Downloaded from GNOVELS.COM.NG This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG For feedback and support Facebook : https://facebook.com/gnovels Twitter : https://twitter.com/gnovels Telegram : https://t.me/gnovels [5/21, 8:02 PM] RIAMCOOL: *BAYAN WUYA* *Book 1* By *Mariam sani Riamcool* *MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION* *Bismillahirrahmanirrahim dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Ubangiji maɗaukakin sarki gagara musali da zai bani damar rubuta wannan littafi,Yadda na farashi lafiya ya Ubangiji ka bani ikon kammala shi lafiya, kuma ya Ubangiji ka bani damar Rubuta Abinda Al'umma zasu amfan بسم الله الر حمن الر حيم *Page 1 &2* Duƙe take a cikin ɗan kurkun kichen ɗinsu tana ta faman, fura wuta hayaƙi duk ya cika kichen ɗin,sai uban hawaye take, da ƙyar ta Samu ɗanyun itacen Suka kama da wuta, fitowa tayi daga kichen ɗin don ida kaye_kayen kayan da ke cikin ɗan ƙaramin gidan nasu,ga wani Hadari da ya harhaɗu garin yai baƙiƙƙirin, Sai uban zafi, Sauri_sauri ta dunga yi harta kammala kaye_kayen,tana kammalawa taje ta kaɗa miya sannan ta shiga wanka,tana fitowa ƙasa_ƙasa ta dinga jin ana kiran *MUNEEBBA* Da sauri ta ɗaura Alwalla kasancewar Magriba tayi,ɗaki ta shiga,tana shiga ta iske Mahaifiyarta ta taso tana daddafa bango,Alamar tana son fitowa tayi Alwalla,Da sauri taje ta kamata tana faɗin "Mamma ki daina tashi ke kaɗai kinga, ga ciwon ƙafa sannan ba gani kike ba,kuma kije wajen tashi ki zame ki ƙara jawo wani ciwon,na ce maki idan zaki tashi ki dinga kirana," ta faɗa a shagwaɓe tana turo ɗan ƙaramin bakinta, Murmushi mai Sauti Mamma ta saki,tana faɗin "MUNEEBBA baki gajiya da Rigima,yanzun dai taimaka man nayo Alwalla nan,naji hadari ya taso," Kamata MUNEEBBA tayi ta taimaka mata tayo Alwalla,Suna fitowa suka shiga ɗaki suka kabbara Sallah,Sun daɗe Suna kaiwa Allah kukansu, Bayan Sun kammala Sallar ne MUNEEBBA ta tashi ta shiga kichen ɗin ta ebo masu Abincin da zasu ci, da Kuma na Khabir, zuwa tayi ta ajiye a gaban Mahaifiyarta Sannan ta dinga ebo Abincin tana bata,Saida ta ƙoshi, Sannan ta fara eba tana ci itama,saida ta ƙoshi, Sannan ta tashi ta wanke hannunta tana kauda kwanonin da suka ci Abinci,tana gamawa sai ga Nepa an maido,ta haska ko ina,ƙura ma,kyakkyawar Matashiyar da ke tsaye Ido nayi,don ganin Madarar kyau a gurinta, Doguwar Mace ce wacce ta haɗa tsayi da ƙwari,ƴar duma_duma da ita, ga dara_daran idanu,da zara_zaran gira, hancinta mai tsayi dai_dai misali sai ɗan Cute ɗin bakinta pink lips,fara ce,amma ba irin can ba,ga gashi da ya kwanta yai Luf_Luf a gaban goshinta,da Saje, Kyawu kuwa Allah ya bata saidai muce Alhamdulillahi da Masha Allah, Kallona na maida ga wata dattijuwar Mata,dake Zaune, ta tanƙwashe ƙafafunta,itama kyakkyawar mace ce, Fara ƙal da ita don da ka ganta kaga cikakkiyar buzuwa,ga idanunta dara_dara don idan ka kalli idanunta baza ka, taɓa cewa bata bata gani da su ba, Saboda buɗe suke tarau dasu, itama,da ka kallesu Mamma da Muneebba suna kama Sosai saidai Haske da Mamma ta ɗarata,ga diri ba'a cewa komai kanshi, Tana Tsaye ne taji an tafka mata Dundu a baya, juyowa tayi a hanzarce tana faɗin "Kai fa Yaya Khabir wallahi ƙetarka tayi yawa kana shigowa kawai sai ka wani sakar man Dundu a baya," ta faɗa kamar ta fashe masa da kuka, Fashewa da dariya yayi yana faɗin "Nifa kawai gaisuwa ce na miƙo amma har zaki gwada mana halin auta," Kallonshi tayi tana turo baki tana faɗin "nidai yanzun ina Alƙawarina? wanda ka ce zaka tafo man da shi," Kallonta yayi yana faɗin "Au ke nayi mawa ma kenan? Ni Mamma nayiwa bake ba," ya faɗa yana tunkaro inda Mamma ke zaune,yana Zuwa ya zauna kusa da ita yana Mammatsa mata ƙafafu,Murmushi tayi tana dafa kanshi tana faɗin "Allah yai maku Albarka Khabir haƙiƙa kunyi man Abinda dukkan ƴaƴa ya kamata ace sunyi wa Mahaifansu yadda kuka yi man Ubangiji ya baku mai yi maku kuma," Da Ameen Suka Amsa Khabir na faɗin "Mamma koda yaushe cikin sa mana Albarka kike, tabbas munyi dace da Mahaifiya ta gari wacce ta zauna ta bamu tarbiyya ta ilmantar damu, Sannan dukda Zagin da ake mana a gari na cewar mu dukkammu bamu da Uba,hakan baisa kin bi takan zantukan Mutane ba kikan haƙuri ki danne wa Zuciyarki,kota wannan ɓangaren kin koyar damu iya Zama da Mutane Sannan Uwa Uba haƙuri da juriya, Ƙara Shafa kanshi da na Muneebba tayi tana faɗin "Saka Albarka wa Yaranka a koda yaushe shine zai sa Allah ya kareshi daga dukkan wata taɓarɓarewar Rayuwa, Tabbas wasu iyayen suke Rusa Rayuwar ƴaƴansu da kansu ta hanyar zagi da la'anta, zaka ga Abinda baikai ya kawo ba, Uwa zata jefi yaronta da Mugun kalami, kuma wannan babban kuskurene mu iyaye muke aikatawa,zaka ga yaro Tun yana ƙarami, Idan yai wani abun zata kirashi Sakarai, ko ɗan banza da sauransu dai,haka zalika tarbiyya ita ce jigon Rayuwa, tabbas duk macen da bata ma yaranta tarbiyya ba bata ceto Rayuwarshi daga hanyar lalacewar zamani ba,kuma ki sani duk wani Abu da kika ɗora yaronki da shi to tabbas da kalar halayyar zai tashi, idan hallayar kirki gareki to da ita zai tashi ko kuma akasin hakan,haka haƙuri shine jigon rayuwar zaman duniya,indai kana da,haƙuri tabbas zaka ci ribar rayuwar zaman duniya, duk mai haƙuri zai dace,sannan juriya da jajircewa kan abinda yake dai_dai,shine zai sa kakai dukkan wani mataki na Nasara wanda yake dai_dai,sannan ina sake gargaɗarku da karku sake ku biye Zancen ta Mutane,Don idan ka biye ta mutane wannan shi Ake kira ba shiga ba fita wai an saka mahaukaci a gadin ƙofa," Mamma ta ƙarashe zancen da sakin Murmushi, Dukkansu Ajiyar Zuciya Suka sauke Suna mai tsananin jin ƙaunar Mahaifiyarsu, gefe guda ga kuma tausayin halin da Suka tsinci kansu a ciki, dogon numfashi Khabir ya sauke yana faɗin "shiyasa a kullum muke ƙara gode wa Allah muke kuma ƙara gode maki, bi ga hanyar Turbar da kike ɗoramu," Murmushi Mamma tayi tana faɗin "ga kiran Sallar Ishsha'i can Maza tashi ka tafi Masallaci, Sannan ka dawo kaci Abinci," Da To ya Amsa yana miƙewa,Sannan yace "Auta tashi ga Alƙawarinki na kawo maki, Sannan kije ki dafa man Ruwa ina son dana dawo nayi wanka," ya faɗa yana miƙo mata ledar hannunshi, Amsa tayi tana zabga mashi godiya har sai da ya ɗallar mata baki sannan tayi shiru, Yana fita ta ajiye ledar ta Taimaka ma Mamma ta tashi suka kabbara Sallah, saida Sukayi Shafa'i da Wutiri Sannan Muneebba ta tashi ta haɗa ma Khabir Ruwan wanka,tana gamawa yana shigowa,kai Tsaye bayi ya shige, ita kuma ta dawo ɗakin ta Zauna tana jawo ledar da Khabir ya bata, Tana buɗewa ta haɗiye wani miyau don ganin balango mai zafi ga sai ƙamshi yake,ɗaukar Naman tayi takai bakin Mamma, kaucewa Mamma tayi tana faɗin "Auta ki ci Ni na ƙoshi," Ɓata rai Muneebba tayi kamar Mamma na ganinta,ta ce "Mamma idan dai baki ci ba Allah nima bazan.ci ba," Jin hakan yasa Mamma amsa don tasan muddin bata ci ba itama Muneebba baza ci ba, saida suka cinye tare da Mamma Sannan Muneebba ta ƙyale Mamma,Ruwa masu sanyi a randa ta ebo mata tasha sannan itama tasha, Koda Khabeer ya fito ya zauna ya gama cin Abinci Sannan ya zauna wajen Mamma tanata basu labarirrika masu daɗi,wanda cikin labaranne take ƙara Nusar dasu Abu mai kyau da kuma Marar kyau, Sai wajen 9:30 sannan Khabir yai masu Sallama ya shige ɗakinshi don yin Bacci. Itama Muneebba Zuwa tayi ta ɗaura musu Net Sannan ta zo ta kama hannun Mamma tana taimakamata ta shige ta kwanta,Suna kwanciya ana ɗauke Nepa, Saboda iskan da ake tayi, maƙalƙale Mamma Muneebba tayi tana jin tsoro, a ɗaɗɗare bacci ya ɗauketa, ita kam Mama bacci ya kasa ɗaukarta,Tunaninka ta dunga yi, wanda ya dinga Tuna mata Rayuwar baya,tunawa tayi da yadda kullum yaranta ke cikin hantara da kuma zagi na cin Mutumci,ga kullum a cikin yi masu gorin Uba ake duk ta sanadiyyarta,hawaye ta dinga jin na bin kuncinta ********************** Saukowa take daga Step ɗin benen, cikin ƙarar takalminta mai tsini a haka harta ƙarasa saukowa daga kan benen Zuwa Falon nata, Kallon Riɗa_Riɗan matan dake Zaune a Falon take, ko waccensu da manyan Wayoyi Suna sarrafasu cikin gwanancewa,yadda suka maida hankalinsu a kan waya kai kace karatun ƙur'ani ne Suke, Itama Dattijuwar zuwa tayi ɗaya daga cikin Manyan kujerun Falon tayi ta zauna, Tana ɗaukar Wayarta, ta fara Operating ɗinta cikin gwanancewa,a Haka dukkansu suka ɗauki tsawon 30 minutes babu wacce ta ɗago daga Abinda take yi,daga Su har Mahaifiyarsu hankalinsu ya karkata kan Wayar da ke hannunsu. Tunda Kyakkyawan Dattijon ya shigo ya Zuba musu idanu dukkansu,yana kallonsu,koda yaushe yaga iyalinshi,cikin wannan ɗabi'a da Mahaifiyarsu ta ɗorasu bisa kanta ya kanji ya shiga damuwa sosai, Sallama yayi har sau biyu Sannan Mom ta ɗago tana amsa mashi, daga bisani kuma ta maida hankalinta kan Wayarta............✍️ Wannan kenan *Comment Shine karsashin Dukkan Marubuci,So Comment, Share fisabilillah* Waɗannan sune ƙwarin gwiwata *Daga Alƙalamin Riamcool* *08109554986* [5/21, 8:05 PM] RIAMCOOL: *BAYAN WUYA* * Book 1 *By Riamcool STAR OF THE SQUAD* *MIKIYA WRITER'S ASS* *Bismillahirrahmanirrahim* Page 3&4 _________✍️girgiza kansa kawai yayi ya haura sama Zuciyarshi na mashi zafi bisa ga halayyar Matarsa,ya san da cewa Uba shi ke zaɓar ma ƴaƴanshi Uwa ta gari amma shi sam baiyi da cen Mata ba dukkan yaranta babu wanda ta Koyar da shi tarbiyya,kowa dukkan abinda yaga dama shi ya keyi,shiya sa ga Matannan duk wacce aka aura sai ta dawo. Tunda Dad ya shiga Mom tana nan tana danna Wayarta bata tashi ko sannu batayi mashi ba ballantana ta tashi tabi bayanshi. Kwance yake bisa tamfatsetsan gadonshi, ya lumshe idanuwanshi, Kyakkyawan Saurayi ne ajin farko,wanda kallo ɗaya zakayi mashi kasan cewar ya kai duk inda ake son ɗa Namiji ya kai,yana da kyakkyawar ƙira irin ta ƙarfafan Maza, dogo ne, fari tas da shi, yana da kwarjini duba da yadda ya haɗe rai kamar bai san miye dariya ba, ƙarar wayarshi ne ya saka shi buɗe lumsassun idanunsa masu kama da na Mage,a hankali yasa hannu ya ɗauki wayar yana yatsina Fuska,ko duba sunan waye ke kira bai tsaya yi ba, yana ɗagawa yaji anyi shiru,shima shiru ɗin yayi na tsawon wasu mintuna,har zai kashe Wayan yaji Muryan Dad yana faɗin "Son duk inda kake kazo ina nemanka," "Ok Dad," shi kaɗai ne abinda ya furta kamar wanda akayiwa dole,ajiye wayan yayi yana ƙara ɓata fuska yana motsa ɗan ƙaramin bakinshi me ɗauke da pink lips,tashi yayi ya shiga Toilet yayi wanka sannan ya fito ɗauki Lotion ɗinsa masu daddaɗan ƙamshi ya shafa,kai tsaye wajen Wardrope ya wuce, kaya ne jere kala_kala, ko wanne da ɓangarensa,ƙananun kaya ya zaɓo wanda zasu amshi jikinsa, a gurguje ya shirya ya fito Securities ɗinsa na take masa baya,da sauri wani security ya buɗe masa Mota ya shiga Driver na jar Motar, cikin shakku Driver ya ce "Sir ina muka nufa?," Da hannu yai mashi alamar inda zasu nufa, kaɗa kanshi Driver yayi ya maida hankalinsa kan aikinsa Haka har suka isa Tamfatsetsan gidan nasu, danna Horn Driver yayi,da gudu masu gadi suka wangale masu makeken get ɗin,suna shiga Driver yai parking da gudu Security yazo ya buɗe masa Motar, a hankali ya zuro ƙafarshi guda, sannan ya ziro ɗayar ya fito cikin Izza da ƙasaita,da kuma taƙama,tafiya yake irin ta ƙarfafan Maza masu ji da kansu, a haka har ya iso Side ɗin Mom, Yana shiga ya harɗe hannuwanshi a ƙirji yana kallonsu da ɗai_ɗai,gyaran murya yayi wacce ta maido da hankalinsu daga kan Abinda suke yi,har Mom da sauri Mom ta taso tana isowa wajenshi tana faɗin "Son miye haka kayi? Kai daga yi maka Maganar aure shine zaka ɗauki fushi dani har kai ƙaura daga gidannan,kasan kuwa irin tashin hankalin da na shiga?," Ta faɗa tana kafeshi da idanunta, A hankali ya buɗe Bakinsa yana faɗin "afuwan Mom," yana gama faɗa ya haura Sama,da Sallama ɗauke a bakinsa ya shiga,ɗagowa Dad yayi Fuskarshi ɗauke da yalwataccen Murmushi ya amsa,zama ƙasa yayi yana tanƙwashe kyawawan ƙafafunsa, Sannan ya gaishe da Dad,amsa masa yayi cikin kulawa yana maido da hankalinshi kanshi," bayan wasu ƴan Second Dad yai gyaran murya yana faɗin "Son miye hakan da kayi? Tsawon 2 weeks baka ɗaukar Wayar Mom ɗinka sannan kabar gidan, dama kaga za'a isheka shine ka kashe Wayoyinka gaba ɗaya ba'a samu,saida na dawo jiya Mom ɗinka ke faɗa man daga tayi maka Maganar aure shine kayi fushi da ita, kana tunanin abinda ka aikata kayi dai_dai kuwa? Ka sani ita Mahaifiya sam ba'a musu da maganarta ballantana har kayi fushi da ita,kasan kuwa iya baƙincikin da ka ƙunsa mata? To maza _maza ka nemi yafiyarta idan ba haka ba kana cikin fushin Ubangiji," ɗago kanshi yayi a hankali ya ce "ayi man Afuwa Dad insha Allah zan nemi yafiyarta,kuma insha Allah hakan bazai sake faruwa ba," "Yawwa ko kaifa Son Allah yai maka Albarka," Dad ya faɗa yana sakin Murmushi Tashi yayi ya fito ya samu Mom zaune ta zuba uban tagumi,a hankali ya tako yazo ya sauke mata hannun daga tagumin da tayi, kallonta yayi yana sakar mata Murmushi sannan ya samu waje kusa da ita ya zauna, sadda kanshi ƙasa yayi yana faɗin "Mom ina mai neman gafararki da ki yafe man akan abinda na aikata maki," Murmushi ta saki tana faɗin " na yafe maka *ASAD* dama ni ban riƙeka da komai ba,Matsalata guda shine rashin amincewarka ga wannan auren," ta faɗa fuskarta ɗauke damuwa Sosai "Indai aure ne damuwarki Mom na amince zan auri Maheer," ya faɗa yana mai tashi daga Falon ya haura zuwa ɗakinsa Kowa na Falon da Mamaki ya bishi,ganin yadda ya amince cikin sauƙi haka don ko ita Mom batayi tunanin zai amince ba,ɗaya daga cikin Matan dake zaune su Ukku, wato Suhaima ta ce "anya Mom bada wata a ƙasa ba? ace Yaya Asad shine ya amince da wuri haka," ta faɗa fuskarta na nuna Alamar tantama. *MUNEEBBA* Tunda sanyi safiya da ta tashi ta kammala ayyukanta da wuri komai ta riga da ta kammalashi, a gurguje ta shirya ta nufi islamiyya,tafiya takeyi sam hankalinta baya tare da ita ta lula wata duniyar ta tunanin Rayuwa,batai aune ba taji ta ci karo da Mutum,ƙamshin Turarensa ya tabbatar mata da ko wanene, a hanzarce ta ɗago dara_daran idanunta tana kallonshi......✍️. Wannan kenan *Comment *Comment Shine karsashin Dukkan Marubuci, So Comment, Share fisabilillah* Waɗannan sune ƙwarin guiwata *Daga Alƙalamin Mariam sani✍️* *08109554986* [5/21, 8:07 PM] RIAMCOOL: *BAYAN WUYA* *BY RIAMCOOL* *MIKIYA WRITER'S Ass* *بسم الله الر حمن الر حيم* *Page* 5&6 ___________✍️A hanzarce ta ɗago dara_daran idanunta ta saukesu akan Nazeer wanda ya kafeta da idanu yana sakar mata lallausan Murmushi,itama murmushin ta sakar masa tana gaida shi, sannan ta turo ɗan ƙaramin bakinta tana faɗin "jiya fa da naita kiran wayarka ban samu ba,gashi kamin alƙawarin zaka zo," ta faɗa tana sake turo ɗan mitsilin bakinta wanda turosa ya zame mata al'ada, Murmushi yayi yana faɗin "kinga yanzun jeki islamiyya idan kin dawo mayi magana." Sallama sukayi cikin shauƙi da ƙaunar junansu,tunda taje islamiyya taketa walwala,don yau batama wani nuna damuwar kyaran da ƴan ajin nasu ke mata ba, Hafsat dake zaune kusada ita ce ta kalleta tana faɗin "waini yau Muneebba wane albishir aka miki ne? kike ta faman farinciki haka." juya fararen idanunta tayi tana faɗin "wannan ai yama fi albishir ɗin Hafsat saboda na haɗu da farincikina Nazeer," ta faɗa tana mai ƙara sakin wani murmushin kallonta Hafsat tayi tana mai girgiza kai saboda tana tausayin ƙawarta akan mugun son da take yiwa Nazeer ɗin, saboda tasan halin mahaifiyar Nazeer ɗin yadda ta tsani talaka, "Allah dai ya barki da Nazeer ɗin nan Muneebba,amma fa wannan son da kike masa yayi yawa Allah." ɓata fuska Muneebba tayi tana faɗin "kinga Hafsat idan ba zaki ƙara ƙarfafa man gwiwa akan naso Nazeer to ƙara kawai kiyi shiru." "Allah ya baki haƙuri keda kan Nazeer sai ki ƙulla gaba da mutum." banza Muneebba tayi mata har aka tashi babu wanda ya kula wani,saida kowa zata shiga lungun gidansu sannan Hafsat tayiwa Muneebba Sallama shima Muneebba nata fushi ta amsa, sannan shiga wani ɗan ƙuƙut ɗin lungu wanda duka gidajensu na marassa ƙarfi ne,wani ɗan ƙaramin gida da yafi na lungun nasu lalacewa naga ta duƙa ta ɗage zanen da suka lulluɓe ƙofar ta shiga da sallama ɗauke a bakinta ta shiga cikin gidan, Sallama tayi taji tsit hakan ya tabbatar mata da Mamma ta shiga lazimi,wucewa tayi ta cire uniform ɗin, wayarta ta ɗauko INFINIX HOT 10 wacce Nazeer ɗin ya siya mata, Number Nazeer ta dannawa kira,saida tayi 3 miss call sanna ya ƙara kira,sosai tai mashi ƙorafi ya lallasheta sannan suka ci gaba da hira da junansu cikin so da ƙaunar junansu, a ranar ne kuma Nazeer ɗin zai ako gidan su Muneebba, sosai ranar Muneebba ta yini cikin farinciki da murna *Bayan kwana biyu* sosai Muneebba ke murnar saka musu baiko da akayi da Nazeer, saidai matsalarta guda ita ce Mahaifiyarsa,don tayi mata warning yafi a ƙilga akan ta rabu da Nazeer amma taƙi, don saida Baban Nazeer ɗin yai mata jan ido sannan ta bari akayi baiko amma ta ci alwashin bazata taɓa bari Nazeer ya auri Muneebba ba, Kwance take bisa cinyar Mamma, Mamma na mata fira tana dariya, shigowar Mutum suka ji babu ko Sallama, ɗaga kanta Muneebba tayi taga Maman Nazeer ce,miƙewa tayi tana ce "Hajiya ina yini" "dalla rufe man baki da ban yini ba kin ganni, Warning nazo buge miki, akan ki ni sanci kanki da yarona,don bani son haɗa jini da marar asali da galihu,ku ɗin nan da ba'a san asalinku ba anfi danganta ku da ƴaƴan shegu, to wallahi na faɗa akan ki auri Nazeer ƙara na saka a nakasa ki,na faɗa miki karma ki ce ban faɗa miki ba" sosai maman Nazeer ta ciwa Muneebba da Mamma mutunci tana gamawa ta kaɗa bujenta ta ƙara gaba faɗawa jikin Mamma Muneebba tayi tana fashewa da wani Matsanancin kuka ta ce "Mamma shin laifi ne danna auri Nazeer saboda ina Talaka, me yasa ake ƙyamar Talaka? talaka yafi kowa ƙasƙanci a gurin wasu masu kuɗi ne???, ni ɗinnan Mamma saboda na kasance talaka kuma marar Mahaifi shiyasa nake shiga cikin tozarcin Al'umma" ta faɗa tana sake fashewa da matsanancin kuka a faƙaice Mamma ta share hawaye tana murmushin takaici ta ce " ko kaɗan Muneebba ke ɗinnan baki rasa uba ba kina da cikakken uba nagartaccen Mahaifi,da Mutane sunsan wanda ya haifeku da ba zasu kuskura ko kallon banza suyi maku ba, sai dai ko wane bawan da tashi ƙaddara mu tamu jarabtar kenan,kiyi haƙuri komai lokaci ne" "Mamma kullum ce mana kike inada uba kuma yana raye, me yasa ya zaɓa mana wannan tozarcin me yasa bai nemu ba duk tsawon shekaru, shin anya uba ne??? bana tunanin cikakken Mahaifi zai iya ƙyale yaransa suyi rayuwan tozarci a cikin Al'umma,Mama naji na tsani Mahai......." wata uwar tsawa Mamma ta daka wa Muneebba daya saka ta yin shiru, cikin matsanancin ɓacin rai Mamma ta ce "kina da hankali ? zaki ce kin tsani Mahaifinki wanda ya kawoki duniya,to karna sake ji idan ba haka ba ranki zai yi mummunan ɓaci" Mamma ta faɗa cikin ɓacin rai Kallonta Muneebba tayi ta ce "Mamma hakan bazai ƙara fitowa daga bakina ba kiyi haƙuri,amma har yanzun kina son wanda ya banzatar dake a rayuwa yaja miki tozarci a cikin Al'umma ya ci amanarki........" "Muneebba!!!! bana son wannan zancen ya ƙara fitowa daga bakinki ki" sosai Mamma take yiwa Muneebba faɗa hawaye kawai ta share tana tashi ta shige ɗaki,ji tayi duniyar yai mata zafi da ɗaci ta ƙara jin tsanar Mahaifinta fiye da kowa na duniyar dukda bata sanshi ba sai dai a labari, sosai take kuka,kukan da ya zame mata jiki a duk lokacin da irin wannan abun ya faru, sosai take baƙin ciki yadda Mamma ke son Mahaifinta har yanzun sosai take ganin tsantsar ƙaunar mahaifinta a idon mahaifiyarta, ita dai har abada ba zata taɓa son mahaifinta ba.........✍️ *Wai minene asalin su Muneebba,me yasa ta tsani mahaifinta insha Allah a next Page zamu ji mafarin lamarin* Wannan kenan Comment Share fisabilillah *Waɗannan sune karsashin Dukkan Marubuci* *By Riamcool, Star of the Squad* Only Call *08109554986* [5/21, 8:07 PM] RIAMCOOL: *BAYAN WUYA* Book 1 By Riamcool *MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION* *بسم الله الر حمن الر حيم* *Page* 7&8 *WAIWAYE* *Wacece Mamma* Mamma dai ƴa ce ga Malam Shitu wanda ƴan asalin garin Agadaz ne su biyu iyayensu suka haifa shi sai yayarsa Ladiyo wanda sai da Ladiyo tai aure sannan Allah ya amshi ran iyayensu, hakan yasa Ladiyo ɗaukar Shitu a hannunta dan akwai tserayya sosai a tsakaninsu haka ya taso a gurinta harya isa munzalin aure Ladiyo wata irin muguwar mace ce tun tasowarsu ba wani ƙaunar Shitu take ba, hakan yasa ta dinga gallaza masa, har kawowar Samartakarsa, koda Shitu ya gwada mata aure yake so hakan yasa tace zata samo masa Mata shi kuma ya gwada mata a'a, hakan yasa ta barshi yai aurensa inda ya auri Mariya wacce Kyakkyawar buzuwa ce, koda aka auro Mariya sai da Ladiyo ta dinga gallaza mata tana bata azaba harya kai ta samu ciki ta haifi ƴarta wacce taci sunan A'isha, kowa cikinsu ba daɗin zama da Ladiyo yake ji ba, don dama tuni Mijinta ya rasu ta dawo da zama gidan Shitu hakan yasa ta ƙara gallaza masu, don tuni ta mallake Shitu da Mariya duk abinda tace ayi shi za'ayi, gadon Shitu na raƙumma dukta cinye, har Shatu ta fara girma bata canza zani ba, don Ai'shatu tafi kowa cin wuyar Ladiyo, ganin a ɗan kwai sauran dukiyar Shitu yasa Ladiyo ƙwaceta suna bin ƙasa_ƙasa suna kasuwancin siyar da dabino, A hankali take tafiya cikin Sahara ranga_ranga kamar zata faɗi, saboda zafi da ranar da ake ƙwalawa,ga ƙishin da take ji wanda shine ya ida tagayyarar da ita, so take ta tsaya ta huta amma babu halin hakan saboda wata matsananciyar rana da ake ƙwalawa,ga yashin sahara kanshi ya ɗauki zafi, bare ta zauna ta huta,ga fitinannanen ƙishin daya addabeta wanda shine ya ida galabaitar da ita da yunwar dake ƙwaƙwular hanjin cikinta, a haka harta iso inda mahaifanta suka yada zango,sun kafa runfa a wajen A galabaice ta iso wajen tana kamfatan ruwa domin ta kai a bakinta, kofin dake hannunta taji an kwaɓe ruwan ya zube a ƙasa, kallon ruwan take yadda ƙasan wajen ya shanye,kuma tayi imani waɗannan ruwan da suka zube ba lallai ta sake iban waƴansu tasha ba, hawaye taji ya cika mata ido ɗago da fuskarta tayi tana duban iyayenta waɗanda suka kauda kansu a gefe guda suka nuna kamar ma basu ga abinda Yaya Ladiyo ta aikata ba, durƙusawa wajen tayi tana share hawayen da suka samu damar gangarowa a kuncinta, a hankali ta samu waje ta sulale tana mai ƙara jin yadda maƙoshinta ya ƙara ƙafewa yana buƙatar ruwan da zai shiga a ciki gashin kanta taji Mamma Ladiyo ta kamo tana jansa da ƙarfi,wanda ya sakata ƙwalla uwar ƙarar azaba, mari taji ta kira mata tas, wanda yasa fatar wajen tai jajir shatin hannuwa ya fito ruɗu_ruɗu cikin ɓacin rai Mama Ladiyo ta dubeta tana faɗin "Shatuwa tun yaushe kika fita saido hatsi a cikin gari? tunfa jiya kamar yanzun tunda kika fita baki dawo ba sai yanzun, ki faɗa man wajen uban wa kika je ya ƙwaƙuleki, jibi yadda Nonuwanki suka sakaka duk an latse su" ta faɗa tana sake faska mata wani marin wanda yasa bakinta fashewa mahaifanta kuwa sun sadda kansu ƙasa, duk wani mari da Ladiyo tayi mata sosai yake sake sake tsarga musu zuciyoyi, basu da wani halin yin magana don mugun shakkun Mamma Ladiyo da suke ji, ita kam A'ishatu wani marayan kuka ta saki tana mai dafa ƙafar Mamma Ladiyo tace "Mamma Ladiyo dan Allah kamar yadda Allah ya temakeki nima ki taimakeni ki bani ruwa da Abinci idan ba haka ba mutuwa zanyi,kuma na rantse miki da Allah ni babu Namijin daya taɓa taɓa man koda ɗan yatsa" ta faɗa da ƙara fashewa da wani irin marayan kuka wanda da kajishi kasan mai yinsa yana fitar da ɗaci da kuma raɗaɗin zuciya ne Ƙafa Mamma Ladiyo tasa tana shure A'ishatu sannan ta ɗaga hannunta mai kama da diga ta ɗaka mata duka a baya wanda yasa cikinta wani irin juyawa bayanta ya riƙe daga duƙen da take ta dinga sheƙa Amai wanda har ta hanci saida ya dinga biyowa dukda ba komai a cikin sai wa ƴansu korayen ruwa da take amayowa kai kace zata zubda ƴan cikinta wani shurin Mamma Ladiyo ta ƙara kai mata wanda yasa numfashinta tsayawa cak idanunta sun wani ƙaƙƙafe, da gudu Mahaifanta suka yo kanta suna kuka wanda kallo guda Mamma Ladiyo tai masu suka janye idonsu daga gareta hawaye na bin kuncin Maman A'ishatu Mariya jawota tayi yadda ta sume ta sakata cikin yashin saharan wanda cikin iyayenta ba wanda ya iya magana ko wane abin na ci masa rai A hankali zafin rana ya fara dukanta wanda kamar ya gasata buɗe lumsassun Idanunta tayi ta ganta cikin rana yashe jikinta na mata tsami ta miƙe tana duƙawa a inda take, don tasan babu damar shiga tantin da suka kafa, don Mamma Ladiyo ba zata barta ta shiga ciki ba koda kuwa Mutuwa zatai hakan yasa ta zama cikin ranar wani masifaffen zazzaɓi na rufeta har dare yayi tana makyarkyatar sanyi wanda yasata yin baccin dole sai safe ta farka A hankali ta buɗe idonta ta miƙe jiki ba ƙwari abinda ta gani ne da kuma Ihun Mamma Ladiyo da take ji ya sakata ware ido tana ƙara duban jinin data gani malale da gudu ta miƙe ta shigaTantin sai dai tana shiga turus tayi tana ƙara ware idonta ganin Iyayenta kwance anyi musu yankan Rago ga Mamma Ladiyo zaune tana sharce hawayen ƙarya wata kalar ƙara A'ishatu ta saki tana sumewa, ganin haka Mamma Ladiyo zuwa ta ɗauko ruwa ta malaya mata don karta zargi wani abun, don kuwa Mamma Ladiyo ce tabi dare taiwa su Malam Shitu yanakan Rago, koda Shatu ta tashi haka ta dinga jan ajiyar zuciya tana saukewa dan ko kukan ya kasa fita sai dai bin ko ina da kallo da take yi, ganin haka Mamma Ladiyo ta rarrasheta tace mata ɓarayi ne suka zo suka yanka su saboda kuɗaɗen dake garesu da suka ƙi badawa, ita kuwa ta bada nata harda na fansar A'ishatu shi yasa basu kashesa ba ko kallonta Ai'shatu ba tayi ba hakan yasa Mamma Ladiyo fita cikin gari ta samo waɗanda zasu sallaci Shitu da Mafiya, A'ishatu naji na gani aka binne iyayenta haka rayuwa taci gaba da tafiya ba wani sauyi, illa sauyin Azaba daya ƙara nunkuwa wa Shatu, haka rayuwa