarfi tare da ɗanna horn, amma tuni sun shige har sun kulle ƙorar falon. Ajiyar zuciya Aslam Yayi,ji yake kamar yayi kuka,amma yayi alƙawarin bazai nunawa Islam yaji haushin abinda tayi ba,zai barta ahalin yanzu har sai ranar da aka ɗaura musu aure,anan zata gane bata da wayo. Cikin Sa'a saiga Aman ma ya dawo.dan haka cikin sauri Aslam ya fara yi masa horn. Fitowa Aman Yayi yana kallon motar yace "to yaya kuma me yakeyi cikin mota har wannan lokacin?bari na gani ko lafiya?naga yana min horn" Aman ya fada yana nufar motar. Yana zuwa ya fara ƙoƙarin buɗe motar amma yaji ta akulle,ɗaga kai yayi ya kalli yayan nashi dake mai alamun ya buɗe motar. Rubuta masa Aslam Yayi cewar,akulle motar take,kaje gurin Islam ka karɓo makullin kazo ka budeni. Ya nuni masa ta gaban motar. Cikin mamaki badai kulle shi Islam tayi ba ?Aman ya kalli yayan nashi,jinjina masa kai yayi alamun yaje ya karɓo. Da sauri Aman ya nufi cikin gidan yana jinjina hali irin na Islam,ya rasa mai yasa take wa yayan sa haka,sam bata tsoron Aslam,duk abinda ta ga dama shi take ma,kuma ahaka ake ƙoƙarin haɗa su aure. Ba kowa cikin Falon, kasancewar mu mommy ɗakunan su suka wuce dan gabatar da salla. Dakin granny Aman ta wuce,dan yasan Islam na can. Lokacin daya shiga granny na sallah, Islam kuma tana zaune tana kurbar tea. "Islam Ina car keys ɗin yaya Aslam?"Aman ya fada daga tsaye yana kallon ta. Ɗago kai tayi ta kalle shi, ita sam tama manta da batun Aslam wllh,ashe shegen yana nan cikin mota?murmushi Islam tayi kafin tace "ya bani ajiya ne zaka tambaye Ni?"ta faɗa tana kurbar tea ɗin ta. "Please Islam ki sanar dani inda key ɗin yake koba komai ya fito yayi sallah?"aman ya fada cikin sigar rarrashi. "To kaduba ɗakin sa mana koyana can,Ni meye zanyi tayi da key ɗin motar sa ahannuna har yanzu ?kaduba kan madubin sa"ta faɗa tana ajiye kofin tea ɗin. girgiza kai Aman Yayi kawai,tare da ficewa cikin sauri.makullin ya dauko agurin data ce,hakan ya ƙara tabbatar masa ita ta kulle Aslam cikin motar. Cikin sauri yaje ya buɗe Aslam daga cikin motar, Ajiyar zuciya Aslam ya sauke mai ƙarfi,lokacin daya fito daga cikin motar,jingina bayan sa yayi da motar kafin ya lumshe idonsa,aƙoƙarin sa na kawar da ɓacin ran da ke cinsa. "Yaya is ok, kayi hakuri karka bata ranka dan Allah"Aman ya fada cikin tausayawa ɗan uwan nasa,Allah kadai yasan tsawon lokacin daya ɗauka cikin motar nan. Buɗe rinannun idanunsa Aslam Yayi tare da kallon Aman,baice masa komai ba ya nufi cikin gidan. Alwala yayi tare da fitowa ya nufi masallaci,yayi alƙawarin bazai sake kula Islam ba,har sai ranar da aka ɗaura musu aure,lokacin zai nuna mata shi ba tsaran ta bane.dan haka koda suka zo cin abinci bai nuna komai ba haka yaci abincin sa ya tashi da wuri. Washe gari da safe ya kai Islam makatan kamar yadda pricipal ya fada,duk irin yadda Islam ke neman sa da bala'i sam ƙin kulata yayi,ta taɓa nan ta taɓa can,ta kunna redio ta kashe haka tayi tayi,amma yaƙi kula ta.dan kanta ta gaji ta hakuri tare da jan tsuka. Duk wani interview da ya kamata ayiwa Islam anyi mata,sosai malaman sukayi mamakin ƙoƙarin ta,hatta uban gayya saida ta burgeshi,dan wata tambayar ma kafin agama take bada amsa.dan haka ajin su hanan aka kaita.kujerar gaba aka ajiye ta kusa da moninta. To ranar dai ƙalau akayi karatu aka tashi islam bata kula kowa ba,hatta hanan bata kula ba. Lokacin da aka tashi,driver yazo ɗaukan su.harta buɗe motar zata shiga ta hango wata yarinya zaune tayi tagumi,da alama jira take azo ɗaukan ta,haka kawai taji yarinyar ta kwanta mata arai.da yake akwai bangaren primary cikin makaranta,yarinyar ma da alama bata wuce aji biyar ba a frimary. Rufe motar Islam tayi tare da nufar yarinyar. Hanan na mata magana akan tazo sutafi ina kuma zata?amma ko sauraron hanan batayi ba. Tana zuwa ta zauna kusa da yarinyar.kyakykyawa da ita mai saurin shiga rai. Tana zama yarinyar ta juyo tana kallon Islam,murmushi Islam tayiwa yarinyar itama ta maida mata martani,tana mai cewa"anty kema ba'azo ɗaukan ki bane?"yarinyar ta faɗa cikin muryar ta mai daɗi tana kallon islam. Kallon yarinyar Islam keyi cike da jin wata irin ƙaunar yarinyar cikin ranta tace"a'a an zo daukana kinga motar can,ta faɗa tana nuna motar tasu,kafin taci gaba--ke na gani shine nazo gurin ki,naga kamar kina cikin damuwa,ya sunan ki?kuma Meya sameki kika zauna anan ke kaɗai?bayan naga an tashi masu irin kayanki tun dazu"Islam ta faɗa tana kallon yarinyar. Turo baki yarinyar tayi kamar zatayi kuka tace "anty tun ɗazu aka tashi,amma ba wanda yazo ɗaukana daga gidan mu,kuma Ni wllh na gaji,kinga yaya Hisham yace zai zo ɗauka na yau,amma baizo ba abbana kuma baya ƙasar"yarinyar ta faɗa tana wani yatsina fuska. Murmushi Islam tayi tana jin son yarinyar sosai cikin ranta,akwai iyayi yarinyar ga wayo. "To kiyi hakuri ya Hisham zai zo yanzu kinji?ya sunan ki? Islam ta faɗa tana shafa kan yarinyar. "Sunana Aisha Amma abbana Yana cemin mamana,anty kema ya Hisham yayan ki ne?"A'isha ta fata tana kallon Islam. Dariya Islam ta ɗanyi mai sauti kafin tace "Ni bani da yaya sai Kani,amma daga yau kema ƙanwata ce kinji?"Islam ta faɗa tana kallon A'isha. Murmushi A'isha tayi kafin tace "to anty mu kulla ƙawance"ta faɗa tana miƙowa Islam hannunta wanda ta sarke yan yatsun ta guda biyu. Dariya Islam tayi kafin ta mika manuniyar ta tare da shigarwa cikin yatsun Aisha tana ware wa. Kafin wani daga cikin su yayi magana sukajiyo horn din mota. Da sauri A'isha ta mike tana tsalle "anty ya Hisham yazo na tafi sai gobe bye bye"ta faɗa tana nufar motar da gudun ta. Murmushi Islam tayi tare da bin bayan yarinyar da kallo,sannan ta mike ta nufi motar su. Hanan sai cika take tana batsewa,amma ba damar magana,dan tsoron Islam take. Tun daga wannan ranar kullum Islam na tare da Aisha,hatta abinci ita ke ba A'isha abaki,kuma bata taɓa yarda wani yayiwa yarinyar koda kallon banza ne.musamma take tafiya bangaren yan frimary ta tambayi A'isha ko wani yayi mata wani abu,duk ranar da ta kama yaro kuwa yayiwa A'isha koda kallon banza ne,saita daddoke yaro kuma tasashi yaba A'isha hakuri.cikin ƙanƙanin lokaci Islam tayi suna cikin makarantar,dan duk wanda ya taɓa ta,saiya yabawa aya zaƙinta.kowa tsoron ta yake cikin makarantar. Shaƙuwa ce sosai tsakanin A'isha da Islam,duk gidan su Aisha ba Wanda bai san da Islam ba,kamar yadda labarin A'isha ya isa gidan su Islam. Iyayen A'isha suna jin daɗin yadda Islam ke kula musu da yarinya,kuma sunyi alƙawarin wataran sai sun ziyarci gidan su Islam,dan yin godiya. Yau saura kwana uku bikin Islam da Aslam,duk wani gyara da akewa jannat shi akewa Islam,kasancewar yawancin abubuwan gyaran masu dadine,wanda maman Yusuf yar mutan saƙkwato ta haɗawa mommy shi,yasa sam Islam bata ƙin ci ko shan duk abinda aka bata. Tayi wani freesh da ita har yar ƙiba ta kara,ba abinda ke damunta,uzurin gabanta kawai take,kuma yau kusan sati guda basu hadu da Aslam ba,tana ta mamakin ina ya shiga kuma oho. Rana bata ƙarya saidai uwar ɗiya yaji kunya,yau ta kasance ranar juma'a,wacce dubban daruruwan mutane suka shaida daurin auren Muhammad Aslam da amaryarsa Islam,akan zunzurutun sadaki,dubu dari da hamsin,sai kuma jannat da nata angon Saleem akan sadaki dubu dari.sosai mutane suka halarci gurin daurin auren,Kasancewar aslam baida abokai hakan tasa koda aka gama daurin auren can part ɗin sa da aka gyara inda zasu zauna ya nufa.ko ina agyare fes sai ƙamshi ke tashi ta ko ina,an tsara part ɗin sosai,yayi kyau.yana zuwa ya cire babbar rigarsa ya kwanta akan gado yana tunanin wai yau shi Aslam aka daurawa aure,kuma da yarinyar da ya tsana,wacce take masa kallon sa'anta,bata bashi girmansa ko kaɗan,cije lips ɗin sa na ƙasa yayi tare da jinjina kai yana tunanin irin yadda zai gyara Islam,duk wannan iskancin nata wllh sai ya saita ta. Yanzu zata gane asalin waye Aslam,yasan zuwa yanzu mommy ta gama aminta yana son Islam,Dan sosai yake nuna kulawar sa agareta idan suna gaban su mommy. Waya ya dauka tare da kiran mommy.tana daga wa yace cikin shagwaba "mommy wllh yunwa nake ji,akawomin abinci please"ya ƙarasa adan marairaice. " Ayya Me yasa ka zauna da yunwa Aslam?har abinci fa na aika maka dazu,amma akace baka nan,yanzu kana ina?"cewar mommy cikin kulawa. "Ina wancan sabon part ɗin "ya faɗa ahankali. "To bari akawo maka abincin yanzu" "To mommyna"Aslam ya fada da ɗan murmushi. Itama murmushin tayi tare da kashe wayar. Gidan acike yake da yan uwan mommy Dana daddy,sosai yan uwan mommy keta jin haushin wannan haɗin na Aslam da Islam,dan gani suke ga ya'yan su amma aka wucesu aka haɗa Aslam da bare.dan basu san asalin wacece Islam ba,kawai mommy tace musu yar abokin daddy ce. Bayan mommy ta gama haɗawa Aslam abincin cikin wani ɗan kwando ta fito dan neman yaron da zai kai masa. kiciɓis sukayi da Islam tana fitowa daga ɗakin granny,tana sanye da wata doguwar riga ta shadda mai shegen kyau da tsada,ba ƙaramin kyau tayi ba,duk da ba kwalliya afuskarta,dan taƙi yarda ayi mata make up.amma tayi kyau sosai simple make up ne afuskarta.ɗan ƙaramin lips ɗin ta sai sheƙi yake na man lebe.kanta yasha gyara anyi facking ɗin sa da riboms masu kyau,sai ƙamshi take bugawa. "Masha Allah ƴata kinyi kyau sosai"cewar mommy tana kallon Islam cike da yaba kwalliyar Tata. Murmushi Islam tayi tace "na gode mommy,Ina zaki da wannan kwandon mommy?ko wani za'a kaiwa?"Islam ta faɗa tana kallon kwandon. "Wllh wai Aslam ke jin yunwa,shine na hada masa abincin ina neman wanda zai kai masa"cewar mommy tana kallon Islam. Wani daɗi Islam yaji cikin ranta,dama neman sa take ruwa ajallo, dan tayi masa tijara .dan haka cikin sauri tace "laaa mommy kawo na kai masa mana"ta faɗa tana karbar kwandon, "Yauwa Islam,yana wancan ɓangaren naku"mommy ta faɗa tana daga wayar ta dake ringing. Murmushi Islam tayi tare da cije lips ɗin ta kafin ta nufi ƙofar da zata sadaka da part din ta cikin Falon. Masu karatu amarya fa ta tafi kaiwa ango abinci koya zata kaya . Anty mammy ce. [10/7/2022, 11:23 AM] Abk: ________Murmushi Islam tayi,tare da cije lips ɗin ta na kasa, kafin ta nufi hanyar dazata sadaka da bangaren nasu ta cikin Falon. Tana ta jin daɗi cikin ranta,wllh yau zata yaɓawa Aslam maganganu,gashi dai yau anɗaura musu aure da ita ,yace ya wuce da ajinta, idan ta aureshi zata sha wahala,to so take taga yadda zai iya wahalar da itan. dan wllh saita gana masa azaba,zata gasa masa aya ahannun sa,saiya gwammace kiɗa da karatu. Tana ta faman zancen zuci na salon mugunta da zata yiwa Aslam, ta ƙara so part ɗin.kai tsaye ta kunna kai cikin Falon. "Masha Allah"shine abinda Islam ta faɗa tana bin falon da kallo.komai na falon ya kasance light purple ne da pinch ,kujeru,labulaye,carpet.hatta docoration ɗin dakin irin kalar ne,banda ƙamshi ba abinda falon keyi,murmushi tayi tana mai lumshe ido tare da shaƙar ƙamshin falon.cikin annashuwa tace "gaskiya falon nan ya haɗu matuka,ga kalolin irin wanda nake so,lallai zanyi tsiya idan na dawo nan wllh"ta faɗa cikin dariya tana nufar wani daki dake kusa da ita. Dakuna ukune acikin falon,amma wannan yafi kusa da ita,tunanin ta nan ya bata Aslam na ciki,dan tanan take jiyo mayen ƙamshin nan nasa. Kai tsaye ta tura ƙofar ta shiga da sallama cikin maƙoshin ta,wacce ko Aslam ɗin bai jita ba,dan yayi nisa cikin tunani. Sai ganin mutum yayi tsulum ya shigo. Da sauri ya tashi zaune ya kafeta da ido,tabbas ko maƙiyi ya kalli Islam yasan tayi kyau baƙarya,rigar ta zauna ajikin ta dass.duk da rigar ta kasance A shape ce,hakan bai hana manyan na shanun ta kunburowa sosai ta cikin rigar ba,sunyi dass amuhallinsu.daga ƙasa kuma manyan hips ɗin ta sun samu guri sun ƙara bajewa. Nan take asalamamiyyar Islam ta fara motsi.dan sosai kwalliyar ta Islam ta tada masa tsohon tsumin sa. Kallon sa Islam tayi bayan ta gama ƙarewa dakin kallo tana murmushi shikuma wannanan ɗakin komai fari ne da pink,shima ya kawatu sosai da sosai. "Wllh ba ruwa na da koma me zai faru,ko kuma nan ɗin dakin waye,tabbas wannan ɗaki,shine nawa.nan na zaɓa matsayina na matar gidan"ta faɗa cikin isa da gadara tana wani murmushi da juya idanu.wanda tana yi ita da sunan batawa Aslam,rai,amma batan san cewa ƙara kunno shi take ba.idonsa akan na shanun ta yake,dama can lokacin Aslam Yana ɗan hannu sune abubuwan da mace ke ruɗarsa dasu,bare yanzu daya kwana biyu bai jisu cikin hannun sa,kuma sai gasu gabansa matsayin mallakin sa. Hakan ya kara ingiza shi faɗawa cikin matsananciyar sha'awa sosai. Zagaya ɗakin Islam ta fara cikin wani irin taku mai rikita mai kallo,duk taku ɗaya idan tayi,aslam ji yake kamar tana kara masa buƙatuwa ne,banda bugawa ba abinda gaban sa keyi,idanun nan nasa sunyi jaaa tsabar jarabar dake cinsu. "Malam Aslam ango,amma fa kayan nan sunyi maka kyau matuƙa,kamar wani ango gaske"Islam ta faɗa cikin murmushi tana kallon Aslam wanda ya zama kamar wani gaula yana Binta da ido. "Na tabbaba ko yanzu ka san wacece Islam rainon dawa ce,idan nasa kaina yin abu babu wani wanda ya isa ya hanani yinsa,kaima shaida ne, kodan wannan auren bogin da mukayi da kai,kuma kasani bazan sake ka ba har saina gama gyara maka zama,zaka yi ta zama cikin ƙunci tare da wacce baka so"Islam ta faɗa cikin dariya sosai . Binta kawai Aslam keyi da kallo zuwa wannan lokaci ya kai matsayin da bazai iya jurewa ba,dan shi ko jinta ma bayayi,kawai Binta yake da kallo, yaga bakinta na motsi kamar tana son yi masa kiss ne,dan haka cikin sauri ya mike tsaye tare da nufar inda Islam ke tsaye tana wani girgiza jiki,batare da tsoron ganin ya nufo ta ba , Islam ta kara gyara tsayuwar tana jiran karasowar Aslam gareta.Aslam kuwa yana zuwa baiyi wata-wata ya kamo fuskar Islam,da hannayensa duka biyun,wanda suke ɗan rawa,bai jira komai ba ya haɗe bakin su guri daya.cikin wani irin salo da zaƙuwa ya fara tsotsar bakin Islam kamar ba gobe,yayin da hannayensa ke yawa cikin jikin Islam, ta ko ina,ba abinda ke fita sai sautin nishin da Aslam keyi kamar yana tsere. Cike da wani zazzafan tsoro da tashin hankali,Islam ta zaro idanun ta waje,meye hakan ?me Aslam keyi mata?ba dai iskanci yake ƙoƙarin yi mata ba, innalillahi.ba abinda yafi dagawa Islam hankali,irin yadda Aslam ke matse mata dukiyar Fulani kamar ya samu fulawa,wato wancan karon ganin su kawai yayi shine yanzu kuma harda taɓa wa? Cikin hanzari da tashin hankali isalam, ta fara kiciniyar kwace wa daga gareshi,saidai kamar mayen ƙarfe haka Aslam ya manne ajikinta.saima ƙoƙarin zuge zif ɗin rigar ta da yake,wanda cikin nasara ya zuge zip ɗin tare da sakin rigar tayi kasa, nan da nan Islam ta zama daga ita sai bra da fant fararen tass, dasu.cikakku kuma tsayayyun na shanu ta suka bayyana cikin farar bra ɗass dasu. Tsoro ne ya ƙara kama Islam ganin Aslam ya cire mata riga,gashi tayi iyakar ƙoƙarin ta wajen tureshi daga jikin ta ko cire bakinta daga cikin nashi amma ta kasa,ji tayi kamar dutse take turewa,nan tsoro ya kara kamata,jikinta sai rawa yake idanun ta suka ciko da kwalla. Aslam kuwa kwata -kwata baya cikin hayyacinsa yayi dogon zango,sam baya ji baya ganin komai sai abubuwan dake gabansa.yamutsa Islam yake iya don ransa,kamar ya sami kayan wanki. Gaba daya Islam ta rasa ya zayi ta kwaci kanta daga gareshi,gashi sosai take jin zafin yadda yake matse mata ƙirji. Wani yunkuri Islam tayi cikin hanzari ta fizge bakinta daga na Aslam,tare da tureshi can gefe guda,jikinta na rawa,tsabar rikicewar da tayi tama kasa ɗaukan rigar ta rufe jikinta sai hannu ta sanya tana rufe ƙirjinta dashi. Aslam kuwa kamar wani dan giya yayi tagal -tagal zai faɗi amma yayi saurin dafe jikin bango,kallo ɗaya zakayi masa kasan baya cikin hayyacinsa. Ɗago rinannun idanuwansa yayi ya saukesu akan Islam,nan take idanunsa sukayi masa arba da kwawawan na shanuntada suka bayya ta mahadar brar dake jikinta,wani irin abune ya tsirga masa,wanda kamar an zabureshi ya ƙara tunkarar Islam,gadan gadan,ganin haka yasa Islam juyawa da sauri ta nufi ƙofa jikinta na rawa,amma taku ɗaya biyu Aslam ya kamo ta,ƙara ta kwalla cikin tsoro tana faɗin"wayyo Allah na mommy kizo Aslam Yana min iskanci,na shiga uku,Aslam meye hakan ka bari bana so ka daina taɓani banaso wayyo Allah mommy kiz....... Kalamanta suka tsaya cak!sakamakon wata damka da Aslam ya kaiwa na shanunta,runtse ido tayi da ƙarfi saboda zafin daya ratsa kwakwalwarta,tareda cije lips ɗin ta. Shikuwa Aslam cikin wata murya mai kama da zaiyi kuka yake faɗin"Please karki gujeni awannan lokacin bazan iya jurewa ba ki tsaya ina buƙatar ki Please Islammm "ya fada tare da jan harafin sunan ta. Ganin abinna Aslam ba alamun hankali,dan gani kawai islam keyi kamar ya haukace ne,yasata fashewa da kuka mai ƙarfi sosai. Aikuwa cakk!Aslam ya dakata da abinda yake mata.saidai ya kasa barin jikinta,amma ya daina taɓa jikin nata.runtse ido yayi da ƙarfi,ahalin da yake ciki ji yake shima kamar ya sanya kukan,dan yakai ƙololuwa wajen buƙatuwa,ahankali ya fara ja da baya idanunsa ko gani basayi sosai,sai lokacin tunaninsa ya fara dawowa jikinsa,zama yayi bakin gado tare da dafe kansa,jikinsa sai rawa yake,idanunsa ko budewa basayi. Zamewa Islam ma tayi agurin tana ci gaba da kukanta,dan ba karya yau kam Islam tasan me ake nufi da tsoro,sosai tsoron Aslam ya kamata. Kusan minti ɗaya Aslam yana dafe da kansa kafin yayi zunbur ya mike tsaye wata loka ya buɗe tare da ballo wata ƙwayar magani ya hadiyeta ba ko ruwa,kamar wani ɗan giya haka yake tafiya ya nufi toilet.yana shiga ya sakarwa kansa ruwan sanyi ko kayan bai iya cirewa ba,yana tsaye ruwan na sauka akansa kusan minti goma kafin ya samu ƴar nutsuwa.ya rasa me yasa ya kasa controling kansa yau,wanda abaya yana iya sarrafa kansa akan Islam,amma yau ji yayi sam bazai iyaba,har saida yakai gareta. Cire kayan yayi tare da rataye su sannan ya sanya rigar wanka bayan ya tsarkake jikinsa.bude kofar yayi tare da fitowa. Rass gabansa ya faɗi, ganin har lokacin Islam na zaune agurin da ya barta,zuwa lokacin nan ba kuka take ba,amma hawaye na zuba akan fuskarta,kuma jikinta bai daina rawa ba.tana jin motsin buɗe kofar da itama ta zabura tare da ƙanƙame jikinta. "Uban me kuma kuma kika tsaya yi min adaki?abinda kike so ɗin ai nayi miki ko?kuma dan me zaki sani gaba kina min kuka?ko bai isheki bane kina buƙatar kari?"Aslam ya faɗa cike da borin kunya,yana son kare kansa. Duk da yadda Islam ke jin tsoron Aslam ahalin yanzu hakan bai hanata balla masa harara ba cikin kuka tace "ai dayake nice nazo na kama ka da kokawar sai ka taɓani,wllh kaji kunya tunda baka iya tsallake haram,kuma saina fadawa mommy kai da kowa ma na gidan nan sai sunsan halin ka na iskanci"Islam ta faɗa cikin mugun jin haushin Aslam,kuma kwata -kwata ta kasa mikewa tsaye,kafafunta rawa kawai suke,amma da tuni ta bar masa ɗakin tun kafin ta fito. Shi dariya ma kalamanta suka bashi,wai baya tsallake haram,kota manta yanzu suna da aure ne?azahiri kuma tsaki yayi kafin yace "banza sakarai,jeki fadawa mommyn mana,kanki zaki ba kunya,dan kowa yasan da aurena akanki,duk abinda nayi miki halal ɗina ne"ya fada yana nufar gaban madubi. Cikin masifa Islam tace "dan an daura mana auren wasan da kai ,shine akace ka tabani?har da taba min...sai kuma ta kasa ƙarasawa hawaye sharr ya zubo daga idanunta,dan taji mugun haushin yadda Aslam yayi ta taɓa mata na shanun ta,kuma wllh bata yafe masa ba. Tsaki Aslam Yayikafin yace "wato kin manta lokacin da kike cewa na taba miki su suna miki kaiƙayi ko?zaki dawo gobe ma kice kina so" ya fada cikin dakiya yana shafa man Zaro ido Islam tayi cikeda mamaki tana tunanin yaushe tace ya taba mata ƙirji wai suna mata ƙaiƙayi? Kodai ta faɗa bata sani ba? innalillahi yanzu da kanta zatace ya taɓa mata jiki? Shiru tayi bata ce komai ba,har ya gama tana zaune agurin ta na hawaye.so yake ya nuna mata shima dan duniya ne,dan haka kayan da zai sauya ya dauko tare da inner wears ya fara ƙoƙarin cire rigar wankan. da sauri Islam ta kife kanta agwuiwarta gabanta na faɗuwa,yanzu saiya cire kaya agabanta ?ta shiga ukun ta ita kam yau. Murmushi Aslam yayi yana faɗin "mara kunyar banza,da saiki ci gaba da rashin kunyar ai"ita dai shiru tayi batace komai ba.saida ta tabbatar ya gama,sannan ta ɗago kanta ko kallonsa batayi ba ta fara ƙoƙarin janyo rigarta ta sanya,sannan ta fara yunƙurin tashi,cikin Sa'a kuwa ta mike tsaye saidai har lokacin ƙafafun ta rawa suke,dafa bango tayi ahankali tana tafiya. Murmushi Aslam Yayi cikeda jin daɗin ya gano lagon Islam kuma wllh ta haka zai ringa hukun Tata. Saida taje bakin ƙofar fita kafin ta juyo tana kallonsa tace"kuma wllh Allah saiya sakamin yadda kayi min kaima sai anyi maka,sannan ka sani wllh bashi ka ɗauka,dan saina rama abinda kayi min azzalumi kawai"tana faɗin haka ta juya taci gaba da tafiyarta. "Duk lokacin da kika shirya ramawa to ashirye nake ina jiran ki"Aslam ya faɗa cikin murmushi.ashe sam Islam bata da wayo,duk rashin kunyar ta iya baki ya tsaya. Abincin sa ya janyo ya zauna yaci ya koshi,amma sam ya kasa mantawa da moment ɗin su na yanzun nan.sai faman murmushi yake. Islam kuwa saida ta sami guri ta zauna ta huta sosai, kafin ta share fuskarta ta nufi cikin gidan,tana shiga falon gidan, gaba ɗaya mutanen dake falon suka bita da kallo,ganin yadda gaba ɗaya shaddar jikin ta ta ya mutse yamutse,sosai ,itama tsarguwa tayi da yadda mutane ke kallonta,dan haka cikin sauri ta nufi dakin granny.... Muje zuwa masu karatu. Anty mammy ce Mrs babi. [10/8/2022, 4:34 PM] Abk: _____________Cikin sauri Islam ta nufi dakin granny,har zuwa lokacin jikinta rawa yake,sosai take jin wani iri ajikinta,ji take kamar har lokacin hannun Aslam akan ƙirjinta yake.cikin Sa'a kuwa bata tarar da kowa cikin ɗakin ba sai granny,dake zaune tana cin abinci. Kai tsaye ta haye gado, tare da kwanciya ta ƙanƙame jikinta. Kallon ta granny tayi,tare da cewa"islama ,lafiya kuwa?naga kinzo kin kwanta,keda ake auren ki?" Granny ta faɗa tana kai loma da ƙatuwar tsokar nama. Shiru Islam tayi, kafin ta turo baki tana mai cewa"granny wllh Aslam Dan iska ne,kinsan abinda yayi min yau kuwa?"ta faɗa cike da alhini tana kallon granny. Ajiye abincin da take ci granny tayi tana mai kallon Islam,cike da taraddadi tace "Ni yar nan me yayi miki na iskancin?" Granny ta fada tana kallon Islam, Tagumi Islam ta buga tareda kafe granny da ido,kusan minti biyu batayi magana ba,ita Bama tasan ta ina zata sanar da granny wannan ta'addancin da Aslam Yayi mata ba,dan kuwa abin yayi mata nauyi,amma dole ta faɗa mata,dan asan matakin ɗauka,tunda yanzu guri ɗaya zasu koma da zama. "Kiyi magana mana islama,wllh kinsa gabana sai lugude yake"cewar granny cikin zaƙuwa. Kallon granny Islam tayi,kafin ta ja dogon numfashi,tace "granny wai daga naje Kai masa abinci fa,kawai ya kamoni ya fara shamin baki,hakan bai isheshi ba harda taɓa min ƙirji bayan ya ciremin riga,kuma wllh Ni bazan yar daba,wannan maganar saita je har gaban daddy"Islam ta kai zancen ta tana turo baki cikin masifa kamar Aslam na gabanta. Salati granny ta fara kwadawa tana tafa hannu,"yanzu wannan yaron dan tsabar jarabar sa bazaiyi hakuri akaiki ɗakin nashi bama?tun anan zai fara nuna miki shi jarababbe ne?kai Allah kayi mana tsari da wannan zamani,yo mu Allah na tuba lokacin da akayi mana aurema ba saikiyi shekara da miji bai ko taba hannun ka ba,to bamu san ma me akeyi aɗakin mijin ba,mudai kawai anyi mana aure,amma yan wannan zamanin wllh jarabar su tayi yawa"granny ta kai dogon zancenta tana riƙe da haɓa. Cikin turo baki Islam tace "wllh granny Ni tsoro ma ya bani, yadda jikinsa ke wani rawa kamar mai zazzaɓi,idonsa kuwa yadda kikasan an saka masa barkono haka yayi ja,da ƙyar fa na kwaci kaina"Islam ta faɗa tana ɗan zaro ido da riƙe haba. "Ohhh Ni yar nan,shikuma inaga kakansa ya gado,irin mazan nan ne da basa iya sarrafa kansu ga mace,lallai dole ki shirya Islam,dan aiki ya ganki,saikin yi hakuri dashi, dan nima haka na sha fama daga ƙarshe . Sannan karki fadawa kowa wannan maganar kinji?dan sirrin kune keda shi"cewar granny tana kallon Islam cikin yanayi na tausayawa. Haɗe fuska Islam tayi tare da kallon granny,lallai ma grannyn nan,wai tayi shiru?kenan yaci banza?wllh bai isaba,saita fadawa mommy, adau mataki,dan bazata koma bangare daya dashi yaci gaba da mata wannan iskancin ba. "Yanzu ke granny idan akace ma zan bar wannan maganar saiki yarda?wllh saina faɗawa mommy ta ja masa kunne,haka kawai yaje ya iskanta ni ina zamana,har yanzu fa ji nake kamar yana taɓani ne"Islam ta faɗa tana saukowa daga kan gadon tare da nufar kofar barin ɗakin. Riƙe haɓa granny tayi tana kallon islam tace "yau naji sakarar yarinya,yanzu ke surukar taki zaki fadawa abinda ɗanta yayi miki?sirrin shimfiɗar ki?wllh bansan baki da wayo ba dai yau,ai saiki je dan bazan hanaki ba ke zaki sha kunya nan gaba"granny ta faɗa tana ci gaba da cin abincin ta. Kai tsaye Islam tana fita ɗakin mommy ta nufa,awannan karon ba ruwanta da yadda ake kallon ta,wasu da basu san itace matar Aslam ba suna tambayar wacece?ana faɗa musu matar da Aslam ya aura ce. Mommy na zaune cikin ƙawayen ta da wasu daga cikin dangin ta dana daddy Islam ta shigo ɗakin,bata kula kowa ba ta nufi gurin mommy, kallo kawai yan dakin suka bita dashi,ganin ba wanda ta gaisar,sai da taje gaban mommy sannan tace "mommy gurin ki nazo kawo karar Aslam" ta faɗa cikin yanayi na shagwaba. Sai lokacin hankalin mommy yayo Kan Islam,kallon ta tayi tare da mikewa ta kamo hannun ta"lafiya islam?me yayi miki,ya naga kayan naki duk sun yamutse? Mommy ta jero mata tambayoyi tana kallon jikinta,tunanin ta ma ita kar ko Aslam ɗin dukan Islam yayi. Cikin turo baki Islam tace "mommy wllh iskanc.....da sauri mommy ta rufe mata baki jin abinda take shirin faɗa,jan hannunta tayi tace "zo muje daga waje" ta fada tana jan Islam zuwa falon ta. Falon ma.cike yake da mutane,dan haka ɗaya dakin dake falon,wanda take saukar bakin ta na jiki ta ja Islam suka shiga.tunda ba kowa cikin dakin,duk suna falo. Bakin gado ta zaunar da islam,itama ta zauna. "faɗa min Islam me Aslam ɗin yayi miki?"mommy ta faɗa cikin damuwa. Cije lips Islam tayi cike da jin haushi kafin tace "mommy kija masa kunne,kinga yanzu guri ɗaya zamu zauna dashi,Ni ba yar iska bace amma shi so yake saiya iskanta ni kuma wllh Ni bazan yar daba"ta faɗa tana ƙara turo dan bakin ta tareda kawar da kanta gefe. Kallon ta mommy tayi cikin rashin fahimta kafin tace"Islam Ni ban fahimci me kike don sanar dani Aslam ɗin yayi miki ba? Ki sanar dani kai tsaye,Ni kuma zan ɗau mataki akan abinda yayi miki"mommy ta faɗa cikin rarrashi tana dafa Islam. "Mommy Dana kai masa abinci ne fa kawai ya rikeni yana shamin baki,sannan ya ciremin riga yana taɓa min.... Da sauri cikin wata irin kunya mommy ta rufewa Islam baki.tana faɗin"haba Islam baki da hankali ashe?me yasa kike faɗar wannan maganar?sirrinku ne keda mijin ki,karna ƙara jin irin wannan maganar kinji?"mommy ta faɗa cike da kunya. Turo baki Islam tayi tana faɗin"mommy taba min ƙirji fa yake,saura kaɗan ya ciremin bra,wllh mommy Dan bakiga abinda yayi min bane,kuma nasan nan gaba ma ƙaramin zaiyi idan bakiyi masa faɗa ba" Dafe kai mommy tayi,ganin duk yadda take rufewa Islam baki,amma saida ta kai aya. "Naji Islam,kiyi hakuri to,kuma dama ai dole zai taba ki tunda ke matar sace,kuma hakan ba haramun bane, lada zaki samu duk abinda yayi miki,dan Allah Islam kiyi hakuri,Aduk yadda kika sami Aslam,ki rikeshi hannu biyu,ki kula da buƙatar sa,Allah zai baki lada sosai, wannan shine auren"mommy ta faɗa tana riƙe da hannun Islam,cikin yanayi na kula take faɗa mata maganar. Kallonta Islam take cike da mamaki,kenan itama bataga laifin abinda Aslam yayi ba? "Yanzu mommy kina nufin duk lokacin da yazo da nufin zai taɓani,karna hana shi? "Eh Islam haka nake nufi,domin hanashin zai iya jefashi cikin wani hali,sannan daga yau karki ƙara fadawa kowa sirrinku keda mijin ki,duk abinda yayi miki kiyi hakuri,kowa da haka ya saba kinji"mommy ta faɗa tana shafa kan islam,dajin sonta sosai cikin ranta. Shiru Islam tayi tana kallon mommy kafin tace "shikenan mommy Amma duk abinda ya faru nidai ba ruwana "ta faɗa tana watsa hannayen. Murmushi mommy tayi,tana mai cewa"ba abinda zai faru ma ƴata sai alkairi in Sha Allah"ta faɗa tana mikewa tare da cewa"kije ki sauya kaya,anjima kaɗan za'ayi dinner,wannan doguwar rigar zaki sa kinji?"mommy ta faɗa tana shafa kan islam. Jinjina kai kawai Islam tayi,azuciyar ta tana faɗin"wllh bazata yarda Aslam Yayi ta taɓa mata jiki da sunan wai ba laifi bane hakan,salon yaje ya lalata ta,kuma azo ana mata kallon yar iska,tab ina ruwan ta?yaje yayi ta shiga wani halin shiya jiyo. Tana faɗin haka ta tashi ta koma can dakin granny tayi kwanciyar ta.ba jimawa barci yayi gaba da ita. Aslam ma Yana gama cin abincin ya kwanta,da nufin ya huta,saidai ko minti biyu baiyi ba,yan uwansa matasa yan dangi suka shigo dakin,bisa jagorancin Aman,nan sukayi ta tsokanar sa da hirarraki kala kala,dan acikinsu akwai masu aure. Duk zancen da suke yi Aslam kallon su yake yana murmushi,yayin da can kasan zuciyarsa ,ba abinda yake tunani sai abun da ya faru tsakanin sa da Islam ɗazu. daga ƙarshe ma kwanciyar sa yayi ya barsu nan suna ta hirarsu. Lumshe ido yayi tare da ɗora hannunsa akan goshinsa,hoton surar Islam ne kawai yake masa yawo,nan da nan yaji jikinsa yayi wani yummmmm!sakamakon tuno yadda yake ya mutsa dukiyar fulanin Islam ɗazu dayayi,nan da nan yaji asalamiyyar sa ta fara kumbura. Da sauri ya juya bayansa ya ba mutanen dakin baya,dan gudun kar suga yadda asalamiyya ke hankoro,shi mamakin kansa yake yanzu,ada sam baya damuwa da Islam,amma tunda aka fara maganar aurensu,yake shiga wani halin idan ya tuna da surar ta,barin ma yanzu daya kaiga hada jiki da ita,shi tsoro ma yake kar yaje abin yaci gaba,harta gano shi,raini yazo ya shiga tsakani. Lumshe idonsa yayi tare da ƙankame jikinsa kamar wanda ke jin sanyi,ba abinda yake so da sha'awa ahalin yanzu daya wuce yaji Islam ajikinsa,tsaki yayi tare da ƙara matse cinyar sa yana mai jin haushin kansa,na yadda ya bari wata Islam ke neman tada masa hankali. Haka yayi ta kwanciya akan gadon kamar mai barci,nan kuwa ba barcin yake ba,sai ma wahala da yake ta faman sha,gashi natacciyar taki barin idanunsa da zuciyar sa. Ganin idan yaci gaba da kwanciya ahaka,to komai zai iya faruwa,yasa shi saurin tashi yana mai daga rigarsa sama dan boye asalamiyyarsa data yi masa tsaye kamar wani sanda ,yayi saurin shiga toilet. Kayan jikinsa ya cire tare da sakarwa kansa shaya yana hararar asalamiyyar tasa.na ganin rashin haƙuri irin nata da kawai ci. Kusan minti talatin ya dauka atoilet ɗin kafin ya fito bayan ya dauro alwala.dan lokacin la'asar tayi,kuma ƙarfe biyarne zasu tafi gurin dinner.shi wllh badan mommy ta dage masa ba,da ba inda zaije. Karfe biyar saura kwata,duk wani wanda zaije gurin dinner ya shirya sun fito farfajiyar gidan,wasu ma har sunyi gaba. Jannat tayi ado cikin town mai kyau da tsari tayi kyau sosai kamar ka ɗauke ta,angon ta ma yana cikin mota,dan tuni yazo, dan su tafi gurin dinner. Aslam ne ya fito cikin wata dakakkiyar shadda mai bala'in kyau da tsada, light blue ce shaddar ba ƙaramin kyau yayi ba cikin shigar tashi,sai ƙamshi yake bugawa. Lokacin kusan duk an tafi gurin dinner sai motar su mommy da Kuma tasu Aslam. Yana zaune cikin mota duk ransa ya gama ɓaci, dan bai so zuwa ba,gani yake wannan duk ɓata lokacine,sai tsaki yake bugawa ganin har yanzu Islam bata fito ba. Waya ya dauko tare da kiran mommy,tana dagawa yace cikin damuwa"mommy nifa wllh na gaji da zama cikin mota,zan koma daki nayi kwanciyata idan bazata fito ba"ya karasa cikin ɓacin rai. "A'a wai kana nufin Islam bata fito ba?bari naje na gani,tun ɗazu na tura mai kwalli ta shirya ta "mommy dake ƙoƙarin fitowa daga falon ta faɗa tare da nufar ɗakin granny. Zaune ta tarar da Islam daga ita sai towel,alamun fitowar kenan daga wanka. Ga mai kwalliya zaune tana jiran ta. Cikin zaro ido mommy tace "Islam me zan gani haka?wai ko shiryawa bakiyi ba?kowa ya tafi saura ku,maza tashi kisa kayan ki inyaso ayi kwalliyar"mommy ta faɗa tana ware rigar Islam irin ta jannat dake ajiye kan gado. Turo baki Islam tayi tana faɗin. "Ni wllh mommy ba son zuwa nake ba,da kin barni kawai" Banza mommy tayi da ita ta fara sanya mata rigar. Cikin hanzari aka gama shirya Islam,wanda ko wajen kwalliya saida mommy ta dage mata kafin ta bari akayi mata. Masha Allah masu karatu, kuzo kuga Islam,bazaku taɓa gane ta ba , saboda yadda tayi wani mafifafen kyau kamar yar aljanu. Mommy da kanta saida tayi ta mata addu'a tana tofa mata saboda baki. Kamo hannunta tayi suka fito farfajiyar gidan,inda Aslam ya kame cikin mota sai kumbura yake kamar zai fashe. Sakin baki da hanci da idanu Aslam yayi yana kallon mommy da Islam,sakamakon wani sihirtaccen kyau daya ga Islam tayi,badan kar ace ya ƙyasa ba, sai yace bai taba ganin wacce kwalliyar amarci tayi mata kyau kamar Islam ba. "Masha Allah"itace kalmar Da fito daga bakin Aslam Yana mai kafe Islam da ido. Har suka ƙaraso bakin motar bai fargaba,saida mommy ta kwankwasa kofar kafin ya farga, Cikin dakiya yayi saurin saita kansa yana mai haɗe rai,ya buɗe kofar motar tareda kawar da kansa daga kallon inda Islam take. Shigar da ita motar mommy tayi,kafin ta nufi tasu motar. Wani ƙamshi ne mai daɗin gaske ya daki hancin Aslam Wanda saida ya lumshe idonsa yana sauke ajiyar zuciya. Har suka fara tafiya ba wanda yayi magana cikin su.Sai turo baki Islam keyi,aganin ta an takura mata ne kawai. Tsaki tayi mai ɗan sauti tana janye mayafin da aka rufe mata ido dashi. "Ina dalili za'a wani rufemin ido kamar wata dodo wllh budewa zanyi,ji yadda idona yayi min nauyi kamar andoramin dutse "ta faɗa tana ɗan tabo gashin idon da akayi mata ado dashi. Juyowa Aslam yayi ya kalle ta,duk da yadda ya yaba da kwalliyar Tata azuciyarsa,amma azahiri sai ya wani taɓe baki,tare da cewa"karki ƙaramin tsaki cikin mota,wani ya tilasta ki yin kwalliyar?dalla dubeki kamar wata aljana"ya fada yana tabe baki. Aikuwa cike da jin haushi Islam ta zare mayafin gaba ɗaya tare da juyowa tana kallon Aslam ,cikin masifa tace..... Hmmmmm malama Islam ta malam Aslam manya . Muje zuwa . Mrs babi ce. Anty mammy. [10/10/2022, 4:17 PM] Abk: ____________Cike da jin haushi Islam ta yaye mayafin gaba ɗaya,tare da mayar dashi bayan ta,kallon Aslam tayi kafin cikin masifa tace "oho maka dai,dama bance kaga kyau na ba,dan wllh badan kai nayi kwalliyar nan ba,mommy ce ta takura sai anyi min,kuma kaine kayi kama da aljanu,amma nikam nasan kwalliya ta tayi kyau,sai dai maƙiya ne zasu kushe" ta kai ƙarshen zancen ta cikin jin haushi tana hararar Aslam. Kallon ta kawai yake,yadda ɗan karamin bakin ta ke motsi kamar gidan tsutsa,shi mamakin masifar Islam yake,sam bata barin ta kwana idan ka taɓota.ahaka idan ka kalle ta,zakayi tunanin irin masu haƙurin nan ne,sai wani abu ya haɗoku zaka gane masifaffiya ce. "To iya bala'i karki cinyeni da wannan ƙaton bakin naki, dama ga haƙoran ki nan yalo shar dasu baki wanke su da gani zasuyi dafi"Aslam ya fada cikin salon neman magana. Buɗe baki Islam tayi cike da baƙin ciki tana kallon Aslam,wai itace mai ƙaton baki?kuma haƙorin ta yalo Bata wanke wa?lallai Aslam ya iya wulaƙanci. Cikin muryar mai cike jin haushi kamar zatayi kuka tace "wllh bakina ba ƙato bane dan abubuwa da yawa ma bana iya sanya su cikin bakina,saidai naka ne ƙato,kuma Ni haƙorana farare ne kaine mai yalon haƙori amma bani ba"ta faɗa cikin wata murya mai kama da tana shagwaba. Kafeta Aslam yayi da idonsa,dan sosai yanayin yadda tayi maganar ya ratsa zuciyar sa.sai yaga ta ƙara masa kyau a idonsa. Baice mata komai ba, kawai ya zuba mata ido. Ita kuwa murguda baki tayi tare da juyar da kanta tana kallon windown motar. Shima jingina yayi da jikin kujerar yana mai sauke ajiyar zuciya. Haka suka ci gaba da tafiya cikin motar ba wanda ya ƙara magana har suka isa gurin dinner. Guri ne daya amsa sunan sa,haɗaɗɗen guri,na manyan mutane,wanda aka ƙawata shi da kayan ado,gurin har ya gaji da haduwa,banda kida ba abinda da ke tashi agurin.kowa ya hallara su kadai ake jira, dan su jannat ma suna wajen gurin basu shiga ba. Motar tana tsayawa Islam ta ja wani dogon tsaki tana faɗin "dan Allah ji yadda ake ta ihu agurin nan,wllh nikam kamar na koma"ta faɗa tana hararar gurin . Shi kansa Aslam ji yayi kansa harya fara masa ciwo,hayaniyar gurin tayi yawa. Kallonta yayi yace "saiki maida mayafin naki mushiga ai,nima ba son wannan hayaniyar nake ba"ya fada yana kallonta. "To tunda haka ne kawai mu koma gida mana,kaga duk Bama son zuwa aka takura mu"Islam ta faɗa itama tana kallon sa. "Mu koma gida muyi me? Bayan kowa ya taho nan?"ya fada idonsa akanta. "Abinda ake yi mana agida,ai ba sai kowa yana nan zamu koma ba"ta faɗa tana ɗan harararsa. Ajiyar zuciya yayi tare da cewa"ok na gano ki,wato jarabar ki ce ta motsa,shine kike son ki maidani gida,dan nayi miki abinda nayi miki ɗazu ko?to wllh Ni bazan koma ba,na gaji gara ki rage wannan jarabar taki"Aslam ya fada yana wani kama kansa irin da gaske yake ɗin nan. Zaro manyan idonta da suka sha makeup Islam tayi, tana mai dafe ƙirji. "Ni yaushe nace maka abinda kayi min dazu nake so mukoma gida kamin?"ta faɗa kamar zatayi kuka. Murmushin gefen baki Aslam Yayi ganin lokaci ɗaya ta wani tsorata,kafin yace "ai ba saikin faɗa ba,nida kaina na gano ki,wannan inaga idan mun koma part ɗin mu,wataran sai kin tsotsemin ruwan jikina tasss! zaki barni"Aslam ya fada yana harararta. Tsabar bakin ciki da jin haushi kawai Islam ta kama jefa masa kayan adon nata,mayafine,jaka ce, dan shi kansa dan kwalin da aka sanya mata akanta irin ta amaren nan,tsigewa tayi tana jefa masa tare da bubbuga ƙafar ta tana cewa"wllh sharri kake min,Ni bana son wannan abun da kake min,tunda Ni ba yar iska bace,kuma saida na faɗawa mommy tace zata hukunta ka,Allah ya kiyaye ince ka taɓani"dariya sosai ta kama Aslam,ganin yadda amarya ke watsi da kayan da aka mata adon dinner dashi,sannan wai ta gayawa mommy abinda ya faru dazulallai akwai yarinya tare da islam.kawai ya sanya dariya yana nuna ta.hakan ba karamin batawa Islam rai ya karayiba.dan haka ta fara kai masa duka tana kukan da ba hawaye. Ganin da gaske so take ta bata kwalliyar yasa Aslam saurin riƙe hannayenta duka biyun,amma bata daina kokawar kwacewa ba. Janyota kawai yayi ya haɗata da jikin sa ya rungume.haka kawai yake jin farin ciki da nishaɗi yau ɗin nan. Ɗif!! Kakeji,Islam ta daina haure hauren nan,sai ma wani runtse ido da tayi da sauri kamar yadda Aslam ma ya runtse nashi idon. Lubb ta kwanta kan faffaɗan ƙirjinsa tana mai shaƙar kamshinsa. Shikuma ba tare da ya sani ba ya sanya hannunsa yana shafa gashin kanta,wanda yasha gyara sai sheƙi da ƙamshi yake. Kusan minti uku zuwa hudu suna cikin wannan yanayin, kafin Aslma ya ɗago kan Islam,har lokacin idanunta arufe suke.tsura mata ido yayi yana kallon kyakykyawar fuskarta,cikin ƙanƙanin lokaci yaji yana son kissing lips ɗin ta daya sha pink and maroon ɗin janbaki sai sheƙi yake. Ahankali ya kai bakinsa kan nata ya fara kissing ɗin ta cikin kwarewa da burgewa. Awannan lokacin Islam ji tayi itama tana bukatar abinda yake matan,hakan yayi tasirin hanata kwatar kanta gareshi,sai ma gara ƙanƙame shi da takeyi.gaba ɗaya sunyi nisan cikin kogin shaukin abinda suke yi,hakan yasa suka manta cewar jiransu ake.dama wanda ya kawo su tuni ya fice. Saida Hanan dake kusa da motar su jannat ta zo ta kwankwasa glass ɗin motar kafin gaba ɗaya suka dawo cikin hayyacinsu. Da sauri Islam ta saki rigar Aslam dake riƙe cikin hannunta,tare da tashi daga jikinsa,gabanta sai bugawa yake,kunya taji ta kamata sosai, tayi saurin sunkuyar da kanta ƙasa. Aslam kuwa ji yayi kamar ya kurma ihu,dan baiso aka katse masa jin daɗi ba,lumshe ido yayi tare da jingina da jikin kujera,gaba ɗaya ji yayi jikinsa ba kwari, Saida aka ƙara kwankwasa motar kafin ya sauke glass ɗin. Harara ya ballawa Hanan cike da jin haushin ta kafin yace "meye "cikin tsawa. Cike da tsoro hanan tace "yaya wai ku ake jira tun dazu"ta faɗa muryarta na rawa. Tsaki ya ja tare da rufe glass ɗin motar. Kallon Islam yayi da ke ta kokarin maida Dan kwalinta,sai kici kici take,gaba ɗaya ta daburce. Hannu yasa ya karɓi dan kwalin ya taimaka mata ta sanya.sannan ya dauko mayafin ya yafa mata shima. Miƙa mata jakarta yayi.kafin ya fito daga motar,zagayowa yayi ya buɗe inda take zaune ya kamo hannunta. suka shiga cikin hall ɗin, wanda dama su jannat suna waje suna jiran su Aslam Dan su shiga tare. Suna shiga gurin ya ɗau ihu da tafi,dan ba ƙaramin kyau sukayi ba. Anyi dinner sosai mai kayatarwa agurin,wanda anjima ba'ayin irin ta ba,sosai suka sha hotuna da kyaututtuka, haka aka gama aka tashi lafiya cike da nishaɗi suka dawo gida. Tun acikin motar Islam ta cire wannan daurin da akayi mata.dasu gashin da aka sanya mata a ido.sai tsaki take tana ita ta gaji wllh bazata ƙara zuwa ko ina ba. Shidai Aslam baice mata ƙala ba,yana zaune can ƙarshen kujera,In banda ciwo ba abinda kansa keyi.dan haka suna isowa ko ta kanta bai bi ba yayi part ɗinsu Dan wanka yake don yi.itama haka ta rike ɗan kwali da gyale ahannu tayi dakin granny. Washe gari mother's day akayi,dan haka cikin gidan aka tara mata,wanda anan aka yiwa amare wa'azi sosai,wanda ya kashewa kowa jiki. Jikin Islam yayi sanyi matuka,duk da tasan cewa Aslam mijin tane ahalin yanzu,amma ita anata tunanin bai kamata koda hannun ta ya taɓaba,tunda ba auren soyayya sukayi ba.amma yanzu jin irin hakkin da miji ke dashi akan matar sa yayi mugu karyawa Islam gwuiwa.haka dai taro ya tashi lafiya,bayan anci ansha. Can kuwa gidan Alhaji isma'il,baban Maryam,idan mai karatu bai manta ba,itace yarinyar da Aslam ya kira lokacin da yazo Nigeria suka haɗu cikin mota suka gama romancing ɗin su ya korata gida,ƴace ga babban aminin daddy Wanda suke komai tare dashi,ita kadaice yarsu,suna matukar ji da ita,ita kuma aduniya ba wanda take so kamar Aslam,shi take son aura. To yanzu ma tana zaune tsakiyar iyayen ta tana kuka harda shashsheƙa,akan ita Aslam take so kuma shi take burin aura. Hankalin iyayyen ta yayi mugun tashi,suna ta rarrashinta akan tayi haƙuri,zata auri Aslam da yardar Allah. Da gyar dai suka samu tayi shiru akan ta basu nan da yan watanni zasu san abin yi. Wannan kenan. Da dare akai jannat gidan mijin ta,tana ta kuka, haka ma mommy da granny ,Suna ta kukan rabuwa da Jannat,lokacin Islam tana ma barci abinta. Haka dai baki sukayi ta tafiya ɗaya bayan ɗaya,inda ya rage daga su sai su. Islam ma aranar aka kaita nata dakin,Wanda mommy ce da granny suka raka ta.ko ajikinta ba wani irin kukan nan na amare.saidai can cikin zuciyar ta take jin kewar iyayen ta da son ganin su. Aslam Yana zaune afalo yagansu, sun shigo.hadasu mommy tayi tare da yi musu nasiha sosai mai ratsa zuciya.haka ma granny,kafin suka barsu suka koma nasu part ɗin. Suna nan zaune shiru Islam yau ji tayi kwata kwata bata da ra'ayin kula Aslam,bare suyi faɗa,hasali ma ita barci take ji,dan haka tashi tayi ta nufi dakin da Aslam din yake ciki tayi kwanciyar ta.ba jimawa barci yayi gaba da ita. Shikuwa zama yayi yaci gaba da aikinsa a laptop.har kusan sha ɗaya,kafin ya tashi shima, kashe komai yayi daya danganci wuta kafin ya shige dakin shima. Tana kwance tayi daidai abinta akan gado,barci take hankali kwance ba abinda ke damunta. Lallai yarinyar nan,wato da gaske take anan ɗakin zata ringa kwana kenan?aikuwa bata isaba ,dole gobe ta koma wancan dakin,dan bazan iya zama da ita daki daya ba,za'a iya samun matsala. Fillow ya dauko ya jefar akan kafet ya kwanta. Saidai cikin dare ya kasa barci saboda sanyi,dan haka cikin barci ya tashi ya haye kan gadon,Islam ma sanyin take ji,dan ta duƙunkune jikinta guri ɗaya,hakan yasa tana jin alamun mutum kusa da ita ta matsa jikinsa,shima jinta ajikinsa sai ya ƙara janyota ya rungume sosai sukaci gaba da barcinsu, rungume da juna... To amare asha barci lafiya. Mrs babi ce Anty mammy. [10/11/2022, 7:20 PM] Abk: __________Barci suka ci gaba dayi rungume da juna,gaba ɗaya Islam ta wani haye kan faffaɗan kirjin Aslam,shi kuma ya zagaye ta da hannayen sa duka biyun,ahaka suke barcin. Koda asuba tayi Aslam shine wanda ya fara farkawa daga barcin,ahankali yake buɗe idonsa tare da karanto addu'ar tashi daga barci(Alhamdullahillazi ahyana ba'ada ma amatana wa'ilaikannushur).yunkurin tashi ya farayi,saidai kuma ji yayi kamar yana riƙe da wani abu,dan haka ya kai kallonsa saitin ƙirjinsa, saidai duhun da ke cikin dakin bai bashi damar ganin Islam clearly ba,hakan ya sashi fara shafa ta da hannayensa,tun daga kanta ya fara shafawa har zuwa gadon bayanta,dogon gashin ta ya fara cin karo dashi,kafin ya zarce da hannayen sa zuwa manyan mazaunan ta,sosai gabansa ya buga lokacin da hannayen sa suka sauka akan mazaunan Islam masu tsananin laushi da girma kamar biredi. Da sauri ya janye hannun sa daga kai,dan zuwa yanzu kam ya gama gane cewar Islam ce kwance,to amma yaushe ta dawo nan kusa dashi?yaushe sukayi wannan kwanciyar haka?sam ya kasa gano lokacin da suka dawo guri ɗaya, Ahankali ya ƙara daga hannunsa ya maida kan mazaunan Islam,dan ji yayi zuciyarsa na muradin kara tabasu, wata ajiyar zuciya mai ƙarfi ya sauke lokacin da hannun nasa suka ƙara sauka kan mazaunan nata,ahankali yake yawo da hannunsa daga bayanta zuwa mazaunan ta,yana sauke wani nishi da sauri da sauri, idanunsa alumshe.yana mamaki da ayyana laushi irin na wannan gurin. Tun da yake bai taba jin lallausan mazaunai kamar na Islam ba,hannu bibbiyu yake shafa su tare da murzawa,wani irin daɗin hakan yake ji cikin rai da zuciyarsa,har ma ya manta cewar ako wane lokaci Islam na iya tashi. Ita kuwa Islam barcin ta take tana kara wani shigewa jikin Aslam,Dan zuwa wannan lokacin gaba dayan jikinta yake shafawa idonsa a lumshe ya na sauke numfashi mai dan sauti.dama ga sanyin asuba ga kuma yanayin da yake ciki hakan ya kara masa kaimi sosai wajen wasa da jikin Islam. Can cikin barci Islam ke jin ana shafa mata jiki, sannan ga wani abu daya tokare mata ciki kamar katako saidai kuma tana jin wani irin daɗi marar misaltuwa,ahankali take wani mikewa tana kara shigewa Alsam,duk atunanin ta mafarki take.saida taji abin dai gaba yake, dan Aslam ya fara rasa nutsuwarsa,sannan ta buɗe idonta ahankali,tayi tsumm !!da ranta.tabbas ba barci take ba,abinda take ji da gaske yake faruwa, saidai yanayin yadda Aslam ke wasa da sassan jikinta sai yayi tasirin hana ta motsawa,sai ma wani lumshe ido da takeyi. Birkitota Aslam yayi ta koma ƙasa shi yana samanta,cikin ɗan ruɗewa ya lalumo bakinta ya haɗe da nashi, kissing din ta yake cikin zaƙuwa kamar zai cinye mata bakin.yayin da hannayen sa ke kan na shanunta yana wasa dasu. Gaba ɗaya Islam tayi nisan kiwo,dan sosai take jin daɗin abinda Aslam ke mata,sai wani banƙaro masa kirji take tana riƙe da damtsen hannun sa. Kusan minti biyar zuwa bakwai suna cikin wannan yanayin,Aslam yayi nisa baya jin kira,burinsa kawai ya samu abinda yake bukata. Dai-dai lokacin ne kuma Islam ta dawo hayyacin ta,ai cikin sauri da hanzari ta ture Aslam,can gefe guda,itama ta koma can karshen gado,tana faɗin. "Na shiga uku,Aslam meye hakan?nifa na faɗa maka bana son wannan abun da kake min"ta faɗa cikin rawar murya tana jan bargo. Aslam kuwa tana tureshi can gefe guda shima ya dawo hayyacinsa,sai dai halin da yake ciki ahalin yanzu yana bukatar taimako,na kulawar ta,amma ta yaya?yasan koda zai mutu Islam bazata amince dashi ba,amma koba komai ma dazata taimaka masa koda rage zafi ta barshi yayi,saidai yasan idan ya nemi hakan raini ne zai ƙara shiga tsakaninsu.dan haka cikin haki da rawar jiki ya jingina kansa da bango yana sauke nishi kamar dan dambe. Shi wllh dama yasan kawai ankawo yarinyar nan ne dan tayi ta sashi cikin mawuyacin hali,kuma ba wani abu dazata iya masa.yanzu dan Allah dubi yadda ta biyoshi har shimfiɗar sa ta tada masa hankali, kuma tana tuhumar sa?muguwa kawai. Islam kuwa cikin tsiwa tace "wllh Ni bana son jaraba ,haka kawai ina barcina kazo ka kama tabamin jiki wannan ai satar hanya ce,saboda kasan idan idona biyu bazan yarda ba shine ɗan kawai jaraba na cinka ka biyoni har kan gado kana min wannan iskancin,wllh bazan dauka ba"Islam ta faɗa cike da tsiwa tana murguda masa baki. Cikin ƙufula da jin haushin halin da tasashi ya shiga Aslam ya zaburo cikin faɗa yana cewa"dalla Malama kimin shiru,uban waye ya biyo wani tsakanin Ni dake?inace bar miki gadon nayi na koma ƙasa?amma daga karshe akan kirjina na tsinceki kina barci.anfaɗa miki Ni dutsene da bazan shiga wani halin ba?wllh yau zaki barmin daki ki koma can,dan bazaki zo ki kashe Ni ba"Aslam ya fada cike da jin haushin Islam,shi fa duk atunaninsa Islam ce ta biyoshi ƙasan dayake kwance. "Lallai wato ma nice na biyoka inda kake kwance ko?nida kai waye ya fara kwanciya akan gadon?saika buɗe idonka kaga a inda kake kwance,kai dai kawai