Downloaded from GNOVELS.COM.NG This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG For feedback and support Facebook : https://facebook.com/gnovels Twitter : https://twitter.com/gnovels Telegram : https://t.me/gnovels D'AN DAKO NA UMMI AYSHA MARUBUCIYAR. AL'MAJIRIN GIDANA AURAN YARINTA WAYA CAN'CANTA AURAN USTAZ ZAMAN TASHA TAYA ZAN GANESHI. AN NOW D'AN DAKO. BISSIMILLAHI RAHMANI RAHIM. YA ALLAH KAMAR YANDA KA BANI IKON FARAWA LAFIYA KASA IN GAMASHI LAFIYA. NA KUDINE AKAN FARASHI MAI SAUKI. DARI UKKU KACAL. KATSINA STATE. ""Katsina garine daya hada jinsin mutane daban daban yan kasuwa da yan boko wayayyi mutane ne ga karatun Addini garine mai yalwar mutane dakuma karrama bako mafarin takenta da KATSINAWA DIKKO DAKIN KARA KUNYA GAREMU BADAI TSOROBA. Tana da yalwar unguwanni masu dumbin yawa na talakawa dana masu kudi. G.R.A Kyakyawar unguwace data tara hamshakan masu kudi yawancin su duk yan bokone sai yan kasuwa unguwace da baka ganin gilmawar mutane barkatai sai dai kowa yazo da abun hawanshi ya wuce sahoda shimfidaddan titine daya wadatu da kwalta da tatafi dodar gefe da gefen titin kuma wasu irin shukokine masu tsawon gaske da sukayima gidajen dake jere reras cikin unguwar kawanya hakan yasa titin yakasance mai masifar kyau da daukar hankali bakajinkomi sai na isakan dake kada shuke shuken . Tsaye nayi ina karema tafka tatkan gidajen dake unguwar kallo ka na gilgiza tare da cigaba da tagiya ina tinanin kamar bazaa mutuba da mutane ke gina irin wannan katafaran gidajen. Wani wawan burki naja gajin wani tamfatsetsen gida dayafi kowane gida akan titin kyau da tsaruwa tindaga get dinsi da kalar penti dake garai da irin furanni da aka zagayeshi da su. Jin ana kakaniyar bude babban get din ne yasa nayi tsaye danba idona abinci. Wani dattijone mai kimanin shekaru hamsin zuwa da biyar ya wangale get din da kyal . Inda wata jar mota kirara FERARI ta sheko da gudu takusanyin kan yatsun dattijon nan da gudu ya kauce tare da tsayawa gefe yana maida numfashi. Ganin motar ta wuce batare da tatsayawaba yasashi gilgiza kanshi tare da bude bakinshi yace Allah ya shiryaki AMNAH yasa kifara ganin daraja manyanki som halinki ba dayaba da mahaifiyarki babu abunda kika rage na mahaifinki. Dakyal yasamu ya maida get din ya rufe tare da zama akan dan bencin dake gefe yafara saita Radio dake hannushi. Wata matashiyar budurwa da bazatafi shekaru 17 bace ta fito da sauri daga cikin faskeken gidan ta nufoshi tanafadin . "Baba Madu wai Amnah fita tayi ne? Da sauri ya ajiye radio ya mike tsaye yace. " eh hajiya Amal tafita badanjimawaba ina kwana." Kanta ta gilgiza tana Aro fararan idanuwanta tace baba da allah kadaina gaidheni nifa jikarkace wallahi mantawa nayi bangaishekaba ina a rudeme tare fa Mamy tace zata aikemu yo sayayya kasuwa wai ita bazatab taita karo da talakawa tafison super market kuma taya za'ayi asaida kayan da Mamy ke rabawa cikin Watan Ramadan super market? Murmushi Baba Madu yayi yace "To kuje inda takeso mana Hajiya Amal. Kanta ta dago ta kalleshi tace baba kayan fa da yawane irinsu masara gero dawa acca Alkama baba kasan sai kasuwa. Shuru yai sai murmushi dayaketa zuvawa batarr dayace komi ba Dan yana ganin matsalar suce ta guda bai kaqta ta shafeshi ba. Juyawa tayi cikin gida ranta amatukar bace . Kallonta yayi ya gilgiza kai tare da cewa allah kenan yayoku ciki daya amma ya bambanta halinku kekuma sai kika rakko na mamanki ita kumabta dauki na babanku. Kai tsaye babvar kofar dake zagaye da glass din palon ta bude tashiga babban falone sosai yasha blue da gold na kujeru da labulaye da carpet bakajin kominaciki sa karar Ac da wani irin sihirtaccen kamshin tiraran Wuta mai masufar dadi. Zama tayi tare da dafe kanta tana jin bacin rai na halin da yar uwarta take nunama talakka. Jin kara tafiya daga saman benen yasata saurin dago kanta inda ta saukesu fess akan kyajyawar fuskar magaifiyarta dake sakkowa fuskarta cike da alamaun mamaki. Kyakyawar macace fara sol da ita daga ganinta buzuwace ko balarabiya sanye take dawani dakeken lace maroom da kyanshi ya usa fallasa asirin tsadarsa yan kunne gold je akunnanta hannayenta sanye da manya manya zobuna gold maeu masifar kyau da tsada. Cikin daddadan magaja ta sakko kasa tare da zama kusa ea Amal tasanya hannunta ta juyo da habar Amal din tare da tambayar. "Lafiya bakuje ba tare bayan naji karar fitar motar Amnah"? Ido cike da kwallah tace Mamy ta tafi ta barni nason ta tafi yin gaban kanta ne ai dama batayi niyyar zuwa kasuwar nan ba som taya za'ayi tace sai super market abinda in kasuwane da munje layin yan Awo zamu shiga gasunan masu kyau sabbi bana super mariet ba da wasu zakiga sun kwashi shekaru saboda ba acen ne mahallinsu yake ba. Shuru mamy tayi ranta abace . Sai da ta nisa kana ta dakko wayar ta ta lallatda ta kara akunne tana huci tare da gilgiza kafarta daya da tasha jan lalle. Jin an daukane yasata fara magana cikin tsanainin fushi. "Kin kyauta kinyi abunda Ranki da Zuciyarki suka Raya miki, Amma wallahi kisani kika siyomun tsaffin kayan da Zanyi sadaka dasu sai ranki ya masifar b'aci, Saboda nafiso in'bada abunda zan iya ci, Sakarai kina Mace amma kinkasance mai kyamar talakawa bayan bakison inda Aure zai kaikiba, Shashasha kawai ta tsinke wayar. Suna zaune kimanin 30mnt sukaji an buÉ—e get din gidan. TSuke fuska Mamy ta karayi tare da maida hankalinta ga waya tana latsawa Bayan kamar ten mnt sukaji an'buÉ—e kofar tare da sakin siririyar Sallama. Sanin muhimmancin sallama yasa Mamy batare da ta dago kai ta kalletaba ta amsa. Masha Allah itace kalmar dana furta lokacin da idanuwana sukayi tozali da kakyawa budurwa da bazata wuce shekaru Ashirin da biyu ba aduniya, Farace sol irin farin Mamy ,Gawasu mayun idanuwa dake gareta wayanda suketa lumshewa kamar zatai bacci, Daga cikin kwayar idon nata kuwa wata zaiba -zaiba ce ke shinning aciki ,ga wani dogon hanci har baka ,sai É—an