ta tafiyarwa Shatu wanda Mamma Ladiyo tun sadda ta kashe su Shitu ta tattara suka koma Kaduna da zama, can take sana'ar siyar da Abinci tana ɗorawa Shatu talla sannan da dare ta ɗora mata tallar goro, wanda ƴan iska sukai wa Shatu caaaa ko wane da baƙin ƙudirinsa a kanta, wanda sai dai A'ishatu tai kuka ta share hawaye tana ƙara kaiwa Allah kukanta ganin yadda ɓata gari ke kawowa Shatu farmaki yasa Mamma Ladiyo jin daɗi hakan yasa ta ƙara kaimi wajen ɗora mata tallar dare kuma idan bata saido shi ba haka zatai mata shegen duka kuma ranar sai tayi mata tsarki na kwaɓaɓɓen barkono Wannan kenan A dage da comments *By Riamcool Star of the Squad* [5/21, 8:08 PM] RIAMCOOL: *BAYAN WUYA* *Book 1* *By RIAMCOOL STAR Of the Squad* *MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION* Bismillahirrahmanirrahim *P.9&10* _________✍️Haka taita gallazawa Shatu azaba kala da kala, da daddare idan ta fita talla goro haka zata daɗe bata saido ba wanda kowa zai siya saiya nemeta da iskanci ita kuma taƙi,hakan yasa take cinɓun goro kuma idan ta koma ba zata canza zani ba daga azabar Mama Ladiyo Tunda ta taho take sharan hawaye don tasan muddin ta koma da goron da bata saido ba sai Mama Ladiyo ta ninka mata azaba fiye data kullum dama da zata fito saida tai mata jan Warning saboda rashin saido goron dare ko abinci tabar bata, sai dai tabi dare ta kankari ƙanzon tukunya tasha ruwa ta kwanta tayi nisa cikin tunani ga dare daya fara ritsawa taji an rufe mata fuska an ɗauke ta ihu take son yi amma babu halin haka saboda rufe mata fuska da akayi, wani kango suka kaita suna ajiyeta wuf tayi ta mike tana cire abinda suka rufe mata fuska dashi kwaɗa mata Mari ɗaya yayi wanda ya sata kwala ihu da ƙarfi, fusata ɗayan yayi ya ƙara faska mata wani marin yace "don ubanki yi mana shiru uban wani yasa iyayen naki su doro miki tallan dare? to wallahi ba zamu iya maida kwaɗayimmu ba dole sai mun tasta ki" ya faɗa yana zuge mazagin wandonsa Ihu ta ƙara fasawa cikin gunjin kuka mai cin rai tace "dan Allah bawan Allah ka dubi girman Allah ku ƙyaleni wallahi ni marainiya ce kada ku yaga man mutuncina da darajata" ta faɗa tana sake fashewa da wani irin masifaffen kuka tunda ya doso wajen yake jin kukan mace cikin kango na tashi sharewa yayi zai wuce sai kuma yaji ba zai iya ba hakan yasa shi kutsa kai cikin kangon, turus yayi yana kallonsu da ɗai_ɗai ganin ɗaya daga cikinsu yana kokarin yaga mata kayan jikinta tana roƙonsa wata zuciya ce ta ciyosa ganin yadda Mutumen ke ƙoƙarin keta mata haddi, nufar wajen yayi yana kaiwa wancan bahaggon naushi wanda yasa shi ƙwalla ƙara har haƙoransa biyu na zubowa, ganin haka wancan ɗayan da gudu ya taketa ya fice, cikin ɓacin rai Mahamud ya shaƙo wuyan rigar wancan yana naushi sai da ya haɗa masa jini da majina sannan da ƙyar ya ƙwaci kansa ya gudu, ita kau Shatu ta rakuɓe waje guda tana gunsheƙar kuka, a hankali ya tako gareta cikin takonsa mai cike da izza ya nufota yana faɗin "miƙe" babu musu ta miƙe suna fitowa daga kangon, tana fitowa taga yadda tiren goron duk ya watse wani kukan ta sake saki tana faɗin "na shiga ukku nasan na koma wallahi sai ta kusa kasheni ƙara karna koma na kwana anan" ta faɗa da wani sabon tashin hankali wanda ya bayyana ɓaro_baro a. fuskarta, da mamaki yake kallonta ya tambayeta akan me take magana, nan ta kwashe komai ta faɗa masa da kalar azabar da zata fuskanta idan ta koma girgiza kansa yayi yana cije lips ɗinsa na ƙasa yana mamakin mugun halin wasu mutane cikin tausayinta ya tambayeta goron na nawa ne, ta faɗa masa na 1k ne, hannu yasa Aljihu ya zaro 3k yana miƙa mata zaro ido tayi tace masa ba zata karɓa ba, wanda da ƙyar ya samu ta amshi 1k da kanshi ya talata gida wanda har Mamma Ladiyo ta kulle gidan tana baccinta hankali kwance, cikin bacci ta taso ta buɗe mata tana shiga ta maida gida ta rufe tana jawo hannu A'ishatu tare da ɗakko wani makeken faskare ta miƙo mata hannu tace "bani kuɗin goron kada ma kice man wani abu ya bata a ciki dan tsab zan iya bazar dake anan ki mutu ubankowa ya huta" jikin Shatu na kyarma ta fito da Naira dubun ta bata wanda ya sata washare haƙora tana amshewa ta miƙe, babu tuhumar inda ta tsaya har dare yayi, tashi tayi ta tafi ta kwanta, ita kam A'ishatu sai da Mama Ladiyo tai bacci sannan tabi dare tana kankare ƙanzon tukunya taci tasha ruwa ta kwanta tunda sadda A'ishatu suka haɗu da Muhammad yake jin bala'in tausayinta hakan yasa da yaga ta fito tallan goro zai mata juye ya bata kuɗin ta koma gida wanda yaiwa Mama Ladiyo mugun daɗi don a tunaninta iskanci Shatu keyi tana siyar da goron, yau da gobe shaƙuwa ce mai karfin gaske ta shiga tsakanin Muhammad da Shatu wanda harya kaisu ga faɗawa soyayya mai ƙarfi wanda hankalin Shatu ya fara kwanciya, nan take ya ɓullo mata da son aurenta zaiyi ta biyu da ita don yana da Mata harda yaro guda, ba tare da wata nuna damuwa ba ta amince masa sai dai matsalarta guda a lokacin ita ce Mama Ladiyo, wanda tunda ta tunkareta da maganar aure Mama Ladiyo tai mata jan Warning akan ta rabu da Muhammad ba shine mijin daya dace da ita ba don ta riga tai mata Miji ɗan Aminiyarta Jimmai wani ɗan shaye_shaye ne, kuka sosai Shatu tayi tana roƙon Mama Ladiyo akan ta barta ta auri Muhammad amma fir taƙi saima horon kulleta a ɗaki da tayi ta ɗaureta da sarƙa wai damma kada ta gudu shi kam Muhammad tun sadda Shatu ta faɗa masa abinda Mama Ladiyo tace hankalinsa yai mugun tashi, babu yadda baiyi ba har da kanshi yaje gun Mama Ladiyo don ta barshi ya auri Shatu amma fir taƙi saima ƙarin cin mutunci da tayi masa *wanene Muhammad* Muhammad ɗa ne ga Alhaji Alhassan mai gwalagwalai Mahaifinsa mashahurin mai arziƙi ne inda ya auri Mahaifiyar Muhammad Hajiya Zinatu wacce babu ruwanta suna zamansu lafiya da mijinta harta haifi Khadijah ita ce ƴarta ta farko sannan ta haifi Sagir sannan Abdulkarim sannan autanta Muhammad wanda shima yai karatunsa har yai digiri ɗinsa, sannan ya auri Mansura wacce ita ce ta liƙe masa harya aureta suna da ɗansu ɗaya, haɗuwarsa da Shatu ita ce ta fara sauya masa rayuwa ta maida shi mai son jama'a da son taimakon Al'umma ta maida shi mai wasa da dariya ga dukkan wanda ya gani cikin ƙunci, ya faɗa cikin tarkon sonta da ƙaunarta haka zalika da son kasancewa da ita yai kwaɗayin zama da ita,ya bata ilimin da bata samu ba, wanda kullum cike yake da mafarkin son kasancewa a tare da ita sai dai kash Mama Ladiyo ta riga tai mai katanga da dukkan wani cikar burinshi akan Shatu, ya shiga cikin damuwa sosai harya kai ga ko walwala ba yayi ɓangaren Shatu ma haka yake kullum cikin kuka take wanda ta ida lalacewa tai baƙi ta ƙara rama, amma a haka Mama Ladiyo babu tausai ta saka Sati guda da bikin Shafu da Idi ɗan Jimmai, hankalin Shatu ba ƙaramin sake tashi yayi ba, tana ji tana gani aka ɗaura mata aure da Idirisa wanda taci kuka ta tabbatar data riga ta rasa gatanta iyayenta, haka aka kaita gidan Idi wanda shima ya ƙara zame mata baƙin kurkuku wanda kullum cikin cin dukan Idirisa take ga cin zalinta da yake dan ko kwanciyar aure sai dai ace fyaɗe yake mata wanda ta ƙara lalacewa sosai ga shaye'_shaye da yake wanda har giya yake sha idan ya shawo haka zai zo ya malaya mata Amai a yace kuma dole sai ta shanye sa,idan taƙi yai mata ɗan banzan duka da taji wahala haka ta gudu ta koma gidan Mama Ladiyo ta faɗa mata komai, amma sai Mama Ladiyo tace mata tayi haƙuri ta komawa nan ai shine zaman auren haka Mama Ladiyo da kanta ta tisa Shatu ta maida ita gidan Idirisa, Abinci kanshi Idirisa bai damu daya bata ba, ganin yunwa zata kasheta yasa ta dinga bin makwabta tana amso wankau tana masu ,wasu tai masu wanke_wanke shine zata samu ɗan Abinci, randa kuma babu ta kwana da yunwa, ta samu ciki ya kai biyu amma fyaɗe Idirsa shike zubar da cikin.......... By Riamcool Star of the Squad 08109554986,only call [5/21, 8:09 PM] RIAMCOOL: *BAYAN WUYA* *Book 1* *By Mariam sani Riamcool* *MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION* Bismillahirrahmanirrahim *P.11&12* __________✍️Wahala ba kad'an take sha ba ta shirya guduwa sau ba adadi amma sanin bata da inda zata yasa ta haƙura a haka har suka cimma shekaru biyu da aure tana cikin uk'uba duk ta ƙara lalacewa idan ka ganta ba zaka taɓa cewa Yarinyar mace bace kuma wacce bata tab'a haihuwa ba,haka zalika dukda ni san da Muhammad yai mata zuciyarta bata taɓa mancewa dashi ba koda da second guda ne kullum cikin kuka take da fatan mutuwa, wata ranar Alhamis tana zaune lokacin Idirisa yayo shaye_shayensa yazo yai mata mugun duka sannan ya had'a mata da saki ukku cir,ba ƙaramin farinciki tayi ba na rabuwa da k'addararren auren, sai dai tunawa da Mamma Ladiyo yasa murna tata komawa ciki dan tasan ta koma za'a dasa aya daga inda aka tsaya don muguntar Mamma Ladiyo ba zata canza zani ba, koda taje ta faɗa mata abinda ya faru, ga mamakinta sai taga tayi murmushi tana lallashinta abin sosai ya d'aure mata kai sai dai tasan wannan murmushin na Mamma Ladiyo ba Alkhairi bane gareta, hakan yasa taci gaba da neman tsari gareta, wani abinda ya ƙara d'aure mata kai bai wuci yadda take bata Abinci akai akai ba, don tun tana tsoron kar tasa mata guba abinci harta dayaye take ci, amma bata saki jiki ba, wani k'arin abinda ya d'aure mata kai harta yarda Mamma Ladiyo tuba tayi shine kukan da take fashewa ta nemi gafararta, wani mugun dad'i Shatu taji ganin cewar Marik'iyar tata ta dawo daga daga rakiyar shed'an wata kalar tarairaya take sha don harta kammala Idda amma Mamma Ladiyo bata d'ora mata talla don Mamma Ladiyo kud'i tayi sosai wanda ta rasa ta inda take samunsa ga fitar daren da takeyi kullum hakan yasa ta dasa mata ayar tambaya da bincikenta a b'oye amma bata gano komai ba tunda A'ishatu ta gama idda take zuwa inda take tallan goro a da wai ko zata ga Muhammad amma shuru kakeji tayi kuka don tasan ta riga da ta rasashi Zaune take fatar nan tata data yamushe a baya yanzu tayi luwai saboda cimar da take samu wajen Mamma Ladiyo hakan yasa ta ƙara fitowa shar da ita fatar nan tata ta buzaye kamar ka latsa jini ya fito, sanye take da wata Atamfa ja mai ratsin yellow riga da zani wacce Mamma Ladiyo ta d'inka mata, fitowar Mamma Ladiyo da shirinta na Alfarma yasa ta maida hankalinta wajen Murmushi Mamma Ladiyo tai mata tana shafa kumatunta tana kallonta da ƴan jajayen idanunta kamar na Mayu harshe ta fiddo sai dai tunawa da wani abin yasa tai control d'in kanta tace "am ki zauna zanje wani bikin d'an k'awata kila na dawo yau ko kuma gobe" ta faɗa tana ficewa da sauri don jin idan ta tsaya ba zata iya dakatar da kanta daga umarnin zuciyarta ba da kallo kawai A'isha tabita zuciyarta na harbawa da sauri tana faɗin Allah yasa kar zarginta ya tabbata don ta tsorata da yadda idanunta sukai ja da tana kallonta hawaye ta share tana zama, sosai ta lula cikin tunani har yaro ya shigo yana sallama bata ji ba sai da yai mata ukku sannan firgigit ta dawo tana tambayarshi me za'a bashi "Ance ana sallama da A'ishatu" da mamaki take kallon yaron don tunda take babu wanda ya tab'a cewa yana sallama da ita idan ba Muhammad ba kuma tasan shi ya riga da yai mata nisa "Kaje kace ba nan gidan bane" ta faɗa tana shigewa d'aki ba da daɗewa ba saiga yaron ya dawo yace "wai ance nan ne ki fito ki ganshi" Ƙaramin tsaki taja tana dauko mayafi ta yafa ta fita sai dai ganin dalleliyar motar dake wajen ya sata zaro ido don tasan anyi b'atan kai ba dai wajenta ba juyawa yayi da nufin komawa taji an rik'e mayafinta k'amshin da taji da bugawar zuciyarta ya tabbatar mata da ko waye a hanzarce ta juyo tana kallonshi yadda ya kafeta da ido yana sakar mata da wani lallausan murmushi ita kuwa k'a waro masa manyan idanunta take don tabbatar da shi d'inne hawayen da take riƙewa ne suka samu damar sauka a kuncinta a hankali yasa hannu yana dauke mata su, "haba Aysher ki daina kukan nan haka nan kinsan fa a halin yanzu ke babba ce da da rabo da kin ajiye babba kamata" ya faɗa da sigar zolaya ba shiri tai dariya tana k'ara kallonsa tana matsa yatsun hannunta wanda yasha ƙunshin ja, "Ina ka shiga?" ita ce tambayar da taji ta fito a bakinta wani murmushi mai ciwo yayi yana share zancen da jawo mata wata fira, itama ganin bai bata amsa ba yasa ta share, a wannan karon ma ya ƙara mata maganar aure wanda zuciyarta taji ta tsinke don tana gudun Mamma Ladiyo ta ƙara yi mata auren dole wanda ba zata jura ba k'ara ta gudu tabar gidan da ta rasa Muhammad a karo na biyu ha sukai sallama jikinta a mace yake tana cikin zullumi, kwanciya tayi tana sak'e_sak'e a ranta bacci ya fara d'aukanta taji ana lashe mata fuska wanda firgigit ta buɗe idonta tana kallon baƙar magen da ke tsaye tak'i matsawa ta kafeta da idanunta juyayi tana fito da jan harshenta tana tand'e bakinta, Addu'a take son yi amma ta kasa da ƙyar ta samu taja wata Addu'a wacce yasa magen ja da baya tana mata Murmushi sannan ta jijjiga kai ta haura katanga,wata kalar zufa ce ta dinga tsatsafo mata cikin tsoro ta samu tayo Arwalla tayi salloli tare da Azkhar har bacci ya ƙara kwasheta da safe Mamma Ladiyo ta dawo ganin jikin A'ishatu na kyarma alamun zazzaɓi ya sata tunkararta tana tambayar ta abinda ya sameta cikin tashin hankali, magani ta bata tasha ta gasa mata jikin haka ta kwana biyu sannan ta warware ga Muhimman bai dawo ba,zaune take tana matsa hannunta bakinta na motsi alamar son ta yiwa Mamma Ladiyo magana, lura da hakan yasa Mamma Ladiyo fad'in "faɗi maganarki mana ƴata naga har yanzun kamar baki ida sakin jiki dani ba" murmushi kawai tai mata cikin shakku ta faɗa mata yadda sukai da Muhammad, a mamakinta murmushi tayi nan take ta amince ta kuma nunawa Shatu jin daɗinta sai da akai sati Sannan Muhammad ya dawo wajen Shatu ba ɓata lkc ta faɗa masa amincewar Mamma Ladiyo wanda yai murna kamar ya taka rawa haka yake ji, ba ɓata lokaci ya turo magabatansa aka tsaida ranaku wanda iya Sati aka saka, sati na zagayowa aka ɗaura auren A'ishatu da Muhammad wanda faɗa maku irin farincikin da masoyan suka shiga ɓata baki ne, wani satin na zuwa ta tare a katafaren gidanta wanda Part biyu ne nata saina Mansura sosai suke zuba soyayya wacce a gaban kowa basa jin kunyar nunawa junansu ita haka sosai dangin Muhammad suke nuna mata harma da Abokiyar zaman ta Mansura wacce ta riƙeta da Amana, da kanshi Muhammad ya samo mata mai koyamata karatun Addini dana zamani, a haka har suka kwashe tsawon shekaru biyu A'isatu na samun ciki yana ɓarewa, wanda anyi na Asibiti dana gida amma babu sauyi, don duk lokacin data samu ciki haka zatai mafarkin magen nan wacce ta taɓa gani tana zaƙulo ɗan cikinta tana cinsa, da tashi cikin jikinta ke zubewa da ƙyar aka samu cikin ikon Allah ciki ya tsaya a jikinta harta haifi Kyakkyawan yaronta mai kamar ubansa wato Khabir wanda duk wata kulawa tashi tana hannun Mansura, haka Habib shima yake kula dashi tamkar wanda suka fito ciki guda sai da yai 7 years sannan A'isha ta samu wani cikin inda ta haifi ƴarta mace sak ita ta biyo, ranar suna yarinya taci suna Muneebba, wanda Muhammad yayi bajinta yai hidima tamkar bai san ciwon kuɗi ba, don tun ranar da Muneebba tazo duniya yake jin sonta daban a cikin yaransa, bayan kwanaki kaɗan itama Mansura ta haifi ƴan biyunta Mata waɗanda suka ci suna Hanifah da Sharifah, haka rayuwa ta gangara har Muneebba ta cika 3 year misalin ƙarfe biyun dare gudu yake sosai harya ƙaraso Part ɗin A'ishatu yana zuwa ya saɓi Muneebba yana tashin Mamma, (wato A'ishatu) a firgice ta miƙe zatai magana ya rufe mata baki ya tado Khabir, a galabaice ya buɗe get ɗin gidan yana Aman jini haka yaja hannunsu suka dinga gudu har suka isa wani wajen Motar da yai parking shiga sukai ya fizgesu Ita dai A'ishatu ta kasa magana illa binshi da ido da take dan ta kasa gane me ke faruwa, ga bakinta yai mata nauyi ta kasa furta kalma koda guda ce wanda take ji tamkar an datse mata baki ne, tun dare suke tafiya sai gab da Asuba suka shigo garin Kano wanda ya saukesu a wata tshohuwar unguwa ya bata maƙuddan kuɗaɗen, ganin da gaske tafiya zaiyi ba mafarki take ba ya sata riƙo rigarsa ta baya wasu hawaye na bin kuncinta, shima kallonsu yake yana hawaye "ba nida zaɓi ne Aysher illa hakan, shine zai baku damar tsira da rayuwarku tabbas rayukanku na cikin haɗari, ba don ina so zan nesanta kaina daga gareku ba, saduwar Alkhairi" yana gama faɗin hakan ya janye hannunta yana shiga Motar ya wuce durƙushewa wajen tayi ta fashe da kuka, da ƙyar ta rarrashi kanta har, tayi shiru. kasancewar unguwar da jama'a yasa ta nemi temakon Jama'a ganin hada yara yasa wani Alhaji Mamman temakonta ta zauna a gidansa har saida ya samo musu gida da kansa, wanda ɗan zamanta a gidan tasha tsangwamar Maman Nazeer wato Matar Mamman wanda ko ɗanta yazo wajen Muneebba da zummar yi masa wasa zata dinga masa faɗa wani sa'in harda duka amma bai daddara haka washe gari zai ƙara zowa gun Muneebba da Khabir Bayan sun dawo gidan sosai abubuwan suka rincaɓewa A'ishah Abinci kanshi na neman gagararsu sai wanda yaga Allah zai taimakesu a hakan ta saka ƴaƴanta makaranta, wanda tun dawowarsu taji mutane na faɗin wai wani yazo ya faɗawa mai unguwa a tada ita don ƴar bariki ce ƴaƴanta ma duka a hanyar bariki ta samesu, nan danan unguwar ta ɗauka wanda taci kuka sosai ta kuma daɗe kunnuwanta dana ƴaƴanta, sosai rayuwa ta ƙara juyewa Mamma a ciki kuwa harda makantarta wacce ta wayi gari kawai ta ganta taje anyi maganin amma duk a banza, ganin bata da isasshen kuɗi yasa ta haƙura, dukda warning ɗinda Maman Nazeer taiwa Nazeer ɗin bai hanasa silalawo yazo gurin Muneebba da kawo mata kayan wasa dukkan wani abu ya samu Muneebba yake kawo mawa harta fara mallakar hankalinta wata kalar shaƙuwa ce ta shiga tsakaninsu da Muneebba, harta fara mallakar hankalinta ta wayi gari da soyayyarsa wanda bata san lkcn data shiga ba, a lkcn Khabir ya fara aiki wani gareji ciki ne suke samun nacin Abinci da ƴan buƙatunsu tun da Muneebba ta wayi gari ta, ta shi da tsanar Mahaifinta wanda a ganinta da gangan ya barsu dan jawo musu rayuwar tozarci, wanda ta Alƙawartawa kanta koda taga mahaifinta ba zata ɗaukesa a matsayin Uba ba, duk lkcn da taga Mamma na kuka takan ƙara tsantar kanta da jin tsanar Mahaifinta, a haka ta taso da tsanar Mahaifinta har kawowar yanzun wanda babu mahaluƙin da take gani cikakken mara tausayi irin Mahaifinta....... (tabɗi rigiji gabji, a kafta wasa farin girki ba'a fara wasan ba) Love U all my Habibties a daure a dinga Share🥰plz Ina godiya ga masu ƙoƙarin Comments Dawowa labari Mu haɗu a next Page [5/21, 8:10 PM] RIAMCOOL: *BAYAN WUYA* *Book 1* *By Mariam sani Riamcool* *MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION* Bismillahirrahmanirrahim *P.13&14* *DAWOWA LBR* _______Tun da ta shiga ɗakin take faman rizgar kuka wanda tana ƙara jin zuciyarta na hauhawa da farashin tsanar Mahaifinta, jin gyaran muryan Mamma yasa ta ɗago da fuskarta wacce tai jawur saboda kuka share hawayen tayi tana kama Mamma ta zauna faɗa Mamma ta soma yi mata kamar zata ari baki, wani kukan ta sake fashewa dashi, banza Mamma tai mata har tayi mai isarta koda Khabir ya dawo yai lallashin duniya amma taƙi sakin jiki taci koda Abinci ne gani take a Silar rashin mahaifinta zata rasa Nazeer wanda ba zata iya juran hakan ba, waya ta ɗauka tana danna masa kira wanda tayi yafi a ƙirga amma bai maido ba, zuciyarta ce ta sake tsinkewa tex ta tura mishi nan ma babu reply shiru, Kwance yake yana juyi bisa makeken gadonsa yana ganin kiran Muneebba na shigowa a wayarsa amma ya gaza ɗauka saboda Hajiya data kasa ta tsare wayar ma hannunta take, kallonsa Hajiya tayi tana taɓe baki tace "wai ni Nazeer na rasa me ka gani a jikin yarinyar nan duk kyau da izzarka amma ace ga ita ka liƙe ita ɗimma ƴar zina marar asali da galihu ga ƴaƴan Manya masu asali da dukiya suna binka amma kaƙi kulasu to bari kaji wallahi indai kaga kayi auren nan bana numfashi, amma aure kasa niyya ban hanaka ba" tana kaiwa nan ta miƙe ta fice da kallo kawai ya bita yana jin wasu siraran hawaye na biyo kuncinsa ko kaɗan baya son kalmar rabuwa ta gifta tsakaninsa da Muneebba da zai iya rabuwa da Muneebba da tun yana ɗan ƙanƙani zai rabu da ita ko dan dukan da yake sha a gurin Mahaifiyarsa amma ina bazai iya ba sonta ya riga da yai masa mugun kamu wanda ya zamto guba a jikinsa, ɗauke hawayen yayi da yatsan hannunsa yana miƙewa ya shiga Toilet Alwalla yayi yai nafila yana fawwalawa Ubangiji lamurransa bacci a ranar sai dai ɓarawo ya ɗaukesa A ɓangaren Muneebba ma hakan ta kasance *ASAD BOBBI* Jerin gwano motoci ƙirar Marcedes Benz farare sol ke tsula gudu a titin wanda ganin irin gudun da suke ne zai tabbatar da ba lafiya ba, hakimce yake a bayan Motar ya lumshe kyawawan idanunsa yana yamutsa sumar kansa gani yake kamar motocin basa gudu buɗe lumsassun idanunsa yayi yana kallon wani gefe daban wanda a zahiri ba can yake kallo ba ya tafi wata duniya ta daban jin tsayuwar Motar yasa hankalinsa ya dawo a gangar jikinsa, a hankali yakai dubansa ga wajen yadda mutane sukai cincirindon da ƴan jaridu kallon Company yake yadda gobarar ta ƙonesa ƙurumis ga kayayyakin da suka ƙone suma ana fito dasu rufe idonsa yai yana ƙara buɗesu, duk fitowa na cikin Motar sukai Sai Motar da yake ciki ce ba buɗe ba, tun tsayuwar Motocin mutane da ƴan jaridu suka zuba ido da son ganin wanda ke ciki har akai 5 Minute, a hankali aka buɗe Motar yana zuro da Kyakkyawar ƙafarsa wacce take cikin takalmi Cover shues masu azababben kyau saida yai wasu ƴan mimtuna sannan ya zuro da gudar ƙafar tasa yana ida fitowa, kowa na wajen kallonsa yake yadda ya wani haɗe rai kwarjini da haiba sun taru a jikinsa, uwa uba Izza da jin kai wanda a jininsa suke, a hankali yake takowa ƴan Jarida nayo masa caaaa ko wane na wullo masa tambaya, wani ɗan Jaridan ne yasha gabansa yana ƙara gyara farin gilashi idonsa "me zaka iya faɗa mana game da ƙonewar Company ka, shin da gaske abokan hamayyarka sune sukai ta'addin ƙonewarsa, sannan..." bai idasa ba saboda wani kallo da Bobbi ya jefeshi dashi wanda yasa shi haɗiye kingin tambayoyinsa yana bashi hanya Kallon ɗan Jaridan yayi yana sakar masa wani killer smile wanda shi kaɗai yasan ma'anarsa, kai tsaiye ya shiga Company da securities ɗinsa kallon Company yake ganin yadda har iyanzu bai daina hayaƙi ba, cije lips ɗinsa na ƙasa yayi sannan ya sake sakin wani shu'umin murmushi "Zaidu" ya furta a hankali Ma'aikan Company ne suka taru suna miƙo gaisuwa babu wanda ya amsa mawa kallonsu yake ɗaya bayan ɗaya yana nazartarsu, wanda kowa cikinsa ya ɗuri ruwa uwa uba Manager Company, bai ce uffan ba har manager ya miƙe yana magana tare da saddar da kansa yace "Oga ka gafarce mu wallahi dukkammu ba musan yadda akai gobaran ta tashi ba" shiru ya ƙara yi na wasu daƙiƙu dan sun fidda ran da zai basu amsa "Ok ban tambayeku ba'asin yadda akai gobaran ta kama ba, bana buƙatar jin wani ƙarin zance daga gareku haka Allah ya riga ya tsara mana" suka ji saukan muryanshi wanda yake yi kamar baya son buɗe bakin nasa don shi magana wahala take masa yana gama faɗa ya miƙe yana fitowa wani ƙaramin tsaki yaja ganin yadda mutane ke kallonsa kamar ba Mutum ba ga hayaniyarsu data fara isarsa sai da ya ɗan ƙara zagaya Company sannan ya futo, buɗe masa Motar akai ya shige sannan kingin suka shiga kai tsaye Guest house ɗinsa suka nufa don yana buƙatar hutu ********* *Yola* *FATTU* wata kalar busa sarewa ce ke tashi a cikin jeji wacce Fattu keyi a duk lokacin data fito kiwon Shanu data fara busa jejin zaiyi tsit tsuntsaye za suna dinga safkowa tana watsa musu tsaba suna ci tana ƙara busawa, wani juyi take ƙara yi tana rugawa da gudu ta hau wani ƙaton dutse dariya tayi tana ƙara kai sarewar a bakinta ta fara busata cikin ƙwarewa da iyawa, wani sautin na daban mai ratsa dukkan gaɓukkan mai sauraro Fattu keyi jejin ne ya ƙara yin shiru yi take harta fara gajiya ganin babu alamunsa yasa Fattu raurau da ido ta buɗe baki tana faɗin "JODDI!!!JODDi!!! JODDI!!!" da ƙarfi take kiran sunansa namma shiru babu alamunsa sarewar ta ƙara kaiwa bakinta ta fara busan da tasan indai yana kusa to tabbas zaizo wata kalar busa yanayinta mai taken ban tausayi take yi Wata kalar feɗuwa aka yi wacce ya sata sauka daga saman dutsen tana bin hanyar da feɗuwar ke fitowa tasan tabbas shine wata kalar busa tayi wanda zaka rantse da usur akayita amma da baki tayi shi nufar hanyar tayi tana ƙara yin wata shi kuma yana feɗuwa da wani kalar sauti, yana ganinta ya nufota da gudu itama da gudun ta nufesa tana kallon yadda yake dafe cikinsa kamo Hannunsa tayi da Yaren fulatanci take faɗin "JODDI ina ka tafi? yau kayi nisa" dukda tasan bazai maido mata amsa ba kuma ba zai fahimci abinda take nufi ba tunda ba hankali ne dashi ba,mamadin ya bata amsa saima haɗe rai da yayi yana nuna mata cikinsa, murmushi ta saki tana jawo hannunsa suka nufo inda ta ajiye masa ƙwaryar furar data damo masa tasha kindirmon Nono zaunar dashi tayi ta ɗauki ludayin ta dinga ɗebowa tana bashi a baki har sai da ya ƙoshi sannan ta ƙyalesa miƙewa yayi da nufin komawa inda ya fito, dama tasan daya sha zai tafi saboda shi kullum take zuwa nan kiwon Shanu wanda ta rasa baya ga tausayinsa me take ji da kanta ta rakasa bukkar data kafa masa tun farkon ganinta dashi sai da ya shiga sannan ta dawo tana kaɗa Shanunta suka sha ruwa sannan ta kaɗasu suka bi hanyar gida kasancewar Magriba data doso sai dai tana tunkarar gidan gabanta ya fara faɗuwa don tasan yau Innaro da Baffalo sai sunyi farfesun Namanta tunda ta ibarwa Innaro fura a ɓoye kuma Saro ta ganta tasan zata faɗa "Ya Allah" ta furta tana nufar garken shanun dasu sannan ta nufi bukkarsu da nufin ta saɗaɗa ta shiga sai dai jin saukar Sanda a ƙwabrin ƙafarta ya sata durƙushewa Baffalo ne ke kallonta cikin Yaren fulatanci yace "ke Fattu yaushe kika koyi sata? furan Innaro irgagga da