ka biyoni kan gado kana son amfana da jikina,shine zaka kama borin kunya,kuma nikam bazan taɓa amincewa da kai ba ehe"cewar Islam itama cikeda jin haushi. Cikin hanzari Aslam ya kunna hasken dakin,mamaki ne sosai ya kamashi,ganin da gaske akan gadon yake,to yaushe ya dawo kan gadon?ko dai aljanu ne suka dawo dashi?shidai iya sanin sa bai dawo kan gadon nan da kansa ba. Da sauri ya juyo yana kallon Islam,wacce take kallonsa cikin yanayi na harara. "Yaushe na dawo kan gadon nan?ko dai kece kika dawo dani?saboda kina son na taba miki jiki kiji daɗi,Ni kuma ki barni cikin azaba ko? muguwa kawai" Ya fada yana sauka daga kan gadon cike da ɗan jin kunya,dan ya fahimci tabbas shi da kansa ya dawo kan gadon.kai tsaye toilet ya shige yayi wanka cikin sauri dan tuni gari ya fara haske,anan cikin dakin ya shimfida sallaya ya tada sallah. Tashi Islam tayi itama tana turo baki ta nufi toilet tana faɗin "haka kawai mutum yana zamansa anzo za'a takurawa rayuwarsa da wani taɓe taɓen jiki"ta faɗa tana shigewa toilet.yana jinta dan da ƙarfi ta fadi hakan. Alwala ta dauro tare da fito ta zari yafi zatayi salla. Cikin tsawa Aslam yace"ke!!!ahaka zakiyi sallar?saboda ke wawiyace ?" Harara ta balla masa kafin tace"to ayaya kake so nayi?"ta faɗa tana watsa hannu. "Bayan kin gama lallatseni kinji dadi kuma saikiyi salla ba tare da kinyi wanka ba?saboda ke kikafi kowa ko?"ya fada yana hararar ta. Turo baki tayi kafin tace"Allah ya kiyaye,Ni ba wani daɗin dana ji bare nayi wanka,kai dai dakajin ai kayi "ta faɗa tana turo baki. "Ai Ni lafiyayye ne shiyasa idan ma naji daɗin,amma ke da yake dutse ce shiyasa baki jiba, saidai ƙoƙarin turomin wannan manyan breast ɗin naki da kike da sunan in taɓa miki su"Aslam ya fada idonsa akan Islam. Buɗe baki Islam tayi da zaro ido, kafin tace"yaushe na turo maka ka tabamin?wllh kaji tsoron Allah,Ni ina ruwana da wannan abun da zan wani ce ka tabamin,kuma wllh niba dutse bace,kamar yadda kake lafiyayye nima haka nake"ta faɗa tana juya ido tare da murguda baki. Kallonta Aslam Yayi cike da jinjinawa ƙuruciya irin ta Islam,kafin yace "oho dai koma menene wllh saikinyi wankan tsarki kafin kiyi salla,ɗan karya kike kice min ba abinda kikaji,yadda kike ta min shishitu da nishi kuma kice bazakiyi wanka ba"ya fada yana mai tsare Islam da ido. Ƙara turo baki Islam tayi,kafin ta jefar da mayafin ta nufi toilet,Dan kuwa gaskiyar Aslam ne lokacin da taje yin alwalar pant dinta sai floshing ɗin sa tayi,saboda yadda ya jike,sai abin ya bata tsantsani. Wankan tayi tana ta mita kafin ta dauro towel ɗin Aslam,ƙato ta fito. Koda ta fito bata sameshi adakin ba,dan haka doguwar jallabiyar alama ta sa, sallar tayi kafin ta ɗan shafa mai da turare,sannan ta ta cire rigar ta maida towel ɗin,komawa kan gadon tayi tare da kwanciyar ta. Aslam kuwa bayan ya idar da sallar,motsa jiki ya fita,daga nan ya wuce part din mommy Dan ya gaisa da su. Sai wajen bakwai ya dawo part din nasu,kwance ya ganta akan gado tana barci,tsabar tsiya irin ta Islam daga ita sai wannan towel ɗin ta kwanta,gashi duk ya tattare ya koma cinyar ta.kawar da kansa yayi tare da shigewa toilet ,wanka yayi sannan ya fito,bargo ya ja ya lulluɓe jikin Islam dashi yana hararar ta,dan idan yana ganin ta ahaka ,bazai iya komai ba,gani yake da gangan take wasu abubuwan ma. Haka dai ya shirya cikin sauri ya fito falo,nan ya samu an kawo musu abinci,dan haka ya zauna yaci ya koshi,sannan ya ɗan kishin gida akan kujera,nan da nan shima barci yayi gaba dashi. "Mommy please kuyi wani abu da wuri,wllh zuciya gab take da tarwatsewa,ina son Aslam,Ina ƙaunar sa kuma kunfi kowa sanin haka,amma kuka ƙiyin wani abu har saida ya auri wata, wllh mommy komai na iya faruwa dani idan aka kara daukan lokaci ban mallaki Aslam ba"husna ke wannan maganar cikin zubda hawaye,sam ta kasa samun nutsuwa tun lokacin da batun auren Aslam ya zo gareta,dan taci burin auren Aslam,kuma ta sanar da Daddyn ta shi take son aure,sannan yayi mata alƙawarin yin magana da Daddyn Aslam ɗin akan batun auren nasu.kawai kuma sai jin daurin auren sa tayi. Cikin sigar rarrashi,mahaifiyar Tata ke share mata hawayen,kafin tace"husna nasha faɗa miki ki daina damun kanki akan batun Aslam,aurene kamar kin aureshi kin gama,koda baya so,akwai Abinda nake jira ne,kawai ki zubamin ido,nayi miki alƙawarin ba abinda zaki nema cikin duniyar nan ki rasa"mommyn Husna ta fada cike da yaƙini. Rungume mommyn nata Husna tayi cikin darinyar kuka tace "na sani mommy na,nasan Indai kina duniya bani ba shan wuya,mommy ki haɗashi da bokan ki,ta yadda zai ji ba wacce yake so aduniya sai ni"Husna ta fada cikin ɗoki. "Ki sa aranki,sai Aslam ya soki kamar ransa,ke dai abinda nake so dake ki daina sa damuwa cikin ranki,ki kwantar da hankalin ki kawai"cewar mommyn nata. "To mommyna"Husna ta fada cikin farin ciki dan tasan mommyn nata sarai. Koda dare yayi Aslam,kin shiga ɗakin yayi,ya tafi can ɗayan dakin ya kwanta,saidai sam barci ya gagareshi, haka yayi ta juyi akan gado,ƙarshe dai ba yadda ya iya dole ya dawo dakin da Islam ke kwance haka ya haye kan gadon ya juya mata baya. Kusan minti ashirin da kwanciyar sa amma ya kasa barcin,sai tsaki yake ,dan ji yayi idan bai rungumi Islam ba bazai iya barcin ba.cikin haka ne kuma Islam tayi juyi tare da rungumeshi ta baya. Wani ɗan zabura yayi dan bai zata ba kawai yaji ta rungumeshi. Sai kuma ya sauke ajiyar zuciya tare da juyowa ahankali ya janyota kan ƙirjinsa sannan ya sauke ajiyar zuciya yana jin kamar wanda aka cire masa damuwa.hannunsa akan mazaunan ta yana shafawa haka barci yayi gaba dashi. Asuba nayi kuwa yayi saurin tashi ya bar ɗakin, dan kar Islam ta kamashi. Karfe bakwai Islam ta gama shirin ta na zuwa makaranta,fes da ita sai ƙamshi take.ta fito zuwa falon nasu,inda Aslam ke cin abinci.zama tayi tare da sanya hannu ta ɗauke tea ɗin daya ke sha ta fara kurba,Binta yayi da ido yana kallonta,baice mata kala ba,dan yasan neman magana take.wani kofin ya ɗauka ya haɗa wani tea ɗin ya fara sha. Har suka gama karyawa ba wanda ya kula wani cikinsu. Shiya fara mikewa yace "kiyi sauri ki gama ina jiran ki amota"yana faɗin haka yayi waje. Hararar bayansa tayi tana mai faɗin"ji yadda yake magana kamar wani boss,waishi adole irin mijina ɗin nan ko?hmmm zakayi bayani ne yaro"ta faɗa tana ajiye kofin hannunta.nan gurin ta bar kayan da sukaci abincin tayi ficewar ta.saida taje lambu taga janbu,dan akwai kofar da zata kaika lambu ta cikin part ɗin nasu.farfajiyar gidan ta fito bayan ta je gurin su mommy . Yana cikin mota azaune fuskarsa aɗaure sai tsuka yake,dan ya gaji da jiran ta. Cikin takun ta mai daukar hankali ta nufi motar tashi.tana zuwa ta bude gidan baya ta zauna.kamar wata Hajiya. Haushi ne ya ƙara kama Aslam,yace "dalla malama fito ki dawo gaba,koni drivern ki ne?ya fada ahasale. Cikin gadara Islam ta ce"kaga malam,karka min ihu ai ban tilasta ka saika kaini makaranta ba,kai ka gadama,dan haka saika zubamin ido kawai,Ni anan nayi niyar zama "ta faɗa tana wani fari da ido. Afusace Aslam ya buɗe motar tare da fitowa.inda take ya zagayo ya buɗe,fincikota yayi da ƙarfi ya fito da ita ya bude gaban motar sa ya jefata tareda ƙullewa. Da ƙarfi yana motar yana huci. "Wllh idan ka karya min hannu ba yarda zanyi ba saina rama"Islam ta faɗa cikin raunin murya kamar zatayi kuka. Banza yayi da ita har suka isa makarantar . "Fita"ya fada akausashe. Banza tayi dashi kamar bata jiba,kuma taki fita. Kallonta yayi ya kara maimaitawa "fita nace"nan ma tayi masa shiru tana turo baki. Yasan halin Islam sarai,idan baiyi mata da gaske ba saita ɓata masa lokaci,kuma akwai inda zashi. "Wllh idan baki ficemin daga mota ba,zanyi maganin ki nasan abinda kike so,saboda jiya banzo nayi miki ba ko?"ya fada yana ɗan buɗe idonsa. Sam Islam bata gane manufar sa ba,dan haka cikin tsiwa tace "tunda ka gane abinda nake so,ai saikayi min,amma wllh kasan nima ba gyale ka zanyi ba,dan ban..... ina kafin ta ƙara sa kawai taji Aslam ya janyota jikinsa tare da manna bakinsa kan nata. Zaro ido Islam tayi waje,dan sai yanzu ta fahimci abinda yake nufi,cikin sauri take ƙoƙarin tureshi amma ta kasa, kissing dinta kawai yake cikin kwanciyar hankali,nan da nan jikin Islam ya kama rawa,ta kasa koda motsi,sai lumshe ido da tayi tana karbar sakon Aslam,saida yayi mai isar sa kafin yayi ta maza ya zare bakinta daga nata,gaba ɗaya baya sukayi tare da jingina da jikin kujera idanunsu alumshe. Ahankali Aslam ya buɗe idonsa tare da kura mata ido,sosai tayi masu akyau,lips ɗin ta sai sheƙi yake. "Ya ?hakan yayi miki ko kina buƙatar kari ne?"Aslam ya fada cikin ƙaramar murya dai-dai saitin kunne islam. Wani yummmmm Islam taji tsikar jikinta ta zuba,da sauri tayi baya,tare da buɗe motar asukwane tayi waje.bayan ta zari jakarta,da sauri tayi cikin dalibai bata ko waiwaye. Murmushi Aslam Yayi tare da ƙureta da ido,har ta bacewa ganin sa. Haka kawai yake jinsa cikin wani irin farin ciki marar misaltuwa. Cike da kasala yana motar sa ya bar makarantar. Muje zuwa.[10/12/2022, 1:21 PM] Abk: ____________Murmushi Aslam Yayi tare da ƙureta da ido,har ta bacewa ganin sa. Haka kawai yau yake jinsa cikin farin ciki marar misaltuwa.kunna motar yayi cike da kasala, tare da barin harabar makarantar. islam kuwa kai tsaye ta wuce gurin assembly,bayan an kammala komai aka fara shiga aji,ita kuwa kai tsaye ta wuce ɓangaren yan primary dan duba A'isha.cikin class ta Sami yarinyar ana musu karatu,dan haka daga waje ta tsaya tare da daga mata hannu,dan A'isha kusa da kofa take zaune,cikin farin ciki yarinyar itama ta dagawa Islam hannu tana dariya. Alamu Islam tayi mata na tayi karatu sosai zata dawo anjima kafin tayi mata bye bye ta juya bangarensu. Tana shiga class ɗin wata ƙawar hanan mai suna maryam,ta buga uban tsaki tana mai faɗin"haka kawai mutum ba dan kowa ba sai faɗin rai,wllh mukam ba'a isa anuna mana jiji da kai ba,dan munsan komai"ta faɗa cikin daga murya tana kallon islam.haka take mata kullum,burinta kawai Islam ta kulata dan haushin Islam take ji,saboda tafisu ƙoƙari. Islam kuwa, bata kula kowa cikin ajin nan,dan gaba dayansu taga masu rainin hankali ne,gasu da son dizga mutum,ita kuma bazata dauki rainin hankali ba,yanzu zata balla yarinya ba ruwanta.dan haka duk da taji abinda Maryam ta faɗa sai tayi kamar bata jiba,ta nemi guri tayi zaman ta. Dariya suka kwashe da ita wata daga cikinsu tace "kai Maryam,ke matsala ta dake tsoro ne dake,inba haka ba kifito fili ki fada mana da wa kike " Cikin isa da gadarar rashin kunya Maryam tace "wa zanji tsoron?yar riko agidan mutanen ? Allah ya kiyaye,to bari kiji da waccan Islam ɗin nake saime?"ta faɗa tana nuna islam. Runtse ido Islam tayi cike da jin wani irin zafi cikin zuciyarta.lallai yau zata koyawa yarinyar can hankali,zata san wacece Islam,ba tsoron su take ji ba. "Hahhhhh lallai Maryam kin cika wallahi,ai nayi tunanin tsoron faɗin suna kike"yarinyar dazu ta faɗa. "Ai kinsan ni Maryam bana jin tsoron ko wanne shege makarantar nan,wllh idan mutum yayi min wani gani_gani yanzu zansa ayiwa yarinya tsirara atiti kuma wl...... Kau !kau!!kau!!! Kake jin ƙarar saukar maruka akan kumatun maryam,wanda ya dauke mata ji da gani na wasu ƴan daƙiƙai. Ihu ta kwalla da ƙarfi tana dafe duka kumatun ta "wayyo na shiga uku an watsamin acid akumatuna,na shiga ukuna Ni Maryam, wayyo Allah na"abinda Maryam ke faɗi kenan cikin ihu da razana,dan marin a bazata yazo mata. Cakumo wuyan rigarta Islam tayi tare da kwara kanta da bango nan take jini ya fara zuba daga hancin maryam.islam ta shaƙar mata wuya,cikin muryar gargadi ta fara magana"dan ubanki Ni ba sa'ar yinki bace,nafi ƙarfin ƙaramar tsagera irin ki,sai manyan kwari,kada tsautsayi yasa kice zaki shiga gonar Islam,zaki sha wahala matuka arayuwarki,banza shashasha mai siffar karuwai"cewar Islam tana hankada Maryam, Cikin masifa wannan ɗayar yarinyar ta taso tana mai cewa islam"ke Islam meye hakan?ko kasheta kike sonyi ne?dallah malama kauce kiba mutane guri" Ai afusace Islam tayi kan yarinyar nan tana duka ta ko ina.duk yadda a kaso rabasu, sam Islam taki yarda sai dukan yarinyar take kamar ta sami jaka. Ajin ya cika danƙam da yan kallo,wasu suna jin daɗin dukan da Islam tayiwa su Maryam,dan sun addabesu dama cikin school ɗin,wasu kuma suna jin haushin Islam ɗin. Saida principal yazo da sauran malamai kafin aka iya raba faɗann nan.shima da gyar Islam ta saki yarinyar,gaba ɗaya ta fasa mata baki da hanci,Maryam kuwa dama tuni jini ke zuba daga bakinta da hancinta. Kai tsaye principal yace su biyoshi office. Koda sukaje office faɗa sosai principal Yayi musu, kafin ya koma kan Islam yayi ta zaginta,sannan yace sajant yayi mata bulala ashirin masu zafi. Haka sajant ɗin nan ya kama dukan Islam,cike da mugunta,dan dama yana fatan Allah ya kawo su wannan ranar yana matuƙar jin haushin Islam. Gaba daya hannun Islam da bayanta ya kumbura,bayanta yayi raɗo-raɗo da shatin bulala,hannunta kuwa wani gurin ma ya fashe.sannan principal ya sata share wani guri mai girma,da gyar take iya daga tsintsiyar saboda yadda hannunta ke mata ciwo.tana gama sharar ta dawo,nan ma saida suka gama ci mata mutunci sannan aka sallame ta,tsabar takaici da ciwon rai,na rashin adalci da aka mata,bata san sanda hawaye ya fara zubo mata ba,can bayan class ta koma tana kuka sosai.tana cikin wannan kukan yaji an dafa kanta.da sauri ta juya ɗan ganin ko waye,cike da ɗoki da mamaki ta sake fashewa da kuka,har da shashsheka. Ba kowa bane ya dafa ta face malaminta, tayi kewar sa fiye da tunani,rabon da yazo inda take tun lokacin daya bata shawarar auren Aslam,tayi ta tunannin Ina ya shiga ?ko shikenan ta daina ganinsa? Murmushi yayi mata tare da cewa"kiyi hakuri Islam,haka rayuwa ta gada,yau fari gobe tsumma,ya zama dole ki koyi hakuri da kawar da kai akan abubuwa,ba komai bane idan akayi maka zaka ɗauki mataki akai, Allah yana son mai hakuri"ya fada yana kallon islam. Jinjina kai Islam tayi,so take ta tambayeshi ina ya shiga?amma ta kasa yin magana kamar kullum. Murmushi yayi yace "nasan kina son kice Ina na shige kwana da yawa bana zuwa gurin ki ko? Da sauri Islam ta jinjina kai . "Wani gagarumin aikine ya sameni, Islam,yanzu haka nazo inyi miki sallama ne sai kuma Allah ya dawo dani,ki rike mijinki da gaskiya,kiyi masa biyayya,sannan kizama mai hakuri akan komai, Allah yayi miki albarka,Ni zan tafi saina dawo,amma zan dauki lokaci mai tsawo kafin dawowa ta,kizama jaruma mai fuskantar dukkan ƙalubalen ta"yana kaiwa nan yayi mata murmushi tare da bacewa. Ta jima agurin tana share hawaye kafin ta tashi ta koma class.lokaci ɗaya zazzaɓi ya rufeta sai karkarwar sanyi take,su Maryam anyi musu dressing agurin da sukaji ciwo,suna zaune sai hararar inda Islam ke zaune ta kifa kanta suke.hanan kuwa tana mai gargaɗin su akan su kiyayi Islam,dan tun kafin su fara tsokanar ta saida tayi musu gargaɗi amma suka ƙi jinta. Har aka tashi Islam na kwance bata ɗago kanta ba,duk malamin daya shigo saidai yayi karatunsa ya fice,dan Islam bata fahimtar komai. Gaba ɗaya yan class din har Hanan haka suka fice suka bar Islam kwance akan desk.ita kuwa Aisha tana can taki tafiya tun ɗazu tana jiran zuwan Islam,dan tasan lokacin tashin su nayi,Islam zata fito suyi sallama,kafin Aishan ta hau mota su tafi.to yau taji shiru,tun ɗazu drivern ta yazo daukar ta amma taƙi tafiya sai taga Islam. Tana ganin an tashi seniors ta fara murna tana dariya saidai gaba ɗaya wucewa suke bataga Islam ba.cike da damuwa akan fuskarta ta nufi ajin su islam,leƙawa ta farayi tana duba Islam,aikuwa can ta hangota kwance akan benci,da sauri ta karasa cikin class din tana kiran "anty! Barci kikayi ashe?antashi tun ɗazu ina ta neman ki, tashi mu tafi kowa ya tafi gida"A'isha ta faɗa tana dafa islam.jin Muryar A'isha ya sanya Islam ɗago da kanta,wanda idanunta sun kumbura sunyi jajur dasu. Murmushin karfin hali tayi,tana shafa kan Aishan, jikinta sai rawa yake ta mike tare da ɗaukar jakarta,sannan ta riƙe hannun Aisha suka fito.ahankali suke tafiya,dan Islam ji take kamar zata faɗi jiri ne ke neman kayar da ita. Kai tsaye bakin motar da ake ɗaukan A'ishan ta kaita,sannan tace cikin Muryar marasa lafiya"Baby kije gida kinji sai gobe,ki gaida mommy ki"ta faɗa tana ɗagawa A'isha hannu. "Anty yanaji muryarki tana son yin kuka?ko wani ne ya dake ki?A'isha ta faɗa tana wani gwabe fuska kamar zatayi kuka. Girgiza kai Islam tayi kafin tace "kinga Ni ba wanda ya dakeni mura nake bye"ta faɗa cikin murmushin ƙarfin hali. Haka drivern yaja motar suka bar makarantar. Ahankali ta juya da nufin samun guri ta zauna,dan taga Aslam bai ƙaraso ba, saidai nata juyawa taji jiri ya debeta, luuuuu tayi zata faɗi kasa,saidai kafin ta kai ga faduwar akayi saurin tare ta. Ahankali Islam ta buɗe idonta dake rufe, dan ganin wanda ya tare ta,ido hudu sukayi da Aslam,Yana kallon ta cike da tsoro,dan zuwansa kenan ya hango ta tana ƙoƙarin faduwa ta dafe kanta,shidai bazai ce gata yadda yayi ba,kawai ya tsinci kanshi ne a gurin.dan ji yayi zuciyar sa ta buga da mugun ƙarfi tsoro ya ziyarci zuciyarsa. Kallon juna sukayi na tsawon lokaci,tana riƙe ahannunsa,gaba ɗaya yaga tayi wani iri,da alama ma kuka tayi sannan ga jikinta nan zafi kau.cikin sanyin murya mai taushi yace "me ya sameki?maimakon Islam ta bashi amsa, sai ji yayi ta kankameshi tare da sakin kuka mai ciwo. Sosai jikin Aslam Yayi sanyi,dan Islam bata taɓa masa irin hakaba, lallai duk abinda ya sata wannan kukan babba ne. Rungumeta yayi shima yana shafa kanta."is ok ba gani ba ,kiyi shiru ai gani nazo ina tare dake"ya fada yana shafa kanta,kafin ya nufi mota da ita. Koda ya zaunar da ita kan kujerar, kuka take marar sauti.haka ya ja motar suka nufi gida.ta can daya kofar sukabi zuwa part ɗin su, gaba ɗaya zuciyar sa ba daɗi,tausayin Islam kawai yakeji ta ko ina ajikinsa.haka ya kamota suka shiga cikin Falon nasu,suna zuwa ta kwanta tare da kanƙame jikinta,dan sanyi takeji sosai.zama yayi kusa da ita yana shafa kanta cikeda tausayawa yace"sannu kinji ?bari na baki magani zazzabin zai sauƙa"ya faɗa yana kamo hannunta. Ɗan ƙara Islam ta saki tana kwace hannun dan kuwa ciwo yake mata.da sauri Aslam yakai kallonsa kan hannun nata. Zaro ido yayi cikeda tashin hankali yana kallon yadda hannun ya kumbura yayi jajur ga wani gurin afashe. Da ƙarfi yace "WHO did this to you?"ya fada cikin tashin hankali da ɓacin rai. Kallon sa Islam tayi cikin hawaye,amma ta kasa magana. Lumshe ido Aslam Yayi,yana jin zuciyar sa kamar zata fashe ,wane mahaukaci ne yayi mata wannan dukan da har ya fasa mata hannu?wllh ko waye yau saiya yabawa aya zaƙinta. Buɗe ido yayi ahankali da ƙoƙarin kawar da ɓacin ransa, ahankali ya kamo hannun nata yana kallo,wani irin zafi yaji cikin zuciyar sa,kallonta ya sake yi ya ce"ISLAM ! ya furta sunan nata cikin tashin murya. Kallonsa tayi itama da kunburarrun idanun ta."meya sameki?waye yayi miki wannan dukan?me kikayi masa?"ya fada cikin sanyin murya. Hawayene ya shararo daga idanun Islam kafin ahankali tace "kullum sai sun tsoakane Ni,bana kulasu,shine yau suke cemin yar riko mai jiki dakai,nikuma na gaji da yadda suke tsokana ta shine na dakesu,principal yasa wannan shegen sajant ɗin yayi min duka gaba ɗaya ya fasa min baya da hannu"Islam ta karasa cikin yanayi na shagwaba. Ƙura mata ido Aslam Yayi tunda ta fara maganar ta har ta kai ƙarshe,wannan wane sankaran ne ?wane marar hankalin ne yayi gangancin dukan islam?matar sa,wacce igiyoyin auren sa ke kanta,koshi bai dake ta ba dai wani wawa?lallai zai gane shi ƙaramin mahaukacine. Hannu yasa ya tada Islam zaune,sannan ya cire mata hijabin dake jikinta,ta tare da wani bata lokaci ba ya zuge zif ɗin rigar ta ya sauke kasa. Da sauri ya runtse idanunsa sakamakon yadda yaga bayan na Islam yayi ruɗu -ruɗu duk ya farfashe. Wani irin nishi yake cike da tsantsar bala'i da ɓacin rai. Mikewa tsaye yayi cikin matsanancin ɓacin rai yayi waje da sauri. Islam kuwa maida rigar ta tayi tare da kwanciya . Kai tsaye Aslam ya hau motar sa ya figeta da gudu,Allah ma yasa mai gadi na kusa yayi saurin buɗe mata get.kana ganin yanayin da Aslam ya fita kasan akwai bala'i Kai tsaye ya nufi makarantar su Islam. Masu karatu nidai ba ruwana wllh,nayi nan. Anty mammyn kuce. [10/13/2022, 12:54 PM] Abk: ___________ Kana ganin Yanayin da Aslam ya fice da motar kasan akwai bala'i. Kai tsaye makarantar su Islam ya nufa cikin wani mahaukaci gudu kamar zai tashi sama.ji yake kamar yayi tsuntsuwa ya ganshi gaban sajan ɗin nan,zuciyar sa banda tafasa ba abinda take. Cikin Sa'a kuwa yana zuwa ya samu gaba ɗaya malaman suna nan,dan kuwa suna meeting me yau.ko rufe motar baiyi ba ya fito cikin fusata,office ɗin principal ya nufa kai tsaye.aikuwa gab da zai shiga,saiga sajan ɗin nan ya nufoshi da buta ahannunsa,ɗaya hannun kuma riƙe da zanbaɗediyar dorina. "Malam ina zaka ne?kada ka shiga principal suna cikin meeting ne, saidai ka jira su fito"cewar sajan kenan yana ƙarasowa da ɗan gudu,dan kar Aslam ya shiga office ɗin. Cakk Aslam ya tsaya tare da juyowa,kallon sajan ɗin yayi tun daga sama har ƙasa,wani ƙazamin kucaki dashi,dagani wannan ko aji bai taba shigaba,amma shine zai kama masa mata yayi mata irin wannan bahagon dukan. Cikin fusata Aslam ya nufi sajan ɗin yana faɗin "kai waye?waye kai cikin makarantar nan?meye matsayin ka?"ya fadi haka ne dan tabbabar da cewa shine sajan ɗin,ɗan karya hukunta wanda baisan komai ba. Cikin washe baki sajan ɗin yace "ai matsayina makarantar nan shine,cin uban tangararrun yara,waɗan da basa jin magana,dan ko dazu saida na zane wata fitinanniyar yarinya,na farfasa mata baya da hannu... Wani wawan mari da Aslam ya ɗauke sajan dashi, saida ya kusan hantsilawa,bai gama dawowa cikin hayyacin sa ba,yaji saukar wasu maruka, ba jiran wani dogon bayani Aslam ya fara dukan sajan kamar an aikoshi.gaba ɗaya sajan ya rikice ya dimauce, dukan shi kawai Aslam keyi ta ko ina,shikuma yana kwance ya kasa koda kare kansa. Ganin Aslam na neman kashe shi ya sanya shi fara ihu da iya karfinsa. Shaƙar wuyansa Aslam yayi ya haɗashi da bango yana faɗin"kasan ko wacece yarinyar daka daka?kasan irin haukar da kayi?kai jahilin inane zaka mata wannan dukan kamar wani ka sami jaka?wllh yau saina daure ka,zan ga uban da ya sanya ka wannan haukar. "Na tuba ranka ya dade,ayimin afuwa,wllh bazan sake ba kayimin rai,wayyo Allah principal ku fito ku ceceni, zai kasheni"abinda sajan ɗin ke faɗi kenan cikin azabar shaƙar da Aslam Yayi ma. Da gudu Principal da malamai suka yi kansu,ganin yadda sajan ke shure shure yana neman mutuwa. Shikuwa Aslam ya shaƙar masa wuya sosai banda huci ba abinda yake. Dagyar suka kwace sajan daga hannu Aslam,sai dai zuwa lokacin tuni sajan ya suma. Cike da ɓacin rai Aslam ke tambayar Principal dalilin da yasa aka yiwa Islam wannan dukan? Shidai Principal haƙuri kawai yake ba Aslam,Dan ya tsorata da yanayin na Aslam,yadda ya fusata. Da gyar Principal ya shawo kan Aslam,akan karya kai kara shima saida ya kira daddy da baya ƙasar,kafin ya ce Aslam ya bar maganar,sannan ya haƙura bayan ya buga musu gargaɗi.dan da cewa yayi ma zai sauya mata makaranta,daddy ne ya hana. "Wllh !wllh!!wllh!!! Ko kallon banza ban amince asake mata cikin wannan makarantar ba,bare baƙar magana ko ta kai ga duka,dan ba ankawo ta bane dan wasu ƙartin banza su daketa, kunci Sa'a daddy ya hanani,da saina kai wannan makarantar kara"Aslam ya fada cikin fushi yana barin gurin. Har zuwa wannan lokacin daya yiwa sajan mugun duka baiji zuciyarsa tayi sanyi ba.gani yake bai ramawa Islam dukan ta ba.haka ya dawo gida zuciyarsa ba daɗi.inda ya bar Islam nan ya dawo ya sameta.tana kwance idonta arufe,zama yayi kusa da ita yana kallon ta cike da tausayi,ji yake kamar ya dawo da zazzabin zuwa jikinsa. Ahankali ya sanya hannunsa ya taba wuyanta.har zuwa lokacin jikinta zafi sosai. Buɗe ido tayi ahankali ta kalli Aslam kafin ta maida idon ta ta rufe,sai juya kanta take,da alama dai tana jin jiki. Tashi yayi ya nufi cikin daki,jimm kaɗan ya fito ɗauke da towel, sannan ya shiga kitchen ya ɗauko wata yar roba mai fadi,ruwa ya dauko mai sanyi amma ba sosai can ba cikin firji ya zuba cikin robar. Dawowa yayi ya zauna kusa da ita. Hannunsa ya sanya tare da zare rigar jikinta ya zama daga ita sai bra da wando short nicker iya gwuiwa. Duk abinda yake tana jinsa,amma saboda yadda take jin zafin zazzaɓi ko yunƙurin hanashin batayi ba.sai kare ƙirjinta da tayi da hannunta ahankali. Kallonta kawai yayi yana jin tausayinta sosai cikin ransa. Haka Aslam Yayi ta tsoma towel ɗin nan cikin ruwan yana shafa mata ajikinta. Banda nishi ba abinda Islam keyi, idonta akulle.ya jima yana shafa mata ruwan ajikinta har saida jikin yayi sanyi.ba jimawa kuwa barci ya ɗauke islam.ɗaukarta yayi tare da kaita daki kan gado ya kwantar da ita sannan ya fito. Haka suka kwana yana kula da Islam sosai,hatta abinci abaki yake bata,da tayi wani motsi zaice meke damunta?sosai Islam ke mamakin iya kula da marar lafiya na Aslam,ashe yana da kirki ?yana da tausayi?dubi yadda yake tattalinta kamar wata ƙanwarsa.sosai take jin daɗin hakan kuma. Ko Yau da safe ma bayan ya haɗa mata ruwan wanka tana kwance yazo ya zauna kusa da ita.ahanakali ya kira sunanta"Islam" cikin taushin murya. Buɗe ido Islam tayi tare da saukesu akansa.dama ba barci take ba. Ahankali ya kai hannunsa saitin wuyanta ya taba yaki koda zazzaɓin,ba zazzaɓi ajikinta hakan yasa yaji daɗi,murmushi yayi mata yace " sannu, meke damunki yanzu? Ahankali Islam ta lumshe ido tare da girgiza masa kai alamun ba komai. Hannunta ya kamo ahankali yana dubawa,ba kumburin saidai alamun ciwon,dan jiya ya sa mata magani dama agurin.ahankali yake shafa hannun nata mai tsananin taushi, Lumshe ido Islam tayi saboda yadda tsikar jikinta ta zuba lokaci guda,ji tayi kamar yana mata tafiyar tsutsa,dan haka cikin sanyin jiki ta zare hannunta. Kallonta yayi yace "ya kamata kiyi wanka saikici abinci da magani,ga ruwa can na haɗa miki"ya fada yana kallonta. Jinjina kai Islam tayi tare da yunkurawa ahankali ta tashi zaune,tana riƙe da bargon data lullaba dashi,dan ba riga ajikinta,daga ita sai bra. Fahimta Aslam Yayi kunyar tashi take ahakan. Dan murmushi yayi yace "ki tashi mana kin riƙe bargo kodashi zakiyi wankan ?" Ya fada yana ƙoƙarin cire bargon. Da sauri ta kara ƙanƙame bargon tare da turo baki tace "Bafa riga ajikina ,kuma ahakan zan tashi ?"ta faɗa cikin sanyin murya tana karya wuya. Murmushi yayi kafin yace "to menene dan mata ta tashi gaban mijinta ba kaya? Nan gaba ma Ni zan saka miki kayan da kaina"ya fada yana ɗan kallonta kasa _ƙasa.jiya wato saboda bata da lafiya ne yasa ta tsaya ya cire mata rigar,hmmm zaki tsara yarinya duk sanda kikazo hannuna.ya faɗa cikin zuciyarsa. Kallonsa tayi itama tare da ɗan buɗe baki,irin na mamakin nan.amma bata ce komai ba kuma bata tashi ba. Ganin da gaske bazata tashi ba ne,yasa ya miko mata babban towel yace idan kina bukatar wani abu kiyimin magana ina falo"yana faɗin haka yayi waje. Sosai Islam ta bishi da kallo,hakika sai yau tasan ashe Aslam Yana da kirki,yadda take zaton sa ba haka yake ba,murmushi tayi tana daura towel ɗin sannan ta shiga toilet. Tana fitowa ta ga kaya akan gado,harda inner wear nan ta sanya bayan ta shafa mai da turare.saidai bata sanya bra ba,kuma bata zuge zif ɗin rigar ba,saboda ciwon bayanta yasha iska sosai. Tana kammalawa ya shigo dakin,ganin harta shirya yace "ya kikasa riga kuma ban sami ki maganin ba? Shiru tayi bata ce komai ba,dan haka kawai taji tana jin nauyin sa yau din. Ƙarasowa yayi ya kama hannunta ya zaunar da ita kan stool ɗin dake gaban madubi,sannan ya ɗauki maganin,ba tare da ya sauke mata rigar ba yake shafa mata maganin tunda zif ɗin azuge yake. Shiru Islam tayi idanunta alumshe,sosai take jin daɗin yadda yake shafa mata maganin,saitaji kamar susa yake mata.harya kammala idonta alumshe yake. Kallonta yayi yadda ta wani lumshe ido alamun tana jin dadin abinda yake mata. Tsintar kansa yayi da jin dadin hakan shima.saida yayi dan murmushi sannan ya ranƙwafo da kansa saitin kunne ta yace" ya dai ?ko kina jin daɗin yadda nake taba bayan naki ne inci gaba?dan naga kamar baki san na kammala shafa maganin ba" Da sauri Islam ta buɗe idonta tare da zarosu waje,sai kuma ta turo baki cike da jin kunya ta tashi daga kan stool ɗin tana mai cewa"Ni wllh ba wani daɗi danake ji ba,kawai zafine yasani kulle idona,karkamin sharri"ta faɗa tana barin dakin. Dafe ƙirji tayi cike da jin kunya,da gaske fa bata san ya gama shafa mata maganin ba,ko me take tunani oho? Shikuwa Aslam dariya yayi tare da ajiye maganin,yana jin wani daɗi cikin ransa, shidai kai tsaye bazaice ga abinda yake ji game da Islam ba, amma yasan yanzu yana jin tausayinta sosai,sannan baya son ganinta cikin damuwa,gashi idan basa tare yayi ta tunanin ta kenan. Hmmmm muje zuwa malam Aslam. Yau koda Aisha tazo makaranta, haka tayi ta neman Islam amma bata ganta ba,sosai yarinyar ta shiga damuwa,har aka tashi bata da wani walwala.ko abincin ta ƙinci tayi,ta saba Islam ke bata a baki suna hira tana ta shirmen ta da bata labarin yan gidansu. Dan haka akan hanyarsu ta koma wa gida kawai takama kuka,duk rarrashin da driver Yayi mata taƙiyin shiru,har suka isa gida,nan mommyn ta ke tambayar ta dalilin kukan, cikin kuka tace"mommy yau antyna batazo makaranta ba,Kuma dama jiya naga kamar zatayi kuka,sannan jikinta da zafi"ta faɗa cikin muryar kuka. Ahankali kyakykyawar matar mai nutsuwa da cikar haiba, ta zauna kusa da ƴar Tata tare da rungumeta ajikinta,sannan ta fara magana"kiyi hakuri uwata kinji,antynki zata zo makaranta gobe,may be wani abunne ya hanata zuwa" "Mommy kullum antyna sai tazo school bata fashi sai yau, nidai mommy ki kaina gurinta"A'isha ta faɗa cikin kuka. Shiru mahaifiyar Aishan tayi,dan tasan rigima irin ta A'isha,idan ta kafe akan abu to zai wahala ta sauka.dan haka cikin dubara tace "yanzu ki bari sai gobe, idan kinje makaranta Kinga antyn naki bata zoba,to sai muje gidansu mu dubata ko" Cike da jin dadi yarinyar ta gyada kai tana dariya.nan dai mahaifiyar Tata ta bata abinci taci akayi mata wanka. Bayan kammala cin abinci Islam ta koma kan kujera ta zauna,magunguna Aslam ya dauko tare da nufota, tana ganin haka ta haɗe fuska tare da kawar da kanta gefe,alamun bata so. Shikuwa kusa da ita ya zauna har suna gugar jikin juna,bare maganin yayi tare da buɗe ruwa yace "oya haa"ya fada yana bude bakinsa. Shagwabe fuska Islam tayi cikin shagwaba tace "Ni wllh bana son wannan maganin ɗaci gareshi" Ta fada tana matsawa nesa da Aslam. Matsowa Yayi shima tare da cewa"idan kika tsaya kika sha ahankali bazakiji ɗacin sa ba,maza karbi kisha"ya fada yana sake miƙo mata maganin.yunkuri tayi da nufin sake guduwa,yayi saurin rukota ya rungumeta agefen hannunsa na dama tare da tura mata maganin abakinta,sannan ya kafa mata bakin jarkar ruwan. Dole tasa Islam haɗiye maganin nan,saidai yana cire gorar ruwan ta fara karin amai. Cikin sauri ya ɗago fuskarta ,ganin da gaske amanzatayi kawai ya haɗe bakinsu guri ɗaya . Muje zuwa masu karatu. Mrs babi ce anty mammy. [10/14/2022, 8:37 PM] Abk: __________Ganin da gaske Islam amayar da maganin nan take ƙoƙarin yi,shikuma baya son tayi Aman maganin.dan haka kawai sai ya haɗe bakinsu guri ɗaya. Luf kakejin Islam ta kwanta jikin Aslam tare da maida amanta, dan tuni ta daina kakarin aman. Shikuwa Aslam kissing din baƙinta yake cikin shauƙi da tausayawa,dan shi da nufin tsayar da Aman Yayi mata haka,amma sai abin nasu ya zarce ba zato ba tsammani kawai yaji Islam ta kamo harshen sa tana masa wani irin tsotsa mai sanya zuciya narkewa,zaro ido yayi cike da wani irin tsantsar farin ciki marar misaltuwa,haƙiƙa yayi matuƙar jin daɗin wannan respond din da Islam tayi.bai taba tsammanin zata iya biye masa ba. Cikin azama da farin ciki Aslam ya ƙara kamo kan Islam yana kissing ɗin ta cike da nishaɗi,Islam ma na maida masa martani,wanda sam ba ma tasan tanayi ba,ita dai kawai yanzu tasan tana matuƙar son Aslam Yayi kissing nata koya taba wani sassa na jikinta,tana matuƙar jin daɗin hakan. Sunyi nisa sosai banda romancing ba abinda Aslam keyiwa Islam,gaba ɗaya ya fice daga hayyacinsa,sai nishi yake,jikinsa har rawa yake,ita kuma Islam ko kaɗan batayi yunkurin hanashi ba. Ƙararrawar da ake ta bugawa aƙofar part ɗin nasu itace tayi silar katse musu wannan farin cikin da suke ciki. Tun ɗazu Aslam kejin bugun ƙararrawar amma yayi shiru abinsa. Saida hankalin Islam ya kai mata kunne ya can ƙofar taji karar, sannan tayi saurin raba jikinta dana Aslam,tana sauƙe numfashi da gyara rigarta. Da sauri ta miƙe ta nufi bakin ƙofar dan budewa,Aslam dake jin kansa yana yawo cikin sararin samaniya yayi saurin cafkar hannunta,idanunsa alumshe yana girgiza mata kai.alamun karta buɗe tayi zaman ta. Zare hannunta tayi tace "naji kamar Muryar granny fa"ta faɗa tana nufar ƙofar dan an ƙara buga ƙararrawar. Tana budewa kuwa sukayi ido hudu da granny,cikin murna Islam ta rungume granny tana faɗin "oyoyo granny na,shigo daga ciki mana"ta faɗa tana kamo hannun granny zuwa cikin falon. "Ai gani nayi tun jiya banganki kinzo can gurin mu ba,shine nace bari dai ninazo na duba ko lafiya,idan kuma kina buƙatar wani taimako saina taimaka miki naga yau ma baki tafi can makarantar ba"cewar granny tana zama akan kujera. Zama Islam tayi kusa da granny tace "wllh granny jiya nayi zazzaɓi ne after school shiyasa ban zoba,amma yanzu nake shirin zuwa dama"Islam ta faɗa tana murmushi. Aslam Yana zaune banda hararar granny ba abinda yake,kawai tazo ta katse masa jin dadin rayuwa,yanzu bashi da tabbas ɗin sake samun wannan damar nan gaba. Kallon sa granny tayi tare da yatsine fuska tace "to ɗan tijara da kake hararata dan nazo gidan ka,wllh baka isa ka hanani zuwa gidan nan ba,dan kuwa jikata na nan ehe ,kuma wllh kasan Ni, kasan halina dan In zage mu ba hamata iska ba wani babban abu bane agurina" granny ta faɗa cikin gatsine da fuska. Ita dai Islam dariya kawai take tana kallon kaka da jikan nata. Hararar Aslam ya ƙara bankawa granny kafin yace"ai wllh kekam kin cika katsewa mutum hanzari,yanzu da kikazo mana da wannan sassafen me zaki mana?ko kuma sa ido kikazo?ya fada aƙufule dan da gaske yaji haushin yadda granny ta katse masa hanzari sosai. "Kai kasani ja'irin yaro marar kunya,dan nazo gidan ka shine kake jin haushi,wllh daga yanzu inna ga dama nan zan dawo da zama ma baki ɗaya,inyaso naga yadda zakayi marar kunya kuma yau anan zan wuni"cewar granny itama tana hararar Aslam. Wani kallon me kikace Aslam yayiwa granny kafin yace "lallai ashe wanda ya mutu zai dawo,wato kizo ki hanani hutawa nida gidana ko,kiyi ta samana ido nida matata,wllh ban yarda ba. Sai kuma ya sassauta murya yana magana cikin rarrashi kinga matar kiyi hakuri ai dani dake bata ɓaci kije ki huta anjima da kaina zan rakota gurin ki haba tawan"Aslam ya fada cikin salon rarrashi . "To ai kaine Asalamu dan nazo gidan ka kake min tsiya,dama Ni ba zama zanyi ba,ƴata na dubawa,kuma ma naga kamar abinda nake tunani bai faruba, dan haka bari na tafi"granny ta faɗa tana mikewa.suma mikewar sukayi,Aslam Yana jinjina tsurku irin na granny wato zuwa tayi tagani ko yayi making luv da Islam ne,yasa tun jiya basu ganta ba?hmmmm ƴar sa ido kenan. Har bakin ƙofa suka raka granny.ga mamakin Aslam sai yaga Islam na ƙoƙarin bin granny.cikin sauri ya janyo Islam tayo baya.ɗan marairaice fuska yayi yana raɗa mata"ina kuma zaki?" Cikin dan basawar Islam tace "zanbi granny part ɗin mommy" Kallonta Aslam Yayi yace "to nan ɗin me yayi miki?keda baki da lafiya Please ki zauna ko zuwa yamma ne sai kije"ya fada yana ɗan haɗe fuska.yama za'ayi tace wani zatabi granny? bayan gashinan yana zaune agida kuma saboda ita. Cikin wani salo na jan aji Islam tace "Ni bana son zama nan Ni kadai ne,gara can ɗin cikin mutane kuma nafi jin daɗin zama acan"ta faɗa tana ƙoƙarin tafiya. Lallai ma yarinyar nan,kenan shi ba mutum bane? Wato bata jin dadin zama tare dashi ai kuwa wllh ba inda zata. Dan haka cikin kama kai yace"wuce mukoma cikin gida bazaki bita ba"ya fada yana bata hanya fuskarsa ba wasa. Turo baki Islam tayi tana dan bubbuga kafa cikin kukan shagwaba take cewa"Ni wllh saina je Ni bana son zama anan Ni kadai"ta faɗa cikin salon ta mai hargitsa tunani ko ina na jikinta motsi yake,kai kace da gangan take motsawar. Saƙare Aslam yayi yana kallon Islam,dan ba ƙaramin tafiya tayi da imaninsa ba,ganin bazai iya jure kallonta tana neman gigita shi ba,kawai ya sungumeta yayi cikin Falon da ita. Kan kujera yayiwa kansa masauki, ita kuma ya zaunar da ita akan cinyarsa. Sai wani narkewa take ajikinsa tana kukan shagwaba. Shikuwa Aslam kamar wani sokohaka ya rungumeta ajikinsa yana shafa kanta. "Is ok baby kiyi shiru ba nace anjima za kije ba?kinga yanzu safiya ce ki zauna ki huta,kuma ina gida bazanje ko ina ba,zan zauna in tayaki hira kinji?Aslam ya fada cikin wata ƴar ƙaramar murya mai cikeda taushi,shi kansa baisan ya iya irin wannan Muryar ba saiyau. Cigaba tayi da shura kafa kamar wata yarinya yar goye tana faɗin ita wllh saita je gurin mommy,shikuwa Aslam ya wani shashance sai rarrashin ta yake tana kan cinyarsa ya rungumeta ajikinsa kamar wani zai kwaceta. Shiru Islam tayi tare da ƙara shiga jikin Aslam,tana shaƙar daddaɗan ƙamshin dake tashi ajikinsa.can kasan zuciyarta kuma tana jin wani irin sanyi da daɗi,ji tayi kamar su dawwama cikin wannan yanayin,har cikin zuciyarta takeji Aslam,batasan me yasa idan tana tare dashi yanzu,jinta take kamar wata yarinyar yar goye,sannan tana jin farin ciki sosai cikin ranta. Bangaren Aslam shima jinsa yake kamar wani sarki,Aduk lokacin da yake tare da Islam,barin ma kwana biyun nan,yana yawan samun kansa da tunaninta ko kuma yayi ta murmushi yana tuna rigima irin ta Islam,ko fita yayi Allah-Allah yake ya dawo gida ya ganta.sosai yake jinta har cikin zuciyarsa. Shidai bazai ce sonta yake ba,amma yasan yana matukar son ganinta cikin nishaɗi sannan baya son ɓacin ranta. Gyara kwanciyarta Islam tayi tare da rungume Aslam ta baya batare da sanin tayi hakan ba. Wata sassanyar ajiyar zuciya Aslam ya saki tare da kaiwa goshinta sunbata. Buɗe ido tayi suka ƙurawa juna ido na kusan minti biyu,kafin Islam ta ɗan turo baki tace "me yasa kayi kissing ɗin forehead ɗina? " Ta fada cikin turo baki . Murmushi yayi kafin yace "sabona nawa ne,ina da ikon yin kissing ɗinsa,bama shiba ko Ina ajikinki mallakina nane,so ba laifi bane dan nayi kissing din forehead ɗinki"ya fada idanunsa akan lips ɗin ta yana wani lumshe ido. Turo baki tayi tace "nidai a'a jikina nawa ne bana kowa ba" "Kin tabbata da abinda kika faɗa?"cewar Aslam . Dan murguda baki Islam tayi kafin tace "eh mana da jikin na waye idan ba nawa ba?nike da iko da kayana saina so wani zai taba"ta faɗa tana wani fari da ido. Dariyar gefen baki Aslam Yayi cikin zuciyarsa yake fadin"aikuwa yanzu zan nuna miki nike da iko da jikin naki,zanyi maganin ki yarinya. Ba tare da wata -wata ba Aslam ya ɗago Kan Islam ya manna bakinsa kan nata. Cikin dan yunkurin bogi ta fara ƙoƙarin kwacewa,saidai kawai taji hannun Aslam inda batayi tsammani ba,zaro ido Islam tayi tana rarraba su,jin yadda Aslam ke yamutsa mata hazo. Tun tana ɗan motsin ƙwacewa har ta saki jikinta itama ta biye masa suka lula duniyar romance. Koda Aisha taje makaranta washe gari bataga Islam ba har aka tashi,hakan ya sanyata cikin damuwa sai haɗe rai take tana son kuka, ranar ya Hisham ne yazo ɗaukan ta,matashine da bazai wuce 16 yrs ba,Amma jin dadi da huta yasa idan ka ganshi zakayi tunanin ya haura 20 ma. kyakykyawa dashi kamar Aisha. Tana ganinsa ta tafi da gudu ta rungume shi tana kuka"shafa kanta yayi tare da durƙusawa daidai tsayinta kafin yace"babyna menene ?fadamin ke dawa kike kuka?ko kunyi faɗa da antynki ne?Hisham ya fada cike da kulawa yana shafa kan yarinyar. Cikin muryar kuka tace "ya Hisham yauma antyna bata zoba,Ni dai ka kaini gurinta"ta karasa da karawa kukanta sauti. Shiru yayi yana kallon yarinyar,yasan irin ƙaunar dake tsakaninta da antyn nata,dan haka cikin sigar rarrashi yace" to kiyi shiru daina kuka zamuje ki ganta,amma sai munje gida kinyi wanka kunci abinci,sai mu tafi tare da mommy kinji?"ya fada yana ɗago kan A'isha. Jinjina kai tayi tana share hawayen idanunta tace "thank you ya Hisham I luv you"ta faɗa tana rungumeshi. "Luv You too my sweetheart"shima ya fada cike da ƙaunar ƙanwar tashi. Tunani ya fara ta ina zasu samo gidan su Islam,dan yasan mommy ma bata san gidan ba.yana tsaye yana ɗan kallon farfajiyar makarantar saiga wata ɗaliba ta fito,da alama dai moninta ce. Da sauri ya karasa gurinta yana tambayar ta ko tasan Islam? Aikuwa yar budurwa taga kyakyakywan yaro cikin iyawa tace bata santa wacce Islam ɗin yake tambaya ba yayi mata bayani yadda zata gane.nan ya kira A'isha dan tayiwa budurwar bayani. Aikuwa kasancewar kusan kowa yasan Islam da Aisha,hakan yasa budurwar na ganin Aisha tace "ok Islam antyn Aisha kake nufi? Da sauri ya gyada mata kai alamun eh. Cikin yanga da kwarkwasa ta bashi address ɗin gidan su hanan ,dan tasan gidan tunda hanan kawarta ce sosai. Godiya yayi mata sannan ya ɗauki Aishan suka tafi gida. Aikuwa la'asar nayi, mommy ta kira wayar Abba ta sanar dashi batun zuwa gidan su antyn A'isha ,nan yace sai sun dawo,kuma ya bada sallahun ayimata tsaraba mai kyau ,ace daga Abban A'isha. Ƙarfe hudu da minti arba'in 4:40 pm suka isa ƙofar gidan su Aslam,cikin rantsatstsiyar motar su,bisa jarogancin Hisham,zo kuga murna gurin A'isha ,kamar zatayi me acikin mota sai tsalle take suna mata dariya,sun lodowa Islam tsara kala-kala. Mai gadi ne ya buɗe musu ƙofa bayan sun sanar dashi sunzo gurin masu gidan ne. Yayi musu iso mommy tace su shigo ciki. Da sallama suka shiga cikin Falon,Wanda mommy,granny da kuma hanan ke zaune suna hira da kallo,Aman baya nan ya fita yawonsa. Amsawa su mommy sukayi gaba ɗaya tare da kai kallonsu bakin ƙofar,cikin azama mommy da granny suka mike tsaye baki buɗe suke kallon matar dake tsaye cikin tsantsar shock da mamaki tana kallonsu... Wacece wannan matar ? Muje zuwa masu karatu. Anty mammy ce. [10/17/2022, 12:53 PM] Abk: __________Azabure mommy da granny suka mike tsaye,tare da kafe matar dake tsaye bakin ƙofa cikin shock da ido. kallon -kallo aka fara tsakanin matar da kuma su mommy.jikin granny Banda rawa ba abinda yake ta kasa cewa komai sai kallon matar kawai take,itama matar idonta na Kan granny,ganin abin take kamar almara,ahankali ta lumshe idonta tare da hadiya wani yawu mai ɗacin gaske,sannan ta buɗe idonta yayin da wasu hawaye Masu matuƙar zafi da ciwo suka zubo daga idanunta. Cikin rawar murya mommy tace "Saratu! Ke ce nake gani ko idanuna ne ke min gizo"ta faɗa tana ƙara murza idanunta dan tabbabar da abinda suka gane mata. Kuka sosai Saratu ta sanya tana mai jijjiga kai,nan take abubuwan da suka faru abaya suka fara dawo mata tamkar an kunna amajigin kallo. Cikin kuka mai tsanani tace "nice anty Aisha,nice ba gizo idonki keyi ba"ta faɗa tana takowa cikin Falon da sauri tana jin wani irin raɗaɗi cikin zuciyar ta. Gaban granny tazo ta durƙushe cikin matsanancin kuka ta kama ƙafar grannyn tana faɗin"bansan da wane baki zan nemi yafiyar ki ba uwata,domin nasan cewa niɗin mai laifice agareki,kin bani tarbiyya kin kula da rayuwata,amma nabiyewa son zuciya da ruɗin soyayya na tafi na barki,banyi tunannin wane hali zaku shiga ba,amma wllh nayi hakan ne dan ceto rai,dan Allah ummata ki yafe min ki gafarceni "Saratu ta fa ɗa cikin kuka mai tsuma zuciya. Awannan lokacin granny ma kuka take,yayin da can cikin zuciyarta take godewa Allah daya dawo mata da ɗiyarta abin sonta,wacce ta rabu da ita shekaru masu tarin yawa,yau gata agabanta sun ga juna kafin ta bar duniya.ahankali granny ta sanya hannu ta ɗago Saratu dake kuka kamar ranta zai fita,hannu ta sanya ta share mata hawayen idanunta kafin tace "na jima da yafe miki Saratu,ban rikeki cikin zuciyata ba,kullum fatana ki dawo gareni yau Allah ya cika min burina Saratu na yafe miki"granny ta faɗa tana mai rungume ƴarta ajikinta. Kuka suke sosai cike da kewar juna,mommy na tayasu,Hanna tana tsaye tana kallon ikon Allah,kamar dai Hisham da A'isha,suma mamaki suke ina kuma mommy tasan wannan matar da suka rungume juna suna kuka. Sun jima suna koke-koke kafin suka zauna kan kujera. Kallon granny Saratu tayi tace "umma ina yayana?matar yaya yaranmu nawa yanzu?ta faɗa tana juyowa ga mommy. Cikin murmushi mommy tace "yaranki hudu,Aslam,Aman,jannat sai kuma hanan"ta faɗa tana nuna hanan. Ahankali ta dafa kan hakan tace "Allah sarki sannu yata niɗin mamanki ce kinji"ta faɗa tana rungumar hanan. Kallon su Hisham granny tayi,kobata tambaya ba tasan wannan jikokin ta ne,dan haka cikin murmushi tace "ku ƙaraso mana yan jikokina Ni kakar kuce, nice na haifi mahaifiyarku"granny ta faɗa tana mai miƙa musu hannu alamun su taho. Ahankali Hisham ya ke takowa,cikin farin cikin da ya tsinci kansa,koba komai yau yaga dangin mahaifiyarsa,kullum dama Faransa kenan.Aisha kuwa da gudu tazo ta haye kan cinyar granny tace"kece kakata?jinjina kai granny tayi tana shafa kan A'isha tace "nice kakarki yarinya " "Amma me yasa baki taba zuwa gurin mu ba,muma bamu taba zuwa ba,kullum mommy sai tayi kuka tana son ganin ki,abba ne yake rarrashinta"A'isha ta faɗa tana ɗan marairaice fuska irin na tausayin nan. Shafa kanta granny tayi tace daga yau bazata ƙara kuka ba,zakuyi ta ganina tare da ku". Nan dai suka zauna suna ta alhini da nuna kewar juna,sun ma manta da batun zuwa gurin Islam da sukayi. Tuni mommy ta kira daddy ta bashi labarin daya sakashi tsantsar farin ciki,nan da nan ya nufo gida. Haka ma Hisham ya kira Abbansa ya sanar dashi,sunga ahalin mommyn su.nan shima yace yana hanya. Islam kuwa suna can suna shan barci ita da Aslam,bayan sun gama romancing juna,wanda Aslam yaso ya angonce awanna lokacin amma Islam taƙi yarda sam,ta nuna masa tsoro take ji kuma lokacin hakan baiyi ba. Da gyar Aslam ya samu ya daidaita kansa,tare da rungumarta suka kwanta,jikinsa sai rawa yake,hakika yana matukar cutuwa,shi dama gashi Allah yayi shi da sha'awa mai ƙarfi sosai,kuma yanzu baya bin matan banza bare yace zai sami nutsuwa acan garesu.haka suka kwanta barcin wahala yayi gaba dashi. Duk da Islam taji tausayin sa sosai,Bama yadda taga jikinta na matukar karkarwa,idanunsa har ruwa suke,amma haka ta waske,bata son sakar masa jikinta ,saita gama fahimtar inda ya dosa,ita kam ta gama yarda azuciyar ta,cewa ta kamu da son Aslam,kuma shima tana ganin zallar soyayyarta cikin idanunsa,amma tana son saiya furta mata da kansa,kafin ta sakar masa jikinta.da wannan tunanin itama barci yayi gaba da ita. Ahankali Aslam ya buɗe idonsa da sukayi masa nauyi,kallonsa ya kai kan Islam wacce ke kwance kan ƙirjinsa tana barci,ba kaya ajikinta sai bargon da suka rufe jikinsu dashi. Shafa kanta yayi yana jin wani abu na taso masa can ƙasar zuciyar sa game da ita,saidai har yanzu ya kasa gane menene wannan abun.kissing koshinta yayi tareda murmushi . Cikin nutsuwa ya mayar da ita kan follow kafin ya tashi ya nufi toilet,ruwan wanka ya haɗa musu sannan ya fito. Ɗaukar ta yayi caak!bai zame da ita ko inaba sai cikin abin wankan daya cika da ruwa. Da sauri Islam ta buɗe idonta tana kallon inda take. Turo baki tayi tana ƙara yin kasa cikin ruwan ,dan kar Aslam ya kalle mata jiki . "Nifa barci nakeyi shine zaka kawo Ni nan?wllh ka mayar dani ba yanzu zanyi wanka ba"Islam ta faɗa cikin shagwaba tana turo baki. Murmushi yayi yace "haba baby lokacin salla yayi fa ,zamu makara "ya fada yana janyota jikinsa. Haka sukayi wankan nan,tun Islam na nokewa har tasaki jikinta,ganin shi ko kaɗan baya wani jin kunyarta.saima wasa da yake da sassan jikinta. Bayan sun shirya sunyi sallane, Aslam yace zai je super market,ya duba yanayin yadda gurin ke tafiya. Islam kuma dama part din su mommy zata shiga. Tare suka fito cikin yanayi na nishadi da farin ciki,suna tafe suna dan hira yayin da hannunsu ke sarke dana juna. Kai tsaye part ɗin mommy suka nufa.gab da zasu shiga Islam taji an rungumota ana ihun "antyna oyoyo antyna " Cikin zaro ido da tsantsar farin ciki Islam ta buɗe baki kafin ta ɗago A'isha,wacce fitowar ta kenan daga cikin Falon da nufin zata dauko teddyn ta amota kawai ta ga antynta. "Babyna kece yau agidan mu? Waye ya nuna miki?keda wa kuka zo?"Islam ta faɗa tana rungume A'isha. Cikin zumuɗi A'isha tace "nida mommy na da ya Hisham,kuma anty kinsan me?Islam ta girgiza kai tana kallon A'isha. Riƙe haba yarinyar tayi cikin iyayi tace "mommyn mu ta rungume wata tsohuwa tana kuka,shine tsohuwar tace wai ita kakarmu ce,suna can ma suna ta hira kuma abban mu ma yace zaizo"yarinyar ta faɗa tana dukan cinyarta da taɓe baki. Shidai Aslam kallonsu kawai yake,yayin da shima yaji lokaci ɗaya yarinyar ta kwanta masa cikin rai,akwai wayo da surutu.amma waye wani