bakinta mai Dauke da pink lips,Atakaice Dai kyakwace ajin farko, gata doguwar mai faffadan jiki dai- dai misali ,Tana da wani irin shape mai masifar É—aukar Hankali, Ga wasu cikakkun Brea's da hips É—inta masu tsananin fadi da girma, sanye take cikin wata Abaya brown mai duwatsu tabi jikinta tayi luf sai kafarta dake sanye da coffe din Tom's da yar jakarta data kasance coffe. Ahankali ta karaso cikin palon Idon'ta naga kan mahaifiyar Tata ,Gudan Hannunta kuma na rike da madaidaiciyar kula. Waje ta samu gefe da ita sosai ta zauna tare da fadin "Mamy nah fushi kike dani? Nifa ba kasuwa naje ba, Naje gidan Nene ne tayimun Danbun kaji gashi fita zatayi shiyasa kamin Amal ta shirya naje na dawo, Amma sai faÄa kike Mamy babu ko Saurarawa, Halan wannan yarinya ta hadamu takarasa tana sakarma Amal harara. Baki Amal ta turo tana sake lafewa jikin Mamy'n. Kai Mamy ta dago jin Abinda tace tare da sassauta fuskarta tace. Ai'nasa gaban kanki kikayi Amnah,Nasanki sarai wallahi zakiyi fiye da haka!. Kanta ta shafa tare da yatsina fuska tace "kema Mamy kibari Abba ya wadata gidan da ma'aikata wayanda zasuna miki komi Amma kinki, Amma kamarmu Ace wai mune zamuje kasuwa muyo wannan sayayya, Inama laifi Ace shinkafane ko drinks Amma kawai sai Aganmu munje yin awo, Som kamanni mu bai dace da hakaba !Takarasa cikin natsuwa kamar ba ita ke maganaba. Ido Mamy ta tsiramata sosai tana kallonta, acikin zuciyarta kuwa Abubuwa da dama take sakawa game da gudan jinin nata, Kanta ta gilgiza tare da faÉ—in. "Ki ajiye wanna Kular Naman kitashi kuje, in kuma bazakiba bani kudina ,Ma'aikata kuma banaso so kuke in lalataku sai an'kaiku gidan aure a koroman ku akan baku iya komi ba ko? Baki Ammah ta turo tace nida gidana nike fatan a wadatashi da kayan more Rayuwa, aÆ™alla inaso inga mutum sama da goma aÆ™al kashina suna mun bauta ina biyan su,Ta yanda ko hakki zan É—auka akwai wanda zayyi saurin mikoman, Saboda abun ya kasance aikin shi ne. Cike da bacin rai mamy tayi kwafa tare da cije bakinta. Cukin natsuwa Amnah ta mike tsaye tare da gyara rolling É—in dake kanta ta sargafa jikkarta key din motar ta ÆŠakko ta rike tana gilgizawa Tare da kallon Amal batare da tace komi ba ta sanya kai ta wuce. Amal tason bazata tankamataba hakan yasa da sauri ta mike tsaye tare da yafa gyalanta tace . "Mamy nah sai mundawo." Fatan Alkhairi tayi musu tare da kishin giÉ—awa akan lallasan kujerun palon tana lallatsa waya ta kanga a kunne. Jim tayi kafin a É—auka. Ana É—aukar wayar kuma ta sauke ajiyar zuciya Tare da faÉ—in. ""Akwai matsala Haj Lubna, Akwai ga garumar matsala wallahi, Halin Amnah yana masifar bani tsoro da mamaki, ita som batason haÉ—a jini da talaka ba ina bauta zai mata ba, batason Æ™ulla mu'amullah da talakka batason shiga inda talakka zaije, Ita kawai ta É—auki talakka An halitto shine dan Yayi bauta a'sallameshi, Kana ta É—auki talaka mutum ne mai kasada Akan Rayuwar shi in Dai zaka bashi kuÉ—i Æ™alilan, Tana ganin Talaka mutum ne wanda zai iya bada ranshi da rayuwarshi dan kudi, Hajiya Lubna ina ganin lokaci yayi da zan zaunar da ita ina warware mata zare da Abawa.. Ajiyar zuciya ta sake saukewa akaro na biyu kana tace shikenan sai na ganki ta kashe wayar.. Amnah Suna fita ta faÉ—a motar ta tare da kifa kanta akai ta sauke ajiyar zuciya, Haka nan take jin wani yanayi marar daÉ—i dakuma bakin cikin da baida musultuwa , Ko kaÉ—an tanajin kamar zatajene inda za'ayan'yanka naman jikinta ,Karshentama tason yanda talakawa basu da hankali suna iya takamata kafarta. Da sauri ta rintse idonta tare da dago jajayen idonta da suka canza launi ta zubasu ga Amal data buÉ—e motar ta shigo. Cikin rawar murya mai hade da tashin hankali tace. "Hankalin ki ya kwanta zaki kaini inda zuciyata bata aminta da zuwa ba ko? Wallahi Amal inajine kamar numfashina zai É—auke saboda masifar baÆ™in cikin da nike ciki, Waiku wace irin zuciyace daku keda Mamy Nason shishigema Talakka? Muna da kuÉ—in da in mutum dubu mukeso mu aje awannan gidan zamu ajeshi kuma zamu kyautata sallamasu, Amal jibi gidan ubanmu jibi irin motar da muke hawa amma ace da ita zanshiga kasuwa takarasa tana dunkule hannunta tare da dukan dayan. Tsoro furgici ruÉ—u suka ziyarci Amal lokaci guda,bata taÉ“a tinanin abun yar uwar nata ya girmama haka ba ,tana ganin da duk abunda take kamar wulakancine sai yanzu ta tabbatar da duk abunda take akan gaskiyarta take yinshi. Motar ta tada Tare da janta afusace. Cikin sauri Amal ta kalleta tare da kallon get din. Ajiyar zuciya ta sauke ganin tini Baba Madu ya bude get din tare da lafewa bayanshi. Karcet ta fita da motar tare da cillata kan titi. Cike da kwarewa take murza sitiyarin har suka fara shigowa cikin gari inda Amal ke mata nuni da Hannu inda zata shiga dan ita batama taba zuwa wajen dake da cinkoso ba irin wannan. Duk inda suka gifta ido ke dawowa kanta, kasancewar motar samanta bude yake. Siririn tsaki taja tare da furta. "Jakai kawai motar ma sai ankalla kai talakka baiba." Ido Amal ta rintse tare da kauda kanta gefe. Ahankai suka shigo cikin faskeken get din da aka rubuta CENTRAL MARKET, inda suka dinga wuce wurare har suka bullo ta get DIN yan Awo. Tsaki ta Æ™araja akaro na ba Adadi Tare da ÆŠakko wani brown din glass ta toshe idonta da shi, Tare da kara tsuke É—an karamin bakinta dake zagaye da pink lips. Amal tace ga inda zamuyi parking cen kana mufito ba. Kallonta tayi a kufule kamar zatai magana sai kuma ta fasa ta tsaya dai dai wajen wasu mutane dake tsaye suna rike da buhun huna gero. Wani dattijone cikin kamala yace yam Mata gero kike sone.? Kamar zata kyakeshi kuma ta daure tace "Eh". Tare da buÉ—e jikkarta ta yago wata paper tayi rubutu kadan tare da mikamai dan gani take tsayawa magana da shima É“ata lokacine. Jujjuya takarda yashigayi dan yakasa fahimtar mita rubuta dan da turanci tayi rubutun. Kafeshi tayi da ido tana kallo dan ta fahimci abunda yake