zata tafi kasuwa ta siyar ita kika ɗiba to yau sai na miki ligib ƴar jakar uba" yana gama faɗin hakan ya ɗaga sandarsa ya dinga sauke mata tun tana ihu a hankali har yakai ga tana yi da ƙarfi sai da ta daku sannan ya ƙyaleta Bukkarta ta shiga tana share hawaye tana ji Innaro da ƴarta Saro suna yada mata habaici ta shige, murmushi ta saki tunawa da JODDi wanda akansa ne akai mata wannan duka ji tayi ma dukkan haushin dukan ya fice, sandarta ta ajiye tana nufar rafi don tayi wanka *Wacece Fattu* FATTU dai ƴa ce ga Mlm Isah Baffalo wanda matansa biyu Innaro da mairo Mahaifiyar Fattu wacce tun tana shan Nono Mamanta ta rasu wanda ta taso cikin uƙubar Innaro tun tana ƙarama take ɗaukar Sarewar Baffalo wanda sana'arsa ce busa Sarewa , hakan yasa itama ta gada, zuwa kiwon Shanun da take ta haɗu da wani mahaukaci cikin jeji wanda ta saka masa sunan JODDI busa Sarewar da take yasa kullum yake zuwa wajenta ita kuma ta tausaya masa tana kawo masa Abinci duk lkcn da zata fito kiwo, tana gama wankan ta shiga jeji ta hau bishiya don can take kwana *KANO* Zaune take bisa bed ɗinta fararen idonta sanye da farin gilashi ta kafe Photon dake jikin Laptop ɗin da ido tana sakin Murmushi tea ta kurɓa tana ƙara zooming ɗin Photon "Yah Bobbi" ta furta a hankali tana lumshe manyan idanunta "Maheer Maheer Maheer" taji Mami na ƙwala mata kira rufe loptop ɗin tayi tana ajiye tana fitowa a hankali take bin step ɗin benen kamar bata son taka ƙasa, ida sakkowa tayi ta nufi Mami tana faɗawa jikinta "Mammi gani" shafa kanta Mammi tayi tace "ki shirya gobe zaki je gidan Mommy, ayi dayi danni na fara gajiya ƙara kije ya dinga ganinki kusa kafin ayi muku baiko, har ya saba dake sannan wannan muskilancin naki da aji ki ajiye shi ki dinga shishige masa ta hakan ne zaki samu shiga gurinsa" tashi tayi daga jikin Mammi tana kallon Mammi tace "Mammi gsky ba zan iya shishige masa ba kinsan Yah Bobbi da diz gi da muskilancin kawai dai zan je gidan" ta faɗa tana miƙewa, da kallo Mammi ta bita har ta haye..... Ba kwa man share fa😞 Habibties ku daure ku dinga man share dan Allah [5/21, 8:10 PM] RIAMCOOL: *BAYAN WUYA* BOOK 1 *BY MARIAM SANI RIAMCOOL* *MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION* *P.15&16* __________koda ta shiga haɗa kayanta taci gaba da yi saida ta haɗasu tsaf cikin Akwati sannan ta faɗa Toilet tayi wanka saida tai nafilfilu da karatun qur'ani sannan ta kwanta Washe gari tana tashi ta faɗa kichen ta haɗa musu break fast a gurguje ta faɗa Toilet tayo wanka haɗaɗɗun Lotion ta shafa sannan ta ɗauki wani Blue ɗin material mai ratsin baƙi ɗinki A shape wanda tasan zai karɓi jikinta, ba wata kwalliya tayi ba amma tayi kyau sosai fuskar nan tata ɗauke da yalwataccen murmushi, parking ɗin dogon gashinta tayi ta ɗauki mayafin Material ɗin ta yana a kanta, ta aza farin gilashin ido wanda yake ƙara fito da ainahin kyanta duban kanta tayi a Mirror tana sakin wani ƙayataccen murmushi Hand back ɗinta da wayarta ta ɗauka ta fito Koda ta fito zaune ta iske Mammi da Daddynta suna break "Morning Mom nd Dad" ta faɗa tana manna musu sumba " da murmushi suka amsa mata ɗaya daga cikin kujerun Dinnig taja tana zama Chips nd plantain kawai taci ta miƙe kallon Mammi tayi tace mata zata wuce "Ok ki gaisheta ki kula da abinda ya kaiki" Mammi ta faɗa tana duban ƴar tata, da to ta amsa tana ficewa da kanta tai Driving koda taje bata wani sha wahalan shiga ba kasancewar an santa parking Space ta nufa ta ajiye motar sannan ta wuce kai tsaye ta wuce sama kasancewar ma'aikatan gidan sun santa ko wane miƙo mata gaisuwa suke, da fara duka take amsa musu, a hankali ta tura ƙofan Falon ta shiga, zaune ta iske mazan gidan JUNAID AFIF ARYAN ZAMEER ABEED HAROON sai IFTIHAR dake gefen ARYAN ana caftar da ita, ganin basu lura da ita ba ya sata gyaran murya tana Sallama, da gudu IFTIHAR ta taso tana rungumeta tana faɗin "Oyoyo Matar BIg bro" dariya tayi tana faɗin "lallai IFTIHAR kina da aiki a gabanki fa ta ina shi Yah Bobbi yasan dama ni" dukan kafaɗarta tayi tana faɗin "lallai kuwa Aunty Maheer kina nufin Mom bata faɗawa Mammi amincewar Yah Bobbi ba?" Kallonsu Zameer yayi yana taɓe baki yace "ke IFTIHAR kiji tsoron Allah yaushe shi Yah Bobbi harya amince kina gani fa saboda auren ya ƙauracewa gidan nan sannan akan auren fa yaiwa Mom hijira wanda har iyanzu bai shiga shirgin Mom a yanzu" dariya ARYAN yayi yana miƙewa yace "kudai ake ji inaga Aljana ta auresa har iyanzu shi yasa" wani kalar dum Maheer taji zuciyarta tayi jin zancen Zameer wato saboda itama ya bar ya bar gida a dalilinta ya bar shiga shirgin Mom, "tabbas ya zama dole ne nabi shawarar Mammi ta haka ne kaɗai zan iya samun Yah Bobbi tunda YAH DEEN ya kubce mini wannan bazan barshi ya kuncemin a karo na biyu ba" ta faɗa a zuciyarta dafata Iftihar tayi tace "tunanin me kikeyi ne?" "Nothing" ta faɗa tana ɗaga kafaɗa tunda Zameer yai maganar JUNAID ya karanci yanayin Maheer dariya yayo yanawa HAROON da ABEED signal da ido dariya sukai HAROON na faɗin "cabɗijam lallai kam da sauran ruwa a kaba, akwai fa wasan game a gidanmu" Maheer da bata fahimci abinda suke nufi ba ta haura sama ɗakin Iftihar ta ajiye akwatin sannan ta zame gilashin idonta tana share hawayen da suka samu damar gangarowa a kuncinta share hawayen tayi, ta fito koda ta fito ta samu Aunty Samha da Aunty Meera waɗanda suna kan ibadar tasu wato danna waya da gudu ta isa wajensu tana rungumesu da murna sosai suka rungumeta suna mata ƙorafin rashi zuwa da ba tayi kwana biyu,Mom ta tambaya aka faɗa mata bata nan tana gun aiki ita da Samha da Seemah ******************** *ASAD BOBBI* Kwance yake a baki Swimming pool ya lumshe idonsa ya ɗauki kusan 10 minute buɗe idanuwan nasa yayi waɗanda sukai masa jajir saboda ƙunci da takaicin da yake ciki, wanda duk da hakan bai hana ainahin kyawun nasa fita ba da sirrin kyawun idanunsa, ba wai yana takaicin rasa dukiyarsa da yai ba, sai don takaicin abinda akai masa meya tare musu? Wanda suke son karyasa kafin su ɗauki rayuwarsa kamar yadda suka ɗauki ta ɗan uwansa Deen wanda har gobe yake cikin raɗaɗi da zafin zuciya na rashin ɗan uwansa wanda suka zauna ciki guda wanda daƙiƙu kaɗan ne a tsakaninsu, ko bacci bai taɓa rabasu ba amma yau azzalumai sunyi nasarar rabasa da wanda yafi ƙauna a rayuwarsa, yasan target ɗinsu na gaba a kansa ne sai dai ina bazai taɓa basu wata dama ba wacce zasu samu ɓaraka a gurinsu, rintse idanunsa ya ƙara yi tunowa da auren Maheer wanda ya ida dagular da zuciyarsa amma zai bi komai a sannu ya warware, miƙewa yayi tare da fara tafiya cikin taƙama da kuzari, tafiya irin ta ƙarfafan masu ji da kansu da cikakkiyar izza,kai tsaye wani ƙofan ya shiga sai gashi ya faɗa a bedroom, bathroom ya faɗa yai wanka ya fito ƙugunsa ɗaure da towel mirɗaɗɗiyar ƙiran tashi duk a waje ga skin ɗinsa se sheƙi take kai tsaye shiryawa yai cikin wasu arnayen ƙananan kaya masu masifar kyau yai parking ɗin gashin kansa tare da ɗauresa kyau bana kaɗan ba Bobbi yayi dukkan wata mace ta gansa sai tayi suman wucin gadi kafin ta dawo hayyacinta, wayoyinsa da keys nasa ya ɗauka har zai fita sai kuma ya juyo a hankali ya tako har zuwa inda wani makeken photo yake wanda sak kamannisa ne keda na jikin Photon sai dai shi wannan Photon anyi sa da fara'a ne, ɗaukar Photon yai yana shafawa "DEEN" ya faɗa a hankali rungume Photon yai yana sakin ajiyar zuciya "bazan kyalesu ba DEEN zan ɗaukar maka fansar ranka" ya faɗa da fitar da wani huci mai zafi ya ɗau kusan daƙiƙu kafin ya ɗauke photon daga ƙirjinsa, ganin zai makara a meeting ɗinsu wanda aka shirya na manyan ƴan kasuwa harma dana waje yasa shi fita a gurguje Securities na take masa baya Manyan jigagan Motoci na Alfarma suka shiga baƙaƙe wuluk dasu guda biyar ta tsakiyar ya shiga Driver naja suka nufi wajen Meeting ɗin ga baki ɗaya kowa ya hallara a wajen shine kawai babu kowa na wajen zuciyarsa cike take da takaicin Bobbi ganin ɓata musu lokacin da yayi wanda kuma koda yazo idan banda Hy daya furta bai sake faɗin komai ba, Zaidu dake gefen Mas'ud ne cikin takaici yace "BObbi wane kalar wulaƙanci ne haka zaka ɓata mana lokaci kuma fa kasan a kanka za'ai wannan Meeting ɗin"ya faɗa da ɓacin rai "Ohh kuma fa so kuyi abinda ya kawo mu kuna ƙara ɓata man lokaci muddin lokacin dana ibarwa kaina ya ƙare zan tafiyata fa 15 minute gareku" ya faɗa kamar baya son maganar yana ɗagewa Zaidu gira tare da kashesa da wani Munafukin murmushi Nan da nan kowa ya fara masifa kan rainin wayon Bobbi, cikin masifa Alhaji Habu ya dubesa yana faɗin "ASAD AHMAD BOBBI na kiraka da manyan baƙi kaji kuma ka ƙara ji ba wani abu bane yasa mu zaman meeting ɗinnan sai don kashe mana companies da kake bamu kaɗai ba har ƴan waje kana neman kashe nasu companies to bari kaji kamar yadda muke saka farashin kayammu da kuma yadda muke sarrafa su kaima haka zakai, bata yuwa kazo ka tarwatsa mana companies na tsawon shekaru" kallonshi yake da rinannu idanunsa waɗanda suka sauya kala ya zuwa na ɓacin rai "shawara kake bani ko umarni?" Bobbi ya faɗa yana ƙare mashi kallon rainin wayo dariyar takaici Alhaji Habu yai yana faɗin "duk yadda ka ɗauka Bobbi, amma ba shawara bace umarnimmu ne yadda kowa yake kaima haka zakai" Kallon agogon hannunsa yai yana faɗin "Time up, lokacinku ya ƙare yana gama faɗar hakan ya miƙe ya fice Kowa da kallo sake da baki ya bisa suna ƙara jinjina rainin wayonsa da kuma taurin kai irin na ɗan uwansa Deen kowa da takaicin abin ya bar wajen tareda alwashin baƙin ƙudiri akan Bobbi Tunda Bobbi ya fita kai tsaye Company B.D Wanda gobara ta kama yaje, Company duka an fara gyarasa an canza masa wani sabon design mai jan hankali Murmushi ya saki yana lumshe idonsa ya buɗe jin kiran waya yasa sa ɗaukar wayar yana dubawa Dad ya gani shiru yai na wasu ƴan daƙiƙu "Asad ni kake so na fara gaisar da kai koya?" Dad ya faɗa shafa dogon gashin kansa yai yana faɗi "No Dad, Afterning Dad" murmushi kawai yai yana ƙara mamakin halin yaron nasa "ok kaje Meeting ɗinne?" "eh" ya furta "ba kadai nuna musu rashin ɗa'ar daka saba ba ko?" "Saidai kar a kuma Dad" dariya kawai Dad yai ya kashe wayar daman yasan Asad ne dai_dai dasu ɗin ******************** MUNEEBBA ranar haka ta kwanta sukuku ta tashi ba walwala Abinci ma don kar Mamma ta shiga cikin damuwa yasa taci, tunda Hajiyar Nazeer tazo tasan ta riga data rasashi kenan inama zata iya fitar da son Nazeer da tuni ta fitar dashi kwance take tayi luf abin duniya dukya isheta jin wayarta na ring ya sata miƙa hannu ta ɗauke ta saman katifa, sunan wanda ta gani ne ya sata miƙewa tana sauke ajiyar zuciya a hankali tai picking call ɗin da sallama ɗauke a bakinta, wata ƙaƙƙarfar ajiyar zuciya Nazeer ya saki "Hayatee" ya kirata da wata kalar sassanyar murya wacce ta sata lumshe idanunta tana buɗewa, "mi ya hana kai picking call ɗina?" yaji saukar tambayarta babu abinda ya ɓoye mata ya faɗa mata dukkan abinda ya faru, murmushin takaici tayi tana share hawaye, tare da barin zancen ta jawo musu wata firar sun jima kamar koda yaushe suna wayar kafin suyi sallama da juna dukkan abinda Muneebba keyi Mamma na saurarenta girgiza kai tayi kawai "Muneebba" Mamma ta Kira sunanta da na'am ta amsa tana zama kusa da Mamma wacce Mamma ta tsira mata ido kamar tana ganinta dafa kafaɗarta tayi tace "Muneebba tabbas ni uwa ce kuma ina jin zafin dukkan abinda ake miki, yadda banyi rayuwar farinciki bana so kema ki taso cikin rayuwar ƙunci, domin duk yadda Mijinki ke sonki indai uwarsa bata sonki to babu kwanciyar hankali da zaman lafiya a rayuwar auratayya, kiyi istihara idan da Alkhairi Allahu zai tabbatar, amma ki rage wannan makahon son da kike yiwa Nazeer" Jiki a mace ta amsa da "Insha Allah Mamma" murmushi kawai Mamma tayi Bayan kwana biyu babu wata matsala da Hajiyar Nazeer ta sake shigowa da ita mu'amala suke da Muneebba tamkar su lashe junansu saboda so ga lokacin bikinsu saketa matsowa tafe take ita da Hafsat a hanyar dawowarsu islamiyya tunda tazo bakin senter gidansu ta hanko Motar data saba gani wacce duk lokacin dawowarta islamiyya sai taga Motar, abinda ke ɗaure mata kai bai wuci yadda dattijon dake bayan Motar koda yaushe yake sakar mata Murmushi, kauda kanta tayi daga kallonsa tana jin zuciyarta na wani kalar harbawa saboda kamannin da take gani tattare dashi zuciyarta ce ta fara ayyana mata wani abun daban da sauri ta girgiza kai tana faɗin "kai ina ba haka bane ba dai shi bane" ta faɗa da sake kallon wajen da Babban Mutumin yake wanda kallo guda zakai masa kasan ya jiƙu da Naira, sai dai ganin mutumin na aman jini yana dafe saitin zuciyarsa yasa Muneebba zaro ido tana taɓa Hafsat tace "kinga kuwa abinda na gani?" da tausayi tace "wallahi na gani Muneebba mutumin gwanin ban tausayi kullum fa sai yazo yana wa almajirai da talakawan Anguwar nan sadaka yanzun nan fa wajen ya ƙetaro naga ya duƙe yana Aman jinin nan" Hafsat ta faɗa kamar tai kuka Jijjiga kai Muneebba tayi da tausayi tana faɗin Allah ya kyauta, a haka har kowacce ta wuce gidansu koda taje kayan islamiyya ta cire ta nufi bayi tai wanka da Arwalla ta fito, bayan sun idar da sallan Ishsha ne ta zauna tana kallon Khabir tana tariyo kamannin mutumin data gani "wai lafiya ne kike kallona haka Muneebba?" Khabir ya faɗa yana kallonta, sauke tagumin tayi tace wallahi Ya Khabir wani mutum mai kama dakai sak na gani dandai shi ba fari bane, amma yadda kuke kama ta ɓaci, kuma fa kullum yana Anguwar nan yana sadaka, wallahi baka gansa ba gwanin ban tausayi ɗazun da zai ƙetaro sashen da muke fa ya kama aman jini baka gani ba" wani dumm_dumm Mamma taji gabanta ya faɗin jin zancen ƴar tata ta tabbatar dashi ɗinne amma ba zata bari yaran nata susan da shine Mahaifinsu ba, "Ayya Allah shi kyauta kin san shi kama babu inda ba'a samun mai kama da kai, ga kaf danginku babu mai kama da Khabir da sai nace wani jinin naku ne" Mamma ta faɗa tana gyara ɗaurin ɗan kwalinta Ajiyar zuciya Muneebba ta sauke jin zarginta bai tabbata gsky ba, ƙwanya Khabir ya sakar mata yana faɗin "kila dai idanunki gizo suke miki" hararan wasa ta banka masa tana turo baki tace "ni wallahi mai kama dakai na gani" dariya kawai yai ya miƙe yana shigewa ɗakinsa ganin itama haka yasa suka kwanta ************************ *FATTU* tafe take tana kora Shanunta tare da rera waƙarsu ta Fulani a haka harta isa jejin, jin kukan tsuntsaye yasa ta fara busa sarewar tata tana watsa musu tsaba, wani fili ta samu taja tana tsalle wanda ya sata tuntuɓe da wani girkakken dutse ta faɗi ƙasa kanta ya bugu da wani ƙaton dutse dake gabanta, nan take kanta ya fashe jini na tsartuwa wata ƙara ta ƙwalla wacce tasa dajin amsa kuwwa A mamadin yaji busa sarewar da yake jira sai jin ƙararta yai wacce tai amsa kuwwa cikin Dodon kunnuwansa, miƙewa yai da zummarsa yana keta itatuwan wajen yana nufo inda take yashe jini na tsartuwa jini kuwa duk ya jiƙa mata farar rigarta ta Fulani, cike da jarumta ya tunkaro inda take yana yatsina fuska da ƙara ɗaureta tamau alamun hakan ya zame masa Al'ada, tunani ya tafi can kuma saiya gyaɗa kai yana yage tsummar rigarsa wacce take fes kamar bata mahaukaci ba, duƙawa yai yana tallafo da kanta ya zuwa azasa bisa cinyarsa tsumman daya yaga ya ɗauka yana ɗaure mata goshin tamau dashi jinin ya daina zuba, ganin bata numfashi ya sashi ɗaukarta kacokan ya azata a kafaɗarsa, yanayin tafiyarsa zai tabbatar maka da cewa gwarzon jarumi ne, da cikakkiyar gadara da Izza wani bakin rafi ya ajiyeta yana ibo ruwan da tafin hannunsa yana shafa mata a fuska kamar wani mai cikakken hankali....... [5/21, 8:11 PM] RIAMCOOL: *BAYAN WUYA* BOOK 1 *BY MARIAM SANI RIAMCOOL* *MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION* *P.17&18* _________Ɗago da fuskarta yai yana azata a cinyarsa bakinsa yakai dai_dai saitin nata yana hura mata iska, a hankali ta dinga ware manyan idanunta tana buɗewa harta waresu duka, yawo ta dinga yi da idonta tana murzawa tana ƙara rufewa don ta tabbatar da cewar mafarki take ganinta bisa cinyar wani murɗaɗden Mutum, ganin ba mafarki bane ya sata ƙwalla ƙara tana miƙewa da azama, da sauri ya ɗago da fuskar tasa yana kallonta wanda itama shi take kallo da mamaki, nunasa tai da yatsa tai da gurɓatacciyar hausarta take faɗin "Hoɗijam JODDI dama ke ƴar iska ne ashe ban sani ba, ashe ke ba mahaukaciya na ba? kike fakewa da hauka, kina shanye man fura wacce kullum sai naci dukan Innaro a kanki, to kwarankwatsa ko ludayi guda kin gama sha man" ta faɗa tana share hawaye ganin ashe Joddinta ɗan iska ne bai fahimci abinda take nufi ba ya miƙe tsaye jikin nan nasa a murɗe ko ina yana tunkaro Fattu wacce take kuka riris ɗago idonta tai tana rufewa da tafin hannu "JODDi karki ƙarasho a gurina bana shonki yanzu Alqur'an tunda baki da kunya dukda kina mahaukashiya, ki juya baya na rufe idona" ƙara tunkarota yake yana nuna mata cikinsa dake murmurɗe, buɗe ido tai ta ƙara arba dashi a hakan, kuka ta fashe dashi tunawa daya taɓa ta kuma ta tabbatar yanzu tanada ciki tunda taji Innarsu Fatse tace duk Namijin daya taɓa mace ciki take shi yasa ko Baffa zata miƙawa abu bata bari hannunta ya shafi nasa, "Honi Fattu JODDi kin shusheni aradu kin mani ciki, Aradu yunwa ta kasheki yau ko ludayin fura bazan baki ba" ta faɗa tana juyawa da gudu tabar wajen da kallo kawai yake binta dan baya fahimtar abinda take faɗa kai tsaye shima ya biyo bayanta bata lura da biyonta da yayi ba, saida taje gurin Shanunta, ganin jini ya sata tunawa da ashe tayi tuntuɓe taɓa goshin tayi taji an ɗauresa, "Ohh Allah Sarki JODDi ashe temakona yai ba ɗan iskan bane, nifa nasan Joddina" ta faɗa tana juyowa kallonshi tai inda ya kwanta yai lamo alamar yunwa yake ji, tausayi ya bata, da kanta ta ɗauki kingin tsummar rigar daya yaga tana yafa masa a jiki, ƙwaryar furar ta jawo ta fara basa, sannan ta jawo kwanon tuwo tana bashi sai da yaci ya ƙoshi ta basa ruwa yasha, yana gamawa ya miƙe yana tafiya itama bin bayansa take har suka isa bukkar tasa, kingin furar ta ajiye masa tana ɗauko wata riga ta basa ta nuna masa ya saka, babu musu ya saka murmushi tayi ta fito daga bukkar tana leƙe_leƙe tana tsoron ace wani ya ganta dukda ƙungurmin daji ne ba masu shigosa sai maharba Ajiyar zuciya ta sauke ganin ba kowa ta fito harga Allah tana tsoron ranar da wani zai gansa don tasan ɗanyen hukunci za'a masa kafin su koresa dukda yana mahaukaci ba zasu ji tausayinsa ba, saida Magriba tayi sannan ya kaɗa shanayenta suka nufi hanyar gida, saida ta fara ɗaure shanayen a garke sannan ta shiga ciki, da sallama ta shiga tana wurwura sandarta babu wanda ya amsa sallamar tsakanin Innaro da kuma Saro, kowa da uwar harara yake binta, saboda ba ƙaramin haushinta suke ji ba, bata kula kowa ba ta shige bukkarta tana ɗaura zaninta ta nufi rafi wanka da can zata tsaya sai kuma taji yau tana son zuwa dandali, da azama ta dawo tana shiryawa ta caɓa uwar kwalliyarsu ta Fulani, kai tsaye dandali ta wuce, an cika da ƴam mata da samari anata kaɗe_kaɗe da bushe_bushe, cikin wasa ita babu abinda yafi burgeta irin busa, usur tayi wanda yasa aka tsaya ana ihu da sowar ganin Fattu dan kowa son busa sarewarta yake, murmushi tayi tana dawowa tsakiyar filin inda makaɗan suke, sarewar ta ɗauka ta fara busata cikin gwanancewa da fitar da wani sauti wanda yasa ƴam matan wajen da samari shiga wani shauƙi da daban, dukkan wani saurayi da budurwa sai sunzo sun mata liƙi, wani ɗan fulanin saurayi ya fito Filin yana zuba mata liƙi tare da aika mata da wani kallo yana murmushi, alamun ya bayyana mata soyayyarsa, kowa na wajen tsit yai har ita Fattun data da kata da busar tana kallonsa da mamaki ganin baya tsoron rayuwarsa tasan tasa ta ƙare, zaro ido waje tai ganin abinda ya faru Ja'e ne ya murɗe wuyan Haruna yai masa yankan rago faɗuwa yai wajen yana shure_shure harya daina jawo Fattu Ja'e yai yana kwalfa mata mari yana huci, cikin fulatanci yace "Fattu sau nawa zance miki ki daina zuwa dandali kina busa kin kuwa san irin kishinki da nake???? a kanki zan iya ɗaukar duka rayukan ƴan garin nan kin sani" Kallonshi tai tana zubar da hawaye zuciyarta na mata zafi "kishi kace Ja'e ? Kishinka ko jahilci da dabbanci tunda harka iya ɗaukar rai, wallahi Ja'e koda rayuwata zaka ɗauka bazan taɓa sonka ba zan dai bi zaɓin Mahaifina amma ba wai don ina sonka ba koda na aureka gangar jikina ce a wajen ka amma ruhina da zuciyata suna wajen wanda zuciyata ta aminta" ta faɗa tana duƙewa wajen tare da sakin wani gunjin kuka da mamaki Ja'e yake dubanta duk garinnan babu wanda ya taɓa gaya masa magana irin Fattu cije leɓensa baƙi yai yana kallon mutanen wajen, murmushin gefen baƙi yai yana damƙo gashin kan Fattu wuƙa ya zaro yana aza mata ita a wuya yace "idan na kasheki fa? kinga zuciyarki da ruhinki ba zasu tafi wani waje ba, muddin na tabbatar da hakan zan aika ki inda ba'a dawowa" yana gama faɗa ya soke wuƙar yana barin wajen Saro dake ganin dukkan abinda ya faru ta saki murmushin gefen baki tana faɗin "kaɗan kika gani Fattu" tana gama faɗa ta juwa tana barin wajen kowa watsawa yai sai Fatse ce data tausayawa Fattu tana miƙar da ita ta rarrasheta kuɗin ta tattara ta bata, kai tsaye ta juya ta nufi inda take kwana, harta hau bishiyar sai kuma taji tana buƙatar zuwa inda yake itama ta kwana acan, dirowa tai akan bishiyar ta nufi jejin tana tafiya ko alamar tsoro babu a tattare da ita, haka taita tafiya harta ƙarasa gurin, tsit dajin yake, zaune yake waje guda ya lumshe idonsa farin wata ya haske wajen lafewa tai a baki bishiya tana leƙensa kamar wata biranya haka ta ɗare bishiyar tana kallonshi, har bacci ya ɗauke ta *KANO* zaune suke a Dinnig kowa ya hallara harda Mazan gidan duka Bobbi ne kaɗai ke babu da Zaidu, su kaɗai ake jira kallon Iftihar Mom tai tace "jeki kira man yayan naku" zaro ido Iftihar tai tace "Mom kinfa san halinsa" dariya Maheer tai tace "Mom ni bari na kirasa" ta faɗa a siyasance tana miƙewa, kallonta JUNAID da Aryan sukai suna dariya ƙasa_ƙasa "Maheer zauna na kirasa kinsan shifa ba'a masa gwaninta koni nasan kafin na fito saina sha koda maruka biyar ne jihadi zanyi kawai" Zameer ya faɗa yana miƙewa dariya AFIF yai yace "tabɗi ai gidan nan aiki ya samemu yanzu zamu zuƙe yunwa ta kamamu tunda Yah Bobbi ya dawo cin abincin ma sai an mana gadara" loma ABEED ya buga yana kallonsu yace "kudai kuka sani sai ku zauna yunwa tai maku illa kafin ya fito, ina dalili na zauna yunwa tai mani ƴaƴa a ciki na haifesu ta ina" ya faɗa yana ƙara kai spoon ɗin Indomie a bakinsa Kaidai ake ji, kai har yanzu kaƙi girma kullum baka da aiki sai cin taliyar yara" Aunty Meera ta faɗi tana dariya, dariya HAROON yai yana faɗin "yo Ina girman Aunty Meera? tunda nifa har yanzu banga taɓarya ba" nifa ina tunanin ABEED mata maza ne wallahi shi ko ɗan ciwon maran nan da samarin gidannan keyi da wankan asuba ban taɓa ganin yayi ba" dariya duka suka saki "zanfa ci ubanka HAROON kuda baku jin kunyar ɓaro zance" Mom ta faɗa tana dariya, shafa sajensa yai yace "Mom kinsan bakimmu ba shida tsarki idan kin gammu ki dinga barin wajen, harararsa Samha tai tace "kudai ake ji ai" ɗaure da towel Zameer ya samu Bobbi yana shiryawa, wani yawu Zameer ya haɗiye yana sadda kansa ƙasa kamar na Allah baki ya buɗe zaiyi magana Bobbi ya dakatar dashi yana keto paper da biro yana rubutu ya miƙa masa, amsa yai yana ƙara mamakin halayen Bobbi wato ko su ƴam gidan nasu ma ba zai buɗe baki yai musu magana ba, juyawa yai yana gunguni ba tare daya bari Bobbi ya gansa ba, Paper ya miƙawa Mom yace "bai yi magana ba ga Paper kiga abinda yasa wai baya buƙatar cin komai, kuji man bala'i ita kanta Muryar tasa rowar jinta yake man" tsaki Zaidu dake baya yai yana zama tareda jawo warmer yana zuba farfesun ƴan cikin tareda haɗa kakkauran Tea babu wanda yaiwa magana ya zauna kallonsu Aryan yai yana buga musu tsawa "wai ku ubanwa kuka raina kamar ni na zauna ina matsayin yayanku amma babu mai gaisar dani amma da Munafukin can ne da tuni jiki na ɓari kun gaisar dashi yana muku wulaƙanci" Bread Junaid ya tura a baki tare da kurɓan tea yanawa Zaidu kallon rainin wayo "kai wa ka gaisar a cikin su Mom da Aunty Meera?" ya faɗa yana hararan Zaidu fatali Zaidu yai da kular farfesun yana miƙewa a zuciye ya bar wajen da kallo suka bisa Zameer yana ɗora hannu bisa kai yace "wayyo ni Zaidu ko baƙin mugu kular farfesun ya zubar shifa nake haɗiyarwa yawu tun ɗazu, wacece ta yisa?" Zameer ya tambaya "Indo mana" Suhaima ta bashi amsa miƙewa yai yana tafiya da gadara kamar bashi ba, dan dukkan ƴan gidan haka suke a gida da barkwanci da an fita kuma su zama masu gadara da Izza wanda wannan a jininsu suke Yana zuwa ya sameta tana gyaran kichen jikin nan nata fes gata ƴar kyakkyawa dukda tana baƙa amma baƙinta mai kyau ne harɗe hannuwansa yai a ƙirji yana haɗe fuska tamau "Ke" ya kira sunan juyowa tai a hanzarce tana sharce zufar da tai yatsina fuska yai yana kallonta a wulaƙance yace "maza kiyi wanka sannan ki ƙara dafa man Peppersoup ɗin da kika yi a ɗazun, sannan kisa detol ki ƙara wanke ƙazamin hannunki kafin ki girka man na baki 10 minute" yana gama faɗa ya juya, hawaye ta share a fakaice idan banda ma ƙaddara mi zai kawota aiki kamar yadda yace haka ta tafi ta wanke hannu sannan ta shiga tai wanka ɗaukar warmer ɗin tai tana nufar ɗakinsa nocking tai come in aka furta a hankali ta tura ta shiga bakinta ɗauke da sallama bai amsa ba shida HAROON saima maida hankalinsu da sukai a game suna dariya tsaye tai tana jiran yai magana "ajiye ki fice daga cewa ki wanka sai ki wani caɓa kwalliya ajiye ware bana son kallonki" ya faɗa yana ɗaure fuskarsa Maheer koda suka gama dinner up stairs ta haye tana haurawa ɗakinta wanda Mom ta ware mata, gado ta faɗa tana fashewa da kuka mai ciwo anya kuwa zata iya samun Bobbi ta ruwan sanyi mutumin da zata iya rantsuwa ta maya bai san fuskarta ba amma shi