Hisham?Meya hadin sa da matar sa?nan da nan yaji kishin Hisham yayi mugun kama shi. Cikin haɗe rai yace "waye kuma Hisham"ya fada yana kallon Islam. "Uncle yayana ne fa,kuma shima yana da irin wannan abun naka "cewar A'isha tana nuna sajen fuskar Aslam. Murmushi yayiwa yarinyar tare da shafa kanta.sannan ya maimaita tambayar sa ga Islam. Ɗago kai tayi ta kalleshi,nan take ta hango zallar kishinta cikin idanun sa. Murmushi tayi tace "is her brother,kuma Nima ban sanshi ba.let go inside and see"ta faɗa cikin wani salo da tuni yasanya Aslam lumshe ido tare da bin bayanta. Hira suke sosai,suna ba juna labarin bayan rabuwa,granny sai matsar kwalla take. Saratu ta juya bayanta tana fuskantar grannyn,itama tana hawaye. Da sallama su Islam suka shigo cikin Falon,gaba ɗaya hankalin Islam na kan A'isha,tana ta zuba mata labari,ita kuma sai biye mata take tana dariya. Har suka ƙara so cikin Falon Islam bata kalli kowa ba, duk kuwa da yadda taji gabanta yayi mugun faɗuwa,runtse ido kawai tayi tare da dafe kirjin nata. zama Aslam Yayi tare da gaida mommyn A'isha ba tare da ya kalli fuskarta ba, hankalinsa yana kan Islam data zaune can gefe ita da A'isha . cikin zubda hawaye tace "Aslam,kai ne kazama haka?baka gane Ni ba ko"Saratu ta faɗa cike da mamakin yadda Aslam ya zama babban mutum,lokacin data bar gida yana ƙarami baifi shekara tara ba. Da sauri Aslam ya ɗago kansa,jin muryam anty Saratu da yayi,haƙiƙi bazai taba mantawa da wannan muryar ba, koda shekaru nawa ta ɗiba, Muryar ƙanwar mahaifinsa ce,wacce yayi matuƙar shaƙuwa da ita,lokacin tana budurwa komai nashi ita keyi masa. Cikin wani irin shock da mamaki Aslam yace "antyna! Da gaske kece nake gani agabana? Ya faɗa cikin wani irin matsanancin farin ciki,dan kuwa yayi kewar ta bana wasa ba.kuma duk garin da yaje saiyayi cigiyarta . "Cikin zubda kwalla tace "nice Aslam! Nice Aslam ɗina "ta faɗa cikin kukan dariya tana ware masa hannu alamun yazo gareta. Da sauri Aslam ya ƙara sa kusa da ita tare da rungumeta, yana jin wani sanyi cikin zuciyar sa,hakika yau rana ce mai matukar muhimmanci agareshi,na ganin antynsa abar sonsa. Kasancewar Islam na nesa dasu hakan ya hana mata jin sautin muryoyinsu sosai,sai da A'isha tace "anty Kinga mommy na can zomuje in nuna miki ita"A'isha ta faɗa tana jan hannun islam. Ita sai yanzu ma ta tuna batayiwa kowa magana ba tun shigowar ta falon Bama tasan suwaye cikin Falon ba,dan kanta a ƙasa ta shigo. Janta A'isha tayi har gaban mommyn ta dake shafa kan Aslam tana mai faɗin "Aslam naji ance kayi aure ?ina matar taka? Da wani irin sauri kamar walkiya Islam ta ɗago kanta tare da zubawa matar dake magana ido,bata ganin fuskar matar dan ta juya musu bayane tana fuskantar Aslam,sai dai koda cikin dubban daruruwan mutane taji wannan Muryar bazata taɓa ɓace mataba, ita ce Muryar data faraji aduniya,ita ce Muryar dake rarrashin ta idan tana kuka, ita ce Muryar dake sanya ta cikin farin ciki idan tana baƙin ciki,ita ce Muryar datafi komai soyuwa agareta. Da gyar Islam ta daga harshen ta da yayi matuƙar yi mata nauyi tace "MOM...M..MMY.."tana nuna matar. Ahankali cikin matsanancin faɗuwar gaba Saratu ta runtse idonta sakamakon jin Muryar Islam ɗinta na mata gizo kamar yadda ta saba mata a mafi yawancin lokuta. Buɗe idonta tayi tare da kallon Aslam dake gabanta,saidai yanayin yadda taga kowa na cikin dakin ya bi Islam da kallone yasa ta saurin juyowa dan ganin abinda suke kallo. Kallon -kallo aka fara tsakanin Islam da saratu.cikin wani irin yanayi suke kallon juna,inda Islam ke rayawa cikin zuciyarta cewa Hakika wannan mommyn tace domin kuwa ba abinda ta manta nadaga fuskar mommyn ta,sannan ba abinda ya sauya ajikin mommyn nata,sai dai yanayi na hutu da jin daɗi daya ƙara bayyana atare da mommyn. Cikin sarƙewar murya Islam ta kara daga bakinta tace "Mo..o..mm...y !! Ni ce... Is.l..am... ɗin.... Maganar ta sarke sakamakon wasu taurari dake yawo kan fuskar Islam,sai kuma duhu ya mamaye ganinta tayi baya luuuuuu!!!! Zata fadi. Da mugun sauri Aslam Wanda ya mike tsaye tun lokacin da Islam ta fara magana, yayi kanta tare da tarota, ta faɗo kan hannunsa.cikin tashin hankali yake jijjiga yana kiran sunanta"Islam ! Islam!! amma ina tuni Islam ta sume. Gaba daya su granny da suka kasa fahimtar abinda ke faruwa sukayi kanta suna kiran sunanta,A'isha kuwa kuka take tana kiran antynta. Ruwa Hisham ya buɗe ƙaton fridge ya dauko tare da mikawa Aslam,karɓa Yayi tare da tsiyaya ruwan ahannunsa ya watsawa Islam akan fuskarta. Ahankali ta sauke wata doguwar ajiyar zuciya tare da buɗe idonta.sannan ta sake lumshewa. Cikin rawar jiki Saratu ta kamo hannun Islam tare da janye hannun rigar Islam ɗin. Nan take wani bakin tabo ya bayyana a tsakiyar gwuiwar hannunta.zaro ido tayi tare da sakin wani irin kuka na farin ciki tana faɗin"Islam !!!wayyo Allah na,Islam ɗina ce umma Islam ɗina Islam ɗina ce,Islam ce umma "gaba ɗaya ta rude abinda take fadi kenan tana janyo Islam daga jikin Aslam. Buɗe ido Islam tayi tare da ƙurawa mommyn ta su,hawaye na zuba kamar an bude fanfo. "Mommyna "Islam ta faɗa tana faɗa wa jikin mommyn ta.kuka suke sosai mai ban tausayi da tsuka zuciya.gaba ɗaya mutanen dake falon saida sukayi kuka. Na tausayin uwa da ƴar Tata.kallo ɗaya zakayi musu kasan sunyi mugun kewar juna. Ana cikin wannan halin daddy ya faɗo cikin Falon da sauri kamar zai kifa,nan fa murna da takara dawowa sabuwa, daddy sai godiya yake ga Allah yau gashi ga ƙanwarsa tilo daya rasa tsawon shekaru.sannan kuma wai Islam da yake riko yarta ce?ikon Allah kenan.kowa yayi mamakin wannan al'amari,duk da sunsan ba abin mamaki bane idan aka tuna iko da buwayar ubangiji. Wayar Hisham ce tayi kara ,yana dagawa Daddyn sa ke tambayar yazo anguwar yazo ya shigo dashi, cikin zumuɗi Hisham yace "daddy yau ranar farin ciki ce agaremu,daddy ashe antyn A'isha ba kowa bace bace ƴar uwata islam yarinyar ku da kuka rasa tsawon shekaru"ya karasa hawaye na cika masa ido. Wani irin farin ciki ne ya lulluɓe daddy cikin rawar baki yake faɗin"ikon Allah hukumullahu ta'ala,Hisham zo kayi saurin kaina cikin gidan nan,kafin na rasa hankalina dan farin ciki"daddy ya fada yana jin wani hawaye na taruwa cikin idanunsa.yau zaiyi tozali da gudan jininsa,farin cikinsa.banda hamdala ba abinda yake ga Allah. Hisham ne yazo ya shigar dashi har cikin Falon. Da gudu Islam ta ƙara sa gareshi tare da fadawa jikinsa ta sanya kuka sosai.tana faɗin "Abbana wayyo Abbana"rungume ƴarsa Abba yayi tsam ajikinsa,yana jin kamar bai taba tsintar kansa cikin farin ciki irin na yau ba.islam ɗin sa ce wllh yaji duminta ajikinsa ya Salam. Ahaka Aman ya dawo gidan ya tarar dasu,shima yayi mamaki sosai kuma yayi murna. Nan suka zauna ana ta jajanta wa juna da neman yafiya. Cikin zallar farin ciki Islam tace "mommy Ina son sanin menene dalilin daya rabaki da su granny?sannan me yasa duk tsawon wannan shekarun baku nemi juna ba?Islam ta faɗa tana kallon mommynta. Ajiyar zuciya mommy tayi tare da kallon mutanen dake cikin Falon kafin ta fara magana da cewa"nasan dukan ku yara kuma buƙatar sanin dalilin barina gida, domin ko Aslam Yayi kanƙantar da zai rike komai awannan lokacin har kawo yanzu"mommy Saratu ta faɗa tana sauke numfashi kafin ta ci gaba da magana. "Mu biyu iyayenmu suka haifa yaya Mahmud saini Saratu, mahaifin mu mai kudine sosai dan shahararren dan kasuwa ne ,wanda ya gaji tarin dukiya gurin iyayensa,kuma shi kadai suka haifa. Gashi duk sun rasu. iyayen mu suna matukar sonmu da bamu kulawa, mahaifinmu ya rasu lokacin ina aji hudu na sakandare,yayin da ya Mahmud ke jami'a.haka umma taci gaba da kula damu tare da bamu kyakykyawar tarbiyya. Tun kafin mahaifina ya rasu sukayi alƙawarin haɗamu aure da dan gidan abokinsa.wanda nikuma lokacin dana sami wannan labarin tuni nayi nisa cikin soyayya da abubakar.wanda ya kasance dan asalin garin Maiduguri,kuma shuwa ne.karatu ne ya kawo shi Kano,sannan yana neman kuɗi kasancewar sa Maraya gaba da baya.sannan yana da hankali da nutsuwa, ga addini da sanin ya kamata. Dan haka na nuna rashin amincewata ga wannan auren,sannan na gabatar da Abubakar ga umma da yaya. saidai sam umma taƙi amincewa da batun Abubakar,acewarta dole saita cika burin mijinta,lokacin da naji wannan batu hankalina yayi matuƙar tashi,nayi ta kuka ina rokon umma,amma sam taki amincewa,ƙarshe ma tace idan ban rabu da zancen Abubakar ba zata tsine min. Hankali tashe na samu abubakar nake sanar dashi akan mu hakura da juna murabu. Abin mamaki kuka sosai Abubakar ya sanya wanda yayi matuƙar tadamin hankali, nima na kama kuka.haka mukayi ta kuka daga karshe ya bani hakuri akan nayi shiru,kuma muyi ta addu'a Allah ya zaɓa mana abinda yafi alkairi,da gyar muka rabu awannan ranar. Lokacin matar yaya itake rarrashina da bani shawarwari. Duk yadda naso na rabu da Abubakar,amma zuciyata taki bani haɗin kai,kullum cikin tunanin sa nake,gashi tun daga wannan rana ban sake ganin sa aƙofar gidan mu ba.hankalina yayi matuƙar tashi. Dan haka ranar na sanar da umma zani ziyara gidan yan uwa. Kasancewar ba fita nakeyi ba umma ta amince min. Da tambaya da komai naje anguwar su Abubakar nan na tarar dashi cikin mawuyacin hali,sai aman jini yake gashi shi kadai ba mataimaki.cikin tashin hankali na karasa gareshi,yana ganina ya sanya kuka yana faɗin bazai iya rayuwa babu Ni ba,dan Allah in taimaka masa. Nima kuka nake ina goge masa jinin dake zuba daga bakinsa.da gyar na samu taimakon wani makocinsa,muka kaishi asibiti.nan likita ke sanar damu zuciyarsa ce ta kumbura kuma ana buƙatar yi maka aiki cikin gaggawa.dan ta harbu sosai idan aka ƙara kwana uku za'a iya rasashi. Cikin tashin hankali na nufi gida,banyiwa umma ƙarya ba na sanar da ita komai ina kuka,sosai umma ta tausayawa halin jinyar da yake ciki,kuma ta bani kuɗaɗen da za'ayi masa aikin,saidai bawai ta bani kuɗin bane dan ta amince da auren mu. Dan kuwa lokacin saura sati biyu bikina da Umar . Haka aka yiwa Abubakar aiki cikin nasara ya sami sauƙi amma likita ya tabbatar idan ba'a bashi abinda yake soba,to za'a rasashi. Sosai na shiga damuwa marar adadi,gashi umma ta hanani zuwa inda yake tunda ya sami lafiya aka sallameshi.yaya kuma bai cika zama a ƙasar ba.awannan lokacin dan yana yawan fita waje,wajen harkokin kasuwancin sa. Ana saura kwana uku bikina saƙon letter daga Abubakar ya sameni,cewar idan har aka daura aurena da wani ba shiba,wllh saiya kashe kansa. Na tsorata sosai,dan nasan irin son da Abubakar ke min,yace Ni kadai ce danginsa, idan ya rasani shima mutuwa zaiyi. Cikin dare na gama shirya yadda zanyi in bar gidanmu,kayana tuni sun jima abayan gida,haka na shiga ɗakin umma na dauki kudi masu yawa na sanya cikin jakata.ina kuka ina kallon ummana dake barci na fice bayan na ajiye mata doguwar wasiƙa. Haka na dawo dakina ina kallon Aslam,Wanda kullum muna tare ,dashi muke kwana ko ina zani yana biye dani,mun shaƙu sosai dashi ina ƙaunar yaron har cikin raina.nayi niyyar tafiya dashi,sai kuma nayi tunanin halin da mahifansa zasu shiga,dan haka nayi tafiyar Ni kaɗai. Ba wani tsoro tattare dani sai tarin tausayin marayan Allah Abubakar.da gyar na samu adaidai ta ya kaini anguwarsu. Ina zuwa na tarar da Abubakar zaune da hotona ahannunsa yana kuka mai tsuma zuciya.ga jini yana zuba ta hancinsa da bakinsa.. Muje zuwa masu karatu. Me babi ce Anty mammy. [10/19/2022, 9:15 PM] Abk: 63/64 ______________Ina zuwa na tarar da Abubakar riƙe da hotona yana kuka sosai,ga jini yana zuba ta bakinsa da hanci kamar wanda yayi haɓo. Cike da tashin hankali na nufeshi Ina tambayar meke damunsa. Sosai yayi farin cikin ganina dan kuwa daga hannu yayi yana godiya ga Allah tare da tambayar me yasa na fito cikin daren nan?shin umma ta amince ya aureni ne? Cike da karayar zuciya na girgiza masa kai alamun bata amince ba. Shiru yayi yana kallo na,kafin ya kai kallonsa ga ƙatuwar jakar dana yi wurgi da ita tun shigowata. Ajiyar zuciya ya sauke mai ƙarfi kafin ya kalleni cikin sanyin murya ya fara magana"Saratu kina nufin gudowa kikayi daga gida? Ya fada idonsa akaina. Cikin alamu na rashin sanin mafita nace masa "wannan itace kawai mafita agaremu,domin umma sam taƙi amincewa da batun auren mu,gashi yaya Mahmud baya nan,saura kwana uku daurin aure na da Umar,idan bamu gudu ba wllh munaji muna gani zamu rasa juna"na faɗa cikin kuka. Shiru Abubakar yayi kafin daga bisani yace "Allah ya sani bana son zama silar rabuwarki da mahaifan ki,amma bani da wata mafita dole mu gudu mubar garin nan dan cikar burin mu"ya fada yana mikewa da sauri ya harhaɗa kayansa gaba ɗaya muka bar ɗakin. Sai gab da asuba muka samu motar da zata kaimu maiguri muka shiga. Saida muka shiga motar kuma zuciyata ta cika da fargaba da tsoro,tunani nake idan umma ta farka taga bana nan mezai faru?wane irin halin zata shiga?shin ya yayana zai ji idan ya samu labarin na gudu?ya Aslam zai kasance idan ya nemeni ya rasa? Cusa kaina nayi tsakanin cinyoyina,Kuka sosai na sanya marar sauti, ina jin zafi sosai cikin zuciyata,saidai bana tunanin zan sauya ra'ayina akan barin garin. Haka Abubakar yayi ta rarrashina da bani hakuri har muka shiga cikin Maiduguri. Wannan shine karona na farko da naje Maiduguri. Kai tsaye gidan liman Abubakar ya kaini,nan yayi masa bayanin Ni marainiya ce iyayyena sun mutu,bani da kowa kamar shi,shine ya kawoni dan yazama waliyyina aɗaura mana aure. Kwanan mu hudu agarin aka ɗaura mana aure. Nan cikin gidan liman muka fara zama,yayin da Abubakar ya fara neman na kansa. Kudin dake hannuna na bashi ya fara kasuwanci dasu,cikin ikon Allah kuwa kasuwar ta karbu sosai,tun yana yawo da kayan a baro har yazo ya buɗe dan karamin shago daga nan kuma sai kasuwa ta bunkasa ya buɗe ƙáton shago,nan ya gina mana gida madaidaici muka koma. Lokacin ne na haifi Islam. Islam tun tana karama ta kasance yarinya mai matukar hazaka da kokari,komai aka koya mata ta rike kenan,mun sata makaranta mai kyau da tsada,shekarar ta takwas, lokacin Hisham yana da shekara hudu. Sosai Islam ke kaunar kanin ta muna damu,tana da tausayi,saidai sam bata barin ta kwana ko yaya akayi mata abu saita rama. Tana da son mutane sosai ga shiga rai. Duk tsawon wannan shekarun kusan kullum sai nayi kukan rashin ahalina,tun lokacin dana bar gida ban ƙara komawa ba saida muka haifi Islam,abin mamaki koda mukaje anbamu tabbacin su umma sun bar garin tuni. Nayi kuka kamar ba gobe,nayi kewar mahaifiyata da ɗan uwana,haka duk gidan da mukaje na yan uwa sai sun taɓa min magana,wasu ko kallona ma basayi,haka muka tattara muka koma Maiduguri. Akwai wani abokin kasuwancin Abubakar wanda suka yawancin kasuwancin su tare,saidai duk wata kwangila Abubakar ke samun ta,hakan ashe yana ƙonawa Alhaji Musa rai. Wata rana abban Islam ke sanar dani sun sami sabani da Alhaji Musa ,har yana iƙirarin dau sai yaga bayansa,nan nayi ta kwantar masa da hankali akan cewar ɓacin rai ne yasa shi faɗin hakan,dan nasan irin alaƙar dake tsakaninsu da juna. Kwana biyar da wannan maganar,cikin dare yan fashi suka shigo gidanmu,kuma aranar aka bawa abban Islam wata kwangila mai matukar tsoka. Cikin tashin hankali A wannan lokacin muka sauke Islam ta saman beni akan muma zamu zauko kafin su ƙaraso inda muke dan mu gudu. Saidai bamu sami damar yin hakan ba suka rutsamu. Hakan yasa muka tsaya ba yadda zamuyi.ganin ba Islam yasa suka ce anemota ahaɗa mu duka aƙona,haka aka basu umarni, cikin tashin hankali na kalli windown da muka sauke Islam,naga tana nan,aikuwa suma nan hankalinsu ya kai kanta sukace a kamota nan abban Islam yace ta gudu. Jin haushin hakan yasa suka kamashi da duka kamar zasu kashe shi.gashi takardar da suka zo nema basu samu ba. Daga karshe suka sanar damu Alhaji Musa ne ya sanya su wannan aikin.sannan suka cinnawa gidan wuta.kuma suka kulle ko ina na gidan, Amma cikin hukuncin Allah da kuma sauran numfashin mu agaba,muka samu muka fice daga gidan bayan samun raunuka da mukayi,mai gadi kam tuni sun kashe shi. Kai tsaye nausa neman Islam,saidai har gari ya fara wayewa bamu ganta ba nayi ta kuka ina cewa mu koma cikin garin mu dubata,amma haka abban Islam yace inyi hakuri yanzu komawarmu cikin gari akwai matsala,dan zasu iya biyo sawu suga idan muna raye. Inyi hakuri mu bar garin daga baya saimu dawo neman ta. Haka muka bar garin Maiduguri cikin tashin hankali,Ni dai zuciyata gaba ɗaya tana ga ƴata. Wani kauye mukaje muka fake acan,sai da akayi wa abban Islam magani ya warke ,dan yaji ciwo sannan wuta ta gonashi garin ceton rayuwar mu nida Hisham. Kullum sai nayi kuka ina tunanin wane hali Islam ke ciki?to tana gurin wa?ko taci abinci?ko kuka take ahalin yanzu?haka nake wuni ina kuka tun ina yi aboye har Abban Islam yazo ya sani.haka zaiyi ta bani baki akan na kara hakuri In sha Allah zamu Sami yarmu cikin koshin lafiya,dan kuwa akwai wasu samari daya sanya sukaje har can Maiduguri neman Islam ɗin kuma har yanzu suna can basu dawo ba. Saidai koda suka dawo bamu sami labari mai daɗi ba,hakan ya ƙara tada mana hankali,Abban Islam da kansa ya nufi Maiduguri neman Islam,amma ba ita ba labarin nan. Nan muke samun labarin cewa, da tana gidan maƙocin mu,amma daga baya aka nemeta aka rasa. Ba inda bamu bada cigiyar Islam ba,amma shiru kakeji nayi kuka nayi kuka har sai da na kwanta jinya wacce ta ɗaukeni tsawon lokaci kafin na warke. Nan ne kuma muka bar Maiduguri muka dawo nan Abuja. Shikuwa Alhaji Musa nemansa akayi akarasa daya sami labarin muna raye,kuma yasan yan fashin sun sanar damu shine ya sasu wannan aikin. Dan haka ya gudu ya bar garin. Kullum fatana Allah ya nuna min yata,yau gashi Allah ya nuna min islam, kuma ahannun ahalina Allah shine abin godiya " Mommyn Islam ta faɗa cikin hawaye tana shafa kan Islam. Kowa yayi shiru cikin dakin ita kawai ake sauraro,sai abban Islam dake gyada kai dan bai manta komai ba shima. Daga masu hawaye sai wanda suke kuka. Kowa ya tausayawa mommyn islam. Shidai Aslam ba abinda yake sai godiya ga Allah, ashe Islam matarsa jinin sa ce?yar uwarsa ya ga antyn sa mafi soyuwa aransa bayan mahaifiyarsa? Alhamdullah. Cikin kuka granny tace "lokacin dana tsinci takardar da kika barmin ba karamin tashi hankalina yayi ba,nan da nan na nufi bangaren A'isha na nuna mata takardar,duk da bansan me ta kunsa ba,amma nasan ba abin farin ciki bane,tunda na duba ɗakin ki banga ƙatuwar jakar ki ba,sannan ga sif abude. Kuka sosai nayi lokacin datake fadamin abinda letter ta kunsa. Nan take muka sanar da yayanki washe gari kuwa sai gashi. Haka mukayi ta nemanki guri_guri amma babu ke, nayi dana sanin ƙin amincewa da auren ku da Abubakar,dan haka na ɗora laifin duka akaina. Dana amince da auren da baki bar gudaba.gashi sai daga baya ma muka sami labarin Umar riƙaƙƙen dan duniya ne,mashayi mai bin mata. Tsabar bakin ciki da takaicine yasa muka bar garin nan muka dawo nan Abuja da zama,kullum cikin neman ki muke amma babu ko wanda yace mana ya ga mai kamar ki. Haka muka haƙura muka mikawa Allah lamarin mu,amma kullum ban fasa addu'ar Allah ya bayyana min keba"granny ta kai zancenta tana face majina. Ajiyar zuciya daddy ya sauke yana mai faɗin "ba abinda zamuce sai godiya ga Allah, daya nuna mana wannan rana mai cikeda tarihi arayuwarmu, Allah mun gode maka,sannan yanzu Abubakar ina labari shi musan?dan wannan mutumin bai kamata abarshi haka ba"cewar Daddy Yana kallon Abban Islam. Jinjina kai Aslam yayi cike da gamsuwa da abinda Daddyn sa ya ce,dole ahukunta Alhaji Musa. "Ai Alhaji tun daga wancan lokacin ban sake jin labarin Alhaji Musa ba,kuma nima ban neme shiba,kawai na barshi da Allah ne " Cewar Abban Islam. Nan dai sukaci gaba da tattauna wa akan abubuwan da suka faru a rayuwarsu,inda Islam ta basu labarin yadda Tata rayuwar ta kasance,sosai mommynta ke kuka,jin cewar yar ta ita kadai ta rayu cikin jeji,amma tayiwa Allah godiya daya kare mata ita. Ranar dai haka suka kai har bayan ishsha suna tare da juna. Inda Islam ta ce tare zasu tafi da iyayenta.ba wanda yace a'a dan kuwa kowa yasan yadda sukayi kewar juna. Aslam kuwa ji yayi kamar an buga masa guduma akansa,ta yaya zai iya kwana ba Islam akan ƙirjinsa?tab wllh saidai su tafi tare . Haka kuwa akayi lokacin da zasu tafi kawai sai ganin Aslam sukayi ya shiga gaban motar Hisham ya kame. Kallon sa mommy tayi tace "Aslam rakiya zakayi musu ne" Kallonta yayi kafin ya kalli Islam dake ƙoƙarin shiga motar . Kafin yace "a'a mommy Nima zan bi antyna ne dan nayi kewarta sosai"ya fada yana wani juya kai. Murmushi mommy tayi, dan ta gano shi tsaf. tace"Allah ya kiyaye hanya to" Haka suka tafi granny tana ta dagawa yarta hannu,tare da cewa lallai ta dawo goben kamar yadda tace. Dan basu gama ganawa da juna ba... Manage please . Ko editing banyi ba wllh,ban ma jima da dawowa daga asibiti ba. Anty mammy ce. [10/20/2022, 8:03 PM] Abk: 65/66 ______________Har suka bace granny bata daina ɗaga musu hannu ba,ji take kamar ta bisu can gidan nasu,dan gani take kamar idan sun tafi bazasu kara dawowa ba. Saida daddy yace "to hajiyata mu koma gida sun tafi ai"ya fada yana ɗan murmushi. Kwalla granny ta share tana mai cewa "kayya dan nan,gani nake kamar idan sun tafi bazasu sake dawowa ba"ta faɗa da yanayin damuwa. Murmushi daddy da mommy sukayi kafin mommyn tace "karki damu Hajiya,ai Saratu ta dawo kenan muna tare da ita har abada,kuma goben nan zata ƙara dawowa ku wuni tare "mommy ta faɗa cikin murmushi tana kallon granny. Murmushi granny ma tayi tana kallon mommy kafin tace "daɗi na dake wllh Aisha wani lokacin kina da hankali da iya magana,kinga yanzu bakiji yadda hankalina ya kwanta ba, sakamakon wannan maganar taki. amma wani lokacin saidai kawai ayi miki uzuri"granny ta faɗa tana nufar cikin gidan tinkis _tinkis da mayafinta a Hannu. Kallon juna mommy da daddy sukayi,kafin sukayi yar dariya marar sauti,dan kuwa idan da sabo sun saba da halin granny. Su Islam kuwa, Suna zuwa gidan suka firfito daga cikin motar,cike da tsantsar farin ciki suka shiga cikin gidan,hannun Islam riƙe dana mommyn ta.gaba dayansu ji suke kamar an musu albishir da gidan aljanna. Afalo suka yada zango,bayan sunyi sallah suka gabatar da cin abinci.nan aka zauna aka sake kafa sabuwar hira.yau kam har Abba aka zauna zaman wannan hirar. Sosai Abba yayiwa su Islam da Aslam nasiha akan zaman aure,sai wajen sha dayan dare kafin yayi musu sallama ya shige part ɗinsa. Aisha kuwa tuni tayi barci tana nata dakin. Nan mommyn ta nunawa Aslam ɗakin da zasu kwanta shida Islam,wanda tuni aka gyara shi sai ƙamshi ke tashi cikinsa. Mommy ma sallama tayi musu ta wuce turakar Abba. Ya rage daga Islam sai Hisham da Aslam. Aslam sai wani narkewa yake yana marairaicewa akan Islam ta tashi suje daki dan su kwanta. Islam kuwa maƙale kafada tayi tare da kashe masa ido ɗaya taci gaba da hirarta da ƙanin ta. Da abin ya ishi Aslam, saiya haɗe fuska ya kalli Hisham,cikin muryar manya da nuna ba wargi yace"kai tashi ka tafi dakin ka,dare yayi"ya fada idonsa akan Hisham. Dan sosa kai Hisham yayi yace "wai da yaya so nake idan ɗaya ta kusa saina je na kwanta,wllh ban gama ganawa da ƴan uwana ba ne jinake kamar mu kwana anan"Hisham ya fada cike da neman magana,dan yana kula da duk abinda Aslam yake yiwa Islam ɗin. Wata uwar harara Aslam ya ballawa Hisham yace"malam tashi ka tafi dakin ka,ka wani zo ka hanani sakewa da matata,wai sai daya,saika zauna kai kadai ka akai dayan ko ka kwana"Aslam ya fada yana tsare Hisham da manyan idanunsa. Murmushi Hisham yayi,kafin ya mike yana ɗan sosa keya yace "sister sai da safe,ma ƙara sa hirar,dan naga yaya barci yakeji sosai"ya fada yana ɗan dariya kasa-ƙasa yana kallon Aslam. Islam ma dariya tayi tana kallon Aslam. Shikuwa hararar Hisham yayi yace "ka jira na kamaka agurin nan,zakaga barci nake ji"ya fada yana mikewa. Ai da gudu Hisham yayi ɗakinsa yana dariya. Juyowa yayi yana kallon Islam,wacce ta wani gyara kwanciya akan kujera tana lumshe ido,sarai ya gane nufin ta ,anan take son tace zata kwanta.dan haka ko kulata baiyi ba ya durƙusa ya sureta yayi dakin da zasu kwana da ita. Turo baki Islam tayi tana mai cewa"nifa ba anan zan kwana ba"ta faɗa tana ƙoƙarin sauka daga kan gadon. Da sauri Aslam ya maidata tare da zama kusa da ita ya rungumeta ta gefe,ahankali ya sanya hannunsa yana shafa soft lips ɗin ta,kafin yace "wai meye ne yau naga kina wani jamin aji?inaga fa dole sai na nuna jaruntata ayau,dan na tsinka ajin nan"Aslam ya fada yana ɗora bakinsa kan na Islam. Sosai Aslam ya zage Yana saukewa Islam hadda, gaba dayansu sun fice daga hayyacin su,Aslam Ya gigice sosai da irin salon da Islam ke nuna masa yau,cikeda buƙatuwa yake ƙoƙarin angoncewa, saidai ƙam yaji Islam ta riƙe hannunsa tana girgiza masa kai,alamun a'a. Cikin ɗimuwa da buƙatuwa yace "why Islam ?me yasa bazaki barmu muji daɗin auren mu ba?meyasa kike azabtar da zuciya da gangar jikin mu?Please kiyi hakuri ki bari na samu nutsuwa dake,wllh idan kika barni haka zan shiga wani hali"Aslam ya fada cikin wata irin murya mai kamar zaiyi kuka.banda tsuma ba abinda jikinsa keyi. Ita kanta Islam tana tsananin bukatar kasancewa dashi,saidai har yanzu bai cika sharuddan da zai sa ta amince masan ba,bata san menene cikin zuciyarsa game da ita ba,bata sani ba ko iya jikinta yake so,dan haka tayi alkawarin bazata bari ya kusanceta ba,har sai ranar daya furta mata kalmar so da kansa. Dan haka cikin sauri ta tashi tare da janyo rigarta ta sanya tace "kayi hakuri bazan iya mallaka maka kaina ba"ta faɗa cikin sanyin murya. Da ƙarfi aslam ya runtse idanunsa,yana jin wani irin zafi cikin zuciyarsa,me yasa Islam zatayi masa haka?shin bata san irin azabar da yake ji bane? Ahankali ya buɗe idanunsa da suka gama rinewa yace"Please Islam ki taimaka min awannan halin da nake ciki komai zai iya faruwa dani,ki daure ki bani hakkina dake kanki nifa mijin kine kuma kinsan ina da hakki akanki"Aslam ya fada cikin yanayi na marairaita yana riƙe mararsa. Girgiza kai Islam tayi tare da saukowa daga kan gadon ta nufi ƙofa "kayi hakuri bazan iya ba"tana faɗin haka tayi waje. Hannu Aslam ya dunkule tare da kaiwa bango naushi.ji yake kamar ana zazzaga masa fetur acikin zuciyarsa.sosai ransa yayi matuƙar ɓaci,wani irin haushin Islam yayi masa dirar mikiya. Wato bata damu ba, koma meye zai sameshi ya sameshi ko?shine tayi ficewar ta ta barshi cikin wannan halin? In sha Allah daga yau,bazai ƙara neman hakkinsa agurin ta ba,taje tayi duk abinda zatayi dashi.duk lokacin dataga dacewar ta bashi ,ta bashi dan kanta. Tsabar ɓacin rai nan take yaji baya jin sha'awar ma ahalin yanzu,wanda kafin wannan lokaci ji yake kamar zai mutu dan sha'awa. Bayi ya shige ya watsa ruwa kafin ya dauro alwala yazo ya kwanta,zuciyarsa cike da jin haushin Islam. Islam kuwa dakin A'isha ta shige ta kwanta bayan ta. sosai take jin ba dadi cikin ranta,tasan bata kyauta ba abinda tayi,amma dai tana da nata dalilin nayin hakan. Tana kwance amma zuciyarta tana gurin Aslam,tunani take ko wane hali yake ciki yanzu?ko yaji haushin ta akan abinda tayi masa? Juyi tayi ahankali tare da janyo A'isha ta rungumeta ajikinta. dan ko kaɗan bata jin dadin kwanciyar,ta riga ta saba kwana akan kirjina Aslam. Haka tayi ta juyi sai can barci yayi gaba da ita. Shima dai Aslam anashi bangaren hakan ce ta kasance,sai juyi yake yana tsaki, ƙoƙarin cire tunanin Islam yake daga zuciyarsa,amma ya kasa ko yaya ya juya ita yake ji ajikinsa,daga karshe ma tashi yayi ya dauro alwala ya kama nafila,san can cikin dare shima barci yayi gaba dashi. Washe gari kuwa da sassafe ya bar gidan,inda ya sanar da mommy akwai wani meeting daya taso masa na gaggawa shiyasa ,zai tafi. Islam kuwa makara tayi kasancewar week end ne ba school,gashi ta jima batayi barci ba,dan haka sai wajen bakwai ta tashi. agurguje tayi wanka tare da alwala,bayan tayi salla ta tashi A'isha itama tayi,sai murna A'isha take ganin tare suka kwana da natyn ta. Kai tsaye Islam ta fito falo,idonta akan dakin da Aslam yake,so take taje taga ya ya kwana,amma tana jin nauyin yin hakan. Dan haka kitchen ta bi mommy bisa rakiyar A'isha. Bayan sun gaisa ne Islam ta tsaya tana kallon mommy tana ta ƙoƙarin haɗa breakfast. Kallon ta mommy tayi kafin tace "Islam bazaki tayani aikin ba"ta fada fuskarta ɗauke da murmushi. Ɗan zaro ido Islam tayi kafin tace"tab Ni kuwa mommy me na iya?nida saidai kawai inga abinci a ajiye,aikina kawai ci"ta faɗa tana ɗan taɓe baki,idonta akan mommy. Murmushi mommy tayi kafin tace "aikuwa dole ki koyi girki, kodan mijin ki,bazai yiwu ace kullum saidai kuci na gida ba,wani lokacin yana buƙatar girkin matar sa shima,dan haka matso ki gani" Tare da Islam dai mommy sukayi girkin nan,Islam sai murmushi take tana jin dadi,ashe haka yin girkin yake da daɗi?aikuwa zata dage da kowa . Lokacin da Islam tasan tun safe Aslam ya bar gidan, abin baiyi mata daɗi ba,kuma tasan haushinta yake ji,duk sai taji haushin kanta takeji,meyasa ta tafi ta bar dakin?koba komai data tsaya ta rarrasheshi ai,tunda dai kusan koda yaushe hakan ce ke faruwa. Haka suka gama komai suka rankaya gidan mommy. Husna ce zaune kusa da mahaifiyar ta,tana mata bayanin yadda zatayi amfani da maganin data karbo daga gurin boka.gefe guda mahaifinta ne shima yana sauraron bayanin da ake mata. "Ki tabbata ya shaƙi ƙamshin wannan turaren,sannnan karki sanya wannan kwallin sai kinyi gab da shiga gidan,da zarar kin sanya, to ki sunkuyar da kanki ƙasa,karki yarda ki kalli kowa sai kinji Muryar Aslam. Shikuma da zarar ya shaƙi wanan turaren zaiyi ya son ku haɗa ido dashi,da zarar kun haɗa ido kuwa shikenan aiki ya gama,kuma shida matar nan tasa sai wulaƙanci da cin mutumci,ke kuwa,sai batun aure,dan boka ya tabbatar min da cewar har yanzu bai tara da matar tashiba, ke kuma da anyi auren ku,kiyi duk yadda zakiyi ki hanashi kusantar matar dan kuwa duk lokacin daya kusanceta,shikenan asirin zai lalace,kuma sakinki zaiyi boka ya fadan hakan"ta kai aya tana mikawa Husna wasu kwalabe guda biyu. Karba Husna tayi cike da farin ciki tana mai rungume mahaifitar Tata tace"kai mommy wllh kin gama min komai arayuwa,In babuke bansan ya zanyi ba ,na gode sosai mommyna"ta faɗa tana dariya . Mahaifin ta yana zaune sai murmushi yake,shi kansa yana jin dadin yadda matar tasa ke kula da al'amuransa, da zarar abu ya shige masa duhu,tana zuwa gurin bokanta shikenan lamari ya zo karshe. Tashi Husna tayi tace "bari naje na shirya mommy "ta faɗa tana nufar ɗakinta da gudu rigija -rigija da uban nonuwa kamar kayan wanki. Suna zaune gaba dayansu afalon,ana ta hira,kowa na gidan yana cikin Falon in Banda daddy da yayi fitar sassafe,sai kuma Aslam,hankalin Islam gaba ɗaya yana can wajen tunanin ina Aslam Yayi?tashi tayi tsam ta nufi part dinsu ba tare da sun fargaba.dan ta kasa jurewa rashin ganin Aslam ɗin. Tana shiga part ɗin taji kamshinsa mai sanyin daɗi,lumshe ido tayi tana mai sakin murmushi,tasan yana ciki.ahankali ta taka zuwa cikin dakin nasu. Da sallama ta tura ƙofar dakin ta shiga. Yana kwance ,ya bawa kofar baya,yana sanye da dogon wando da riga kanana kayane masu kyau , kallo ɗaya idan kayi masa zakayi tunanin barci yake,nan kuwa idonsa biyu,yana jin sallamar Islam yaji wani sanyi cikin ransa,amma so yake ta nuna mata yayi fushi da ita.dan haka yayi kamar barci yake. Sallama Islam ta sake yi amma taji shiru. Ahankali ta taka cikin sanda ta nufi inda yake,leƙa fuskarsa tayi,taga barci yake. Ahankali ta sauke ajiyar zuciya tana mai bin fuskarsa da kallo,masha Allah Aslam ba karamin kyakykyawa bane,komai nashi kwanin burgewa,hannunta ta daga da nufin shafa fuskarsa,amma saita maida hannu.tayi haka kusan sau uku,kafin ta daure ta ɗora hannunta kan sajensa tana shafawa ahankali.kallon lips ɗin sa tayi wanda suka yi pink sosai kamar ya shafa janbaki,ahankali ta furta "so cute "kafin ta Dora baƙinta ahankali Kan nashi bakin tayi masa kiss ahankali . Saura kaɗan Aslam ya fallasa kansa ,saboda yadda kiss din nata ya shiga jikinsa,amma ya daure.kallonsa taci gaba dayi tana murmushi,kafin ta mike ahankali cikin sanda zata bar dakin. Carab !!taji an riko hannunta.zaro ido tayi sosai gabanta na mugun bugawa,badai idonsa biyu ba?ya Salam"ta faɗa tana runtse idanunta da ƙoƙarin zare hannun ta. "Ina kuma zaki?bayan naga kamar baki gama abinda kikeyi ba"ta tsinkayo muryar Aslam. Dafe ƙirji tayi da sauri, shikenan wllh yana jin duk abinda nayi masa,wayyo ni islam ya zanyi da kunya?ta faɗa tana mai runtse idonta sosai. Jawo ta Aslam Yayi ta dawo gabansa,ƙureta yayi da ido,yana kallonta,sosai yake jinsa cikin nishadi idan yana kallon fuskarta.islam kuwa ta kasa bude idonta bare ta kalleshi. Ahankali ya ɗago fuskarta yana kallon bakinta.ji yake kamar yayi ta kissing dinta,Amma yayi alƙawarin sai lokacin da taso hakan da kanta. "Buɗe idonki"ya fada cikin muryarsa mai daɗin sauraro. Ahankali Islam ta buɗe idonta ta sauke akan fuskarsa. Murmushi yayi mata kafin yace"meye najin kunya? dan kinyi kissing lips ɗin mijinki?ko laifine yin hakan?ya fada yana saukowa daga kan gadon, dan idan yaci gaba da zama kusa da ita,to tabbas zaiyi watsi da alwashin daya dauka. Turo baki Islam tayi tace "nifa dama zuwa nayi in faɗa maka mommy tazo"ta faɗa tana wani ƙaryar da wuya. Murmushi yayi yana mai kama hannunta yace "to muje can ɗin" Tare suka fito riƙe da hannun juna,suka nufi part din su mommy. Suna bude kofar falon ,wani irin ƙamshi ya doki hancin Aslam,Wanda nan take yaji kansa yayi mugun sarawar da saida ya dafe kan nashi yana mai runtse idonsa. Kallonsa Islam tayi tace "lafiya"tana kallon yadda lokaci ɗaya yanayin fuskarsa ya sauya. Girgiza kansa yayi yace "ba komai muje" Haka kawai yaji yana son ganin Husna, yau ɗaya,wacce shi yama manta da ita sam,amma yau kam ji yayi yana son ganinta. "Ya aslam ina kwana"yaji muryar Husna ta doki dodon kunnen sa. Da sauri ya kai kallonsa inda take zaune,aikuwa carab,idanunsu suka sarke cikin na juna. Wani irin abu yaji ya cakeshi cikin ƙahon zuciyarsa,lokaci guda ya daina ganin kowa agurin sai Husna. Nan take yaji wata muguwar soyayyar Husna ta shiga zuciyarsa,ba shiri ya saki hannun Islam yayi gurin da Husna ke zaune yana sakar mata murmushi. Cike da mamaki Islam tabi hannun ta daya saki da kallo,kafin ta bishi da kallo shima. Wacece wannan ɗin ? Islam ta faɗa cikin wani irin zazzafan kishi,tana kallon yadda Aslam ya zauna kusa da husnan. To fa muje zuwa masu karatu. Nagode sosai da addu'ar ku gareni, alhamdullah naji sauki sosai,Allah ya bar kauna. Anty mammy ce. [10/22/2022, 12:42 PM] Abk: 67/68 "Wacece wannan ɗin" Islam ta faɗa cike da wani irin zazzafan kishin da taji ya taso mata lokaci ɗaya.tana kallon Aslam wanda ya zauna kusa da Husna yana sakar mata ƙayataccen murmushi. Cikin haɗe rai Islam ta karasa cikin Falon,ta zauna kusa da mommynta ba tare da tace komai ba,saidai kallo ɗaya zakayi mata kasan ranta abace yake. Su mommy kuwa hirarsu suke hankali kwance,basu kawo komai aransu ba dangane da zaman da aslma yayi kusa da Husna, Aslam kuwa ji yake kamar ya maida Husna cikinsa,dan wani irin so da kauna yaji yana yi mata marar misaltuwa. Kafeta yayi da ido yana kallonta,ita kuwa cike da kissa ta ɗago idanunta tana kallonsa tare da yi masa fari da ido tace "kai yaya Aslam ya haka da kallo ?"ta faɗa tana wani juya ido kamar mujiya. Shikuwa Aslam ji yayi kamar wanda ta jawo zuciyarsa,wani irin kyau yaga ta ƙara masa cikeda wata murya mai dauke da tarin ƙauna da shauƙi yace"badan kar kice nayi karya ba,sai ince ban taba ganin macen data kaiki kyau ba,ke ɗin ta musamman ce domin sosai nake kinji cikin raina"Aslam ya fada yana aika mata wani sihirtaccen kallo mai cike da ma'anoni kala-kala. Wani irin dadine ya cika zuciyar Husna, lallai aikin boka yayiDomin ga alamu nan sun nuna hakan,dubi yadda Aslam mai ji da kai da rashin sakin fuska,yake ta zuba mata tsadajjen murmushinsa?kuma agaban matar sa,wayyo daɗi. Cike da kissa tace "kai yaya Aslam Banda zuga fa?niɗin ina naga wani kyau?kawai dai kana fadane dan naji daɗi"ta faɗa tana kafe shi da ido. Murmushi ya sake yi akaro na barkatai,kafin ya gyara zama yana kallon ta,cike da kallon ƙauna yace "ai Ni a idona kinfi kowa kyau,kuma bana ganin kowa sai ke,dan haka zanzo gidan ku ma anjima sarauniya"ya fada yana mai jin wani sonta na ƙara shiga zuciyarsa.yayin da agefe guda kuma yake jin wani ƙunci acikin zuciyarsa. Saura kaɗan Husna ta sanya ihun tsabar murna,lallai tsafi gaskiya ne,yanzu da mommyn tasan da wannan aikin,ta barni nake ta shan wahala da soyayya?Husna ta fada cikin zuciyarta. Tana mai kallon Aslam kamar ta cinyeshi take ji dan so. Duk abinda sukeyi,hankalin Islam na kansu,wani irin tuƙuƙin baƙin ciki ke azabtar da zuciyarta,ji take kamar zata kama da wuta,wannan wane irin cin fuska ne Aslam ke mata?gaba ɗaya yama manta cewar tare suka shigo falon,kuma agabanta yake fadawa wannan banzar irin wannan kalaman?domin duk abinda suke fadi akan kunnen ta,dan sam bata sauraron abinda su mommy ke faɗi.wacece wannan matar wai?meye alakarta da Aslam?ga dukkan alamu dai sun jima da sanin juna,kuma daga yadda suke kallon juna zaka fahimci masoya ne na hakika, tab lallai akwai babban rikici kenan. Ahankali Islam ta sauke wata ƙaƙƙarfar ajiyar zuciya,lokacin da Husna ta mike Aslam ma ya mara mata baya,sallama tayiwa su mommy cike da kunya, Amsawa sukayi tare da cewa ta gaida mommyn ta. To tace tana mai sunkuyar da kanta. Kafin ta matso kusa da inda Islam ke zaune,murmushi tayi sannan ta kalli Islam tana mata murmushin nata na rainin hankali tace"yan mata ykk"ta faɗa tana daga mata yan yatsun ta biyu. Wani kallon zanci uwarki ,Islam tayi mata tare da sakin tsaki mai ƙarfi ta kawar da kanta.murmushin jin dadi Husna tayi tana faɗin,yarinya bakiga komai ba,saima na shigo gidan nan,wllh saina hanaki shan ruwa,bakin ciki saiya kasheki da irin abubuwan da zaki gani. Azahiri kuma kallon Aslam tayi wanda ya kafeta da ido kamar zai cinyeta tayi,kafin tace " ya Aslam wannan yarinyar fa?ba sanya agidan nan ba"ta faɗa tana kallon Islam . Kallon Islam shima yayi kafin ya dan taɓe baki yace "ƙanƙara ce karki damu da ita" ya fada idonsa akan ta. Murmushi tayi tana mai kashewa islam ido ɗaya tace "ok bari na tafi ya Aslam kar mommy tace na dade,dama zuwa nayi mu gaisa kuma na ganka"ta faɗa da ɗan daga murya yadda Islam zataji. Aikuwa tajin, gabanta banda faduwa ba abinda yake,kallonta takai ga Aslam jin amsar da ya ba husnan. Dakuma wacce yake bata yanzu. "Muje to na madam na rakako da kaina,dan bana son ki wahalarmin da kanki,amaryata"yana faɗin haka suka yi waje. Binsu Islam tayi da ido kamar wata zautacciya,amarya ?amarya kuma ?shine abinda take ta nanata wa cikin zuciyarta. Gaba ɗaya ta nemi nutsuwarta ta rasa, ita Bama ƙanwar tashi ɗaya ce bane ya fi daga mata hankali, kamar kalmar amaryata. kallon su mommy tayi banda hira ba abinda suke,su sam basu san wainar da ake toyawa ba. Ahankali ta yunƙura ta bi ƙofar da zata sadaka da part ɗin su ta bar falon. Tana zuwa ta shige cikin dakin nasu ta kwanta.wani irin zafi zuciyarta keyi,wanda bata san lokacin data fashe da wani kuka mai ban tausayi da tsuma zuciya ba. Meyasa Aslam zaiyi mata haka?me yasa zai fifita son wata?, agabanta yake nuna zallar kulawa da soyayya ga wata?koba komai yayi mata kara,duk da tasan dama ba sonta yake ba,ya fadi hakan abaya yafi aƙirga,amma saboda rashin wayo da hankali irin nata,har ta bari soyayyarsa ta shiga zuciyarta.jin daɗinta ɗaya ma da bata mallaka masa jikinta ba,da shikenan ya cutar da ita ta ko ina. Kuka take sosai akan gadon nasu ta tura kanta cikin fillow,ba abinda take ji cikin zuciyarta face tsanar wannan matar mai manyan nonuwa kamar guga. Shikuwa Aslam saida suka jima suna tattaunawa da Husna, kafin ya buɗe mata mota tashiga.yana jadda da mata zuwanshi anjima. Ita kuwa sai wani rawar kai take da zumuɗi,haka sukayi sallama ta ja motar ta bar gidan. Tsaye Aslam Yayi agurin yana bin sawun tayoyin motar Tata da ido,wani yanayi yake ji cikin zuciyarsa marar daɗi,sannan yana tunanin kamar yayi wani abu ba daidai ba. Ahankali ya dafe kansa dake sara masa kaɗan -kaɗan,kai tsaye ya nufi part ɗinsu Dan ya Dan kwanta. Yana shiga ɗakin ya jiyo shashshekar kukan Islam,gabansa ne ya fadi sosai,dan sai lokacin ya tuna da ita. Kuma yasan tare suka shiga part din mommy Amma bazai iya cewa ga lokacin da suka rabu da juna ba. Da sauri ya karasa bakin gadon tare da zama kusa da ita sosai,cike da karaya ya sanya hannun sa ya dagota gaba ɗaya yana kallon ta. Islam ma buɗe ido tayi, jin an tabata, karab idanunta ya sauka akan na Alsam, wani irin mugun haushinsa taji ya darsu cikin zuciyarta. Dan haka azafafe ta fizge jikinta daga nashi tana mai balla masa harara kamar idanunta zasu faɗo. Mika hannu yayi da nufin sake kamota,tayi saurin ja da baya tana faɗin"karka sake ka tabani wllh,kaje can ita da take da muhimmancin daya fi nawa ka taba ta,amma bani ba"ta faɗa cikin muryarta dake rawar kuka. Kallonta Aslam Yayi tare da sassauta murya yace "Please mana Islam menene kuma?me nayi miki?ya fada cikin marairaita kamar zaiyi kuka,dan shi wllh yama manta menene abinda ya faru,bare yasan wane laifin yayi mata,dan yasan duk abinda ya sanya Islam kuka haka,to babbane. Wani shegen kallo Islam ta wurga masa cike da jin haushinsa tace "ban sani ba nima,nace ka gyaleni dan Allah wai dole ne saika kulani?kaje can ku ƙarata da waccan mai nonuwan kamar guga,amma wllh karka sake damuna mugu kawai"ta fada tare da juya masa baya tana ci gaba da kukanta.babban abin ahushinta maimakon taji ta daina sonshi,sai kawai takejin wani irin sonsa na fizgarta jima take tana bukatar ya rungumeta ajikinsa. Kallonta Aslam yake cike da wani irin tausayinta,sosai yake jin ba daɗi yadda take kukan nan,shi baisan me yayi mata ba bare ya bata hakuri. Ahankali ya haura kan gadon zuwa inda take,zama yayi abayanta tare da sanyata atsakanin cinyoyinsa,kafin ya sanya hannunsa ya rungumo ta baya. Kansa ya dora akan kafafunta tare da sauke ajiyar zuciya yace "am sorry Islam,koma me nayi miki kiyi hakuri,bada sanina bane bani da burin sanyaki cikin damuwa ki yafe min Islam am sorry"ya fada Asaitin kunnenta . Runtse idonta tayi da ƙarfi tana sakin ajiyar zuciya,so take ta kwace jikinta amma zuciyarta sam ta ƙi bata goyon bayan yin hakan. Sai kukan data sake saki marar sauti. Shikuwa Aslam har cikin ransa yake jin kukan nata,ƙara rungumeta yayi sosai ajikinsa,yana mai kissing ɗin dokin wuyanta cikin ƙoƙarin sa na mantar da ita damuwar dake ranta. Lumshe ido Islam tayi tana mai jin yadda yake kissing ɗin wuyan nata so romantic,ta so ace hakan na faruwa ne da dinbin soyayyarta cikin zuciyarsa,sai dai kash!!! Ba soyayyarta azuciyarsa ko kaɗan,yana son yin amfani da damar sa ne dan samun biyan buƙatarsa. Tunanin hakan da tayi yasa ranta ya ƙara ɓaci, Da sauri ta tureshi daga jikinta tare da sauka daga kan gadon tayi waje. Binta kawai yayi da ido,lallai akwai Abinda ke damunta, kuma yana da alaƙa da shi.amma to menene haka yayi mata?wanda ya ɓata mata rai sosai har tayi fushi? Falon ya fito yaga ko nan ta koma amma sai yaga ba kowa cikin Falon.dan haka ya koma cikin dakin ya kwanta. Islam kuwa kai tsaye tana fitowa tayi garden,can taje ta haye kan bishiya tare da rungumar janbu ajikinta. lallai soyayya masifa ce,lokaci ɗaya ta sanya Islam tayi wani laushi ta koma kalar tausayi sosai. Da gudu Husna ta shiga cikin ƙaton falon nasu tana kwalla kiran sunan mommynta. "Mommy !mommy!!mommy!!!har sau uku. "Mommy wai kina ina ne ?kizo kiji abin daɗi da sanya farin ciki,wllh aikin boka yana ci.mommy na kusa zama matar aure" Husna ta fada tana rungume mommynta data ke saukowa daga saman bene, sakamakon kiran yar Tata datajiyo. Cikin farin ciki mommy ta rungume yar Tata tana faɗin"Ni dama na san Indai kinyin aikin nan dai-dai,to ba Aslam ba, ko ubansa ne wllh sai ya soki,fadamin ya akayi?"cewar mommy cikin dariya tana zama kan kujera tare da kama Husna ma ta zauna. Dariya Husna tayi tare da faɗin"wllh mommy bakiga yadda Aslam ya ruɗe ba,gaba ɗaya kamar wani sakarai ya koma daga ganina,agaban matar sa fa, ga su mommy Amma ya bar matar yayi gurina ya zauna kinga yadda yake rawar ƙafa?kuma bawanda ya ce wani abu,ke mommy da yamma ma zai zo yace"Husna ta kai zancenta tana buga cinya da taɓe baki cikeda farin cikin samun nasara. Dariya mommy tayi tana mai cewa"ai ba wanda zaice wani abu dama,dan dukkan su saida nasanya boka ya rufe musu baki akanki,koda anyi auren ma,sai yadda kikaso zakiyi agidan,saidai ki kula dan boka yace itama matar tashi hatsabibiyar kanta ce,asiri baya cinta,sannan idan ta fiye kebewa da Aslam ɗin ma,to na jikinsa ma karyewa zaiyi" "To mommy yaushe zan barsu su kema ɗin ma? ai wllh kullum muna tare dashi bazan bari ko dakin ta ya shiga ba,mommy afara shiri dan Allah anjima zai zo fa"Husna ta fada tana mikewa tsaye,bari nima naje na fara shirin tarbar masoyi"ta faɗa tana nufar ɗakinta da gudu rigija-tigija. Dariya mommyn tayi tana mai jinjinawa aikin boka,tace "ai wllh na yarda da boka dari bisa dari,duk abinda ya faɗa tabbas saiya tabbata. Sai wajajen azahar sannan Islam ta dawo part din nasu,shima salla take son yi,ta ɗanyi wanka. Lokacin data shigo Aslam Yana kwance yana barci.kasancewar yanayine na sanyi,hakan yasa Aslam ya dan takure jikinsa. Kallonsa Islam tayi tana jin wata zazzafar kaunarsa na ratsata,har zata wuce,amma ta kasa ganin yadda ya takure jikinsa, ta gane sanyi yake ji. Dan haka ta dawo kusa dashi tare da ɗaukar ƙaton bargo ta lullubeshi sannan ta wuce toilet. Wanka tayi tare da ɗauro alwala.agurguje ta shirya cikin doguwar riga ta atamfa ko sallar bata tsaya yiba,dan bata so ya farka daga barcin ya ganta. Part din mommy ta wuce ,anan tayi sallar ta sannan ta zauna sukaci abinci tare da ci gaba da hira da mommynta da granny. Aslam kuwa yana cikin barci yaji kamar wanda aka soka masa mashi cikin zuciyarsa,azabure ya farka yana kiran sunan husna. Hakan kuma ya faru ne sakamakon kiran sa da mommyn Husna tayi ,ta cikin wata kwaryar tsafi da boka ya bata. Cikin azama ya tashi ya shiga toilet,wanka yayi agurguje yayi Sallah,sannna ya shirya cikin wata ubansu shadda mai kyau da tsada. Yayi kyau sosai sai ƙamshi yake zubawa. Part din mommy ya nufa cikin hanzari, Duk suna falon azaune suna hira. Mommyn Islam ce ta ce"kai mashá Allah dana,daga nan sai ina kuma ?irin wannan kyau haka?"ta faɗa cikin murmushi. Murmushi Aslam Yayi shima kafin yace "wllh antyna gidan su Husna zani, shine nake sauri kartayi ta jirana. Dammmmm!!!gaban Islam ya buga da karfi,har saida ta dafe ƙirjin nata .