nufi, tsaki ta saki sosai wanda yasashi juyowa ya kalleta saikuma yafara kokarin magana. "Babaaaa" Itace kalmar data ratsa dodon kunnasu ta katsema dattijon magana da yake kokarin yi. Ahankaki ya juya ga saurayin da yayi shigar buzaye inda ya rufe fuskarshi baki É—aya da baÆ™in rawani, Ƙafar shi sanye da slipas masu saukin kuÉ—i, BaÆ™in wandone jikinshi sai farar riga ta wani yadi da yasanya ,Baka ganin komi sai kwayar idonshi . Dattijon yace Yawwa Habu kaimun wannan takarda shagon Mai Shadda kace nace ya fad'amaka Abunda akasanya saika kawoman. Dan jim yayi kana ya dago ya kalli mutumin baice komi ba kuma yafara tafiya cikin sassarfa. Anan na karemai kallo dogone sosai gashi da wata irin kira ta karfafan maza ,Cike da sassarfa yake tafiyar har ya shawo wata kwana inda ba yawan mutane sosai Kana yasamu wuri ya zauna ya duba takarda baki dayanta yana gama dubawa ya tashi ya maidata aljihu yayi gaba ya dawo inda dattijon yake. "Akausashe yace bayanan amma na haÉ—u da wani na bashi ya dubaman tana bukatar gero dawa masara acca alkama buhu hamsin- hamsin sai kamata lissafin kudin kana Asamata mota,Ya Æ™arasa yana kokarin wucewa. Yalwataccen murmushi ya faÉ—aÉ—a ga fuskar Dattijon yace. " Kai amma Alhamdulillah dama yau mukayo sabon sari duk zata samu, Kai Habu kaje store ka kwasomata kayayayyakin kana sawa a'mota ko kunzo da motane Hajiya? Ya tambayi Amnah. Bakinta ta tabe ta juya kai da sauri Amal tace aa baku da D'AN DAKO ne wanda zai kai a'mota? Da sauti yace ga Habu nan zai kai maku duk inda kuke so. Kallonshi Amal tayi sosai tace sai kasasu a'mota kabiyomu ko? Kanshi ya gilguza batare da yace komi ba. Cikin sauri yafara tafiya zuwa wani É—an shago dake tsaune da hatsi cike da jarumta yake sabo buhun nan y'ana sasu bayan motar. Sosai Amna ke kallanshi tanaji inama ace kasanta yake dayasha bauta son rai , Da n daganinshi zai jure wahala . Saida ya Tabbatar da ya cika bayan karamar mota kana ya koma wajen Dattijo'n cikin wata irin murya da som batai kama da ta buzaye ba yace . "Baba nagama amma duka buhu hamsin nasanya zanje indawo sai inkwashi sauran. Da sauri Baban ya daga kai tare da cewa yawwa kaga kana da naira dubu biyar kenan a wayanda ka É—ora, kuma suna son buhu kusan dari biyu kaga yakama zaka samu dubu ashirin yau kenan. Bai ce komi ba haka kuma babu wani alamun farin ciki a abunda aka faÉ—amai ya juya ya shiga yar gwatsar motar ya tada inda duk ya wuce zakaga hayaki mutane kuma na kiranshi da Bukar Buzu . Duk uban kiran da akemai sai dai ya juya ya É—aga musu hannu amma babu wanda ya taba cewa ga kalar fuskarshi ko kalar magana shi sai Dattijo. Tafiye suke har suka shigo cikin gari sosai inda keda cunkoson ababe hawa. Cikin fushi ta tsaida motar . Ganin haka yasashi shima tsaida tashi dake bayan tasu. Afusace Amnah ta fito ta isa wajenshi rai aÉ“ace. "Tace kai wane irin shashashane kidahumi ? taya zaka cikamun kunne da ihun wannan gwatsar motar taka ?Miyasa bazaka bari inyi nisaba kamin ka biyoni? Matsala mu_amullah da jahilai kenan talakawa masu aiki irin na dabbobi,Dan kaja al'umma su raina ajina kaja aga tare muke ,ina mu'amullah da kazami irinka wawa kawai mtssss. Tinda ta fara magana bai tankamata ba haka kuma babu niyyar tankamata a'tattare dashi. Afusace Tace kai D'AN DAKO Bakajinane. Shuru yamata yana kallon titi. Dogon tsaki taja tare da watsamai yawu ta wuce. Ahankali yasanya gefen rawaninshi ya share baice komi ba sai Yatsun hannunshi da ya dinga É—aÉ—É—agawa ahankali saman sitiyarin motar. Motarta ta koma ta tada tare da cillata bisa titi aguje. Tada tashi yayi yabi bayanta har suka ido kofar gidan nasu. Hon tayi da sauri Baba madu ya bude ta danna hancin motar ciki . Ganin haka shima yasanya tashi aciki dai- dai tsakiyar gidan yayi parking bai yarda ya karasa wajen da ta ajiye tataba ya fara sakko dasu cikin Sauri, Cikin Æ™anÆ™anan lokaci yagama yayi tsaye yana jiran abashi cikon da zai kaima Baba kana ya ÆŠakko sauran. Amal ce ta fito da sauri ta karaso wajenshi ta mikamai kudi tace dan Allah kayi hakuri dazu naga kamar Aunty Amnah namaka faÉ—a ko? Kai ya gulgizamata cike da gundura shi kudin shi kawai yakeso tabashi ya wuce ta tsayamai tambaya. Kudin ta mikamai tare da fadin munafa jiran sauran yanzu. Bai cemata komi ba ya faÉ—a motar yafara Æ™oÆ™arin tadata amma taki tashi. Ahankali ya sakko Tare da kwanciya Æ™asan wajen ya danyi taÉ“e -tabe 'nshi kana yakoma yatada amma still taki tashi. Fitowa yayi tare da dafe kanshi yanajin kamar ya saki kuka ga wata mahaukaciyar yunwa da kishi da yakeji , Babu abunda yaci ya fita kasuwar yana zuwa kuma aka haÉ—a shi da wannan aikin. Tausayi sosai Yaba Amal dake tsaye gashi ya nade fuska duk uban zafin da ake da alama ruwa za'ayi dan garin ya É—auki wani mahaukacin zafi, Cikin sauri ta koma palonsu tare da shiga kicin ta samu wani katon flat tazubo shinkafa da miya da taji naman kaji da coslow gefe ta dauki wani flat madaidaici ta cikashi da Pepe chicken tare da É—aukar kunun Aya mai sanyi ta tsiyaya a madadaicin juk ta É—auki robar ruwa guda daya ta shirya kayan akan babban tire tafito da sauri. Akan hanyar fitane daga palon sukaci karo da Ammah ta bita da kallo. Fuska Amal É—in ta É—aure sosai tare da buÉ—e kofa tayi saurin ficewa. Kai tsaye inda yake ta nufa tare da. " Cewa sannu kana ta shan rana motar yaki tashi ko? "Um" yace agajarce. Dago kanta tayi ta kalleshi ganin yanzu har girar shi ana gani sabanin É—azu da kwayar idon shi ke rufe. Ganin hakan ne yasa da sauri ya jawo rawanin ya lullube ko in nashi yabar kwayar idon nashi abuÉ—e. Murmusi ta saki tare da cewa ku buzaye bakwajin zafi bakwajin kuma nawi? Shuru yamata yana jin É“acin ran surutunta shidai yatsani atasashi gaba anamai magana . Abincin ta ajiye gabanshi tace" ÆŠan Allah ka zauna kaci sai in'kiramaka mai mana gyaran mota kaji? Kai ya gilgiza cikin kuma yanayinshi na sanyi ya bude baki . Yace nakoshi Allah