zuciyarta ke kawo mata, ya zama dole tabi dukkan wata hanya dan ganin mallakar zuciya Bobbi, share hawaye tai tana ɗaukar phone ɗin ta Mammi ta dokawa kira tana ɗauka ta fashe mata da kuka "Mammi bamu haɗu ba har yanzu,bashi ma zama gidan yanzu" "Calm down Daughter ki ƙara haƙuri kin san dai Bobbi ya zama naki an gama tunda harya amince tunda baiko ma goben na za ai maku shi, duk wani abu ki bari sai an ɗaura auren sannan ki mallake zuciyar Mijinki ke kamar ba mace ba" ajiyar zuciya Maheer tai, Mammi tana ƙara kwantar masa da hankali *BOBBI* Zaune yake a katafaren office ɗinsa ya kwantar da kansa kan kujera ya tafi duniyar tunanin daya saba, ajiyar zuciya ya sauke yana ɗauka Cup ɗin Tea yana kurɓawa a hankali, P.A ɗinsa ne ya shigo hannunsa ɗauke da takardun a ladabce Hafiz ya gaida shi gyaɗa masa kai kawai yai yana nuna masa wajen zama, zama yai sannan ya dubi Bobbi yace "Sir sun kawo mana share na Company S.M sunce ka faɗi kaso nawa kake so su zuba" gyaran zamansa yai ya ɗauko Paper da biro yayi ƴan rubuce_rubuce ya basa amsa yai yana miƙa masa takardu ya cike ya miƙo masa, karɓa Hafis yai yana risinawa ya fice da kallo ya bisa harya fita yana motsa bakinsa "kunyi naku S.M yanzu lokacina ne" ya faɗa yana shafa dogon gashin kansa wanda bai ɗauresa yau ba ya zubo sa a kafaɗa ne Sallar azabar yayi ya nufi wani meeting daya haɗa na manyan ƴan kasuwa masu neman Share na Company sa wanda harda turawa, tunda ya shiga idonsa ya shiga kan na Alhaji Madu wanda ya hakimce waje guda, murmushi ya saki ganin wasan na tafiya yadda ya kamata zama yai suka fara tattaunawa tareda faɗin duk wanda ke son Share na A.A.B Company dole sai ya zuba kaso 50 na rabin dukiyarsa, ba tareda ɓata lokaci ba suka zuba dukkansu, da kallo Alhaji Madu ke bin Bobbi,Wanda Bobbi na lura da hakan ɗage gira guda yai yana ɗan murmushi ya miƙa masa hannu cikin wayancewa sukai musabaha, tare da ɗan taɓa firar kasuwanci wanda duk dan Alhaji Madu ya fidda tantama a kansa ne Bayan kwana biyu anyi baikon Maheer da Bobbi iya one month aka saka, wanda tunda tazo koda so guda ne basu haɗu ba, danshi gogan mantawa ma yake da wani baiko nasa, su Mom ne kaɗai ke rawar gaban hantsi, haka kwanakin keta tafiya harya rage saura sati biyu *MUNEEBBA* Zaune take ana mata dilka wanda tayi wani haske na ban mamaki kyau bana kaɗan ta ƙara ba saboda gyaran da take sha wajen wata maƙociyarsu wacce take gyarata saboda gabatowar auren wanda bai wuci 3 days ba, Kasancewar Muneebba bata da wasu ƙawaye ya sata bata wani shirya event ba............. [5/21, 8:11 PM] RIAMCOOL: *BAYAN WUYA* book 1 *By Mariam sani Riamcool* *MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION* *P.19&20* ________Kasancewar Muneebba ba tada wasu ƙawaye ya sata bata wani shirya event ba, tun bayan Sati aka kawo lefe wanda akwati goma sha biyu haka yai mata kuma dukkan kayan masu tsada ne wanda Hajiya da kanta ita ta haɗa don tasan abinda take shiryawa shi yasa ta nuna ta saduda, Kallonta Hafsat tayi tana faɗin "wai kinga kuwa wani kyau na ban mamaki da kikai Muneebba, wannan idan Nazeer ɗin ya ganki anya zai ganeki?" dariya Muneebba tai tana miƙewa, sallama sukai wa Matar sannan suka nufi gida, da sallama ɗauke a bakinta ta shiga sai dai fara'arta ce ta ɗauke sakamakon ganin Mamma Ladiyo wacece ta wani caɓa ado Alamun kuɗi da hutu sun zauna mata, harga Allah Matar batai mata ba, sai dai ta danganta hakan da azabar data bawa Mahaifiyarta shi yasa bata sonta kallon Mamma Ladiyo Muneebba tai tana gaisar da ita da ƙyar, fuska a sake ta amsa tana binta da kallo ƙasa_ƙasa wanda take ayyana abubuwa da dama a ranta, shafa haɓar wuyanta tai tana maida kallonta ga Mamma, wani Munafukin murmushi ta saki ko iya haka tabar A'ishatu tayi farinciki sai dai dukkan wani abu da zai kawowa Shatu kwanciyar hankali da jin daɗi ba sonsa take ba, ya zama dole kuwa ta ƙara tashi tsaye Washe gari Mutane ne cike da gidan anata hada_hadar buki wanda yawancinsu duk ƴan unguwar ne sai kuma ƙawayen Mamma Ladiyo Sanye take da wani material fari tas ɗinkin Fitted gown na bride an zuba mata Make up fuskar nan sai sheƙi take da haske ga jan lallen da aka zana mata wanda ya ida fiddota sosai, kallonta Nazeer yake ta Vedio call yana ƙara tazbihi ga Ubangiji da zai mallaka masa wannan Kyakkyawar halitta "Masha Allah Hayatee nagodewa Ubangiji sarki gagara misali da zai mallaka man wanna haɗaɗɗiyar kyauta, Muneebba ba zan kwatanta miki yanda nake ji a raina ba kwatankwacin yadda nake sonki ba zai faɗu ba bana fatan wani abinda zai gifta a tsakanina dake bana fatan kalmar rabuwa ta gifta a tsakanimmu, zan riƙe ki na tarairayeki kamar tsoka ɗaya a miya zan kula dake mu haifi ƴaƴa mu tarbiyantar dasu" Wani murmushi ta saki mai kashe zuciya tana lumshe ido ta waresu a fuskarsa "Thanks dear insha Allah dani da kai mutu ka raba" murmushi yai yana mata sallama dan zuwa yai wanka, "ok bye take care" ya furta tare da kashe mata ido Murmushi tai tana rufe fuskarta da tafin hannunta, da ƙyar ya kashe wayar shima dan Abokansa na masa tsiya ne kar lkc ya ƙure ango ya makara Ajiyar zuciya ta saki yau jinta take cikin maɗaukakin farincikin da bazai musaltu ba, miƙewa tai Hafsat na ɗaukar su Photo wanda sunyi kyau sosai Ƙarfe 2:30 wajen ɗaurin auren damƙam yake da mutane da manyan jiga_jigan motoci na alfarma wanda kowa sai da yai mamakin ganin manyan Mutane da suka zo ɗaurin auren Zaune yake a bayan mota mai baƙin glass Wanda babu wanda ke ganisa fuskarsa sanye da farin gilashi janye gilashi yai yana share hawaye, ya gaji da wannan bakar rayuwar da yake ciki wanda dashi da iyalinsa sai dai kallo daga nesa Anya zai iya kuwa? ace ana ɗaura auren Ƴarsa guda wacce take mafi soyuwa a rayuwarsa amma ba zaije ba, kamar ba babban mutum ba haka ya fashe da kuka mai ban tausayi, Manyan Motocin da suka Kunno Kai su suka saka sa tsayawa da kukansa yana kallonsu, fitowa na cikin Motar yai tareda Securities murmushi ya saki ganin Ahmed A Sadis ya hallara tunda Motocin suka hallara gaba ɗayan Mutanen wajen hankalinsu ya dawo wajen ganin shahararren ɗan kasuwa mai ji da kuɗi, murmushi yai ya samu waje ya zauna, nan ya bayyana musu shi ɗan uwan Mamma ne yana so a bashi waliccin babu ɓata lokaci za'a fara gudanar da ɗaurin aure cikin hamzari Nazeer ya miƙe jikinsa har ɓari yake jijiyoyin kansa sunyi ruɗu_ruɗu "bana buƙatar auren nan bana so na fasa auren kada a ɗaura man aure da Muneebba wallahi bana so na fasa" ya faɗa da ƙarfi kamar zuciyarsa zata fito tsit wajen yai kowa na kallonsa da mamaki yanda yake kuka riris tareda sheshsheƙa, da gudu Alhaji Mamman yazo yana faɗin "Nazeer kana cikin hankalinka kuwa? idan baka cikin hankalinka ka dawo, ko wani abun Muneebba ta aikata?" "Wallahi bana sonta kawai na fasa dan Allah a janye auren nan kowa ya tafi" Nazeer ya faɗa, babu yadda ba'ai da Nazeer ba amma yaƙi hakan yasa Mutane fara haramar tafiya, sai dai ɗan shelar da yai magana ne akan kowa ya dawo za'a ɗaura aure yasa su dawowa ana zama, Nan take Dad ya fiddo 500k yana bada sadaki bai tsaya wani dogon tunani ba, Sbd ɓacin rai, mutane saiji sukai ana faɗin an ɗaura Auren Muneebba Muhammad tareda Asad Ahmad Bobbi akan sadaki 500k lakadan ba bashi, Nan take wajen ya kaure da hayaniya ganin abinda Dad yai tare da mamakin babban millionaire Asad BObbi da Muneebba ta aura nan take yanke ƴan faɗi ba'a tambaya ba suka fara watsawa a media, ana gama ɗaurawa Dad ya miƙe da nufin zuwa gidan su Muneebba dafashin da yaji anyi ya sashi juyawa yana kallon Abbie wanda ya dora kansa a kafaɗa yana kuka riris tareda Habib shima wanda kukan yake, ɗago da Abbie Dad yai shima hawayen nason taruwar sai dai yai ƙoƙarin shanyesu yana ƙaƙalo murmushin dole, "haba Muhammad miye na kuka kamar ƙaramin yaro kaga yadda mutane hankalinsu ya fara dawowa wajenmmu, kayi shiru mana" "Dad wallahi dole Abbie damu kammu muyi kuka baka san halin da muke tsintar kammu ba har yanzu kasan kuwa ita kanta halin da Ummi ta shiga dalilin haka fa har yanzu Ummi ko magana ba tai, ita Mamma makanta Ita Ummi rashin magana, shi Abbie Aman jini, shin Dad ka faɗa mana wanna ba abin ai kuka bane?" Habib ya faɗa tareda share hawayensa "bani da abinda zance maka Yah Ahmad haƙiƙa ji nake a yau ka maye mani gurbin yayyena banda abinda zance maka na fitar da ƴata kunya dakai, bani da bakin gode maka" Abbie ya faɗa tare da share hawayensa Murmushi Dad yai yana dafa kafaɗarsa tareda ɗago haɓarsa yana share masa hawayen yace "Muhammad ba batun gdy a tsakanimmu nima ai ƴata ce bata da wani banbanci tsakaninta dasu Iftihar kamar yadda suke ƴaƴa itama haka take a wajena, kayi haƙuri komai mai wucewa ne" A can gidan kuwa gidan ya kacame da guɗa ana faɗin an ɗaura aure, Muneebba dake ɗaki wani irin farinciki ya kamata tana tashi ta rungume Hafsat tace "Alhmdllh yau burina ya cika na zama matar Nazeer Hafsah ko yanzu na koma ga mahaliccina nayi farinciki" ta faɗa tana dariya, dariya itama Hafsat ta saki tana tsokanarta tare da kingin Abokansu, Khabir ne ya shigo jiki a sanyaye jiki ba ƙwari "bada Nazeer aka ɗaura ba Mamma wallahi bada Nazeer bane" Khabir ya faɗa yana fashewa da kuka tareda rungume Mamma kamar wani ƙaramin yaro, Salati Mamma Ladiyo ta saki da ƙarfi yadda kowa zai iya jiyowa har maƙota tace "Nazeer kana nufin bada Nazeer aka ɗaura auren Muneebba ba, to waye mijin??? Innnalilahi wa'inna ilaihirraji'un A'ishah kuna ganin jarabta" Mamma Ladiyo ta ƙarasa zancen sa fashewa da kukan Munafurci wanda kowa zaiyi zaton daga zuciyarta yake fitowa MUNEEBBA dake ɗaki tana dariya jin zancen da Mamma Ladiyo tai ya sata fitowa ɗakin da gudu tana kallon Yah Kahabir da Mamma wanda suke hawaye, kallon Mamma Ladiyo Khabir yai yana faɗin "Mamma Ladiyo Nazeer cewa yai ya fasa baya son Muneebba wallahi da kansa ya furta ya fasa" wani irin zillo zuciyar Muneebba tai tareda harbawa baki na karkarwa da jikinta tace "Yah Khabir wallahi ba gsky ka faɗa ba, ka gyara kalamanka Nazeer bai taɓa ƙina ni nasan da Nazeer aka ɗaura man aure kada ka ƙara danganta igiyar aurena tare da wani Yah Kahabir Nazeer ya riga daya zama nawa" ta faɗa tare da durƙuahewa wajen tana sakin wani marayan kuka tareda fatan Allah yasa ba dai dai kunnuwanta suka ji mata ba, "Ai kam Muneebba sai haƙuri yanzu Rabilu kefa ce man bada Nazeer aka ɗaura ba da wani Asad BObbi ne wanda duniya tasan dashi, kuji ikon Allah" Rabi maƙociyarsu data yafo zani ta faɗa basu ankara ba sai jin faɗuwar Muneebba sukai ta zube ba numfashi a tare da ita, idanunta sun wani ƙaƙƙafe, "Innnalilahi wa'inna ilaihirraji'un Muneebba ki tashi dan Allah, mukaita asibiti" Hafsah ta faɗa tana kuka, Mamma ma kukan take ita da Khabir wanda ya ɗauki Muneebba da gudu ya nufi ƙofar fita da ita, karo suka ci da Dad Wanda yake yunƙurin shigowa hankali a tashe shima ya amshi Muneebba yana nufar motar da ita Sbd tashin hankali da ƙyar Mamma tasa Hijab ita da Hafsat suna shiga Motar tareda Khabir Dad kuma na wata motar wani gudu suke shararawa har suka isa Private hospital Wanda aka karɓeta da gaggawa ganin halin da take ciki kuka Mamma keyi riris Hafsat na bata baki, taƙi tai shiru, dukansu zaune suke sunyi jugum_jugum, Abbie dake daga gefe can yana kallonsu hawaye na bin kuncinsa, dashi da Habib wanda babu halin zuwa wajensu su duka, kallonta yake zuciyarsa na masa zafin yadda take zubar da hawaye, " wannan ma na gani Aysher ban san iya kukan rashina da kikai ba, dole nazo wajenki koda kuwa a yau ɗin nan zan fitar da numfashin ƙarshe ba zan juri ganin hawayenki ba Aysher na kasa jurewa" ya faɗa da ƙoƙarin tunkaro inda take, Habib ne ya jawosa yana girgiza masa kai hawaye na zuba yace "Abbie na roƙeka kada kaje zamu iya rasaka kasan kuwa iya jinin da kake zubarwa wajen yunƙurin zuwa garesu? Abbie kada ka ƙara cilla mu a wata matsalar ka barmu da iya wacce muke ciki ba dammu ba sai dan Mamma da kuma Ummi da suke buƙatar ka samo musu mafita" ya faɗa tareda riƙe ƙafar Abbie yana kuka shima, hawaye Abbie ya share yana dawowa ya ɗago Habib yana kallo yace "naji Habib ba zanje ba amma zanyi nesa da ƙasar nan ko dan ku da iyayenku, zan bar ƙasar gaba ɗaya na nisanci kaina daga Iyalina tunda hakan shine mafitata" ya faɗa yana barin wajen da sauri, da kallo Habib ya bisa yana share hawaye shima yabi bayansa dukkan wata zirga_zirga Dad ne ya dinga yinsa wannan ne ya tabbatarwa Mamma lallai zasu iya kular mata da ƴarta, hakan yasa hankalinta ɗan kwanciya suna jiran tsammani don Doctor ya Kira Khabir da Dad, ganin sun fito fuskarsu da ƴar walwala yasa Hafsat sauke ajiyar zuciya, kallon Mamma Dad yai da tausaya a fakaice yana share hawaye yace "Alhamdulillahi tunda an samu nasar daidaita Numfashinta, dama shine yake barazanar ɗaukewa yanzun anyi nasarar daidaita sa, bacci take yanzu sai tsawon 3 hours ta farka, sai dai na sake baku haƙuri akan abinda ya faru tunda lallai wannan auren sai dai muce nufin Allah ne wanda ba muyi zato da tsammani ba haka zalika shine mijin da Ubangiji ya rubuta zata aura tun dirowarta a doron duniya, ita ƙaddara zanen zabo ce, kuyi haƙuri da kalar rayuwar da kuka tsinci kanku insha Allah komai mai wucewa ne Bayan wuya sai daɗi" ya faɗa da Murmushi hawaye Mamma ta sake sharewa tana faɗin "bawan Allah ni bani da abinda zan gode maka dan ka fitar da ƴata kunya dani kaina da ka rufa mana asiri lallai na yadda da cewa komai a rubuce yake bawa bai isa ya sauya zanen ƙaddararsa ba, haka Allah ya tsarawa Muneebba bama da tsimi da dubara, Allah yasa hakan shine mafi Alkhairi yasa kuma Abokin rayuwa ne" Mamma ta faɗa cikin dauriya Murmushi Dad yai yana ƙara jinjinawa Mamma akan tawakalli da yarda da ƙaddara, take away yai musu da yi musu sallama akan gobe zashi dawo, ɗakin da take kwance suka shiga,kwance take fuskar nan tayi fari fat hancinga sanye da oxygen hawaye Hafsat ta share tana duƙawa a wajen ta kama hannunta tana riƙewa gam, Alwalla Mamma tai tana salla la'asar da Magriba wanda tashin hankali bai barta tayi ba sai da daddare Khabir shima ya tafi zuciyarsa cunkushe da damuwa Misalin ƙarfe 3:30Am a hankali take ware manyan idanunta harta waresu duka akan farin silin ɗin Idanunta na zubar da hawaye wanda ta tabbatar da lallai ba Nazeer bane Mijin nata wani ne daban aka ɗaura mata igiyar aurensa a kanta, "Ya halayyarsa take, wane kalar mutum ne, wanene shi, wace sabuwar rayuwar ƙaddara zata gudanar, shin mai kyau ko akasin hakan?????" Waɗannan tambayoyi sune ta ɗinda maimaitawa kanta tana hawaye Gidan Mom sosai ya kacame da hayaniyar Mom tun la'asar take abu guda wanda ganin auren Bobbi na yawo a media ga kuma fuskar Dad wanda ke murmushi wannan ya tabbatar mata da lallai auren Bobbi ɗinne su kansu su Zameer abin ya ɗaure musu kai,uwa uba Maheer wacce take kuka taƙi magana sai dai bin kowa da ido, wannan ne ya ƙara tada hankalin Mom ta dinga kiran Dad da Bobbi ba ji ba gani....... Wayyo akwai fa cakwakiya, ina uban gayyar yake ma🥺ku dai yi haƙuri yau ba'a taɓo ɓangaren Fattu ba da kuma Bobbi [5/21, 8:12 PM] RIAMCOOL: *BAYAN WUYA* Book 1 *By Riamcool* *MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION* *P.21&22* ___________Tayi kiran iya kira babu wanda ya ɗaga a cikinsu daga baya ma Bobbi kashe wayoyinsa yai dan lokaci shi kanshi yana buƙatar keɓewa Dad kuwa lokacin yana Asibiti wajen Muneebba sai daga baya yaga kiran kai tsaye gidan ya nufa da sallama ɗauke a bakinsa ya shiga fuskarsa a haɗe tamau babu alamun wasa ko rahama kallon ƙasa da sama Mom tai masa cikin ɓacin rai ta miƙe "mi kayi haka? wannan wane kalar tozarci da cin mutuncin kaja mana kasan kuwa abinda ka aikata?" ta ƙarashe zancen da huci "Yes nasan abinda na aikata dan na isa ne shi yasa na aikata aure na yiwa yarona kuma ita ce wacce na zaɓa masa abokiyar rayuwa ta har abada babu wanda ya isa ya hanasa zama da ita" ya faɗa yana haura up stairs binshi tai da azama tana faɗin "wallahi ba zai zauna da wata shegiyar ƴa ba in ba Maheer ba Maheer ce zaɓina kuma ita zai aura wannan kuwa ranar da tazo gidan a ranar zata barshi dan sai ya mata saki ukku cir, wanna wane kalar rayuwa ne ka saka ƴar mutane a damuwa gashi tunda Maheer taji auren nan ko Abinci bata ci ba ƙarshe ma kulle kanta tayi a ɗaki to wallahi tallahi indai ni na haifi Bobbi sai na saka ya saki ƴar matsiyatan can kuma zanyi bincike" kallonta yai yana kauda kansa gefe guda Sbd ɓacin rai "idan bake kika haifesa ba fa?" yai mata tambayar yana kafeta da ido, itama kallonsa tai tana sakar masa wani Miskilin Murmushi daga bisani kuma ta jijjiga masa kai tana barin wajen da sauri, da kallo ya bita har shiɗa, haurawa sama yai yana shigewa bedroom ɗinsa zama bisa bed yai yana dafe kansa dake masa ciwo Mom kuwa tana shiɗa dasu ABEED ta fara cin karo suma sunyi jugum_jugum kallonsu kawai tai ta wuce, duk lkcn data gansu ranta yana sosuwa sbd ta tsani Mahaifiyarsu ganinsu kansa tuna mata yake da Mahaifiyarsu, ita ce mafarin tarwatsa mata farinciki ita ce sarauniyar Ahmad ita ce magadiyar wannan gida Sbd haifafar ƴaƴa Mazan da tayi taya zata ma bari su kansu ƴaƴan nata suyi farinciki wasan na nan zuwa kansu *Asad BObbi* A hankali yake saukowa daga Step ɗin haɗaɗɗen benen wanda ƙarafen benen kanshi na zallar azurfa ne cikin gadararriyar tafiyarsa ta ƙarfafan maza yake saukowa harya ƙarasa saukowa a haɗaɗɗen Falon wanda yaji Furnitures Set Ukku haɗaɗɗu, dukkansu zubinsu na kalar gidan sarakai ne ga wani lallausan Cafet dake malaye a tsakiyar Falon zama yai ɗaya daga cikin kujerun yana ɗaukar wayarsa ya kunna, Missed call ɗin Mom ya gani yafi hamsin ɗaga giransa guda yai yana taune lips ɗinsa na ƙasa Data ya kunna yana ƙara shiga Instagram wanda anan ne Vedio yafi yawo kallon vedio yake yana ƙara maidosa baya ya tabbatar da lallai shi ɗinne aka ɗaurawa aure ba wani ba "Mace" ya furta yana ƙara tauna lips ɗinsa, babu halittar da yafi tsana a duniya sama da mace, mace ita ce maƙasudin cin galaba a kansu mace ita ce maƙasudin shigarsa ƙuncin rayuwa wacce bai san ranar fitarsa ba, Mace ɗaya ce yake so a faɗin duniya ita ce Mahaifiyarsa, shi abinda ya ɗauki Mace ita ce makira maƙaryaciya maci amana, kuma shi ɗinne ake son yayi rayuwa da mace har biyu "ta ina zan iya? ina bazan iya ba na tsani mata kuma bazan zauna dasu ba dole ko wace ta kama gabanta" ya faɗa a hankali tare da lumshe idonsa tuno da DEEN ɗinsa mace ce ta haɗa makircin kashe masa Deen shiko ta Ina zai iya mancewa da mace, ganin tunani zai masa yawa ya sashi tashi yana shiga wani Coridor wanda zai sadasa da wani haɗaɗɗen Bedroom wanda bai cika wani karikitai da yawa ba makeken Bed ne guda ɗaya kawai sai Wardrope da mirror bethroom ya faɗa yayo wanka ya fito iya boxes ya kwanta dashi yana jan blancked ko 5 Minute bai yi ba bacci ya ɗauke sa *MUNEEBBA* tunda ta farka take faman zubar da hawaye tana motsi da bakinta Mamma dake Lazimi jin motsi ya sata juyowa tana lalube harta lalabo Hafsat dake kwance "Hafsat duba man Muneebba ce ta farka" ta faɗa tana ƙara lalabo gadon da Muneebba ke kwance, kallon inda Muneebba ke kwance Hafsat tayi tana murmushi da hawaye tace "eh Mamma ita ce" da gudu Hafsat ta fita tana kirawo wani Doctor Oxygen ɗin ya cire mata, hannuta Mamma ta kamo tana jin shesheƙar kukanta "Muneebba" Mamma ta Kira sunanta cikin dakiya "na'am Mamma" "MUNEEBBA ke ɗin musulma ce kinsan ƙaddara kinsan jarabta, ina son ki ɗauki dangana da haƙuri ki ɗorawa rayuwarki Muneebba duniya ba dukkan abinda kake so kake samu ba, zata iya yuwa abinda kake so ba Alkhairinka bane wanda baka so shine Alkairi, dukkan musulmi ana son ya zamto mai haƙuri kinsan kuwa shi kanshi haƙuri yana da ladarsa, sannan ki zamto mai yadda da ƙaddara da dangana, indai ni Mahaifiyarki ce Muneebba kuma ni na haifeki ina so ki cire Nazeer a ranki kisan cewa da igiyar aure a kanki Tunanin wani ɗa Namiji bai kamaceki ba dukda nima kaina na ɗanɗana gubar da kika lasa Muneebba sai dai har abada bana so kiyi rayuwar dani nayi, ina so kiyi rayuwar farinciki Muneebba, Muneebba dan Allah ki cire damuwar nan a ranki" tunda take maganar Muneebba ke kuka "Mamma kece kika haifeni Mamma nai maki Alƙwarin zan cire Nazeer a raina dukda shi so baya taɓa ciruwa sai dai ya ragu amma ni zanyi ƙoƙarin ciresa zan koyi son wanda igiyarsa take a kaina,sai dai ban san wace rayuwar zan gudanar ba a sabon littatafin kundin rayuwata, wane shafin sabuwar ƙaddarar zan buɗe? wannan ne ban sani ba Mamma, kuma ko ke nasan kina wannan tunanin" ta faɗa da sakin murmushin takaici mai ciwo "Muneebba kada kice haka ki yiwa kanki kyakkyawan yaƙinin jin daɗi a gidan Mijinki insha Allah wahalarku ce ta yanke saƙa" Hafsat ta faɗa tana shafa kan Muneebba, kallonta Muneebba tai tana faɗin "Hafsah akwai kingin rina a kaba" ta faɗa tana lumshe ido, yanzu ne take jin tabbas akwai wata gagarumar ƙaddararriyar rayuwa da zata gudanar, tabbas jikinta ya faɗa mata zata buɗe shafin kundin ƙaddararta ne sai dai ita yanzu komai ya sameta zata godewa Mahaliccinta dan haka yake son ganinta shiru dukkansu sukai har ɗan bacci ya ɗauke su, har sunso makara sallar Asuba,babu laifi jikin Muneebba da sauƙi, koda suka gama sallah sunyi Azhar da karatun Alqur'ani, a haka har gari yai haske rana ta fito zaune suke suna ɗan fira jefi_jefi wanda Muneebba ta ɗan saki jikinta, sallamar Mamma Ladiyo da maƙotan su Muneebba ya saka su maida hankalinsu a kansu, da azama Mamma Ladiyo ta ƙaraso tana kama hannun Muneebba "sannu ƴar nan kinji Allah yasa hakan ne mafi Alkhairi kinji kuna ganin Jarabta" ta faɗa da share hawaye dukkansu sunyiwa Mamma ya mai jiki sannan Rabi maƙociyarsu wacce gulma ta kawota tace "Ohh rayuwa kenan shi kanshi Nazeer ɗinfa tunda aka ɗaura auren ya faɗi wanda yanzu haka yana asibiti bai farfaɗo ba,ance saima an fitar dashi ƙasar waje yau zasu tafi don ko motsi bashi yi" ta faɗa da sigar gulma wacce ke cinta wani kalar dum gaban Muneebba yai ba zata iya jurewa ba ita ƙara ace ciwon ya hau kanta da gudu ta tashi ta nufi Toilet tana kullewa sakin shawa tai tana sulalewa ta fashe da wani matsanancin kuka mai cin rai sai da ta daɗe sannan ta wanke fuskarta ta fito wanda kallo guda zakai mata kasan cewa kuka tasha sai dai ganin babban Mutum kamili hakimce a gadon yana sakar mata murmushi ya sata sadda kanta ƙasa tana gaisar dashi a ladabce, Amsa mata yai yana sakin Murmushi gefe kuma ga Iftihar wacce take mata kallon raini da wulaƙanci tana tauna chewing gum yafitota da hannu yai yana mata nuni data zauna, ƙasa ta nemi waje tana zama kanta a ƙasa tana wasa da yatsun hannunta, haƙuri ya fara bata da kuma tabbatar mata zata gudanar da rayuwar farinciki daga bisani ya haɗa mata da nasiha mai sanyaya jiki wanda jikinta ya ƙara sanyi laƙwas,sosai ya kwantar mata da hankali wanda hankalinta ya ɗan kwanta ganin yadda Dad bai ɗauki girman kai ya ɗorawa kansa ba dukda matsayi da kuɗaɗen dake garesa wanda ita sai a Jarida ta sanshi batai tsammanin haka yake da son mutane ba, sai dai tana fatan ace kamar yadda yake haka kingin Ahalin nasa suke ya ɗan daɗe sannan yai masu sallama suka tafi wanda Iftihar kamar ta fasa ihu haka take ji, suna fita Mamma Ladiyo ta bisu da kallo tana jijjiga kai idanunta sun sauya kala ya zuwa ja, ganin komai zai iya faruwa ya sata ficewa daga ɗakin ta dinga tafiya harta nufi ƴar wata hanya cikin asibitin inda ba kowa tsayawa tai tana huci "me na aikata kenan? Wallahi da nasan haka abin zai kasance da ban hana auren ba wace mafita garan yanzu nasan dama guda gareni kuma nayi amfani da ita babu batun sake dawo man da ita yan ya zanyi? Muneebba ta tsallake tarkona, wallahi bazan taɓa bari A'ishatu kiyi rayuwar jin daɗi ba keda ƴarki" ta faɗa tana huci tare da zama tana tunanin mafita, ta daɗe kafin yanayinta ya dawo, da murmushi ta shiga ɗakin tana faɗin "wai ɗan zazzagaya marassa lafiyar nai kinsan ana son dubiyar marar láfiya, kai jama'a wasu mutanen na cikin hali wallahi A'ishatu ba kiga wata mata dana gani ba sai da na zubar mata da ƙwalla" ta faɗa tana matso ƙwallon ƙarya Murmushi Mamma tai tana faɗin "Allah sarki ai kin kyauta Mamma Ladiyo" koda Doctor yazo yaga jikinta yadda yai sauki sosai ya basu sallama, tattarawa sukai suka koma gida, nan mutane suka dinga shigowa dubiya akasarinsu gulma ce ke kawosu Wata ashariya Mom ta danna jin zancen Iftihar "ƴar talaka kika ce? Dad ɗinku ya rasa wacce zai aurawa sai ƴar talaka kuma ƴar matsiyata wallahi ba zata saɓuba" "saɓuwa kau taka tas da soso da sabili Naja'atu wallahi aure anyishi an gama babu wanda ya isa ya warwaresa muddin ina numfashi da rayuwata wurin zama kuwa tuni na tanadar mata ki shirya tarbarta a goben nan" Dad ya faɗa da ɓacin rai kallon baka isa ba Mom tai masa tana tashi fuuu ta bar wajen, Aunty Meera ce tabi bayanta kallonta Aunty Meera tai tace "Mom calm down mana kinsan dai kina da iko akan Bobbi ranar da aka kawota ma zaki iya sakasa ya saketa to name tada hankali" kallon ashe ba kida hankali Mom ta wurgawa Aunty Meera tana faɗin "Ameera wane iko garan akan Bobbi? banida wani iko akansa tunda har yaga kirana bai maido ba kuma yake ƙaurace man ki faɗa man wane iko nake dashi akan Bobbi" ta faɗa tana tauna leɓenta na ƙasa "koma dai miye Mom ki kwantar da hankalinki kisa yarinyar can kamar ta bar gidan nan" banza Mom tai da ita dan ita kaɗai tasan abinda ke damunta, shigowar Maheer da akwati a hannunta ya sata kallonta tana faɗin "Maheer ina zaki? "gida Mom" ta bata amsa a taƙaice tana murmushi "Maheer duk lallashinki da nai baki haƙura ba?" "Lah ko kaɗan Mom haka Allah ya tsara man can dama ba ni kaɗai bace Matar Yah Bobbi" girgiza kai kawai Mom tai tana tashi ta rakota har garden wajen Parking space shiga Maheer tai tana jan Motar wanda zuciyarta kamar ta rabe gida biyu haka take ji *YOLA* ************** *FATTU* duƙe take tana rizgar kuka kamar ranta zai fita "Baffalo ka yiwa girman