ɗago kai tayi ta zubawa Aslam ido, shikuwa ko kallon ta ma baiyi ba. Ɗan jimmm mommyn Islam tayi kana kallonta kasan bataji daɗin amsar daya bata ba,amma saitayi murmushi tace "to agaisheta "ta faɗa tana kallon Islam. Wacce tayi kasaƙe tana kallon Aslam ɗin.sosai taji tausayin yar tata ya kamata,dan abinda ba dadi sam. "Mommy na wuce saina dawo"Aslam ya fada yana kallon mommyn sa. "To Aslam ka gaidamin da ita sosai,da mommynta"ta fada tana cin apple. Da mamaki Islam ta kalli mommy,kenan da saninta ma Aslam din zai tafi zance? Bata gama wannan mamakin ba taji granny na faɗin"yarinyar kirki mai kunya ba,nima kace Ina gaisheta sosai,sai mun zo" To kawai Aslam ya iya furta wa dan tuni yayi bakin ƙofa cikin sauri. Kallon juna Islam sukayi ita da mahaifiyarta,wacce ke kallon yar Tata tun ɗazu cike da tausayawa. Lumshe ido mommyn Islam tayi tana mai ƙoƙarin kwantar wa da yar Tata hankali tace"Islam baki nuna min dakin naki ba fa !maza tashi muje ki nuna min"ta faɗa tana kamo hannun Islam ɗin.wacce ke zaune kamar butun-butumi. Binta kawai Islam keyi amma zuciyarta kwata -kwata bata tare da ita. Su granny kuwa sai hirar Husna suke da yaba halinta. Muje zuwa. Mrs babi ce Anty mammy. [10/24/2022, 11:41 AM] Abk: 69/70 Suna zuwa part din su Islam,mommyn ta ta zaunar da ita akan kujera,kallonta tayi cike da tausayawa,itama Islam kallon mommyn nata takeyi, tana ji kamar ta kurma ihu. Cikin kwantar da murya mommy ta fara magana tana shafa kan Islam. "Islam ita rayuwa da kike gani a sannu ake bin komai,kuma ba duk abinda mutum ke so yake samu ba,ki zamo mai juriya da kawaici akan dukkan al'amuranki,sai kiga kinci ribar abun nan gaba,kada ki bari wani abu ya sanya kiji haushin mijin ki ko yaya ne,yana da dama da ikon yin duk abinda yake so,domin addini ya bashi wannan damar. Ko menene zai faru kada ki damu kanki, kiyi ta addu'a komai yayi zafi maganin sa Allah,kuma idan kika mikawa Allah lamarin ki,zakiga nasara arayuwarki"mommy ta kai ƙarshen zancenta tana mai kallon Islam. Ahankali Islam ta sauke wata ƙaƙƙarfar ajiyar zuciya tare da kama hannun mommyn ta tarike cikin nata, murmushi takeyi,amma kana gani kasan na karfin hali ne,to ta yaya ma zata iya kwantar da hankalin ta?ta yaya zata kai zuciyar ta nesa?sam koda tayi ƙoƙarin yin hakan,bazata iya ba,amma zatayi duk maiyi ta takura zuciyarta wajen kawar da kanta akan duk abinda Aslam zaiyi.dan haka cikin murmushi take cewa"na gode mommy,kuma in Sha Allahu zanyi amfani da duk abinda kika faɗa min"ta faɗa hakan cike da kwarin gwuiwa. Murmushi mommy tayi tace "da kyau ƴata, Allah yayi miki albarka ,ya kare ki da dukkan nin sharrin abin ƙi"cewar mommy cike da jin daɗi. "Ameen mommyna" Islam ta fada. Nan Islam ta fara nunawa mommy part din nasu,albarka ta sanya musu kafin suka koma can part din mommy sukaci gaba da hira. Kasancewar Aslam gudu yayi ahanyarsa ta zuwa gidansu husna,dan ji yayi kamar ana azalzalar zuciyarsa dan yaje ga husnan.hakan yasa bai wani jima ba ya isa. Yana zuwa dama tuni an sanar da mai gadi zuwan nashi,dan haka kai tsaye ya wangale masa ƙofar get ɗin ya shiga. Husna najin ƙarar motar tayi wani uban tsalle tana ƙara duba kanta cikin madubi. Tana sanye cikin wata matsatstsiyar doguwar riga,Wacce ta kama jikinta sosai,dagyar take nunfashi,ga uwar zugudar ta nan tayi shirim acikin rigar. Cike da ɗoki ta ce "mommy yazo wllh kinji ƙarar motar sa can "ta faɗa cikin tsantsar farin ciki tana kallon mommyn ta dake zaune bakin gado,hannun ta riƙe da wata yar kwallaba da wani kalar ruwa blue aciki. "Ke dalla ki kama kanki mana,ko so kike ya gane dama kin ƙagu yazo gareki ne?maza ungo wannan turaren ki shafa agoshinki da tafin hannun ki"cewar mommyn Husna tana mika mata kwalbar. Karba Husna tayi cikin rawar jiki ta buɗe ta tsiyaya ta goga akan goshinta cikin sauri,dan Allah-Allah take taje gareshi. "Mommy bazaki gane bane wllh,ina cikin farin ciki ne,dan ina ƙaunar Aslam sosai araina"ta faɗa tana mike mata kwalbar,bayan ta gama shafawa. Wayar ta ce ta fara ƙara alamun ana kira.da sauri ta zari wayar tana murmushi. "Mommy kingani harya kira "ta faɗa tana dagawa . "Barka da isowa jarumina" Ta fada tana wani fari da ido kamar tsohuwar karuwa. Acan bangaren kuma Aslam ji yayi kamar ya suma dan daɗin jin muryarta,cikin zaƙuwa yace "kiyi hanzarin fitowa,dan nayi tozali da kyakykyawar fuskar nan taki ko naji daɗi cikin raina" Wani shegen daɗi ne ya mamaye zuciyar Husna cikeda zumuɗi itama tace "gani nan zuwa gareka autan maza"tana faɗin haka ta ajiye wayar tareda rungume mommyn ta tana tsalle"wllh mommy Yayi mugun kamuwa,kinji kalaman da yake faɗa min kuwa?kai gaskiya mommy ki ƙarawa boka kudi"Husna ta fada tana barin dakin cikin sauri ta nufi ɗakin baki, dan ta bada umarnin yana zuwa a kaishi can.an gyara dakin sosai sai ƙamshi yake,ga kayan makulashe da aka tanada tun kafin yazo,an jerasu kan center table. Murmushi mommyn Husna tayi,aduniya ba abinda yake so irin taga Husna na farin ciki. Dan haka zata iya yin komai dan farin cikin tilon yar Tata. Da sallama Husna ta shiga ɗakin saukar bakin,Tana wani tafiya tana girgiza jikinta,wanda yake aƙame kamar wani icce,ba inda yake motsawa kamar jikin maza. Idonta akan Aslam tana sakar masa murmushi. Kasaƙe !!Aslam yayi yana kallonta,domin tayi matukar yi masa kyau a idanunsa,gani yake kamar wanda aka sake ƙerata, ga wani shu'umin ƙamshi daya shaƙa daga gareta,wanda azahiri idan mutum yaji wanna ƙamshin tsaf zaiyi amai,amma shi da yake asirce yake,ji yayi baitaba jin ƙamshi mai daɗi irin na wannan turaren dake jikinta ba. Lumshe ido yayi tare da budewa yana zuba mata wani finannen kallo. Cikin rangwada ta ƙaraso kusa dashi sosai ta zauna.fari tayi masa da ido tana faɗin"Barka da isowa babban bakona" murmushi Aslam Yayi tare da gyara zama yana kallon Husna ,ji yake kamar ya maidata cikinsa. "Barka dai moyiyata,abar alfaharina,kinga yadda kika haske dakin nan kuwa gaskiya wannan kwalliyar tayimin kyau sosai ,dole na biya kudin "ya fada yana mai kallonta da lumsassun idanunsa. Murmushi tayi kafin tace "kaine ka ƙarawa dakin haske bani ba,domin kayi kyau matuka,kuma ba saika biya wannan kwalliyar ba,domin anyi tane dan kai " Ajiyar zuciya Aslam ya sauke kafin yace"gaskiya ina komawa gida ,zan sanar da daddy azo nemamin auren ki,dan bazan iya kai nan da sati guda,ba tare da na mallakeki matsayin matata ba"Aslam ya fada yana kurbar lemun da Husna ta bashi,wanda yasha magungunan surkulle kala kala. Daɗi da Farin ciki kamar ya kashe Husna,tace "Indai ta bangare nane bani da matsala ,domin nafi kowa son kasancewa dakai,kullum hakan shine burina,dana koma zan sanar da Daddy na Nima"ta faɗa tana wani kashe ido kamar tsohuwar mayya. Sun jima suna shira,dan har saida akayi magrib,sannan Aslam ya tafi, saidai duk yadda Husna taso Aslam Yayi romancing ɗinta Sam yaki,yace sai sunyi aure saidai kissing din hannunta da yayi kawai. Amma shima da gyar ya iya barin gidan dan ji yayi zai iya kwana tare da Husna yana kallonta. Lokacin daya koma gida,su mommyn Islam sun tafi. Daga mommynsa sai Islam da granny da kuma hanan zaune afalo,kowa da abinda yake yi. Islam na zaune tana tunanin har yanzu Aslam yana can tare da wannan ƙatuwar bijimar, hankalinsa kwance,ita ya barta da ciwon rai da tarin damuwa. Da sallama Aslam ya shigo cikin Falon cike da nishaɗi,akan fuskarsa,saidai kuma deep down Yana jin wani irin ɓacin rai da ciwo cikin zuciyar sa,wanda baisan na menene ba,kuma bazai iya furta wa ko nuna ɓacin ran nashi ba. Zama yayi akan kujera,sam bai kula da Islam ba,dan tana kan kujera ne can gefe guda ta kwanta kamar mai barci,yayin da granny ke zaune tana kallon Film ɗin da ake haska a arewa 24, "Aslam harka dawo?" cewar mommy cikin kulawa. "Wllh mommy na dawo,da gyar ma ta bari na taho,gaskiya mommy da zaran daddy ya dawo ki sanar dashi aje ayi magana iyayen Husna,dan so nake ayi komai da wuri,wllh bakiji yadda nake jin yarinyar cikin raina ba"Aslam ya fada cike da shaukin soyayya yana ɗora kansa akafadun mommy. Murmushi mommy tayi,tana mai shafa kan Aslam ,tare d cewa"ai Ni kaina bana son adauki lokaci,tun da dai duk gida ne,anjima nan zanyiwa Daddyn ku magana,In yaso konan da jibi ne,sai aje agama magana ko ya kikace granny?"mommy ta faɗa tana kallon granny. Jinjina kai granny tayi tana cewa. "Ja'irin yaro ba daga ganin yarinya kabi ka rikice,to Gara kam ayi komai cikin lokaci agama,Dan Nima yarinyar ta kwanta a raina sosai,tana da hankali sannan bata da rawar kai zamansu zasuyi lafiya da islam" Ajiyar zuciya Aslam Yayi Yana mai kallon granny yace"granny nifa banki ace yau ma akawo min ita matsayin matata ba,dan wllh bakiji yadda nake jin so da ƙaunar ta cikin zuciyataba" Aslam ya fada yana wani lumshe ido cike da farin ciki. "To wllh dai kayi adalci tsakanin matan ka,karka auri wannan kace zaka wulaƙanta min jika,wllh ba yadda zanyi ba,kasan halina sarai,bana tsoron mu ba hamata iska da mutum ehe"granny ta faɗa tana tafa hannu da hararar Aslam. Shikuwa murmushi Yayi Yana mai faɗin" ina Ni ,ina wannan dambe naki granny? Kwantar da hankalinki,ai kowa da matsayinsa,ita Islam ƙanwata ce, jinina, wannan kuma masoyiyata ce abar sona, dan haka kowa zai zauna a matsayinsa" Ya faɗa yana mai gyara zamansa,sannan ya cire hular da ke kansa ya juya da nufin ajiyewa akan dan table ɗin dake gefen kujeru. Carab idanunsa suka sauka akan Islam,wacce ke kwance kamar mai barci,sai dai azahirin gaskiya kallo ɗaya zakayi mata kasan idanunta biyu,duba da yadda jikinta ke ɗan rawa,sannan tana sauke wani irin numfashi da sauri-da sauri. Sosai kalaman Aslam ke yawo cikin kwakwalwarta,lallai ta yarda ta kuma aminta Aslam baya ƙaunarta,agabanta yake faɗin irin waɗannan kalaman akan wata?ba ko kunya bare kara?wato ita amatsayin kanwa take agareshi,waccan itace abar ƙaunarsa. Wai shin me yasa ma zuciyarta tayi mata rashin adalcin kamuwa da son Aslam ne?me yasa ta yarda ta auri Aslam? Shikuwa Aslam ji yayi jikinsa yayi sanyi,dan kuwa harga Allah baisan cewa Islam tana falon nan ba,da bazaiyi wadan nan maganganun haka ba,koba komai ita ɗin matarsa ce ,kuma dole taji ba daɗi,duk da yasan bawai sonshi take ba,amma dai bai kamata ya fadi irin wannan kalaman agaban taba.kuma yasan tabbas taji duk abinda suka tattauna dasu mommy. Kallonta kawai yake ya kasa cewa komai,kusan minti biyu yana kallon yadda jikinta ke rawa,tana sauke numfashi,ahankali ya kai hannunsa tare da dafa kafaɗunta. Islam kuwa kamar wanda aka ɗora mata wuta, tayi sauri zabura tare da ture hannunsa daga jikinta,wani irin kallo mai cikeda ma'anoni kala kala take jifansa dashi, kafin ta mike cikin hanzari ta bar falon.part dinsu ta nufa cikin sauri, Kai tsaye ta wuce dayan dakin ta sanya masa key . Zama tayi bakin gado jikinta yana rawa,wani irin masifaffen kuka ne ya kwace mata mai matukar zafi da ƙona zuciya.da ƙarfi kukan ya kufce mata ba tare da ta shiryawa hakan ba,cikin sauri ta sanya hannunta ta toshe bakinta,dan hanawa sautin kukan nata fitowa,duk da hakan baiyi wani tasirin hana kukan fita ba. Kuka take sosai tana jin tausayin kanta,na kamuwa da don wanda bata ita yake ba,mutumin da yayi zurfi cikin soyayyar wata,son da baya hanashi faɗin yadda yake ji game da masoyiyarta tashi gaban kowa,ciki kuwa harda ita dake matsayin matarsa. Mmn Aslam kuwa yana ganin ta tashi shima yayi saurin biyota,dan yasan bai kyauta mata ba, saidai kafin ya ƙaraso tuni ta rufe kofar. Tsaye yayi abakin ƙofar yana kallon ta. Har zuwa lokacin da yaki ta fashe da wanan kukan mai zafi. Runtse idonsa yayi yana jin kamar an watsa masa dalma cikin zuciyarsa,sosai yake jin zafin kukan nata cikin zuciyarsa,sam baya son jin ta ko ganinta cikin damuwa.amma ba yadda zaiyi,zuciyarsa cike take da kaunar Husna,kuma baya jin zai iya fasa auren ta. Jin yadda Islam ke kukan kamar zata shiɗe ne,kuma bata da niyyar dainawa,yasashi fara buga ƙofar yana kirana sunanta. "Islam !Islam!! Islam!!! Please ki buɗe kofar nan muyi magana,an sorry Islam,dan Allah ki daina kukan nan,wllh zuciya zata buga bana son jin kukanki ko kaɗan Please Islam"ya fada cike da damuwa kamar zaiyi kuka. Wani malolon baƙin ciki ne ya tokare zuciyar Islam,wai baya son jin kukanta?kuma zuciyarsa zata fashe?kuji rainin hankali fa? Ita zai maida karamar yarinya hmmmm wllh daga yau tayi alkawarin ta daina yarda koda zama suyi guri ɗaya da Aslam,bare ya Sami damar taba jikinta,tunda ta gane ba sonta yake ba,jikinta kawai yake muradi. Banza tayi dashi taci gaba da kukanta,har saida taji kanta na neman yi mata ciwo kafin ta hakura. Alwala ta dauro tayi sallar ishsha. Sannan ta kwanta. Aslam Yana kwance adakinsu, saidai sam ya kasa barci,sai juyi yake yi tunanin Islam,ga wata irin faduwa da gabansa keyi,da zarar ya fara tunanin Islam,sai yaji gabansa ya faɗi sosai, sai kuma Husna ta fado masa. Haka dai yayi ta juyi zuciyarsa ba dadi har gari ya waye. Koda gari ya waye Islam tana shiryawa tayi saurin fitowa daga part ɗin. Gaba ɗaya haushin yan gidan take ji,dan tana ganin duk da amincewarsu Aslam yake ƙoƙarin kara auren,dan haka bata shiga koda part din mommy ba,tayi fitowar ta daga gidan sanye da uniform ajikinta. Bata da ko sisi bare ta hau adaidaita. Haka ta kama hanyar makarantar aƙafa. Aslam Yana tashi ya nufi dakin da Islam ya kwana,dan da asubama saida ya zo yayi mata magana amma tayi banza dashi.ganin dakin abuɗe yasa shi gane ta fice kenan. Da sauri ya fito shima,baba mai gadi ya tambaya ko yaga gilmawar Islam?nan yake sanar dashi yanzun nan ta fice da uniform ajikinta. Dafe kai yayi tare da runtse ido,yanzu ta yaya zata iya zuwa wannan makarantar mai nisa aƙafa? Da sauri ya shige motarsa ya fice dan bin sawun ta. Aikuwa saida yayi tafiya mai ɗan nisa kafin ya hangota,tana tafe cikin nutsuwa,wanda damuwar da take ciki suka ƙara sanyaya mata jiki,hakan yasa take tafiya ahankali. Shan gabanta yayi da mota tare da budewa ya fito . "Dan me zaki fito kice zaki tafi school aƙafa?me amfanin motocin gidan? Haba Islam me yasa kike son azabtar da kanki ne"ya fada cikin sigar rarrashi yana kokarin kamo hannunta. Da sauri ta ja da baya tana maida hannunta baya.harara ta banka masa tana faɗin"karka sake kace zaka taɓani,domin an wuce wannan lokacin,kuma ina ruwanka dan zan tafi makarantar aƙafa? Shin kafarka ce ko tawa"Islam ta faɗa cikin fushi tana hararar Aslam. Murmushi Aslam Yayi yana mai faɗin"na ji koma me zaki ce shigo muje na kaiki,kinga akwai nisa,bazaki iya zuwa aƙafa ba kaf....." "Bazan shiga motar taka ba"Islam ta katseshi cikin daga murya tana hararar motar. Sanin da yayi wacece Islam,yasanyashi,shammatar ta ya sureta ya tura cikin motar. Da sauri ya kulle tare da dannan key bayan ya shiga shima. "Malam ka budemin kofa in fita,ko dolene sai an shiga motar taka?"Islam ta faɗa cike da jin haushin yadda ya tilasta mata shiga motar. "Ki fita mana ai ban hanaki ba ko"Aslam ya fada ba tare da ya kalleta ba . Ƙofar motar ta kama kici-kici dan budewa,amma ko motsi ƙofar batayi,tsabar haushi kawai ta sanya kuka. Shiru Aslam yayi baice mata komai ba har suka karasa cikin makarantar. Tsayawa yayi tare da kallon ta,sosai wllh yake jin tausayinta,bayajin daɗin ganin ta haka. Ahankali ya kira sunanta"Islam, Please ki fadamin meke damunki? Me yasa kike jin haushina kwana biyu?" Ya faɗa yana kallon fuskarta,wacce take fayau ba ko mai bare kwalli,sai sheƙi take kamar fuskar jarirai. "Budemin mota zan fita"Islam ta faɗa idonta na kallon window. Ajiyar zuciya Aslam ya sauke,wato bazata bashi amsa ba kenan? "Tambayar ki fa nake Islam,ki sanar dani meke damun ki? Men..... "Kai ke damunta Aslam! Ka takurawa rayuwata,dan Allah ka gyaleni in huta kaje kayi rayuwarka,nima ka barni nayi tawa"Islam ta faɗa cikin masifa da tsantsar kishi,wanda kallo ɗaya zakayi mata ka gano hakan. Kallonta kawai Aslam yakeyi,ya gane tana jin haushi ne akan batun Husna,amma dole tayi hakuri dan bazai iya fada auren Husna ba. Cikin sigar rarrashi yace"yanzu kina ganin hakan shine dai-dai?ta yaya zaki ce in barki kiyi rayuwarki?Nima nayi tawa?ok shine jiya kika kulle kanki adaki kikaƙi fitowa ?wannan shine matakin da kika ɗauka akan abinda Allah bai hana ba?aure fa zanyi ba wani mugun abuba. Aslam ya fada yana kallon ta. Runtse ido Islam tayi,dan maganar da takeyi dashima yanzu,ji take kamar ta shaƙe shi, "Aslam ka budemin kofa in fita,an faɗa maka wani banzan auren da zakayi ya dameni ne?wllh in kaso kaje ka auri hudu,inyaso nika bani takarda ta,dan kasan dama baka gabana bare naji haushin auren ka kona ɓata raina,Ina Dana sanin yarda danayi ne na auri mutum irin ka wanda baisan menene kara ba" Islam ta faɗa cikin masifa kamar zata cinye Aslam. Shikuwa Aslam bakin ciki ne ya turnuke masa zuciya,wato bata damu dashi Bama,duk wannan abun da take tana nufin bawai kishinsa take ba?wato ya auri hudu ma,In yaso ita ya bata takardar ta bata damuba? Cike da ɓacin rai ya dannan securityn motar ta buɗe yace "fita !"da ɗan ƙarfi cikin ɓacin rai. Taɓe baki Islam tayi kafin ta fice daga motar,ko waiwayensa batayi ba ta shige cikin ajinsu. Shikuwa Aslam ransa abace yaja motar,dan me Islam zatace bata damu dashi ba,kenan duk abinda yake mata ita Bama sonshi take ba?ƙwafa yayi tare da figar motar da gudu. Kamar yadda mommy ta faɗa kuwa, balance ta kasance,ta sanar da daddy batun Aslam da Husna,abin mamaki kuwa ba musu ba komai ya amince,nan take ya kira abokansa su biyu,yasanar dasu akan zasuje nemawa Aslam aure da yamma. Dan mommy ta sanar dashi granny ma ta amince .duk da haka saida yaje suka tattauna akan maganar. Washe gari kuwa akaje aka nemawa Aslam auren Husna,ba bata lokaci suka gama komai,nan da sati biyu za'ayi auren. Lokacin da za'aje neman auren,daddy ya nemi abban Islam akan suje tare ,amma baya ƙasar,hakan ya hanashi zuwa,saidai yayi musu fatan alkairi. Murna gurin Aslam kuwa ba'a magana ,bare kuma uwar gayya Husna. Lokacin da labarin ya sami Islam,bata nunawa su mommy komai ba,tayi fatan alkairi garesu,sannan ta bar falon. Kai tsaye ta nufi lambu,can saman bishiya ta haye ta kwanta tare da lumshe idanunta.xuciyarta naci gaba da tafasa kamar garwashin wuta... Hmmmm muje zuwa masu karatu. Anty mammy ce Mrs babi. [10/25/2022, 4:52 PM] Abk: 71/72 ____________Saman bishiya Islam ta haye,tare da kwanciya jikin wani reshe ta lumshe idanunta. Zuciyarta na ci gaba da tafasa kamar ana izamata wuta.tana rungume da janbu ajikinta,kamar wata marainiya haka take jin kanta. So take ta kawar da damuwarta,ta cire batun auren Aslam daga cikin ranta,amma abin nema yake yafi karfin ta,dama haka kishi yake?lallai kishi zai iya hallaka mutum,domin a yadda take jin zuciyarta na bugawa, to idan batayi wasa ba lallai gab take da fashewa. Ko kaɗan bata ƙaunar wannan husnar,dan ita zuciyarta ma bata amince da itaba,ga dukkan alamu bata da gaskiya,dan tana kallon ta taji hankalinta ya tashi. Nan gurin dai Islam tayi kwanciyarta tana ta fama da raɗaɗin zuciya. Da daddare bayan an kammala cin abinci,wanda Islam cakala kawai take,dan bata wani jin dadin abincin abakinta. Aslam Yana zaune yana kula da yanayin ta,duk da ta bata masa rai dazu,amma ko kaɗan baya jin dadin ganinta cikin wannan yanayin,kamar ba Islam ɗin daya sani ba,mai neman tsokana da tsiwa,duk ta maida kanta shiru-shiru bata hira,bata tsokana,yanzu seniorityn ma ta daina,duk abun nata ya zama sukuku. Su mommy kuwa hirarsu kawai suke,ta yadda za'a hado kayan lefen Husna,da irin abubuwan da za'a sanya acikin lefen,za'aje flazar Aslam gobe adebo kayayyakin acan. Da abin ya ishi Islam kuwa, Mikewa tayi daga kan danning table ɗin,dan bazata iya jurar sauraron wannan hirar tasu ba. "Ina kuma zaki Islam ana cin abinci?" Mommy ta faɗa ganin Islam ta mike. Ahankali Islam ta kalli mommy kafin tace "mommy barci zanje nayi na gaji "ta faɗa tana mai kawar da kanta dan gudun su gano damuwar dake cikin ranta. "To Islam kodai kishi kikeyi ne?naga ana zancen kayan auren kishiyarki zaki gudu ɗaki,wllh dai karki zama raguwa dan ninan da kike gani jaruma ce ba komai ke daga min hankali ba"granny ta faɗa tana watsa hannaye. Wani kallo mai cike da jin haushi Islam ta jefawa granny kafin cikin murya mai dauke da ɓacin rai tace"Kodama dai kishi halitta ne,amma kisani bazan tsaya ina bata lokacinna wajen kishin wanda baya gabana ba,ina ruwana da zancen ku da zai dameni, kawai ina jin rashin daɗi ne,ta yadda ahalina suke fifita soyayyar wata akaina,wanda tsabar son da suke mata agabana suke hirar kaunarta garesu,sun ma manta cewar yarsu ce ni. Amma karki damu granny,Islam rainon dawa ce,Ni kadai na dama na tashi,kuma zan iya rayuwata Ni kadai" Islam na kaiwa nan a maganar ta ,ta nufi hanyar part dinsu cikin sauri. Sosai jikin su mommy Yayi sanyi,gaskiya abinda suke mata sam basu kyauta ba,amma sun rasa menene abinda ya rufe musu ido,har suke mantawa Islam jininsu ita za'a kawowa kishiya,kuma kasancewar Islam aguri, baya hanasu yin hirar husna.koba komai sa tayata jimami idan basu hana auren ba. "Kai wllh sai yanzu nake jin tausayin Islam,yarinyar nan tayi kawaici akan mu,kullum zancen mu Husna bata taɓa yin magana ba sai yau,amma dole tayi hakuri,ta saba da hakan tunda dai itama husnan gab take da zama yar gida"cewar granny cikin jimami. Mommy kuwa kallon Aslam tayi,wanda yayi zaune riƙe da cokali ahannunsa yana kallon Islam,tunda ta fara magabata ,harta kammala. Shi kansa baya jin daɗin yadda ake hirar agabanta,amma abinda ya lura da yan gidan nasu,sun kamu da son Husna sosai suma,har basa iya boye soyayyar da suke mata. "Aslam kaje ka rarrasheta Please,dan ranta ya ɓaci"mommy ta faɗa cikin sanyin murya. Tashi Aslma yayi tare da bin bayan Islam ɗin. "Gaskiya mommy ba'a kyauta wa Islam agidan nan,gaba ɗaya kana kallon Islam kasan tana cikin damuwa,kullum baku da zance saina Husna Ni wllh husnan nan bata wani min ba ko kaɗan,abu shirin kamar kayan wanki"Aman ne ke wannan maganar cikin ɓacin rai,yana ajiye cokalin hannunsa yayi hanyar ɗakinsa. Dan sosai yake tausayawa Islam da wannan auren da yayan nashi ke ƙoƙarin yi, Kallo kawai suka bishi dashi,kafin grannyn tace "ja'irin yaro,kuma ahaka zata zama antyn ka ko kana so ko baka so,ai baka fimu son Islam din ba,ba yadda zamuyi ne,tunda aure sunnar ma'aikin Allah ne" "Allah nima tausayi Islam take bani,duka -duka ma yaushe akayi bikin nasu?amma yaya zai kara mata wani auren, Ni wllh idan mijina zaimin kishiya bazan zauna ba,saidai mu rabu"hanan ta faɗa tana turo baki. "To hanan muma fa tana bamu tausayin,kawai muna son karfafa mata zuciya ne,amma kishiya kam ai kowa ya sani ba daɗi"cewar mommy tana ci gaba da cin abincin ta,can kasan zuciyarta kuma tana jin tausayin Islam. Islam kuwa tana zuwa falo ta zauna akan kujera,abin yana matukar bata mata rai,yadda danginta suke nuna soyayya kiri-kiri akan husna sama da ita,sam basa tayata kishi,gaba ɗaya yanzu gidan ya fita daga ranta,ba abinda take bukata illa tajita jikin mommyn ta,tayi kukanta son ranta,koba komai tasan zata samu nutsuwa. Kuka take cikin sauti marar ƙara,lallai duniya juyi -juyi,wai yau ita islam,itace ke zaune tana kuka akan damuwa?kuma bata da hanyar magancewa kanta damuwar. Duk wannan Aslam ɗin ne ya jawo mata,wllh yanzu jima take ta tsaneshi ,bata son ko kusa da ita yazo. "I hate you Aslam,na tsaneka"ta faɗa cikin muryar kuka tana shura kafa. Karab!! Kalamanta suka sauka akan kunnen Aslam,runtse idonsa yayi da ƙarfi,dan ji yayi kamar ta caka masa mashi cikin ƙahon zuciyarsa.ya tsani yaji tana furta irin waɗannan kalaman akansa. Fuska ba walwala ya shiga cikin Falon,zama yayi dan nesa da ita ya tsira mata ido,gaba ɗaya ta sauya,kamar ba Islam ba,har wata yar rama tayi. Ahankali yace "Ya kamata ki daina wannan kukan Islam,bakya tunanin zai iya haifar miki da wata matsalar?haba Islam gaba ɗaya kin sanya kanki cikin damuwa kin zama kamar bake ba,Please ki dawo Islam ɗin dana sani abaya,nafi son ganinki ahaka " Aslam ya fada cikin yanayi na damuwa. Ita kuwa Islam ko ci kanka bata ce masa ba. Cikin damuwa yace "Islam ,me kike so nayi miki yanzu?ya fada cikin sanyin murya. Da sauri ta juyo tana kallonsa,wanda da tayi banza dashi taki kallon inda yake, Cikin zubar hawaye tace "so nake inkoma gidan mu,gurin mommy na"ta fada hawaye naci gaba da zuba kamar an bude fanfo. Kallonta yayi na dan wasu sakwanni,yace "idan na kaiki gidan anty shikenan?shikenan zaki daina kukan?"ya fada yana kallon idanunta da suka danyi ja,zai kaita taga antyn,yasan zata ji sassauci cikin zuciyarta.inyaso saiya dawo da ita . Cikin tsiwa da harara tace "Wannan kuma bai shafe ka ba,kaga malam, nifa tafiya ta zanyi dan zan iya zuwa da kaina ba neman taimakon ka nakeyi ba, kawai inason ya kasance kaine ka amince min da kanka Dan mommy na ta tasan bada kaina nazo ba"ta faɗa cikin masifa tana mikewa tsaye. "Shikenan to,kiyi hakuri shirya muje na kaiki da kaina,In kuma ba haka bazaki je ko ina ba,zan kira mommyn in faɗa mata bada amincewata zaki zo ba" ya fada yana kallon ta . Dan jimm tayi na wani lokaci,kafin ta mike Daki ta shiga jim kaɗan ta fito riƙe da mayafinta,ko magana batayi masa ba,tayi waje abinta. Girgiza kai Aslam Yayi kafin ya bi bayanta. Shiga tayi cikin motar ta zauna fuskarta ahade ba alamun fara'a ko kaɗan. Haka suka nufi anguwar su mommy. Yana ta Jan ta da magana amma tayi banza dashi.suna cikin tafiya kuma Husna ta kirashi a waya,jikinsa har rawa yake wajen daga kiran nata. "Hello ranki ya dade gimbiyar mata"ya fada kamar an fizgi maganar daga bakinsa. Ta can bangaren kuwa,juyi Husna tayi akan gadon ta, tare da lumshe ido sakamakon jin daddaɗar muryar Aslam dake ratsa sannan jikinta . "Tare da kai autan maza angon Husna "ta faɗa cike da shauki. Cikin murmushi Aslam yace "ya ake ciki ne gimbiya ta? Husna kuwa cike da shagwaba tace"idanuna ke buƙatar ganin kyakykyawar fuskarka agabansu" Ajiyar zuciya Aslam Yayi tare da cewa"kisa aranki ganinan har na zo gareki masoyiyata,domin nima nawa idanun na mararin kallon kyakykyawar fuskarki"ya fada yana ɗan juya sitiyarin motar cikin nishadi. Tuni wata bala'ey'iyar zuciya ta gama ciyo Islam,wanda Bama tasan lokacin data fizge wayar daga kunne Aslam ta doka ta da ƙasan motar ba,cikin hucin ɓacin rai ta fara magana"wllh kayi karya Aslam,niba lalatacciyar mace bace,wacce zaka wulakanta yadda kaso ba,baka da wannan matsayin na kiran budurwa agabana kana faɗa mata kalaman soyayya,idan bana gurin kaje ku cinye juna da kalamai ma bai dameni ba,amma baka isa ka tozarta ni ba "Islam ta faɗa numfashinta na cikowa kamar zata shiɗe. Ikon Allah,wllh gaba ɗaya Aslam yama manta da cewar Islam na cikin motar nan,tunda Husna ta kirashi, kuma haka ke kasancewa dashi,Aduk lokacin da yake tare da husna kota kirashi,komai ma mantawa yake dashi,yanzu ma tana kiransa ya mance da wata Islam cikin motar,hakan yasa yayi ta sakin magana son ransa.sai da Islam ta warce wayar sannan ya tuna da ita. Da sauri ya tsayar da motar agefen titi,dan yaga Islam nema take tasa suyi accident,Dan ta rike sitiyarin motar tana faɗin ya tsaya ta sauka. Ko tsayawar bai gama yiba,ta fara kiciniyar bude motar. Ahalin da ake ciki yanzu ,wllh ta tsani Aslam,ko ganinsa bata son yi,kuka ke ƙoƙarin kufce mata,amma tana iyakar ƙoƙarin ta wajen danne hawayen ta. Ganin yadda jikinta ke rawa tana jijjiga motar, aƙokarinta na son ficewa daga motar ne yasa Aslam saurin kamo hannayen ta duka biyun"ki nutsu Islam karki jiwa kanki ciwo Please"ya fada cikin sanyin murya. Da wani mugun hanzari Islam ta warce hannayen ta,wani kallo mai cikeda tarin tsana take jifan Aslam dashi"karka ƙara taɓani Aslam,wllh dakasan yadda na tsaneka azuciyata,wllh da ko inda nake bazaka raba ba,ka budemin motar nan in fice "ta faɗa da wata irin murya wacce ta sanya Aslam Dan tsorata. Idanunta yayi jajur kamar wuta,banda rawa ba abinda jikinta keyi,kai kishi bala'ine,Islam tana da wani irin mugun kishi akan abinda take so matuka. Cikin sanyin murya da kwantar da hankali Aslam yace "is ok zan bude miki,amma dan Allah ki kwantar da hankalin ki bari in kaiki gidan, kinga mun kusan zuwa ki nutsu Islam kar wani abu ya sameki kinga dare ne"ya fada cikin yanayi na tarin damuwa,ya rasa ya zaiyi da rayuwarsa,shifa idan zai iya ganewa ma,wllh ji yayi kamar tsoron Husna yake ji,Indai abu ya shafe ta baya iya controling kansa,ko sunanta aka ambata sai gabansa ya faɗi da ƙarfi,kuma nan take zaiji kamar wanda ake kwarara masa dalmar sonta cikin zuciyarsa. Haka nan can kasan zuciyarsa,yana matukar tausayin Islam,sannan yana jinta har cikin ransa,baya son ganinta cikin damuwa.. "Ka budemin ƙofa nace"Islam ta faɗa da ƙarfi tana toshe kunnenta, dan bata son jin ko muryasa ma. Da sauri ya dannan unlock ƙofofin motar suka buɗe. Afusace Islam ta fice daga motar,Allah ma yasa ta gane gidan,dan sun kusan zuwa,kwana kwai zata sha ta iya hango gidan nasu. Tana tafe cikin mugun ɓacin rai da radadi, banda bugawa ba abinda zuciyarta keyi. Shikuwa Aslam Yana biye da ita cikin motar,tausayinta kamar ya hallaka shi,dan zuwa yanzu ya gano tsantsar kishi ke damun Islam, to kodai ta fara sonshi ne? Dama hakan zata kasance,dayafi kowa farin ciki wllh. Da ƙarfi ta rinƙa buga kofar gidan nasu kamar zata karya get ɗin. Aguje mai gadi ya taho da sandarsa, dan ganin wanda ke musu irin wannan bugun kamar zai balla kofar. Yana budewa Islam tayi cikin gidan da sauri bata ko bi takan mai gadi da yake mata sannu da zuwa ba. Tana shiga falon ta tarar da mommyn ta da kuma A'isha suna home work.da gudu A'isha taje ta rungume Islam,amma ko kula yarinyar Islam batayi ba,ta tureta daga jikinta tare da nufar cikin daki. Kallo mommyn tabi Islam dashi cike da mamakin meke damunta haka? Dan dangi ba acikin hayyacinta take ba,to ita dawa suka zo?badai ita kadai tazo da daren nan ba?bari dai taje yaji ko menene ke faruwa. Ta yunƙura kenan zata bita dakin Aslam ya shigo. Kallo ɗaya mommyn tayi masa,ta gano tarin damuwar dake cikin ransa,shima. " Ashe tare kuke? Lafiya kuwa Aslam ?meke faruwa? Mommy ta faɗa tana kamo hannunsa ta zaunar dashi akan kujera. Kallon mommy Yayi kamar wani Maraya yace "mommy bansan me nayiwa islam ba,gaba ɗaya ta tsaneni kwanan nan,mommy bata kulani,bata yarda mu zauna guri ɗaya,yanzu ma muna cikin tafiya cikin mota tace in sauketa, Dan kawai na amsa waya agabanta,mommy akafa ta ƙaraso"ya fada kamar zaiyi kuka. Zama mommy tayi tana mai kamo hannun Aslam,tace"haba Aslam,karka zama ragon maza mana,aure fa kake shirin karawa,idan kana haka ta yaya zaka iya kula da matan ka?kasan dole ne ka fuskanci kalubale daga gurin Islam,domin kishi gaskiya ne,amma idan ka jajirce da anyi auren komai zai dai-dai ta In sha Allah.ka daina damun kanka"mommy ta faɗa cikin sigar rarrashi. Ajiyar zuciya Aslam Yayi yace "Amma mommy king.... "Naga me? Mommy ta katsar dashi "ka kwantar da hankalinka karka damu,zanyi magana da Islam ɗin" "To anty Bari naje zan dawo sai mu koma gida"ya fada ahankali yana mikewa tsaye. Jinjina kai Mommy tayi,tana kallonsa harya fice daga falon. Gana ɗaya dagashi har Islam abin tausayine. Dakin da Islam ta shiga nan mommyn ta shiga itama,kwance ta tarar da Islam ɗin tana sauke ajiyar zuciya, ga A'isha zaune agefen ta tayi tagumi,da gani kasan tana cike da tarin damuwa. Mommy na zama Islam ta tashi tare da rungumeta ta fashe da kuka. Shafa kanta kawai mommy keyi,ba tare da ta hanata yin kukan ba,dan tasan kukan ne kawai zai sanyaya mata zuciya. Nan take itama A'isha ta kama kuka,rarrashinta mommy tayi,yarinyar tayi shiru,ahaka har barci ya ɗauke ta. Saida tayi kuka ma ishi,kafin mommyn tace "ya isa haka Islam,ya isa kuka ba abinda zaiyi miki,ki mika lamarinki gurin Allah,shi zai miki maganin damuwarki, Ki daure zuciyarki,kizama mai juriya,karki bari shaidan yayi galaba akanki. Duk kin tada hankalinki,kin tada na mijinki,akan zai kara aure?saboda me islam?komai fa na Allah ne,kuma tun ran gini tun ran zane,dan haka kiyi hakuri kiyi ta addu'a"mommy ta faɗa tana sharewa Islam hawayen idanunta. "Mommy agabana fa suke maganar ta,yanzu ma agabana yake waya da ita yana faɗa mata kalamai masu dadi,mommy Ni wllh bana son shi bazan koma gidan nan ba"Islam ta faɗa tana kwanciya akan cinyar mommynta. Murmushi mommy tayi,kafin ta ci gaba da rarrashin Islam,tana bata shawarwari. Kai tsaye Aslam kuwa yana fita ya wuce gidan su Husna,inda aka cikashi da magunguna mallaka kala -kala. Cikin lemo, wanda gaba ɗaya kansa ya juye,ya manta da batun Islam dake gida. ,yana barin gidan su Husna ya tafi gida abinsa... Muje zuwa Mrs babi ce. Anty mammy. [10/26/2022, 2:37 PM] Abk: 73/74 ______________Aslam yana barin gidan su husna kai tsaye gida ya nufa cikeda shaukin kaunar Husna.ji yake kamar ya janyo kwanakin auren su ya dawo gobe,sam ya manta da batun Islam dake gida cikin ɓacin rai. Koda ya koma gida ,su mommy duk basa falon kowa ya kama gabansa,dan haka shima kai tsaye ya nufi nasu part din, Yana shiga ya wuce daki,wanka yayi tare da sanya kayan barcinsa, ya gaji sosai dan haka kawai yake jin jikinsa ba dadi,kwanciya yayi tare da rufe idanunsa, da sauri ya buɗe idonsa tare da zaro ido waje. "Islam "ya fada yana tashi zaune,wayarsa daya ɗauko daga inda islam ta jefar dazu,ya janyo tare da duba agogo,ƙarfe 10: 12pm na dare ya gani. Da sauri ya sauko daga kan gadon ya nufi bakin ƙofa,saidai yana sanya hannu da nufin bude kofar wayarsa ta dauki ruri,da sauri ya kai kallonsa kan wayar,ba kowa bace face Husna,nan take kuwa Aslam ya manta me ma yake ƙoƙarin yi yanzun,cike da ɗoki ya daga wayar yana komawa kan gado ya kwanta. Suka fara hirarsu cike da shaukin juna. Mommyn Islam kuwa tana ta jiran zuwan Aslam Amma shiru,hakan yasa ta kirashi awaya ,amma user busy,duk Kiran datayi masa bata sameshi ba. Islam tana kallonta tace "mommy wai wakike kira ne?" Ta fada adan shagwabe. "Wllh Islam kinga wai Aslma nake kira, yace zai dawo ku koma gida,amma kinji shiru gashi wayar tashi user busy"mommy ta faɗa tana ƙara kiran wayar. Haɗe fuska Islam tayi tare da cewa"mommy Dan Allah ki daina kiransa,wllh yana can gurin wannan uwar lukutayen ko kuma yana waya da ita ne,kuma ma Ni bazan koma yanzu ba"Islam ta faɗa tana buɗe fridge ta dauko ruwa. Kallonta Hisham yayi wanda ke zaune yana assignment a computer sa. Yace "sister yau kuma anan zaki kwana ki bar yayan?"ya fada yana ɗan kallon ta. "Eh anan zan kwana"ta fada tana zama kusa dashi. "Amma sis lafiya kuwa? Hisham ya fada yana ɗan maida hankalinsa kanta. Ruwan ta ajiye bayan ta gama sha ta kalle shi tace"banda abinka saida wani abu zan kwana agidan mu?kawai bana buƙatar kwanar musu agida ne,shiyasa nima na dawo namu gidan"Islam ta faɗa tana haɗe fuska,kana jin yadda tayi maganar kasan cike take da haushin Aslam. Shiru yayi yana ɗan nazarin yanayin yayar tashi kafin yace "shima yaya Aslam bansan dalilin da yasa yake son kara auren nan ba,kuna zamanku lafiya ya sanya mu ku damuwa,wllh Ni ban.... "Kai Hisham!! meye hakan?so kake ka kara tunzurata kome?irin naka gudunmawar kenan?"mommy ta faɗa cikin ɓacin rai . "Kiyi hakuri mommy kawai ina taya yar uwata jimami ne "Hisham ya fada yana ɗan yamutse fuska. "To wllh ka kiyayeni karna karajin bakinka akan wannan maganar,akan ta aka fara kishiya kome?idan bazaka bata shawarar tayi hakuri ba to kayi shirunka yafi alkairi"mommy ta karasa cikin faɗa. Hakuri Hisham ya bata tare da tattare kayansa yayi mata sallama da Islam ya tafi ɗakinsa, amma yana jin haushin kishiyar da za'a karawa Islam sosai cikin ransa. Haka dai mommy tayi ta kiran wayar Aslam user busy,sai hakura tayi suka kwanta,dan Aslam bai gama waya da husna ba sai wajen dayan dare da yan mintuna. Washe gari Islam bataje makaranta ba,dan dama bata taho da uniform ba. Aslma kuwa cikin sauri yake shiryawa dan zuwa gidan anty,baisan me zaice mata ya hanashi dawowa jiyaba,amma kawai zaice ya barta ne ta kwana anan ɗin dan ta sami nutsuwa. Haka ya gama shirinsa cikin gaggawa ya nufi gidan antyn nashi. Lokacin daya isa gidan suna breakfast. Yana sallama Islam taji gabanta ya fadi,gashi dama tunaninsa take ta faman yi tun jiyan. Da fara'a sosai mommy ta taryeshi,zama yayi kusa da mommyn shima yana janyo flate tare da fara zuba soyayyen Dankali da kwai,dan dama yunwa yake ji sosai. "Antyna Ina kwana ya yar rikici"Aslam ya fada yana kallon Islam,wacce ta haɗe rai sosai kamar zatayi ihu,nan kuwa cikin zuciyarta dadin ganinsa taji sosai. Murmushi mommy tayi tana mai cewa"ai jiya inata jiran dawowarka dan ku koma gida,sainaji shiru,kuma na kira wayarka user busy" Shiru Aslam Yayi Yana kallon Islam,kafin yace"amm mommy jiyan dama na barta ne ta kwana anan,dan ta sami nutsuwa,kuma waya nayi jiya daddare mai muhimmanci"ya fada yana ɗan kame -kame,abinka da ba'a saba karya ba. "Yaya ina kwana"Hisham ya fada. "Lafiya Hisham baka tafi school ba?"cewar Aslam Yana mai jin dadin katse tambayar mommy da Hisham yayi. "Eh yanzu zan wuce,mommy na tafi,sister saina dawo"ya fada yana kama hannun A'isha. "Anty bazakije school ba yau?"A'isha ta faɗa tana ɗan yamutse fuska. Sai lokacin Islam tayi magana"eh sister yau bazan je school ba,bana jin dadi saikin dawo ayi karatu mai yawa "ta faɗa tana ɗan shafa kan yarinyar . "A'a nima bazani ba anty,bana jin dadi"A'isha ta faɗa tana kwace hannun ta daga cikin na Hisham. Kallon yarinyar Islam tayi tare da ɗan haɗe fuska tace "school ɗin ne bazaki ba?ta faɗa fuska ba wasa,maza ki kama hanya,nima zanje gobe ai, kinji"ta ƙara sa kuma da yanayin rarrashi. Jinjina kai A'isha tayi tare da kama hannun Hisham suka tafi.adawo lafiya mommyn tayi musu,da Aslam. Suna ficewa Islam ta yunƙura zata bar gurin. Da sauri Aslam yace "ki shirya mu tafi gida yanzu" Ko inda yake bata kalla ba,sai kara haɗe fuska da tayi. Kallon mommy Yayi yana marairaicewa yace"mommy kingani ko?har yanzu fushin take,ko gaisheni ma batayi ba"ya fada yana maida kallonsa kan islam.wacce ta fara tafiya mommy ta dakatar da ita. Tsayawa tayi ba tare da ta juyo ba. Bata son juyawa ta kalli Aslam,domin Aduk lokacin da ta kalleshi,tana ƙara jin sonshine cikin ranta,ita kuma ahalin yanzu,so take. ta ma daina son nashi gaba ɗaya. "Dawo nan" Mommy ta faɗa cikin bada umarni. Ahankali Islam ta juyo tare da dawowa inda ta tashi sannan ta zauna. "Shin bakiga Aslam bane? Cewar mommyn. "Na ganshi mommy "Islam ta faɗa cikin shagwaba tana turo baki. "To bai isa ki gaida shi bane?ko bakisan gurin wa yazo ba?mommy ta sake faɗa tana kallon Islam. "Ina kwana "Islam ta faɗa tana turo baki tare da balla masa harara. Murmushi Aslam Yayi ganin irin hararar da take balla masa,yasan ko sunje gida akwai masifa kenan,dan har yanzu bata huce ba. "Lafiya Islam,ya kika kwana?"Aslam ya fada da son jan maganar tasu tayi nisa. Banza Islam tayi dashi tana hararar sa ta kasa. Tashi mommy tayi tana dauke kwanikan da aka ci abincin,da sauri Islam ma tayi zuruf ta mike tana diban kwanikan. "A'a kinga barsu kawai,kije ki shirya kizo ku tafi gida"mommy ta faɗa tana karbar na hannun Islam ɗin. Turo baki Islam tayi tare da nufar dakin ta tayi kwanciyarta. "Wllh ba inda zani dan ya raina min hankali,sai yau zai zo yace mu tafi,tun jiya yana tare da waccan bijimar shine yanzu zai wani kwaso kafa yace inzo mu koma gida?tab " Islam ta faɗa tana gyara kwanciyarta . Shiru Islam bata fito ba har kusan minti talatin,mommy da Aslam suna zaune suna hira. "Aslam jeka duba yarinyar nan me takeyi ne har yanzu" Mommy ta faɗa aɗan hasale. Da sauri kuwa Aslam ya mike dama abinda yake so kenan. "To anty "ya fada yana nufar dakin. Tana kwance abinta idanunta alumshe,kamar mai barci.ƙarasawa Aslam yayi bakin gadon ya zauna. Ido ya zubawa kyakykyawar fuskarta kamar yau ya fara ganinta.sosai yake masifar jin sha'awar Islam na ratsa dukkan sassan jikinsa,yana muradin jin ɗumin jikinta, ahankali ya kwanta agabanta,suna fuskantar juna,kallonta yayi na wani lokaci yana ƙara jin bukatarsa gareta na karuwa,cikin sanda ya sanya hannunsa kan kyakykyawan lips dinta Yana zagayewa da ɗan yatsansa. Nan take Islam ta tsinci kanta cikin wani irin shaukin mijin nata.tayi lub kamar mai barcin gaske. Zare hannunsa yayi tare da matso da fuskarsa sosai ya dora bakinsa kan na Islam ya fara kissing. Duk abinda yake Islam na jinsa,saidai gaba ɗaya jikinta yayi wani irin sanyi,kasala ta kamata ta yadda ta kasa koda daga hannunta bare ta hanashi abinda yakeyi, domin har ga Allah itama ta na bukatar hakan. Aslam kuwa sosai yake romancing Islam,cikin zaƙuwa da bukatuwa,yake wasa da sassan jikin Islam,saiga Islam tana wata irin mika tare da da kara matsowa jikin Aslam sosai. Saida tafiya tayi nisan da Aslam jikinsa har ya fara rawa, asalamiyyar sa kuwa sai haniya take da neman abinci,zuwa wannan lokacin tuni Aslam ya rabasu da kayan jikinsu. Kamar wanda aka tsikar Islam tayi saurin zabura tare da ture Aslam daga jikinta. Sai haki take tana lumshe ido,dan itama ta kai matuka wajen bukatar Aslam ɗin. Cikin rawar jiki Aslam ya matso jikinta sosai kamar zaiyi kuka yace "Please Islam dan Allah awannan lokacin karki gujeni,karki hanamin abinda Allah ya halatta min,dan Allah ki tausaya mana,dagani harke muna bukatar juna"Aslam ya fada cikin rawar murya yana ƙoƙarin kamo islam. Da sauri ta kara matsawa baya tana hararar sa. "Wannan shine amfani na agareka ko?wato ka amfana da jikina kafin ka koma gurin waccan jakar ko?to kayi kuskure,wllh bazan taɓa amincewa da kai ba,dan kuwa na riga na gano jikina kake bukata,kuma bazaka taba samu ba"Islam ta faɗa tana ƙoƙarin sauka daga kan gadon. Cike da tarin damuwa jiki na rawa Aslam ya sauƙo shima tare da riƙe hannun Islam,kamar ya kwalla ihu take ji,me zaiyi ko ya nuna mata tasan yana cikin tsananin buƙatuwa da ita? "Islam nifa mijin kine Ina da hakki akanki dan me bazaki bani hakkina ba?me yasa bazaki tausayawa halin da nake ciki ba? Aslam ya fada cikin huci yana jin kamar zuciyarsa zata kama da wuta. "Saboda kai ba abin tausayi bane,kuma so kake ka cutar dani,nikuma bazan taɓa bari hakan ta faru ba,me zai hana ka jira ita masoyiyar taka,ko kuma kaje ta baka yanzu ma tunda an kusa daura muku aure?amma Islam kam tayi maka nisa ita da jikinta"tana faɗin haka ta warce hannunta tare da shigewa toilet. Dafe kai Aslam Yayi cikeda tarin damuwa,"why Islam ?why ?me yasa bazaki tausaya min ba?me yasa kika kasa fahimtar irin son da nake miki?bani da nufin cutar dake kece burin raina,Islam bani da inda zanje da bukatata sai gurin ki,idan kika gujeni zan shiga mawuyacin hali Please Islam ki tausaya min "Aslam ya fada kamar zai ƙwalla ihu yana mai zama jagwab abakin gadon. Sosai yake jin mararsa ta kulle masa kwanciya yayi akan gadon kamar wani maraya.idan ka ga Aslam awannan lokacin,dole ya baka tausayi. Islam kuwa tana shiga toilet din ta sanya wa kofar makullin,zamewa tayi agurin tare da sanya kuka,sosai Aslam ya bata mugun tausayi,saidai ba yadda zata iya,bazata yarda yayi amfani da jikinta kuma ya watsar da ita ba. Amma ita kanta tana matukar bukatar mijinta ajikinta,dan ita ba dutse bace,sannan kullum cikin cin abubuwa masu gina jiki da kayan fruit take,Dole zataji ta cikin wani yanayin lokuta da dama. Aslam ya jima kwance cikin mawuyacin hali,da gyar ya samu ya iya mikewa ya sanya kayansa,idanunsa sunyi jajur dazu, Kansa har wani ciwo yake masa,ahankali yake takawa ya fito falo,inda Allah ya so shi ma mommy bata falon dan haka da ɗan hanzarin sa ya bar falon,cikin mota ya shiga tare da kwantar da kansa jikin sitiyarin motar.ya rasa dalilin da yasa Islam taki tausaya ma,bata kalli halin da yake ciki ba haka ta tsallake ta barshi,daga yau in Sha Allah inhar ya amsa sunansa na Aslam,bazai ƙara neman wani abu daga garetaba, zaiyi ƙoƙarin kula da ita matsayin matar sa,amma zai barta da jikinta tunda gani take jikin nata kawai yake bukata. Da ƙarfi ya furxar da iska mai zafi daga bakinsa,lokacin daya ɗago kansa daga jikin sitiyarin. Wayarsa ya dauko ya kira lambar mommyn Islam,cikin sanyi murya yace "mommy Ina jiranta awaje,idan ta shirya"ya fada asanyaye. To mommy tace tana nufar dakin Islam ɗin. Mai take shafawa ajikinta mommy ta shiga"Islam wai tun ɗazu baki shirya ba ne?kinbar mijinki yana ta jiranki,maza kiyi sauri ki sameshi"mommy ta faɗa tana ƙoƙarin barin dakin. Turo baki Islam tayi tace"mommy nifa bance ya jirani ba,Dan Ni ba yanzu zan tafi ba" Kallon baki isaba mommy tayiwa Islam,kafin tace "Islam tashi kisa rigarki kije ku tafi tun kafin raina ya ɓaci"mommy ta fada ahasale. Turo baki Islam tayi kafin ta sanya rigar Tata,sannan ta dau mayafinta tana ta kunbure -kunbure ta fice. Tana zuwa ta shiga cikin motar tana ta ture turen baki. Haka suka kama hanya ba wanda ya ce da wani ci kanka. Kowa da abinda yake tunani.ahankali Aslam ke jan motar,dan gaba ɗaya jikinsa ba kwari,sai ajiyar zuciya yake saukewa. Suna isowa Islam tayi part dinsu ɓata ko kalli part ɗin Mommy ba. Da alama suma fushin ake dasu.kallo kawai Aslam ya biya daji kafin ya girgiza kai ya fito daga motar ya nufi part din nasu shima,dan yasan me Yakamata Kwanci tashi asarar mai rai,yau gashi har gobe za'a daura auren Aslam da husna.gida gaba ɗaya ya kacame da hidima,kowa da abinda yakeyi Abangaren ango kuwa, tun ranar da wannan abun ta faru agidan su Islam,gaba ɗaya ya fita daga harkar ta,duk da hakan yana masa zafi sosai cikin ransa,amma yayi alƙawarin bazai sake takura mata ba. Iyakar sa da ita ya kaita school ya daukota. Hakan kuma ba karamin damun Islam yayi ba,ashe Gara ma yake shiga sabgar Tata suyi koda fadan ne ta sami sassacin soyayyarsa dake azalzalar zuciyarta. Abubuwa sunyi mata yawa ga exam da suka fara jiya,ga batun kishiya,dan ma kullum mommyn ta na gidan ana hidimar biki.itake ƙara rarrashinta. Yau juma'a ta kasance ranar da za'a daura auren Aslam da husna. Islam tun safe take dakin ta wanda ta koma da kwana yanzu,banda kuka ba abinda takeyi. Tana kwance akan gado ta duƙunkune jikinta kamar mai jin sanyi. Da sallama Aslam ya shigo cikin dakin nata,yana sanye cikin farar shadda mai matukar kyau da tsada,kana ganinsa kaga ango. Cikin takunsa na kasaita ya ƙara so bakin gadon da take kwance tana kuka.wanda kamshinsa gaba ɗaya ya ciki dakin. Kuma shigowarsa bata sanya Islam daina kukanta ba. Tsayawa yayi daidai saitin kanta.fuskarsa ba wani walwala yake kallonta,amma cikin zuciyarsa yana mugun jin tausayinta,haka kawai yau yake jin jikinsa ba dadi kamar ba ango ba. "Menene yake damunki?"ya fada cikin muryar sa mai cike da jarumta. Shiru Islam tayi kamar an dauke ruwa ta daina kukan saidai hawaye dake zubowa. "Idan baki da lafiya ki sanar dani kafin na fita,dan zan jima ban dawo ba"Aslma ya fada cikin yanayi na rashin damuwa. Nan ma shiru Islam tayi,batace komai ba. Dage kafada yayi da ƙoƙarin nuna bai damuba,ya juya zai fice. Kawai sai ta kara sanya kuka mai sauti harda shashsheƙa. Tsayawa yayi ƙyam !agurin da yake ,tare da runtse idanunsa.har cikin ransa yake jin kukan nata. Juyowa yayi suka haɗa ido tana kallonsa tana kuka. "Islam !zo nan"ya fada cike da nuna tausayawa. Kamar wata yarinya haka Islam ta sauko daga kan gadon ta nufoshi tana murtsuka idonta. Tana zuwa ta tsaya agabansa. "Menene yake damunki"ya fada cikin kulawa. Shiru kawai tayi tana kukanta. Ahankali ya sanya hannunsa ya janyota kusa dashi tare da rungumeta ajikinsa. Ƙam islam ma ta rikeshi tareda kara sautin kukanta. Muje zuwa masu karatu. Mrs babi ce Anty mammy. [10/30/2022, 7:45 AM] Abk: 75/76 ___________Kuka Islam kawai keyi ta ƙanƙame Aslam,ji take kamar rayuwarta ake ƙoƙarin daukewa,gaba ɗaya zuciya da gangar jikinta sun sare,wani irin yanayi mai kama da kewa take ji acikin jikinta. Tana ji kamar Aslam zaiyi nisa da ita ne,ko kaɗan zuciyarta bata raya mata abu mai daɗi game da auren Aslam. Kusan minti biyar zuwa goma suna tsaye. Islam na kuka mai tsuma zuciya,kukan da kana jinsa kasan kuka ne mai ciwo acikin zuciya.hakan ya sanya Aslam yin shiru bai hanata kukan ta ba,yasan koba komai yin kukan zai rage mata kaso da yawa na cikin damuwarta. Saidai shima cike zuciyarsa take da damuwa,sosai yake jin daci cikin ransa,bai san me yasa gabansa ke ta yawaita faduwa ba, sam bazaice ga yanayin da yake ciki ba, farin ciki ne ko akasin hakan,shidai yasan yana ji aransa bazai iya fasa yin auren nan ba,sannan kuma yana jin Husna har cikin zuciyarsa ko da yaushe.sai dai Islam na maƙale cikin zuciyarsa,hasali ma ita ke yawaita fado masa cikin rai akoda yaushi, saidai da zaran hakan ta faru,gabansa ke yanke wa ya fadi,sai kuma tunanin Husna ya Kunno masa kai. Wayar sa ce ta dauki ƙara alamun ana kiransa. Ahankali ya zare hannunsa daya tare da dauko wayar,numbern Abba ya gani,hakan yasa shi saurin dagawa yana faɗin "hello Abba"da siririyar murya mai cike da damuwa. Ta can bangaren kuwa Abba ne yace "wai Aslam kana inane? Har yanzu baka zo ba?zamu daura auren nan fa idan baka zoba ba"cewar Abba cike da ƙosawa. "Abba kayi hakuri ganin zuwa yanzu in Sha Allah"ya fada yana maida wayar aljihunsa. Ahankali ya ɗago fuskar Islam wacce tayi jajur tsabar kuka,idanunta sun kumbura sun ɗanyi jaa. Kallon juna suka fara cikeda so da kauna,wanda ko wannen su keyiwa dan uwansa. Ahankali Aslam ya sanya hannunsa yana sharewa Islam hawayen idanunta wasu na zubowa. "Islam kiyi hakuri,ki ɗauka wannan auren da zanyi ƙaddara ce,wacce bamusan dalilin hakan ba sai Allah,Islam nayi miki alƙawarin bazan taɓa cutar dake ba,inhar ina cikin hayyacina, domin kedin ta musamman ce cikin zuciyata,akwai maganar da nake son faɗa miki mai matukar muhimmanci,amma lokaci bazai bani damar faɗa ba yanzu,saidai idan na dawo zan sanar dake sirrin dake cikin zuciyata,ina so kiyi min alƙawarin bazaki ƙara kuka ba"ya fada yana kara share mata hawayen. Kallonsa Islam kawai keyi,tana tunanin wacce maganar zai sanar da ita haka ?me yake son faɗa mata? Katseta yayi da cewa"kinyi shiru baki ce komai ba,ki fadamin bazaki sake kuka ba har na dawo"ya fada yana janyota jikinsa sosai. Ahankali Islam ta daga masa kai,alamun tayi alkawarin bazata sake kukan ba. Murmushi yayi tare da sumbatar goshinta yace "good girl yanzu kije kiyi wanka kiyi kwalliya domin ni, ina buƙatar kiyi min kwalliya mai kyau ki jira zuwana kinji my...lo" Sai kuma yayi shiru tare da kara kissing lips dinta na Dan wani lokaci,kafin ya kalli idanunta yace "karki manta zan sanar dake magana mai matukar muhimmanci,ki jirani " Dan turo baki Islam tayi tare da murguda baki tana ɗan ƙunƙuni. Murmushi yayi tare da cewa"ina son wannan dan bakin na rashin kunya,amma akwai lokacin da zanyi maganin sa sosai"ya fada yana kissing lips dinta kafin ya nufi ƙofa.harya kai bakin ƙofar ya juyo yana kallonta dauke da murmushi akan fuskarsa yace "saina dawo Islam,karki manta kece hasken zuciyata kuma abar tunanina akoda yaushe,kina da gurbi mai girma anan"Aslam ya fada yana nuna saitin zuciyarsa,kafin yayi waje da sauri. Kasaƙe !!Islam ta tsaya kamar an dasata,sosai kalaman Aslam suka tsaya mata aranta,itace abar tunaninsa kuma hasken zuciyarsa?kodai Aslam ya fara sonta ne?wayyo Allah , Allah ya tababbar mata da zarginta, amma kuma idan sonta yake mai yasa zaiyi aure?kodai ita budurwarsa ce ada husnan?Amma koma dai menene zata jira dawowar tasa,dan jin me zai faɗa mata. Murmushi tayi cikeda jin sanyi cikin zuciyarta,tana mai hasaso cewar ga Aslam nan zaune gabanta yana furta mata kalaman soyayya,wani irin lumshe ido tayi tare da fadawa kan gado ta kwanta idanunta arufe.filo ta janyo ta ƙanƙame shi aƙirjinta,tana jin kamar Aslam ta ƙanƙame haka. "Ina sonka Aslam,Ina ƙaunar ka,Please kaima ka soni kamar yadda nake sonka,kada ka juyamin baya bazan iya jurar hakan ba"ta faɗa ahankali idanunta alumshe. Da sauri ta miƙe ta shiga toilet tayo wanka,zama tayi yau karon farko arayuwarta tayi kwalliya,ba ƙaramin kyau kuwa tayi ba,ita kanta batasan cewar ta iya kwalliya haka ba sai yau.wasu sabbin riga da siket ta dauko wanda bata taɓa sanyawa ba ma,ta sanya.cif suka zauna ajikinta,kamar ajikinta aka dinka. Haba hips ɗin nan yayi ɗam_ɗam cikin fisis siket din. Ga yar rigarta mai bala'in kyau,Brest cube ɗin nan yayi cas atsaye ƙam kamar zai tsokanewa mutun ido. Lol. Kasancewar bata iya daurin dan kwali ba,sai kawai ta daure uban tulin dogon gashin kanta,ta sake jelar baya .sannan ta daura ɗan kwalin ta soke shi ta gefe.haba sai ya bada wani style mai matukar kyau. Islam da kanta saida ta yaba kyan da tayi. Murmushi tayi tunowa da Aslam da tayi,ko yaya zaiganta idan ya dawo?ko zaiji dadin kwalliyar da tayi domin shi? Turare ta fesa ajikinta mai daɗin ƙamshi.sannan ta sanya flat shoe ta nufi part din mommy gurin mommynta. Gidan cike yake da jama'a ana ta hidindimu. Duk inda Islam ta ratsa sai an bita da kallo,Masha Allah kawai wasu ke cewa,wadanda suka san Husna kuwa suna mamakin ta yaya Aslam Yana da wanna matar zai auri Husna? Ba ƙaramin daɗi mommyn Islam da granny sukaji ba,ganin Islam ta sake har tayi wanna kwalliya mai kyau kuma ta shigo cikin jama'a. Nan sukayi ta rarrashinta da kalamai masu dadi. Kuma ba laifi ta saki jikinta ba kamar yadda take yi daba, kuma ba komai ke kara karfafa mata gwuiwa ba sai maganar da Aslam yace zai sanar da ita mai muhimmanci,tana kyautata zaton maganar zata faranta mata rai,dan kuwa yanayinsa ya nuna hakan. Lokaci zuwa lokaci zakaga tayi dan murmushi,Bama idan ta tuno yace itace farin cikin sa,kuma abin tunaninsa. Kasancewar anyi walima bayan daurin auren,hakan yasa Aslam bai dawo da wuri ba,sai wajen azahar. Wanda zuwa wannan lokacin Islam ta fara sarewa akan anya kuwa zai dawo. Tana zaune kan gadon granny ta buga uban tagumi,hancinta ya shaƙo mata daddaɗan ƙamshin Aslam. Lumshe ido tayi gabanta na faɗuwa. Ahankali Aslam ya ƙaraso kusa da Islam ya zauna,hannu ya sanya ya zare mata tagumin yana kallonta. Itama ɗago kanta tayi tana kallon shi. "Masha Allah Islam ɗita,kinyi kyau matuka kwalliyar ki ta haskaka min zuciya "Aslam ya fada yana riƙe hannun Islam. Murmushin farin ciki ne ya kwacewa islam,idanunta akan Aslam tace "kace zaka fadamin magana mai muhimmanci idan ka dawo,tun ɗazu nake jiranka"Islam ta faɗa cikin zazzafar muryarta. "Ina sane Islam ban manta ba,amma tashi mu koma part din mu,saina fada miki acan"cewar Aslam Yana kama hannunta suka fito daga part ɗin mommy zuwa nasu. Mutane sai kallon su suke,ana ƙus-ƙus. Kai tsaye ɗakinsa ya shigar dasu.abakin gado ya zaunar da islam,shi kuma ya janyo stool din gaban madubi ya zauna. Hannunta ya kamo ya rike cikin nashi yana ɗan murzawa ahankali. Hannun nasu Islam ta bi da kallo,kamar yadda shima Aslam ke kallon hannun nasu dake sarƙe dana juna. Ahankali ya ɗago kansa yana kallon Islam,kafin ya kira sunanta cikin wata kalar voice"islam"ya fada ahankali. Wanda saida tsikar jikin Islam ta zuba yummmm, sakamakon yadda harafin sunan nata ya fita daga bakinsa. Ahankali cikin faduwar gaba Islam ta ɗago kanta ta zuba masa kyawawan idanunta. Kallon juna suke kamar yau suka fara ganin juna. Saida ya sauke ajiyar zuciya kafin ya fara magana kamar haka"Islam,bansan ta yaya zaki karbi magana ta ba,bansani ba ko zaki yarda da abinda zan sanar dake yanzu ba,amma nikam na sani har cikin zuciyata haka abin yake.ya dan yi shiru yana sauke ajiyar zuciya,tare dakai hannun Islam bakinsa ya sumbata. Kafin yaci gaba---"islam tun lokacin baya da Bama shiri dake,kina cikin raina,lokuta da dama nakan zauna na bata lokaci wajen tunanin ki,saidai a wancan lokacin ina daukan hakan ne amatsayin kiyayyar dake tsakanina dake,shine dalilin da yasa nake yawan tunaninki,kullum idan ban ganki ba bana jin dadi,ina shiga wani yanayi na damuwa. Na gwammaci in ganki koda zamuyi faɗa,kece mace ta farko da take kallon cikin idanuna tayi min rashin kunya,kuma ina kasa ɗaukan mataki akanta,kece mace ta farko da idan nayi niyyar yi mata wani mugun abu nakanji bazan iya ba. Kece mace ta farko data fara kiritamin tunani sakamakon ganin surarta,kece mace mafi ƙarancin shekaru dana taba mu'amalantar ta har nake tsayawa muyi jayayya,kinsan me yasa ? Saboda inyi ta sauraron muryarki,duk da raina yana ɓaci da irin zafafan maganganun da kike fadamin matsayina na wanda na girmeki,amma ina jin dadin sauraron muryarki,dan ita ke sanyani farin ciki. Islam bazan taɓa iya cutar da ke ba,koda kuwa ke zaki cutar dani,sannan bana iya jurar ganin wani yana cutar dake,kinsan halin da na shiga lokacin dana kulleki cikin mota?ya fada cikin yanayi na damuwa da jimami. Kallon sa kawai islam keyi ta kasa cewa komai,mamaki take sosai cikin ranta.duk wannan abubuwan da suke faruwa tsakaninta da Aslam,kenan shi hakan daɗi yake masa?kenan baya jin haushin yadda take masa rashin kunya? Ci gaba yayi da maganar sa"ji nayi kamar In shaƙe kaina ,sosai naji haushin kaina da kaina,sannan abun da ya kara sanya Ni cikin damuwa, shine yadda mukaje asibiti naga kinki yimin magana,kuma kin saurari likita,wllh awannan lokaci ji nayi kamar In kashe shi,sosai naji haushin ki wanna lokacin. Sannan lokacin da wannan shegen sergant ɗin ya dakeki, hmmmmm.ya sauke ajiyar zuciya mai cike da ɓacin rai.kafin ya dan matse hannunta yace "ina fita kai tsaye makarantar ku na wuce,wllh badan sunzo da wuri ba zan iya kashe shi, yadda nake jin zuciyata na tafarfasa. Islam duk waɗan nan abubuwan da suke faruwa bansan asalin meke damun zuciyata ba sai yanzu,Islam zuciyata acike take da tarin farin ciki Aduk lokacin dana tunaki kona ganki" Shiru Aslam Yayi tare da sauke ajiyar zuciya mai ƙarfi yana sumbatar hannunta . Kallon ta yake ido cikin ido,fuskarsa ɗauke da murmushi mai kayatarwa.sannan yace Islam yau zan bayyana miki sirrin dake zuciya ta,koda kuwa bazaki karbe shiba,hakan zai rage min raɗaɗin da nake ji game da ke acikin zuciyata. Islam ina matukar sonk....