ya amfana . Ido ta zaro tare da haÉ—a hannayenta tace dan Allah da manzonsa ka zauna kaci abincin nan, Na rokeka, in'ba hakaba Amnah zatamun dariya wallahi, ka taimaka takaras tana dora kanta akan wuya alamun roko. Dan jim yayi sai kuma yace shikenan na gode amma kijuyemun aleda kar in É“ata muku kwanikka yakarasa cikin sanyi. Tausayi yabata sosai wato yana ganin bai kai matsayin da zaici abinci cikin kwanan da zasu ciba kenan. Cikin natsuwa tace aa mudakai duk yan Adam ne bawani abu kaci kawai. Jin cikin shi namai wani mahaukacin yatsinawa ne yasashi mika hannu biyu ya É—auki kayan abinci tare da buÉ—e Bayan motar ya ajiye kana yashiga ciki shima yayi shuru yana jiran ta tafi. Fahimtar hakan yasata juyawa ta koma ciki tana mamakin yanda yake da kamun kai haka da kunya kamar ba DAN DAKO ba dan tason su da fitsara. Yana ganin wucewarta ya juya ya kalli ko ina ganin babu kowa sai mai gadi da shima ya juya baya yasashi kai hannushi bayan rawani ya kwance tare da fara zagaye fuskanshi dashi har ya kwance. Ahankaki ya ÆŠago kanshi yana sauke numfashi. Wani irin tsalle zuciyata tayi da tasani sakin wayar batare da na shirya ba...... 5/18/22, 09:33 - MY MTN 2: 🌹D'AN DAKO MALLAKI UMMY AYSHA🌹 3ï¸âƒ£&2ï¸âƒ£ ""Masha Allah itace kalmar da ta samu fitowa daga cikin baki na. Wani irin haÉ—aÉ—É—an saurayine fari sol irin farin larabawa, ga wata tausassa sumar da tayima kanshi Æ™awanya, ga sajenshi da yayi ma sumulmula fuskarshi kyau yayi shar sakamakon zufa da fuskarshi tayi, Wani irin dogon hanci gareshi da yatafi D'oÉ—ar har baka, ga wasu jajayen lips da suka dace da kyakyawar fuskarshi, yana da idanuwa masu masifar kyau da É—aukar hankali. Ahankali yaja hannun rigarshi sama kutt na furta lokacin da idanuwana sukai tozali da kyawawan hannayenshi da suka kasance farare sol, Ga galgasa da tama hannu rumfa irin dogayen nan mai tsananin sheki da sulÉ“i. Robar ruwan ya É—auka tare da fidda hannunshi waje ta window mota ya fara wanke hannun shi. Yana gamawa yaja kwanikkan tare da buÉ—e su. Idon shi ya lumshe dan yaushe rabon da yaga abinci mai kyau kamar wannan. A'hankali yayi Bissmillah tare da fara tsakurar abincin kaÉ—an -kaÉ—an yana ci. Baiwani ci da yawaba ya ture tare da turo hannun shi still ya wanke ya É—aga cup din Kunin Ayar yasha sosai saida yayi rabi kana ya ajiye. A'hankali bakin shi ke motsawa alamun Addu'a yake ta bayan gamacin abinci(ALHAMDULILLAHI LAZI AÆŠÆŠA'AMANI HAZA, WARA ZAKNIHI MIN GAIRI HAULIN MINNI WALA KUWWA) Idon shi ya lumshe tare da jingina kanshi da motar. Dai -dai kuma lokacin ne aka fara iska mai tsananin karfin dake nuni da ana gaf da sakko da Ruwan sama. Idon shi ya lumshe tare da shaÆ™ar kanshin Æ™asa dake tasowa. Da kallon gefen da kayan daya ajiye musu yake wanda ya tabbatar da in ruwa ya safka akansu sun gama yawo. Cikin natsuwa ya maida rawanin fuskar shi tare da fitowa yafara tsakula motar dan yasamu ta tashi yakara gaba kar ruwan ya safko amma motar taki tashi. Tsananin fushi yatasomai wanda yasashi kaima motar wani wawan dukan dayasa marfin É“allewa ya fita. AÆ™ufule ya kwaso tiren kayan abinci tare da ajeshi cen gefe inda za'a iya gani kana ya dawo yana É—aga kanshi sama ganin yanda garin ke rinewa sosai. Tsaki yasaki tare da fara kokarin tafiya. Dai -dai lokacin ne kuma Amal da mam6y da Amnah suna fito cikin sauri Amal tace . "ÆŠan uwa dakata mana." Shuru yayi batare da yatsayaba kuma bai fasa tafiya ba. Yana gab da cimma get Amal tace katsaya Dan Allah. Cak yatsaya batare da yajuyo ba. Rai É“ace da ganin yanda yaketa izza Amnah da tasha wasu riga da wando da suka masifar yimata kyau rigar orange mai ratsin Black sai wandon kuma daya kasance Black mai ratsin orange kanta sanye da wata Black din hula data É—an turata baya yalwataccen gashin goshinta duk yafito, daga Baya kuma foygon gashinta ya bazu akafaÉ—ata sai sheki yake,Cikin isa tafara tako cike da izgili har zuwa inda yake. Cikin tsananin É“acin rai tace. "Mene Acikin Tumbi banda kashi,Ina É—an burburi ina niganci,Ina talakka ina girman kai,Ina D'AN DAKO ina iskanci da har za'adinga kiranka amma kayiwa mutane banza ka kyalesu kai ga shashasha ko? Wawa baÆ™auyen da yakasa gane gabas da yamma, Kayi maza kaje anason ganin ka koba sallamaka za'aiba da kake nunama mutane iko, Takarasa tana nunamai inda su Mamy suke tsaye akan Bagala.. Da zata lura baki dyayan jikinshi kyarma ya d'auka kyarma da rashin ganin fuskarshine yasa aka kasa ganewa... Amal tace Mamy kije da kanki kartamai wani abu fa. Cikin amincewa da maganata Mamy ta tattako cikin dattako har inda suke tsaye. Sallama tayi tare da cewa bawan Allah munata magana amma shuru . Baice komi ba sai juyo da kanshi da yayi ganin Babba maca ce cikin mutunci ya buÉ—e bakin shi ya gaishe ta . Amsawa tayi cikin fara'a . " Tace dan Allah ko zaka iya zuwa ka kwashemun kayan nan, Naga kamar za'afara ruwa kuma munan bamu da masu kwashewa wancen Tsohon bazai iyaba saboda halin girma ta nuna mai gadi. Kai ya jinjina batare da yace komiba yayi gaba cikin sassarfa. Yasa hannu zai É—auki kayan kuma yayi tsaye yana tinanin ta ina zai dosa dasu ga bakin shi yayi Nawin da bazai iya magana ba. Mamy takatse mai tinani da faÉ—in ga inda zaka ajiyesu acen, Wancen store É—in dake kusa da dakin Baba Madu. Baice komi ba sai kwasar kayan da ya fara cikin jarumta yana kaiwa kamar ya d'auki kwali. Yana gab da gamawa akafara iska mai matsanancin Æ™arfi. A'hankali ya duÆ™a yakama kowanne buhu da hannu É—aya yazamana buhu biyu ke ahannunshi yafaraja da sauri. Suduka kallo suka bishi dashi inda Mamy jarumtar saurayin ta burgeta, Hakanan taji sha'awar samunshi amatsayin wanda zai dingamata hidimar gida koda kuwa aikin kula da get ne, Dan taga dakyal Baba Madu ke buÄeshi yana rufewa. Zai kai buhun karshe cikin sauri jin ana yayyafi gefen buhun ya fashe wanda yasa Dawar dake ciki fara shatata. Saurin ajeshi yayi cikin zafin nama ya