Allah kada ka aura man Ja'e wallahi ban sanshi kisa fa yake a gabanmu fa ya kahe Haruna, nima ya ce zai kasheni" sandar dake hannun Baffalo ya rafka mata yana hankaɗata yace "Fattu ki shiga hankalinki baƙin cikin Shanayen da mai gari zai bani kike? da zaki ce ba kya auren Ja'e to aradun Allah ko mutuwa kika sai na aurawa Ja'e gawarki.......... [5/21, 8:12 PM] RIAMCOOL: *BAYAN WUYA* Book 1 *By Riamcool* *MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION* *P.23&24* __________"Wallahi Fattu ba zakiyi man buƙulun arziƙi ba, arziƙi na biyoni kina masa dundu, ki sani aurenki da Ja'e kamar anyi an gama ne ko mutuwa zaki bazan fasa aurar dake ba" kallonsa take da rinannu idanunta tana girgiza kai bakinta na karkarwa alamun magana take so amma ta kasa koda furta A saboda baƙinci, da gudu ta tashi ta nufi bukkarta kuka tasha sannan ta miƙe tana fita, ta bayan gari tabi don bata son wani yabi sawunta ballantana har aga JODDi kai tsaye dajin ta nufa, dutsen da take hawa tai busa nan ta hau tana shesheƙar kuka har tayi mai isarta saukowa tayi tana bin dajin tana zagayawa tana tsigo da ƴaƴan itatuwa Kai tsaye inda tasan zata sameshi ta nufo zaune yake ya haɗa kansa da gwiwa wanda wannan ya zame masa Al'ada, murmushi tayi tana tunkaro inda yake da dariya, ɗago da fuskarsa yai yana kallonta wanda itama shi ɗin take kallo Zama tai tana ɗibar ƴaƴan itatuwan data tsigo tana bashi, sannan ta ɗauki madarar shanu tana basa, sai da ya ƙoshi sannan ya miƙe yana haɗe rai yana shiga bukkar da kallo ta bisa tana murmushi ta bi sa a baya,kwance yake rigar jikinsa a cire daga shi sai dogon wandon jikinsa ko ina ka kalla yana glowing dukkan wata sura ta jikinsa ta fito duk mace mai lafiya ta kallesa tabbatas sai taji wani abu a kansa lumshe manyan idanunta tayi tana jin wani abu na daban na ziyartarta tun daga ƙafafuwanta har ya zuwa brain ɗinta kallonta yai yana nuna ta da yatsa alamun magana yake so yayi amma ya kasa,dafe kansa yai yana ƙara sama da hannunsa, Fattu ganin halin da JODDi yake ciki ya saka hankalinta ya ɗan tashi ta nufosa,hannunsa ta kama tana saukewa sannan ta ɗago da fuskarsa tana ƙare masa kallo tare da lumshe masa ido,kallonta ya keyi kamar mai son tuno da wani abu ya haɗe rai yana fincike hannunsa tare da tu reta yana miƙewa ya fito daga bukkar,ƴar ƙara ta saki tana miƙewa tare da turo baki ta miƙe itama tana fita sai dai turus tayi tana ɗora hannu a ka da zaro ido waje ganin waɗanda suka kewaye JODDi da kuma makamai a hannunsu *MUNEEBBA* rungume take a jikin Mamma tana faman rizgar kuka fuskarta lulluɓe da mayafin Lifaya wacce ta amshi jikinta fari mai ratsin zanen Flower gold jinta take duniyar tai mata ƙunci ji take da mutuwa zata zo mata tabbas babu abinda zai hana tai taimaraba da ita,ranar data daɗe tana mafarki da son kasancewa a ɗakin mijinta yau ita ce tazo mata a yadda batai zato da tsammani ba, wanda taci burin tarewa a gidansa ba shine wanda Ubangiji ya rubuta a Alƙalamin ƙaddararta ba Kuka ta sake fashewa dashi tare da sake shigewa jikin Mamma,shafa kanta Mamma tai itama hawayen na son zubo mata amma tai ƙoƙarin hanasu tana ƙara rarrashin Muneebba tare da mata nasiha mai kwantar da hankali wacce ta ratsa jikin Muneebba ta kuma shirya zaman aure tsam a ɗakin mijinta tare da amsar ƙaddararta Ƙwallon da akai a tsakar gida shi ne ya janyo hankalin su Muneebba da kuma Mutanen tsakar gidan kallon jiga_jigan matan suke yadda ko waccensu ke taunar Chewingum fuskarsu sanye da Glass ko wace fuska ba fara'a ko annuri wata uwar Ashariya Aunty Meera ta ƙunduma tana faɗin "ban zaci baƙin talaucin ya kai har haka ba,ko a mafarki ban zaci zan shigo area irin wannan ballantana haɗa zuriya da irinku"ta faɗa wani tuƙuƙin baƙin ciki na cinta wani wawan tsaki Seemah ta buga tana faɗin "Amma Dad yaci mutuncinmu da kuma arziƙimmu ko a ƙaddararren mafarki ban taɓa tsammanin zan haɗa hanya da wannan cin mutuncin ba,ke dalla fito muje" ta faɗa tana faɗawa ɗakin da Mamma da Muneebba suke harda yunƙurin take ƙafar Mamma cikin takaici da tuƙuƙin baƙinciki Muneebba ta ɗago tana dubanta baccin rashin kunya ba halayyarta bace da babu abinda zai hanata ciwa matar nan Mutunci ,kauda kanta tai tana taune leɓe tare da saukar wasu siraran hawaye waɗanda ta rasa gane na miye Miƙewa Mamma tai tana dafa kafaɗar Hafsat wacce itama baƙinciki ya hanata magana, kama Mamma tai suna fitowa tsakar gidan wanda lokacin su Aunty Meera har sun wuce suna jiran fitowar su Muneebba Mamma Ladiyo ce ta shiga ciki tana kamo Muneebba tana ƙara gyara mata mayafin lifayar tare da sakin wani Munafukin murmushi wanda ba kowa ne zai gane ba,hannunta ta kamo tana fitowa da ita tsakar gida, ɗakin Mamma Muneebba ta shiga wacce ta tsirawa waje guda ido Alamun tayi nisa a tunani da fata Muneebba tai wanda ya saka ta dawowa duniyar tunanin data lula, murmushin dole ta ƙaƙalo tana mata wanda ya kashe jikin Muneebba, dubanta Mamma tai ta ƙara mata nasiha wanda ta dinga kuka,har sai da aka fito da ita, koda zata fita taga Yaya Khabir ta rumgumesa tana sake fashewa da wani irin kuka, kallonta Khabir yai yana rarrashinta wanda shima dauriya kawai yake kamar kada ta bar gidan haka take ji har suka fito daga gidansu da ƴan rakiyarta sai Hafsat, kasancewar lungun nasu ba wajen ajiye motoci ya saka su ƴar tafiya har suka fita bakin Titi wanda security ne tako ina, ga manya manyan Motoci na Alfarma ƴan ubansu baƙaƙe wuluk, guda biyar, cikin ta tsakiyar Muneebba ta shiga kingin kuma ƴan rakiya ta gaban kuma su Aunty Meera da Seemah ne a ciki, A hankali Motocin ke tsula gudu cikinsu sai ƙamshi da kuma wani ni'imtaccen sanyi mai ratsa gaɓukka, a hankali ta runtse idonta ƙirjinta na mata wani nauyi wanda kamar an saka nannauyan dutse an danne mata shi haka take ji,ji take a yanzu ne shafin littafin kundin ƙaddararta ya buɗe, ta gaza fitar da Nazeer a cikin ranta,wanda tuno halin da yake cikin shine ke sakata kokowa da ɗaukewar Numfashinta,rufe idonta tai wasu hawaye masu ɗumj na sauka a kuncinta Wata haɗadɗiyar Anguwa ta jiga_jigan manyan masu kuɗi suka nufa tun daga get ɗin farkon shiga Unguwar kansa abun kallo ne, ƙerarrun gidaje ne haɗadɗi kai kace a ƙasar London aka ƙera su, ko a London sai ka amsa sunanka zaka iya kera gidaje irin wannan,ba zaka taɓa cewa a Nigeria akwai Anguwa irin wannan ba,zamanta sai shahararren mai kuɗi da jiga_jigan ƴan siyasa masu amsa sunansu da kuma manyan shahararrun ƴan kasuwa gidan da yafi tsari da haduwa nan suka nufa inda driver ya Danna Remote nan take Makeken Get ɗin farko ya wangale,ga samudawan sojojin dake ta muzurai suna tsaye sun kame a wajen Wani kalar dum gaban Mamma Ladiyo yai lokacin da taci karo da kalar gidan yadda get ɗin farkon kansa kamar ka shiga a wata duniya ta daban sbd haɗuwarsa da tsaruwarsa get na biyu suka tunkara inda zuciya ta kawowa Mamma Ladiyo iya wuya, gani kanshi get na biyu yanda yake wani sheƙi da walwali kamar da zallar Zinare aka kerasa,ga wasu kalar samudawan Security da suka kame a wajen, ɗaya daga cikinsu ne ya tunkaro Motocin yana dubawa, kafin ya koma ya danna Wasu Numbers nan take ya wangale suna kara danna hancin motarsu a ciki Wayyo zuciyar Mamma Ladiyo kasa ne kawai ke bata fado ba Sbd takaici,mazgewa tai tana ƙakalo fara'ar dole ta sakawa kanta, a get na Ukku suka ƙara shiga nan Aljannar duniya ta bayyana,(ku hasaso irin tsaruwarsa da haɗuwarsa, don sai na kare Page 3 ban gama zayyano maku shi ba) fitowa mutanen suka fara yi, sannan Muneebba ta fara zuro da farar ƙafarta wacce ke cikin flat shues haɗaɗɗu ƙafarta tasha jan lalle wanda ya ƙara ƙayata kyakkyawar ƙafarta a hankali ta ida zurowa da gudar tana fitowa Rabi da Hafsat ne suka kamata suna bin su Seemah wanda suka nufi wani Coridor wanda ya sada su da wani haɗadden Part mai kyau................ Only call me 08109554986 Chat me 09074759493 [5/21, 8:12 PM] RIAMCOOL: *BAYAN WUYA* Book 1 By: RIAMCOOL *MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION* Bismillahirrahmanirrahim *P.25&26* ____________Wani Coridor suka bi wanda ya sa da su da haɗaɗɗen Part, Ƙofar Seemah ta tsaya tana danna wasu Numbers nan take kofar Falon ta buɗe haɗaɗɗen Falo ne wanda yaji Funiture da kayan more rayuwa, ga wani uban sanyi da ƙamshi dake tashi, A hankali kowa ya shiga suna zama kan lallausan Cafet ɗin dake Malaye a tsakiyar Falon, ɗago da kanta Muneebba tayi ta cikin mayafin lifayar tana duban Falon wani iska mai zafi ta fuzar hawaye na bin kuncinta, duk daular da ta shigo ji take kamar ta shigo a matsatsin kurku ne, hatta sanyin Ac dake fita ji take kamar ana buso mata da hucin zafi, lallausan Cafet ɗin da take zaune ji take kamar tana zaune a bisa ƙaya ne, ta ina zata fara karɓar ƙaddarar data tunkarota?ta riga da tasan yanzu ne zata fara buɗe babin kundin ƙaddararta ƙwas ƙwas ƙwas sautin ƙarar takalminta ke badawa tana bin step ɗin a hankali tare da tauna Chewingum jikinta sanye da dakakkiyar Shadda blue color wacce taji aiki da Stone sai walwali take,wuyanta sanye da sarƙar Gold, hannunta ɗaure da Watch ɗin Diamond yatsunta ma ɗauke da zabban Diamond sai walwali suke,wani kallon ƙasƙanci da ƙyama Momm ta bisu dashi tana zama ɗaya daga cikin kujerun Falon ta ɗora ƙafa ɗaya bisa ɗaya tana ƙare masu kallo, "Meera!!! Meera!!!" ta faɗa da ƙarfi fitowa Aunty Meera tayi,"Meera me yasa zaki kawo man jinin talauci a Falo? kamar ba ki san inda zaki saka ƴan aiki su kaisu ba" ta faɗa da ɓacin rai kamar ba Mahaifiyarta ba haka Aunty Meera ta taɓe baki tana faɗin "To Ni miye laifina zaki iya sakawa a kaita a Falon" ta faɗawa tana shigewa wani Coridor Indo ta ƙwalawa kira tana sakawa ta nunawa su Muneebba Part ɗinta,tare da ƙaresu da zagi da cin mutunci, Indo na gaba suna biye har suka iso Part ɗin mai kyau da tsari shima,Falon suka shiga wanda komai na ƙawa da kayan more rayuwa yaji, kamar wacce ƙwai ya fashewa haka Muneebba taja ƙafafunta tana faɗawa bisa ɗaya daga cikin kujerun Falon ta fashe da kuka mai tsuma zuciya, kama hannunta Mamma Ladiyo tayi tana faɗin "Muneebba kiyi haƙuri da kalar rayuwar da kika tsinci kanki komai na rayuwa muƙaddarine da Ubangiji ya riga ya rubutasa tun kafin dirowarki a doron duniya, ki sani shi bawa baya wuce ƙaddararsa,duk yadda kika tsinci kanki a rayuwa ki godewa Mahaliccinki,sannan kiyi haƙuri da juriwa wajen zaman aurenki mu muna miki fatan Alkhairi zamu tafi dan ba zamu tsaya a ƙara ci man mutunci ba" wani kukan ta sake saki tana kama hannun Hafsah tare da furta "Hafsat kema tafiya zaki yi ki barni a cikin wannan baƙin gida mai cike da tarin Azababbiyar jarabta,na san ke masoyiyata ce ta gsky Hafsat kada ki barni a gidan nan mu tafi a tare wallahi ba nison auren nan mai cike da tarin ma'anoni da ƙangin bauta tun a saka ƙafata gidan nan nasan da cewar na riga da na shigo baƙin kurku, akwai abinda zai sameni Hafsat idan kuka barni ku tafi dani" Kuka Hafsat ta fashe dashi tana girgiza mata kai "don't say that Muneebba kiyi haƙuri in sha Allah komai mai wucewa ne,kiyi haƙuri kiyi zaman aurenki da zuciya ɗaya, mu zamu tafi saduwar Alkhairi" ta faɗa tana ɓanɓare hannunta da fita da sauri wani kukan na tafo mata don ba zata iya jurar ganin halin da ƙawar tata take ba tana ji tana gani haka suka fice kowa jikinsa mace laƙwas, sulalewa tayi tana gunsheƙar kuka mai ban tausayi wanda har muryarta ta sauya, sbd tsabar kuka shigowar da aka yi ce ta sakata ɗago da fuskarta tana duban Indo wacce itama ita ɗin take kallo "ga Abinci Hajiya kici" ta faɗa tana ajiye mata warmer ɗin a gabanta Ɗaga kai kaɗai ta iya mata, da tausayawa Indo ta bar Falon tana ja mata ƙofar, miƙewa tayi kamar wacce aka yiwa shegen duka, Bedroom ɗin da ke Falon na gefe ta faɗa tana ƙarewa ɗakin kallo, zuciyarta taji ta ƙara cunkushewa da wani Azababben baƙin ciki da ɗaci, Toilet t faɗa tayi wanka da Arwalla ta mayar da sallar Magriba da Ishsha'i, Abinci kuwa kaɗan ta ɗan tsakureshi tana jiran shigowar Mijin da aka ce an ɗaura mata aure ganin har 10pm ta wuce ya saka ta kulle ƙofar ɗakin tana kwanciya don jin kanta na ciwo kamar ya tsage gida biyu *MAHEER* kwance take bisa cinyar Mammi idanunwanta na tsiyayar da hawaye "Mammi wata ta fara shiga rayuwar Yaya Bobbi ba ni ba, wata ce ta fara zama uwar gidan sa kafin ni, amma na san haka Allah y ƙaddara man, Mammi na tashi da soyayyar mutun biyu na kaunacesu a lokaci guda sannan nake tsantsar kishinsu su biyu kafin Mutuwar Yah DEEN na soshi na ƙaunacesa da tsatsagwaron kishinsa,shi da Yah Bobbi, cikin ɗayan biyu na rasa wane nafi so" shafa kanta Mammi tayi cikin tausayin ƴar tata, "Daughter zanyi komai domin ganin farincikinki tabbas zan raba Auren Bobbi dashi da yarinyar ke ɗaya ce ƙwal a wurinsa " "Mammi ba zan barki ki aikata wannan zunubin ba a kaina zan zauna da Yah Bobbi ko da ace yana da Mata 3 ne ni zan zauna a ta 4, saboda ƙaunar da nake masa dukda bai san dani ba, Mammi na kasa samun zuciyar Yah Bobbi" "Daughter zaki samu zuciyar BOBBI, zan samar miki da ita tabbas zan mallaka miki zuciyar BOBBI ko da ace zan rasa rayuwata ta wannan hanyar, sannan ko da ace DEEN na raye tabbas zaki zauna dasu su biyun zaki mallaki zuciyarsu" wata doguwar Ajiyar zuciya Maheer ta saki tana du ban Mammi da mamaki "Mammi me kike nufi" "ba zaki gane abinda nake nufi ba Maheer" Numfashi Maheer ta ja, tana tashi daga cinyar Mammi, hawayen dake ambaliyar a kuncinta, ta saka hannun ta share, tare da miƙewa ta nufi ɗakinta dan jin tsohon mikin daya daɗe mata a zuciya na tashi, wato Soyayyar DEEN wanda ba tasan shi da BObbi waye tafi ƙauna ba, jiki a mace ta faɗa bedroom ɗin ta tare da faɗawa bisa makeken Bed ɗinta ta fashe da kukan tausayin kanta,zuciyarta na azabtar da ita da soyayyar mutum biyu, sai da taji kamar kanta zai tsage gida biyu sannan tai shiru tana mayar da numfashi,bacci ɓarawo na ɗaukar ta ********************** *ASAD BOBBI* Ƙit ƙit ƙit sautin ƙarar agogon ɗakin ke badawa a daidai ƙarfe 2:00Am na dare a dai_dai lokacin ne kuma wayarsa ta fara ƙara Alamar Alarm ne ya buga, A hankali ya fara ware manyan idanunsa tare da motsa bakinsa A hankali yana karanto Addu'a, kamar an tsikaresa yai wuf yana miƙewa da azama, Bathroom ya faɗa ya fito, wasu kaya da ke gefe baƙaƙe wuluk ya ɗauka yana sakawa sannan ya ɗauki baƙin ƙyalle yana rufe fuskarsa, komai na jikinsa sai da ya rufe da baƙin ƙyalle, wayoyinsa ya kashe yana ajiyesu a gefe ya fice wani Coridor yabi yana tafiya har ya isa ɗan ɗakin,mabuɗi ya saka yana buɗewa tare da haska Tocilan ɗin hannunsa, du bansa ya maida gefe yana kallon Mutumen dake kwance shi ma da kalar shigarsa, cikin tafiyarsa ta Jaruman maza ya tunkarosa, duƙawa yai yana yaye baƙin ƙyallen daya rufe fuskarsa ya kware, ƙare masa kallo yai yana sakin wani Miskilin Murmushi, tare da zare ID card ɗin da ke gaban rigar mutumin da kuma phone ɗin sa, da azama ya fito yana rufe ɗakin tare da bi ta ƙofar baya, wanda babu wanda zai taɓa cewa akwai wata ƙofa a tanan, ɗan gudu gudu yake haɗawa, harya fice bakin layin gidan nasa, wayar y kunna yana turawa Number dake cikin Sim ɗin message, kamar jira ake sai ga wata mota baƙa wuluk, dai dai wajensa ta tsaya ana buɗe masa murfi, da Azama ya faɗa cikin motar, rufe marfin Motar aka yi mutumen dake gefensa yana saka masa baƙin ƙyalle ya rufe masa Idanu, da ƙarfin gaske suka figi mota suna sharara Uban gudu kamar zasu tashi sama,sunyi tafiya ba ta wasa ba sannan suka isa mugun ƙungurmin jejejin wanda ba zaka taɓa tsammanin mutum zai kawo kansa a gurin ba Fitowa sukai suna tsayawa bakin gidan tare shigewa a ciki,taresu wasu ƙazdawan Mutane sukai tare cewa su nuna ID card nash, nunawa sukai sannan suka shige, wata ƴar hanya suka bi wacce ta sadasu da wani ɗan ƙaramin Holl, da bismillah ya ɗaga ƙafafunsa yana shiga, kujera ya ja ya zauna suma haka mutanen da suka tafo a tare, Mutane nen wajen ya kalla a ƙalla sun kai 12 a wajen taune lips ɗinsa na ƙasa yai yana bin kowa da ido Miƙewa wani mutum yai yana zagayasu tare da ƙirga su, sannan ya dawo ya zauna, tare da gyaran murya ya fara magana da muryan mugaye masu ji da ta'addanci "As you know, every beginning of the year we have this meeting bcos muna son ƙara ƙwatarwa wannan ƙungiya tamu ƴanci, sannan muna kawar da duk wanda ya shige mana gaba,a wannan shekarar muna buƙatar akwatin wasiƙar sirrikan Company A.A.B limited don shine ya shige mana gaba yanzu ya hana masana'antummu ci gaba, shi ne ya saka aka fara zaƙulu gurɓatattun Company mu, da wasiƙar ce kaɗai za mu iya cin galaba a kansu, wannan shi ne Step one wanda idan yai za muje a Step 2, ina son a fitar da gwarzon Namiji wanda zai iya satar Akwatin wasiƙar a ƙasar Italian" wajen tsit yai kowa na Imagine cikin dakiya da murmushi Bobbi ya miƙe yana sauya muryarsa ya zuwa ta gwarazan maza da tantirai "Can I choose someone who can do this job for you?" da kallo mutumin ya bisa yana miƙewa ya daki kafaɗarsa "Yes you can as long as we have a mailbox" Murmushi ya saki yana furta "ok Sir" fitowa yai yana zagayasu, kafin ya ƙure ƙazdin Mutumin dake zaune a wajen wanda tabbas ya ganesa kuma ya sansa gun a jajircewa wajen ta'addanci da cin galaba yana son a kara a wasan shi ya sa zai zaɓesa, hannu ya saka yana nuna sa "Of course wannan zai iya, in har yai nashin nasara nine zan karɓi hukuncinsa ina da sure akan zai mana abinda muke so" Shiru shugaban yai yana furta " rashin nasara fa yana dai_dai da fitar numfashinka, muddin muka faɗi a matakin farkon nan za kayi ban kwana da rayuwarka, ka san mu kammu abin sai ya shafemu a wajen manyan Shuwagabannin ƙungiyar nan" "Yes na Amince" ya faɗa yana zama tare da danna zoben hannunsa yana binsu da ido, kowa bashi dama akayi akan su faɗi ra'ayoyin su akan zaɓen wanda zai saci mailbox din, wasu suce bai yi ba wasu suce yayi, waɗanda suka fi raja'a shine zaben da akayi yayi shi yasa aka bar wanda Bobbi y zaɓa ************** *YOLA* Fattu cikin tsoro da razana Fattu ke bin Ja'e da su Sa'adu da kallo, girgiza kai tayi hawaye na biyo kuncinta, wani wawan mari Ja'e ya kwalfa mata, yana ƙara sauke mata wani a kunci, "Fattu dama ke ƴar iska ce? Wato iskancin naki ya fi ƙarfin ki bi na gari sai dai ki jawo mana baren kwarto ki kawo mana,to wallahi yayi ta rayuwarsa zan rabasa da duniyar, sannan nayi abinda nake son yi dake a yanzu kafin aurena dake, zan yaga miki rigar mutunci Fattu" ya faɗa yana kai hannunsa jikinta yana kince zanin jikinta durƙushewa tayi a wajen tana fashewa da wani kalar marayan kuka mai ban tausayi tare da girgiza masa kai.......... [5/21, 8:13 PM] RIAMCOOL: *BAYAN WUYA* *Book 1* *By: RIAMCOOL* *MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION* *P.27&28* _____________Durƙushewa tayi a wajen tana sakin wani marayan kuka tare da ƙanƙame jikinta tana girgizawa Ja'e kai bakinta na karkarwa "Wallahi ban taɓa abinda kake zato ba, haka zalika ban taɓa kusantar zina ba, ina ƙyamatar zina ina ƙyamatar mai yin ta, kamar yadda Ja'e kai ma nake ƙyamatarka na tsani halayyarka ta zinar" ta faɗa tana zubar da hawayen takaici wani wawan mari ya sake kwalfa mata wanda ya saka bakinta fashewa yana tsartuwar jini, dogon gashin kanta yaja da ƙarfi yana ɗagota kafin ya fashe da wata muguwar dariya yana bin manyan Boobs ɗin ta da kallon haɗama,fuskarsa ya kai dai_dai sai tinsu yana gogawa, wanda nan take wani matsanancin ɓacin rai ya ziyarci Fattu, turesa take da iya ƙarfinta tana ihu, tare da kiran JODDi wanda tunda Ja'e ya riƙe Fattu ya ke dubansa da rinannun idanunsa bakinsa na karkarwa tare da jikinsa kamar mazari rigar jikinta yake ƙoƙarin zarewa wanda ya riƙeta da iya ƙarfinsa yana son cimma burinsa, kamar mai nazari haka JODDi ya lula yana kallon dutsen dake gabansa, hannun ya saka yana ɗaga ƙaton dutsen da iya ƙarfinsa yana saukewa Ja'e a kai, wata muguwar ƙara Ja'e ya saki yana dafe sai tin gefen kansa wanda ya fashe yana tsartuwar jini, cikin dakiya da tafiyar ƙarfafan maza ya tako ya zuwa gun Ja'e yana ƙara shaƙosa da iya ƙarfinsa, ya ƙara kai masa wani wawan duka a gefen wuyansa wanda ya saka sa tafiya luuuu yana faɗuwa idanunsa na rufewa wanda numfashinsa ya tsaya cak cikin razana Sa'adu yaja da baya yana yada makaminsa,yana barin wajen da gudu cikin tashin hankali, jikin Fattu na karkarwa ta miƙe tana ja da baya tare da ɗora hannu a ka, kallonta JODDi yai yana ɗaukar zaninta ya miƙa mata tare da kauda kansa gefe yana shigewa bukkar Zanin ta ɗora tana duƙewa wajen ta fashewa da kukan tashin hankali,domin tabbas ta san akwai babban Abin da zai biyo baya muddin Ja'e ya mutu, yan zun ta san da cewar rayuwar Joddinta na akan haɗari, amma taya zatai ta cecesa daga wannan ƙangin daya jefa kansa a ciki ta ina zata ja sa su gudu domin tsira da rayukansu waɗanda suke daf da gangara ************************* MUNEEBBA Kiran sallar Asuba ne ya tasheta daga barcin wahalar daya kwasheta mai cike da mugayen mafarkai masu firgitarwa bakinta ɗauke da Addu'a ta miƙe tana ƙara buɗe idanunta waɗan da su kayi mata nauyi ta kasa buɗesu saboda kumburin da su kayi kamar wacce aka yiwa shegen duka haka ta miƙe ko ina na mata ciwo Toilet ta faɗa tana wanka da ɗauro Arwalla tare da kabbara salla, bayan ta idar ta hau rera karatun Alqur'ani wanda ya fara sanyaya mata zuciya, ta daɗe tana karatu kafin ta ɗaga hannayenta sama tana kaiwa Ubangiji kukanta,bata tashi daga kan sallayar ba sai da rana ta fara fitowa sannan ta fito Falo tana kwanciya nan take wani sabon baccin ya sake kwasheta ruwan sanyin da taji an zuba mata ya sakata tashi a razane tana furta sunan Ubangiji, bata ida dawowa ba taji an kwasheta da mari tare da ƙara mata wani,hannunta dafe da kunci ta ɗago tana kallon Mommi wacce take Binta da kallon wulaƙanci "ke har kin samu wajen zama ki kwanta ki huta ko? to ki sani wallahi tun yanzu zaki fara karɓar hukuncinki, na aurar man Yaro da ki kayi, ke da rayuwar jin daɗi a gidannan har abada, ki sani Auren bauta ne ya kawoki gidan nan domin bauta ce zaki ci gaba da yi mana tun daga yau" tun da Mommi ke maganar Muneebba ta mayar da kanta ƙasa hawaye na mata ambaliya a kunci "Ya Allah wannan wace kalar ƙaddarariyar jarabawa ce ka jarabceni da ita a lokaci guda? baya ga wacce nake ciki"ta tambayi kanta "Maza tashi ki sauya kayan jikinki ya zuwa na hause mad kizo ki shige cikin ƴan aiki domin tun daga yau zaki fara aiki,yau ko mai kece za kiyi, sannan tun daga yanzu ina son duk wanda zai zo ki nuna masa cewar ke ƴar aiki ce, har Mijin naki karki nuna masa cewar kece matarsa zan san yanda zanyi" kamar wata taɓaɓɓiya haka Muneebba ke bin Mommi da ido da mamaki, wanda marin da ta sake ɗauketa dashi ne ya sakata dawowa hayyacinta, da yatsa Mommi ta nuna ta tana furta "ke ki bini a sannu wallahi ba'a min da wasa ki aiwatar da abinda na umarceki ga kaya nan na baki nan da 5 Minute ki canja ki fito" ta faɗa tana juyawa kamar jira Muneebba take ta fita ta fashe da kukan da sai yanzu ta samu ya fito, wace kalar baƙar rayuwa ce ke shirin tunkarota? baya ga ƙaddarar rabuwarta da Nazeer,ga kuma wata na shirin ɓullo mata ta ɓoye kanta a gurin Mijinta, hawayen ta share tana cire kayan jikinta ta mayar dana house mad wanda riga da skert ne blue color, hular ta ɗauka tana saka ma kanta, kamar wacce ƙwai ya fashewa haka ta fito tana tafiya a hankali tsayawa tayi ta rasa ta hanyar da zata bi taje Part ɗin Mommi, bubbuga bayanta da taji anyi ya sakata juyowa tana kallon Indo wacce take sakar mata Murmushi wacce daga gani ba zata wuce sa'arta ba, "Sannu ko Hajiya ce tace nazo naje dake mu fara aiki" Indo ta faɗa da ƴar fara'a murmushin yaƙe Muneebba ta ƙaƙalo tana ɗaga mata kai ba tare da tace ƙala ba, duk inda Indo tayi nan Muneebba ke Binta, wani Coridor ta jata in da zata kaita waje shugabarsu ta bata aiki, tafiya suke har suka isa Side ɗin ƴan aiki waɗanda kowa aikin gabansa yake, ɗakin dake daga gefe Indo ta shiga da ita da sallama ɗauke a bakunansu, amsa musu ƴar dattijuwar dake zaune tayi cikin mutuntawa Muneebba ta sake gai sar da ita "Ok kece wacce Hajiya tace sabuwar ƴar aiki za a kawo na baki aiki?" "Eh" ta furta tana wasa da yatsun hannunta, "ok Indo je ki gwada mata Falon Hajiya da ɗakunansu in da ita ce zatana dinga kula da gyaransu, sai fannin girkin da zaku ɗin ga shiga kichen a tare" Baba Sa'a ta faɗa *Asad BObbi* bai baro wajen ba sai ƙarfe 4 na dare wan da sai da aka rufe masa idanunsa da baƙin ƙyalle sannan aka mai do sa in da aka ajiyesa ta ƙofar baya daya fito ta nan yabi ya koma yana shiga ya cire vaƙar shigar da yai yana shigewa ciki, haɗaɗɗen Falonsa ya nufa yana zama kan ɗaya daga cikin kujerun zobe dake hannunsa ya kalla yana murzasa, nan take ya kawo wata jar danger, murmushi ya saki yana miƙewa.ya faɗa bedroom tare da dauko Laptop ɗin sa, zama yai yana kunnata kafin ya fara sarrafata cikin gwanancewa hannun ya saka yana zare zoben hannunsa tare da ɓalle dutsen sama ya fito da ƴar wata na ura, Flash ya ɗauko yana sakawa a ciki, sannan ya saka cikin computer, Vedio da ta naɗa ya Kunno yana kallonsa a tsanake, tun daga shigarsa motar har ya zuwa isarsu jejin da akayi Meeting ɗin Ƙara kallon vedio yake tare da kallon hanyar da suka bi, wacce babu wanda zai yi tsammanin akwai wata hallitar ɗan Adam da zata iya ratsawa cikin ta cikin jejin,Ajiyar zuciya ya saki yana lumshe manyan idanuwansa "shin ta ina zai fara tarbar wannan gagarumin aikin dake tunkarosa?" ........... Plz ayi manage da wannan 😊 [5/21, 8:13 PM] RIAMCOOL: *BAYAN WUYA* *By: RIAMCOOL* *MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION* *Assalamulaikum Habibties kuyi haƙuri bi sa ga tsayawata da Rubutun Bayan wuya kwana biyu, I'm Appreciate da kulawa* *Bismillahirrahmanirrahim* *P.29&30* _______________Miƙewa yai yana faɗawa Bathroom yai wanka tare da ɗoro Arwalla kasancewar Asubah tayi, jikinsa ɗaure da towel y fito ɗayan towel ɗin