ƙarar da wayar shi ta dauka ne ya katsar dashi daga maganar da yake,cikin sauri ya dauko wayar tashi.kan kuce me tuni jikinsa ya dau karkarwa,cikin hanzari ya daga wayar yana mai karawa akunnensa. Kafin yayi magana Husna tace "Honey kayi sauri kazo zamuje gurin dinner kasan yau za'a kawo ni gareka" Cike da faduwar gaba Aslam ya ce"yadda kika ce hakaza'ayi Madam,ganin zuwa yanzu" Yana faɗin haka ya ajiye wayar,jikinsa dai rawa yake ,ya nufi toilet. Cike da mamaki Islam ke binsa da kallo,anya kuwa Aslam Yana cikin hayyacinsa?kodai bashi da lafiya ne?yanzun nan fa yake faɗa mata kalamai masu sanyi,yake sanar da ita irin yadda yake jinta aransa,amma daga kiran waya yama manta da abinda yake? Kodai karya yake faɗa mata dama? Yanzu kiran waccan shashashar yafi masa muhimmanci akan faɗa mata abinda ya sanya mata rai akai? Nan da nan ran Islam ya ɓaci hankalinta ya tashi sosai,me yake son cewa aƙarshen maganarsa?so yake fa yace yana sonta,amma wannan kamar ta katsar dashi. Tana nan zaune Aslam ya fito daga toilet cikin hanzari yake shiryawa.inda yake cewa islam"Please Islam kiyi hakuri idan na dawo zamu karasa maganar tamu,yanzu ina sauri wani uzuri mai muhimmanci ya sameni" Ya faɗa yana feshe jikinsa da turare bayan ya kammala sanya wata zazzafar shadda mai shegen kyau. Kallonsa kawai Islam ta tsaya yi zuciyarta kamar zata kama da wuta.cikin fushi za zafin zuciya Islam ta sauko daga kan gadon ta nufi ƙofa. Binta Aslam Yayi da kallo kafin ya fara kiran sunanta,amma ina ko inda yake bata kalla ba tayi waje cikin fushi. Muje zuwa masu karatu. Please kuyi hakuri na jina shiru kwana biyu,kunsan yanayin jikin sai ahankali . Idan a jini shiru ayimin afuwa 🙏 Na gode. Anty mammy ce Mrs babi. [10/30/2022, 7:47 PM] Abk: 77/78 ____________Binta Aslam Yayi da kallo,kafin ya fara kiran sunanta. Ko inda yake bata kalla ba,bare yasa ran zata tsaya. Ficewar ta tayi cike da ɓacin rai,lallai wannan husnan tayi nisa cikin zuciyar Aslam,ita ta rasa me yasa duk irin yadda Aslam ke yin wani abu mai muhimmanci,da zarar ta kira shi awaya yake zama kamar wani sakarai,ita gani ma take kamar tsoron husnan yake,har wani rawar jiki yake idan ta kirashi awaya. Cikin dakin ta ta shige tare da fizge dankwalin kanta ta jefar dashi,ta fizge ribom ɗin ma ta jefar shi aƙasan dakin tana hararar sa kamar shine yayi mata laifin. Ji take ahalin yanzu idan da zata ga wanna n Shegiyar Husnan,saita shaƙe mata wuya ta mutu kowa ma ya huta. Dan taga alama nema take ta rabata da farin cikinta,tun kafin ta shigo gidan kenan,ina kuma ga ankawota cikin gidan? Dole ta zage itama,ta kowane hali ta ga cewar husna bata rabata da mijinta ba. Tana zaune tana jiran Aslam ya shigo dan ya rarrasheta. Saidai shiru shiru bai shigo ba,hakan tasa ta mike tare da fitowa daga cikin dakin. Shiru ba motsin Aslam aɗakin nashi,kodai tafiyarsa yayi?Islam ta faɗa cikin ranta. Da sauri ta shiga ɗakin nashi,aikuwa baya ciki. cike da mamaki da mutuwar jiki ta zauna abakin gadon dakin tana kafe kayansa daya cire da ido. Shikuwa Aslam tana fita yaji wani irin ba dadi cikin ransa,so yake yaje ya bata hakuri,amma yana fitowa ya tsinci kansa da wucewa kofar fita kai tsaye.ba tare da ya ko kalli dakin Islam ba. Saidai can kasan zuciyarsa yana jin bai kyauta wa Islam ba,amma bazai iya ketare maganar ƙiran da Husna ke masa ba. Dan haka ya wuce kawai akan idan ya dawo zai rarrashe ta. Islam kuwa dataga zaman ba abinda zai kara mata sai ɓacin rai,saita tashi ta koma dakin ta,Dan kwalinta ta ɗauko sannan ta fito zuwa falo.tsaye tayi tama rasa me Yakamata tayi. Ta nan tsaye saiga mommyn ta ta shigo part din,Dan taga ficewar Aslam. Dama tun dazu hankalin ta yana kan Islam ɗin. Tana ganin yanayin da Islam ɗin ke ciki,tayi saurin ƙarasowa cikin Falon. Dan taga kamar bata cikin hayyacin ta ma.ta kure guri ɗaya da ido alamun tayi kisa cikin tunani. Nan dai mommyn ta ƙaraso tare da kama hannun yarta suka koma cikin dakin ta. Nan tayi ta mata nasiha da bata shawarwari masu amfani. Misalin ƙarfe takwas na dare,motocin kawo amarya sukayi jerin gwanon zuwa gidan su Aslam,inda anan amarya ma zata zauna kafin Aslam ya kammala ginin tanfatsetsen gidan sa da yake ginawa. Ba karya idan ka ga dakin Husna kasan yar gata ce ta gaske. Dan ankashe kudi mahaukata wajen kayata mata dakunan ta zuwa kitchen. Lokacin da suka kawo amarya Islam na zaune adakinta ita da sauran yan uwansu da suka zo bikin. Tun daga yanayin da suka shigo gidan kasan ba arziki,dan sai yada habaici sukeyi.haka dai suka gama rashin mutuncinsu suka bar amarya ita kadai adakinta. Haka ma yan uwan Islam suka rarrasheta sannan suka barta. Mommyn Islam ma sosai tayiwa yarta nasiha da addu'oin zama lafiya kafin ta bar gidan. Kuma anan aka bar A'isha dan debewa Islam kewa. Islam na zaune ita da A'isha,ta rungume yarinyar ƙam ajikinta,zuciyarta na mata zafi sosai,inda Allah ya taimakata ma shine,addu'ar da take cikin zuciyarta. Ba jimawa ango ya shigo cikin gidan,kai tsaye ya nufi dakin Islam,dan so yake ya ganta,tun ɗazu itace aransa. Harya kama handle din kofar dakin zai bude ya tsinkayo Muryar Husna "honey ! Ina kuma zaka shiga?bayan kasan yau da gobe da sati guda ma duka nawa ne ?ta faɗa cikin yanayin shagwaba tana nufoshi. Lokacin har ta sauya kaya daga less din da aka kawo ta dashi zuwa wasu tsinannun nighty,Wanda suda babu ba maraba.gaba ɗaya rabin na shanunta awaje yake. Da sauri Aslam ya juyo yana kallonta,dan baiyi tsammanin jinta agurin nan yanzu ba. Murmushi ya sakar mata cike da jin wani irin shaukin ganinta da yayi ahakan, duk da ba wani fasali bane da ita,amma agurinsa gani yayi kamar tafi kowa kyan ƙira da zati. Nan da nan tsohon tsuminsa ya tashi. Saidai can cikin ransa yana mamakin yadda daga kawota yau har ta iya yin irin wanna shigar kuma ta fito har babban falon part din nasu. Saidai idonsa ya rufe dan haka sakin handle din kofar yayi tare da nufota,hannunsa riƙe da ledojin kaji. Cikeda tafiyar jan hankali Husna ta nufi cikin Falon tana Gara goga turaren dake hannunta a tsakanin ƙirjinta. Nan take kuwa Aslam ya shaƙi wannan turare,tuni tunaninsa ya gushe ya nufi Husna arude. Rungume ta yayi sosai ajikinsa yana sakin ajiyar zuciya. Ba kunya bare kawaici Husna ta lalubo bakin Aslam ta jefa nata ciki ta fara missing dinsa kamar zata cinyeshi. Abinka da wacce ta jima tana neman wanna damar. Nan shima ya biye mata suka fara lalube juna,cike da zaƙuwa. Islam kuwa tana zaune rungume da A'isha taji kamar ana taba kofar ɗakinta.hakan yasa ta kasa kunne amma bataji an shigo ba,saidai tana iya jin maganganu ƙasa-ƙasa, dan haka kwantar da A'isha tayi tare da nufo ƙofar ta fito zuwa falon. Wata irin faduwa da gaban Islam yayi, saura kaɗan ta fadi kasa.sakamakon arba da su Aslam da tayi suna neman amarcewa afalo. Da sauri ta dafe bango tare da saurin juyawa ta koma daki.banda bugawa ba abinda gabanta keyi. Dafe ƙirjinta tayi cike da tarin baƙin cikin abinda idanunta suka gani.lallai na miji ɗan kunama ne,kalli yadda ya barta anan yaje yana lalube wata. Zama tayi bakin gado ta janyo A'isha jikinta,kawai kuka ya kwace mata. Sosai ta ƙanƙame A'isha kamar zata karya ta ajikinta,har saida Aishan ta fara mutsu-mutsun tashi kafin ta sassauta mata rikon. Kuka take ahankali marar sauti,saidai gaba ɗaya jikinta rawa yake. Su kuwa su husna da gyar Aslam ya kwaci kansa yana haki,idanunsa gaba ɗaya sun rine sun kankance.kamar yadda na Husna ya koma jajur, da gani Husna irin jarababbun matan nan ne masu kokarin tsotsewa na miji ruwan jikinsa idan suka tarfa shi. Sai wani layi take tana kara kamo Aslam. Hannunta ya kama suka nufi dakin ta.bayan ya dauki ledar kajinsa. Suna shiga ya zaunar da ita abakin gado kafin ya nufi kitchen da kansa ya dauko plate da kofuna. Tana zaune sai mutsu-mutsu take tana tattaba ƙirjinta. Dibar musu tasu yayi kafin ya dauki leda ɗaya yace "amaryata bari na kai wa Islam wannan na dawo yanzun nan"ya fada yana shafa uban nonuwanta da sukayi rigija cikin rigar barcin. Yamutse fuska tayi tare da haɗe rai tace "a'a fa bana son shiga hakki honey ka ajiye mata afalo mana ka kiranta tazo ta dauka" ta faɗa cikin haɗe rai tana turo baki kamar shantu. Dan jim aslam yayi yana kallonta,ganin yadda ta bata rai sai yaji ba dadi,dan haka ya ajiye ledar yana mai cewa"to my love ya kike so ayi"ya fada yana zama kusa da ita tare da rungumeta ta gefe. "Kawai ma bani na kai mata da kaina inyaso ma saimu gaisa da ita"ta faɗa tana daukar ledar bayan tayi wani tunani cikin ranta. Ko kaɗan Aslam bai so hakan ba,Amma ji yayi bazai iya mata musu ba.dan haka yana ji yana gani ta dauka ta nufi ƙofar fita daga dakin,cikin wannan shigar tata,ba kunya ba tsoron Allah. Runtse ido Aslam yayi tare da kwanciya rigingine,sosai yake jin ba dadi cikin ransa,so yake yaje yaga Islam ya rarrasheta,dan yasan zuwa yanzu tana nan cikin damuwa da tashin hankali,ko kuka ma take waya sani. Husna kuwa kai tsaye ta haifa dakin da take tunanin shine na Islam,kallon wulaƙanci take bin dakin dashi kafin ta taɓe baki ta shiga can uwar dakan ba ko sallama. Kasancewar Islam ta juya bayanta ne,hakan yasa tayi saurin share hawayen ta jin an bude kofar,dan atunaninta Aslam ne.saidai kuma wani irin warin turarene mai ƙarfi da ya ziyarci hancin ta. Hakan yasa ta gane ba Aslam bane Dan haka da sauri ta juyo,idanunta suka sauka akan fuskar Husna. Nan aka fara kallon kallo. Cike da rainin hankali Husna ke kallo islam, tana wani tabe baki da girgiza jiki. Islam kuwa kwantar da A'isha tayi tare da mikewa tsaye itama,ƙugu ta kama tare da kanƙantar da ido tace"ke uban me ya kawo ki dakina?har kikazo kina min girgije -girgije kamar bishiyar mangwaro da wannan jikin naki na garada" Islam ta fadi haka cike da rashin tsoro. Husna kuwa buɗe baki tayi da mamaki tana kallon Islam,lallai yarinyar bata da kunya,har ita take fadawa waɗannan maganganun kai tsaye ba tsoro?itane mai kama da bishiyar mangwaro?aikuwa dole taci uban yarinyar nan wllh. Cikin ɓacin rai da jin haushin abinda Islam ɗin tayi mata tace "ke dan uwarki Ni kike fadawa wannan maganar?saboda baki da kunya?ko ba babba agidanku ne" Husna ta fada cikin hayayyaƙowa islam kamar zata daketa. "Saidai uwarki dan ubanki,wllh idan kika ƙara zagina zaina ci uwarki ,karuwa marar kamun kai banza kucaka,kuma wllh ki ficemin daga daki kokuma yanzu nayi maganin ki"Islam ta fadi cikin zallar masifa tana nufo Husna. Husna ma cikin masifa da ɓacin rai tace "lallai yarinyar nan wuyanki ya isa yanka,wllh zaki gane baki da wayo,zaki san kinyiwa Husna rashin kunya"ta faɗa tana jefar da ledar kazar dake hannunta tayi waje,kafin Islam ta ƙaraso. Dan taga yarinyar tsayayyace, kuma da alama zatayi karfi. Ƙwafa Islam tayi tana mai tura ƙofar ta da ƙarfi tace "shegiya tsohuwar guzuma,da kin tsaya kinga danyen kai wllh" Ledar kazar ta dauka ta feho ta falon sannan ta kulle ƙofar ta ta koma cikin dakin. Kwanciya tai tare da rungume A'isha ajikinta,ranta abace sosai.Aslam ya nuna mata iyakarta,wato kazar ma saidai matarsa ta kawo mata?saboda ga mayunwaciyar kaza ko?hmmm duk zatayi maganinsu ne. Husna kuwa cike da ɓacin rai ta koma ɗakinta buguzun -buguzun. Tana shiga ta nemi guri ta zauna tana hura hanci. Da sauri Aslam ya taso yazo gareta yana tambayar lafiya ?Meya faru da ita take bata rai. "Wannn yarinyar ashe bata da kunya?harni zata kalla tana fadawa magana son ranta?wllh saina koya mata hankali agidan nan,yauma Sa'a taci ina cikin farin ciki amma d saina ci uwarta wllh"ta faɗa cikin huci tana kumbura baki. Hmmmm shi dama Aslam yasan za'ayi haka,dan dai Husna bata san wacece Islam ma,amma da bazata tunkareta bama. Cike da son kwantar mata da hankali ya janyota jikinsa yana faɗin"haba babyna karki bari ɓacin rai ya bata mana wannan ranar mana.ki barta kawai kishine ke damunta kawai.amma zan ja mata kunne karta ƙara yiwa babyna rashin kunya"ya fada yana janyota jikinsa tare da fara bata tsokar kaza. Nan dai suka ci sukasha,tun agurin Husna ta haye cinyar Aslam tana masa salo iri-iri,nan dai aka fara damben arziƙi. Abin mamaki mai makon aji ango yana zuba sanbatu da surutai,a'a wannan kam amarya ce ta kwace wannan fagen,dan ihu ta rinkayi tana sunbatu da zantuttuka iri -iri. Kana ji kasan bana zafi ko ciwo bane na jin dadi ne.yayin da ango kuwa gaba ɗaya kansa ya kulle,dan shikam kawai yana yi ne ,amma badan yana jin dadin abun ba, maimakon yaji farin ciki da nishaɗi ma,a'a sai wani irin kunci da ɓacin rai daya mamaye zuciyarsa,duk da bai taba kusantar mace haka ba,amma yasan cewa Husna ba cikakkiyar budurwa bace,dan kuwa kai tsaye yaji ya shigeta ba wani gargada. Hakan na nufin ba shine wanda ya fara kusantar Husna ba. Sosai ransa ya ɓaci ,saidai bazai iya tuhumar ta ba ko kaɗan. Haka ta gama haukanta da sumbatu, yana jinta. Bayan komai ya lafa ne Husna ta jirkice can gefe tana sharbar barci,yau taji zumar da bata taba dandanar irin taba,ta samu abinda rai da zuciyarta ke so. Kallonta kawai Aslam keyi,ransa abace sosai ,daga karshe ya tashi ya shiga toilet Yayi wanka sannan ya dawo ya kwanta tare da juya mata baya. Can cikin dare yana barci kawai sai jin mace yayi ta haye kansa tana ƙoƙarin zare masa wandon dake jikinsa. Ranar dai Aslam yaga abinda yafi karfinsa,dan gaba ɗaya Husna ta hanashi barci minti kaɗan zai jita ajikinsa.har gari ya waye. Gaba ɗaya jikinsa ciwo yake,shiba da jin dadiba amma shine da shan wahala. Wanka ma tare sukayi,bayan sun shirya suka fito falo,sai wani maƙale masa take,shikuma yana riritata kamar jaririya, amma cikin ransa wani irin kunci da ɓacin rai yake ji. Ga ciwo da kansa keyi. Muje zuwa Mrs babi ce Anty mammy. [11/9/2022, 11:23 AM] Abk: 79/80 _______________Gaba daya jikin Aslam ciwo yake,shiba da jin dadi ba amma shine da shan wahala,sai yazama tamkar shine amaryar, Husna kuma angon. Wanka ma tare sukayi,inda badan yayi da gaske ba,a toilet din ma so tayi ta far masa,yana gocewa. Haka dai sukayi wanka suka fito,bayan sun shirya ne suka fito babban falo,sai wani maƙale masa Husna keyi,duk ta hanashi sakat, shikuma sai riritata yake kamar wata jaririrya, duk da yadda yake jin zafi da radaɗi gami da ƙunci cikin zuciyarsa,haka yake biye mata yana riritata. Islam kuwa bayan sunyi sallar asuba ita da A'isha,kwanciya suka ƙarayi, sai wajen bakwai na safe kafin suka farka.wanka tayiwa Aisha tare da shiryata cikin wasu riga da wando na jins masu kyau,sannan ta daure mata gashin kanta mai uban yawa.da yake mommyn Islam dibo musu kayansu tayi suka ajiye agidan saboda biki. Islam ma cire kayanta tayi tare da sanya rigar wanka,wacce ta tsaya mata iya gwuiwar ta,rigar fara ce mai ɗan kauri. Kanta ba ko huta bare dan kwali,hakan ya ba gashin kanta damar bazuwa gadon bayanta yayin da wani yake zubowa yana ɗan rufe mata fuska,saita sanya hannu ta kawar dashi. Bayi take ƙoƙarin shiga,A'isha tace ""anty zan sha yoghout" Juyowa tayi tana kallo yarinyar kafin tace "to jirani nayi wanka saina dauko miki afalo,kinga Ni bani da yoghout anan"ta faɗa tana juyawa dan shigewa cikin toilet ɗin. "Ni anty ki dauko min kafin kiyi wanka,yanzu zansa"A'isha ta faɗa cikin yanayin murya mai nuna tana son yin kuka,dan A'isha mayyar yoghout ce,bata da wani aiki saina shan yoghout. Juyowa tayi tana kallon yadda yarinyar ke murza ido da son yin kuka,ahankali ta tako zuwa gaban yarinyar tace "to kiyi shiru karkiyi kuka kinji?bari na dauko miki"ta faɗa tana shafa kan A'isha tare da nufar ƙofa. Kai tsaye ta bude kofar da zata sadaka da babban falon,ko kaɗan bata kula da su Aslam dake zaune akan kujera ba,wanda Husna ke ta faman kissing bakin Aslam, ta wani zauna rigija akan cinyar sa. Cikin takunta mai cike da ɗaukar hankali ta nufi ƙaton fridge din dake cikin falon,budewa tayi tare da dauko ƙatuwar jarkar yoghout,sannan ta rufe ƙofar fridge din ta juyo. Carab idanunta ya sauƙa cikin na Aslam,Wanda tun fitowarta ya ƙureta da idanuwansa,kallonta yake cike da tsantsar so da kauna,yayin da wutar sha'awarta ke ƙara ruruwa cikin zuciyarsa,nan da nan yaji asalamiyyar sa ta fara hanƙoro,ba ƙaramin kyau da shigar dashi cikin shauƙi ganin Islam cikin wannan shigar yayi ba. Da ƙarfi gaban Islam ya buga sakamakon ganin su da tayi ahaka,nan da nan ta karajin haushin Aslam cikin ranta.Wata uwar harara ta banka masa,taka tsaki mai karfi tare da juyawa cikin sauri ta nufi ɗakinta. Lokacin ne kuma Husna ta kalli Aslam,Dan gaba ɗaya ta fahimci hankalinsa baya kanta,sannn taji ƙarar tsaki,inda taga Aslam yabi da kallo itama tabi,cike da jin haushi da bacin rai take kallo Islam,da irin yadda take tafiya tana juya jikinta kamar wata tarwada. Cikin wata murya wacce ita adole shagwaba takewa miji tace"honey ! Kana ganin yarinyar nan,ta shigo mana ba sallama,da sassafen nan,sannan tana yiwa mutane tsaki,kuma bata gaida kowa ba kamar wasu sa'o'inta?gaskiya bazan dauki wannan rainin ba,daga yau karta ƙara shigowa falon nan dai-dai wannan lokacin,ai iskanci ne wannan, da son riskarmu cikin wani yanayin dan tasan duk wata mata mai matsayi yanzu tana tare da mijinta"ta kai zancen ta tana wani kwantar da kanta akan ƙirjin Aslam,tare da shafa kwantaccen gashin dake kwance akan ƙirjinsa.tana bugawa Islam harara. Ɗan kallon ta Aslam Yayi,kafin ya maida idanunsa kan,Islam,wacce tayi tsaye riƙe da jarkar yoghout ahannun ta, jin abinda Husna ke faɗa. Juyowa tayi suka haɗa ido da Aslam,hannunta ta sanya wanda ba komai acikinsa,tare da riƙe ƙugunta tana jiran jin amsar da Aslam zai bayar. Shikuwa cikin kwantar da murya kamar wanda yake jin tsoro husnan yace "baby ki barta kawai,kinga nan babban falone,kuma dole kowa acikinku zai shigo yayi wani uzurin.ki kwantar da hankalin ki,ki barta ta rinƙa shigowa tayi uzurinta"ya fada yana shafa gefen fuskarta,aƙoƙarinsa na kwantar mata da hankali. Taɓe baki Islam tayi cike da jin haushin amsar da Aslam ya bayar,wato dai idan ta fahimta fa kamar tsoron Husna yake? "Gaskiya honey nikam za'a takura min,haka kawai da sassafen nan,mutum yana hutawa da mijinsa adameshi da sintiri?nikam kawai ka hanata shigowa falon nan"Husna ta fada tana turo baki da juyar da kanta alamun tayi fushi. Kafin aslam yayi magana Islam ta rigashi. "Da yake nan ɗin gidan ubanki ne, shine zaki ce karna ƙara zuwa falon nan ko? To bari kiji koshi mijin naki matsoraci wanda yake yiwa mace biyayya,bai isa ya hanani shiga duk inda nake so agidan nan ba,kuma wllh ina gargaɗin ki,ki fita hanyata, dan wllh idan kika cika min ciki saina koya miki hankali.banza mai siffar akori kura,anƙi agaidakin kiyi duk abinda zakiyi "Islam na kaiwa nan azancen ta bankawa Husna harara tayi juyawarta ta shige dakin ta.dama ta kusan shiga ɗakin. Wani irin ihun ɓacin rai Husna ta sanya tana mikewa tsaye. "Kan kazakazar uban nan,honey kana jin abinda yarinyar nan ke fadamin?zagina fa tayi?wllh yau saina ci uwar uwarta agidan nan,shegiya dangin tsiya wllh na tsani wannan yarinyar"cewar husna kenan cikin daga murya tana ƙoƙarin bin Islam ɗakinta. Da sauri Aslam ya riko hannunta,sosai ransa ya sosu da zagin da tayiwa Islam,koba komai ai tasan Islam yar uwarsa ce,kuma idan ta zagi dangin Islam,tamkar nashi ta zaga.ransa ya ɓaci sosai,amma kash!! bazai iya nuna mata ɓacin ransa afili ba. Dan haka cikin kwantar da murya da rarrashi yace"haba baby Dan me zaki kula wannan yarinyar?bata da hankali fa ai kinfi karfin yin faɗa da ita,kiyi hakuri kodan ni, kinga ƙanwata ce bata da kunya nima bana kula ta bare ke"ya fada yana janyota jikinsa bayan ya zauna. "Wllh honey bazan yarda wannan Shegiyar mai kama da aljanu tana min rashin kunya ba,aini ba sa'arta bace"ta faɗa cikin huci tana hura hanci. "Sorry baby ki kwantar da hankalin ki,yanzu kije ki shirya zanje nayi mata magana,zan ja mata kunne akan karta ƙara miki rashin kunya, idan kuma tayi min ba dai-dai ba jikinta ya fada mata"Aslam ya fada yana ɗan haɗe ransa dan ta yarda da gaske hukunci zaiyiwa Islam. Shashashar kuwa cikin farin ciki tace wllh jeka kayi mata duk hukuncin daya dace na rashin kunyar da tayi mana shegiya mai dogon hanci kamar biro" Husna ta fada tana mikewa tsaye,ɓatar -ɓatar,rigija rigija ta nufi ɗakinta tana faɗin"karfa ka dade kuma idan ka shiga,sannan ban amince koda kallon da zaisa taji daɗi kayi mata ba"ta faɗa tana kallonta dai -dai lokacin da taje kofar ɗakinta. Ɗan haɗe fuska yayi kafin yace "Allah ya kiyaye waccan yarinyar zan wani tsaya yiwa kallon da zataji daɗi?wannan ai saike ginbiyar mata "ya kai ƙarshen maganar yana sakar mata ƙayataccen murmushi. Wani fari tayi cikin jin daɗi kafin tace "yawwa honey na,kayi sauri ina jiranka"ta faɗa tana shigewa cikin dakin. Bin ƙofar Tata Aslam Yayi da kallo,haka kawai ya tsinci kansa da jin wani irin haushinta cikin ransa,tsaki yayi tare da nufar dakin Islam. Yana shiga falon yayi arba da ledar kazar daya siyo jiya ,har lokacin tana nan ayashe agurin da Islam ta wurgar da ita, gadai falon da alamun an gyara,amma ledar ko tabata ma ba'ayi ba. Kallon yabi falon dashi, A'isha ce ita kadai zaune tana shan yoghout dinta. "Oyoyo yaya Aslam"ta faɗa cikin dariya tana dirowa daga kan kujerar tayi gurinsa tare da rungumeshi. Murmushi yayi yana shafa kan yarinyar,yana sonta sosai dan kusan komai nata irin na Islam ne, hatta yanayin murmushinta saidai kawai Islam tafiya kyau sosai. "Oyoyo Easha, kin tashi lafiya?" "Lafiya kalau yaya,ina matar taka?ance aurenka akeyi "ta faɗa tana kallon fuskarsa. "Murmushi yayi tare da cewa"kina son ganin ta ne?" Da sauri tace "eh yaya ina son ganinta,yanzu ta zama antyna itama"ta faɗa cikin murna. "Murmushi yayi yace "to ina anty Islam take? "Tana cikin daki tana wanka"ta bashi amsa tana kurbar Yoghout dinta. Shiru yayi tare da kallon ƙofar uwar dakan islam kafin yace"to ki zauna anan,bari na dubota,inna dawo sai muje kiga dayar antyn naki ko?"ya fada yana shafa kanta. Dariya tayi cikin murna tace"to yaya ina jiranka,ka dawo yanzu fa!" Jinjina kai Aslam Yayi tare da tashi ya shige dakin Islam. Wani daddaɗan ƙamshine ya ziyarci hancinsa,wanda saida ya sanya shi lumshe ido,ahankali ya buɗe idon nashi yana bin dakin da kallo.ko ina agyare fess, ba kowa cikin dakin,sai ƙarar ruwa da yaji daga toilet.dan haka zama yayi abakin gadonta tare da jin wani irin sanyi da nutsuwa na ratsa sassan jikinsa. Islam kuwa tana kammala wankan ta ta daura wani dan guntun towel,Wanda da kaɗan ya wuce mazaunan ta ta fito. Fuskar nan tayi fayau, sai sheƙi take,sam ba alamun wasa akan fuskarta,dan fuskar Tata ahade take. Domin har zuwa lokacin tana jin haushin Aslam da matarsa cikin ranta,sannan tana jin wani irin kishi na yadda ta gansu afalon dazu.Hakan saiya haddasa mata damuwa sosai ta yadda kwata-kwata ta kasa walwala. Shikuwa Aslam kallo yabita dashi lokacin data fito,tun daga zara-zaran yatsun ƙafarta ya fara kallonta,har saida ya dire idannunsa akan santala -santalan cinyoyinta masu tsananin kyau da ɗaukar hankali,sai sheƙi suke,ga Dan damshin ruwan dake jikinsu,hakan ya kara musu wani yanayi na sanya mutum cikin shaukin kallonsu, wata ajiyar zuciya Mai haɗe da shashsheƙa Aslam ya sauke,kafin ya ɗago idanunsa,wanda suka fara sauya kala daga fari zuwa ja,ya sauke su akan tudun na fulaninta, wanda take ƙoƙarin cire towel din Dan sanya inner wear ,ai tuni Aslam yaji yawunsa ya tsinke,nan da nan yaji tsikar jikinsa na zubawa,lumshe ido yayi tare da huro iska mai sauti daga bakinsa. Sai lokacin Islam tayi saurin ɗago kanta tare da saurin maida towel din data fara warwarewa. Idanunta ne ya sauka akan Aslam,Wanda ya buɗe idonsa dake cike bukatuwarta yana ɗora su akan fuskarta. Islam kuwa kara haɗe fuska tayi sosai kamar wacce aka aikowa sakon mutuwa,duk da cewar taji daɗin ganin nasa sosai,dan idanunta cike suke da son kallon kyakykyawar fuskarsa,saidai sosai take jin haushinsa. "Malam Meya kawoka dakina ?ta faɗa cikin ɗaure fuska tana zabga masa harara. Lumshe ido Aslam ya karayi,dan sosai yake jin sa cikin kasala,sannan jin muryarta ya ƙara saukar masa da wata kasalar. "Laifine dan miji yazo dakin matarsa? Ya maida mata amsa. Harara ta ƙara balla masa kafin tace "can dai kaje gurin waccan mai kama da giwar,itace matar ka,ba niba"ta karasa tana murguda dan karamin bakinta dake sheƙi. Ahankali Aslam ya turo harshen sa tare da lasar lips ɗinsa da suka bushe yanzu-yanzu.sannan ya gyara zamansa tare da kara kanƙantar da idanunsa yace"ok kin bar mata Ni kenan ko? Ya faɗa cikin wani salo na jan hankali. Da sauri Islam ta kawar da kanta daga kallon cikin kwayar idanunsa,dan wani irin zuummmm take ji ajikinta idan tana kallon nasa.kafin tace "oho maka kai ka sani,nidai ka tashi ka ficemin daga daki,dan bana buƙatar ganin ka agabana,kaje gurin wacce kake so da ƙaunar, wacce take da muhimmanci agareka,kuma kake shakkar ta baka son ɓacin ranta,dan ina da buƙatar kasancewa Ni kadai "ta faɗa cikin zafin zuciya da ɓacin rai. Wanda kana jin yadda kalaman ke fitowa bakinta kasan cike take da ɓacin rai. Kallonta kawai Aslam keyi,dan duk yadda take motsa bakinta,ji yake kamar ya kama lips dinta ya cinye koya huta da yadda zuciyarsa ke tsananin bukatar shansu. Cikin yanayi na kokarin kwantar mata da hankali yace "Islam me yasa kike faɗin irin wannan maganar agareni ne?ko kin manta Ni mijinki ne?kuma ina da damar da zan zo inda kike akoda yaushe. Tun jiya nake fama da tunaniki, da son zuwa inda kike ,shin ke bakya son ganina ne?"ya fada yana ɗan karkatar da kansa cikin kalar tausayi. Wani haushine ya ƙara kama Islam,wai tun jiya yake son zuwa inda take,lallai Aslam ya Raina mata hankali wllh.afusace ta juyo tana watsa masa wani kallon ka raina min hankali.tace "Ai nasan tun jiya kake son ganina dama,shiyasa ka kasa zuwa inda nake ka aikomin wannan jakar matar taka marar kamun kai,saboda ga mayunwaciyar kaza shine ka bata ta kawomin,kai baka da lokacin zuwa inda nake da kanka,wllh duk ranar da tsautsayi yasanya matarka ta sake zuwa cikin dakin nan,saina sauya mata kamanni,kasani kuma idan nace zanyi to sainayi"tana kaiwa nan ta zauna gaban madubi ta fara shafa manta. Tunda ta fara magana Aslam yake kallonta,tabbas yasan bai kyauta mata ba,domin kamata yayi ya hadasu duka ajiyan yayi musu nasiha,sannan ya rarrashi Islam,amma sam baiyi hakan ba,saidai ba yadda zaiyi,ba laifinsa bane shima.baisan abinda ke damunsa ba,Aduk lokacin da Husna ta shigo gabansa,mantawa yake da komai. Ahankali ya tashi ya nufi inda Islam ke zaune.kan lokar madubin ya hau ya zauna tare da kafeta da lumsassun idanunsa, ita kuwa sosai ta daure fuskar ta tare lakuto mai ta fara shafawa ajikinta cikin nutsuwa. Saida ya dau lokaci yana kallonta kafin ya kamo hannun da take shafa man ya rike cikin nashi. Kallon -kallo suka fara yiwa juna kafin ya fara magana cikin kwantar da murya"am sorry islam !!wllh bani da nufin bata miki ko cutar dake,abinda ya faru jiya ma is an incident ,Amma wllh kinji ma rantse miki dake na kwana cikin raina,Islam duk abinda nakeyi bana mantawa dake,kina cikin zuciyata,saidai i don't now what wrong with me,Ina kasa aiwatar da abubuwan da suka dace Aduk lokacin da Husna ke tare dani,Islam kiyi hakuri dani"ya kai zancen sa yana mai kissing hannun Islam. Hmmmm!!! Wato a takaice dai so yake ya sanar da ita yadda yake tsananin kaunar Husna,shine yake faɗa mata asaye ko?idan yana tare da husna yakan manta da komai dake kansa? Cikin zafin nama Islam ta warce hannunta tare da mikewa tsaye.cikin hucin ɓacin rai take cewa"shikenan,ka koma inda take,kaje kayi ta mantawa da nauyin dake kanka, idan yaso ma ka cinyeta tsabar so,nida baka so kuma ka kasheni,amma daga yau karka ƙara koƙarin faɗamin yadda kake sonta bai shafe ni ba, inka so ma daga yau karka ƙara tunawa da wata Islam,dama nasan ba sona kake ba ai,basai ka fadamin hakan zan tuna ba"Islam ta kai zancenta hawaye na zubowa daga idanunta,tsabar bakin ciki da ɓacin rai. Juya bayanta tayi tana mai ci gaba da kukanta marar sauti,wanda tayi iya kokarinta wajen hanashi zuwa,amma ina !!saida ya kwace mata. Da ƙarfi Aslam ya runtse idanunsa, zuciyar sa zafi take masa sosai,shifa bada wata manufa ya fada mata hakan ba,ya fada matane dan ta fahimci ba laifinsa bane,zuciyarsa ke sashi ya aikata hakan,kuma bada son ranshi ba.amma Islam tayiwa maganarsa wata irin fahimta. Saukowa yayi daga kan madubin ya zagayo gabanta kamar zaiyi kuka yace "Please Islam try to understand me mana,ba abinda nake nufi kenan ba,kuma waye yace miki bana sonki?kefa yar uwata ce,wllh Islam yadda na damu dake azuciyata bazai misaltu ba.dan Allah ki fahimceni"ya fada yana riko hannunta. "Ni ka sanar min hannu,kaje can gurin waccan giwar da kake so ba ruwana da kai nima"Islam ta faɗa cikin kuka da Muryar shagwaba tana ƙoƙarin kwace hannunta. Ganin yadda take ƙoƙarin kwace hannun nata yasanya Aslam janyota ya mannata da ƙirjinsa. Gaba ɗaya atare suka sauke wata ajiyar zuciya mai ƙarfi,yayin da Islam taci gaba da rera kukanta cikin kasa-ƙasa da sauti. Shi kuwa Aslam Yana rungume da ita tsam ajikinsa kamar wani zai kwace masa ita.har cikin ransa yake jin sautin kukanta,yayin da yake jin tamkar ana disa masa dalma idan hawayen nata ya zubo. Husna kuwa tana can kwance akan gado tana jiran miji ya dawo ta kara tara masa gajiya,sai kace wata harija,wai amarya ce ahakan. Shiru -shiru bai dawo ba,da tana ta dariyar lallai Aslam Yana can yana cin uban marar kunyar can,waya sani ma ko dukanta yake?kai gaskiya aikin boka fa yayi, ƙarshe ne,aikuwa zata fadawa mommynta su koma dan ayi maganin waccan Shegiyar marar kunyar. Saidai har ta kira mommynta suka gama maganar su ,amma Aslam bai dawo ba,sai kuma ta shiga wani tunanin,karfa take tana nan shikuma yaje ya kusanci yarinyar can aiki ya lalace?kan uban can,ai da mugun hanzari ta mike har tana neman faduwa,da gudu-gudu ta nufo dakin Islam. Tana zuwa falon ta tarar da Aisha zaune tana wasanta. "Laaaaa anty yanzun nan yaya yace zai kaini gurin ki idan ya fito daga ɗakin anty"A'isha ta faɗa cikin murna tana nufar Husna. Husna kuwa cikin jin haushi da tsanar yarinyar ta tunkudeta can gefe tana mai cewa"shegiya gayyar tsiya karki taɓani dan ubanki,niba antyn ki bace,ina Aslam din yake?"ta faɗa cikin tsawa tana zarewa A'isha ido.tare da ɗora mata kafa a cikinta. Tsoron Husna ne ya kama Aisha sosai ta sanya kuka mai sauti tana faɗin"wayyo anty kizo kigani tana zaremin ido,zata dakeni cikina anty"yarinyar ta faɗa jikinta sai rawa yake tana kwance aƙasan kafar husna. Da sauri su Islam suka rabu da jikin juna ,jin ƙarar da A'isha keyi,alamun naiman taimako. Har rige-rige suke wajen fitowa dan ganin abinda ya sami yarinyar. Zaro ido sosai Islam tayi lokacin da idanunta suka sauka akan ƙafar Husna dake kan cikin A'isha..... Hmmmmm,masu karatu muje zuwa. Na gode sosai da addu'oin alkairi da samun sauki da kuke tayi min,wanda suka kirani da wanda sukayi min online,da wanda sukayi azuciyarsu. Allah ya bar zumunci,ya kuma kara mana lafiya. Duk masu juna biyu Allah ya saukesu lafiya. Anty mammy ce Mrs babi. [11/20/2022, 11:20 AM] Abk: 81/82 ___________Zaro ido sosai Islam tayi,lokacin da idanunta suka sauka kan ƙafar Husna dake kan ruwan cikin A'isha. Wani irin numfashi Islam take saukewa mai tsananin zafi da suka,gaba ɗaya jikinta ya kama rawa nan da nan idanunta suka kada sukayi jaaa tamkar wacce aka watsawa barkono acikinsu. A'isha kuwa tana ganin Islam ta kara sautin kukanta tana mika mata hannu "wayyo antyna kizo ki daukeni zata dakeni ƙafarta nauyi zata fasamin ciki"abinda yarinyar ta faɗa kenan cikin kuka tana riƙe da ƙafar Husna. Aslam cike da mamakin rashin hankalin Husna yake kallonta,yadda ta riƙe ƙugu tana girgiza ko ajikinta kamar ba dan mutum ta ɗorawa ƙafa ba. Cikin dakiya yace "Husna meye hakan kikeyi,?yarinya ce fa karama ,kike taka mata ciki baki tunanin wani abu ya sameta?" Aslam ya fada yana mai kallon husnan.kafin Husna tayi wani yunƙuri kawai sukaji Islam ta kwalla wani kara cikin mugun ɓacin rai ta nufi Husna gadan gadan.ba wata-wata tana zuwa ta sanya hannunta tare da angije Husna da mugun ƙarfi,ji kake rigijib,Husna ta fadi kasa, ƙafarta ta bugu da jikin ƙofar dakin. Kukun kura Islam tayi tare da afkawa Husna. Dukan ta take ta ko ina tana zabga mata lafiyayyun maruka da naushi kamar wata yar caskale. Gaba ɗaya tunaninta ya gushe,ba abinda idanunta ke haskowa sai kafar Husna akan ruwan cikin A'isha. Ƙafar ta Husna islam ta cafko ta baya tare da lankwasawa da mugun ƙarfi. Ihu Husna ta kwalla cike da azaba tana kiran "wayyo Allah Aslam kazo ka taimakeni,zata kasheni,wayyo kafata wayyo bakina na shiga uku,wllh ba mutum bace wannan zata kasheni wayyo mommyna"abinda Giwa Husna ke faɗa kenan tana kokarin ture Islam daga kanta, amma inaaa!! Islam ta zage sai gibgarta take kamar ta sami jaka. Banda naushin bakin Husna da bata lafiyayyun maruka ba abinda Islam keyi. Ganin da Aslam yayi ana shirin yin kisan kai ya sanya shi zaunar da A'isha akan kujera,wacce ya dagata lokacin da Islam ta angije Husna tare da rungumeta yana rarrashi. Da sauri ya nufi Islam wacce ta shaƙewa Husna wuya tana dukan bakinta. Husna sai kakari take tana shura kafa,dan ko kare kanta ta kasayi, domin ba karamin duka take sha agurin Islam ba. Da sauri Aslam ya ɗago Islam daga kan Husna yana mai faɗin"Islam barta haka mana zaki kasheta fa " Tureshi Islam keyi tana ƙoƙarin komawa kan husna,wacce tayi ragwab akwance tana tari,dan tama kasa mikewa bare ta gudu. "Ka kyaleni,wllh yau saina ci uwar azzalumar matar nan,haka kawai take ƙoƙarin kashemin Aisha,me tayi mata?wllh saina illata ta"Islam ta faɗa tana kaiwa Husna kafa. Da sauri Aslam ya janye ta yayi ɗakinta da ita.yana zuwa ya turata ciki tare da kulle ƙofar ,dan yaga da gaske Islam kamar zararriya haka ta koma,kuma idan ya barta ba karamin illata Husna zatayi ba. A'isha na zaune jikin ta sai rawa yake tana kuka,Aslam yazo ya mika mata makullin dakin Husna yace"sorry eeshan mommy,daina kuka kinji?bari na kai anty asibiti na dawo,idan kinga mun fita saiki budewa anty kofa "Aslam ya fada cikin yanayi na rarrashi tare da tausayin yarinyar. Karba A'isha tayi tare da cewa"yaya Ni gurin mommyna zani,ka kaini gurin mommy"ta faɗa atsorace tana kallon inda Husna ke kwance. Kafin yayi magana suka jiyo Islam tana buga kofar kamar zata karya tana faɗin"ka budemin kofar nan kona ballata,wllh bazan yarda ba idan wani abu ya sami ƙanwata, A'isha zoki budemin kofar nan kinji"Islam ta faɗa cikin daga murya tana buga ƙofar. Tsoro sosai ya kama A'isha sai rawar jiki take tana kuka tare da kallon Aslam. "Karki budeta yanzu kinji eeshan mommy?ki Bari saina fitar da anty saiki bude kofar. "Yaya tsoro nake ji,dan Allah ka kaini gurin mommy"yarinyar ta faɗa cikin kuka. "To kiyi shiru bari naje na dawo "ya fada yana mai ɗago Husna dake kwance sharab tana kuka ta kasa tashi. "Wllh bazan yarda ba saina ɗauki mataki akan wannan yarinyar,kana kallo tayi min dukan Kawo wuka kamar ta sami jaka,wllh saina fadawa daddy na ya dauki mataki,wannan ba ita kadai ke wannan dukan ba ,harda aljanu "Husna ta fada lokacin da Aslam ya taimaka mata ta mike tsaye. Saidai fa tana mikewar ta kwalla ƙara tana faɗin"wayyo kafata na shiga uku ta karya min ƙafa "ta faɗa data neman zubewa a ƙasa. Da kyar dai Aslam ya fitar da ita daga dakin zuwa nata dakin,dan ya fahimci fa Islam tayi mata targade ne akafar. Hanan ce tazo kawo musu abinci ta tarar da wannan hatsaniya,inda bayan ta ajiye kulolin abincin sai ta shiga ɗakin Islam,nan ta tarar da A'isha tana ta kici-kicin bude Islam tana kuka. Da sauri ta karasa gareta tana tambayar ta meke faruwa? Nan Aishan tace" anty hanan ki buɗe anty,Ni bazan iya ba"ta faɗa tana mika mata makullin dakin. Karba hanan tayi tare da buɗe kofar. Tana budewa Islam dake bakin kofa ta fito. Da hanzari ta janyo A'isha wacce ta ƙara tsorata ganin fitowar Islam,atunanin ta zata daketa ne tunda taki budeta"anty dan Allah kiyi hakuri yaya ne yace karba buɗe sai sun fita,dan Allah karki dakeni"A'isha ta faɗa gwanin tausayi,jikinta sai rawa yake. Rungume yarinyar Islam tayi tsam ajikinta tana jin wani hawaye mai zafi na tausayin yarinyar yana zubo mata.cikin kwantar da murya tace "kiyi shiru Aishana,ba dukan ki zanyi ba kinji?ki daina kuka ƙanwata"Islam ta faɗa tana zama tare da kara rungume A'isha. Zama hanan tayi kusa da Islam tace "yar uwa meke faruwa ne ?"ta faɗa tana dafa kafadar Islam. Ajiyar zuciya Islam tayi tare da labartawa hanan komai. Sosai hanan tayi mamakin haukar Husna,yanzu wannan yar yarinyar zata takawa ruwan ciki? Sosai tayi ta rarrashin Islam saida taga hankalinta ya ɗan kwanta sannan ta bar part din. Tana zuwa kuwa ta sanar dasu mommy abinda ke faruwa abangaren su Islam. Aikuwa cike da ɓacin rai granny ta fara ɓaɓatu da masifa. "Wllh bazan yarda da wannan zalunci ba,ashe haka yarinyar nan take?har nawa Aishan take dazata taka mata ciki?wato so take ta kashe ta ko? Wllh bazan amince ba zuwa zanyi inji dalilin dukan , wando ma zan saka koda zata kaimu da dambatuwa da yarinya ehe " granny ta faɗa tana nufar kofar fita daga falon.mommy da hanan suka rufa mata baya. Mommy na fadin "kiyi hakuri granny abi komai ahankali"dan Ita dai mommy bataso suje bangaren nasu yanzu da safen nan ,amma tana gudun abin da zai biyo baya.dan haka dole tabi bayan grannyn. "Saboda ba yarki aka yiwa dukan Kawo wuka ba ko?muguwar mata,dama na jima da fahimtar ki ai sam ke baki da imani to wllh ki kiyayeni,dan kema ba tsoronki nake ji ba"granny ta faɗa cikin masifa tana hararar mommy. "Allah ya huci zuciyarki granny"shine kawai abinda mommyn ta faɗa tana bin grannyn da tayi gaba abinta. "Da haƙurin ta mutu sadakar nawa kika bayar abiyaki?muguwa "granny ta fada tana tura ƙofar falon nasu Aslam. Aslam kuwa yana zaune riƙe da hannun Husna dake kwance akan gado,fir taki yarda suje asibiti dan tace ta yaya daga kawota gidan aure jiya-jiya kuma yau a ganta asibiti da raunuka? Ita wllh ba inda zata je. Shikuma yana rarrashinta akan suje kodan ciwon dake jikinta ga ƙafa nan har ta aune. Ita kuwa sai wani kuka take tana juya kai cikin kuka. Kai tsaye granny ta shigo babban falon tana kiran "ina kuke?gaba ɗaya ku fito naji dalilin dukan da akayiwa A'isha? Granny ta faɗa cikin daga murya. Islam ce ta fito riƙe da hannun Aisha wacce ta sha kuka sai ajiyar zuciya take,dan ta tsorata sosai. Da sauri granny ta riko hannun yarinyar tana duba jikinta cike da tausayi tana faɗin"Allah sarki yar malaikar Allah,yanzu idan ba rashin imani na wannan yarinyar ba ,meye abin duka ajikin wannan yarinyar?harda su taka ruwan ciki? Salon taje ta fasa mata kindini.