sungumi É—aya'n yayi É—aki. Dawowa yayi ya kai wanda ya fashe tare da Sunkuyawa yana kwashe wadda ta zube. Fararan ya tsunshi yasa yana tattarawa yana tsaka dayi Saiji yayi an takemai su da Æ™arfi da tsinin takalma. Wanda hakan yasashi saurin juyowa da karfi ya sauke kwayar idon shi cikin ta Amnah. Bin dogayen yatsunshi take da kallo ganinsu wasu irin farare tass har wani jaja sukeyi ga tsintsiyar hannu A yalwace da galgasa.. Ido takashe tanamai kallon kurullah tare da kara É—aro idonta a murzazza fatar shi datayi lumi. ""Kai ÆŠan Dako ne kuwa? In har takasance haka miyasa kamuna asara? Kana aiki da hankali kuwa? Kai da kake Talakka kai ya kamata ace kafin kowa iya tattali, Amma saboda ba gidan Tsoho bane sai a wifintas? Shuru yayi har lokacin kanshi a sunkuye yake sai hannunshi data danne da takalma da yake kallo wanda still tana akai taki É—agawa shima bai motsa ba.. Mamy takaraso wajen tare da dakamata tsawa da ta sata matsawa. KuÉ—i mai yawa Mamy ta Æ™ilgo tabashi tare da cewa. "Dan Allah kayi hakuri kaji ko,Yarinta na damunta ,ƘarÉ“i wannan maza katafi kaga am'fara yayyafi wannan kabarshi ba damuwa ko Baba ya ba tsuntsaye. Mikewa tsaye yayi tare da ƘarÉ“a kudin ya kilga ya dauki dubu biyar yace. Ga sauran nan na kilgi abunda ke hakkina . Mamaki sosai yaba Mamy wanda ta bishi da kallo na ganin yanda yabata maÆ™udan kudin da ita kanta batason adadinsu ba. Murmushi ta saki tare da cewa" ka rike nabaka ai. Kai ya gilgiza alamun a'a... Tsawa Amnah ta dakamai tare da faÉ—in basu kazo nema ba? Kuma zaka tsaya kana ja'inja da ita munafuki ka ƘarÉ“a ka wuce daga nan ka cikamu da warin talauc.... Tass!Tass!Tass!!! Haka Mamy ta wanketa da kyawawan maruka guda ukku wanda sukasata Tuntsirawa. Kamin mamiu ta juyo har yakai get cikin sauri tare da kwance rawanin kanshi yafara tafiya. Kiranshi mamy keyi ko tsayawa baiba. Cikin ikon Allah yana fita yaga mai Machine ya. Haye tare da" faÉ—in ya kaishi kasuwa. Ganin mai machine na kallon shine ya sashi tunowa da ashe fuskarshi ba É—aure take ba, Da sauri ya naÉ—e fuskar yabar kwayar idon shi. Cikin rawar jiki da son samun shiga mai machine yace "Wallahi Dan uwa kaman kama da wani Soja mai suna Sadeeq daya Æ™asance ÆŠan Gidan Matawalle... Tsawa sosai ya daka mai tare da faÉ—in saukeni! Dan na hau machine É—inka shike nuni da kasamu damar da zakamun tambayoyin da Ranka keso ?Maza saukeni anan kamin in maka abunda bakai tinani ba, Duniya ba akamane da zaka tsareni da tambayar banza yakarasa cikin sauti da rawar jikin da ta furgita Mai Machine. Cikin Rawar É—ari mai machine yace "Kayi hakuri Wallahi nima cewa nayi kamace saboda na taÉ“a ganin shi so É—aya gidan da nike kai yaransu makaranta Lokacin ma da kek.... Kan ya Æ™arasa ya saki wata gigitatta tsawa da tasanya mai machine saurin yin parking tare da direwa ya yanka da gudu.. Tsaki sosai ya saki tare da sauka yafara tattakawa da sauri dai-dai lokacin ne kuma aka tsuge da ruwan sama sosai. Babu abunda yashamai kai tafiyar shi yake cike da zafin nama sa hannayenshi da yasa ya tare Duka aljihun shi saboda wayarshi da kuma kudin Baba daya karb'o. Abangaran Mamy kuwa afusace ta kalli Amnah tace ke da kinson Asalina da naki da kuma wahala rayuwa danasha Wallahi da baki kyamaci talaka ba , Saboda...Sai kuma tayi kwafa tare komawa ciki tana share Kwallah a fakaice. A É“angaren Amnah kuwa. Kyarma sosai jikinta ya É—auka akan talakka yau aka mareta aka kaskantar da rayuwar ta agaban wanda baida matsayi. Jin ruwa ya kaule da karfi yasata tashi jiki asanyaye tayi É—akin ta tare da É—aga waya ta Daddana. "Please Abbah ka dauka" Tafada tana yarfe hannu tare da matse Kwallah. Jin ta kase bai É—aga ba yasata hakura sai kwanciya da tayi akan makeken gadonta ta saki wani mahaukacin kuka mai tattare da Æ™unar zuciya.. AÉ“angaran Mamy kuwa tana shiga É—aki ta dyauki Æ™aramar wayar ta tare da kiran Mijinta Alhaji Isa mai Zinarai da number shi ta sirri da bakowa yason shi da itaba sai amintaccen shi. Bayan ya É—auka suka gaisa . mamy take tambayar yaushe zai dawo sunyi kewar sa? Murmushi ya saki tare da faÉ—in nima haka amma next week ina nan dawowa insha Allah ina Yara na?.. Farin ciki sosai Yakamata inda tace" To Allah yakawoka lafiya zanma tarba ta mussam man . Murmushi yasaki mai sauti yaire da faÉ—in nasani matata nason zakimun fiye da haka . Dan jim tayi batace komi ba dan gane da yabon da yamata. Daga cen É“angaran yace. "Are you ok Sweetie? ÆŠan nisawa tayi kana cikin raunatata murya mai haÉ—e da roko tace Hubby wallahi alfarma nike nema awajenka. Ajiyar zuciya ya sauke tare da faÉ—in Alhamdulillah da awajena kike nemanta ba awajen kowa ba, indai har kinsanni kinsan waye ni to kinson babu Abinda zan gagara yimiki, Dan haka faÉ—i buÆ™atunki kai tsaye nida abunda kikeso duk mallakainki ne ... Wani irin sanyi ya ratsata cike da kwarin gwiwa tace "Hubby agasjiya ina da bukatar sabon mai aiki , Saboda Baba ya manyanta, Ga rabon nan da zanyi bazan iya cewa komi sai su Amnah zasuyiba kadai son halinta zamuyita samun matsalane da ita. Shikenan Tsadadda "Matata duk abunda kikeso haka za'ayi insha Allah zanyi Æ™oÆ™ari sosai wajen samo miki wanda ya dace. Da sauri tace ''Am nace ba ... Nan ta kwashe duk abunda ya faru game da wanda yama su Amnah Dako tare da jaddada mai cewa zai iya dayuke duka ragamar gidan baki É—aya, Fatan ta dai ya bata izinin zuwa nemanshi wajrn mahaifinshi dan taga alamar yayi fushi da abinda Amnah ta mai duk da ba komi ta fad'amai ba tana ganin sirri ta ne tsakaninsu da Yar ta. .. Cike da fahimta haÉ—i da kwarin gwiwa yace "Na amince miki Hajiyata duk abunda kikeso ina sonshi, Ke kinson matsayinki awajena sannan kinson burina da farin cikina inga kinsamu abunda kikeso. Fira suka shiga yi cike da shauki kana ya kashe wayar. Ganin babba wayar shi Amnah ta kirane yasa da sauri ya maida mata kira. Cikin shagwaÉ“a take faÉ—in "Abbana bakasona yanzun kwana