kuma yana goge gashin kansa, Jallabiya ya zura yana ɗaure dogon gashin kansa ya fita Masallaci Ko da ya dawo a gajiya ya kwanta yana rufe idon sa wani bacci mai mai nauyi na ɗibarsa Bashi y farka ba sai wajen sha biyu na rana ya buɗe idanuwansa, bakinsa ɗauke da addu'a y tashi yana janye dogon gashin kansa wanda y rufe masa fuska, cikin jarumta da kuzari Bobbi y miƙe yana shiga Bathroom wanka ya sake yi ya fito, cikin tafiyarsa ta ƙasaita ya ƙaraso , haɗaɗɗu Lotion ɗin sa masu ƙamshi ya shafa, kasancewarsa ba ma'abocin saka manyan kaya ba ya saka sa ɗauko ƙananan kaya ƴan ubansu masu matuƙar haɗuwa da tsada brown color, sai rigar cikin da take fara , agogon Diamond ya ɗora a tsintsiyar hannunsa wacce ta zauna tsam a Kyakkyawan hannun nasa, kama dogon gashin kansa yai yana ɗaurewa wanda yake vaƙiƙƙirin sai ƙyalli yake, turaruka masu tsada da ƙamshi y feshe jikinsa dasu, sosai y zuba uban kyau dan tabbas duk wata ƴa mace mai jini a jiki ta gansa dole wani abu y ɗarsu a ranta, kyakkyawan Ba indiye sak Bobbi ya fito, fuska a haɗe ya ɗauki wayarsa yana nufo inda Photon DEEN yake, murmushi ya saki wanda fararen hakoransa suka bayyana yana shafa photon kamar yacce ya saba duk lkcn fitarsa da kuma dawowarsa, a faffaɗen ƙirjinsa yaiwa Photon masauki yana rungumesa tsam a jikinsa tare da sauke Ajiyar zuciya "DEEN ta ina zan fara ɗaukar maka fansa ne?," Ya tambayi kansa ya jima a haka kafin ya sauke Photon a ƙirjinsa yana ƙarewa Photon kallo wanda DEEN ɗin ke dariya, lumshe idanuwansa yai yana ƙara buɗesu ya mannawa Photon sumba ya fice koda ya fita escord nashi na nan a baki ƙofar ɗakinsa, fararen motoci farare sol aka shirya masa ƙirar Bugati masu matuƙar kyawu da birgewa, cikin ta biyu aka buɗe masa yana shiga y hakimce a baya tare da ɗora ƙafa ɗaya bisa ɗaya yana lumshe idanuwansa wanda wannan ya zame masa Al'ada,ba tare daya kalli Driver ba y bashi Address ɗin inda zasu nufa, cikin tsari da tsaruwa motocin suka bar harabar gidan nasa suna nufar gidan Dad, a hankali Motocin suke tafiya gwanin burgewa da tsari don tun da suka hau Titi duk wan da yaga tabbas y san wani babba ne zai wuce, hakan ya saka ana kaucewa a basu hanya ba tare da ɓata lokaci ba suka isa gidan tun daga wucewarsu get ɗin farko Bobbi ya tsinci kanshi cikin wani kalar ɓacin ran daya rasa na miye, Addu'a yaci gaba da yi harya samu zuciyarsa ta lafa da ɗacin da tai, jin ƙara buɗe murfin motar y saka sakasa dawowa tunanin daya tafi, yayi five minute kafin ya fito, A hankali yake tafiyarsa mai cike da Izza da tsantsar jarumta, ƙofar Falon ya buɗe bakinsa ɗauke da sallama wacce ba ta fito ba, Mommi da Mammi da suke zaune suna ƙara tsara yadda bikin Maheer da Bobbi zai kasance, ganin Bobbi ya saka Mommi miƙewa tana tunkarosa rungumesa tayi tana sakin kuka "Asad ina ka shiga? ka barni cikin zullumin halin da kake ciki akan auren da akayi ma" ta ƙarashe da kuka hada sheshsheƙa, hannunsa ya saka yana ɗago da fuskarta ya share mata hawayen tare da sakar mata Murmushi, yana furta "Ba abin da ya faru dani,Ayuka ne su kai man yawa,ki kwantar da hankalinki Mommi" da to ta amsa tana kamo hannunsa tana zaunar dashi murya a dashe ya gaisae da Mammin Maheer,kallonsa Mommi tayi tana kiran sunansa "Asad" da na'am y amsa yana mai da dukkan wata nutsuwa tasa a gunta "Asad me ka ɗauki wannan auren na Maheer?" Mommi ta tambaya, cikin ko in kula y furta "Auren haɗi" wani ɗaci da zafi ne y ziyarci zuciyar Mammi akan furtawar da yai auren haɗi, wato ƴarta ce kaɗai ke hauka, ƴarta ce kaɗai ta makance a soyayyar Bobbi,ba tare data kallesa ba ta furta "Bobbi auren haɗi fa kace ?" "Yeah" ya furta yana miƙewa ya bar Falon, da kallo ta bisa tana girgiza kai"Anya Yayah Naja'atu zan iya bayar da auren Maheer ga Bobbi?" "Coz of what da ba zaki iya bayar da Maheer g Bobbi ba? bayan magana ta ƙare saura fa 5 days aurensu ya ɗauru ,ita Maheer ɗin ba mace bace da ba zata iya sace zuciyarsa ta hanyoyi daban_daban ba?" dogon Numfashi Mammi taja tana furta "duk abinda kika lissafa zata iya mana, sai dai ina ƙara tsoron wulaƙancin Bobbi da kuma kishiyar ta don kin san talakawa da baƙin hali,yanzu haka baki san abinda take shiryawa ba, dole fa mu tashi tsaye Yaya Naja'atu ina tsoron kishiya ta kassara man yarinya" dariya ta fashe da ita tana furta "su ɗin talakawa wane power garesu? da zata iya dukkan abinda kika lissafa, ai tun da ta shigo gidan na wllhy harta iyayenta ta rabu dasu dan ko nan da can ba zan barta taje, ba sannan sai na mayar da ita jakar gidan nan" *MUNEEBBA* duƙe take cikin rana, ga Uban wankin dake gabanta, tana cizga sai faman miƙewa take tana sharce zufa, ga Aunty Meera dake zaune bisa kujera cikin inuwa tana korawa da lemu hannunta riƙe da wayar wuta, jin bayanta ya riƙe ya saka Muneebba ɗagowa tana yarfe hannunta tare da sharce zufa tana sauke wahalallen numfashi "Ke!!!! uban mi ya kaiki ɗagowa ba cewa nayi ba dukkan wankin dake gabanki sai kin wanke sannan ki ɗago" hawaye ta share tana furta "yi haƙuri bayana ne ya riƙe shi yasa na ɗago" Taɓe baki Aunty Meera tayi tana furta "Bayan naki ya ƙille idan y tashi ba damuwata bace" ba tare data ƙara cewa uffan ba ta mayar da hankalinta kan wankin ga cikinta dake ta faman uban ƙugin yunwa don Aunty Meera tace ba zata ci Abinci ba sai ta idar da wankin dake gabanta, tabbas ta san da ace a gidan Nazeer take da tana can suna gudanar da tsabtacciyar soyayya, sai dai ƙaddararta data juye a bisa yacce ta santa, tazo mata a bai _bai tare da sanyata cikin halin rayuwar da batai tsammani ba, tabbas wannan auren sai dai ta kirasa da auren Bauta domin bautar ce ta kawota, cikinta taji yana juya mata da wani kalar tuƙar Amai ga gaɓoɓin jikinta ji take kamar an mata shegen duka,jiki ba ƙwari ta ci gaba da wankin, har ƙarfinta ya ƙare sannan ta ida, miƙewa tayi tana tafiya kamar zata faɗi saboda jirin dake son yada ita, wajen Baba Sa'a ta nufa tana zama, cikin yanayin tausayi Muneebba ta kalli Baba Sa'a tana faɗin "Baba Sa'a dan Allah Abincin zaki bani nafci yunwa nake ji" "Ayya ƴar nan Abinci kuwa tuni ya ƙare sai dai ki haƙuri a girka wani, idan kuma ba zaki iya ba kije wajen Hajiya ta sam miki" Jiki a mace ta miƙe dan babu yadda ta iya dole taje, kamar wacce ƙwai ya fashe mawa haka ta nufi part ɗin Mommi a hankali ta tura ƙofar Falon bakinta ɗauke da sallama daga Mammi har Mommi shiru su kayi suna jifanta da ƙasƙantaccen kallo wanda ya saka ta kauda kanta gefe guda tana haɗiye abinda ya tsaya mata a maƙoshi, durƙusawa tayi tana sadda kanta ƙasa tare da furta "Hajiya kamar yadda Allah ya temakeki ki taimakeni wllh yunwa nake ji idan ban ci ba ji nake kamar zan mutu dan Allah ki bani Abinci naci" ta ƙarashe zancen tare da saukar wasu hawaye kallon takaici Mommi ta bita dashi tana furta "A gidan uwarki zan baki Abinci ai wallahi wahala ce kin ɗaura aure da ita kenan shegiya jakar banza matsiyaciyar talaka, ƴar gidan talakawa marar Asali da galihu, har yanzu baki fara ganin komai ba na yankin azaba, wallahi sai kinyi da na sanin shigowarki gidan nan" sosai mu nanan kalmomin da Mommi ta jefeta dashi suka tsayar mata a rai tare da ɗago idanunwanta tana duban Mommi dasu wacce ke ƙara jifanta da kallon tsana, "Fice man a Falo ko nayi miki shegen dukan da ba za'a iya ganeki ba shegiya mai kama da Mayun daji" jiki a mace ta miƙe tana fita daga Falon,zuciyarta na mata wani kalar suya da zafi, ta ina zata fice ta bar wannan baƙin gida wan da y zame mata baƙin kurkuku, da ƙyar ta idasa fita daga Part ɗin tana nufar Garden ta nemi inuwa tana zama,Idanunwanta ta ɗaga tana kallon sama hawayen tausayin kanta na zubo mata da kuma tunanin Mamma da Yah Kahabir, zamewa tayi daga zaune tana kwanciya tare da dafe cikinta wanda take jin tamkar babu komai a cikinsa, ga jikinta dake ta faman Kyarmar masassara, Jin ƙarar tafiya na tunkaro inda take ya sakata tashi da ƙyar tana bin inda take jin sautin tafiyar da kallo, Tafiya yake cikin ɗan sassarfa jikinsa sanye Da Kayan Pajames Kafaɗar sa rataye da School bag miƙewa tayi jikinta na rawar sanyi da karkarwa ta tunkaro ABEED tana zubewa a gabansa ",Ƴal laɓai dan Allah kai taimakeni da Abincin da zan ci yunwa nake ji" ta ƙarashe zancen da ƙyar sbd galabaitar da tayi ɗago da fuskarsa yai yana kallonta tabbas dai wannan Ma'aikaciyar gidan ce "Amma taya kika zauna da yunwa baki ci Abinci ba, naga dai gidan ko ina wadace yake da Abinci" ya faɗa yana ƙarewa Muneebba kallo "Naje ko ina sun ce babu ya ƙare sai an girka wani" ta faɗa tana kallonsa Jim yayi sannan yace "ok bani minti biyu" da to ta amsa tana komawa inuwar ta zauna bai fi minti biyun ba sai gashi ya fito da Flat ɗin Abinci da ruwa, waje ya samu ya zauna da murmushi ɗauke a fuskarsa ya miƙa mata, hannunta har ɓari da kyarma yake wajen amsar Abincin, buɗewa tayi taga Shinkafa ce da miya sai Salat da zaƙo_zaƙon nama a ciki, spoon ɗin ta fidda tana gyara zama tare da bismillah ta fara cin Abincin ba ƙaƙƙautawa hannu baka hannu ƙwarya, tun da ta fara cin Abinci yake kallonta da mamaki, don duk uban Abincin dake shaƙe a Flat ɗin sai da ta cinyesa tas, sannan tabi da ruwan sanyi,wani ni'ima taji na saukar mata, ɗago da idonta tayi tana furta "Nagode" "Don't mind but You New house mad? ya tambayeta da ƴar dariya Itama cike da jin kunya da kuma tausayin kanta ta ɗaga masa kai tana miƙewa ************************************ *YOLA* *FATTU* cikin ta shin hankali ta shiga bukkar da niyyar Jawo JODDi su bar rigar don tana jin tsoron Abinda zai biyo baya kwance ta samesa ya ɗaga kansa sama idanunwansa a buɗe "JODDi zo muje" ta furta tana ƙara leƙawa bai fahimci abin da take faɗa ba illa bin ta da ido da yake, kamar Fattu ta kurma ihu haka take ji sbd ta shin hankali Jin hayaniya na tunkaro inda suke ya sakata leƙawa tana kallon dandazon Mutanen da suka nufo inda suke ko wane da makamai a hannunsu......... [5/21, 8:13 PM] RIAMCOOL: *BAYAN WUYA* *BOOK 1* *By: RIAMCOOL* *MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION* *BISMILLAHIRRAHMANIRRAHIM* *P.31&32* ______________Ganin Mutanen na ƙara tunkarosu ya saka jikinta kyarma don tabbas ta riga da tasan kashe mata Joddinta za ayi,ita kuma sai ta karɓi hukunci tsatstsaura idan har Ja'e bai mutu ba da gudu ta tunkari JODDi hawaye na bin fuskarta hannunsa ta kama tana son miƙar dashi "JODDI miƙe mu tafi za su ƙaraso" ta furta tana son ta dashi haɗe rai yayi yana ture hannunta tare da turata gefe guda yana kallonta, bata bi takan wannan ba ta ƙara tun karosa tana fashewa da kuka,ganin yadda suka shigo haiƙam da mugayen makamai a hannunsu, gabansa ta tsaya tana karesa tare da girgiza musu kai tana furta "ku ƙyalesa don Allah wallahi bai san komai ba, nice na dace da hukuncin ba shi b......" bata idasa ba Baffalo ya ɗaga hannu ya wanketa da mari yana furta "Fattu kin cuceni Allah ya isa tsakanina dake, dama ashe yawon iskanci kike zuwa daga yau na fidda ki a jerin Ƴaƴana ki fidda ran cewar ke Ƴata ce, na barwa duniya ke Fattu, wallahi nayi da nasanin haifarki kin jawo man abin faɗa a gari" ya ƙarashe yana juyawa cikin ɓacin rai Fattu kam dukkan wani aiki da ƙwalwarta keyi cak ta tsaya kalmar Allah ya isar da Mahaifinta yai mata na dawo mata da kuma furta ya barwa Duniya ita, "waye zata faɗa mawa ya yarda da cewar ita ba fasiƙa bace sannan abin da suke zato ba haka yake ba" ta faɗa wasu zafafan hawaye na bin kuncinta juyawa tayi da nufin ƙara kare Joddinta amma sai taga wayam babu shi, sai dai hayaniyar dake dakwai, da gudu ta fita tana nufar wajen cincirandon Matasan dake gewaye da JODDi, turesu tayi ta wuce, hannu ta ɗora a kai tana kurma ihu tare da son nufar in da Joddinta yake a kwance cikin jini malale gashi ko motsi ba yayi, riƙeta kam wani Hassanu Abokin Ja'e yai yana ƙara wanka mata mari, tare da fizgarta yana tafiya da ita duk cikin mutanen babu wanda yai yunƙurin da Katar dashi, kowa Allah wadai yake da Fattu, cikin rashin Imani da tausayi Hassanu ya fizge zanin Fattu da kuma rigarta yai mata zigidir cikin Al'umma, Kuka riris take tana niyyar kare jikinta amma babu hali sbd mugun riƙon da akai mata, a haka suka dinga tafiya har aka isa fadar mai gari da ita, wan da nan ma mutane ne cike da ita daga Mata har maza, JODDi suka fara ɗaurewa a iccen bedi wanda jinin har yanzu bai daina zuba ba Fattu ma ɗaureta sukai wacce ta kasa ɗaga kanta ta kalli kowa, idanunwanta basu daina zubar da hawaye ba, Kowa na wajen tsit yai ana sauraren hukuncin da mai gari zai yanke, shiru mai gari yai yana kallon Ja'e wan da aka samu jinin ya tsaya domin harya farfaɗo,gyaran Murya mai gari yai ya fara magana "To kamar dai yadda kuka sani dukkan wani na cikin garin nan muka kama sa da aikata zina za muyi masa horo mai tsanani sannan mu koresa daga nahiyar garimmu, don haka hukuncin Fattu da za muyi mata ai mata bulala ɗari sannan idan an gama ina da buƙatar a kaita ɗakin duhu na cikin gidana,tayi tsawon wata biyu a ciki, kafin ta bar garin, sannan shi wannan akan kisan daya so aikatawa duk da ba mai hankali bane shima hukuncin kisa ya hau kansa ina da buƙatar a halin yanzu ku zazzaga masa fetur ku ƙonesa, Sannan kai Baban Fattu na janye Auren Fattu da Ja'e don haka kai ne zaka bayar da tarar Shanaye Goma" kan Baffalo a duƙe ya amsa da to kamar ya fashe da kuka a cikin ransa yana jin kamar ya shaƙe Fattu ta mutu, ji yake dama Fattun ce ta mutu ba wai ace ya bada shanayensa ba, kowa na wajen yai na'am da zancen mai gari Fattu kuwa kuka take kamar ranta zai fita tana son kuncewa daga ɗaurin da aka yi mata domin ceton Joddinta ,duk da tsawar da bafaden mai gari ke mata bata dai na kici_kicin kuncewa ba,sharɓeɓiyar dorinar dake hannunsa ya ɗauka yana zuba mata a jiki wacce ta sakata shiɗewa wata azaba na ziyartarta, nan take farar fatar jikinta ta fara fashewa har jini na zuba,bata ida dawowa hayyacinta ba ya ƙara zuba mata wata wacce ta saka Numfashinta tsayawa cak jikinta na ƙara malalar da jini, dukkan wani mai tausayi da imani yaga halin da Fattu take sai ya tausaya mata,ba tare da tausayawa ba yai mata bulala ɗari cif lkc babu alamar rai a tare da ita,jikina duk ya ɓaci da jini kamar an yanka dabba kunceta sukai ana samun zani tare da lulluɓa mata a jikinta don an tabbatar data riga ta mutu JODDi ma da zasu zazzaga masa Fetur liman ya hana sai dai dukan da sukai masa wanda ba zaka taɓa ganesa ba, dan lkcn ko numfashi babu a tare dashi, Umarni mai Gari ya bayar aka fita da gawarwakin su Fattu daga cikin garin ******************************** *MAMMA* Zaune take waje guda tayi zugum duk abin duniya ya isheta tun ranar da Muneebba ta bar gidan hankalinta ya kasa kwanciya,ga miyagun mafarkan da take yi akan Muneebba, Mamma Ladiyo dake kallon Mamma tun da ta lula duniyar tunani tace "Wai Shatu ba zaki cire damuwa a ranki ba? Muneebba fa na cikin kwanciyar hankali dan fa baki ga yadda Uwar mijin ke nan da nan da ita,mu kammu mun ga karamci a gidan nan". wata doguwar Ajiyar zuciya Mamma ta saki tana faɗin "Wallahi Mamma Ladiyo kwanan nan miyagun mafarkai nake akan Muneebba shi ya saka hankalina ƙin kwanciya" Wani kallo Mamma Ladiyo ta bita dashi mai cike da tarin ma'anoni tana furta "Ayya ba abinda zai sameta sai Alkhairi Shatu ki kwantar da hankalinki A'ishah" ɗaga mata kai Mamma tayi ba tare da zuciyarta ta nutsu ba akan zantukan Mamma Ladiyo, Misalin ƙarfe 3 na dare Mamma Ladiyo ta miƙe tana leƙa fuskar Mamma wacce bacci ya ɗauke ta zanin jikinta ta kunce tana ɗauko ƙullin baƙar leda ta kunce tana barɗawa Mamma bisa jikinta tayi minti biyar tsaye a kanta tana wasu surutai kafin ta miƙe ta shiga ɗakin, Akwatin kayanta ta jawo tana buɗawa ta fito da wani madubi wan da yake lulluɓe da jan ƙyalle mai ratsin baƙi,yaye ƙyallen tayi tana buɗesa nan take wani baƙin duhu ya ƙara mamaye ɗakin baka jin motsin komai sai wani gurnani dake tashi zubewa tayi ƙasan madubin tare da kai goshinta ƙasa tana sujjada, tayi tsawon mituna a haka kafin ta ɗago tana duban madubin, wani kalar duhu ne ya mamaye madubin baka ganin komai a cikinsa, buɗe bakinta tayi ta fara wasu surutai masu wuyar ganewa da wata murya mai kama data yara aka fara faɗin "kurwa zanci ki bani kurwa naci ko ki bani na riƙe na dinga lasarta kwaɗayin kurwa nake" ɗago da kanta Ladiyo tayi tana duban madubin tare da bugawa yarinyar dake cikin madubin tsawa tana faɗin "Julaisa kina bani aiki wallahi a gidan wa zan samo maki kurwa a cikin daren nan?" dariyar mugunta Yarinyar ta fashe dashi tana faɗin "kin riga da kin san sharaɗin dana gindaya maki a duk lokacin dana nemi kurwa kika hana ni taki zan kama taki kuma dama irin taki nake kwaɗayi daga gani zata yi maiƙo da mai wai har kin ja kwaɗayina ya tas.....?" bata idasa Mamma Ladiyo ta buga mata tsawa tana faɗin "Julaisa Aniyarki ta biki kika ƙara irin waɗannan baƙaƙen maganganun wallahi sai nayi maki mugun hukunci mai tsauri kin san yanzu dai ke baiwa tace baki da ikon a kaina har sai na karya maki sharaɗi don haka idan kurwa kike nema yanzu yanzu zani baki ita" dariya yarinyar ta sake fashewa da ita tare da ƙwalalowa Mamma Ladiyo manyan idanunta tana fito da harshenta, miƙewa Mamma Ladiyo tayi tana fita daga ɗakin, kai tsaye inda Mamma ke kwance ta nufa,nan take wani abu mai kamar fara ya fara yawo a sama, damƙesa tayi tana murmushi ta shiga ɗakin, madubin ta kalla tare da miƙawa Yarinyar cikinsa farar, amsa Yarinyar tayi tana kallonsa sannan ta yatsina fuska tana kallon Mamma Ladiyo "wannan tayi ƙadas da yawa babu maiƙo daga gani ma ba zata ciyu ba sai dai na dinga lasarta,sannan jinin Mutumin can da nake sha yanzu babu yai nesa da iyalin nashi" "na baki abinda kike so ban san wani dogon tsogwami ki ɓace man da gani" Mamma Ladiyo ta furta dariya yarinyar ta sake fashewa da ita tana faɗin "ban so kika samo man kurwa ba naso ace taki ce na lashe dan kullum haɗiyar yawu nake, ɓacin rana kawai nake jira tazo naga kurwarki a hannuna" Jan ƙyallen Mamma Ladiyo ta saka tana rufe madubin sannan ta ajiyesa cikin kayanta tana fitowa waje ta samu ta kwanta tana sakin wani sheɗanin murmushi tare da kallon Mamma ******************************** Tun da Muneebba taci Abinci ta miƙe ta nufi side ɗin ƴan aiki don a can ne aka mayar da ita, ko da taje waje ta samu tana kwanciya don jin masassarar ta ƙara rufeta ga kanta da bai daina ciwo ba, Indo ce ta shigo taga halin da MUNEEBBA take cikin tausayawa tai mata sannu sannan ta taimaka mata ta miƙe ta rakata wajen Doctor ɗin su tai mata Allura da bata maganin Bayan kwana biyu sosai gidan ya kacame da hidindimu kasancewar bikin Maheer daya matso anata hidima amma babu ango hakan ya sakasu dakatawa da wasu Event waɗanda suka shirya kuka sosai Maheer taci ganin irin halin da take ciki da kuma mijin da zata aura wanda bai ma san tana yi ba zaune take fatar nan tata sai glowing take tayi sumul sai ɗaukar ido take saboda tsabar gyaran da tasha, kayan dake gabanta ta tisa tana kallo zuciyarta cunkushe da damuwa tayi nisa cikin tunani taji an dafa kafaɗarta wanda ya sakata juyowa tana duban Maheer wacce ta kafeta da ido murmushi ta ƙaƙalo tana dubanta "wai Maheer ba dai zaki cire damuwa a ranki ba kullum cikin tunani kike" murmushin takaici ta saki wanda wasu zafafan hawaye na biyo kuncinta "ba zaki gane ba Iftihar" ta faɗa tana miƙewa........ Love Yhu All my Habibties, thanks for your comments, much love and ƙauna lodi_lodi🤩💖💖💖💖 [5/21, 8:17 PM] RIAMCOOL: *BAYAN WUYA* *Book 1* *By Riamcool* *MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION* *BISMILLAHIRRAHMANIRRAHIM* *P.33&34* koda Maheer ta miƙe iya Toilet ta faɗa tayo wanka fitowa tayi jikinta sanye da towel, wajen bakin Bed ta samu tana zama tare da kallon Iftihar wacce ke haɗa mata kayayyakinta tsab cikin Akwati "Iftie ina zaki tafi dasu ne? Maheer ta tambaya Kallonta tayi tana furta "Maheer gidammu zamuje dake kamar baki san yau ne Mother's day ba, ki wuf ki shirya mu tafi dan yau hada Yaya Asad nasan zai zo" Murmushi tayi tana miƙewa tare da shafa Lotion masu daɗin ƙamshi, sannan ta ɗan yi Kwalliya sama_sama, wani dakakken leshi blue mai ratsin pink sabo ta ɗauka ta saka, ba ƙaramin kyawu tayi ba, tsam haɗaɗɗiyar doguwar rigar tai mata, zama tai ta kashe ɗauri mai masifar kyau sannan ta ɗauki Haɗaɗdiyar sarƙar Gold da awarwaro ta saka, mayafin leshin ta ɗauka tana azawa a kai,ga haɗaɗɗun Flowers na ƙunshi da akai mata wanda zai tabbatar maka da cewar Amaryar ce, wani ƙayataccen murmushi ta saki tana ƙara bin jikinta da Mayun tururaku masu masifar ƙamshi "Wow Mrs Asad BObbi wanna kyawu haka kamar zaki tafi gasar kyau" Zulaihat dake shigowa ta furta da ita da sauran ƙawayensu, dariya Maheer tayi tana juya idanu,zuzuta irin kyawun da Maheer tayi suka ci gaba da yi kanta na ƙara fasuwa Sai bayan la'asar sannan dukkansu suka nufi gidan Mommi, cike gidan yake sosai anata hada_hadar biki,Kai tsaye Part ɗin Mommi suka nufa *Muneebba* Sauri _sauri take tafiya har tana neman yin tuntuɓe, bakinta ɗauke da bismillah ta tura ƙofar ɗakin tana shiga hannunta riƙe da tsintsiya alamun shara za tayi, tun daga Falon take ƙare masa kallo tana jijjiga kai, dubanta takai kan wani tangameman Photon Bobbi dake liƙe jikin bangon ɗakin, ƙare masa kallo take tana taɓe baki tare da ƙara godewa Allah da zata zauna ma ba tare daya santa ba duk da kasancewarsa Mijinta amma bata fatan haɗuwarta dashi, tun da shima kansa bata ita yake ba, cikin sauri ta gyara ɗakin kasancewar ba datti dan kullum sai ta gyara kuma da alamu ba'a amfani dashi yadda ta gyara sa haka zata zo ta iskesa shi yasa wani lokacin take kwanciyarta a ciki ganin babu mai amfani dashi, yau tana gamawa ta fice kanta ƙasa take tafiya dan hankalinta sam baya a jikinta, karo ɗin da taci da Mutum ne ya sakata ɗagowa da azama tana dubansa sai dai gabanta ne ya faɗi tana zaro manyan idanunta tare da ja baya ganin wanda ta bangaje, ba tare daya kulata ba ko ya kalleta ya ida haurawa sama yana kakkaɓe jikinsa tare da kakkaɓe inda ta shafesa "Yeah shine Bobbi dai Mijina" ta furta a hankali tana bin sa da ido Daga kafaɗa tayi tana ida safkowa kai tsaye side ɗin da aka bata ta nufa dan tayi wanka, tura ƙofar Falon tayi taji ta a buɗe da mamaki ta shiga sai dai mamakinta ne ya koma ganin Mom zaune ta hakimce tana dubanta a ladabce ta durƙusa tana gaisar da ita, a yatsine ta amsa tana dubanta "ke ga kaya nan kiyi wanka ki saka zan turo miki da mai kwalliya yanzu, anjima za'ai Mother's day ɗin Mijinki da abiyar zamanki shine zan haɗeku koda wasa idan kika rufe fuskarki karki buɗe" Da to ta amsa jiki a mace,tun da Mom ta fita ta samu damar fashewa da kuka ko zuciyarta zata samu salama, sai da tayi mai isarta sannan ta tashi ta shiga wanka fitowa tayi jikinta ɗaure da Towel jikinta ta goge sannan ta shafa Lotion tana zama, bata daɗe ba mai kwalliyar tazo ta tsantsara mata,make up haɗaɗɗen Bride Material red color ta saka, wanda ya fiddo ta tai masifar kyawu haɗaɗɗen ɗauri mai kwalliyar ta kashe mata wanda ya fiddota sosai, sarƙar Gold ɗin ta saka a Awarwron kafin ta yana mayafi a kanta, zaune tai bakin Bed hannunta riƙe da Hand bag tana jiran Aiken Mom Iftihar ce ta shigo babu ko Sallama "ke taso muje" ta faɗa tana yatsina ba tare da tabi ta kanta ba ta miƙe suna fita, tunda ta fito ta rufe fuskarta da mayafi har suka fito farfajiyar gidan inda Mutane ke nan mata da maza ƴam Mata da samari tun da ta doso wajen gabanta yai mummunar faɗuwa ganin wanda ke tsaye a wajen Mutane na ɗaukarsa pictures da murmushi Mom ta tunkarosu tana kama hannu Muneebba ta nufi inda Bobbi ke tsaye shida Maheer ana daukarsu picture, hannu Bobbi ta kama da murmushi ta haɗa dana Muneebba,ba tare daya kalleta ba aka ci gaba da pictures har Ishsha'i ta wuce sannan aka kawo manyan Motocin da zasu nufi wajen Mother's day ɗin motar da tafi ko wace haɗuwa ita Amaren suka shiga, hadda Bobbi Wanda babu wacce ya kula ko ya kalla, kamar Muneebba ta fasa ihu haka take ji haɗaɗɗen Hall Wanda ya amsa sunansa yaji Naira nan suka nufa, maƙil da jama'a wajen yake tun daga tsayuwar Motocin aka fara vedio wanda Bobbi ya fara fitowa sai kuma Muneebba wanda ya sagalo hannunsa da nata haka ma Maheer tafi da sowa wajen ya ɗauka har suka nufo cikin Hall ɗin, kai tsaye wajen da aka tanaza dan su suka nufa suna zama, Anci an sha Anyi bajinta an gwada wa Naira zallar rashin imani, sannan anyi rawa ta bajinta da tsari basu suka tashi ba sai wajen karfe 1 na dare, sannan suka dawo gida, Muneebba da sauri take tafiya dan ta nufi part ɗin ta ganin dare yayi gata da tsoron dare, abu taji ta buge a gabanta har mayafin kanta na zamewa da sauri ta ɗago tana duban Zaidu dake tsaye wanda shima Binta da ido yai gabanshi nan take yai mummunar faɗuwa yana ƙare mata kallo From top to bottom , baki na rawa ta furta "yi haƙuri wallahi ban ganka ba" bai iya magana ba illa lumshe idanuwansa da yai yana ɗaga mata kai, sannan ta wuce da kallo ya bita yana cije leɓensa na ƙasa cikin zafi da raɗaɗi "Me yasa Bobbi yai man zarra a komai ne, yanzu wannan ce matar tasa?kai ina wallahi ba zan bari ya mori yarinyar can ba dole ne nayi mai yiyuwa wallahi ********************************* *Yola* *Fattu* Sosai akai nisa dasu JODDi a garin sannan aka ajiyesu, ko wanensu yashe suke a dokar dajin wanda baka jin motsin komai idan ban da kaɗawar itatuwa da kuma kukan tsuntsaye, Tunda sanyin Asuba ya doso numfashin Fattu ya fara dawowa tana buɗe kumburarrun Idanunta "JODDi!!!! karku kashe man Joddina ku ƙyalesa ku ƙyalesa karku kashe man shi dan Allah na roƙeku" ta furta da ƙarfi jin shiru ba'a amsa ba da kuma jinta kamar a ƙasa kwance ya sakata ƙara ware idanunwanta dishi_dishi ta fara gani kafin ta murza idanunwanta ta ɗan fara gani, ganinta kamar a dokar daji ya sakata miƙewa da ƙyar tana bin ko ina da kallo idanunwanta ne suka sauka kan JODDi wanda yake kwance babu alamar numfashi