(wai tana nufin kidney) saida hanan tayi murmushi ita da mommy. "Ke kuma Islam kika tsaya kina kallonta zata kashe miki ƙanwa dan asara baki tattaka mata ruwan cikin ba ita"granny ta faɗa tana hararar Islam. Shiru Islam tayi dan zuciyarta zafi take mata sosai ,ganin Aishan taci gaba da kuka. Aslam ne ya fito da sauri, yana tunanin ya akayi granny tasami labarin abinda ya faru?cikin yanayi na nuna ba abinda ke faruwa yace "granny, keda wa kike ta ɓaɓatu da safen nan?mommy meke faruwa naganku gaba ɗaya?ya fada yana kallon mommy. "Kaji ja'irin yaro ko?wai tambaya ma yake meke faruwa irin baka san abinda waccan matar taka ta aikata ba ko? Granny ta fada tana buga masa harara. "To granny me akayi?dan Allah karki zo ki tada min hankalin gida da sassafen nan,mu ba abinda ke damun mu"ya fada cikin haɗe fuska. Aikuwa nan granny ta hau fada kamar zata aro baki,mommy dai sai hakuri take bata. Har cikin dakin Husna ta shiga tayi mata kashedin dukan A'isha nan gaba, abinda ya sanyaya mata zuciya ma ganin husnan da tayi kwance alamun dai Islam ta dauki mataki kenan. Husna kuwa sai wani yatsina take tana hararar granny da juya ido. Haka granny ta fito tana ta masifa ta fice da A'isha ahannunta. Mommy ce tayi musu nasiha sosai akan zaman lafiya,fir Husna taki fadin cewa Islam ce tayi mata duka harda su targade,tace faduwa tayi atoilet. Gani take wannan ai abin kunya ne ace wannan yar yarinyar ce tayi mata dukan tsiya,amma wllh bata daki banza ba,zata rama . Wannan ma shigar sauri tayi mata bata shirya ba shiyasa. Bata san cewa su mommy sun fita sanin wacece Islam ba ,dan kuwa sun san aikin tane wannan. Sosai hanan tayi dariya tana mamakin asaranci irin na Husna ,wai Islam ce tayi mata wannan dukan haka. Haka dai Aslam ya samo mace mai gyara ta gyarawa Husna kafar ta,ƙatuwar banza haka tayi ta ihu gaban mommy,lokacin da ake gyara mata targaden. Yau kimanin wata guda kenan da daura auren Husna da Aslam,abubuwa sun faru da dama wasu masu dadi wasu akasin hakan,cikin marasa dadin kuwa harda kasa kusantar Islam da Aslam yakeyi,Dan yanzu duk yadda ya kai da son kusantar ta to Sam asalamiyyar sa bata tashi,saita kwanta luf,abin yana matukar damunsa,tunda ba haka ke faruwa dashi ba idan yana dakin Husna,kalau yake mu'amalantar ta. Amma idan Islam ce,saidai yayi iyakar yinsa,amma bazai iya komai ba. Tun abin baya damun Islam harya fara damunta sosai,gani take kamar da gangan yake jagwalgwala mata jiki ya barta. Kullum gani take rainin hankalin Aslam Kara yawa yake,dan ko ranar kwananta saidai ya saci jiki cikin dare ya shigo dakin nata,kuma ba biyan bukata. Haka Husna zata fito falo tayi ta falli idan taga Islam,tayi ta mika tana jikinta ciwo jiya Aslam ya wahalar da ita. Shikuwa yayi ta basarwa Dan baya son Islam ta ji ba dadi. Ahankali munanan halayen Husna suka bayyana gaba ɗaya ga yan gidan,har dashi kansa uban gayyar,wato Aslam. Sam bata iya komai ba,hatta dakin ta saidai shi ya gyara mata,kaya kuwa inda ta cire nan take jefarwa,ga rashin kunya,ko kaɗan bata girmama mommy da granny,sai taga dama take zuwa ma su gaisa,shima atsatstsaye. Gaba ɗaya ta fice daga zuciyar ahalin gidan,ba wanda ke son ta ahalin yanzu sai Aslam. Wanda shima son na dole ne,sosai yake jin tsanar ta cikin ƙasa zuciyarsa,amma baya iya nuna mata koda akan fuskar sane. Islam sun kammala makarantar su ta secondary cikin nasara,inda tafi ko wane dalibi kaykykyawan sakamako,gaba ɗaya A ta samu.saidai muce Allah ya bada sa'ar zuwa wata makarantar. Yau ta kasance ranar juma'a, Islam na zaune afalonta yayin da janbu ke tsalle-tsallen sa akan kujera.gaba ɗaya damuwa ta hanata sakat,kullum tunanin halin da suke ciki ita da Aslam take,ta kasa gane menene abinda ke damunsu, to kodai basu da lafiya ne?kai amma idan da hakane ai itama Husna bazai iya kusantar ta ba,amma ba wata alama ta baya kusantar husnan"kodai nice bani da lafiya?" Islam ta faɗa afili cikin damuwa. Ahankali Aslam Wanda tun ɗazu ya buɗe kofar Tata ya tsura mata ido amma bata san da zuwan shiba ma,tsabar nisan da tayi cikin tunani. Shigowa yayi cikin dakin ya zauna kusa da ita. Juyowa tayi da ɗan sauri ta kalleshi,dan bata ji zuwansa ba kwata -kwata. Kallon juna sukayi na dan lokaci kafin Islam ta kawar da kanta gefe guda tare da turo baki tace"ya hakane wai? Saikayi ta zuwa kana min labe kayi ta tsoratani "ta faɗa tana ɗan murguda baki. Murmushi yayi tare da rungumeta ta gefe yace "Matsoraciya kawai,da kin ɗauka Husna ce tazo zaneki kome?ya fada cike da tsokana yana ɗan murmushi. Da sauri Islam ta ɗago daga jikinsa tana mai buga masa wani kallo tace "ai wllh kasani Ni nafi ƙarfin in tsaya jin tsoron waccan bijimar taka,kaidai da kake tsoronta kayi ta fama amma nikam bata isa ba"Islam ta faɗa cikin hasala tana matsawa daga kusa dashi. Murmushi Aslam Yayi Yana jinjina karfin hali irin na Islam da jarumta,dan Husna tayi kusan ukunta ajiki,amma sam bata tsoron husnan.sai dai ma ita husnan daya ga kamar tana ɗan shayin Islam ɗin tun lokacin data targada mata kafa.kuma yayi mamakin. Da husnan bata sanar agidan su ba. Kallon Islam ɗin yayi yadda take wani huci kamar zakanya. Cikin sanyin murya yace "Islam tunanin me kikeyi ne ?na shigo tun ɗazu amma baki sani ba,sannan naji kina tambayar ko kece baki da lafiya?meke damunki?Aslam ya fada da son kawar mata da ɓacin ran Husna . Shiru Islam tayi tare da tunanin ta yaya zata sanar dashi abinda ke damunta?ai sai yayi tunanin kamar so take ya kusanceta ma,ita kuma sam ba hakan bane babbar damuwarta, tana tsoron ko wata matsalar ce a tare dasu. Matsowa Aslam yayi tare da kamo hannayen ta ya sumbata kafin yace "Islam ki sanar dani damuwarki Please,dan baki da wanda zaki fadawa damuwarki ahalin yanzu sama dani"ya fada cikin sanyi murya yana ɗan matsa hannunta. Ajiyar zuciya Islam tayi kafin tace " ina tunanin makomar zaman mune, kaga kamar acikin nida kai fa akwai mai matsala,kawai mai zai hana ka sawwakemin tunda dama ba da son ranmu akayi auren ba"Islam ta faɗa gabanta na bugawa,yanzu idan Aslam yace ya amince kuma ya zatayi kenan? Ido kawai Aslam ya zubawa Islam, yana jin ba dadi cikin ransa,wato ta gaji da zama dashi ba tare da yana biya mata bukata ba kenan? Yanzu ta yaya take tsammanin zai iya rabuwa da ita? "Yanzu Islam har kin gaji da zama dani?kin gaji da yadda na kasa sauke miki hakkin ki dake kaina? Islam yanzu zaki iya rabuwa dani ashe?kenan bakyajin abinda nake ji game dake cikin raina ?Aslam ya faɗa cikin yanayi na damuwa sosai yana kallon Islam wacce tayi dana sanin furta waɗan nan kalaman. Ahankali ya sauke ajiyar zuciya tare da mikewa jiki ba kwari yace "shikenan Islam,kiyi hakuri ki bani lokaci,zanyi miki abinda kike so,domin bani da burin shiga hakkin ki ko kaɗan,amma ki sani inayin iyakar ƙoƙarin wajen sauke miki hakkin ki,saidai bansan meke damuna ba, Aduk lokacin da nayi ƙoƙarin kusantar ki,nakan rasa dukkan kuzarina ta yadda duk yadda naso da yin sex dake saidai na hakura,amma hakan na azabtar dani,yana matukar damun zuciyata,kiyi hakuri ki bani kwana biyu "ya fadi hakan cikin raunatacciyar murya tare da barin dakin. Zaro ido sosai Islam tayi tana mai dafe ƙirji"na shiga ukuna !kenan sakina zaiyi? Nifa bada gaske na fadi hakan ba, innalillahi"Islam ta faɗa tare da mikewa tsaye,harta nufi ƙofa, sai kuma ta tsaya tare da sanya kuka.. Muje zuwa Anty mammy ce. [11/21/2022, 11:13 AM] Abk: 83/84 ______________"Innalillahi"Islam ta furta cikin rawar murya tana mai ƙara dafe ƙirjinta tare da mikewa tsaye. Hanyar kofa ta nufa cikin sauri,harta kama handle ɗin kofar sai kuma ta saki tare da sanya kuka. Durƙushewa tayi agurin tana rera kukanta. "Ni fa bance ka sakeni ba,kai baka san maganar da bata gaskiya ba?daga nace mu rabu shine zaka ce wai zakayi tunani nan da kwana biyu,wllh bazan yarda ba idan ka sakeni"Islam ta faɗa cikin kuka tana jifa da fillows ɗin kan kujera. Wani ƙayataccen murmushi Aslam ya saki, Wanda tun fitarsa yake tsaye jikin ƙofar Tata cikin damuwa,amma jin abinda take fadi ya sashi sakin murmushi mai cike da tsantsar farin ciki da nishaɗi. Hakan yana nufin Islam ma tana kaunarsa kenan?bata son rabuwa dashi?kenan duk cika bakine irin nata? "wayyo Allah daɗi, Alhamdullah " Aslam ya fada tare da lumshe idanunsa cikin farin ciki. "Honey meye hakan? Me kake yi anan gurin kuma?Aslam ya tsinkayo Muryar Husna nayi masa magana. Da sauri ya buɗe idanunsa ya sauke su akanta,tana sanye da rigar barcin data kwanta da ita tun jiya,ko wanka batayi ba bare ta cire ta. Sosai yaji wani ɓacin rai can cikin ransa,haka kawai yake jin tsana da haushin Husna,wanda kuma sam baya iya nuna mata hakan azahiri,ya rasa gane me hakan ke nufi. Murmushi yayi tare da nufarta yana mai faɗin"dama ke nake jira ki fito dan muje lambu,kuma naga baki shirya bama"ya fada yana kama hannunta ya sumbata. Kallonsa tayi cike da rashin yarda na dan lokaci kafin tace "shine kuma kazo ƙofar ɗakinta ka wani tsaya kana murmushi ?ta faɗa cike da tuhuma. Murmushi yayi cikin basarwa yace "baby muje inyi miki wankan Please muje musha iska" ya fada yana kama hannunta suka nufi ɗakinta. Islam kuwa tana cikin wannan kukan taji wata irin Iska mai sanyi na kadawa cikin dakin nata,wanda har saida ta ɗan ƙankame jikinta. Ahankali dakin yayi haske sosai, lumshe ido Islam tayi,tana mai share hawayen dake zuba daga idanunta. Kafin ahankali ta buɗe idon tana. Lokacin ne kuma hasken ya fara gushewa ahankali fuskar malaminta ta fara bayyana, har ya gama bayyana gaba dayansa. Yana sanye da wasu irin kaya masu kamar na sarauta,kansa nannaɗe da farin rawani,sai wata sanda dake hannunsa,dayan hannun nasa kuma na dama casbaha ce mai matukar kyau,sai walwali take kamar zinare. Fuskarsa ɗauke da shahararren murmushi mai kyau yake kallon Islam. Da hanzari Islam ta mike tsaye tare da zaro ido cikin murna ta nufi inda yake tsaye .tana zuwa ta tsaya kusa dashi tare da sanya kuka . Murmushi yayi tare da cewa"Assalamu Alaiki ya Islam,ki daina kuka lokacin kuka ya kare gareki,ki sani komai yayi farko,zaiyi karshe. Sannan ko wane dan adam yana da kalar tashi jarrabawar,karki damu nasan komai dake damun ki keda mijinki,kuma da yardar Allah komai ya kare,Islam zauna ki share hawayenki"ya fada cikin nitsatstsiyar murya mai cike da kamala. Zama Islam tayi tare da tankwashe kafafunta a ƙasa tana mai kallon malamin nata cikin murmushi. Wata kujera ce mai kama data zinare ta bayyana inda malamin Islam ya zauna akanta. Cikin yanayi na farin ciki Islam ta buɗe baki tace "nayi kewarka malamina,na shiga damuwa da kunci kala -kala,naso ace kana nan dan ka bani shawara,malamina ina cikin matsala Aslam,ya Kara aure kuma yanzu sakina ma zaiyi"Islam ta fadi hakan cikin shashsheƙar kuka tana murtsuka ido. Murmushi malamin Islam yayi cike da nutsuwa da kamala yake kallon Islam tana magana har ta kammala. "Islam" ya kira sunanta cikin nutsuwa da Muryar rarrashi. Dagowa tayi tare da kallonsa cikin damuwa.cigaba yayi da maganarsa--" ki kwantar da hankalin ki,mijinki bazai taba rabuwa dake ba,domin yana matukar so da ƙaunar ki.. Da sauri Islam ɗago kanta daga sunkuyen da yake bakinta abude cikin tsantsar farin ciki tace "da gaske malamina ?da gaske yana sona ?kuma bazai sakeni ba?ta faɗa cike da ɗoki tana murmushi mai dauke da hawaye. Jinjina mata kai malamin nata yayi yana mai cewa"hakika mijinki na sonki fiye da tunanin ki,sannan bazai taɓa rabuwa dake ba,matsalar dake tsakanin ku kuma,sihiri ne,akayi muku don ana son rabaku,Amma in Sha Allahu zan baki maganin da zai karya wanann sihirin dake jikin Aslam,Wanda anyi shine dan kawai acireki daga zuciyar Aslam,saidai hakan bazai taba yiwuwa ba,makarin wannan sihirin kuwa shine duk lokacin da wata akala ta aure ta shiga tsakaninku da Asalm. Shine dalilin da yasa aka hana Aslam mu'amalantar ki.amma daga yau komai yazo ƙarshe In Sha allah"malamin Islam ya kai ƙarshen dogon jawabinsa yana mai ciro wata kwalba cikin aljihun rigarsa mai kama da alkyabba . Mikawa Islam kwalbar yayi wacce ke dauke da wani farin Ruwa mai ɗan kauri a cikinta. Hannu Islam ta sanya ta karba cikeda mamakin wai ashe asiri akayi musu ita da Aslam?Dan kawai Araba tsakanin su,lallai kuwa ya tabbata ba kowa ne yayi wannan aikin ba face Husna. Cikin karayar zuciya da jin matukar tausayinsu yana ratsa jikinta tace "malam asiri kuma?waye yayi mana ? Ta faɗa tana riƙe da kwalbar hannunta. Murmushi malam yayi kafin. Yace "abokiyar zamanki itace tayi wa Aslam asiri,dan ke asiri bazai taba cin kiba, kuma auren ta dashima ba yin kansa bane,an hada shine ta hanyar asiri,aka cusa masa sonta dan haka yake abubuwa kamar yana tsoronta, kiyi amfani da wannan turaren dana baki,ki zubawa Aslam cikin ruwan wankan sa,sannan ki saka masa cikin man shafawarsa,sannan duk inda kika san yana zama ko yana zuwa cikin gidan nan,to ki zuba wannan turaren agurin, Yau kishiyarki zatayi bakuwa ,kuma zata kawo mata maganin da zata kara nesan taki da Aslam, Da zarar bakuwar ta tafi Husna zata rakata kekuma kishiga dakin Husna ki duba kasan gadon ta zaki ga wasu layoyi kiyi bismilla sanann ki yayyafa turaren nan akansu ki dauko su.sannan kije dakin Aslam,ki daga kasan katifarsa duk abinda kika gani ki dauko bayan kinyi bismilla kin yayyafa wannan turaren akansu,ki hada da wannan layoyin zanzo in karba . Islam ki kula sosai,ki zamo mai yawan addu'a da tsayuwar dare,sannan daga yau zamu fara karatu domin kina da kurakurai sosai akan harkar addini,dama na barine har zuwa wannan lokacin da zaki hadu da iyayen ki,kafin In kammala komai daya kamata inyi miki.sannan kiyi ƙoƙarin wajen kula da rayuwar Aslam,harya rabu da wannan matar dan kuwa annobace ita agareku" Shiru kawai Islam tayi tana sauraron malaminta cikeda mamaki da jinjina rashin imani irin na wasu mutanen,lallai tasan dama ba haka aka bar Aslam ba,Dan rawar kansa akan Husna tayi yawa,In sha Allahu kuwa zatayi duk abinda malam ya ce tayi ba kuskure. "Kije yanzu ki fara aikin dana saki,kafin Aslam ya shiga wanka kije ɗakinsa ki hada masa ruwan wanka ki zuba wannan turaren,sannan ki zuba Aduk inda nace miki,Ni zan tafi ana can ana kirana,zan dawo zuwa goben in karbi abubuwan dana ce ki dauko"malamin Islam ya fada yana mai mikewa tare da ambaton sunan Allah,nan take kujerar ta bace shima ya zama farin haske tare da bacewa. Ajiyar zuciya Islam tayi mai ƙarfi tana mai ƙara cika da mamakin abubuwan da taji yau,aikuwa zatayi duk mai yiwuwa wajen sanya Aslam ya kusanceta,kodan wannan sihirin dake jikinsa ya karye. Kai tsaye ta nufi dakin Aslam,kamar yadda malam ya umarce ta haka ta aiwatar,ta zuba turaren nan cikin duk wani abu da Aslam ke amfani dashi. Gadon ne kawai bata daga ta dauko abun dake ciki ba,tunda malam yace sai gobe. Fitowa tayi daga dakin bayan ta hada masa ruwan wanka.dakin ta ta koma ta zauna bakin gado tayi shiru,tana tunanin ya kamata fa ta fara nunawa Husna itama ba kanwar kasa bace,dole tayi maganinta. Dan haka cikin azama ta tashi ta shiga toilet ta sake wanka ta fito,cikin hanzari ta shafa mai tayi yar kwalliya mai sauki,sannan ta feshe jikinta da turaruka masu ƙamshin gaske da shiga jiki,ma'ajiyar kayanta ta buɗe tare da ƙurawa uban tulin kananan kayanta ido,wanda bata amfani dasu tun zuwa ta gidan,amma yanzu lokacin amfani dasu yazo,dan haka wata jar riga mai roba ta zaro,wacce bata wuce gwuiwarta ba,saman rigar irin open neck ɗin nan ce hannu daya gareta sannan daga bayanta,awaware yake har zuwa wajen mazaunan ta. Sanya rigar tayi ajikinta ba tare da ta sanya bra ba,aikuwa kasancewar rigar robace daf-ta kama ajikinta ko ina ya fito tsaf-tsaf,hatta shatin nipples dinta kana iya hangowa ta jikin rigar. Tsayawa tayi jikin madubi tana karewa kanta kallo,masha Allah ita kanta tasan ta hadu,hips dinta yayi mugun fitowa ɗas cikin rigar. Murmushi tayi tare da kama gashin kanta ta daure da jan ribom. Wato ba kowa bane idan ya kalli Islam a wannan lokacin zaiyi tsammanin tana jin hausama bare kuma ace bahaushiyar ce, murmushi tayiwa kanta akaro na biyu,sannan ta kara feshe jikinta da turare kafin ta sanya flate shoe tayi waje. Cikin takunta mai matukar girgiza zuciyar yan maza,da sanya su cikin shauƙi take tafiya kamar wata tarwada ko ina na jikinta motsawa yake,ga wani sihirtaccen ƙamshi dake tashi ajikinta. Kai tsaye dakin Aslam ta nufa,da siririyar muryarta tayi sallama tare da murda handle ɗin ƙofar ta shiga. Baya falo dan haka ta wuce can cikin dakin nashi. Aslam kuwa bayan ya lallaba Husna akan tayi wanka suje su huta alambu, shine shima ya dawo cikin ɗakinsa dan ya watsa ruwa,dan kuwa saida Husna ta tara masa gajiyarta ta kullum kafin ya fito daga dakin yana ta mitar jarabar Husna tayi yawa. Kai tsaye ya shiga toilet inda ya tarar da ruwan wanka ahade yana ta zuba uban ƙamshi,nan da nan yaji zuciyarsa na son yayi wanka da ruwan,dan haka ya zage ya shiga cikin bahon wanka yayi wankansa, inda yake jin wani irin yanayi yana shiga jikinsa,zuciyarsa tana nutsuwa daga kuncin da take ciki tunda ya auri Husna.sannan yana jin kamar zai iya gaba da gaba da Husna ,zai iya sanar da ita duk abinda ke zuciyarsa ba tare da tsoro ba. Bayan ya fito ne ya zauna yana shafa mai ajikin sa,ba abinda yake so da burin sake gani kamar islam. Shi kadai sai murmushi yake yana shafa mai. Yana cikin wannan halin ne kuma ya tsinkayo muryarta tana sallama. Da sauri ya waiga yana kallon ƙofa dan gasgata cewar ita ɗin ce kuwa ?dan shikam ya manta rabon Islam da shigowa ɗakinsa . Cike da mamaki da tsantsar farin ciki yake bin jikin Islam da kallo,wacce tayi tsaye jikin ƙofar dakin nashi cikin wani salo tana kallonsa. Gaba ɗaya Aslam ya nemi nutsuwarsa ya rasa,wani irin kyau yaga Islam tayi masa na ban mamaki,shi dama irin wannan shigar tana matuƙar burgeshi ga mace,bare matarsa mai ƙira irin Islam. Idanunsa ya saukar akan kyakykyawar fuskar Islam,yana mai jin wani irin daɗi na ratsashiYama kasa ƙarasawa inda take,tunda Ita bata shigo ciki ba. Islam kuwa cikin salon shagwaba da jan hankali tace "ko ina koma ne naga kamar ba kayi maraba da zuwana ba"Islam ta faɗa tana ɗan yin kamar zata fice daga ɗakin. Ai wata sufa da Aslam yayi,sai ganinsa tayi agabanta ya riko hannunta,cikin wata shaƙaƙƙiyar murya wacce tsabar sha'awar Islam ta sauya masa muryarsa yanzu,yace "haba pretty idan kika tafi kuma ai ni mutuwa zanyi awannan yanayin da nake ciki,shigarki da kyan da kikayi,sune suka daskarar dani,suka hanani koda ƙwaƙwƙwaran motsi,pretty me yasa tun farko bakiyimin irin wannan shigar?Aslam ya fada yana janyo Islam zuwa jikinsa,gama ya matseta cikin jikinsa yana sauke wata ajiyar zuciya mai ƙarfi. Dadine sosai ya kama Islam,ganin cewar lallai zata kama Aslam sosai ta wannan bangaren ,cikin salon shagwabar ta tace"ai kaine baka ce kana so ba,yanzuma ai Ni naga damar sawa dan kaina, kuma zuwa zanyi in cire"Islam ta faɗa cikin lumshe ido,dan yadda take jin hannun Aslam na yawo a sassan jikinta ya fara sauya mata mood, "Noo!! Islam ɗina karki cire min kayan nan Please,kullum kiyi ta sanya irinsu ina matukar son irin shigar nan ga mace "Aslam ya fada yana mai ɗago kan Islam tare da haɗe bakinsu guri daya. Ba wani musu Islam ma ta tsafke bakin nashi,suka fara aikawa juna zafafan kisses masu shiga rai. Husna kuwa tana fitowa daga wanka ta jefar da towel din jikinta,turare ta fesa ajikinta sannan ta janyo wata doguwar riga yar kanti matsatstsiya ta sanya. Gaba daya Husna bata da wani fasali mai kyau,hakan saiya sanya rigar tayi mata wani iri ajiki, ta sama tayi wani hankarara da ita,yayin da ta kasan ta wajen hips da mazaunan ta suka wani motse suka takure tare da curewa guri ɗaya. Ataikace dai husna kirar zaki gareta ,bata da fasali irin na mata ko kaɗan,sai uban nonuwa kamar kayan wanki. Haka ta fito rigija -rigija tayi dakin Aslam, tana zuwa bako sallama ta tura ƙofar ta shiga,ganin baya falon yasata wucewa cikin uwar dakan tana faɗin "honey na shirya Please fito muje wllh iskar lambu nake bukatar shaka, kasan..... Maganar ta ce makale lokaci guda kuma numfashinta ya tsaya na wucin gadi. Wani uban ihu Husna ta kwalla tana riƙe kanta,abinda idanunta suka gane mata yau yafi karfin masifa agurinta,wani irin romancing juna Islam da Aslam keyi,wanda kana gani kasan cewa azaƙe suke da juna,kuma idan abin yayi nisa komai na iya faruwa. Da sauri suka saki juna tare da juyowa dan jin ihun Husna da sukayi akansu,da sauri Islam ta ja rigarta tare da rufe ƙirjinta ,dan tuni Aslam ya sauke tilon hannun rigar yana wasa da albarkatun ƙirjin Islam. Cikin karaji da bala'i Husna ta fara magana"Honey meye hakan kake yi da wannan yarinyar?cin amanar kake dama abayan idona?na shiga uku koma dai ka taba kusantar ta ne ban sani ba ?wllh bazan yarda ba,ashe kai azzalumi ne maci amana ban sani ba?ke kuma yau zakici kan ubanki,wllh zaki san cewa ke karamar karuwa ce shegiya mayya"Husna ta fada tana yiwa kan Islam kamar zararriya. Aikuwa cikin abinda bai gaza sakwan daya ba,Islam ta riga Husna ƙarasowa gareta,bata jira komai ba da dauke Husna da wani gigitaccen maruka har biyu masu matuƙar zafi da radaɗi..[11/22/2022, 12:24 PM] Abk: 85/86 ___________Wasu gigitattun maruka Islam ta ɗauke Husna dasu masu matuƙar zafi da shiga jiki. Wanda yayi silar daukewar wutar Husna na wasu tsayin daƙiƙai,banda juyawa ba abinda kanta keyi. Cikin tsantsar fushi Islam ta fara magana. "Ke wacce irin dabbar mata ce?wacce irin kidahuma ce ke wacce batasan inda ke mata ciwo ba?ko kinyi tunanin ke kadaice matar gidan?dazaki fado mana daki ba sallama tsabar jahilci,sannan kuma ki tuhumemu akan muna cin amanar ki?shin baki san nima ina da hakki akan mijina ba?ko an faɗa miki dan kinga nayi shiru bansan kaina bane?to wllh kinyi na farko kuma kinyina ƙarshe,duk lokacin da kika ƙara min irin wanann iskancin wllh saina karya miki ƙafa,banza shashasha wawiya daƙiƙiya,kuma ki sanya ido ki gani burinki akan Islam da Aslam,bazai taba cika ba,nan da lokaci ƙalilan zasu hade su zama abu guda ke kuma ki girbi abinda kika shuka na ha'inci da zalunci"Islam ta kai karshen maganar ta tana huci da hararar husna. Saƙare husna tayi tana kallon Islam,zuciyarta kamar zata buga dan tsabar tsanar islam. "Ni kika mara? Husna ta fada cikin tsabar ɓacin rai tana huci. "An marekin,kiyi duk abinda zaki yi koba asiri ba? dan Allah karki ragamin kuma karki daina, kici gaba kiga inda zai tsaya,ke dai baki isa ki rabani da mijina ba"Islam ta faɗa tare da juwa ta koma jikin Aslam,bata wani tsaya jiran komai ba,ta kama bakinsa tare da hadewa da nata,saida tayi masa kiss iya son ranta kafin ta cire bakin ta cikin nashi,ko kaɗan kuma aslam bai hanata ba,saika Tataya da yayi. Cikin salon ta na jan hankali tace "Ina nan ina jiran zuwan ka gareni da safe,ko dare ko rana ashirye nake da baka hakkin ka mijina"tana faɗin haka tayi hanyar fita daga dakin,zuciyarta fari tass kamar auduga. "Wllh muddin ina raye keda Aslam ya kusanceki har abada,kuma zakiyi dana sanin wannan marin da kikayi min ƙaruwar gida kawai" Husna ta fada cikin daga murya. Ko juyowa Islam batayi ba bare ta kula Husna,dan koba komai yau kam tasan ta ƙonawa Husna rai dama zuciya bani ɗaya. Hankali kwance ta bi ko ina na gidan ta yayyafa turaren nan kafin ta koma ɗakinta ta kwanta. Bayan fitar Islam daga dakin Husna ta juyo da kallonta kan Aslam,Wanda Yayi tsaye ya haɗe hannayen sa akan ƙirjinsa,shi ko kaɗan baiji komai game da abinda Islam tayiwa Husna ba saima burgeshi da Islam ɗin tayi,dan tayi maganin husnan,nan gaba idan zata shiga daki,ta koyi da'ar shiga ɗakin,wato sallama. Cikin fushi da tsabar rashin kunya Husna ta matso kusa dashi sai huci take "wllh ka bani mamaki,yanzu kana gani agabanka waccan karuwar ta zabga min maruka har biyu?kuma kana kallo bakace komai ba?bayan cin amanar da kuka maƙale cikin daki kuna min?wllh ban taba sanin kai lusari bane sai yau,kuma wllh bazan yarda ba mugu azzalu.... "Keeeeeh Husna!!! Ki iya bakinki,kisan da wa kike magana kinji"Aslam ya katse mata maganar ta cikin daka mata tsawar da saida ta sanyata matsawa daga gareshi,cike da mamaki take kallonsa,yadda yake huci kamar wani zaki "Honey Ni kake yiwa tsawa haka?dan na fadi gaskiya akan cin amanar da kukayi min?Husna ta fada,fuskarta ɗauke da mamaki. Wani shegen kallo Aslam ya watsa mata kafin yace "for God sake Husna ki daina ambaton cin amanar nan,raina yana ɓaci sosai,ke yanzu kin manta irin abubuwan da mukayiwa yarinyar nan?watan ki nawa agidan nan?shin kullum ba tare muke kwana dake ba?kin taba ganin na kwana adakinta?shin duk lokacin da kika bukaceni ba biye miki nake ba?baki san itama matata bace ?kuma tana da hakki akaina,amma ko kaɗan bana bata wannan hakkin nata,duk kuma saboda ke? To ki sani daga yau bazan kara cutar da Islam ba,zan raba muku kwana kamar yadda yake aƙa'ida,ko wacce zanyi kwana biyu tare da ita,kuma saidai kuzo dakina bazan je nakuba"Aslam ya fada cikin ɗaure fuska yana zarewa Husna ido,dan ko kaɗan ji yayi cikin zuciyarsa baya shayin ta,sannan ga wani irin haushinta da yake ji . Cikin kuka da tarin damuwa Husna tace "wllh baka isa ba,Ni zaka maida yar iska akan waccan shashashar yarinyar ?wllh bazan raba kwana da ita ba,saidai ka zaba ni ko ita Shegiyar karuwar" ta faɗa cike da rashin kunya tana karkaɗa motsatstsen ƙugunta. "Wllh !Husna,idan kika ƙara kiran matata da karuwa ranki saiya mugun ɓaci ,ke in banda baki da hankali ma,har. Kya kira wata karuwa,ke kin manta ya taki rayuwar take abaya?wane irin iskanci ne bakiyi ba banza kawai shashasha, ficemin daga daki"Aslam ya fada cikin tsawa mai ƙarfi. Mamaki,tsoro,fargaba sune suka cika zuciyar Husna,wanda har zallar mamakin ya bayyana ƙarara akan fuskarta,anya kuwa asirin jikin Aslam bai karye ba?yanzu ita yake iya kallo yana fadawa waɗan nan bakaken maganganun harda gorin ita karuwa ce? "I said get out of my room"ya ƙara daka mata tsawa. Da gudu Husna ta fice tana kuka haikan. Yau Aslam yaci mutuncinta,kuma wllh saita ci uwar Islam . Waya ta dauko tana kuka ta rika mommynta. Cikin kuka take faɗin"na shiga uku mommy,wllh asirin da mukayi ya karye,bakiga yadda Aslam yaci mutuncina akan wannan Shegiyar yarinyar ba yau,mommy Dan Allah ki taimaka min"Husna ta fada cikin kuka sosai harda shashsheƙe. Cikin damuwa mommy tace "kinga kiyi shiru Husna,ganinan zuwa gidan naki,dama zan kawo miki sako. Ki kwantar da hankalinka Aslam din banza daga shi har Islam ɗin, wllh basu isa komai ba,kijirani yanzun nan"mommy ta faɗa cikin ɓacin rai,tana mai janyo mayafinta. Haka Husna ta zauna tana kuka akan gadonta cikin damuwa da abinda Aslam yayi mata yau. Islam kuwa kwanciyarta tayi akan gado,ranta fari tass,koba komai yau ta konawa Husna zuciya,murmushi tayi tare da mikewa da sauri bayan tayi wani tunani cewar zuwa anjima Husna zatayi bakuwa,ya kamata ta kara kunsa musu daga ita har bakuwar Tata. Dan haka ta mike cikin farin ciki ta buɗe sif ɗin ta,wasu riga da wando ta dauko wandon baki ne tree quarter wandon roba ne sosai yayin da rigar ta kasance jace mai adon bakaken fuwalowi, sannan irin mai high neck ɗin nan ce rigar da dogon hannu.feshe su tayi da turare mai daɗin ƙamshi,sannan ta cire rigar jikinta ta sanya kayan,wayyo masu karatu,hakika dole duk na mijin da yayi tozali da Islam awannan shigar saiya rude, Dan kuwa kayan na neman magana ne,ko mace idan ta kalli Islam da wannan shiga sai taji dama ita ke da ƙira irin ta Islam,bare kishiya. Wannan karon cire ribom ɗin kanta tayi tare da bazo da gashin ta baya.jan baki ta dauka ta ɗan ƙara shafawa abakinta. Ja ta danyi da baya kaɗan tana karewa jikinta kallo,murmushi tayi tare da faɗin"Islam rainon dawa ajiyar Allah matar Aslam... "Kuma abar sonsa akoda yaushe ba " Islam ta tsinkayo Muryar Aslam daga bayanta yana faɗin hakan. Ɗan zaro ido Islam tayi tare da juyowa tana kallon Aslam dake tsaye jikin ƙofar dakin,ya shirya tsaf cikin blue ɗin shadda ya kafa hularsa kalar shaddar,sai ƙamshi yake zubawa. Ƙuri ya kafeta da ido kamar yau ya fara ganinta. "Islam !!Ya kira sunanta cikin wani kalar voice mai cike da nishaɗi. Ahankali ta ɗago kanta cikin wani salo na jan hankali tare da lumshe idonta kafin ta buɗe su fess akansa. Lumshe ido Aslam yayi tare da dafe saitin zuciyarsa yana sauke ajiyar zuciya mai ƙarfi. Buɗe idonsa yayi yana mai faɗin" I love You Islam, ina matukar so da ƙaunar ki,kece hasken zuciyata . Ke mai kyau ce komai naki yana da shiga rai Islam, zan je na dawo ki sani yau ranar taki ce yau ce nake ji ajikina Islam da Aslam zasu zama abu daya.na shiryawa wannan ranar "ya fada yana mai kissing hannunsa sannan ya huro mata iskar,ya fice cikin sauri. Dan ya sami kiran gaggawa ne akan harkar kasuwancinsa, kuma yasan idan har ya shiga cikin dakin nan na Islam,ahalin yanzu,to fitowar kam sai ta allah.yanzu haka mugun dauriya yayi bai rabeta ba. Wani irin tsalle Islam tayi tare da sakin wani dan kara na murna tana faɗin "alhmdllh yau dai ya fada min yace yana sona wayyo Ni Islam am happy "ta faɗa tana tsalle . Saida ta gama tsalle -tsallen ta na farin ciki kafin ta fito zuwa babban falo, fridge ta nufa ta dauko lemo ta dawo ta zauna,tsiyayawa tayi a cup ta fara kurba cike da farin ciki. Tana nan zaune cikin farin cikinta taji ana kwankwasa ƙofa, mikewa tayi tare da ajiye kofin hannunta ta nufi ƙofar da takunta mai daukar hankali. Buɗe kofar tayi tare da kallon wanda ke kwankwasa kofar. Kallon kallo aka fara tsakanin ta da mahaifiyar Husna,wacce tayi tsaye cikin takaici tana karewa Islam kallo tun daga sama har ƙasa,lallai wannan yarinyar idan bada asirin ba,to bazata bar Husna ta zauna cikin gidan nan ba,ko da iya wannan jikin nata zata kwace miji,kalli wannna Shegiyar shiga dake jikinta . "To zaki kauce ne ki bani hanya ko kuma tsaurin ido zaki tsaya min kina kallon cikin idona"mommyn Husna ta fada cikin faɗa ,kana jin muryarta kasan bakin ciki ne fal ranta. Murmushi Islam tayi kafin ta ɗan sanya hannunta ta maida gashinta baya tana mai cewa"Ayya ai baki sanar dani ko gurin wa kika zo ba,dan gaskiya Ni ban gane kiba,kuma kinsan duniyar nan yanzu sai ahankali,amma naga kamar kina kama da waccan ƙatuwar matar ta gidan nan,to bismilla shigo "Islam ta fada fuskarta ɗauke da murmushi tana kaucewa daga bakin ƙofar.dan sarai ta gane mommyn Husna. Kallon ashe baki da kunya mommyn Husna tayi mata kafin tace "ke yarinya karkimin rashin kunya,dan wllh dai -dai nake dake nima cikakkiyar yar bariki ce da kike ganina"mommy husna ta faɗa tana shigowa cikin Falon. "Na ga alama kam"cewar Islam tana nufar kujerar data tashi,cikin taku irin na yan fashion ɗin nan. Binta kawai mommyn Husna tayi da kallo,kafin ta jinjina kai tace "dani kike magana yarinya zaki gane baki da wayo. Husna ce ta fito tare da kama hannun mommyn ta suka nufi dakin nata,Bama ta kula da Islam ɗin ba,dan hankalinta tashe yake. Dariya Islam tayi cike da nishaɗi tace "hmmmm ku gama kulle kullenku duk zan kwashe su in bata muku aiki ne"tana faɗin haka ta nufi ɗakinta ta dauko wannan kwalbar ta dawo ta zauna. Husna kuwa kuka take sosai tana sanar da mommynta abinda ya faru. Rarrashinta mommyn tayi kafin ta dauko wata yar kwarya ta mika mata tace "kinga wannan kwaryar,to zuciyar Aslam ce aciki,muddin kikayi yadda nace kiyi dai-dai to ba Aslam ba ko uwarsa da ubansa sai abinda kika ce musu,ita kuwa wannan yarinyar Kashima saiya fita daraja agidan nan"mommy ta faɗa tana mikawa Husna kwaryar,wacce ke dauke da wani ɗan karamin ƙoƙo da wani jan abu aciki yana ta motsi da tururi kakar hanta. Karba Husna tayi cikin farin ciki tace "har naji daɗi mommy wllh kuwa saina Gara kan yan gidan nan Dukansu,dan naga dama sun fara min wani gani gani. Waccen Shegiyar kuwa zatayi bayani ne"ta faɗa cike da mugunta tana ƙwafa. "Yanzu maza ki tashi ki daga katifarki ki ajiye kusa da waccan tsohuwar ajiyar sannna ki barbada wannan garin maganin agurin,shikenan komai ya kammala"cewar mommy tana miƙa mata wani garin maganin. Cikin azama kuwa Husna ta fara aiwatar da abinda mommyn ta sata har ta kammala murna kamar zata kasheta. Bayan sun kammala ne mommy tace "Ni zan tafi sai naji sakamako,Daddyn ki ma yace agaida ke"ta faɗa tana mikewa tsaye. "To mommy Nima kice Ina gaida shi,kuma mommy kinga dai har yanzu Ban sami cikin ba"ta faɗa cikin shagwaba. "Yawwa kinga na manta ma akwai wani maganin samun ciki dana karbo miki muje cikin mota saina baki,kina sha da zarar ya kusanceki shikenan sai ciki,idan kika haihu kinga dukkan dukiyar sa ta zama tamu"mommyn ta faɗa tana kama hannun Husna sukayi waje cikin dariyar farin ciki. Suna fitowa falo Islam ta ce"bakuwa kin fito kenan?amma fa kun gama da wuri,to agaida gida ko,aniyar kowa ta koma kansa "ta faɗa cikin murmushi tana dagawa mommy Hannu. Da sauri Husna ta yunkuro zatayi kan Islam mommyn ta ta riƙe ta tace "barta kawai ai mun gama da ita " Harara Husna ta zabgawa Islam kafin sukayi waje. Suna fita Islam tayi saurin nufar dakin Husna,inda bata tsaya komai ba ta daga katifar ta dauko duk tarkacen dake kasan gado bayan ta yayyafa turaren nan,layoyine kala kala,harda su gashin zaki,dasu kwai cikin kwalba,tarkace dai iri-iri. Duk cikin kwaryar da aka kawo asirin yau ta watsasu kafin tayi saurin fitowa. Ɗakinta ta kai ta ajiye kafin ta koma dakin Aslam nan ma ta ɗauko layoyin dake ƙasa. Gadonsa ta fito. Daki ta kai ta ajiye sannan ta dawo falon ta zauna. Husna ce ta dawo cikin Falon da murnarta. Kallon Islam tayi tare da riƙe ƙugu tace "yarinya zan baki shawara ne,Gara tun wuri ki fara hada kayanki dan barin gidan nan,dan kuwa nan da lokaci ƙalilan zaki zama abar tausayi,badai Ni kika mara ba har karo biyu wllh saikin san kin taba Husna " Husna ta fada cike da gadara. Murmushi Islam tayi kafin tace "ina nan ina jira Malama Husna giwar mata, amma fa ki sani da Islam rainon dawa kike fafatawa, ba'a cin nasara akan Islam"Islam ta faɗa cikin murmushi tana kurbar lemonta. Takaici kamar ya kashe Husna ta nufi ɗakinta bugun bugun. Muje zuwa masu karatu. Anty mammy ce. [11/23/2022, 12:26 PM] Abk: 87/88 ____________Takaici kamar ya kashe Husna,haka ta nufi ɗakinta buguzun -buguzun tana huci,saidai tana tunowa da shirin da sukayi akan Islam,sai taji zuciyarta tayi sanyi sosai. Islam kuwa tashi tayi tare da komawa cikin ɗakinta,doguwar riga ta dauko ta sanya,sannan ta kulle ɗakinta ta nufi cikin gida. Granny ta samu da mommy suna zaune afalo,sai jannat wacce zuwan ta kenan gidan, tana zaune kusa da granny da katon cikinta. Murmushi sukayi wa juna ita da Islam,kafin Islam ta zauna kusa da jannat tana mai faɗin"maman biyu kece atafe? Sannu fa" Islam ta faɗa tana dafa kafadar jannat. Murmushi jannat tayi kafin tace "nice sister nace bari dai yau nazo na kawo muku ziyara,baki taba zuwa gidana ba sister"jannat ta faɗa tana ɗan kwabe fuska. "Zanzo amma sai kin haifa min baby tukunna"cewar Islam tana dafa cikin jannat. "Ke kiji rashin zuciya fa,yanzu Islam maimakon kema kiyi fatan ki haifi naki,saidai kirinka cewa ahaifa miki,wllh Gara ki dage tun kafin waccan mai ƙirar agwagwar ta rigaki aje yara agidan,Ni wllh sai yanzu ma nake mamakin ta yaya Aslam idonsa ya rufe har ya auri waccan guzumar "cewar granny kenan tana taɓe baki. Dariya Islam da jannat sukayi kafin jannat tace "wllh granny ba ruwanmu keda yaya kina fadawa matarsa sunaye iri-iri" " Yo yayan banza yayan wofi,ko agabansa ne ai zan fada, idan kuma yayi min magana wllh in zage in gabgabje masa baki ba ruwana"cewar granny tana wani bugun cinya. Dariya sukayi sosai harda mommy wacce ke dariyar ta aboye,gudun sababin granny. Saida azahar tayi kafin Islam ta koma part dinsu shima so take taje tayi wanka ta sake kwalliya kafin oga ya dawo, Kai tsaye ta wuce ɗakinta,bayi ta shiga tayi wanka tare da dauro alwala sannan ta fito salla ta farayi kafin ta shafe jikinta da mai me ƙamshi sosai kafin ta tsara kwalliya mai kyau afuskarta. Wannan karon doguwar riga ta sanya wacce ta kamata daga sama,sannan daga ƙasa rigar ta buɗe sosai irin rafar nan ce yar kanti. Tayi kyau sosai lokacin data roller Dan kwalin rigar akanta kamar mayafi. Haka kawai taji tana son yiwa Aslam girki,dan haka fitowa tayi tana ta buga uban ƙamshi ta nufi kitchen Din falon. Husna na zaune riƙe da rimot ahannunta,tun kayan data sanya dazu, sune har yanzu ajikinta,kuma wannan zaman tayi shine ana jiran miji ya dawo suci abinci,dan tun ɗazu yan aiki suka kawo abincin daga part ɗin mommy. Kallonta Islam tayi cikin murmushi tace"Hajiya Husna ana hutawa kenan,Barka da aiki fa" ta faɗa cike da zolaya. Afusace Husna ta mike tsaye "ke wllh ki kiyayeni niba sa'ar ki bace,na wuci ajikinki wllh,banza mai kama da karuwa"Husna ta fada cikin huci. Dariya Islam tayi tana mai faɗin"kai ashe Ni karuwa ce ban sani ba?amma Gara da kika tunatar dani wllh, amma kinyi kuskuren kirana da wannan sunan,dan haka saiki shirya dan kallon karuwancin rainon dawa kala -kala"Islam ta faɗa tana mai yin gaba abinta cikin takunta na izza. Binta kawai Husna tayi da kallo cike da takaici.wannan kirar ta Islam tana mugun sanyata cikin damuwa,Shegiyar yarinya kamar wanda aka sassakata. "Wllh saina ga bayanki cikin gidan nan "Husna ta fada tana komawa kan kujera ragwab ta zauna. Islam kuwa nutsuwa tayi ta shiryawa Aslam lafiyayyen girki mai rai da lafiya.gaba ɗaya gidan banda ƙamshi ba abinda yake zubawa. Hankalin Husna duk yana kan me Islam keyi haka yake ta ƙamshi kamar a restaurant?. Islam kuwa Tana kammalawa ta zubo cikin lafiyayyun kuloli ta kawo falon ta ajiye sannan ta dauko lemon kwakwar data hada shima ta sanya cikin fridge . Sannan itama ta nemi guri akan daya daga cikin kujerun ta zauna. Kallon juna sukayi Islam ta dagawa Husna gira daya tace "yadai Malama da kallo haka?Ni karki gama kallemin kwalliya wanda nayi domin sa bai kalla ba"Islam ta faɗa tare da murguda dan bakinta,wanda ya Sha light pink din Jan baki. Tsaki Husna tayi cikin takaici tana mai cewa"aikin banza wannnan mummunar fuskar taki zan tsaya kalla?kijira ki gani wanda kike iƙirarin kinyi domin shi ɗin ma bazai kula kiba,bare harya ci wannan jagwalgwalon da kikayi da sunan abinci"Husna ta fada tana hararar Islam. Dariyar baki da hankali Islam tayi kafin tace "haka kika ce ko?let watch and see malama Husna"ta faɗa cike da ƙarfin gwuiwa tana jingina da jikin kujera. "Aikin banza aikin hofi wllh idan juninki asiri kuma kina takama da shi ne ,to yarinya gidansa kika zo, duk inda kika shiga dan ki farraƙa tsakanina da honey, to kisani kinyi kadan keda masu taimaka miki,dan inda mu muke zuwa ko za'a kashe ahalinki duka baku isa zuwa gurin ba"Husna ta fada cike da rashin hankali irin nata. Kallonta Islam tayi tana mai jinjina ka tare da sauke ajiyar zuciya tace "aikuwa kinji asara dake da uwar taki,da baku da aiki saina asiri,wllh kuji tsoron Allah in ba hakaba wuta zai jefaku keda ita "Islam ta faɗa kai tsaye ba wani shayi. Aikuwa cikin zafin rai Husna ta mike tsaye tayo kan Islam"dan uwarki nida mommyn nawane yan wuta?wllh yau saikin fadamin uban daya daure miki ƙugu kike rainani, ko dan kinga Ina gyaleki?wllh yau saina illataki "Husna ta fada tana rarimo wani ƙaton abinda ake jere irin kayan marmarin nan na roba Dan decoration, Cike da mugunta ta daga abun tana niyar rafkawa Islam,wacce ke zaune ko kezau batayi ba. "Kee! Kee!!keee!!! Husna meye hakan?me kike ƙoƙarin aikatawa?kisan kai zakimin agida? Baki da hankali ne kike ƙoƙarin buga mata wannan katon abun ? Aslam ne wanda shigowar sa kenan cikin gidan yayi tozali da abinda husna ke ƙoƙarin yi,Wanda saiyaga kamar ma Islam ɗin bata san da zuwan Husna ba,shammatar ta take sonyi dan ta illatata. Da sauri Husna ta juyo tana kallonsa,kamar yadda Islam ma ta juyo tana kallonnasa. "Honey zagina fa take,wai nida mommyna yan wuta ne "Husna ta fada cikin shagwaba kamar zatayi kuka,dan bataso shigowar Aslam yanzu ba,taso ace saita rotsewa Islam kai kafin ya shigo. "Dan ta fadi haka shine kike ƙoƙarin kasheta?"Aslam ya fada cike da ɓacin rai. Tsaye Husna tayi hannunta riƙe da abun dukan ta tana mai jin takaicin rashin nasarar da tayi. "Wllh koba yauba saina ci uwar yarinyar nan,kuma banga dan iskan daya isa ya hanani ba"Husna ta fada cikin rashin kunya tana jijjiga jiki. Afusace Aslam Yayi kanta yana faɗin "wato nine dan iskan ko?ya fada cikin tsawa. Ja tayi da baya tana ajiye makaminta tace "oho,amma idan ahakan ka ɗauka to da kai nake"ta faɗa tana murguda masa baki. Afusace ya ƙara yin kanta zuciyarsa kamar zata yi bindiga.ita kuwa tana ganin haka ta zuba da gudu zuwa ɗakinta,tana shiga ta kulle da key tana faɗin"wllh idan ka sake ka tabani da sunan duka bazan yarda ba,ka tabowa kanka bala'i da masifa daga kai har zuri'arka, mugu kawai azzalumi maci amana" Ran Aslam idan yayi dubu ya gama ɓaci wllh da ace zai kama Husna Ahalin yanzu,tabbas saiya kakkaryata,harshi take zagi haka?ai ko Islam da sukayi yar tsama da ita bata zaginsa kai tsaye,amma zata gane kurenta ne . Dawowa yayi tsakiyar falon cikin ɓacin rai ya tsaya kusa da inda Islam ke zaune tana kallon dramarsu,ko tari batayi musu ba. Kallon Islam yayi yadda tasha ado gwanin sha'awa,nan da nan yaji zuciyarsa ta fara yin sanyi. Ahankali ya kira sunanta "Fretty"ɗago da kanta tayi tare da sauke kwayar idonta cikin tasa tana ɗan langabar da kai cikin salon shagwaba. Mika mata hannu yayi yana mai cewa"come to me pretty, is ok"cikin salo da jan hankali Islam ta mika masa nata hannun ya kama ,taimaka mata yayi ta mike tsaye tana mikewar shikuma ya janyota zuwa jikinsa ya rungume sosai.ajiyar zuciya yayi ta saukewa yana jin kamar ana zare masa damuwar dake cikin zuciyarsa,da ɓacin ran da Husna ta sanya shi yanzu. Sun jima ahaka ba tare da ya saketa ba,saida taga abin nashi bana ƙare bane kafin cikin taushin murya tace "ya kamata muje kayi wanka na dafa maka abinci yau da kaina, sai kazo kaci"Islam ta fada masa daidai saitin kunnensa. Ƙara lumshe ido yayi cikin farin ciki yace "da gaske Fretty na tayimin girki?wow can't wait to eat,muje nayi wankan"Aslam ya fada yana kamo hannunta suka nufi dakin shi. Ihun kuka Husna ta kwalla wacce ke tsaye bakin ƙofa tana kallonsu duk abinda ke faruwa.cikin kuka take faɗin "wllh baka isa ka kusanci yarinyar nan ba yau saidai in bana raye,mugu kawai azzalumi " Ko jinta ma basuyi ba suka shige dakin na Aslam tare da ƙullewa. "Wayyo na shiga ukuna Ni husna,shikenan kashi na ya bushe wayyo mommy kina ina "Husna ta fada cikin kuka tana ɗora hannu aka,jiki na rawa ta dauko wayar ta ta rika mommy. Cikin kuka take cewa"mommy sun shige daki wllh na shiga ukuna sun kulle ƙofa mommy shikenan idan ya kusanceta nikuma tawa ta kare mommy"takai karshen maganar ta kara sanya kuka. Cikin damuwar jin kukan nata mommyn tace "Husna ki kwantar da hankalinki,ba abinda zai faru kinji?shigarsu daki ta banza ce dan ba abinda zai iya yi mata kuma zakice na faɗa miki karki damu kanki kiyi shiru,ai saisu gane akwai wata a ƙasa" Shiru Husna tayi tana mai share hawayen idonta kafin tace "mommy dazuma saida mukayi rikici da yarinyar nikuwa nace mata bokanmu yafi nasu zafi idan juninta asiri"Husna ta karasa maganar cike da wawanci. Dafe kai mommyn Husna tayi,tana takaicin rashin wayo da hankali irin na Husna,idan tayi wani abun ko kare bazai ciba. "Yanzu Husna meye maki na faɗa mata hakan?kinga kin bata kofar suma suje suyi nasu asirin kenan,dan Allah Husna ki daina wannan wawanci naki, kefa ba yarinya bace"mommy ta faɗa adan hasale. "To mommy Raina min hankali zatayi nikuwa na faɗa mata hakan,amma bazan karaba. Nan dai mommyn tayi ta rarrashin da kitsa mata makirci iri-iri. Islam kuwa ruwan wankan ta haɗawa Aslam inda ya dage saidai suyi tare amma taki fur, tace ita tayi nata,murmushi kawai yayi yace "kunya ko ?yau dai zan fitar da wannan kunyar gaba dayanta"yayi shigewarsa toilet. Murmushi Islam tayi tana mai ɗan jin faduwar gaba,amma tana tunowa cewar makarin asirin dake jikin Aslam ne yin hakan,saita karfafa zuciyarta. Bayan ya fito ne ya shafa mai tare da sanya kayansa wanda agaban Islam ya sanya kayan, sai itace ta runtse idonta cike da kunya,shikuwa yayi ta mata dariya. Cikin nishadi suka fito falon suka zauna gurin cin abinci sosai Aslam ya danni abincin nan yana santi, bai taba tsammanin Islam ta iya girki haka ba. Bayan sun kammala suka dawo falo suka zauna.janyota yayi jikinsa ya rungume suna kallo. Gaba daya farin ciki ya gama baibaye masa zuciya gashi ga Islam dinsa. Husna ce ta fito daga ɗakinta dan yunwa ta isheta,wannan karon anyi wanka an sake kaya zuwa doguwar rigar atamfa.fuskar nan tasha makeup kamar zata je gurin biki. Tsaki tayi lokacin da ta gansu rungume da juna tace "aikin banza mutum yayi ta liƙewa ƙanwar bayansa ba ko kunya ya kamata dai idan angirma asan angirma arinka kama kai"ta faɗa tana hararar Aslam, Cikin fushi ya yunƙura zai tashi,Islam tayi saurin rikoshi tana girgiza kai "Please karka biye mata kai babba ne fa"ta faɗa cikin shagwaba. Komawa yayi ya zauna yana huci ransa ya ɓaci sosai da wannan iskancin na husna. Ganin ransa ya ɓaci ya sanya Islam,juyo da fuskarsa saitin Tata ,kallon juna sukayi ta sakar masa murmushi,shima yayi mata,bakinsa ta haɗe da nata ta fara aika masa zafafan kiss aƙoƙarin ta na mantar dashi haukar Husna. "Keee !!meye hakan? Na shiga uku jama'a kunga ƙaruwar yarinya, agabana kike masa kiss dan rashin kunya?wllh wannan da gani tasan maza" Husna ta fada cike da takaicin islam. Cire bakinta Islam tayi daga na Aslam tana mai shafa gefen fuskarsa ,kafin ta tashi daga jikinta ta nufi gurin Husna. Tsaye tayi tare da rungume hannayenta aƙirjinta tana murmushi kafin ta fara magana"tace waike daga kiss kawai shine kike wani tada hankalinki?hahhha Islam tayi dariya tana tafa hannu.kafinta dora--ai wannan ba komai bane,ki bari na san namijin tukunna,wannan lokacin ne zaki ga zallar karuwanci,dan yanzu bakiga komai ba,kuma ba da jimawa ba anjima kaɗan zansa namiji kamar yadda kika sanshi,zan shayar dashi zumar da bazai taba mantawa da ita ba arayuwarsa,kinsan yau ranar tawace,yaune zamu angonce nida mijina,yaune zaisan yayi aure ya auri sabon jini,dan kuwa wannan keda mai haihuwa biyar baku da maraba,nasan ba abinda ya tarar agurin banda wahala, dan angama rabarwa maza titi kafin aka kawo mishi saura,am nidai Ina baki shawarar ki sanya auduga ki toshe kunnenki dan kar ihun Ango ya hanaki barci"Islam ta faɗa fuskarta ɗauke da murmushi ƙayatacce. Galala Husna tayi tana kallon Islam tsabar mamaki da iya yaɓa magana irin na Islam sun hanata cewa komai. Tana ji tana gani Islam ta kama hannun Aslam suka shige cikin daki. Tare da kulle ƙofar dakin bayan Islam ta juyo tayi mata bye -bye. Ihu Husna ta kwalla tare da nufar dakin Aslam tana dukan kofar da faɗin "wllh baki isa ba,sai kun bude kofar nan,bazaka kusanceta ba wllh wayyo na shiga ukuna Ni husna"abinda take ta faɗa kenan tana dukan ƙofar..... Muje zuwa masu karatu . Anty mamy ce. [11/24/2022, 12:11 PM] Abk: 89/90 ____________Wllh baka isa ka kusanci yarinyar nan ba,nizaka ciwa amana?na shiga ukuna Ni husna,Aslam kazo ka buɗe kofar nan kufito, wllh zan maka ihun kwarto"abinda Husna ke faɗi kenan,da alamu bata ma cikin hayyacinta. Runtse ido Aslam yayi cikeda takaici,baya son ya biyewa husna har zuciya ta sashi yi mata abinda bata tsammata ba,amma yaga alamun Husna so take ta kaishi bango,wai zatayi amsa ihun kwarto,saikace islam ɗin ba matarsa bace,ya fahimci bayan jahilci abin na Husna da iskanci ma . Kuma wllh zai koya mata hankali. Ahankali Islam ta sanya hannunta masu taushi tana shafa gefen fuskar Aslam,cike da alamun rarrashi,kallonta yayi fuskarsa ba walwala,lumshe masa ido tayi alamun yayi haƙuri. Ajiyar zuciya ya sauke mai nauyi, dake nuna ranshi abace yake. Murmushi Islam tayi masa tana mai shafa lips ɗinsa da hannunta,kafin ta kama hannunsa suka zauna bakin gado. Kansa ta janyo tare da kwantarwa akan cinyoyinta tana mai shafa lallausan sumar kansa wacce tasha gyara. Aslam kuwa hannunsa ya sanya tare da zagaye Islam ta rungume ƙugunta ƙam ,yana mai jin sanyi na ratsa masa zuciya.ahankali kuma ɓacin ransa ke gushewa. Suna jin Husna sama sama tana ta haukarta har ta hakura ta bar gurin. Tashi Aslam yayi zaune tare da kama fuskar islam da duka hannayensa, kallon juna suke cike da soyayya. Ahankali yace "Islam ina sonki !ina kaunarki bansan menene soba sai akanki,nayi nufin sanar dake hakan lokuta da dama,amma bansan meke hanani yin hakan ba. Saidai kalmar tana cina cikin raina,amma tun da na furta ta gareki akaron farko,nake jin kamar an saukemin wani nauyi ne cikin raina,Islam ina fatan kiyimin koda kwatan son da nake miki ne azuciyarki"Aslam ya fada yana mai kissing lips ɗin bakin ta. Cike da tsabar kauna Islam ke kallon fuskar Aslam,haƙiƙa kalamansa sunyi mata daɗi fiye da kima,wannan sune irin kalaman da take burin ji daga gareshi akoda yaushe,yau gashi Aslam da bakinsa yana furta mata kalaman soyayya,lallai nasara na tare ga mai hakuri. Ajiyar zuciya Islam tayi tare da cewa"lokacin sallah yayi "ta faɗa cikin siririyar Muryar ta mai kama da ana busar sarewa. Juyawa Aslam Yayi tare da kallon ƙaton agogon dake kafe jikin bango,sannna ya juyo zuwa ga Islam yace "muje muyi alwala yau nine zan ja mana jam'i "ya fada tana mai miƙar da Islam tsaye. Bayan sunyi sallar la'asar ne Aslam ya ɗora hannunsa tsakiyar kan Islam ya fara jero addu'oi.kamar haka "(Bismillahi allahumma inni as'aluka khairaha wa khaira ma jabaltaha alaiya,wa azubika min sharriha wa sharri ma jabaltaha alaiya.) Haka yayi ta kwararo addu'oi kala kala hannunsa na tsakiyar kan Islam. Koda ya kammala suka shafa addu'ar tare da nade sallayar suka koma bakin gado,tashi Aslam yayi tare da cewa Islam,ta bashi minti biyu. Ficewa yayi daga uwar dakan ya nufi falo,kai tsaye ya shiga kitchen . Fridge ya buɗe tare da dauko ƙatuwar kaza agyare mai kyau,cikin hanzari ya gasa kazar nan cikin oven,sai ƙamshi take, haka ya fito da ita daga cikin oven din ya sanya kan wani kyakykyawan flate,sannan ya sanya wuka da fork,ya nufi dakin nashi. Islam na zaune riƙe da wayar Aslam tana game sai ganinsa tayi da kaza ahannu. Murmushi tayi tana mai karbar kazar ta ajiye akan table ɗin daya matso dashi zuwa gabanta. Dan shagwabe fuska Islam tayi tare da cewa"sannu da aiki,shine kaje kayi da kanka maimakon kace inzo inyi"ta faɗa tana ɗan turo baki da kif-kifta ido. Murmushi yayi yana mai riƙe haba yace "ina Ni ina sanya amarya aiki yau?ai kiyi zamanki kedai ki zage kici kaza saboda aikin da zakiyi ba karami bane duk da nasan Islam ɗina jaruma ce kuma ba raguwa bace ko? Ya faɗa yana ɗan leka kan Islam dake sunkuye. Murmushi tayi tare da daga masa kai alamun haka ne. Dan cije lips Aslam Yayi Yana dariya ƙasa -ƙasa tare da jinjina rashin wayo islam,sam yaga ba wani alamun tsoro sosai atare da ita,gani take abun dake shirin faruwa da ita yanzu mai sauki ne. Fita ya karayi ya dauko madara tacacciya mai kyau cikin fridge da ruwa ya dawo. Zama yayi kusa da islam,da kansa ya ciyar da ita kazar nan,sosai ya dura mata madarar bayan ya tabbatar da ta koshi da kazar nan,shima ci yayi ya koshi sosai.kafin ya ɗauke kayan zuwa falonsa. Dawowa yayi ya zauna kusa da islam,tare da riƙe hannunta yana ɗan matsawa cikin nashiSunkuyar da kai Islam tayi,sai lokacin kuma taji gabanta na bugawa tsoro ya darsu cikin zuciyarta, fargaba ta cikata. Ahankali Aslam ya ɗago habarta Yana mai kallon cikin idanunta wanda tsoro ya bayyana cikin su.murmushi yayi yana mai faɗin"ya akayi ne pretty,why this silent hummm?"ya fada yana mai hada goshinsu guri ɗaya tare da goga tsinin hancinsa kan nata hancin. Lumshe ido Islam tayi cikin shagwaba tace "am scared "ta faɗa kamar mai rada ahankali. "No pretty don't be scared ok,I will be gentle to you" ya fada yana mai kama lips dinta ya fara tsotsa. Ahankali yake romancing din Islam,cikin salo da ƙoƙarin cire mata tsoron dake tare da ita,aikuwa tun tana jin tsoron har ta manta da batun sa,itama ta fara maida masa martani cikin salo mai tafiya da imani. Gaba ɗaya sun fita daga hayyacinsu ba abinda kake jiyowa sai saukar numfashi su cikin sauri,baka iya ganin su sosai,dan tuni Aslam ya kashe hasken dakin.sai dakin yayi dan duhu dan labulayen dakin duka asake suke. Gaba daya Aslam ya rabasu da kayan jikinsu inda ƙaton bargonsa yayi musu sutura ta hanyar lulluɓe jikinsu da sukayi dashi. Addu'ar saduwar da iyali Aslam ya fara dan kuwa kwata -kwata yau asalamiyyar sa bata kwanta ba,tana nan tsaye ƙyam kamar karfe.