nawa banjika ba? Murmushi yasaki tare da cewa "Amnah nah in bansoku ba wazan So? Cikin jin dadi tace babu Abbah . Dama faÉ—a ma zanyi Mamy ta mareni akan ÆŠAN DAKO ko,kuma Abbah agabansa fa,Basai ya rainani ba ya raina ajina?takarasa tana sakin kuka mai sauti. Take muryarshi ta canza cikin byacin rai yace Mamy taku ta mare ki akan wani banza barni da ita anjima zamuyi magana yakashe wayar yana Huci. Lokaci guda kuma ya É—auki wayar shi Afusace ya kira Mamy da dai-dai lokacin ta fito daga toilet ta É—auro Alwallah. Mamaki ya kamata ganin wayar shi bayan yanzu suka gama waya. ÆŠauka tayi tare da yin sallama...... Amsawa yayi.cikin É“aci'n rai yace mi"Amnah ta miki da kika Mare ta akan wani ÆŠan Dako.. 5/18/22, 09:33 - MY MTN 2: D'AN DAKO🌹 MALLAKI🌹 UMMY AYSHA🌹 🅿ï¸5ï¸âƒ£&6ï¸âƒ£ "" Shuru tayi ba Tare da ta ta kaba. Cikin fushi yasake cewa "kina fa jina Fulani! Nasha faÉ—amiki ban yarda da abunda zai shafi É“acin ran Yarana ba, Akan wani sakarai zaki zauna ki Mari yarin yata ,in kika mata illah fa, mizakice ,Ki kiyaye daga yau ya kashe wayar... Shuru tayi ranta na Æ™una akan bin bayan rashin gaskiya da yayi. Sai da ta bada kamar ten mint kana ta É—auki wayar shi tamai Text kamar ''haka." ""Hubby Kayi hakuri banyi wani abu dan É“ata ranka ba Amma ni nason som Amnah halin da take ba mai kyau bane amatsayinta na ya mace, Amma in maganata tamaka zafi kayi hakuri ka yafeni kason fushinka masifane akaina, Har kullum fatan neman yarda Allah da taka nike saboda aljnnata na kasan tafin kafarka, Ina sonka sosai mijin marainiya(SUNAN DA TAKE KIRANSHI KENAN IN TAGA YANA CIKIN FUSHI SABODA YAKAN KARYA MISHI DA ZUCIYA) ta turamai. Cikin kankanan lokaci wayar shi ta shigo wayar ta. Murmushi ta saki tare da É—aukar tace'' Ka sirace Hubby.. Murmushi ya saki yace kiyi hakuri da abunda ya faru kinji sweety ,kinson bana iya control din kaina akan soyayya yarana, É—an allah ki daina cewa kedin nan marainiyace bayan kina dani ga kuma NENE .. Murmushi tayi mai sauti ta ce" shike nan yanda kace. Daganan sukai sallama ta ajiye wayar tare dayin Sallah. Bayan ta gama ta É—aga hannu sama tana kwararo Addu'a da hawaye jage- jage a fuskar ta wanda banson na minenen ba. AÉ“an garan Habu ÆŠan Dako kuwa cikin sauri yake tafiya baki É—aya kayanshi sun jike inda suka lafe jikinshi suka fiddo kyakyawan zatinshi na zama cikakken Namiji mai zarra. Bayyi wata tafiya ba ya Æ™araso kasuwa saboda dama sun kusa. Koda yazo kai tsaye Rumfar da Baba suke yashiga ya samesu tsaitsaye suna É—aure Buhun hunan hatsin su. Sallama ya musu suka amsa ya koma gefe tare da kwaso Damen kuÉ—in yaba Baba. Murmushi yayi yace "Habu ka kasa hakurin ruwa ya É—auke ka taho cikin su.? Kamar bazai magana ba kuma ya nisa cikin Æ™asa da murya yace" Motar ta lalace bata tashi shiyasa na barota acen . Ido Baba ya zaro cikin É“acin rai tare da cewa" Wai kai wane irin mutum ne, Haba ina dalili nan da G.R.A din amma sai da kamun asara É“atamun mota, To da ubanmi zan koma gida ?Habu kana da matsala wallahi badan Amanar kaba da tini na rabu da kai ,kai kason kaf É—in kasuwar nan babu wanda ya rufama asiri kamar ni É—an kwal uba har yau banson fuskar kaba na yarda dakai na sakar ma dukiyata na baka Amintatta motata da ba kowa nike ba 'ba , Amma saboda Ƙaton banzane kai sai da ka lakata to Wallahi sai kabiyani yaÆ™arasa yana neman yin kuka saboda tsananin son motar da yake... Duk da Habu na cikin É“acin rai hakan bai hana kwayar idonshi ta kasa fallasa yalwattace. Murmushin dake rufe da fuskar shi ba. Kallonshi Baba yayi baki asake yake karema idonshi kallo. Kuka yasaki yace "Habu ni kake ma dariya?Ni ka É—auka mahaukaci ka sacemun mota kuma kazo kace lalacewa tayi Habu ni???? Dakyal ya gimtse dariya dake tasomai yace. "Baba zaka iya bina muje kaga motar ka tana cikin aminci , Sai dai na É“alle murfi É—ays data batamun rai yakarasa hankali kwance cikin kuma tabbatar da gaskiya.... Salati Baba yasaki yana zama Æ™asa tare da É—ora hannunshi akai yasaki kuka mai karfi da yasanya matasan wajen kwashewa da dariya dan kowa yason yanda yakeji da motar shi da Abun hannushi ,Baya tauyema kowa hakki amma kuma bayasoAmishi asara kota kwabo, Mafarin ko tukin motar bai yarda kowa yayi ba sai shi sai ko Habu daya Amincemawa gashi kuma yau ya zalunce shi... Cikin shasheka da rikicin tsufa yace" Habu ka cuceni ka zalinceni bansonkaba na baka amana kayi ha'inci Allah yasakamun kuma ba zan bika ba kaje ka saidani babu ni babu kai har abada, Kaje na koreka kai Iro bishi ka karÉ“omun motana yafada yana nuna wani matashi. Dariya Iro yayi yace walkahi bazan bishi ba nima fa ban sonshi ba kawai kai dai ka aminta dashi ya zauna cikin mu. Duk kan maganar da suke Habu na jinsu kuma yason Gaskiya sukai su kadai suka aminta dashi batare da sun taÉ“a ganin fuskarshi ba yazama dole ya cire musu kokwanto a ransu! A'hankali yasanya hannun shi yafara warware Rawanin shi har ya gama tass. Wata irin zabura Baba yayi tare da Æ™oÆ™arin shiga cikin buhun geron dake gabanshi da bai wuce kwano goma ba. Iro da jikin shi ya É—auki rawa shida wasu samari guda biyu dake cikin shagon yakamo hannu Baba ya makalkale yana zare ido. Ihu Baba yasa tare da faÉ—in" DAGA TAIMAKO Ashe aljani muke tare da shi tsawon wata shidda, Wayyo ni Audodo naga ta kaina nashiga ukku na lalace Zai kasheni yau namai faÉ—a, Wayyo Allah na yakarasa cikin kyarma. Kyakyawar fuskar shi ya ÆŠago ya zubama su Baba ita tare da cewa" Ka kwantar da hankalinka Baba ni mutum ne bawai Aljani ba, Kuma ni ba Macuci bane dole tasani rufe fuskata bawai dan ra'ayina ba , Amma namaka alkawari daga yau bazaka sake ganin fuskana arufe ba amma kataimaka ka barni bakin aikina kai kaÉ—ai kamun halaccin ÆŠaukana.Sama da wata biyu ina cikin kasuwar nan ina yawo lungu da sako dan samun wanda zai taimakamun da aiki amma haka nike gama yawo na inkoma inda nafito bansamu komi ba, Saboda mutane naganin cewa ni