a tare dashi ƙara ta fasa tana miƙewa ta nufesa don ta manta ma ciwon dake jikinta da kalar Azabar dake ratsata, hannu biyu ta saka tana tallafo fuskarsa fashewa da wani matsanancin kuka mai ban tausayi tayi tana furta "Innnalilahi wa'inna ilaihirraji'un sun kashe man JODDi , dan Allah ka miƙe karka mutu kar ka tafi ka barni bani da kowa, wajenka nake raɓa naji sanyi JODDi bana da wanda ya Fika ka taimakeni ka tashi" ta faɗa wani kuka mai ciwo na ƙara kufce mata ganin shiru ba Alamar zai tashi ya sakata miƙewa tana ratsa wata hanya da gudu tana binta sosai take gudu har Numfashinta na shiɗewa taci uwar tafiya sosai amma babu motsin koda Mutum ɗaya ne a cikin jejin, kasancewar ta san magunguna ya sakata ƙara dosar cikin Jejin tana ƙara duba itatuwan dan ta tabbatar JODDi ba mutuwa yai ba, ganyayaykin data sani ta ɓallo tana biyo hanyar ta dawo kamar ranta zai fice haka take tafiyar kota ciwo jikinta bata bi da jirin dake ɗibarta *Pls Habibties ayi manage da wannan dan Allah love U All my lovely Habibties ina matuƙar ƙaunarku har cikin zuciyata* *Riamcool ce* [5/21, 8:18 PM] RIAMCOOL: *BAYAN WUYA* *Book 1* *By Riamcool* *MIKIYA WRITTER'S ASSOCIATION* *BISMILLAHIRRAHMANIRRAHIM* *P.35&36* A haka harta ƙaraso inda ta barshi kwance, har iyanzu koda ɗan yatsa ne baya motsawa, hawayen da take riƙewa ne suka ƙara samun damar zubowa, a hankali ta saka ɗan yatsanta tana ɗaukesu tare da duƙawa ƙasa ta ɗauko ganyen maganin tana matsa ruwansa, a hankali take buɗa masa bakin tana matsa masa ruwan a haka harta ɗan bashi ya shiga, kingin kuma ta shafe masa jiki dasu babu kamar inda yaji raunuka sun ɗauki tsawon kwanaki cikin jejin kafin ta samu jikin Joddi ya fara dawowa dai_dai Kwance take ta ɗaga kanta sama tana tunanukan dake ƙara karyar mata da zuciya, hawayen da taji ya biyo kuncinta ne ya sakata sanya hannu tana sharewa tsawon kwanakin da suka ɗauka basu ga koda gibcin wani mutum a cikin jejin ba hakan ya sakata yanke shawarar dan tafiya ko sunga mutane, miƙewa tayi tana zuwa wajen JODDi masa magana "JODDi miƙe muje" miƙewar yayi dan a ɗan zamansu yanzu yana fahimtar magana sai dai mayarwa ne baya iya yi, tafiya suke iya ƙarfinsu dan sunyi tafiya mai ɗan nisa kafin su shiga wani ɗan ƙaramin ƙyauye, hamdala Fattu tayi tana sauke wahalallen numfashi kafin ta samu wuri ta ɗan tsaya shima tsayawa yai ƙyam yana ƙarewa wurin kallo hannuwansa mai dai a baya, kallonsa tayi taga kamar wani mai cikakken hankali dan babu wanda zai kallesa yai masa kallon mahaukaci "Zauna" ta furta masa da Yaren fulatanci zama yayi bakinsa na motsi amma ya gaza furta wani abun, murmushi kawai ta saki tana kawar da kanta gefe sun juma anan zaune rasa inda zasu nufa, "Bayin Allah tun ɗazun na ganku anan zaune amma ku baƙi ne?" ɗan Dattijon ya tambaya da murmushi sosai a fuskarsa, itama Fattun Murmushin ta saki da hausarta marar fita tace "Ye mu baƙi ne bamu shan kowa anan ba dan Allah ko zaka iya taimaka mana wallahi bamu da kowa a duniyar nan bawan Allah ka taimakemu idan har kana da hali" ta faɗa wasu hawayen na sake biyo kuncinta da tausayawa mutumin yace "Ayya ku taso muje gidana" babu musu suka bisa har gidansa, iso yai masu suka shiga har cikin gidan ruwa ya fara sakawa a kai musu na wanka dan yaga suna da buƙatar hakan,bayan sun gama aka basu Abinci da ruwa suka sukai nak,kallonsu mutumin yai yace "ko zaku iya bani ɗan takaitaccen labarinku?" "Eh Baba" Fattu ta furta nan take ta faɗa masa labarinsu tun daga farko har ƙarshe batai masa ƙarya ba, da tausaya yake binsu da ido shi kanshi yai matuƙar tausaya musu, "Sannu kunji ko, lallai Ubangiji ya kareku daga ma sharrin shaiɗan da har baku aikata wani abun ba dukda ba isasshen hankali ne dashi ba amma bai kamata kuna yawo babu aure a tsakaninku ba, abinda nake gani a karo na biyu zan sake taimakonku, zan ɗaura muku aure a goben nan in sha Allah" wani dummm gaban Fattu ya faɗi jin kalmomin mutumin taya zata iya rayuwar aure da JODDi? ita fa a matsayin Yaya ɗan uwanta ta ɗauki Joddinta da kuma soyayya ta Addini musulunci ita haka take gani, amma komai Ubangiji ya ƙaddara mata mai kyau bata da ikon jayayya akan lamarin da Ubangiji ya tsara mata, zata amshi ƙaddararta a yadda tazo mata, ita a yanzu dukkan wata rayuwa da zata zo mata hannu biyu zata saka ta karɓeta ta godewa Ubangiji, "Ƴata naji kinyi shiru" ɗago da fuskarta tayi tana faɗin "Baba duk hukuncin daka yanke mai kyau ne yadda ka taimakemu Ubangiji ya baka mafiyinshi mun gode shoshai" "babu damuwa Ƴar Nan Addinina na hidimta mawa taimako shi wani abu ne mai tsananin lada a duk lokacin da kaga ɗan uwanka na buƙatar temako kayi ƙoƙarin tai maka masa da iyakar ƙarfinka kaima Ubangiji zai taimake ka a dukkan wani hali da ka tsinci kanka, rayuwa kake amma gaba kaima baka san inda zata kaika ba" ɗaga kanta tayi tana matsa yatsun hannunta, dukkan maganganun da suke tsab JODDi ya riƙesu yana binsu da ido wani abu na daban na masa yawo a brain ɗinsa tsab kalmomin da Mutumin yai suka buɗe masa wani abu daya rufe masa ƙwalwarsa "waye Ni?" ya furta yana dubansu a mugun razane Fattu ta ɗago idanunta tana kallonsa "Joddi kana magana dama, ka tuno waye kai??" Tai masa tambayoyin a jere da ido ya bita yana faɗin "Ni dai ban san waye ni ba nima haka kawai na ganni" jijjiga kai tayi sannan tai hamdala ga Ubangiji daya buɗewa JODDi bakin yin magana "Masha Allah tun da Ubangiji ya buɗe masa baki yanzu dare yayi kije wajen mai ɗakina ki kwanta zuwa gobe da safe zan isa wajen mai gari na sanar masa da buƙatarmu" Dattijon ya furta da to ta amsa zuciyarta na bugawa dan bata san kalar matar da zata taras a gidan ba wataƙil ma ƙara Innaro da ita, bakinta ɗauke da sallama ta shiga amsa mata ƴar Dattijuwar dake zaune tayi tana furta "shigo ƴar nan kin jiko Malam ya sanar Mani da zuwanki" ta faɗa da Murmushi tana miƙewa Ajiyar zuciya Fattu ta sauke ganin Matar ba irin Innaro bace, a ladabce ta gaisar da ita tana zama, amsa mata matar tayi da fara'ar sosai, kamar ta goyata haka ta dinga nan da nan da ita harta kwanta tana tunanin halayen Mutanen nan biyu dama akwai mutane irin haka? ta tambayi kanta, a ranar dai wani bacci mai masifar daɗi ya ɗauke ta wanda zata iya rantsaewa tun da take bata taɓa yin Bacci mai daɗi irin wannan ba *Washegari* koda suka tashi daga Fattu har JODDi Mutumin ya kaisu wajen mai gari, tsab cikin hikima Dattijon ya ɗan faɗa masa wani abu daya saka su baro gida sannan ya kawo musu buƙatarsa, babu musu mai gari ya Amince sannan ya tara mutanen garin ya faɗa musu buƙatarsu, mai gari ya bayar da sadaki, kallon JODDi Dattijon yayi yana furta "Ya sunanka?" kamar wani mai Imagine haka JODDi ya tafi can kuma sai ya cije baki da ƙyar yana furta "Muhammad" "Sunan Mahaifinsa fa?" Mai gari ya tambaya "Ahmad" JODDi ya furta, babu ɓata lokaci aka ɗaura auren JODDi da Fattu *********************** zaune take bisa Ƴa kujera ta guragu tana kallon fuskar mijin nata da tausayawa wanda take matsa mata ƙafafuwan ta, Allah kaɗai ya san irin ƙunci da baƙin cikin Abinda take ji idan harta ga Mijin nata cikin wannan hali kullum hankalinsa ba a kwance ba ga matsanancin ciwon da yake fama dashi, itama kenan da take kallonsa ina ga A'ishatu wacce yai mata nisa a iya tsawon shekaru to ita wane baƙin ciki ma ne bata ƙunsa ba? hawaye ta share tana jana Majina, ɗago da idonsa Abbie yai yana kallonta "Mansura kukan ne baki daina ba, ita fa ƙaddara babu yadda bata zuwar wa mutum ko wane bawa kika gani da tashi jarbtar sai dai wata tafi wata kiyi haƙuri da rayuwar da kika gammu a ciki, kiyi tunani da Ƴar Uwarki Aysher mana ki hasaso dake ke cikin halin da take ciki ya zakiyi? amma tai haƙuri ta jure taci gaba da rayuwarta ba wai dan bata jin ɗaci da zafi bane a a sai ɗan wadatar zuciya da Ubangiji yai mata,nayi Imani da mahaliccina babu ranar da zata fito ta koma Aysher ba tayi tunanimmu ba ko kuma kewarmu, tabbas akwai ciwo ke kin rasa ƙafa da baƙi ita ta rasa idanuwa, kin san ma kuwa irin tsangwamar da take fuskanta a Al'umma da ita da yaranta ƙazafi babu wanda Aysher bata gani ba, kuma duk ina kallo amma babu halin taimaka mata abin na man zafi da ciwo yadda baki tunani, babu ranar da zata fito ban zubar da hawaye ba,amma a haka Mansura kullum ƙara godewa Ubangiji nake"Abbie ya ƙarashe da murmushi mai ciwo tunda yake zancen hawaye masu raɗaɗi da zafi ke biyo kuncinta tabbas ita tafi tausayin A'ishatu a kanta A'ishatu Ƴar uwa ta ɗauke ta ba a matsayin kishiya ba, tabbas tasan duk ɗaci da raɗaɗin da take ciki A'ishatu ta fita shiga cikinsa shin ita ya take ji? share hawayen tayi tana mai kawar da kanta haka shima Abbie bai ƙara magana ba kasancewar Abinda Ya tsaya masa a maƙoshi ga zuciyarsa dake wani harba masa da sauri_sauri daman ya san za'a rina domin duk lkcn da yai maganar A'ishatu haka ce take faruwa dashi, Anya zai iya wannan rayuwar tabbas zai karya Alqawarin daya ɗauka ya fito da gaskiya fili sannan ya fashe rufaffen ƙwan daya daɗe ba a ƙyanƙyasa sa ba sai dai komi zai faru ya faru koda kuwa hakan yana nufin zai rasa nasa numfashin ne ********************************* Alhamdulillahi anyi biki lafiya an ƙarashe lafiya inda Maheer ta zama matar Bobbi, ba ƙaramin farinciki Maheer ta tsinci kanta ba a lokacin da ta zama mallakin Bobbi sai dai zullumin ta ɗaya ne yadda zata sace zuciyar BOBBI ta tabbatar abu ne mai wahala sace zuciyar mutum kamar Bobbi ba ƙaramin kuka da dana sanin son maso wani Maheer tai ba a lokacin data kwana ɗaya bata ga Bobbi yazo gunta ba da niyyar raya wannan dare, ko wace Amarya na farinciki A daren farkon data kwana ɗakin mijinta amma ita sai tarin baƙin ciki da takaici ta ƙunsa tabbas ta shiryawa wannan rana domin fayyacewa Bobbi soyayyar da tayi mata mugun kamu tayi niyyar fayyace masa dukkan wani sirri na zuciyarta a daren farkon ta amma sai dai kash bata samu wanna ikon da damar ba kwance dake jikinta lulluɓe da blancked idanunwanta sunyi luhu_luhu saboda kukan data sha Nocking ɗin da taji anyi ne ya sakata miƙewa da ƙyar tana gyara gashinta "come in" ta furta a hankali, kanta a sunkuye ta ɗago tana duban Maheer tace "Am Hajiya tace ki sabko kici Abinci" fuskarta da ɗan murmushi tace "ok you can go" harta tafi kuma sai taji Yarinyar ta birgeta cikin ɗan ɗaga murya tace "Nace ba" ɗan juyowa tayi tana haɗiye abinda ya tsaya mata a maƙoshi tace "na'am" tana kallon Maheer wacce ke murmushi "Ya sunanki?" Maheer ta tambaya tana kallonta "Muneebba" ta furta ba tare data kalleta ba "wow nice Name you can to be my friend?" "Yes Mah" ta furta tana ƴar dariya, itama dariyar tayi "ok you can go pretty" ok ta furta tana fita tana mamakin halayen Maheer a farko ta saka zata yi girman kai da wulaƙanci amma sai taga saɓanin hakan, a yau da ta samu wacce ta ɗan sake mata fuska sai taji ta wata ta daban,duk damuwar da take ciki sai taji ta ɗan rage, amma sai dai idan tasan da cewar ita ɗin ko wacece ta tabbatar sai ta sauya mata ta musguna mata may be tama fi su Mom ƙuntata mata Dan ganin Mijinta take aure da wannan tunanin harta safka ƙasa ba tare dama tasan ta safka ba "ke!!!" taji daka tsawar Mom A hanzarce ta ɗago tana dubanta "na'am Mah" ta furta bakinta na kyarma, a wulaƙance Mom ta bita da kallo "gidan Uban wa zaki tafi? baki isar man da saƙon dana aikeki dashi ba" baki na rawa ta furta "Sorry Mah, tace gata nan sabkowa" taɓe baki tayi tana furta "da tsiya sai kinyi turanci kina ƴar matsiyata faƙiriya, maza zo yi Saving namu" dariya su Aunty Meera suka fashe da ita, sosai Muneebba taji ta muzanta da kalar cin mutuncin da sukai mata ga Mazan dake zaune waɗan da suke Binta da kallo hakan ya saka taji ta ƙara muzanta jiki ba ƙwari ta iso wajensu kamar ta fasa ihu, kallonsu ABEED yai yana ɓata rai "haba Mom miye laifinta za kuyi mata wannan cin mutuncin, shin shi talaka dan ya zama Silifas abin takawa? zakuna dinga mata cin mutuncin laifi ne dan tazo nema a karkashinku zaku wulaƙantata kunsan gaba yadda Ubangiji zaiyi daku ne, shin kun san kalar baiwa da ni'imar da Ubangiji zai mata nan gaba ne?" harara Mom ta zabga masa tana furta "to sannu Malam, wace baiwa Ubangiji yaiwa talaka idan banda baiwar faƙiranci kaga riƙe wa'azinka" shiru kawai yai yana danna wayarsa dan yasan ba zasu gane ba "Mom a kira Indo tai man Peppersoup" Zameer dake ida safkowa daga Step ɗin benen ya furta, hakan ya saka Muneebba ɗagowa tana dubansa "wow bala'in can Mom Ina kuka samu House maid balarabiya?" Zameer ya furta yana kafeta da ido, kawar da kanta ƙasa tayi taci gaba da yin Saving nasu, wata uwar harara Mom ta zabga masa "to na Mamajo sarki mata kai dai mace indai fara ce koda Mayya ce tana burgeka, ina ruwanka dama ko wace kala ce inda ƴar aiki ce" "To ita ƴar aikin ba mace bace?" ARYAN ya furta , Zameer ne yace "a to gane Mani hanya, ke Ƴar nan ban son naga farar mace balarabiya kamarki tana wahala ajiye na ida Saving nasu ni dai indai akan farar mace ne na zama bawa daga yanzu" "Alqur'an ban ga laifinka ba, dama baƙaƙen Ƴan aiki sunyi wa gidan nan yawa babu ƴan Farare" Afif ya furta yana dariya, dariya dukkansu saka saki harda shewa kamar wasu mata, Mom kuwa bata ƙara cewa ƙala ba, Maheer ce ta safko fuskarta wasai babu wanda zai kalleta yace ta sha kuka, a ladabce ta gaida Mom sannan taja kujera tana zama,dasu Aunty Meera suka gaisa a mutunce sannan su Zameer, Muneebba dake tsaye ta jawo Warmer tai saving ɗin Maheer "tnx pretty" Maheer ta furta da murmushi itama murmushin tayi tana ja baya ta tsaya, Tunda Zaidu ke sabkowa yake kallon Muneebba da kuma Mamakin abinda ya sakata sanya kayan House maid ya dai tabbatar wannan ɗin ita ce Matar Bobbi ba wata ba, Murmushin gefen baki ya saki yana kallon Muneebba, babu wan da yaiwa Magana,ya kalli Mom yana furta "Mom ki aika wannan House maid ɗin takai man Abinci a ɗakina" ya furta fuskarsa ɗaure tamau tsam Zameer ya miƙe yana jawo Warmer ɗin Abincin yace "Yah Zaidu bari na kai maka Alharam abinda za'a aikata kasan muna kare martabar Musulunci babu yadda za'ayi zuƙeƙiyar budurwa fara tas jinin larabawa taje kai maka Abinci a Bedroom".................. *Riamcool ce* [5/21, 8:18 PM] RIAMCOOL: *BAYAN WUYA* *Book 1* *By: RIAMCOOL* *MIKIYA WRITTER'S ASSOCIATION* *BISMILLAHIRRAHMANIRRAHIM* *P.37&38* Da wani kalar kallo Zaidu yabi Zameer yana tauna leɓe,basarwa yai yana ɗaga kafaɗa "ok kai man a ɗaki" Wata wahalalliyar Ajiyar zuciya Muneebba ta saki tana hamdala ga Ubangiji, "Mah an gama zan iya tafiya" ta tambaya bakinta na kyarma, wani banzan kallo Mom ta watsa mata tana faɗin "daman na riƙe maki ƙafafu ne na hanaki tafiya?" jiki a sanyaye ta fita tana matso hawayen da suka tarar mata a fuska, da wani kalar sheɗanin kallo Zaidu ya bita yana sakin murmushin gefen baki Koda ta fita kai tsaye Part ɗin da zai sada ta da ɗakin Bobbi ta nufa key ta zaro tana buɗe ɗakin, a hankali ta furzar da iskar bakinta tana sauke ajiyar zuciya kamar wacce tai gudun tseral, bisa ɗaya daga kujerun Falon ta samu tana zama tare da dafe kanta dake mata Azababben ciwo,ɗan kwanciya ta samu tayi ko taji sawaba nan take bacci mai masifar nauyi ya ɗauke ta ba ita ta samu ta farka ba sai wajen 1:30pm sannan ta fara buɗe lumsassun idanunta,a hankali ta ida ware su tana miƙa tare da furta Addu'a, wata irin zabura tayi tana miƙewa jikinta na kyarma ganin wanda ke cikin Falon yana dannan Laptop ɗin sa hankali kwance, "ina....wuni" ta furta a rarrabe cikin tsoro, ba tare da Bobbi ya ɗago ba ya furta "miye ya shigo dake ɗakina?" "gyara zanyi" ta furta tana matsa yatsun hannunta wanda wannan ya zame mata Al'ada cikin kallon tarin tsanar mace ya ɗago da fuskar sa yana dubanta fuska a haɗe tamau babu alamar sassauci ko rahama ya furta "daga yau bana buƙatar sake ganinki a koda sashen nan, kar ki ƙara shigo man ɗaki da niyyar gyara idan ba haka ba ranki zaiyi mummunan ɓaci" murya a can ƙasa ta furta "ok sir" tana jifanshi da kallon tsana wanda lokaci guda wata kalar muguwar tsanar Bobbi ta dirar mata a zuciya, cikin daka tsawa ya furta "miye na tsaya man a kai kina kallona maza fice man a Falo" ya faɗa kamar yai mata dan banzan duka A hanzarce ta fice ta fita daga side ɗin ma baki ɗaya, waje ta samu tana fashewa da kuka, ita shi kenan duniyar nan kowa ya tsaneta kowa ta raɓa sai ya nuna mata tsana, duniyar nan wane laifi ta aikatawa Mutane da har suke nuna mata tsana har haka? kuka taci sosai dan sai da taji kanta na neman tsagewa sannan tai shiru tana nufar famfan dake gefe ta wanke fuskarta, *Maheer* tun shigowar Bobbi Maheer ta gani hakan ya sakata shiga bathroom ta wanka sannan tazo ta cancanɗa uwar kwalliya kamar zata tafi gasar kyau, ƙara kallon kanta take jikinta sanye da rigar dakakkiyar Shadda Arsh color ɗinkin Straight gown wacce taji aiki da Ado sai walwali take gashi ba ƙaramin fito da ainahin hasken fatarta tayi ba da kuma surarta, wuyanta sanye da sarƙar Gold wacce keta walwali da sheƙi, jikinta tabi da manyan turaruka ta feshe shi, Agogon Diamond ta ɗauka tana ɗaurawa a haɗaɗɗen tsintsiyar hannunta, ba ƙaramin kyau tayi ba dan babu namijin da zai ganta bai ji wani abu a kanta ba, ƙayataccen murmushi ta saki, tana ficewa daga ɗakin nata, kai tsaye Part ɗin sa ta nufa gabanta na tsananta faɗuwa koda tazo kan ƙofar shiga ja tayi ta tsaya tana furta sunan Allah shahada tayi tai Nocking,ta ɗan jima tana yi kafin taji an furta "come in" A hankali ta tura ƙofar Falon kanta a sunkuye tana tafiya cikin nutsuwa da kuma birgewa, cikin ɗaya daga cikin kujerun Falon ta samu ta zauna tana kallon Bobbi kamar ta cinyesa, sun ɗauki tsawon lokaci babu wanda ya cewa wani ci kanka, ɗan ɗagowa yayi yana furta "mi ke tafe dake?" hawayen da take riƙewa ne suka samu damar zubo mata a kunci zuciyarta na mata zafi da ƙuna "Au haka ma zaka ce Yah BObbi? shin laifi ne dan kaso wanda zuciyarka ta Aminta dashi, dacewa ne Abin da ka aikata ace A daren farkommu baka ziyarceni ba,ina ga ko auren ƙiyayya mukai da kai bai kamata kai man haka ba akwai ciwo abinda ka aikata man" ta furta wani sabon kukan na sake kubce mata tun da take kukan Bobbi ke jifanta da wani kalar mugun kallo mai rikita wanda ake mawa, "yaushe mace ta samu damar da zata furta masa haka, yaushe mace ta samu zarran kallon ƙwayar idonsa harta furta masa haka, mace ita ce wacce yafi tsana a rayuwarsa, Abinda ya ɗauki Mace maƙaryaciya maci Amana muguwa kuma Azzaluma, makira, mace ce mafarin tarwatsa masa dukkan wani farin ciki, shi yasa bama zai taɓa bawa mace damar da zata furta masa koda kalma ɗaya bace" ya furta a zuciyarsa yana sake bin Maheer da kallon tsana tun da yake bin ta da kallon jikinta yai sanyi wani kalar tsoronsa da shakkarsa ta shigeta,ba tare daya tanka Mata ba ya miƙe yana tattara Laptop ɗinsa ya shige bedroom,da kallo ta bisa tana miƙewa itama fuskarta tayi jawur ɗan sai ta nutsuwarta tayi tana fita,kai tsaye wajen Mom ta nufa tana shiga Falon ta faɗa cinyar Mom tana fashewa da wani kalar sabon kukan, "Maheer mi ya faru" Mom ta tambaya hankalinta a tashe "Mom wallahi ba zan iya jurewa ba,Yah BObbi har yanzu bai damu dani ba,yanzu haka da naje wulaƙanci yai man" Maheer ta faɗa kamar zuciyarta zata faɗo ƙasa dan takaici da baƙin ciki "duk magana da nasihar da nayi Wa Bobbi bai ji ba, kiyi haƙuri Ƴata kiyi shiru Ni da kaina zan jawo hankalin Mijinki" Mom ta faɗa shiru tayi tana share hawaye "Amma Mom ai nasan ita waccan ba haka yake mata ba nice kawai baya ƙauna" kallonta Mom tayi tana furta "haba ita ɗin banza ita da ƴan aikin gidan nan ma sun fita gata da ƴanci kisha kuruminki ke ɗaya tal a wajen Bobbi babu kamarki Ni da kaina zan jawo maki hankalin mijinki sannan ita waccan na mayar da ita kwandon shara a gidan can dan har Abada bazan taɓa barin Bobbi saninta ba, Dan na mayar da ita cikin Ƴan Aiki ba zaki taɓa gane cewar Matar Bobbi bace" girgiza kanta Maheer tayi "Amma Mom kina ganin kin kyauta abinda kuka aikata itama fa Ƴa ce kamar ni" kallonta Mom tayi tana faɗin "Maheer ba zaki gane ba, nasan kin ga wacce na aika maki a ɗazun kizo kici Abinci, kinga kalarta kinga surarta wane Namiji ne zai ga wannan bai sota ba? bana son BObbi ya ganta ne ballantana harya faɗa tarkon sonta,gashi kin san ɗiyan talakawa da iya Asirce _Asirce" gaban Maheer ne ya faɗi jin cewar Muneebba ce Matar Bobbi, "Duk da haka Mom baki kyauta ba dan Allah ki cire ta a jerin ƴan aiki ni wallahi tun a ganina da ita na farko naji ta kwanta min a rai sannan zubinta da yanayinta ya bani tausai" kamar Mom ta rufe Maheer da duka haka take ji dan takaici "wallahi Maheer baki da hankali har yanzu baki hankali ba aka gaya miki ita kishiya abar tausayi ce to wallahi janza hali tun wuri" girgiza kai kawai Maheer tayi ta san da cewar tabbas Mom sunyi nisa ba zasu gane ba, hakan ya sakata miƙewa ta haura Up stairs, da kallo Mom ta bita kawai A haka rayuwar taci gaba da tafiya ba wani sauyi sannan a hankali Maheer ta din ga jawo Muneebba a jikinta, haka ɓangaren Zaidu kullum da baƙin ƙudiri akan Muneebba ya shiryawa Muneebba tarko kala_kala amma Allah na tseratad da ita, Tsaye take ɗakin Zaidu hankalinta duk ba'a kwance, ba dan babu yadda ta iya tun da Mom ce ta sakata gyaran ɗakin Zaidu, a hanzarce ta fara gudun karya zo ya sameta, tana kammalawa ta fito daga bedroom ɗin sai dai turus tai ta tsaya gabanta na tsananta faɗuwa ganin yadda Zaidu ya rufe ƙofar Falon key ɗin a hannunsa yana wasa dashi, wani yawu ta haɗiye tana tunkaro ƙofar da nufin buɗewa, hannu ta saka ta buɗe amma taji ƙofar ƙyam da ita a rufe, juyowa tayi tana faɗin "dan Allah ka taimaka ka buɗe" Murmushin gefen baki ya saki yana dubanta sama da kasa kafin ya taso yazo daf da ita har numfashnsu na haɗuwa ,Hijab ɗin dake jikinta ya cire "wow" ya furta lokacin da idanuwansa sukai arangama da manyan Boobs ɗin ta wanda suke cike tab a riga, ƙanƙame jikinta tayi tana rufewa, hawaye na biyo kuncinta,tana girgiza masa kai bakinta na rawa saboda tashin hankali " Kada ka keta man haddi ka dubi girman Allah ka ƙyaleni" shafa gefen bakinsa yai yana cire ƴar singlet din dake jikinsa ya rage daga shi sai Boxer, rufe idonta tayi tana kiran sunan Allah,jawota jikinsa yai yana ƙara ƙare mata, kallo yadda ko ina na jikinta ke cike ,wani yawu ya haɗiye yana kai hannunsa kan Manyan mazaunanta ya fara shafawa yana lumshe idanu,so take ta kufce amma ta kasa saboda riƙon da yai mata ba na wasa bane,"kaji tsoron Allah ka daina taɓa jikin da ba naka ba, ka dubi girman Allah ka ƙyaleni, kada ka keta man haddi, kada kaci mutuncina ta haramtacciyar hanyar nan," "tabbas yau zanci mutuncinki sannan naci mutuncin Auren dake kanki, tun da shi mijin naki yaki yai abinda ya dace bari Ni nayi" ya faɗa yana kai hannunsa kan Boobs ɗin ta, wani ƙarfi taji yazo mata ta turesa tana ja da baya jikinta na kyarma tare da kare jikinta tunkarota ya sake yi a karo na biyu yana neman zare Boxer ɗin dake jikinsa, idanunta ta sake rufewa kam tana jiran tsammani sai dai shirun da taji ne ya sakata buɗe idanunta tana kallon inda yake waya kara a kunnensa,"ok" ya furta yana sauke wayar a kunnensa tare da jan dogon tsaki, kallonta yayi yana furta "kin tsallake target ɗina da yawa amma ki sani next target ɗina ba zaki taɓa tsallakesa ba" Yana gama faɗar hakan ya wuce bedroom, wani kalar Ajiyar zuciya ta saki tana ɗaukar Hijab ɗin ta ta zira sannan ta ɗauki key ɗin daya ajiye ta bude kofar tana fita da sauri, Tun daga lokacin dukkan wani dukkan wata hanya da zata haɗata da Zaidu take a kauce mata Maheer tsaye take tana fito da wasu ƙwayoyin magunguna waɗan da na tada Sha'awa ne sosai hakan ya sakata tanadar su dan yau so take shirinta yayi akan Bobbi, Dan ta Gaji da zaman haƙurin da take koda yaushe matsananciyar Sha'awa na damunta, kai tsaye ɗakin Bobbi ta nufa key ɗin data ɗauka tun tuni ta saka tana buɗewa a hankali, murmushi ta saki tana nufar Freezer ta buɗe ajiyar zuciya ta saki gani lemo ɗaya ne ya rage A Freezer ,ɗaukar lemon tayi tana zuba ƙwayar maganin ciki ta jijjiga shi sannan ta mayar tana ajiyewa , tare da fatan Allah ya sa haƙarta ta cimma ruwa, dan ta tabbatar zai sha kuma yanzu lokacin dawowarsa ne daya zo shi zai fara sha, tun da komai sai da ta tsaya ta fara karantarsa kafin ta aiwatar, da sauri ta bar Falon tana rufewa ta nufi nata Part din, koda ta shiga wanka ta shiga *Bobbi* Tsit ɗakin yake sunyi shiru yayin da Bobbi ya gama magana,jiki a sanyaye ɗaya daga cikin mutane huɗun dake zaune ya kalli Bobbi yana furta "Amma Sir rayukan mu tabbatas suna cikin haɗari, wanda na tabbatar suka gane muna cikin ƙungiyar su da wata manufa to tabbas dukkammu sai munyi ta rayuwarmu, sannan ina ganin da haɗari basu damar da kayi akan su samu nasarar Sace Mailbox ɗin da keda sirrikan Company ka," Murmushi mai tarin Ma'anoni Bobbi ya saki yana furta "Yes na basu dama ne domin ina son mu fara buga wasan game ɗin dasu ne tun a yanzu, kamar yacce a baya suka dinga buga wasan Game damu har suka ɗauki rayuwar ɗan Uwansa, ta wannan hanyar ce kaɗai zan iya masu tarkon da zan kama su, sannan hanyoyin dana faɗa muku tasu kaɗai nake son kubi, kada wanda ya kuskura yai kuskure Akan abin da na faɗa muku kubi komai a tsari,kamar yadda suke da tsare_tsare muma haka muke da, namu tsarin,fatan kun fahimta? Sannan ku fara shiri tun a yanzu" "Ok sir " suka furta dukkansu sannan suna ƙara jinjina girman Aikin da za suyi wanda yake dab da rasa rayukansu, wala su suyi nasara wala kuma ai nasara a kansu, zuciyar kowa da abinda yake saƙawa har suka gama zaman Meeting ɗin shi kanshi Bobbi yana ƙara jinjina girman aikin dake tunkarosa, wan da tabbas ya san idan yayi sake bashi ba harna kusa dashi sai an cutar,dafe kanshi yayi ƙwalwarsa na sake tariyo masa abubuwan da suka wuce a baya,a duk lokacin daya shiga tunanuka irin wannan yana son ya keɓe shi kaɗai, amma yau yaji yana da buƙatar tunkarar gidan nasu,kai tsaye can yace a nufa dashi,koda yaje ta Falon Mom ya bi ya wuce iya gaisar da ita kawai yai ya haura Up stairs ɗin, da kallo ta bisa kafin ta miƙe ta shiga kichen da kanta ta haɗo masa Abinci sannan ta fito tana neman wanda zai kai masa, kamar daga sama sai ga Muneebba ta shigo domin shiga kichen tayi musu sabon girki, kanta a ƙasa ta gaisar da ita wani mugun kallo ta watsa mata tana taɓe baki kafin tace "ke zo ɗauki Abincin nan ki kaiwa Bobbi sannan idan zaki shiga ki rufe fuskarki karki bari yaga fuskarki" da to ta amsa zuciyarta na bugawa dan ko kaɗan bata buƙatar shiga ɗakin Bobbi Tun lokacin da Bobbi ya shiga Kai tsaye Freezer ɗin Falon ya nufa yana buɗewa ruwa ya fara ɗauka ya sha, sannan ya ɗauki lemo ɗaya daya rage cikin ɗaya daga cikin kujerun Falon ya samu yana zama,buɗewa yai yana ɗaga kai yana sha,lumshe idanuwansa yayi yana jin wani abu na daban na ziyartarsa, miƙewa yai da nufin tashi ya shiga bedroom ɗin amma sai dai cak yaja ya tsaya sakamakon abinda yaji, nan take jikinsa ya fara rawa wata zufa na fara yanko masa, Zama yai yana sauke wahalallen numfashi, a dai_dai Lokacin ne kuma Muneebba ta fara Nocking jin shiru ya sakata tura ɗakin fuskarta lulluɓe da niƙabin da Mom ta sakata sanya wa, ta gefen ido Bobbi yaga tsayuwar mace nan take wata muguwar sha'awa ta dirar masa, hankalinsa ya fara gushewa, "fi.......ki rufe man ɗakin " ya faɗa a rarrabe ba zaka gane ma abinda yake faɗa ba bata ji abinda yace ba illa kawai ta rufe ɗakin, zuciyarta na dukan uku_ukku ta rufe ɗakin tana dawowa gabansa ta tsaya tare da zazzare idanu alamun tsoro sun bayyana a gareta, Bobbi kuwa ganin mace a gabansa ya saka hankalinsa gushewa babu abinda yake gani da so sai son kasancewa da ita hakan ya sakasa tashi kamar wani tsohon zaki yana jawo Muneebba wata uwar ƙara ta saki bai bari ta ida ƙara sawa ba, ya cire niƙabin dake kanta yana haɗe bakinsu waje guda a zafafe, wani kalar tsosa ta fitar hayyaci yake yiwa bakin nata wanda kai kasan ba a cikin hayyacinsa ya ke yinsa ba, ihun neman ceto Muneebba ke son yi amma babu hali ko damar yinsa, cire bakinsa yayi yana cire mata Hijab ɗin Tata da riga wanda ba ƙaramar kokowa suka sha ba harya samu galabar cire mata kayan jikinta, kuka take da ihu amma babu mai jinta, saboda muryanta daya dishe............ *Tabɗi jam,Koya zata kaya tsakanin Bobbi da kuma Muneebba? Mu haɗu a next Page, Habibties, ina matuƙar godiya ga ƙoƙarin comments ɗinku, much love All* *Riamcool ce* [5/21, 8:18 PM] RIAMCOOL: *BAYAN WUYA* *Book 1* *By: RIAMCOOL* *MIKIYA WRITTER'S ASSOCIATION* *BISMILLAHIRRAHMANIRRAHIM* *P.39&40* Kamar wani tsohon mahaukacin Zaki haka yake sarrafata, da ƙyar ya samu ya cire kayan jikinsa, duk yadda taso ƙwatar kanta ta kasa har sai da ya cimma burinsa a kanta wani kalar Azababbiyar ƙara ta saki lokacin da ya ratsata ya wuce, tun tana kuka harta sadaƙas da tabbas mutuwa za tayi, ya daɗe a kanta yana aiki kafin ya saki ƙara tare da ƙanƙameta kamar zai ida tsagata gida biyu, lamo yai a jikinta yana sauke ajiyar zuciya, da ƙyar ya sauka daga jikinta yana samun gefe ya kwanta nan take wani wahalallen bacci ya ɗauke sa, kuka Muneebba keyi sosai tana ƙara jin tsanar Bobbi a ranta, ji take duk duniya bayan Mahaifinta babu wanda ta tsana sama dashi, Anya shi cikakken mai imani ne? ta tabbatar dashi ɗin mugun mutum ne marar tsoron Allah mai aikata saɓo da ɗaukar zunubi a wajen Ubangiji, shin Ƴam mata nawa ya aikata ma haka, nawa ya zalunta tare da sakasu kuka? ba tare da yasan ita ɗin matar sa bace ya kusanceta, da ace ba Matar sa bace da yau ya zubar mata da mutuncin data daɗe tana riƙewa, ta faɗa a zuciyarta wasu zafafan hawaye na bin kuncinta Sosai jikinta yai tsami hakan ya sakata ƙoƙartawa tana miƙewa tare zaune da ƙwalla uwar ƙara jin azabar data ziyarceta, cije leɓe tayi tana ida miƙewa kamar ta fasa ihu haka take ji, cikin dakiya da dauriya ta shiga bedroom nashi dan ta gasa jikinta, koda ta shiga Toilet ruwa masu zafi ta haɗa a Sit bath ɗin zama tai ta fara gasa kanta dauriya kawai take, tayi gashi tayi ya kai sau ukku kafin ta samu taji ta ɗan fara dawowa, dai_dai, wankan tsarki tayi tare da ɗora Arwalla kasancewar Ishsha'i ta wuce fitowa tayi a hankali kamar wata mai koyon tafiya, rigarta ta mayar da Hijab ɗin sai niƙab, har lokacin hawaye basu daina zuba ba a fuskarta, key ɗin ta ɗauka tana fita daga Falon,jawo kofar tayi tana saka key ɗin ta kulle, a tsorace tabar side ɗin tana fita ta ƙofar da tasan baza a ganta ba, taci Sa'a harta shiga side ɗin ta bata ga kowa ba,A Falon ta zube tana mayar da numfashi, Sallar da ƙyar ta idar da ita tana kwanciya wani Zazzafan zazzaɓi na rufeta, da ƙyar ta samu baccin wahala ya ɗauke ta Maheer ce tsaye tana kai da komowa ji take kamar ta fasa ihu dan tun bayan dawowar Bobbi ta nufi part ɗin shi sai dai tayi bugun duniya bai buɗe ba, haka zalika ta saka key ɗin bai buɗe ba, Alamun akwai key a jikin ƙofar hakan ya sakata dawowa kamar ta fasa ihu, tana fatan Allah ya hana Bobbi Shan lemon, bakin bed ta samu tana zama, ta daɗe a zaune kafin ta samu ta kwanta, bacci ɓarawo ne ta samu ya ɗauke ta A hankali Bobbi ke ware lumsassun idanuwansa yana furta sunayen Allah, ga kansa dake mugun sara masa ida tashi yai zaune yana duban jikinsa da mamaki da kuma tashin hankali ganinsa tik babu kaya ga jini duk ya ɓata wajen daya ke zaune "Innnalilahi wa'inna ilaihirraji'un" ya furta da matsanancin tashin hankali, Abin da ya aikata ne ya fara dawo masa a brain wan da a lokacin da yake aikatawa sam hankalinsa bai jikinsa gani yake tamkar a mafarki, dafe kansa yai yana nanata sunaye Allah tare da dafe kanshi dake barazanar tarwatse masa, shine yau da aikata Zina,wace mace ce ya aikatawa haka, da wane ido yarinyar daya aikatawa hakan zata kallesa da wane bakin zai iya bata haƙuri, mai ya saka mata suke shiga rayuwarsa su tarwatsa masa farinciki a koda yaushe, waye ya aikata masa wannan ɗanyen aiki??????????????? Dan ya san tabbas lemon daya sha ne ya saka sa a babban haɗari, shin wai ma mi ya kawo yarinyar a ɗakinsa? tabbas da wata manufar aka aikata masa hakan, waɗannan tunanukan su suka addabi zuciyarsa, da ƙyar ya miƙe ya faɗa Toilet yai wanka, salla ya fara yi kafin ya fara karatun Alqur'ani ko zai ji sauƙin abinda ke zuciyarsa, ya ɗanjj sauƙi hakan ya sakasa miƙewa ya fito Falon da kanshi ya gyara Falon duk inda jinin yake y gyarasa tas A Daren ranar ko rintsawa bai samu yayi ba, Washe gari ya daɗe kafin ya fito, kai tsaye Part ɗin Mom ya fara shiga, bai sameta a Falo ba hakan ya sakasa tunkarar bedroom ɗin ta, zaune take tana damna waya, ciki ciki yai sallama, gaisar da ita yai tana amsawa a hankali tare da dubansa, cikin fara'a "Mom tambayarki zanyi" hankalinta ta tattara ta mayar dashi kan Bobbi "Ina saurarenka son" "Shin kin aika man wata a jiya ne ta kai man abinci" "Eh" Mom ta furta, da ɗan gabanta na faɗuwa, "shin wacece ita wacce kika aika man?" "Son na mance wacce na aika maka a jiya, dan ba tantancesu nake ba kasan yawan ƴan aikin gidan nan ba a ganesu" "Ko wacce ke man gyaran ɗaki ce kika aika man?" da sauri Mom ta girgiza kanta "ba ita bace ita wannan ma ai ta tafi garinsu dubo gida ina tunanin gobe ko jibi ma zata dawo,amma mi ya sa kake man waɗannan tambayoyin?" "Saboda ina son na gargaɗeta ne ta daina shigar man a Falo koda an aiketa" ya furta yana miƙewa tare da ya mutsa fuska kamar da gaske, Ajiyar zuciya Mommi ta saki jin ba abinda zuciyarta ke zato bane, amma taya harya gane tana masa gyaran ɗaki? tana tsoron kada Bobbi ya dinga ganin Muneebba harya faɗa sonta, hakan kuwa ma ba zata taɓa faruwa ba dole ne tama ko wace hanya ta hana Muneebba sake haɗuwa da Bobbi, Koda ya fita kasa sukuni yai, dan yau ko Office bai je ba, Muneebba kuwa tun da ta tashi take jin jikinta na mata tsami ga hakan ya sakata ƙara gasa jikinta, da ƙyar ta samu kingin Maganin zazzaɓi tasha, tana kwanciya dan har rana ta fito bata fita ba, kwance take taji an ɗaka mata duka wanda ya sakata saurin miƙewa tana kallon AUNTY Samhat wacce ke Binta da matsiyacin kallo "ke Uban mi ya hanaki fitowa yau?" Samhat ta faɗa murya a cunkushe ta furta "ban lafiya" taɓe baki Aunty Samhat tayi tana furta "babu ruwana da ciwo ki fito ki gyara man ɗaki na sannan kiyi man haɗaɗɗun delicious, zanyi baƙi yau" "Wallahi bazan iya ba"ta furta da muryan tausayi, ji kake tasss ta wanketa da Mari tana furta "harni zaki faɗa wa baki da lafiya wallahi tashi muje sai kinyi abinda na sakaki Shegiya ƴar matsiyata" Hawaye na bin fuskarta haka ta miƙe tabi Samhat jiri na ɗibanta, dukkan Abinda ta sakata sai da tayi, fitowa tayi tana layi kamar zata faɗi da sauri Maheer ta riƙe ta tana furta "lafiya Muneebba?" "Aunty ban lafiya ki taimakeni" ta faɗa tana hawaye, da sauri Maheer ta taɓa jikinta tana faɗin "subhanallahi Muneebba ba lafiya kuma kike aiki kuma baki sha magani ba, wai me kike son mayar da kanki ne kin san nasan komai ke ɗin matar Yah BObbi ce, shin aure kika zo ko bauta, wallahi Muneebba idan baki tashi ba sai kun zama shara abar watsawa, ki ƙwaci ƴancin ki da kanki mana" tunda take maganar Muneebba ta shiga shock jin cewar tasan ita ɗin matar Bobbi ce, "da gaske kin san ni Matar Bobbi ce?" kallonta Maheer tayi "eh Muneebba nasan ke ɗin matar Bobbi ce kada kiji komai a ranki ki ɗaukeni tamkar yayarki nima haka na ɗauke ki a matsayin ƙanwata,ba kishiya na ɗauke ki ba abokiyar zama na ɗauke ki" ta faɗa da Murmushi ajiyar zuciya Muneebba ta saki tana yaba kyakkyawar zuciya irin ta Maheer, "na gode Sosai Aunty" ta furta, Maheer da kanta ta bata magani sannan ta tisata taci Abinci a yinin ranar wajenta ta yini tana kula da ita, Kwanaki na tafiya makwanni na shuɗewa, kullum a wajen Bobbi bashi da kwanciyar hankalin abinda ya aikata, yayi bincike bai ganota,ba ga babban tashin hankalin da yake ciki shine fara aikin dake gabansa yaƙara abokan hamayyarsa, a wajen Muneebba kuwa ta warke tuni sai dai har yanzu ciwo da ɗacin da take ji bai bar zuciyarta ba,ga wani kalar bacci da cin Abinci da take yawan yi ta rasa gane ko minene a tunaninta cutar bacci ce ta kamata, sosai ta sake cikowa ko ina nata ɓul ɓul, Tsaye take a kichen ita da Indo suna faman girki, hannunta toshe da hancinta saboda ƙamshin manjan da take ji, cikinta taji ya hautsina hakan ya sakata fita da gudu tana zagayawa ta baya nan ta fara sheƙa Amai kamar Ƴan cikinta zasu fito saboda Amai, wani wahalallen numfashi ta sauke lokacin data gama, kichen ɗin ta koma da niyyar ci gaba da aikin kallonta Indo tayi tana furta "sannu ashe baki láfiya? kin ga ki barni na ƙarasa jeki kisha magani ki kwanta" ɗaga mata kai kawai tayi tana fita daga kichen ɗin domin ji take tabbas ta tsaya tana shaƙar ƙamshin manjan tsab zata ƙara wani Aman,shigewa tai side ɗin ta tare da kulle ƙofar Falon saboda mugun baccin dake fizgarta kwanciya tayi nan take bacci mai nauyi ya ɗauke ta tun tun Azahar take abu guda sai wajen shidda na yamma ta farka da wata masifaffiyar yunwa, wanka da salloli ta fara yi kafin ta samu ta fita Abinci ta samu ta zubo wanda sai mutum biyar yaci sa, tun da take cin abinci Indo ta ƙura mata ido da mamaki ganin ta cinye Abincin tas "Wai nikam Muneebba lafiyarki? Naga kwanan nan duk kin canza Abincin Mutum biyar kike cinyewa zama ɗaya, ga bacci kamar kasa, ko dai wata cutar ce ta sameku?" Cikin ɗan tsorata da furucin Indo Muneebba ta zaro ido tana furta "kuma fa nima Abin nan na bani tsoro Indo ga kasala da nake ji ko dai wata cutar ce zata kamani?" "A gaskiya Kije kiga Doctor Dan ba láfiya kike ba" Indo ta faɗa Da to ta amsa kawai jikinta a sanyaye tare da Alwashin zuwa ganin likita, haka kwanaki sukai ta tafiya Muneebba bata je ba gashi abin nata sai gaba yake, tun Mom bata lura ba harta fara lura da yanayinta bata kawo komai a ranta ba sai dai ma ƙara Azzarawa Muneebba da tayi Zaune take ita da Indo a gaban Doctor ɗin tana kora mata jawabi, shiru likitar tayi yayin da Muneebba ta gama kora mata jawabi, test ɗin fitsari da gwaje-gwaje ta turata tayi, koda tayo kawo mata tayi ƴan rubuce_rubuce tayi tana bata result tare da furta "congratulations, kina da juna biyu na tsawon 1 Month" Cikin razana da firgita ta yada result ɗin tana furta "what Doctor Anya kinyi bincike dai_dai kuwa kada ki furta man haka mana Doctor kice Abinda kunnuwana suka jiye man ba gaskiya bane" ta faɗa da son gazgatawa cikin mamaki Doctor tace "tabbas tana da juna biyu,abinda kunnuwanku suka ji shine, miye na tada hankalinku kuda za kuyi murna da godiya ga Ubangiji" girgiza kai kawai Indo tayi tana jan hannun Muneebba suka fice a Office ɗin, tafiya suke babu wanda ya tankawa wani, har side ɗin ta Indo da kanta ta rakata har side ɗin ta, shiru tayi wasu zafafan hawaye na bin kuncinta, tabbas ya zama dole ta nemo Bobbi ko dan ta fitar da kanta "Miye na damuwa Muneebba gdy ga Ubangiji za kiyi tunda cikin ya kasance ɗan sunna, na san da cewar tabbas cikin jikinki na Mijinki ne tunda kina da aure na san ke ce Matar Asad BObbi ce" Indo ta furta Da mamaki Muneebba ta kalleta tana faɗin "amma taya kika san nice Matar Bobbi?" "Tun ranar da kika sako kafarki gidan nan nasan kin mance ni lokacin dana zo kawo maki Abinci na ganki,a lokacin dana ga kin dawo cikin House maid ba ƙaramin mamaki nayi ba, ki ƙara haƙuri kawai d ƙaddararki Muneebba" Wani wahalallen numfashi ta sauke tana furta "tuni na amshi ƙaddarata tun ranar da igiyar Auren Bobbi ta hau kaina nasan na buɗe shafin kundin ƙaddarata" cikin tausaya mata da ƙara kwantar mata da hankali Indo ta dinga furta mata kalamai masu kwantar da hankali,a haka Muneebba ta share kwanaki kullum cikin neman Bobbi take a gidan amma babu shi a yadda taji wajen Maheer yayi tafiya kuma zai ɗauki lokaci bai dawo ba hakan na nufin Dole sai cikinta ya fara fitowa sannan zai dawo, taya zata fitar da kanta a wajen mutane waye zai yarda cewar cikin jikinta na Bobbi ne, wane mataki Mom zata ɗauka yayin data gano tana da ciki????? Waɗannan tambayoyin su take yawan nanata wa a koda yaushe, ga wani sabon Al'amarin na Zaidu dake tayar mata da hankali a kullum sai ya haɗa mata tarko tana tsallake sa, ita yanzu ma tsoro sosai abin ke bata ranar wata Asabar tana zaune a garden wajen furanni tana shaƙar ƙamshinsu dan a yanzu kullum sai tazo shaƙar ƙamshin furanni, tsaye taga mutum hakan ya sakata ɗagowa tana dubansa gabanta na faɗuwa sosai, tare da neman tsarin Ubangiji ya kareta da mugun sharrin Zaidu, cikin murmushin mugunta ya dubeta yana furta "kin ƙi bani kanki ta ruwan sanyi to muddin yanzun baki bani kanki ta ruwan sanyi ba zaki ga abinda zan aikata maki wanda fita ma sai ta gagareki mutuncin da kike riƙewa sai na zubar dashi a wajen kowa, na baki kwana biyu ki kawo kanki idan ba haka ba zaki yi da nasani" da mamaki take kallonsa tana maimaita sunayen Ubangiji ta furta "in Sha Allah Allah ba zai taɓa baka nasara akan cutar danj ba, tabbas dana ci amanar aure gara komai za kayi kayi nasan Ubangiji ma ba zai baka nasara ba, ka sani zalunci baya nasara akan gaskiya, kai wane kalar mutum ne?" da kallo ya bita yana girgiza kansa sannan ya wuce, waɗannan kalmomin sune suka dinga bawa Muneebba tsoro a koda yaushe ta tuna su, Zaune take cikin wani kogon baƙin dutse tana surutan da ita kanta bata ganewa saboda tsoro, wata kalar dariya taji an fashe da ita wajen na girgiza da kururuwa cikin ihu da ƙara ji aka furta "to la'ananniya taɓaɓɓiya me kike so wace buƙata kike da ita yanzu yanzu ba tare da kin bar wajen ba zata biya" cikin ɗan tsoro ta furta "Ya la'anannen baƙin sheɗani Marƙudus ina da buƙatar yarinyata ta mallake zuciyar Mijinta ta samu soyayya da kulawar sa sannan da baƙar mallaka, sannan ina so a san yacce za'ayi da Kishiyarta" wata sheɗaniyar dariya aka saki ana furta "Buƙatar ki kafin ki kai ta biya sannan ita kishiyar faɗa Mani hauka ko mutuwa kike so tayi" cikin ruɗewa ta furta "baƙin hauka nake son tayi ta haukace ya sheɗani ka haukatar man da ita ko mi kake so zan baka" dariya ya fashe da ita "yace an gama kalli gabas ki nanata kalmomin da kika furta yanzu" Kallon gabas Mammi tayi tana nanata wa tare da rufe idonta "buɗe idon" taji an furta buɗe wa tayi tana kallon ƙaton madubin da Muneebba a cikinsa, tana bacci Da murya me tsoratarwa ya furta ga jinin da kika kawo can ki ɗakko sannan wancan baƙin zanin mahaukaciyar dake zaune ki yanko sa ki kawo a wajen gunkin can, duk yadda yace tayi haka tayi, wata baƙar ɗiyar roba ta sakawa zanin mahaukaciyar tare da bin ko ina ta ƙulla mata baƙin ƙyalle da kuma jan ƙayalle, "zagayata sau ukku kina nanata kalmomin da kikayi" Zagayata tayi har sau ukku tana furta kalmomin, kamar wata mai rai haka ɗiyar robar ta miƙe tana wata girgiza haka Muneebba dake kwance itama ta fara wata jijjiga sai da ɗiyar robar ta tsaya sannan itama ta tsaya, tana buɗe idanunta tare da dafe kanta dake mata wata irin juyawa "Hhhhhhhhhhhh aiki ya biya kije ki nemo baƙin mahaukaci kiyi zina dashi, sannan nan da kwana biyu ki kawo man jinin da nake buƙata" Amsawa tayi da to tana fita da baya_baya harta fice daga kogon, tsayawa tayi ƙyama tana fito da wani baƙin zobe tare da murzasa tana rufe idonta, buɗe idon tayi ta ganta a bedroom ɗin ta, ƙarƙashin gadonta ta nufa tana jawo wani ɗan ƙaramin akwati ta buɗe wata ƴar siririyar kwalba ta fiddo tana buɗe ta nan take baƙin hayaƙi ya fara fitowa ************************** tun da Muneebba ta tashi take jin kanta na wani irin juya mata wani abubuwa na daban na shigarta gashi. ta kasa faɗin sunan Allah,da ƙarfin gaske aka turo ƙofar Falon ta wanda Indo ce da kallo Muneebba ta bita tana furta "Indo láfiya naga hankalinki duk a tashe" itama Indon kallonta take tana faɗin "Muneebba miye ma bai faru ba,yanzu naga wani sabon tashin hankali wajen Nazifa Muneebba wallahi Vedionki na gani dake da wani kuna aikata Alfasha kuma tabbas fuskarki ce, yanzu Vedio ya bazu ko ina, kizo ki gani" "Ke Indo kin san kuwa abinda kike faɗa Ni ɗin ce nake aikata fasiƙanci da wani sannan harda Vedio na kuma fuskata ki dai bincika mai kama da nice" Muneebba ta faɗa a ruɗe, tana tuna kalmomin Zaidu Indo ce tace "wallahi Muneebba ke ce na gani tabbas fuskarki ce kece ba wani ba, ki fito ki gasgata da ido ki" "Innnalilahi wa'inna ilaihirraji'un, Indo waye zai fitar dani daga baƙin sharrin nan ga cikin dake jikina babu wanda ya san dashi Mijina shi kanshi bai san dashi ba ki faɗa man waye zai yarda dani, waye shedata????" ta faɗa tana fashewa da wani sabon kukan "Muneebba Allah ne shedarki, indai baki aikata ki taso muje kiga nayi" Tashi tayi kamar zata faɗi da ta fito tun da ta fito taga jerin gungun Mutane ana kallonta tare da zinɗenta a ciki ma kuwa harda, masu zaginta, ita kanta tafiyar dai kawai ta keyi ba tare da tasan in da take sanya ƙafafunta ba, hannunta taji an kama hakan ya sakata duban matar dake sanye da baƙaƙen kaya da baƙin abu ta rufe fuskarta, hannunta matar tai taja har suka nufi get ɗin gidan, kallonta Indo ta dinga yi tare da faɗin ina kuma zata tafi ita kaɗai dan ita kaɗai taga tana tafiyar, ganin ta buɗe get ɗin farko ta fita ya sakata Binta da gudu amma sai taji kamar an riƙe mata ƙafafu ta kasa Binta bakinta yai mata nauyi,tafiya Muneebba suka dinga yi da matar wanda duk security na kallon Muneebba babu wanda yai yunƙurin tsaida ita ko bincikarta, a haka har suka fita daga gidan gaba ɗaya, dan ita Muneebba bata gane komai a lokacin sam hankalinta ya gushe, baƙar Motar dake fake a wajen suka shiga, wani baƙin ƙyalle matar ta yafa mata da shafa mata powder nan take ta faɗi a wajen, a tserace motar tabar wajen *Bobbi* Dukkan wasu shirye _shiyen sun gama su a yau ne ake da buƙatar ƙara tantancesu a cikin ƙungiyar wanda wannan ba ƙaramin haɗari ne suke ciki ba, tun safe yake ƙara faɗawa Abokan aikin nasa su huɗu yadda tsare-tsare zasu tafi, Misalin ƙarfe 3 na dare tsaye suke a cikin dokar daji fuskokinsu lulluɓe da baƙin ƙyalle idanuwansu kaɗai ake iya gani, wani da kansu idanun sai da Bobbi yai masu yacce baza'a gane nashi bane,zagayesu Ogan nasu yake yana furta "kamar dai yadda kuka sani kwanakin baya mun tattauna akan yacce ake son tsarin ya tafi na sace Mailbox,a yanzu an shirya jirgi wanda zai ɗaukeku a ciki amma muna da buƙatar ko wane ya buɗe mana fuskokinsa tare da ƙara tantanceku" gabansu ne ya faɗi musamman ma na Bobbi da abokan aikin nasa, cikin su goma biyar suka fara buɗe fuskokinsu kafin azo kan Bobbi Wanda ya ɗaga mayafin da niyyar buɗewa tare da sadaƙarwa tabbas Aikinsa ya lalace sannan ya tabbatar suka ganesa ba zasu ƙyalesa ba sai sunyi masa kisan wulaƙanci kamar yadda suka kashe masa DEEN ********************************* *Fattu* Tun lokacin da aka ɗaura aurenta da JODDi ta kasa tantance yanayin da take ciki ta rasa tsakanin farinciki da kuma tausayin halin da suka tsinci kanta wane take ciki,kamar koda yaushe zaune take ita da Mama suna ɗan fira jefi jefi, dan ba ƙaramin daɗin zaman suke ji ba a gidan, kasancewar Allah bai taɓa basu Malam Ali haihuwa ba ya saka su ɗaukar son duniya suka ɗorawa su Fattu tamkar su suka haife su,kallonta mama tayi tana furta "Fattu dare yayi ya kamata kije gun Mijinki" A kunyace Fattu tace "To" tana miƙewa, ɗakin da aka ware masu su zauna nan Fattu ta shiga,kwance ta iske Joddi hakan ya sakata tunkararsa tana zama kusa dashi tare da ɗora kanta bisa cikinsa tana shafa gashin dake ƙirjinsa, bai hanata ba dan tun yana tureta.idan tana yi harya daina turata, shafawa take tana wani.lumshe ido tare da jin matsananciyar buƙatuwar Mijinta,hancinta takai saitin nasa tana gogawa,wani numfashi suka saki daga shi har ita, kayanta ta cire da nashi sannan ta fara sarrafashi,lura da yana cikin buƙatuwa shima ya sakata bashi damar kusantarta, da kanta ta temaka masa harya shigeta,dauriya kawai take yi, lokacin daya shigeta saboda jin wata irin azaba ta ratsata, ya daɗe a kanta kafin ta tabbatar ya samu nutsuwa,da kanta ta temaka masa ya zare jikinsa,kwanciya yai yana mayar da numfashi, nan take bacci mai nauyi ya ɗaukesa, da ƙyar ta samu ta lallaɓa cikin dauriya ta fita ta haɗa ƙirare ta saka ruwan zafi,gasa jikinta tayi tai wankan tsarki, Bata kwanta ba sai da ta gyara jinin daya ɓata wurin, cikin wani shauƙi da farincikin data tsinci kanta ta shige jikin Joddi tana kwanciya wani bacci mai daɗin gaske ya ɗauke ta kamar daga sama cikin bacci taji an hankaɗar da ita ana furta "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un" da sauri ta ida tashi tana kallon JODDi dake Binta da wani mugun kallo "wacece ke ina ɗan uwana Bobbi,mi kuka aikata mana????" Ya jero mata waɗannan mugayen tambayoyin cikin mamaki da maɗaukakin farinciki ta ɗago tana furta "haƙiƙa ina mai matuƙar farinciki da godiya ga Ubangijin daya bawa mijina lafiya har kana iya magana sannan ka tuno waye kai" Dubanta yake yana ƙara Binta da kallon mamaki "waye mijin naki,ki faɗa man dalilin daya saka kika kawoni nan" girgiza masa kai tayi hawaye na bin kuncinta tana furta "kada dawowar tunaninka ya sakaka mance wace Ni a rayuwarka, ka tuna zamana dakai Fattunka mai son kasancewa dakai a koda yaushe, sannan kuma Matarka mai tsananin buƙatar kulawarka a wannan lokaci" Tunda take zancen bai fahimci koda kalma ɗaya a zancenta illa ƙara tunkarota da yai yana Binta da ƙasƙantaccen kallo yana furta "ban fahimceki ba kuma bana buƙatar fahimtarki, ki ajiye karyarki da kika shirya a gefe da kalamanki na cewar ke mata tace" Kuka mai ban tausayi Fattu ta fashe dashi tana furta "mi yasa zaka zamo mai butulci na baka abu mafi mutunci da ƙima, kaine mutum daka Sanni a ƴa mace ka mayar dani cikakkiyar mace mi yasa kaki fahimtana idan kaƙi fahimtar ni Matarka ce kazo akwai shedu, ta faɗa tana kama hannunsa, Sai dai tassss kake ji ya kasheta da maruka har ukku cikin huci ya furta "kuskurenki na farko da za kiyi shine gigigin haɗa fata dani sannan furta cewar ni Mijinki ne da kuma furta na sanki a ƴa mace ki gyara kalamanki, sannan babu inda zanje neman sheda a yanzu ba sai Anjima ba zan bar nan na koma inda na fito bana fatan sake gani wannan fuskar taki" *End of Book 1* *Tofa tabɗijam rigiji gabji yanzu aka fara wasan* *Shin cikin dake jikin Muneebba kuwa kowa zai yadda na Bobbi ne,ballantana shi uban gayyar koda ta faɗa masa nasa ne shin zai yadda idan yaga vedio da aka yaɗa tana aikata Alfasha, shin zai yadda da cewar ita ce yarinyar daya nema baya ga Mommi ta faɗa masa tayi tafiya* *Shin waye zai yadda da cewar Muneebba bata aikata Alfasha ba* *Shin Muneebba kuwa zata haukace kamar yadda Mammin Maheer ta aikata mata baƙin sihiri, shin su waye suka sace Muneebba* *Shin da gaske Asirin Mammin Maheer zai saka Bobbi yaso Maheer ta mallaki zuciyarsa* *Shin ya abun zai kasance idan Mom ta ga Vedio sannan taga akwai ciki a jikin Muneebba * *Shin taya aikai aka haɗawa Muneebba vedio Alfasha na ƙarya sannan Zaidu ne ko wa?* *Shi ya abun zai kasance idan har Ogan ƙungiyar yaga fuskar Bobbi wane mataki xaya ɗauka shin kashesa zaiyi ko ya?* *Shin mike shirin faruwa da Fattu da Joddi,hankalinsa ya dawo shin zai bar Fattu kamar yadda ya furta? Sanna wane hali Fattu zata shiga idan JODDi ya barta?* *Shin wai ina labarin kurwar Momma da Mamma Ladiyo ta bada shin ya zata kaya a gaba* *Ina labarin Abbie Wanda yake son ya fasa rufaffen ƙwan daya daɗe a rufe* Hmmmm yanzu za'a fara soma wasan *Duk zaku samu tarin amsoshinku a Book 2 wanda yake akan ₦300 kacal, za kuyi making payment a wannan account ɗin 9074759493 MARYAM ZUBAIRU SANI opay bank* *Mai son neman ƙarin bayani ya tuntuɓeni ta wannan Number 09074759493* *Habibties mu haɗu a Book 2 in Sha Allah* Downloaded from GNOVELS.COM.NG This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG For feedback and support Facebook : https://facebook.com/gnovels Twitter : https://twitter.com/gnovels Telegram : https://t.me/gnovels