(allahumma jannabnash shaiɗana wa jannabash shaiɗana marazaƙtana) ya furta cikin rawar murya da sarƙewar numfashi. cikin sauri Islam ta riƙe hannun Aslam jikinta na rawa tace "Please karka yi am scared tsoro nakeji,Ni kawai na fasa "ta faɗa tana mai ƙoƙarin turesa daga jikinta,cikin tsoro. Shima cikin rawar murya yace "no Islam karkiyimin haka Please,bazan iya jura ba,kiyi haƙuri bazan miki da zafi ba kinji? karki tsorata"ya fada cikin rawar murya da jiki. Shiru Islam tayi,tana mai ambaton sunan Allah cikin ranta,dan kuwa sosai ta tsorata da yanayin na Aslam,barin ma yadda taji Asalamiyyar sa na tokarinta kamar wani rodi. Shikuwa ci gaba yayi da uzurinsa cikin zaƙuwa da gaggawa yake komai. Wani irin ƙara mai ƙarfi Islam ta kwalla tare da ƙanƙame Aslam ƙam idanunta aruntse,sakamakon wani irin azababben radadi da taji yana ratsa kwakwalwarta da dukkanin sassan jikinta. Ihu ne irin wanda duk mutumin da yaji yasan cewa mai afkuwa ce ta afku,kuma kwalla ihun nata yayi daidai da fitowar Husna daga ɗakinta da nufin zuwa ta ƙara buga musu kofar ta yadda zata damesu su kasa aikata komai. Zaro ido tayi cikin mugun faduwar gaba,tana mai dafe ƙirjinta,shikenan komai ya kare "na shiga ukuna Ni husna,na lalace Wllh ya kusanceta,ya kusance wllh shikenan asirin ya karye, wayyo Allah na mommy kina Ina mommy kizo ki hanashi wllh ya kusanceta "Husna ta fada cikin rawar baki tana nufar kofar dakin Aslam da saurin ta. Wanda zuwan ta yayi daidai da karan da Islam ta sake kwallawa,wanda tana ajiye nata na Aslam ma ya biyo baya,zamewa Husna tayi abakin kofar dakin tana kuka kamar ranta zai fita. Buga kofar take tana faɗin"ka bari Aslam,Dan Allah karka kusanceta zaka lalata min shirina,zaka tarwatsamin rayuwa wayyo Allah na shiga ukuna" Abinda take fadi kenan tana buga kofar cikin kuka. Can cikin dakin kuwa, Islam kuka take sosai tana dukan Aslam akan ya bari bata so ta fasa,amma ina shima kukan yake yana ambaton sunan Allah. Tun tana iya dukan nashi harta kasa tayi lamo,kukanma baya fita saidai hawaye kawai. Saida Aslam ya kwashe lokaci mai tsayi yana abu daya kafin ya samu nutsuwa,irin wacce bai taba tsammanin ko jin labarin akwai irinta aduniya ba ma,bare yayi tunanin samun ta. Gefen Islam ya kwanta tare da janyota jikinsa ya kankameta kamar wani zai kwace ta daga gareshi. Banda ajiyar zuciya ba abinda yake yi,hawaye kuwa sai zuba yake daga idanunsu baki daya. Ahankali yake shafa kan Islam alamun rarrashi,wacce daga karshe barci yayi gaba da ita na tsabar wahala. Da ƙyar Husna ta yunƙura ta tashi ta nufi dakinta,kuka take sosai kamar wacce aka aikowa saƙon mutuwa.ta riga tasan cewa tata ta ƙare,amma tana mamakin ta yaya asirin jikinsa ya karye?bayan mommyn ta faɗa mata cewar anyi masa asirin da bazai iya kusantar Islam ɗin ba. Wayarta ta dauko tare da kiran mommyn nata cikin kuka take cewa"mommy me yasa kikayimin karya?kince Aslam bazai kusanci yarinyar nan ba,amma gashinan ya kusanceta shikenan komai ya lalace kin cuceni wllh mommy I hate you "ta faɗa tare da jifa da wayar tana kuka kamar zararriya. (Nikuwa nace ƙarfin hali kenan wai barawo da sallama,mutum da matarsa kice bazai raya sunna ba?. Allah ya kyau yasa mufi karfin zuciyarmu ameen). Lokaci daya Aslam ya farajin wani irin amai yana taso masa,da sauri ya kwantar da Islam ya nufi toilet,inda yayi ta kwarara wani jan amai kamar jini,daga baya kuma ya koma baki ƙirin dashi,amai yake kamar zai mayar da kayan cikinsa. Tun yanayi daga tsaye harya durƙushe ƙasa,sosai ya galabaita dan ko tashi ka ya kasayi. Ahankali Islam dake kwance idonta abude tun lokacin daya kwantar da ita ta buɗe ido,ahankali ta yunƙura tana mai runtse idanunta dan tsabar azaba,da ƙyar ta zauna tana mai riƙe bayanta.sosai take jin kakarin aman na Aslam. Wani towel ta janyo tare da daurawa ajikinta,sannan ta sauka daga kan gadon,tana dafa bango da runtse ido ta nufi toilet din. Kwance ta tarar da Aslam Yana kakarin amai idonsa na rufewa da budewa. Zaro ido tayi tare da ƙarasawa cikin toilet din da sauri,zama tayi da ƙyar tare da ɗago kansa ta ɗora akan cinyarta, tana shafa kansa hawaye ne kawai yake zuba daga idanunta. Muryarta ta dashe dan haka ko maganar ta baka iya jiyowa. Numfashi kawai Aslam ke saukewa da sauri da sauri yana riƙe da hannun Islam kam cikin nashi,ahankali kuma idanun sa suka rufe ruf kuma ya daina sauke numfashin sannan ya saki hannun Islam daya riƙe gam..... Muje zuwa masu karatu. Anty mammy ce Mrs babi. [11/25/2022, 12:43 PM] Abk: 91/92 ____________Ahankali numfashin Aslam ya fara daidaita,sannan ya sassauta rikon da yayiwa hannun Islam,yana lumshe ido cike wahala. Gaba ɗaya jikinsa ba ƙarfi haka yake ji, ga wani irin yanayi da yake ji yana shiga jikinsa.ji yake kamar wanda ake zare masa ƙaya cikin jikinsa. Ahankali Islam ke shafa kansa cikeda tausayawa,yayinda itama jikinta yayi zafi sosai alamun zazzaɓine ya rufeta. Ahankali ya sanya hannunsa tare da shafa kuskarta cikin muryar jigata yace"pretty you are sick am sorry nine ko?"ya fada cike da tausayawa,dan yasan tasha wahala sosai agurinsa. Lumshe ido Islam tayi tana mai jin yadda jikinta yayi mata ba dadi, ko ina ciwo yake mata. Kallonta Aslam yake cike da wani irin bala'in so da kaunarta da yake jin yana ratsa dukkan wasu sassan jikinsa,sosai yake jin kamar ya maida ta cikinsa dan so. Islam ta shayar dashi zumarta mai tsayewa cikin rai wanda harya koma ga Ubangiji bazai taba mantawa ba. "Islam na gode ,Nagode da mallaka min kanki da kikayi, ayau kin sanyani cikin farin ciki marar misaltuwa,Islam bansan da wane irin baki zan miki godiya ba,ke ɗin ta musammance, kamar yadda komai naki yake na musamman,Allah yayi miki albarka yasa nayi ajiya cikin wannan cikin naki"ya fada yana mai shafa cikinta cike da ƙarfin gwuiwa. Hawaye ne ke zuba cikin idanun Aslam,kamar yadda Islam ma ke zubda hawayen amma saida ta ɗan murmusa kanta aduke,saidai nata hawayen yana da ma'anoni da dama,na farko tana farin cikin asirin jikin Aslam daya karye,sannan na biyu kuma tana kukan ciwon da jikin ta keyi,ji take kamar ana barbada mata barkono aƙasanta,zaman da tayi yanzuma kawai dauriya take .lumshe ido tayi tare da jingina kanta da jikin bango tana mai cije lips. Kallonta Aslam Yayi cike da tausayawa, yasan zafi take ji dan haka yunkurawa yayi yana mai ɗan dafe kansa dake sarawa ya tashi zaune,kafin ya mike cikin juriya, dan jiri yake ji sosai. Kai tsaye gurin kwamin wanka ya nufa,saida ya cika shi tab da ruwa,kafin ya zuba sinadaran rage radadi da turaren wanka. Dawowa yayi kusa da islam dake zaune har yanzu kanta jingina da jikin bango,kuma idanunta arufe. Bai jira komai ba kawai ya durƙusa ya ɗauke ta cilak ya nufi bahon wankan da ita. Buɗe ido tayi tana kallonsa cike da shagwaba tace "nifa zan iya tafiya da kaina"ta faɗa tana mai lumshe idonta. Murmushi yayi kafin yace "ai taimaka miki kawai nayi nasan kedin jaruma ta ce akwai dauriya,tunda har kika iya sanya Aslam kuka da idanunsa lallai kin cancanci yabo Islam na"ya fada cikeda nishaɗi da tsantsar farin ciki,wanda ya bayyana akan fuskarsa,sumbatar lips dinta yayi wanda yake sheƙi kamar ta shafa man lebe. Yana zuwa bakin kwamin ya zauna agefensa tare da sanya Islam cikin zazzafan ruwan. Wani irin kwalalo ido da Islam tayi tare da zabura,saikayi tunanin wuta aka watsa mata,hakan kuwa ya samo asali ne ta yadda taji wani irin azababben zafi daya ziyarci ƙasanta. Da sauri Aslam ya riketa tare da maidata cikin ruwan,yayi kalar tausayi sosai yana faɗin"sorry pretty ki daure zaki ji dadi idan ruwan ya ratsaki"ya fada yana mai ƙara riketa sosai,dan sosai jikin Islam ya dauki rawa. Cikin matse fuska tace "is hot ,akwai zafi ruwan dan Allah ka fitar dani Ni bana so"ta faɗa cikin Muryar shagwaba tana mai riƙe damtsen hannunsa. "Sorry na sani akwai zafi amma yanzu zai daina kinji yi hakuri daure farin cikina"ya fada cikin sigar rarrashi yana mai shafa gefen fuskarta. Runtse ido tayi sosai tana juya kai dan sosai ruwan ke ratsa kasusuwanta, hawayene ya zubo daga idanunta zuwa kumatunta wanda Bama tasan suna zubowa ba.cikin shagwaba ta ɗago ta ballawa Aslam harara tana mai cewa"dama ai saida nace maka ka bari Ni na fasa,amma kaki bari,gashinan yanzu ciwo gurin yake min"Islam ta faɗa cike da shagwaba. Shafa kanta Aslam yayi tare da dan shagwabe fuska shima yace "to ai kece kika rikitani na kasa dainawar,amma bazan sake ba,am sorry kinji?ya fada yana ɗan kama kunnensa . Murguda baki Islam tayi tana turo baki. Murmushi yayi kafin yaci gaba da shafa kanta yana faɗa mata kalamai masu daɗin gaske wanda sukayi tasiri wajen sanyata daina jin zafin ruwan. Sau uku yana sauya mata ruwa saida ya tabbata ta gasu sosai,kafin ya zuba musu wanda zasu tsarkake jikinsu,sai anan kuma Islam tace bazata yi wanka dashiba,wai kunya takeji. Dariya sosai Aslam yayi kafin ya janyota cikin ruwan ya rungumeta.haka sukayi wanka tana ta nokewa suka fito da cikin toilet ɗin zuwa cikin dakin. Sai lokacin Aslam ya ga yadda zanin gadon ya ɓaci sosai da jini,dan haka daukeshi yayi tare da shimfida wani,mai ya shafawa Islam tare da sanya mata doguwar rigarsa jallabiya sannan ya kwantar da ita bayan ya bata paracetamol tasha. Zama yayi bakin gadon yana shafa kan Islam,ji yake kamar ya cinyeta dan so da ƙauna,lallai Islam yar baiwa ce ta karshe,sosai yake jin sonta na ƙara ratsa sassan jikinsa. Ita kuwa Islam barcine ya ɗauke ta . Kwan dakin ya kashe tare da gyara mata lulluɓewar jikinta, sannan ya fice bayan ya sunbaci goshinta da lips dinta. Mommy Husna kuwa cike da mamaki take bin wayar ta da kallo jin irin abinda Husna ke faɗi,ta yaya hakan zata kasance?bayan bokanta ya tabbatar mata da cewa har abada Aslam bazai iya kusantar Islam ba?yace asirin da yayi musu na musamman ne,wanda idan ma yaje da nufin kusantar ta ,zaiji tana warin jaɓa ne,amma kuma yanzu Husna tace mata wai ya kusanci islam ɗin ?kuma aranar da ta kai mata asiri na musamman? Kai gaskiya akwai matsala gagaruma. Cikin yanayi na son karin bayani Alhaji Musa Daddyn Husna ya kalli matar tasa yana mai cewa"Hajiya meke faruwa ne?naga gaba ɗaya yanayinki ya sauya?ko wani abune ya sami husnan?ya fada yana mai kallon mommyn Husna da son jin karin bayani. "Alhaji ai aiki ya lalace, domin kuwa wannan shegen yaron saida ya kusanci yarinyar nan,yanzu haka husnace ta kira tana kuka take sanar dani"mommy ta faɗa cikin damuwa sosai,dan kuwa boka ya kafa mata sharadin karta bari asamin matsala,dan duk abinda ya biyo baya ba ruwansa. Cike da damuwa Daddyn Husna ke kallon matar tasa kafin yace "dama saida na faɗa miki Gara muyi komai cikin gaggawa tun dama na hannunmu,kikace a'a, a barta taci amarcin ta,gashi yanzu abinda jinkirin ya jawo mana,shikenan komai ya lalace Hajiya ,duk wani shiri dana bata lokaci inayi ya ɓaci"daddy ya fada cikin damuwa mabayyaniya yana mai firfita da hular kansa. "Karka damu Alhaji zan koma gurin boka yau _yau ɗin nan,ba abinda zai gagara,ai basu isa suja damu ba"ta faɗa cike da yarda da kai. Husna kuwa kukanta tasha ta koshi, harsaida taji kanta na ciwo kafin ta hakura,fitowa tayi falo da nufin dubawa ko har yanzu suna dakin. Tana fitowa sukayi kiciɓis da Aslam ya fito daga ɗakinsa,kallo ɗaya tayi masa taga yadda yake wani irin sheƙi da haske kamar wani tauraro. Wani irin bakin ciki ne da kishi ya turnuƙe ta ganin irin yadda yake sakin murmushi shi kadai.ko kula da ita baiyi ba ya zauna akan kujera riƙe da laftop dinsa ya fara latsawa. Wani wawan tsaki Husna ta ja tana mai sakin wani banzan ashar " wllh dai anji kunya,kuma an fadi ba nauyi, mutum yaje ya haikewa ƙanwar bayan sa,harya buɗe baki yana tayiwa mutane ihu,wannan asaranci yayi yawa "ta faɗa cike da rashin kunya da neman magana tana jijjiga jiki. Tunda ta fara magana Aslam yayi tsam !!yana sauraronta, ba tare da ya ɗago kansa ba,shifa wllh yama manta da cewar akwai wata Husna cikin gidan nan,kuma wai matsayin matarsa sai yanzu da yaji maganarta. Ɗago da kansa yayi tare da kallon Husna,wani irin ɓacin rai ne yaji ya mamaye zuciyarsa,wai shi ta yayama ya auri wannan banzar yarinyar harta tsaya gabansa nata fada masa wadan nan maganganun haka? Husna kuwa harararsa tayi cikin rashin kunya tana mai jijjiga jiki da cewa"wllh kuma Indai ni ce Husna baku ba zaman lafiya agidan nan,kuma kaida ƙara kusantar yarinyar nan har abada mugu kawai"ta faɗa cikin bakin ciki da ɓacin rai. Afusace Aslam ya mike tare da ture laptop din daga kan cinyarsa, Allah ya taimaka ma bata fadi kasa ba,ta faɗa kan kujerar. Gadan -gadan ya tunkari hunsa,ita kuwa ko gezau batayi ba ganin ya tunkarotan. Shikuwa yana zuwa baiyi wata wata ba ya daga hannu tare da wanke kumatunta da maruka masu matuƙar zafi da shiga jiki har guda uku. Agigice Husna ta kwalla ihu tana mai neman hanyar guduwa amma Aslam ya tare hanyar. Cikin mugun ɓacin rai da tsana yake faɗin"ki kula da kalamanki,dan kuwa kinsan wanene Aslam,bana daukar rainin mazama bare ke jaka kidahuma.idan kikayi wasa dani zakisha matukar wahala banza yar tasha. Dakike batun nayi ihu,ai sai mace ta cika ake mata ihu dan ana saduwa da ita,ba irinki bushashshiyar bishiya marar ganye ba. Nayi dana sanin auren karuwa marar hankali irin ki wacce ta gama rabar da mutuncinta atiti banza fanko wacce bata da ko digon ni'imar da zata sanyaya wa mutum zuciya yar asara. "ya fada yana mai tunkudeta can gefe, ya juya tare da ɗaukar laptoo dinsa ya koma ɗakinsa. Burgima Husna keyi atsakar ɗakinta tana kuka da fadin ta shiga ukunta ta lalace.. Hmmmm Husna dama rana dubu da barawo ce rana daya tak ta mai kaya. Muje zuwa ... Anty mammynku ce Mrs babi. [12/15/2022, 4:24 PM] Abk: 93/94 ______________Birgima sosai Husna keyi cikin ɗakinta kamar wata zararriya,ba abinda take fadi sai "na shiga ukuna na lalace,Islam ta kasheni ta karya min asirin da nayiwa Aslam,shikenan ya daina sona,ya daina jin magana ta,wllh bazan yarda ba,saina dauki mataki akanki,saina ga bayanki muguwa azzaluma" Abinda Husna ke faɗi kenan tana turza ƙafarta atsakar dakin nata,wanda yayi buju-buju da kayanta masu dauda da take jefarwa ko ina. Aslam kuwa kai tsaye ya koma dakin sa,inda ya bar Islam na barci, zama yayi kan kujerar dake jikin gadon ya sanya Islam gabansa,yana aiki yana kallonta. Nan take yaji ɓacin ransa ya kau. Mommyn Islam kuwa ba ɓata lokaci ta nufi gurin boka,inda tana zuwa cikin damuwa ta fara faɗin"ran boka ya dade an sami matsala gagaruma,domin kuwa yaron nan ya kusanci matar sa ,kuma komai ya lalace,yanzu haka Husna ta kirani tana kuka,boka asan abinda za'ayi ataimaka wa yata,bana son ganinta cikin damuwa ko kaɗan"cewar mommyn Islam fuskarta ɗauke da damuwa. Wata irin dariya mai kama da kukan jaki murgujejen mutum dake zaune kan wata kujera mai tsini ya sanya,fuskarsa bakikirin ba alamun rahama atare dashi. Cikin wata kakkausar murya ya ke faɗin "kunyi ganganci,kunyi saken da bazaku sake samun damar da kuka samu abaya ba,domin yanzu komai ya lalace, Kuma mijin ƴarki,ya dawo cikin hayyacinsa,ahalin yanzu ƴarki bata da iko akan mijinta hahhhhhhhooii" yakai zancensa yana mai sakin wata hatsabibiyar dariya. Cikin tashin hankali da jin haushi , mommyn Husna tace "kaga boka karka raina min hankali mana,ya zakace komai ya lalace,bayan kace idan na yarda da kai na tsawon wata guda ba abinda zai karya asirin nan,sai yanzu zaka ce wai komai ya lalace? wllh baka is...... "Keeeeeh!!! La'ananniyar mata,ki kula da bakinki,inba haka ba,yanzun nan zaki bagunci lahira, ba saida nayi muku kashedi ba?akan karku bari ya kusanceta? tsinanninya yar wuta,zaki san niba sa'an ki bane,bani da imani ko kaɗan "boka ya fada cikin tsawar data katsewa mommyn Husna maganar da take yi. Jikinta kuwa take ya dau rawa, tsoro da fargaba suka kamata,subutar baki da ɓacin rai suka sanyata mancewa da wanene bokan,dakuma rashin imaninsa. Cikin rawar baki tace"tuba nake bokan bokaye,hatsabibi uban hatsabibai, subutar baki nayi,amma ayafe min"mommyn Husna ta fada kanta aduƙe. Cikin fusata bokan ya ƙara daka mata tsawa yana mai fadin"kinyi ganganci shaidaniya, kuma ki sani bazan yafe miki ba,daga yau albarkata ta bar gareki kije can ki ƙarara" Ya fada yana mai zare mata manyan jajayen idanunsa. Ka yafeni boka zanyi duk abinda kace nayi nidai ka taimaka min ƴata tana cikin damuwa"mommy Husna ta faɗa kamar zatayi kuka. Kallonta bokan yayi yana mai lasar lips ɗinsa kafin yace "shikenan,amma ki sani sharadin aikin nan shine,dole zaki bani kanki na tsawon sati guda domin akwai wasu ɗalasumai da zan sanya miki ajikinki,wanda idan ya shiga jikinki, aljanu zasu maida shi jikin ƴarki,dan haka idan kin amince shikenan"boka ya fada yana mai kafe mommyn Husna da idanu. "Wllh na amince boka,akayi na wata guda ma bare na sati? Ko yanzu ma kawai afara"mommyn Husna ta fada tana cire mayafi. Lasar lips boka ya karayi yana mai cewa"maza shiga ɗakin sirri,dan kuwa yanzu zamu fara aiki" Haka mommyn Husna ta shiga dakin nan ba tsoron Allah,boka ya tara mata gajiya,dan kuwa da ƙyar take daga ƙafarta, banda tsami ba abinda jikinta keyi,ga warin jikin bokan duk ya isheta. Haka ya gama budurinsa kuma ya ce taje gobe ta dawo,kuma bai bata maganin komai ba. (Wannan batan basira da rashin imani da tsoron Allah na mommy Yayi yawa,haka kawai wani ƙaton banza yayi amfani da ita da aurenta kuma babu abinda ya dameta, Allah kasa mufi karfin zuciyarmu ameen) Islam kuwa sai gab da magrib sannan ta farka daga barcin da tayi,ahankali take buɗe idonta,harta budesu tarr, Ahankali abinda ya faru dazu yake dawowa cikin kwakwalwarta,yanzu kenan itama ta zama cikakkiyar mace?shikenan sun zama abu daya ita da Aslam?kuma asirin jikinsa ya karye?lallai wannan rana dole ta sanya ta cikin kundin tarihinta, dan kuwa rana ce mai cike da tarihi agareta. Ahankali ta yunƙura ta sauko daga kan gadon,jikinta ciwo yake mata da ƙasanta, dan runtse ido tayi lokacin data taka ƙafarta aƙasa. Ahankali take takawa har zuwa toilet.wanka ta sake yi tare da gasa jikinta,aikuwa sosai taji daɗin jikin nata.mai ta shafa tare da sanya turare ajikinta. Ba kayan da zata sanya aɗakin,dan haka ta bar rigar wanka dake jikinta ta nufi ƙofar babban falon gidan,dan zuwa ɗakinta ta shirya. Cikin nutsuwa da mutuwar jiki take takawa.kallo ɗaya zakayi mata ka fahimci akwai Abinda ya faru,dabu da yadda take dan ɗingisa ƙafarta da takawa ahankali. buɗe kofarta yayi dai dai fitowar Husna daga nata dakin,idanunta sunyi jajur dasu,kana gani kasan taci kuka ta koshi. Idanunta ne suka sauka akan Islam tana tafiya ahankali da rigar wanka ajikinta,ga gashin kanta nan ajiƙe yana ɗan zubar da ruwa. Wani irin bakin ciki ne da takaici suka taso mata,batama san lokacin data ƙundumo wani wawan ashar ta maka ba.tana faɗin. "Allah ya isa na islam,kin cuceni kin lalata min rayuwa,wllh bazan barki ba saikinyi dana sanin kusantarki da aslam yayi, shegiya karuwa kawai"Husna ta fada cikin bakin ciki,jikinta har rawa yake. Juyowa Islam tayi tare da kallon Husna,sai lokacin ma ta san da ita afalon. Murmushi tayi mai cike da rainin hankali tana mai kallon Husna sama da ƙasa,kallo irin na baki da hankali, sannan tana tunanin hauka irinna Husna,ƙiri -ƙiri take nuna kishi da jin haushinta afili.lumshe ido tayi tare da yin miƙa tana wani juya jikinta,dan kashe ido ɗaya tayi tana kallon Husna,ba tare da ta maida hannunta kasa ba.cikin murya mai cike da nishaɗi tace"washhh bayana ciwo yake sosai,anya ma zan iya ƙarawa da daren nan kuwa?Please bijimar Aslam,ko kina da wani magani ne da kike amfani dashi,wajen magance gajiya kidan bani,ko kuma shawara da zata sanya indan daina jin ciwon jikin nan,dan naga alama ogan namu....ta ɗan kashe ido kafin taci gaba---ba dama ne,akwai iya riƙe wuta,wllh ya gajiyar dani sosai,kusan awa biyar ana abu daya. Hmmmm saidai naji yana ta ihu da faɗin yau yasan yayi aure wai zumata zata kashe shi,kina ganin idan na ƙara bashi ta dare anya bazamu rasashin ba kuwa?"Islam ta faɗa tana mai sauke hannunta tare da riƙe kumatunta irin alamun jimamin nan,sannan idonta akan husna,wacce take jin wani irin zafi zuciyarta sai bugawa ta keyi,cikin ɓacin rai da ƙunar zuciya tace"wllh karya kike ke ɗin banza da har Aslam zaice kin fini,me kike dashi? shegiya wacce ta girma cikin namun dawa,keda gaba ɗaya yan farauta sun gama dake, guntun dawa,karuwar daji kawai,idan har kika ce zaki raina min hankali saina murde miki wuya agurin nan kin mutu kowa ya huta, Muguwa azzaluma mai shiga tsakanin ma'aurata,saina ga bayanki wllh yar gadon karuwanci,. Husna ta fada cikin daga murya tana huci. Dariya sosai Islam ta sanya tana mai nuna husna tace "ashe Ni ƙaruwar daji ce? Lallai niɗin jaruma ce tunda iskancina da mafarauta nake ƙila ma harda aljanu da namun daji ko? Amma ina da tambaya mai dattin dan kwali, wai shin ita a ina take nata karuwanci?dan nasan ita ogarmu ce tunda saidai tayi da matsafa,waya sani ma kedin ko yar wani ƙasurgumin matsafince aka likawa malam sallau ya karba tunda an shanye shi bashi da katabus sai abinda mace tace masa"Islam ta faɗa cike da rashin damuwa tana mai kafe Husna da idanunta. Husna kuwa wani ihu tayi cikin maɗaukakin ɓacin rai tayi kan Islam bigijim bigijim.tana zuwa ta daga hannunta da nufin wankawa Islam mari, saidai kafin ta kai ga marin Islam ɗin taji saukar wasu kyawawan maruka har guda biyu akan fuskarta Islam ta zabga mata su. Ihu ta kara sanya wa tana mai dafe kumatunta tare da sauke hannunta da ta ɗaga da nufin marin Islam. "Ni kika mara ?Husna ta fada cikin ƙara ji. "An marekin,ko zaki rama ne ?cewar Islam dake dan jingina da jikin bango,dan sosai kafafunta suka gaji da tsayuwar,sai dan rawa suke. "Wllh bazan yarda ba,saina rama yau saina kasheki agidan nan,shegiya muguwa wllh saikin bar gidan nan na tsaneki"cewar husna kenan yayin da take rarumo wata wuka dake ajiye akan danning table,da alama kayan freut aka gama sha da ita.cikin hanzari tayi kan Islam tana mai daga wukar sama tana faɗin wllh saina ga bayanki,yar karama dake kiyi ta marina kamar wata ƴarki?wllh saina kasheki islam,na tsaneki bana son ganinki aduniyar nan"Husna ta fada tana mai kaiwa Islam suka aciki da wukar hannunta. Cikin wani irin zafin nama da hanzari Islam ta kauce,garin kaucewar ta buge kanta da bango wanda nan take gurin ya fashe,cike da azabar radadi ta tafe goshinta tana mai runtse idonta. "Wash" Ta furta sakamakon wani irin sarawa da taji kan nata yayi. Husna kuwa kara daga wukar tayi zata sokawa islam,kawai sai ji tayi an murde hannunta tare da kwace wuƙar kuma aka hankadata can gefe.aikuwa ta fadi timm,ta buge hannunta,ihu ta sanya tana mai kallon wanda yayi mata wannan angijewar. Idonta ne ya sauka akan fuskar Aslam,Wanda kallo ɗaya zakayi masa kasan ransa yayi mummunan ɓaci,dama ganin Islam tana barci ne,yasanya shi fita dan zabo mata waya,mai kyau da tsada,dan ya fara nuna mata irin farin cikin da yake ciki da ita.yana can amma yaji hankalinsa yayi gida,kuma gabansa sai bugawa yake,hakan yasanyashi tahowa cikin sauri. Yana zuwa ya tarar da Islam durkushe,sannan ga Husna na kokarin soka mata wuka. Baisan lokacin daya jefar da ledojin hannunsa ba yayi kanta. "Ashe baki da hankali husna?haukar taki da gaske ne?wuka zaki sokawa matata?acikin gidana?Aslam ya fada cikin wata irin razananniyar murya mai cike da bacin rai.kumatunsa har rawa suke. Ya nufi Islam dake durkushe kanta na sarawa. Dagota yayi cike da tausayawa akan fuskarsa,ahankali ta mike tsaye tare da dan jingina ajikin Aslam. Kallon goshin Islam yayi wanda ya ɗan tashi kadan, hannunsa ya sanya tare da dan taba gurin,yana mai jin kamar zai mutu dan ɓacin ran ganin ciwo ajikin Islam. Dan yamutse fuska Islam tayi,cikin shagwaba tace "zafi" Tana mai kwantar da kanta akafadar Islam. Cikin mugun tausayi Aslam yake shafa gefen fuskarta yace "am sorry pretty sannu bari na sa miki magani" Ya fada cike da tausayawa,kafin Afusace ya kalli husna,wacce tsabar bakin ciki ya hanata motsawa daga inda ta faɗin. Yace "wllh idan wani abu ya sami matata saina daureki,banza ballagar mace marar hankali"yana faɗin haka ya suri Islam kamar wata yar jaririya yayi daki da ita. Ihu Husna ta kwalla tare da kwanciya atsakar falon tana kuka kamar ana yankata. Takaici,ɓacin rai,bakin ciki sun taru sun mata kane kane cikin ranta,wannan wane irin wulaƙancine haka?Islam ta mareta,Aslam ya hankadeta kasa,kuma ya dauki Islam ɗin agabanta sun shige daki,waya sani ma ko sake kusantar Islam ɗin zaiyi?hakan data tuna yasanyata ƙara kwalla ihu kamar wata zararriya. Wanda ya sanya granny ƙarasowa cikon ɗakin da gudu ta,tana faɗin"ikon Allah kodai aljanu aka tayar agidan nan?ke Husna meye hakan wani burgizaza dake kina burgima atsakar daki?jama'a kuga wani sabon iskanci,wllh idan baki tashi ba,zagewa zanyi in gabjeki ba ruwana"granny ta faɗa cike da jin haushin yadda Husna ke wani shura kafa kamar jaririya,abin ko kyan gani babu. Cike da son huce haushi Husna tace"bazan tashi ba yar shishshigi,kiyi abinda zakiyi,tsohuwar banza gadon mugunta da tsiya" Galala granny tayi tana kallo Husna,mamaki cike aranta,tace "Husna Ni kike zagi? Granny ta faɗa tana nuna kanta. "Kedin ake zagi banza tsohuwar kilaki azzuma"Husna ta fada cike da rashin kunya.tana tashi tsaye tare da bankawa granny harara. "Ke yar nan kinsan da wa kike magana kuwa?granny ta faɗa cikin mamaki tana riƙe haɓa. "Na sani mana uwata ce ke da zan ji tsoron ki?wllh ko kifice kona zazzabga miki mafi agurin nan"Husna ta fada tana daga hannunta kamar zata mari granny,sosai take jin haushin grannyn. "Keeeeeh grannyn zaki mara? Kakata?kuma acikin gidana? lallai yau zaki bar gidan nan,kije gidanku akoya miki tarbiyya da ɗa'a . juyowa sukayi gaba dayansu dan ganin mai wannan maganar. Aslam ne ke fitowa daga dakin sa kunnensa suka jiye masa Husna na faɗin zata mafi granny,badan Yana gudun karya illata Husna ba,daba abinda zai hanashi dukanta. Kuka Husna ta sanya cike da nadama tana mai faɗin"dan Allah kayi hakuri karka ce in tafi gida,wllh subutar baki nayi,bazan sake ba " Ta faɗa tana mai hada hannayenta guri ɗaya alamun neman afuwa. Ko inda take Aslam bai kallaba, sai kama hannun granny da yayi suka nufi dakin nashi. Granny sai matsar kwalla take,ba'a taba mata rashin kunya irin na yau ba. Zaunar da ita Aslam yayi akan kujerar falonsa,yana mai share mata hawayen yace "ya ce haba matar meye na kuka kuma?kiyi hakuri zanyi maganinta ne" Cikin girgiza kai granny tace "wannan yarinyar ba yar arziki bace,wai nice tsohuwar kilaki,kuma Ni zata mara?wllh daka barni da zagewa zanyi mu doku"granny ta faɗa tana dukan taron hannunta. Murmushi yayi yana mai cewa haba dai ai nine ya kamata na dauki mataki da kaina grannyna" Haka dai yayi ta rarrashin granny yayin da islam ta fito itama suka rarrashi grannyn tare,inda take tambayar ina Islam taji ciwo,sukace bushewa tayi. Husna kuwa cikin ihun kuka ta nufi part din mommy tana kuka.. [12/16/2022, 6:36 PM] Abk: 95/96 ______________husna kuwa cikin kuka ta nufi part din mommyn Aslam.tana fadin "Wayyo mommy kizo ki taimakeni Aslam yace intafi gidan mu akoya min tarbiyya,wllh Islam ce tayi masa asiri,itace ta karyamin nawa,shine Aslam ya daina sona,ya daina jin maganata, komai sai islam,wllh na tsaneta bana sonta"abinda Husna ke faɗa kenan lokacin data shiga part din mommy,Wanda fitowar mommy kenan daga kitchen.hanan tana zaune tana duba laptop dinta. Da hanzari mommy ta ƙaraso gurin Husna tana mai riketa,ganin kamar ba acikin hayyacinta take ba yasa mommy ta zaunar da ita akan kujera tare da buƙatar hanan ta kawo mata ruwa. Mikewa hanan tayi tana mai taɓe baki,dan ita wllh kwata -kwata bata son ganin husnan nan agidansu matsayin matar Aslam.dan bata da mutunci ko kaɗan. Ruwan ta kawowa mommy cikin kofi. Karba mommyn tayi tare da mikawa Husna kofin dai-dai bakinta akan tasha ko zata sami nutsuwa. Amma saboda tsabar iskanci irinna Husna ta sanya hannu ta kaɓar da ruwan har saida ya jiƙa mommy. Tana faɗin"niba shan ruwane ya kawoni ba kiyiwa Aslam magana yace intafi gidan mu,wllh kuma Ni bazan tafiba, dan kuwa waccan Shegiyar Islam ɗin ita ta sanya shi,asiri tayi masa,kuma wllh ƙarya take daga ita har wanda suke taimaka mata,bokana yafi nasu ƙarfi"Husna ta fada cike da rashin hankali da sanin me take cewa. Galala mommy tayi tana kallo da sauraron abinda Husna ke faɗi,wato kenan asiri suke yiwa Aslam?shine take zargin Islam ma asirin tayi masa,lallai tayi sake wajen nemawa danta tsari,dole kuwa yanzu ta mike da yi masa addu'a akan mugayen mutane irin su husna. "Kee Malama meye hakan ko bakya ganine?dubi yadda kika jika mata jiki da ruwa kuma da gangan kikayi hakan"hanan ta faɗa cike da jin haushin Husna. Afusace Husna ta juyo kan hanan,tana faɗin"dan uwarki an zuba mata ruwan,ko zaki rama mata ne?marar kunya fitsararriya wllh idan kika ƙara shiga sabgata saina illataki"Husna ta fada cikin huci da masifa. Buɗe baki kawai mommy tayi tana kallon husna,duk da tasan rashin kunya irin na Husna ,amma bata taɓa tsammanin zata iya zagin hanan agabanta ba. Hanan kuwa cike da jin haushin zagin da Husna tayi mata, itama ta zaburo tace "wllh badai uwata ba,saidai taki,kuma wllh idan kika ƙara zagin uwata saikin gane kuren ki ban..... "Ke hanan meye hakan?baki da kunya ne?agabana kike yiwa matar yayanki rashin kunya? tarbiyya dana baki kenan?"mommy ta faɗa cikin haɗe rai da yiwa hanan gargadi. "Amma mommy kina jin abinda take fadamin itama?zagina fa take dan kawai nayi mata magana akan abinda tayi"hanan ta faɗa kamar zatayi kuka. "To ki kyale ta mana ko ke ta jiƙa?ban son rashin kunya hanan" "Ai gara ki barta ta nuna min rashin tarbiyyar tata afili,yo idan batayi haka ba, ai bazan san yar gadon rashin tarbiyya bace, kuma wllh dai -dai nake da kowane dan iska agidan nan"cewar husna kenan cike da rashin da'a da tarbiyya tana hararar hanan. Cike da fara gajiya da irin yadda take yadawa mommy magana ta rashin kunya,mommy tace "Husna !ya kamata ki iya bakinki,kisan ne Yakamata ki fada, dan kuwa kome kike ce akan hanan,to damu kike"mommy takai zancenta tana kallon Husna da ɗan ɓacin rai akan fuskarta. Husna kuwa taɓe baki tayi cikin gatsali da raini tace "ita yar taki bakijin abinda take fadamin ne?wllh ba wanda ya isa ya hanani maida martani akan duk abinda akayi min,dan kuwa nima yace kamar kowa,mutane ba abinda suka sani sai son kai da mugunta"Husna ta fada tana mai yatsina fuska da murguda baki. Aikuwa amugun zafafe hanan tayi akan husna tana huci tare da faɗin"wllh baki isa kiyiwa uwata rashin kunya agabana ba,kedin banza baki isaba wllh"hanan ta faɗa cikeda masifar dataji ta taso mata yanzun nan. Saidai kafin ta kai ga Husna mommy ta tare ta. "Meye hakan ne hanan,baki jin magana ko?ki barta ai duk wanda ya raina iyayen wani,to nashi ya raina,kuma kowa yayi na gari,kansa" "Kidai iya bakinki,karki sake ki zagi iyayena wllh,kuma Ni ban raina iyayena ba,can dai wannan Shegiyar yar taki, itace ta rainaku badai niba,kuji muguwar mata mai son kai, haka kawai kisani gaba kina ta yimin baki,uwata ce ke? A'a wllh banaso dan kuwa wllh niba...... Kau! Kau!! Kau!!! Husna taji saukar wasu zafafan maruka, masu matuƙar zafi da radaɗin daya haddasa mata daukewar ji da gani,na wani lokacin. Wani gigitaccen ihu Husna ta kwalla,wanda bata gama fitar da ihun ba taji saukar belt ta ko ina ajikinta, ihu Husna keyi tana ƙoƙarin tashi daga faduwar datayi sakamakon marin da tasha,saidai ta kasa tashi, gaba ɗaya ta gigice ta rasa ina zata sanya kanta.dan ba tasan ma ta ina dukan yake sauka ba, jinsa kawai take from no whare. Da sauri mommy ta riƙe belt din da ake zabgawa Husna,cikin ɓacin rai tace "meye hakan kake yi ?agabana kake dukan yar mutane kamar ka samu jaka? Wannan wane irin hali ne ka daukarwa kanka, agabana fa"mommy ta faɗa cikin ɓacin rai sosai. Cikin zafin zuciya da mugun bacin rai marar misaltuwa,Aslam Wanda suka taho domin rako granny part din mommy,shida Islam,Dan ta dage ne saita zo itama shiyasa ya taho tare da ita, kuma tuni granny ta fahimci abinda ya faru da Islam,dan ta kula da yadda take tafiya ahankali kamar yar kaciya, duk da ta gasa jikinta sosai. Haka granny ta sake bata kulawa ta musamman irin tasu ta tsofi, tayi murna sosai da farin ciki,tare da fatan Allah ya basu zuri'a dayyiba. Zuwansu kenan falon cike da farin ciki suke tafe yana riƙe da hannun Islam,granny tana ta masa tsiyar bashi da kunya, kuma tana masa gargaɗin wllh ya bar mata jika ta huta. Kawai kunnensa ya jiye masa yadda Husna ke zazzagawa mahaifiyarsa rashin kunya kamar sa'arta. Baisan lokacin daya saki hannun Islam ɗin ba ya shiga falon da mugun sauri ya fara mata da maruka masu kyau,kafin ya zaro belt ɗinsa ya Dora dashi. Huci kawai yake yana kallon Husna,ji yake aduniya ba wanda ya tsana sama da husna,zai iya jure zama da ita koda baya sonta,amma bazai taba daukar cin mutunci ga mahaifiyarsa ko ahalinsa ba. Kuka sosai Husna keyi tana mai sosa jikinta, sai lokacin hankalinta ya dawo jikinta,kallon Aslam tayi cikin kuka ta fara magana"wllh bazan yarda ba, akan wannan matar mai son kai zaka dakeni ?baka daki banza ba,mugu azzalumi,dan kawai ana sonka shine zakayi ta dukan mutane ?wllh zaka san ka dokeni kuma agaban wannan tsinanniyar matar taka dangin tsiya masu asiri,ke kuma ki jira kiga abinda zai biyo baya,wllh saikinyi dana sani.." Zabura Aslam yayi cikin zafin nama zai kara yowa kanta mommy tayi saurin rikeshi tana tace"Aslam fice daga falon nan tun kafin raina ya ɓaci"ta faɗa tana mai tsare shi da idanunta ba alamun wasa. Cike da ɓacin rai Aslam ya kalli husna yace na tsaneki,nayi dana sanin auren ki,kuma kije gidanku na datse igiyar aurena daya akanki. Yana fadin Haka yayi waje, ko kaɗan bai so mommy ta hanashi sake gyarawa Husna zama ba,dan yaga bata saituba har yanzu. Ganin yadda ya fita afusace, yasan ya Islam binsa da sauri tana ɗan ɗingisa ƙafarta. Ihu Husna ta sanya tana ɗora hannunta aka"wayyo Allah na,na shiga uku ya sakeni Shegiyar kuma ta bishi, na shiga ukuna, wllh bazan barki ki huta ba Islam,sainaga bayanki tsinanniyar yarinya dangin tsiya" "Keee yarinya ki iya bakinki fa, dan nan ba sa'anki, mune tsiyar kome kike nufi? Ai yayi daidai daya sakekin, marar kunya kawai, kuma ba abinda kika isa kiyiwa jikata wllh,Allah yafi karfin ku idan juninki asiri,wllh sai yanzu nake jin takaicin auroki da Aslam yayi,abu ba fasali ba komai,kalleki sai tsabar rashin kunya,wllh ba wani abu bane agurina in zage mu danbatu dake mu raba raini marar tarbiyya kawai. Cewar granny kenan tana cin damara da ɗan kwalinta. Kallon bata taki na ke ba Husna tayiwa granny kafin ta miƙe tsaye ta riƙe ƙugu"bani da lokacin ki yanzu tsohuwar duniya, ki jira in gama da jikar taki,kema zan dawo kanki,ba ke kadai ba ma,da duk masu son yimin shishshigi arayuwata. Wllh duk saina ɗauki mataki akanku" tana gama faɗin haka tayi hanyar fita daga falon tiɓi -tiɓi. "Aikuwa wllh barin gidan nan zakiyi tunda ya rabu dake, marar kunya mai siffar jakin dawa,wllh ban taba ganin fitsararriya yarinya irinki marar da'a ba"faɗa sosai granny keyi tana ba mommy labarin irin rashin albarkar da Husna tayi mata. Hakuri mommy tayi ta ba granny tare da rarrashinta akan tayi shiru,dole ayiwa tubkar hanci.dan bataso Aslam yayi saurin furta sakin ba. Islam kuwa cikin daki ta tarar da Aslam Yana kwance akan gado ya ɗora hannunsa akan goshinsa,inda idanunsa ke rufe.amma kallo ɗaya zakayi masa kasan ransa amatukar bace yake. Ahankali Islam ta karasa cikin dakin, bakin gadon taje ta tsaya tana kallonsa tayi shiru ba tare da tace komai ba. Buɗe idonsa yayi wanda suka kada sukayi jajur tsabar ɓacin rai, kallonta yake shima,tana tsaye kamar an dasata . Mika mata hannu yayi alamun tazo gareshi. Cikin sanyin jiki Islam ta kama hannun nashi tare da hawa kan gadon,akan faffaɗan ƙirjinsa yayi mata masauki tare da rungumeta tsam-tsam kamar wani zai kwace masa ita. Ajiyar zuciya yake saukewa kamar wanda yasha kuka ya ƙoshi, sosai yake jin zuciyarsa tanayin sanyi daga suyar da take masa. Islam kuwa tayi lamo akan ƙirjin nashi tana sauraron yadda zuciyarsa ke bugawa da sauri da sauri. Hannunta ta sanya tare da balle maballin gaban rigarsa, kwantaccen yalwataccen gashin ƙirjin nashi ya bayyana,cikin nutsuwa da ɗan rawar hannu ta cusa hannun nata cikin ƙirjin nashi,ahankali ta fara shafa saitin zuciyar tasa cikin salo da hikima. Tuni Aslam ya fara lumshe idanunsa,dan ji yayi kamar waiwayi take masa tare da zuba masa ruwan sanyi. Cike da so da kauna Aslam ke shafa bayan Islam,yana jin wata irin muguwar kauna da sha'awarta na motsa masa.amma sanin ba dadi take jiba yasashi danne sha'awarsa tare da kara kankameta ajikinsa. Ahankali ya furta "ina sonki Islam,kece farin cikina,maganin damuwa da ɓacin raina,kici gaba da kula da ni,ki kasance kusa dani akoda yaushe,ina sonki islam" ya fada cikin wata irin murya mai cike da shauki. Wani irin sanyi zuciyar Islam tayi,soyayyar Aslam na ratsa dukkan sassan jikinta,ji take bazata iya rayuwa ba Aslam ba.cikin shaukin so da kauna tace "nima ina sonka mijina,zan kasance dakai har karshen rayuwata". Ta faɗa tana mai kara shigewa jikinsa sosai. Dadi da farin ciki ne suka baibaiye zuciyar Aslam.da sauri yace "da gaske kina sona kema ? Ya fada cike da zumuɗi. Jinjina kai Islam tayi tare da cewa"fiye da yadda kake sona" "Alhamdullah na gode wa Ubangiji domin ya gama min komai arayuwata,ina sonki Islam "Aslam ya fada yana kissing din Islam ta ko ina. Sabuwar wayar daya siyo mata ya dauko tare da saita mata komai ya bata. Murna sosai Islam tayi tare da yi masa godiya.nan dai suka buge da soyewarsu. I Husna kuwa tana fita daga falon mommy, kai tsaye motar ta tashige ta figeta aguje.gidansu ta nufa tana zuwa ko kashe motar batayi ba ta nufi falon nasu tana kuka. Iyayen ta gaba ɗaya suna zaune afalo,suna kitsa yadda surkulle su zai kasance, Da kuka Husna ta fado musu cikin Falon tana faɗin "wayyo Allah na mommy wllh ya daina sona,dukan tsiya yayi min da belt bayan ya zabzabga min maruka.wllh bazan yarda ba ku daukar min mataki akan wannan dukan,kuma bazan bar mata shiba,asiri tayi masa"Husna ta fada tana mai fadawa kan mommynta. Hankalinsu ba karamin tashi yayi ba,ganin shatin belt ajikin Husna,nan da nan suka harzuka mahaifin Husna yace bazai yarda ba,dan koshi bai taba dukan yarsa ba bare wani aslam, Nan take suka tashi gaba dayansu suka nufi gidan su Aslam... To fa!!! Ko wace wainar za'a toya? Oho ? Muje zuwa . Mrs babi ce. [12/23/2022, 8:11 AM] Abk: 97/98 _____________Hankalin iyayen Husna ba karamin tashi yayi ba ,sakamakon ganin shatin belt da sukayi ajikinta,wanda koda wasa su basu taba koda yi mata tsawa ba bare duka. Yau kuma gashi wani da sunan mijinta yayi mata duka harda belt,lallai bazasu yarda ba,dole su dauki mataki mai kwari akan wannan al'amarin. Cikin zafin rai da matukar jin haushi,mahaifin Husna ke faɗin"Ni Alhaji kabeer zaiyiwa haka?Ni ɗansa zai yiwa yata irin wannan dukan kamar ya sami jaka?to wllh bazan laminta ba,shi baisan darajar wannan yarinyar yake ciba,shiyasa har yanzu yake raye? To lokaci yayi da zan aiwatar da ƙudurina akansa,wanda na daga masa ƙafa ada, tun lokacin daya sami damar tsallake tarko na farko,amma yanzu ninasan mai zanyi akan al'amarin nan"Daddyn Husna ya kai ayar zancensa cikin huci. Mommy dake shafa kan husna cikin damuwa da sigar rarrashi,ce ta ɗago ta maida kallonta kan mijin nata,hakika ranta itama yayi mugun ɓaci,kuma wllh bazata yarda da wannan wulaƙancin ba,saboda Aslam Yana auren yar uwarsa,shine Hajiya A'isha ta zuba masa ido yana wulakanta mata ɗiyarta tilo kamar rai. "Ai wllh idan ma kai baka dauki mataki ba,to Ni nan zan dauka,dan ban haifa musu yar dansuyi ta duka ba,akan me?kwanaki ma marinta yayi sai kace jakarsa? Maza ki share hawayenki yanzun nan zamu je dan daukan mataki akan wannan zaluncin meye ma abinda ya jawo dukan ?"mommyn husna ta faɗa tana sharewa Husna hawayen dake zuba a idonta. Ita kuwa sai wani kuka take tana narkewa jikin uwar kamar wata sakara. "Mommy akan wannan tsohuwar matar ta gidan fa da matarsa ya dakeni, dan kawai tamin shishshigi nayi mata magana,shine naje na fadawa uwarsa itama take min baki,nikuwa na gaggaya mata magana kawai sai jin saukar duka nayi ta ko ina" Husna ta faɗa tana mai kallon uwar tata. "Yo ai kinyi min dai-dai, nice nan na saki ,duk wanda ya kawo miki wargi ki nuna masa kurensa,idan ba lalacewa ba ma kina suruka kike yiwa matar danki katsalandan, da shishshigi kuma dan tayi magana kike mata baki? Shegiyar mata,ai duk tana haka ne dan tana duniyar,idan ta barta kinga shikenan kowa ya huta"cewar mommyn Husna tana miƙar da husnan tsaye. Daddyn Husna kuwa tuni yayi waje dan fito da motarsa. Haka suka dunguma zuwa gidan gaba dayansu, har uban,saboda rashin hankali,maimakon suyi bincike mai kwari kafin su san matakin dauka,kawai suka biyewa diyarsu. Lokacin da suka je tuni anshiga sallah,dan haka kowa na gidan yana Sallah,aikuwa neman guri sukayi suka zauna a babban falon suna ta yada magana har alhajin kamar wata mace shima. Mommy ce ta fara fitowa daga ɗakinta,da sauri ta ta ƙaraso tana faɗin sannunku da zuwa hajiya,Alhaji kune da magaribar nan?sannunku "ta faɗa fuskarta ɗauke da murmushi. Wani banzan kallo suke bin mommy dashi,inda mommyn Husna tace "dole kice haka mana,saboda bakiyi tsammanin Husna na da gatan da za'a bi mata hakkinta awannan lokacin ba, wllh kin bani mamaki Hajiya A'isha,ace kina gani wancan gantalallen dan naki, ya kama min ya yayi ta jibga kamar ya sami baiwa, sannan ya dunguma mata saki ,amma kika ƙyale shi ko ajikinki,saboda bakin hali da mugunta dan ba ƴarki akayiwa hakan ba ko?to wllh bazan yarda ba,ƙara zamu kai dole abi mata hakkin dukanta da kuma na sakin da yayi mata ehe"mommyn Husna ta faɗa cikin masifa tana zazzare ido kamar mujiya. Shikuwa Daddyn Husna sai wani gyada kai yake yana hura hanci,saida matar ta kai kare maganarta shima ya dora da nashi yana cewa "to in banda zalunci ma,husnan nawa take?da za'a sanya mata karfi wajen duka kamar wanda na kawo muku baiwa, sannan daga ke har mijinki kunyi shiru baku ce komai ba, to mukam bazamu yarda ba,dan kuwa Shari'a zamuyi daku" Daddyn Husna ya fada da ɗan daga murya yana wani baza malum malum kamar na Allah. Mommy kuwa saroro tayi tana kallon ikon Allah gurin waɗan nan mutanen,ita tayi tunanin sunzo ne dan asasanta,ashe ba hakan take ba, bamamaki kuwa bai barta tace komai ba,sai kallonsu da take ɗaya bayan daya.tana kuma jinjina rashin dattako da hankali irin nasu. Cikin sanyin murya da son kwantar musu da hankali,duk da taji zafin maganganun su,akan danta tace"ayya Alhaji da Hajiya,kuyi hakuri,tabbas anyi muku ba dai-dai ba, amma ina mai baku hakuri kuma yanzu haka jiran dawowar Alhaji nake,koda baku zo ba mu zamu zo har gida mu baku hakuri sannan shima Aslam zai zo ya baku hakuri,Husna ai tamkar ya take awajenmu,ba ta yadda za'ayi mu cutar da ita da gangan,ko mu bari ta cutu kuma muna kallo. Yaran zamani ne sai haƙuri,ka haifi da ne baka haifi halinsa ba,amma ita husnan ai tana ji da ganin yadda na nuna masa ɓacin raina akan abinda yayi Kum... "A'a wllh Ni karya kike min,banji ba kuma banga lokacin da kike nuna masa ɓacin ran naki ba,hasali ma ba kece kika haddasa komai ba?koba ke kika ja ya sake niba?"Husna ta tari numfashin mommy ta hanyar katse mata zancen da take cikin daga murya da rashin kunya. Shiru kawai mommy tayi tana kallon Husna,zuciyarta na tafarfasa,amma tana ta kokarin danne ɓacin ranta,dan tana bukatar zaman lafiya ne. "Yanzu Husna nike miki karyar? Mommy ta faɗa cikin sanyin murya. Cikin rashin kunya Husna tace "Ba ƙaryar kikayi ba?ko za'a hanani fadane?" Ta faɗa tana murguda baki. "A to za'a hana yarinya fadar gaskiya ne?idan ba karyar kikayi ba,ai bazata fada ba"cewar Daddyn Husna kenan yana zare ido. Sosai mommy take mamakin rashin kunyar Husna ,da kuma yadda iyayenta ke goya mata baya,gaskiya Sai yanzu tasan Aslam baiyi dacen mace ba.sam ba yar gidan mutunci bace,kuma kome tayi gado ne. "Wai hayaniyar me nake jiyowa ne tun ɗazu ina salla?wane karnukan ne suka shigo mana gida da magaribar farin nan?"granny ke faɗin wannan maganar,dan kuwa tana iya jiyo sautin muryoyinsu tana cikin ɗakinta,dan haka tana idar da sallar ta fito,idonta ne ya sauka akan husna dake wani yamutse fuska tana harare harare,tace "au! wannan marar kunyar ce?me ya dawo dake cikin gidan nan?ko kin dawo ne ki sake zage mu tas,kamar yadda kikayi dazu?to wllh ki shiga taitaiyinki,dan kuwa yanzu idan kika min rashin kunya,wllh jikinki ne ,zai gaya miki,marar tarbiyya kawai"granny ta faɗa cikin masifa da jin haushin da tsanar husnan. "Eh lallai kuwa,Alhaji gadai gani agaban idonmu ma kenan, ina ga bayan idonmu,ka duba dai wannan mata tsofai tsofai amma kaji abinda take fadawa yar cikinta,wllh girma dai ya faɗi" "Haba Hajiya ya kamata aringa sanin abinda za'a fada,koba komai agirmama furfurar mana" Gaba dayansu juyawa sukayi dan ganin mai maganar.ba kowa bane face Aman, Wanda shigowarsa kenan yaji mommyn husna na faɗin waɗan nan kalaman ga granny. Baya garin kusan wata guda kenan yana kaduna,sai yau ya dawo gida. "To rashin kunya zakayi min kenan?marar tarbiyya to kasani dai dai nake da kai duk wani salon rashin kunyar ka,kasani tawa ta wuce nan"mommy Husna ta faɗa tana wani zaburowa kamar zata daki Aman. "Ba rashin kunya zanyi miki ba,domin ba'ayi min wannan tarbiyyar ba,saidai ki sani bazan taɓa zuba ido ina kallon ki kina cin mutuncin ahalina ba,wllh sai inda karfina ya kare"Aman ya fada cike da haɗe fuska,dan ya fuskanci rashin mutunci mommyn Husna ke ƙoƙarin aikatawa. "To muzuba Ni da kai,shege ka fasa dan halal sai yanka,wllh ko uwarka bata isheni ba, bare kai karan kada miya"cewar mommyn husna tana huci. "Ba ita zakayiwa rashin kunya ba,Ni Yakamata kayiwa,tunda Ni na mijine nine zamu iya zagewa mu daku dakai,dan kuwa wllh nafika tashanci" Daddyn Husna ne ya zo gaban Aman yana faɗin wanann maganganun,kamar wanda ya sami sa'ansa yake faɗa dashi. Cikin ɓacin rai aman yace "wai mommy me waɗan nan mutanen sukeyi agidan nan ne?dan me zasu zo su tada mana hankali ? Mommy su fita dan kuwa raina ya fara ɓaci,komai na iya faruwa tunda gaba dayansu basu san girma ba" "Aman ya isa kayi shiru kawai karka sake cewa komai"mommy ta faɗa tana mai riƙe hannun Aman, Dan taga ransa yayi mugun ɓaci,kuma komai na iya faruwa,dan aman yana da hakuri sosai,saidai bai iya zuciya ba,idan ransa ya ɓaci, har yafi Aslam faɗa. "Dan me zakice yayi shiru?so kike ya zuba musu ido suna ci mana mutunci agabansa ya kasa daukar fansa?wllh bazai yiwuba, dan Ni ahalina ba asararre ko kaɗan,nina baka dama Amanu idan suka ce kule,kace musu casss-cararassss! ehe"granny ta faɗa tana tafa hannaye,tare da riƙe ƙugu. Wasa wasa kirici su mommyn Husna ke son tayarwa acigidan surukan na yarsu,Dan kuwa cire malum malum Daddyn Husna yayi,wai zasu danbatu da Aman. Hanan ce ta dauki wayarta ta kira daddynsu ta sanar dashi halin da ake ciki,inda yace gashinan zuwa yanzun nan. Hankali tashe yayo gida dan ganin abinda ke faruwa. Tana gama waya da daddynsu ta kira ya Aslam tace yazo gida ga iyayen Husna sunzo sai rashin mutunci suke. Aikuwa cikin matsanancin fushi da ɓacin rai Aslam yayi gida,dan dama kira ya samu daga store dinsa na gaggawa,shine ya fita. Duk wannan hatsaniya da ake yi cikin Falon mommy Sam Islam bata san wainar da ake toyawa ba,domin tana can bangaren su tare da malaminta,wanda zuwansa kenan ta bashi wannan tarkacen asirin nasu Husna. Karba yayi tare da kallon tarkacen yana jinjina kai.kusan minti biyu kafin ya ɗago ya kalli Islam,yace "Islam ki godewa Allah daya baki kariya,amma wannan abun da aka kulla muku ba ƙaramin sihiri bane da zai farraƙa tsakanin ki da Aslam. Ina son kici gaba da amfani da wannan maganin dana baki,sannan ki yawaita addua da neman tsari, Allah zai kare ki da mijinki.ungo wannan kirinka shafawa ajikinki,bayan kinyi alwala,domin ahalin yanzu kishiyarki da mahaifanta zasu tashi tsaye sosai wajen ganin bayanki,dan kuwa abinda ya faru dazu yayi matuƙar kona musu rai,kuma ke suke ɗorawa laifin"malamin Islam ya fada yana mai mika mata wata yar tasa fara mai shegen kyau da sheƙi,banda ƙamshi ba abinda tasar keyi. Duk da tasancewar malamin nata ba mutum bane,amma tayi mamakin yadda yasan abinda ya faru dazu.dan haka cike da ɗan mamaki tace "malamina,ya akayi kasan abinda ya faru dazu?alhalin baka zo gidan ba lokacin da abin ya faru?" Islam ta faɗa tana ɗan gyara zaman ta. Murmushi malamin na Islam yayi kafin yace "Islam Allah yana sanar damu abubuwa da dama,wanda ku baku sani ba,Ni rauhani ne kuma basarake,inada ƙarfin fikira sosai atare dani, ba wannan bama, nan da wani dan lokaci kaɗan wani al'amari zai faru mai girma na ban mamaki, kiyi ƙoƙarin hada mahaifin ki da mahaifin kishiyarki su hadu ido da ido.bayan haka Husna da iyayen ta suna cikin gidan nan ahalin yanzu"malamin Islam ya fada yana ɗan murmushi. Jinjina kai Islam tayi cike da tunanuka iri iri,meyasa zata hada iyayen nasu ido da ido?meye alaƙar Abban ta da mahaifin Husna? Dagowa tayi dan tambayar malamin nata,shikuwa cikin hanzari ya daga mata hannu yana murmushi kamar kullum. "Kada ki tambaye Ni komai Islam,keda kanki zakiga komai,zaki samu amsar tambayar ki duk lokacin da kika hada mahaifanku guri ɗaya"yana fadin haka yayi mata murmushi tare da yin kalmar shahada ya zama farin hayaki ya bace. Jimm Islam tayi azaune kafin ta ajiye tasar ta nufi part din mommy.inda tana fitowa suka hadu da Aslam Yana koƙarin