wanine ko kuma kyan da Allah yamin yafi karfin ace ina neman Aiki DAKO, bayan Allah shike tsara halittar bawan shi ba wai bawa ke tsarama kanshi halitta ba , Shikenan sai ace gidan talakawa ba zasu samu yara masu kyau ba ko me? Halitta" Ubangiji ke yinta yayi Æaki acikin fari haka yayi fari acikin baÆ™i, Da haka ka daina mamaki inka amincemun zan zauna da kai ,in kuma baka amince ba kana ganin babu yarda zan fita in samu wani aikin.. Illahirin jikin Baba rawa yake jin yanda yake rattafo zance da halshen hausa dan ko makaho yaga Habu yason Æ™aryane yace shi bahaushene, Dan ko kaÉ—an shi bai kama da hausawa ba sai dai ko kasashi cikin jinsin Larabawa ko indiya wa.... Cikin Rawar murya yace Habu kaga dai da gaskiya na rikeka ko? To Dan Allah karka cutar dani ka kama gabanka Dan Allah nagode kuma kamun kwatance inda gidan yake a'ida kai masu kayansu in ÆŠakko motata. Murmushi ya saki mai ciwo tare da kwatan tabmusu cikin fahimta ya tashi ya musu bankwana da godiya akan Alkhairi da sukaimai na rikeshi tsawon kwanaki. Cikin sauri Baba yace bakomi bakomi jeka ga hakkinka ya bashi dubu biyar. Karba yayi tare da turawa aljihu yafita daga rumfa yafara takawo cikin ruwan da basu da niyyar tsayawa. GabaÆ™i É—aya'n masu shagunna kasuwar kallo shi ake wasu harda fitowa bakin rumfunan su suna leken baturen da yashigo kasuwa yana tafiya da kafa ganin irin cikakkiyar sumar shi tayi linkim da ruwa duk ta balbaje tayi masifar kyau. Sosai ya tsargu da irin kallon da ake binshi dashi hakan yasashi fara tafiya da sauri cike da sasarfa da kuma É“acin rai. Dan kallo na É—aya daga cikin abinda ya tsana arayuwar shi ya rasa ubanda yasa mutane ke kallonshi haka kamar sun samu Tv. Gabaki É—aya ya fita kasuwar yana fitowa ya tare keke napep ya shiga. Tinda yashiga napep din kaÉ—an kaÉ—an mai napep ya juyo ya kalleshi amma bai ce komi ba shikuma tinda yaga haka ya Æ™ara haÉ—e fuskarshi tamau. ''yallabai wace unguwa zan kaika? "Tudun wada.* Yabashi amsa agajarce. Kai tsaye suka nufi unguwar ahaka ya dinga nuna mishi har suka karaso wani dan matsakaicin gida da Æ™ofar ke saye. Sauka yayi ya bashi kuÉ—in tare da kutsa kai cikin gidan ya tura kyauran yashiga da sallama. Yason ruwan da ake bazai ba na ciki damar jiba kamar yanda bazai bashi damar jin ko an amsa ba. ÆŠan Æ™aramin gidan nasu yatsaya karema kallo da keda ÆŠakuna ukku biyu ajere sai daya dake kallon su sai dan karamin tsakar gida da baifi zaman mutum biyar ba sai toilet da karamin kiching. Ba laifi tsakar gidan nada kyau dan ashafe yake tas ga pent da yasha komi a'killace yake ba wasu hayaniya. Dayan É—akin da ke aware yayi saurin turawa tare da shiga ya maida kofar ya rufe tare da danna Sakata Babu komi.acikin É—akin sai wata tabarma da kuma karama katifa sai Alkur'ani sai wani truly babba guda É—aya .. Yana shiga yabi É—akin da kallo jin yanda yake ta busa kamshi tsintsiya da akasamai gashi agyare tsaf. Cikin natsuwa ya fara cire kayanshi tare da sasu awani babban boket dake bayan kyauran, Yana gamawa ya É—aura wani HARAMI akugunsa tare da É—aukar É—aya'n ya yafa akafaÉ—ar sa. Wani irin mahaukacin kyau yayi kamar wani Balarabe dake filin Arfa. Soso da sabulu ya É—auka tare da boket din dakayanshi ke ciki ya fita dasu . Ajiyesu yayi tare da faÉ—awa toilet din dake tsakar gidan É—an madaidaici ba laifi yana da kyau akwai shower da toilet sit da Æ™aramin pampo ciki. Wankan ya faÉ—a tare da murzar jikinshi sosai cikin lokaci ya fito tare da duÆ™awa ya wanke kayan daya cire tass ya shanyasu akan igiya. Alwallah ya É—aura saboda Al'adar shi ce zama da Alwallah yana gamawa ya nufi É—akin shi ya zaro wata tattausa brown din jallabiya dake linke mai gajeran hannu ya sanya. Wani irin mahaukacin kyau tamai gashi ta sake fito da Hasken farar fatar shi da kuma zatin shi da murzazza fatar da Allah yamai mai kama data ya'yan hutu. Kai tsaye ya fito tare da nufar É—akin dake kallon nashi ya tura guda da salllama a' bakin shi. Wata murya ce mai sanyi ta amsamai sallama tare da bashi izinin shigowa. Shiga yayi cikin É—akin yana takawa A'hankali kamar wanda ke tsoron Æ™asa. Wata farar matace dake hakim ce akan kujera hannuta rike da littafin Adduo'1i tana dubawa ,hukunta sanye da wani kace mai kyau da tsada. Kai ta ÆŠago ta kalleshi tare da fadin. SADEEQ Kadawo?Sannu ya aikin naku?Ina fata komi yana tafiya yanda ya dace? Da fatan dai bakajin yunwa ko? tamai tambayoyin duk ajere. Wani kyakyawan murmushi ya sakarmata tare da DuÆ™awa kasa ya ya dafa gwaiwar ta yace. "Ammina Barka da gida kin cikani da tambaya waccen/ kikeso in am'samiki? ya Æ™arasa yana turo baki cike da shagwaÉ“a . Murmushi Ammi tamai mai tsananin kama dashi ta ya mutsa sumar kanshi tace duka nike so ka amsamin,Saboda É—an jarumi ne ,kuma Nason in akwai wadda tafi wannan zaka amsamun. Hannunshi da Amnah ta rike ya É—aga yana murzawa A'hankali saboda yana tinanin tamai rauni, cikin RaÉ—aÉ—in da zuciyar shi kemai yace" Ammi nah komi lafiya klau Alhamdulillah , Sai dai inaso kisani Addu'a da bakin ki mai Albarka, wanda nike Æ™asan shi sama da wata shida yau ya koreni tinda yaga fuskana yana ganin kamar cutar su zanyi kuma na fahimtar dasu sun kasa ganewa yakarasa cikim.