shiga falon mommy.Tsabar yadda ransa yake ɓace,kallon Islam kawai yayi ya wuce cikin falon, ba tare da yayi mata magana ba. Bin bayansa tayi tana tunanin meye ya bata masa rai haka? Kusan tare suka shiga falon,dan basu da wani nisa da juna . Daidai lokacin da Aslam ya tura ƙofar falon.idonsa ya sauka akan husna,wacce ke zazzagawa mommynsa rashin kunya tana faɗin"wllh ko kina so ko bakya so saina koma dakina,dan ba wanda ya isa ya rabani da mijina, tsabar mugunta ke taki yar tana can agidanta ,shine ni kika kashemin nawa auren,wllh ki sani kamar yadda kika sa aka sakeni kema sai nayi silar da zaki bar gidan nan kuma..... Wani irin yunkuri Aman yayi cikin zafin nama da mugun bacin rai,ya fizge rikon da mommy tayiwa hannunsa,ya tunkari Husna gadan -gadan. Saidai kafin ya karasa inda husnan take ,sai ihunta kawai suka jiyo,gaba ɗaya hankalinsu yayi kanta,dan ganin abinda ya sanyata ihun nan. Islam suka gani ta maƙure Husna ajikin bango,ta shaƙe mata wuya da hannunta daya,yayinda dayan hannun kuma take dukan bakin husnan dashi. Aslam ma cikin zafin nama da ɓacin rai ya ƙaraso cikin Falon,dan tuni Islam ta rigashi shigo lokacin da taji abinda Husna ke fadawa mommy.... Kuyi hakurin jina da kukayi shiru kwana biyu,abubuwa da dama sun faru dani,amma alhamdullah yanzu komai ya dai daita. Ina fatan zakuyi min afuwa🙏🙏🙏 Luv You all guys 💞 Mrs babi ce [12/23/2022, 9:05 PM] Abk: 99/100 ______________Aslam ma cikin zafin nama da ɓacin rai ya tunkari Husna,saidai ganin yadda Islam ke wassafa ta yasashi tsayawa tare da harɗe hannayensa aƙirji. Kallonsu kawai yake yana jin Islam na ƙara burgeshi sosai,sannan yana jin tsanar Husna na mamaye zuciyarsa . "Ashe rashin mutuncin naki ya kai kina zagin Mommy?kinyi ƙarya wllh saidai idan bana gurin,amma baki isa ki zagi babba agabana ba,wllh dole na koya miki hankali, Ni rainon dawa ce,bana daukar rainin yan iska irin ki"islam ta fada cikin huci. Ita kuwa Husna sai zare ido take tana kawar da kanta daga bugun da bakinta kesha wajen Islam. Ihu mommyn Husna ta kwalla tare da tunkude Islam da iya karfinta. Wanda hakan ya sanya Islam ɗin faduwa tare da buge hannunta jikin kujera. Da ƙarfi ta runtse idonta,ɗan jin yadda hannunta ya bugu sosai,ga wani radadi daya ziyarci hannun nata. Da sauri Aslam ya dagata tare da kamo hannunta wanda ta bugu ajikinsa. "Sannu bakiji ciwo ba sai ko?kinsan idan akace mutun ya ci kai ,to zai iya komai ma"saidai..ya fada tare da dan ja mata hannun . Ɗago kai yayi tare da zuba idanunsa akan mommyn Husna wacce ta tallafi husnan dake kuka bilhakki,ga gefen bakinta afashe. "Na shiga uku mommy ta fasamin baki,wllh bazan yarda ba saita biyani bakina shegiya mai ƙarfi kamar doki"Husna ta faɗa cikin kuka da asaranci. "Banza ƙatuwar wofi yanzu Husna ki tsaya wannan yar yarinyar da haihuwar kaji kin haife ta,tayi ta mazge miki baki?Kamar ta samu giginya?wllh kinbani haushi "mahaifin Husna ke faɗin wannan maganar cike da jin haushin yadda yarinya karama ta kama Husna tana lodarta kuma agabansu,sannan ita ta kasa koda yunkurin kwatar kanta ne. "To dazaka ce ta baka haushi,baka ganin shigar sauri tayi mata?wannan abun dama shiryayye ne,an shirya hakan tun kafin zuwanmu,amma wannan Shegiyar ta isa ta daki Husna koda wasa ma bare har taji mata ciwo"mommyn Husna ta faɗa itama cike da jin haushin mijin nata,na bayar da yar tasu da yayi gaban maƙiya,dan ita ta jima da sanin cewar husna bata da ƙarfi ko kaɗan sai tsabar kuri. "Hehehehe Islam kinyimin dai dai wllh haka ake son dan halak, idan yaji ana cin zarafin iyayensa sai inda karfin sa ya kare,ku kuma maza-maza ku bar gidan nan,tun kafin. Mu naɗa muku na jaki wallhi" granny ta faɗa tana wani dunƙule hannu kamar yar dambe. "Wllh ba inda zamuje sai yan sanda sunzo sun kama mana ku,dan kuwa kun cutar damu,dole hukuma ta dau mataki,maza Alhaji ka kira yan sanda,ka sanar dasu cewar ga wasu ahali suna kokarin kashemu"mommyn Husna ta faɗa tana mai bashi umarni. Aikuwa cike da bin umarnin nata ya dauko waya yana kiran yan sandan. Ran mommy sosai ya ɓaci da irin wannan tozarcin da suke ƙoƙarin yi musu.kallon mommyn Husna tayi tana mai cewa"yanzu Hajiya yan sanda zaki kira mana?da mutuncin mu da komai?" "Kwarai kuwa dole yan sanda suka ma ku wllh,dan bazaku ci banza ba mugayen mutane kawai. Cikin ɓacin rai Aslam yace"Please mommy ki barsu,su kira sojoji ma ba yan sanda ba,ai ita hukuma ba mahaukaciya bace, da tunani suke aikinsu,ba cikin jahilci ba"ya fada yana mai kawar da kansa ransa abace. "To takadari,marar kunya da tarbiyya,muna matsayin surukan ka kake neman zagin mu ko? Saboda baka san da'a ba,sannan ina son sanin dalilin sakin da kayiwa yarmu yanzun nan" mommyn Husna ta faɗa cikin gadara da isa. Wani banzan kallo Aslam ya watsa mata,kafin yace "saboda bana sonta,bana ƙaunar ta,sannan bata da tarbiyya,bayan haka awancan lokaci saki daya nayi mata ko?ya fada yana mai dage gira guda daya kafin ya kalli husna wacce ta yi galala tana kallon Aslam din cike da fargaba.kafin ya dora da cewa" to kisani Ni Aslam na datse sauran igiya guda biyu ta aure dake tsakanani da ƴarki ,daga yau ba wata alaƙa ta aure atsakina da ita" Aslam ya fada kai tsaye yana mai kallon cikin idon mommyn husna,wanda itama tayi saƙare tana kallon Aslam ɗin,mamaki,al'ajabi da kuma dana sanin faɗin maganar da tayi,sun dabaibaye mata zuciya. Husna kuwa wani wawan ihu ta kwalla wanda yayi silar da daddynta ya shigo cikin Falon da gudunsa,dan yana waje yana yiwa yan sanda kwatancen gidan,kasancewar gidansu Aslam ba boyayyen bane yasa yan sandan suka gane cikin sauƙi. "Meya faru kuma?sake dukanta akayi ko me?"mahaifin Husna ya fada yana mai zare ido. "Wayyo Allah na,na shiga ukuna ,daddy ya sake sakina saki uku kenan wayyo rayuwata na shiga ukuna Ni husna,mommy kin cuceni kin lalata min rayuwa, kin rabani da mijina,meyasa kika faɗa masa wannan maganar ?gashinan ya sake sakina, wllh bazan yarda ba ,ba inda zani bazan rabu da shiba,wayyo Allah daddyna" Husna ta faɗa cikin kuka mai sauti tana yarfe hannu. "Ahayye nanaye !!!Allah na gode maka,Asalamu ka cika ɗa, yau ka nunawa tsagerun nan kana son iyayenka.wllh kayi dai-dai,Allah yayi maka albarka. Maza afitar mana daga gida gayyar tsiya"granny ta fada cikin nishadi da annashuwa. Hanan ma ba karamin dadin wannan sakin taji ba,shikenan sun yarda kwallon mangwaro sun huta da ƙuda. Aman ma sosai yaji yayan nashi ya burgeshi,dan sai jinjina kai yake yana murmushi. Islam kuwa kallon Aslam tayi da ɗan marairaita afuskarta,shikuwa ya ɗan lumshe mata ido alamun rarrashi. Kafin kowa ya ƙara cewa wani abu,saiga jiniyar motar yan sanda yuyuyuyu!ta shigo farfajiyar gidan. Wanda shigowar motar yayi dai -dai da shigowar motar daddy,ko farking baiyi ba motar Abban Islam ta Kunno Kai cikin gidan. Cike da mamaki daddy ya fito daga motarsa yana tambayar yan sandan lafiya?cikin girmamawa sukayi masa bayanin ankirasu ne akan ana ƙoƙarin yin kisan kai agidansa, dan haka suka taho da gaggawa,kuma idan ba damuwa suna son shiga dan ganin abinda ke faruwa. Ajiyar zuciya daddy Yayi,dan yasan komai,tunda ya kira hanan tayi masa bayani,saboda kasa daurewa yayi,gashi ya hadu da tsaiko akan hanyarsa ta dawowa gida . Cikin kwarin gwuiwa daddy yace" ba damuwa zaku iya shiga" "Wai yaya meke faruwa ne agidan nan? Mommyn Islam ta faɗa cikin damuwa tana riƙe da hannun A'isha. Kallonta daddy Yayi kafin yace wata yar hatsaniya ce tsakanin Aslam da surukansa,shine suka kira mana yan sanda"ya kai zancensa cike da takaici. Zaro ido mommyn Islam tayi tana mai faɗin "yanzu yaya abin harya kai ga yan sanda ?" Jinjina kai daddy Yayi yana mai faɗin"sam ban san Alhaji Musa zai iya min wannan tozarcin ba,da mutuncina da komai agari ya kiramin yan sanda?hmmmm ba komai,mushiga daga ciki Abubakar "daddy ya fada yana mai kallon Abban islam dake tsaye shima cikin mamaki. "Kayi hakuri Alhaji, kasan mutanen yanzu sai ahankali,ba kowa yasan ya dace ba"cewar Abban Islam kenan suna mai nufar cikin Falon . "Yawwa officers kun ƙaraso?ga masu laifin nan ku kamasu"Daddyn Husna ya fada yana nuna su mommy gaba dayansu. "Cike da son gasgata muryar da kunnensa yajiyo masa yace "Alhaji Musa" Da hanzari shima Daddyn Husna ya juyo dan ganin mai kiran sunan nasa,dan ya ba kofar baya . Tsoro,mamaki,fargaba da kuma razani sune suka dirarwa Daddyn Husna lokaci ɗaya,sakamakon haɗa ido da Alhaji Abubakar da yayi. Cikin rawar murya yace "Alhaji Abubakar,kaine kana raye dama ,baka mutu ba?Daddyn Husna ya fada cikin mugun tsoro da firgici. "Ina nan da raina,Allah ya ƙaddara nida ahalina muna da sauran shan ruwa adoron duniya,sannna ya kubutar damu daga zalunci da cin amanarka,me nayi maka nida iyalina?me muka tsare maka wane ci gaba muka dakushe maka aduniya daka yi yunkurin ganin bayanmu"Daddyn Islam ya fada cikin yanayi dake nuna yana jin zafin abinda ya faru dashi abaya. Cikin inda inda da in ina,Daddyn Husna ya fara kame kame yana faɗin"dan.... Allah kakkakayi hakuri Alhaji Abubakar,ka manta da komai,duk abinda ya faru abaya,sharrin shaidan ne,kuma Ni bance su kashe kuba, nace kawai su daukomin takarda ,amma kayi hakuri "Daddyn Husna ya fada yana haɗe hannayensa jikinsa sai rawa yake. Gaba dayan falon yayi tsit,kowa sai kallon Daddyn Husna da Abban Islam yake,gaba ɗaya sun sanya su a duhu,domin basu fahimci me suke nufi da kalamansu ba.islam cikin ranta take faɗin kodai wannan shine mutum daya so kashe mu? Maganar mommynta ce ta katse mata tunaninta. Inda mommyn ke fadin "Wai Alhaji kana nufin wannan shine Alhaji musan daya sanya a kashemu ta hanyar sa mana wuta? Mommyn Islam ta faɗa cike da mamaki . "Kwari kuwa shine Alhaji Musa,abokin kasuwanci na,wanda ya biyewa son zuciya da eudin duniya,yaci amanata,ya turomin yan ta'adda har cikin gidana dan su kasheni nida iyalina. Salati gaba dayan dakin suka dauka,kowa yana al'ajabi da mamakin rashin imanin Alhaji musa. Mommyn Husna da Husna sunyi tsilli-tsilli.husna kuwa mamakin mahaifin nata take, bata taba zaton zai iya kashe mutum ba. Kuka granny keyi tana tafa hannaye,"ohh,yanzu dama kaine kake kokarin kashemin ya da iyalanta?sannan ka turo yarka dan ta hana jikata sakat agidan aurenta?Allah ya toni asirinku annamimai yan sandoji,kuna dai ji da kunnen ku,dan haka ku kama mugu" Tuni yan sanda suka yi kan su hunsa da nufin kwamushesu. Kuka Husna keyi tana ƙanƙame mommynta, Haka aka tusa ƙeyar su gaba dayan su har husnan zuwa folice station. Mommyn Husna sai zage zage take tana fadin anyi musu sharri.... Muje zuwa. [12/24/2022, 8:59 PM] Abk: 101/102 ______________kuka sosai husna keyi tana ƙanƙame mommynta, ita bazata police station ba. "Wayyo Allah Aslam ka taimake ni,Ni matarka kace,dan Allah karka bari su tafi dani na shiga uku"abinda take fadi kenan tana kuka wiwi tare da miƙawa Aslam hannu. Shikuwa Aslam gaba ɗaya mamakin mahaifin Husna ya gama cika masa ciki,yanzu wannan mutumin rashin imanin sa ya kai har ya iya sanyawa a kona mutane da ransu? Lallai dan adam sai ahankali,mutane sam ba amana.yayi dana sanin auren yar wannan macucin maha'inci azzalumi,inda ya godewa Allah ma, da bai hada zuri'a dasu ba. Wani ƙasƙantaccen kallo ya watsawa Husna,kafin yace "har abada bana fatan koda haduwa dake ahanya,bare wata alaƙa ta hadamu, karki ƙara kiran sunana domin na yanke duk wata alaƙa dake tsakanina dake,kuje ku girbi abinda kuka shuka acan Ni yanzu matata ɗaya ce kuma ita zataci gaba da kasancewa matsayin matata har abada domin aurena dake ƙaddara ce wacce ta riga fata"Aslam ya fada yana mai riƙe hannun Islam tare da nunawa Husna. Ita kuwa Husna sai Ihun kuka take kamar ranta zai fita tana faɗin ba laifinta bane,dan Allah karya rabu da ita.haka aka fitar da Husna daga gidan zuwa motar yan sanda, Mommyn Husna sai zage -zage take tana faɗin akyalesu,basu aikata komai ba ita da yarta,akama alhaji shine mai laifi. Saida Dan sandan ya daka mata tsawa yana mai faɗin ta shiga taitaiyinta,su ba abokan wasanta bane,sannan tayi shiru.dan ta san hukuma ba wasa. Gaba daya sun fito farfajiyar gidan suna kallon yadda ake kokawa da Daddyn Husna,kan shi bazai bi yan sanda ba,saidai ya taho amotarsa.su kuwa sunce bazasu kyaleshi ba,saiya bisu. Daddyn Aslam kuwa sam ya kasa magana ma,dan cike yake da mamakin abokin nashi,yadda rashin imaninsa yakai ya iya kashe rai,ba daya ba harda na kananan yara Kuma ma ƙanwarsa ? Ana ƙoƙarin tura Daddyn Husna mota ne,wayarsa ta shiga ruri, nan ya fara kokarin dauko wayar daga aljihunsa,saidai kafin ya dauko wayar,tuni Aslam ya zura hannunsa cikin babbar rigarsa ya dauko wayar.dan yana zargin wani abu akan Daddyn Husna game da harin da aka kaiwa daddynsa da Aman kwanaki wanda Allah yasa Islam ta cecesu. Yana duba wayar kuwa saiga Sunan jaga ya fito baro-baro akan fuskar wayar.hakan ya sanya shi ƙara karfafa zargi sa akan Daddyn Husna,dan dagani sunan nan bana mutanen arziƙi bane. Tuni gaban Daddyn Husna ya fadi, tsoron sa ya ƙara bayyana,dan kuwa jiya sukayi da jaga akan zai bashi cikon kudin aikin daya sanya su, na bibiyar mahaifin Aslam,Dan su gano ta yadda zasu kawar dashi.amma yaƙi cika masa kudin ajiyan,dan yace baya cika masa aiki idan ya sanya shi dan haka bazai biya kudin aikin ba, Wanda hakan ya fusata jaga yace,idan har Daddyn Husna yayi saken kin cika masa kudinsa zuwa washegari,to wllh saiya dauki mataki mai ƙarfi akansa. To yanzu ma kira yayi dan ya sanar da Daddyn Husnan ya saurari hukuncin da zai dauka akansa. "Aslam karka daga wannan kiran,dan Allah karka daga,wllh shidin mai kisa ne,kuma zai iya yin komai akan kuɗi,sannan wannan wayar sirrina ne karka daga"Daddyn Husna ya fada cikin yanayi na firgita da tsoro,dan yana tsoron kar wani asirin ya Kara tonuwa. "Aslam ka daga wayar,ka sanyata a sifika kowa yaji,dan na tabbata wannan kiran daga mutanen dayake sanyawa aikin kisan ne"Daddyn Aslam ya fada cikin bada umarni. "A'a Alhaji dan girman Allah karka sanya yaron nan ya daga wayar nan,wllh akwai gagarumar matsala Gara ku kaini police ɗin cikin wannan motar ayimin hukuncina,akan ku daga wayar nan,sirrina ce"Daddyn Husna ya fada cikin firgici da tsoro fiye dana da. Jin irin yadda ya tada hankalinsa ya sanya Aslam saurin daga kiran,wanda harya kusan tsinkewa. "Kai Alhaji Musa ,Ni zaka mayar dan iska?kaƙi cika min kudin aikina, sannan wayata ma saika ga dama zaka daga?to wllh nafika akuyanci,baka isa ka sanyamu aiki kuma kaki biya ba,kai kanka ka sani wancan lokacin har videon yadda muka sanya motar Alhaji kabeer hatsari da hoton gawarsa saida muka nuna maka,amma da yake ehh Allah yayi da sauran shan ruwansa bai mutu ba.kuma tunda ga wancan lokacin.kasanya mu muke bibiyar rayuwar sa,Allah yana kubutar dashi, mun samo maka mafitar yadda zaka iya kashe shi yanzu,shine zaka juya mana baya?karya kake wllh jaga cikakken dan tasha ne ,wllh saina zo har gidan ka,agaban idonka zanyiwa yarka fade,da matarka,sannan inba yarana suma su aikata su,kafin in kashe su kisa mafi muni agaban idonka. Wannan shine hukuncin maci amana irinka "jaga yana gama faɗin wannan maganar ya kashe wayarsa. Gaba daya mutanen dake gurin,sandarewa sukayi cikin shock,bama ya Daddyn Aslam,zuciyarsa tayi rauni matuka hankalinsa ya tashi sosai,jikinsa kuwa tuni ya kama rawa,saida Aslam yayi saurin rikeshi yana faɗin"ka kwantar da hankalinka daddy everything will be ok"ya fada yana jingina mahaifin nashi da jikinsa. Cikin dacin zuciya Daddyn Aslam ya kalli Alhaji Musa,wanda ya sunkuyar da kansa,tunda jaga ya fara magana,sai yanzu yake dana sanin kin biyan jaga cikon kudinsa. Da yanzu asirin sa bai tonu ba. "Yanzu Alhaji Musa,dama kaine wanda ya sanya akasheni akan hanya ta nida ɗana? Sannan kaine wanda ke son ɗauke takardar dana sanya hannu akan maƙudan biliyoyin kuɗaɗen mutane? Wannan shine sakamakon janyoka danayi jikina?ashe da gaske makashinka na tare da kai?shin wannan Shine sakayyar da zakayi min Musa? Shin ka manta ahalin dana daukoka? Kana almanirinka na daukoka na sanya ka jikina,nayi maka aure na baka gida na inganta rayuwarka,sannan na sanya ka cikin harkokina,na aurawa dana yarka,duk wannan alkairan da nayi maka da kisa zaka sakamin ? Bayan kayi ƙoƙarin kashe ƙanwata da mijinta ,tare da ƴaƴansu? Me kake nema Alhaji Musa? Me zaka ajiye aduniyar ?"Daddyn Aslam ya fada cikin wata irin murya mai kama da zaiyi kuka. "Alhaji sharrin shaidan ne dana zuciya,kuma Ni wllh karya ma wannan yaron yake min,bansanshi ba kawai yana son ya... Tasss!!!Daddyn Aslam ya ɗauke fuskar Daddyn Husna da mari mai matukar shiga jiki. "Rufemin baki macucin banza maci amana maha'inci officers ku tafi dasu muma muna tafe bayanku, dan bada bayani"daddy ya fada yana huci. "Alhaji dan Allah kayi hakuri wllh sharrin zuciya ne ka gafarceni" Abinda Alhaji Musa ke faɗi kenan yana zare ido. "Ku daukeshi daga gabana officers" daddy ya fada cikin fushi. Aikuwa yan sandan ma cike da tsanar su Daddyn Husna suka tasa ƙeyarsu zuwa police station,Dan sun Sha mamakin cin amana irin na wannan bawan Allah. "Kuka sosai granny ta sanya tana tsinewa musa"Allah ya isa tsakanina da mutumin nan,ashe shine yayi kokarin kashemin yayana har biyu, wllh sai munyi shari'a dashi azzalumi kawai" Rarrashinta su mommy sukayi tayi hartayi shiru,sannan suka koma cikin Falon cike da jimami,gaba dayansu zama sukayi zuciyoyinsu cike da alhini da kuma ƙara godewa Allah, daya bayyana musu wannan gaskiyar,suka gano cewar suna zaune da mugayen mutane tsawon lokaci ba tare da sanin su ba. Ajiyar zuciya daddy ya sauke mai ƙarfi,kafin yace "alhamdullah,Allah shine abin godiya,domin cikin hikima da taimakon sa muka gano wannan gaskiyar da ta jima aboye, tabbas,Alhaji Musa ya cutar da mu,ya ha'incemu,amma Allah shine zaiyi mana sakayya akansa,na daukeshi tamkar dan uwana na jini,na maidashi babban abokina,kuma abokin shawarata,amma yaci amanata"daddy ya fada cike da karyewar zuciya. "Dama haka halin dan Adam yake ,wanda ka yarda dashi,ka bashi amana shine yake cinyeta,yanzu ka duba ka gani menene baka yiwa Musa ba?ba kallon kai ba,nima tamkar da haka na daukeshi, Haka muka ƙi jininmu muka nuna son nashi,ta hanyar aura mata Aslam,Ni wllh sai yanzu nake tunanin anya ba asiri sukayi mana ba? Dan awannan lokacin wllh ji nake tamkar na daukota na dawo da ita gidan nan matsayin matar Aslam,Amma yanzu sam bana jinta cikin raina "cewar granny kenan tana taɓe baki. Girgiza kai daddy Yayi tare da kallo Daddyn Islam yace "ya kamata muje can police station ɗin ko?ya fada yana mai mikewa tsaye. "Haka ne Alhaji karsuyi ta jiran mu,dan wannan case ɗin babban ne "cewar daddy Islam shima yana mikewa tsaye. "Aslam ka tashi muje kaima dan akwai bayan da za'a bukaci ji daga gareka"daddy ya fada yana mai kallon Aslam,dake zaune kusa da islam hannunta cikin nashi. Mikewa Aslam yayi tare da sakin hannun Islam,yace "to daddy "sannan ya kalli Islam yayi mata murmushin kwantar da hankali,dan yaga gaba ɗaya jikinta yayi sanyi kamar ba Islam dinsa daya sani jaruma ba. Ahankali yace "idan kina jin barci ki kwanta anan,idan mun dawo zan tasheki mu koma part dinmu,sannan ki kwantar da hankalinki kinji?" Ya fada yana mai kafeta da idanuwansa masu sanyata jin kasala. Jinjina kai kawai tayi ba tare da tace komai ba,dan jikinta asanyaye yake sosai. Haka su Aslam suka rankaya zuwa police station din... Muje zuwa. Mrs babi ce [12/27/2022, 7:50 AM] Abk: 103/104 _______________Jinjina kai kawai Islam tayi ba tare da tace komai ba,dan jikinta gaba ɗaya asanyaye yake sosai,ashe duk tsawon wannan lokacin suna tare da mutumin da yaso halakasu ita da nahaifanta?sannan kuma shine wanda yaso kashe yayan mahaifiyarta sannan surukinta? Wannan fa shine ake kira rashin sani ,wanda yafi dare duhu. Haka su Aslam suka rankaya police station da su daddyn,yayinda aka bar Aman agida,Dan ya kula dasu mommy,tunda gaba dayansu jikin kowa yayi sanyi. Koda suka je police station din,sun tarar dasu Daddyn Husna da Husna tare da mommynta akulle. Inda mommyn Husna sai masifa take akan ita da diyarta basu da laifi,abudesu. Shikuwa Daddyn Husna yana zaune yayi shiru yana kallon yadda diyarsa ke kuka sosai,tunda gurin da aka kullesu yana kallon juna ne. Bayan su daddyn sun gama bada bayani ne Daddyn Aslam ya bukaci da a fito da su husna,dan su kam basu da wani case dasu. Hakan ta sanya aka fito dasu Husna akan sharadin bazasu bar garin ba har zuwa sanda za'a mika Alhaji akotu, sannan zasu zauna bisa kulawar yan sanda saboda furucin su jaga. Koda aka fito dasu Husna,sai kuka take tana rokon Aslam ya maidata ɗakinta, shikuwa ko kallo bata ishe shi ba. Saboda dattako irin na Daddyn Aslam,har rarrashin Husna yake akan tayi shiru ta daina kuka. Haka dai su husna suka tafi gida bisa rakiyar yan sanda guda biyu. Suma su daddyn suka dawo gida. Su daddyn Islam basu jima da dawowa ba,suka tafi nasu gidan suma. Aslam ma Bangaren su suka koma shida Islam,tunda dare yayi. Gaba daya Aslam baya cikin yanayi na jin dadi,damuwa ta bayyana sosai akan fuskarsa. Suna kwance akan gado shida Islam,inda yake rungume da ita asaman ƙirjinsa,bayanta yake shafawa ahankali yana tunanin ta yaya ya auri yar mutumin daya so kashe masa haifi da antynsa? Shifa badan yasan cewar ba ta yadda za'ayi ya zauna da Husna gida ɗaya ba tare da aure ba,to da saiyace shi baisan lokacin da aka ɗaura musu aure ba. Jinda Islam tayi shirunsa yayi yawa ne yasata ɗago kanta ahankali ta kalli Aslam,aikuwa ta cikin dan hasken dimm light ɗin dakin ta hango fuskarsa, idonsa biyu ba barci yake ba,saidai kana gani kasan yayi nisa a kogin tunani. Shiru tayi tana tunanin abinda zatayi masa dan kawar masa da damuwar dake ransa. Tana son faranta masa,saidai tana tsoron wahalar da zata sake sha. Amma ya zame mata dole awannan lokacin ta kuka da Aslam. Dan haka cikin nutsuwa da ɗan dari-dari ta matsar da fuskarta saitin bakinsa. Kawai jin bakin Islam yayi cikin nashi. Aikuwa abinka da mai neman kuka,kuma aka jefeshi da kashin shanu. Ba jiran wani abu Aslam ya karɓe bakin Islam,nan dai suka fara ƙoƙarin faranta ran juna. Yau ma dai Islam taji ajikinta,saidai ta daure sosai dan ganin Aslam ya samu nutsuwar da ta kamata. Aikuwa ya samu nutsuwar da ta ɗauke masa duk wani damuwa dake ransa. Bayan komai ya lafa yana rungume da Islam ajikinsa,albarka kawai yake sanbado mata, yayin da yake jin so da ƙaunarta na ƙara nutso cikin zuciyarsa. Fata yake Allah yasa yayi ajiya ajikin Islam daren jiya. Washe gari da safe aka mika case ɗin su daddy zuwa kotu.inda aka sanar dasu ranar Monday za'a fara zama ɗan saurarar case ɗin nasu. Kai tsaye suka wuce dan ganin Daddyn Husna,har zuwa wanann lokacin Daddyn Aslam Yana jin ba dadi game da kulle Daddyn Husna da akayi,dan kuwa indan ta tashi ne wllh yafe masa zaiyi,dan yana ganin cewa Alhaji Musa baida kowa sai shi,shine ya zame masa uwa,uba,yaya kuma aboki. Dan Alhaji Musa Maraya ne baida uwa baida uba. Dan haka yake jin damuwa sosai cikin ransa na ganin Alhaji Musa cikin kurkuku. Koda aka fito dashi daga inda aka kulleshi, sosai Daddyn Husna ya tausaya masa,ganin yadda jikinsa yayi dukun dukun,sannan ga dukkan alamu baici komai ba,kamar ma dukansa akayi,dan da kyar yake taka ƙafarsa. Allah sarki daddy cike da zafi da jin ciwo azuciyarsa yake kallon Alhaji musa yace "yanzu Musa wannan itace rayuwar daka zaba wa kanka?wannan shine abinda kake burin ganin kanka ciki?me yasa musa?me yasa ka aikata wannan danyen aikin?kasan yadda nake ji cikin zuciyata ganin ka ciki wannan halin? Musa ka cuci kanka,ka lalata rayuwarka,me yasa baka cemin kana bukatar wannan kudaden na baka su ba?meyasa baka yi tunani Ba kafin aikata wanann danyen hukuncin?na dauke ka matsayin dan uwana amma kaci amanata Musa, yanzu ga abin da gari ya waya" Daddyn Aslam ya fada muryarsa na rawa. Kuka Alhaji Musa ya sanya mai ciwo,sai yanzu yake dana sanin ƙoƙarin cutar da Alhaji kabeer da yayi tayi,lallai wannan mutumin, mutumin kirki ne kamar yadda ya sani tun baya,yanzu duk wannan abinda ya faru,amma yana nuna tausayawarsa akan sa. "Dan Allah Alhaji kayi hakuri,hakika na cutar da kaina na zalunci rayuwata,na zamo mai son zuciya da kwadayin abin duniya,wanda suka sa na manta da menene zai iya faruwa dani nan gaba, dan Allah Alhaji ka yafe min"Alhaji Musa ya fada cikin kuka yana haɗe hannayensa alamun neman yafiya. Shi kansa Daddyn Islam yaji tausayin Alhaji Musa,amma ya kamata ahukuntashi,domin ya cutar da al'umma sosai. Haka suka tafi suka barshi yana ta kuka,wanda suma saida sukayi kwalla. Mommyn Husna kuwa kwana tayi tana kitsa abubuwan da yawa cikin ranta,bata bari gari ya waye ba,ta saci jiki ta fice daga gidan,kawai sai jin karar tashin mota yan sandan nan sukayi. Ƙoƙarin Binta sukayi,amma ina tayi musu nisa,dan ko ganin ƙurar motar ta basuyi ba. Haka suka hakura suka dawo gidan, inda suka tarar da Husna zaune ta hada kai da kwuiwa tana kuka. Kai tsaye mommyn Husna ta nufi gurin bokanta,tafiya mai nisa tayi kafin taje gurinsa. Ahargitse ta shiga dakin da bokan yake,sai haki take,dan sai kayi tafiyar kasa kaɗan zaka je inda bokan yake,saboda aɗan saman wani dutse yayi dakin nashi.kuma mota bazata je ba. Yana ganin mommyn Husna ya sanya dariya mai sauti yana nuna ta da isgar dake hannunsa. Zama tayi tana mai hararar bokan,dan afusace tazo gurin nashi,saboda ya karya musu alkawari, ba wani aiki da yayi musu,kawai yayi ta amfana da jikinta ne ya yaudareta. "Boka meyasa zakayi mana haka?me yasa zaka ci amanata?ashe baka yi mana aikin da kace zakayi ba? Kaci amana ta boka,yanzu haka mijina yana kulle,duk wani laifi daya aikata aboye yanzu ya fito fili,ansan dashi wllh kaci amanata makaryacin banza mugu kawai Allah ya isa tsakaninmu da kai"mommyn Husna ta faɗa cikin ɓacin rai da mugun jin haushin bokan. "Wata irin hatsabibiyar dariya bokan ya sake sanyawa,kafin ya turɓune fuska,kallon mommyn Husna yayi da jajayen idanunsa yace cikin tsawa"ke la'ananniyar Allah,mushirika mai bin bokaye,ki sani kinyi kuskuren fada min bakaken maganganu,yau zaki yabawa aya zakinta, da kin dauka duk mai bin boka yana karewa lafiya ne?wannan shine karshen rashin bin Allah da duk wasu masu irin tunaninki suke riskar kansu,Ni kaina nasan karshe na bazaiyi kyau ba, dan haka ina fatan akashe mijin naki ma,sannan kema kiyi mutuwar wulaƙanci"ya kai zancensa yana mai fashewa da dariya. Hawayen bakin cikine suka fara zubowa daga idanun mommyn husna "Allah ya isana boka,Allah ya tsine maka albarka,mugu mai dulmiyar da mutane marar tsoron Allah,In Sha Allahu tun aduniya zaka gone gurmus shegen mutum, kuma bazanyi mutuwar wulaƙanci ba,saidai ka gani akanka"mommy ta faɗa tana mai mikewa dan barin dakin.saidai taku biyu tayi,taji an fizgota tare da maka ta da ƙasa. Ihu mommy ta kwalla na azaba,kafin tayi wani yunkuri kuma tuni boka ya haye ruwan cikinta yana ƙoƙarin zare wando. Kokawa suka fara da mommyn Husna,amma ina saida ya kaima abinda yake so,tana ji tana gani bokan nan yake sex da ita cikin wulaƙanci da mugunta. Hawaye ne kawai ke zubowa daga idanunta,cikin wannan kuka ta lalubo wannan kwarangwal ɗin kan mutum ɗin dake ajiye gefen gurin zaman boka,bata jira komai ba ta rabka masa a keyarsa. Wani wawan ihu bokan ya kwalla wanda Saida dajin ya amsa,sannan ya fadi nan gefenta jini na malala daga ƙeyarsa,sai shure Shure yake. Cikin hanzari da tsoro mommyn Husna ta mike tare da zubawa aguje,tana zuwa ta shige motarta tana kuka wiwi jikinta sai rawa yake. Tuki take cikin rashin nutsuwa kamar ma bata cikin hayyacinta,tana cikin tukin taga wani ƙaton zakara, wanda girmansa ya kai raƙumi,sannan da ƙaho ɗaya akansa ,ya tunkarota da gudu. Ihu ta kwalla maimakon addu'a,aikuwa tuni kan motar ya kwace mata, taje ta bugu da wata ƙatuwar bishi,nan motar tayi ta wuntsilawa ta na dukan bishiyoyi.kan kace kwabo motar tayi taga raga, inda mommyn Husna tayi kaca kaca da jini ƙafarta ɗaya ta cire kanta ya fashe ta gefe kamar wanda aka sare shi. Wannan shine karshen mommyn Husna ,ta mutu mutuwa ta wulaƙanci da tozarxi. (Allah kasa mufi karfin zuciyarmu,ka hane mu aikata shirka ameen). Wasu masu wucewa ne suka ga hadarin inda sukayi saurin sanar da yan sanda akazo aka tafi da gawar mommyn Husna wanda aka tattara sassan jikinta cikin akwati. Kan kice me tuni labarin hadarin ya watsu cikin garin. Ana ta fadi gidan talabijin da kuma lambar motar da aka gano da ƙyar. Aikuwa ahauce Husna ta nufi asibitin da aka kai gawar mommyn ta. Tana ganin gawar ta shaida mahaifiyarta,nan take ta fadi asume. Labari ya iskewa su daddy haka suka rankaya asibitin cike da jimami inda suna zuwa suka tarar da an kawo jannat haihuwa. Kafin su gama cukucukun karbar gawar jannat ta haifi diyarta mace kyakykyawa . Haka suka dauki gawar suka je suka gudanar da jana'iza aka kaita makwancinta,saidai muce Allah yasa mu dace. Koda labarin mutuwar ya riski Alhaji musa,kuka yayi tayi kamar karamin yaro yana tuba ga ubangijinsa.Hankalinsa yayi mugun tashi game da mutuwar matar tasa,gashi ko gawarta bai sami gani ba,dan lokacin da aka zo dashi tuni an binne ta, shima saida Daddyn Aslam ya, sanya baki aka barsa' kabarinta kawai ya gani,yaso kwarai akaishi yaga yarsa amma,ina sam yan sandan nan sunki,dan sunce case dinsa babbane kuma suna tsoron ko wani plan din ne suka hada dan inyaje asibitin ya gudu . Haihuwar jannat itace ta ɗan sanyaya musu zuciya,game da damuwa da alhini da suke ciki, inda suka cika da murna samun baby. Husna kuwa koda ta farka,kamar zararriya haka ta koma kuka take tana ihun mommyn ta,(to Husna sai muce Allah ya bada hakurin rashi.... Mrs babi ce [12/31/2022, 8:09 AM] Abk: 105/106 ____________Husna kuwa koda ta farka,kamar zararriya haka ta zama,kuka take kamar ranta zai fita tana kiran mommyn ta. Idan ka ganta awannan lokacin,dole ta baka tausayi. idanunta sunyi luhu luhu,da kyar take iya budesu,mutane sai bata hakuri suke,amma ko sauraraonsu ma batayi bare tasan me suke cewa. Daga karshema danne ta likitoci sukayi tare da yi mata allurar barci,dan bata cikin hayyacinta. Koda aka shiga kotu kuwa,sam Daddyn Husna bai musa tuhumar da akeyi akansa ba,dan kuwa gaba ɗaya yanzu,ya sare duniyar ma ta fita akansa,kullum cikin kuka yake,gashi yana matukar son ganin yarsa,ko zai ji sanyi cikin ransa,sam baya magana saidai kuka yayi ta istigfari da neman yafiyar Allah. Lokacin da za'ayi zaman kotun daddyn Aslam da kansa yaje ya taho da husna daga asibiti.dan itama kullum cikin kuka take tana cewa akaita gurin Daddyn ta. Lokacin da aka shigo da Daddyn nata taga yadda ya koma,yayi baki ya rame sannan idanunsa sun kumbura alamun kuka da rashin barci. Wani irin tausayin sa ne ya kamata,batasan lokacin da ta sanya kuka ba.shima Daddyn nata yana ganin husnan kukansa ya ƙara tsananta, wanda da dama saida suka ba mutane tausayi. Kasancewar daddyn Husna bai musanta akan tuhumar da ake masa ba, kuma bai wahalar da Shari'a ba,sannan Daddyn Aslam ya nema masa sassauci akan hukuncin da za'a yanke masa,hakan ya sa alkali ya yankewa Daddyn Husnan hukuncin daurin rai da rai. kuka sosai Daddyn Husna keyi lokacin da za'a tafi dashi kurkuku,yana rungume da yarsa,ji yake kamar zuciyarsa zata fashe,damuwa, danasani da takaicin irin rayuwa da kuma tarbiyyar dasuka ba Husna yana mai damun zuciyarsa,sam lokacin da suke bata dukkan wata dama da take nema ta yin abinda taso,basuyi tunanin zuwan wnanan rana irin ta yau ba,gashi Dukansu sunyiwa Husna nisa,nisan da bazai basu damar gyara barnar da sukayi abaya ba. Cikin matsanancin kuka Daddyn Husna ke faɗin"ki yafe min Husna,ki gafarceni Husna,mun cutar da rayuwarki, mun bata miki tarbiyya,ta yadda bakya gane mai kyau da marar kyau,mun ɗoraki akan tafarki marar kyau,yau gashi mommy ki ta tafi ta barmu,nima kuma zanyi miki nisa, nisan da koda munga juna bashi da wani amfani,domin ba abinda zan iya miki,Husna bani da kowa Ni Maraya ne,amma ban riƙe maraicina ba,na sanya kaina cikin rayuwa marar kyau,sannan mahaifiyarki bata da alaƙa mai kyau da danginta, nasan bazasu riƙe mana ke ba,Husna nayi dana sani da Allah wadai da rayuwata,ban zama uba na gari ba Husna ki..kik.... kuka ya hana Alhaji Musa ƙara sa maganar da yake son fadawa husnan. Itama Husna tana ƙanƙame da mahaifin nata,inda take wani irin Kuka mai tsananin ban tausayi,kai bakace itace husnan nan marar mutunci ba,dan duk rashin imanin ka,saika tausaya mata.kuka kawai take tama kasa magana sai neman shidewa take. Daddyn Aslam,Daddyn Islam,Aslam,dakuma Aman,gaba ɗayansu saida suka tausaya wa su husna,dama wanan shine ƙarshen maci amana ai. Cikin kuka Daddyn Husna ya riko hannun Husna zuwa gaban Daddyn Aslam, "Alhaji nasan na cutar da kai,ban zamo mai saka alkairi da alkairi ba,amma dan Allah ina rokon ka,ka taimakawa rayuwata ka kulamin da Husna,dan nasan zuciyarka ba ba irin tamu bace,kai adali ne mai manta sharrin wani agaresa. Husna bata da kowa ahalin yanzu sai kai,sai Allah"ya kai zancensa yana mai sunkuyar da kansa hawaye kuwa kamar an bude fanfo. Ƙwallar data ciwa Daddyn Aslam ido ce ta sami damar zubowa,sakamakon rufe idanunsa da yayi.hannun Husna ha kamo tare da dafa kafadar Daddyn Husna yace"In Sha Allahu Musa zan kula maka da diyarka,kamar yayan cikina,zan zame mata uba kuma zan cike mata gurbin ku data rasa"ya fada cikeda tabbatarwa. Kara karfin kukansa Daddyn Husna yayi,yana mai faɗin"na gode alhaji,na gode Allah ya biyaka, ka yafe min Alhaji,kaima Alhaji Abubakar Ina neman yafiyarka" Yan sandan da zasu tafi da Daddyn Husna ne suka fara jan hannunsa mai ankwa dan tafiya. Ihu Husna ta sanya tana mai bin Daddyn nata da gudu "wayyo daddy karka tafi ka barni,wayyo Allah na daddy ka dawo bani da kowa saikai da mommy ita ta tafi ta barni,kaima zaka tafi ka barni, wayyo Allah na"kalaman da Husna ke faɗi kenan tana bin motar da aka sanya Daddyn ta ciki. Da kyar Daddyn Aslam ya rike ta yana rarrashinta. Koda suka dawo gida sosai granny ta fara fadan me ya kawo Husna gidan? Sanar dasu komai daya faru daddy Yayi,amma firr granny tace Husna bazata zauna dasu ba. Karshe dai da kyar suka shawo kanta ta yarda akan mommyn Islam zata tafi da ita can gidan ta. Anyi sunan jannat inda aka sanyawa yarinyar khadeeja,suna kiranta da Nana. Bayan wani lokaci,komai ya lafa,rayuwa ta dai -dai ta,inda Aslam da Islam suka buɗe sabon babin soyayya mai cikeda aminci,tausayawa tare da jinkan juna . Aslam ya kammala ginin tamfatsetsen gidan sa,wanda faɗin kyau da tsaruwar da yayi ba'a magana,yau kwanansu uku da tarewa agidan,suna zaune afalo,inda Aslam Yayi matashin kai da cinyar Islam,ya kafeta idanunsa masu cikedazallar soyayyarta, dan hure masa ido tayi tare da yin fari da idonta tace "Ni kaga malam karka gano muni na da wanann kallon"ta faɗa cikin salon jan hankali. Murmushi Aslam Yayi tare da sauke ajiyar zuciya mai ƙarfi kafin. Yace "Akullum Islam ina ƙara godewa Allah daya mallaka min ke matsayin matata,kedin alheri nace kuma sanyin idanuna ,ina godiya ga Allah Islam "ya fada sounding so happy. Ahankali Islam ta saki ƙayataccen murmushi mai sanya zuciya zurmawa cikin kogin soyayya. Kafin ta ɗan marairaice fuska tace "Saidai har yanzu na kasa baka dawwamammen farin ciki,ta hanyar haifa maka yara kamar yadda kake fata da buri,abin yana matukar damuna zaujee"Islam ta faɗa idanunta na cikowa da hawaye.yau kimanin shekara guda kenan da aurensu, amma har lokacin Islam bata sami ciki ba,abun yana matukar damunta,dan tasan yadda Aslam ke matukar son yara. Dan haɗe rai Aslam yayi tare da sanya hannu yana share mata hawayen daya gangaro da idanunta kafin yace "zaki fara ko? Kinsan bana son irin wannan maganar,ai bake kika hana kanki samun cikin ba,Allah ne bai ga damar bamu ba,ko kina son yiwa Ubangiji butulcine ?ya fada yana mai kallon fuskarta . Cikin sauri Islam ta girgiza kanta,alamun a'a. "To ki daina faɗin wannan maganar kinji?ki godewa Allah daya yiki matsayin musulma,kuma ya baki rai da lafiya,idan muna da rabo zamu sami haihuwa,maza ki share hawayen nan,bana don ganinsu suna sanyani damuwa kinji?"ya fada yana mai shafa kumatunta. Jinjina kai tayi tare da sanya bayan hannunta ta share hawayen dayayi saura a idonta. Sannan ta kalli Aslam ashagwabe tace "to Ni ka goyani ka kaini lambu gurin janbu" ta faɗa tana wani langabe kai irin na shagwaɓaɓɓun yaran nan. Murmushi Aslam yayi tare da mikewa tsaye yana mai jin kaunar Islam ta ko wacce kafa dake jikinsa,yana matukar son yadda take shagwaba idan suna tare,hakan yana sanya shi nishadi sosai. "Angama yan matana maza tashi ki hau,In kai ki duk inda kike bukata"ya fada yana mai ɗan ranƙwafawa yadda zataji daɗin hawa bayan nashi. Cikeda farin ciki da doki Islam ta mike tare da hayewa bayan nashi,shikuwa ya nufi garden da ita. Sosai garden din nasu ya kawatu matuka,dole idan kana gurin kajika cikin nishadi da farin ciki. Jikin bishiyar ayaba ya ajiye ta,dan yasan can zasu taradda janbun. Kallonta yayi lokacin data sauka daga bayan nashi,tana sanye da wando iya gwuiwar ta,sai wata yar karamar riga mai hannun best,kayan sun kamata sosai, sunyi mata kyau. Dan ƙanƙantar da ido Aslam yayi kafin yace "madam,wai menene sirrin ne? Kallonsa tayi cikin rashin fahimta tana shafa bayan janbu daya sauko da gudu sakamakon hangota da yayi. "Sirrin me fa"ta faɗa da son jin karin bayani. "Cike da salonsa na son sanyata Farin ciki ya sanya hannunya ya kamo hips ɗin ta yace "waɗan nan abubuwan nawa fa sai ƙara bajewa suke,sannna wannan kayan laushin suma sun kara girma da kyau, ya fada yana shafo breast dinta da suka cika rigar atsatstsaye.ke gaba dayan ki ma fa kin canza kin zama yar lukuta meye sirrin ne? Turo baki Islam tayi,kafin tace "kaine sirrin mana,kulawarka ce akansu ta kai yadda suke bukata,amma kwana biyun nan girman nasu karuwa yake sosai dayawan kayana sun min kaɗan "ta faɗa tana dan shagwabe fuska. Shiru yayi yana kare mata kallo,anya kuwa Islam ba ciki gareta ba? Kamo hannunta yayi yace Islam when kikaga period dinki? Ɗan shiru tayi tana nazari,idan bata manta ba,kimanin wata biyu kenan bata gani ba. "I think tun last two months"ta faɗa tana kallonsa. Cikin tsantsar farin ciki taga ya sureta yana juyi da ita . "Alhamdullah Islam I think you are pregnant" ya fada cikin farin ciki. Itama Islam ɗan zaro ido tayi,sam ta manta cewar idan mace bataga period dinta ba,zai iya zama ta samu ciki ne. Ba wani bata lokaci kuwa suka shirya sai asibiti. Binciken Farko ya nuna Islam na dauke. Da ciki har na tsawon wata biyu. Masu karatu, zo kuga murna wajen su Aslam. Faɗin irin murnar da sukayi ma bata lokaci ne. Haka suka dawo gida suka fara rainon cikinsu. Cike da so da kulawa suke rainon cikin,inda gaba ɗaya aslam ya maida hankalinsa akan Islam,kome zatayi shike mata,baya barinta tana motsi mai ƙarfi, Gashi cikin nata saiya fara sanyata laulayi mai zafi,komai taci saita mayar dashi,kullum zaka ganta kwance jikin Aslam,tana zuba tabara son ranta. Shikuwa da tace wai zaice me kike bukata?me za'ayi miki?kingaji da kwanciyar ne? Haka dai ire -iren waɗan nan tambayoyin zaiyi ta jero mata,har saitace ba komai. Hannunsa kuwa kullum yana cikin rigar Islam yana shafa cikinta. Kaf dangi ba wanda baisan Islam na da ciki ba, dan waya suka rinkayi suna sanar da yan uwa. Mommy Islam da suka kirata ma dariya tayi tayi musu ganin yadda suke ta bata labarin cikin. Lokacin da grannyn tazo ganin Islam,dole ta sanyata zama agidan,dan ganin yadda Islam ɗin ke shan wahala,kamar ba ita ba,ta zama shiru shiru ta ɗan rame,saidai tayi fari sosai ta kara kyau. Saida cikin ya kai wata biyar sannan ta daina laulayin, sai ci kamar gara,koda yaushe cikin ci take. Yauma kamar kullum,suna zaune afalo,yayinda Islam tayi matashi da cinyar Aslam, tan cin yalo,shikuma Yana nasa aikin wato na shafa cikinta. Kamar wacce aka mintsina ta tashi zunbur . Da sauri Aslam ya riko hannunta yana faɗin"lafiya pretty ?menene?ya fada adan ruɗe yana kallon jikinta. Kallonsa tayi tare da ɗan zaro ido kamar wacce take cikin mamaki ko al'ajabi tace "ji nayi kamar ana Min zillo acikina"ta faɗa tana ɗan riƙe mararta saitin dataji motsin. "Da gaske pretty?Aslam ya fada yana mai ɗora hannunsa inda ta ɗora nata. Aikuwa cikin Sa'a shima yaji cikin yayi motsi har sau biyu. Da sauri ya ɗago kai suka haɗa ido da Islam,kawai sai suka sanya dariya cikin farin ciki. Kunne Aslam ya ƙara acikin nata yana mai faɗin"hi baby ya kike?mom and dad luv you so much"ya fada kamar wanda yake magana da mai wayo. Dariya Islam tayi tana mai shafa kan Aslam din. Grannyn ce ta fito daga ɗakinta tana faɗin"wai nikam dariyar me kuke yi ne ?tun ɗazu nake jiyo babatun dariyarku" Ta faɗa tana ƙarasowa cikin falon,. Sai lokacin ta hango hannun Aslam akan cikin islam. Tafa hannu ta fara kamar wacce taga wani abun mamaki kafin tace "yanzu kai kuwa wannan yaron bazaka bar wannan masifar taka ta shafa cikin matarka ba?shikenan baka da aiki sai kayi ta lalubewa yarinya ciki?ke kuma ki zauna kina masa dariya ke adole miji yana son cikin ki ko? To wllh kiyi ahankali in ba haka ba,wannan da tsabar jarabarsa saiki kara samun wani cikin"granny ta faɗa tana harararsu. Dariya suka sanya tare da tafawa .Aslam yace "yau nake ganin ikon Allah,wai mutum da abunsa dan ya taba kuma ake sa masa ido?nifa wllh kobaki zo ba zan iya kula da matata, haka kawai kinzo kina ta faman samana ido "ya fada yana ci gaba da shafa cikin Islam cikeda tsokanar granny . "Nazo,kuma bazan koma ba har sai Islama ta haihu sannan mutafi gida wanka,In yaso ka zauna ka cinye kanka"cewar granny. Wani kallon me kikace Aslam Yayi mata kafin yace "tab wllh ba wanda zai kaimin mata wani wanka,duk ruwan gidan nan bai isheta wanka ba sai an kaita gida?a'a wllh garama kiyi tafiyarki tun yanzu,dan ba inda zata"Aslam ya fada cikin yanayi na jinki nake. "Ja'iri marar kunya wato so kake abar maka ita agidan,salon shekara na zagayowa ta sake haihuwa ko? To baka isaba kayi tsururu ruwan randa"ta faɗa tana riƙe ƙugu. Dariya sosai taba Aslam ganin yadda ta dage da gaske tana faɗa. Islam ma dariya take kasa-ƙasa. "Au dariyama kake min ko?to ka tsaya in ƙaraso gurin da kake wllh saimun raba raini dakai,dama jikina yayi min nauyi "grannyn ta faɗa tana nufo Aslam. Da sauri ya tashi tare da sanya dariya yana mata kwalo.ita kuwa ta dage saiya tsaya sun raba raini. Haka yayi ta zagaye falon yana wahalar da yar tsohuwa,data gaji saita zauna tana faɗin "zaka zo ka sameni ne ja'iri.tana zama agurin ta kama barci. Cikin dariya Aslam yazo ya ɗauke Islam suka gudu daki suka bar granny anan. Cikin Islam na cika wata tara da yan kwanaki ta haihu,cikin nasara ba tare da ta sha bakar wahala ba,ta haifi yaranta biyu,mace dana miji. Masu karatu kuzo kuga murna gurin su Aslam,dashi ake karbar Barka,ko kuma sai yan Barka sunzo ake karbo yaran agurinsa. Ranar suna aka sanya musu sunan mommyn Aslam da Daddyn Islam. Wato A'isha da Abubakar inda ake ce musu haneef da haneefa. Yaran sun taso cikin kulawa da soyayya inda gaba daya haneef ya dauko halin mahaifinsa na son girma da manyance. Haneefa kuwa halin Islam gareta saidai ita akwai iyayi da tsiwa. Kowa na son yaran gasu da shiga rai. Rayuwar Husna agidansu Islam rayuwace mai tsafta abin so,domin mommyn Islam na bata kulawa sosai . Yanzu ta nutsu ta daina duk wata mummunar harka,kullum cikin shigar kamala zaka ganta da hijabinta. Ta shiga islamiyya kullum bata aiki sai karatu da istigfari ,cikin haka ta sami wani malamin islamiyyar tasu zata aureshi. Matansa biyu da yara goma.amma ta amince zata aureshi. Bayan shekara biyar zuwa shida Islam na hango cikin haɗe dakinsu. Sanye,take da doguwar riga abaya tayi rolling da babban dan kwali hannunta riƙe da rigar likitoci wato lapcot,yayin da Aslam ke gefenta yana tajewa haneefa gashin kanta. Haneef kuwa yana yiwa arfat yar kimanin shekara daya da watanni wasa.sai dariya take. Cikin yanayi na shagwaba Islam tace"zaujee nikam na kammala shiryawa,ku nake jira,wllh idan kuna shiryawa bata lokaci ne daku"Islam ta faɗa tana ɗan turo baki Kallonta Aslam yayi yana mai faɗin "sorry Madam prettyna yanzu zamu kammala" Ya fada yana mai haɗe hannayensa guri daya. Haneefa ma kallon ammin nasu tayi tare da dan marairaicewa tace "preetyn daddy kefa ƙawata ce amma bazaki bari agama min kwalliyar gashina ba?ta faɗa tana wani kashe ido ɗaya. Turo baki Islam tayi kafin tace "to ai kune zaku batamin lokaci bayan kunsan yau muke passing out "ta faɗa tana karyar da kai tare da kallon haneef. Shima ita yake kallo ganin yadda take kamar zatayi kuka, Cikin yanayin faɗa irin na yara yace " Preetyn daddy kawai mu tafi mu barsu,nima na gaji"ya fada yana kamo hannun Islam. Kuka haneefa ta sanya tana faɗin "daddy wai zasu tafi su barmu" Cikin sigar rarrashi yake shafa kan yarinyar yace "barsu uwata,idan suka tafi muma bazamu je dasu park ba"ya fada yana kallon haneef dan yasan shine mayen zuwa park. Shiru yaron yayi yana kallon Daddyn nashi.kafin yace"daddy zamu jiraku fa amma kuyi sauri, kaga preetyn ka zatayi kuka"ya fada yana kallon fuskar Islam,wacce ta wani kwabe fuska kamar zatayi kukan gasken. Murmushi Aslam yayi tare mikewa yace to bari na rarrasheta "ya fada yana kallon Islam tare da kashe mata ido yace "nasan me kike so fa,amma kinga nan akwai yara muje dakina in rarrasheki acan" Ya fada yana kashe mata ido. Zaro ido tayi tare da kallon haneef daya kuresu da ido,tace "nidai ba ruwana wllh kana kallon dan jaridar ka yadda ya kasa ya tsare yana daukar rahoto"ta faɗa cikin dariya. Shima dariyar yayi yana mai shafa kan yaron yace "haneef dan jaridana" "Daddy me yasa bazaka rarrashi preetyn ka anan ba sai kunje daki?haneef ya fada yana kallon Daddyn nashi da son jin karin bayani. Kallon juna Islam da Aslam sukayi kafin Islam ta toshe bakinta tana dariya tace "saika bashi amsa" "Yarona ,zan bata sweet ne aɗakin nawa dan tayi shiru kartayi kuka kaji?"ya fada yana shafa kan yaron. Haneefa ce ta sauko riƙe da wata yar mitsitsiyar jaka sai faman sabata ake tana saukowa tace "daddy Nima inason ka bani sweet din" Cikin dariya Islam tace "a'a saidai ya siyo miki taki daban ,wannan sweet ɗin ta pretty ce kawai" Dariya Aslam ya sanya yana mai daukar arfat karamar diyar tasu. "Kuzo kuyi hoto maza"ya fada yana ɗora haneefa akan cinyarsa. Islam ta zauna kefensa ta dauki haneef, suka fara hotuna.cike da farin ciki da annashuwa. ALHAMDULILLAH. Wannan shine karshen littafin rainon dawa,kurakuren dake cikin sa Allah ya yafe mana,gyaran kuma Allah ya bamu ikon yin amfani dashi. Sannan ina mai baku hakuri masoyana masu bibiyar wannan littafin na rainon dawa,sakamakon tsaikon da akayi ta samu,wanda ba dabi'ar rubutuna bane,idan na fara littafi bana tsayawa saina kammala.amma an sami tangarda sosai akan wannan littafin.ina neman afuwarku, hakan bazata sake faruwa ba in Sha Allah. Ina kaunarku Aduk inda kuke,domin kune ni,saida ku nake jin dadin rubutuna. Allah ya sadamu agidan aljannar firdausi. Ina sonku bil hakki har cikin zuciyata. Sai mun haɗe cikin sabon littafina mai suna SIRRIN ƁOYE. Labarin littafin na daban ne salonsa daban yake karku sake baku labari Ga kaɗan daga cikinsa. Ɗanɗano daga littafina na gaba wanda zai zo muku nan gaba In Sha Allah. Yarinyar ce wacce akiyasin shekarunta bazasu gaza sha biyar zuwa sha shida ba. Zaune take kan tarin wata ƙasa da aka zubeta gaban wani ginin laka,da alama kasar ginin gidan da take kusa dashi ake. Kuka take sosai kamar ranta zai fita, Ahankali ta kara rungume jaririn dake hannunta,aƙokarinta na kareshi daga sanyin da ake zabgawa cikin tsakiyar daren,wanda ba komai jikin yaron sai wani yalolon zani data lullubeshi dashi. Banda haushin karnuka ba abinda kake jiyowa. Cikin tsoro take waige -waigen gefen ta sakamakon jin ƙarar takun mutane da tayi. Wannan kenan. "Waikai al'ameen baka da wani aiki sai na sex? An faɗa maka niɗin jakar ka ce ,ina laifi sau biyu fa kake kusantata Aduk watan duniya,ina ce ko sati biyu bakayi da kusantar tawa ba, shine yanzu ka lallabo ina barci na ka tasheni? To wllh ba abinda zanyi maka" "Please baby ki taimaka min mana,idan banzo gurinki ba ina kike so naje?kefa matata ce dan Allah ki taimaka min ,wllh ina cikin wani hali " "Ina ruwana kaje duk inda zaka je ma bai shafe ni ba, taimako daya zanyi maka shine ,kaje ka jika kanwa da lemon tsami kasha..... Wai ya batun yaron nan da na ce ku sanar da iyayensa su turo million goma? Idan basu turo ba lallai kusanar dasu inda zasu dauki gawarsa. "An gama ranki ya dade,su kuma wadannan yaran da muka dauko jiya ga sun damemu da kuka Ya kike ganin za'ayi musu? "Ku sanya musu kwaya mai ƙarfi cikin ruwa ku basu,ta yadda hankalinsu zai gushe. Hmmmm masu karatu me kuka fahimta da wannan littafin? Kudai ku biyoni sannu kan hankali ɗan jin warwarar wannan ƙulle ƙullen. Mrs babi ce Downloaded from GNOVELS.COM.NG This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG For feedback and support Facebook : https://facebook.com/gnovels Twitter : https://twitter.com/gnovels Telegram : https://t.me/gnovels