Æ™una rai da taune jajayen lips É—in shi. Shuru matar tayi batace komi ba sai kanta da ta sadda Æ™asa cikin kankanan lokaci ta fara kwallah masu tsananin zafi da Æ™una rai. Saurin ÆŠago kanshi yayi arikice tare da karasawa wajenta ya rike gwaiwarta illahurin jikinshi rawa yake idonshi yayi jawur cikin Æ™anana lokaci,Murya na rawa yace. "Ammi Dan girman Allah da manzon sa karkimun kuka na rokeki Ammi, ku kanki shine zai raunata zuviyata inkasa zama Namiji na ,Ke kinson waye É—anki Ammi akan ki zan iya É—auke komi amma banda ganin hawayen ki, Bani da mafita shiyasa na zaÉ“i faÉ—amiki saboda ko ba komi nason zakimun Addu'a kuma addu'arki gareni batada hijabi karbabiyane muyi hakuri mu fauwalama Allah,Domin shi ne zai kawo muna mafita, in kuma kina ganin in dingama fuskana penti kamin in fita sai inyi Ammi, Amma wallahi ni kaina abun na da nike naÉ—awa na matukar damuna Ammi kinson Ni banason zafi da abu mai nawie... Hawayenta ta share cike da tausayin yaron nata. Rungume shi tayi sosai tare da sakin wani mahaukacin kuka taf ara kiran shi da Sadeeq!Sadeeq!!Sadeeq!!! Munga rayuwa, Rayuwa tamuna juyin waina a Tanda, Sadeeq yanzu kaine wai.... Saurin rufemata baki yayi tare da gilgiza kanshi idonshi jawur yace" ki daina wata magana Ammi abunda ya wuce ya wuce munma rasa mahaifinmu mun hakura ballantana wata rayuwa cen ,karki damu Ammi nah ina Hamrat? Hawayenta ta share tare da nunamai inda wata kyakyawar yarinya ke kwance akan katifa da ba tafi shekara goma ba, Bacci take cikin jin DaÉ—i da kwanciyar hankali. Cikin natsuwa ya zare jikinshi daga na Ammi ya Æ™arasa wajen yarinya ya aza gwiwowayin shi Æ™asa tare da riko hannunta ya ÆŠan murza ahankali yana kallon fuskarta da ke tsananin kama da tashi... Kanta yafara shafawa A'hankali yanajin wani irin yanayi mai wuyar fassarawa game da yarinya,baison dalilin da yasa duk sadda zai kasance da yarinya ba yakejin wani tarin rauni dakuma matsanancin tausayin ta ,Æ™anÆ™anuwar yarinya ke cikin wannan rayuwa da suke ciki fatanshi ya nema dan ya wadatasu amma yau gashi an koreshi akan abunda bai kai ya kawo ba. Amma ya tabbata babu wadda ta jamai kamar wannan yarinya da som batada É—a'a da tarbiyya. Hannu shi ya kalla inda ta takemai har ya fashe gashi yayi jawur. Lips É—inshi ya Æ™ara taunewa akaro na ba a Dadi.. Mamy ta katsemai tinani da faÉ—in ga abincin ka nan kazo kaci. Cikin ladabi yace"Ammi minene kika dafa muna? Murmusi tayi tare da faÉ—in"Wakene sai shinkafa da salad harma da Æ™wai na siyo nasamaka takarasa tana Murmushi. Tausayi tabashi sosai ganin yanda take farin cikin ta Da É—aÉ—amai ta hanyar samai kwai duk da cikin shi a'cike yake amma bazaiso É“ata farin cikinta ba,Haka ya zuba kaÉ—an ya fasa kwan yaci yanata mata santi ita kuma tana tajin daÉ—i tare da mai kallon tausayi. Gidan su Amnah kuwa Baba Habu yaji anama gidan wani mahaukacin bugun da yasashi ÆŠakko Sanda da yar Æ™aramar wuka ta yanka albasa yafito tare da buÉ—e kyauren cikin kasada ba tare da ya tambaya ba ya lafe baya. Iro ne ya turo kyauran da karfi wanda yasashi matse Baba madu . Ihu ya saki tare da watsar da Sanda da wuka . Cikin furgici Iro ya juyo tare da fadiyn lafiya malam kake ihu munzo É—aukar mota ne muna tare da Bakanike ba masu Sata bane.. Ajiyar zuciya Baba Madu ya sauke tare da É—aukar waya Yace" Dama Hajiya tace in anzo É—aukar motar a'mata magana Bari in fad'ama ta. Tsaye sukayi suna jira har ya mata waya ya fad'amaka sai gashi tafiyo ita da Amal suna sanye da hijjob. Ƙarasawa tayi tana binsu da kallo ganin bataga buzun da ya kawomata kaya ba. Cikin dube -dube tace yo ina ÆŠAN DAKO kayan yake? Cikin matsananci ÆŠumi dake cin Iro ya fara magana" Ai Hajiya É“arnar da yama Baba mu ta mota yau shiyasa aka koreshi , Saboda Baba bayaso amai É“arna ga mota, sabodama yarda da shine yasa ya bashi to amma kinga harda marfi ya cire mata uwa uba kuma Baba baison fuskar shiba tsawon watanni shidda sai É—azu ya buÉ—emuna ita, Wallahi Hajiya abun mamaki ashe Bature ne shegen aka turoshi ya ga asirin Dukiyar Baba Dan yaje ya faÉ—ama yan uwanshi azo ayi KIDGWASHIN É—in Baba asaceshi, Aiko Baba ya korai tin É—azu ba mu son inda yake ba... Wata ityin dariya Amal ta kwashe da ita ganni yanda yaketa rattafa zance harda ambatar sunan kidnapper's da kidgwashin .. Sosai jiki Mamy yayi sanyi hakanan taji yaron ya shiga ranta cikin sauri tace" Toni yanzu wazai ida kawoman sauran kayana, Gashi gobe zanyi rabon nan, Kana dan Allah inda hali ni ku nemomanshi inason ganin shi . Iro Yace" Ga sauran kayanki nan cikin babbar mota wasu suzo mukama dan gaskiya ni ko Rabin buhu ban iya dakkowa, Saboda Hakarkarina ciwo suke banima da isasa lafiya. Cikin bacin rai "tace to ina wancen yake ku kiraman jarumin mana sai aturoman lusari irin ka mizakaman wannan ma ai haukane inane gidan su? Iro yace wallahi bansani ba Hajiya. Mamy tace "number wayar shi fa? Iro yace" eh ina da ita gatanan ya faÉ—a yana nuna mata wayar shi. Karba tayi ta kwafe awayar ta tare da kangawa a'kunne. Shi kuwa Habu dake É—akin Ammi suna fira yaji wayar shi na Ring. Ganin bakuwar number ne ke kiranshi hakan yasa ya É—auka tare dayin sallama. Daga É“angaran Mamy amsawa tayi cikin Dattaku tare da mai bayanin kanta akan tanaso É—an allah ta ÆŠaukeshi aiki duk wata zata biyashi dubu É—ari in ya amince zai dinga kulawa da wasu hidimar gidan sauran bayani dai in yazo yaji. Shuru yayi kan shi a'kasa saima wani irin É“acin rai dake tasomai akasan zuciya "Dubu dari yasake maimaitawa akan laɓɓanshi tare da taÉ“e bakinshi ya saki wani murmuahi Mai ciwo. Ammi dake jin duk abunda suke faÉ—a ta É—agami kai alamun ya amince.. Bazai iya tsallake umarnin taba duk da baisoba saboda Yarinya gidan amma bazai iya fad'amata ba. Cikin dusashiyar muryarshi yace" Na amince. Farin ciki sosai mamy taji inda ta hau zubamai godiya kamar yamata wani abu. Idon shi ya limshe batare da yace komi ba. Cikin É—oki tace to kazo yanzu.dan Allah akwai aikin da zakamun. Uhm yace yana kashe wayar shi. ÆŠago kan da zayyi yaga fuskar mahaifiyarshi ayalwace da farin ciki. Hakan yashi tsiramata ido ko kyaftawa bayayi aduniyar da suke ciki yana fatan yagan ya zama farin cikin iyayen shi, Yana so yaga mahaifiyar shi ta samu gata ta dalilin shi da yar Æ™anwar shi da baida kamar ta da ta taso cikin halin Rayuwa. Murmushi ya saki Dan Æ™aramata kwarin gwiwa, murmushin daya bayyana asalin kyanshi da kwarjinshi gawata siririyar wushirya data bayyana a tsakiyar fararan jerarun hakoran shi. Mamy ta É—aga hannu sama tace" Allah nagodemaka daka kawomana mafita cikin gaggawa, Allah ga bawanka ka saukaka mai wahalar da yakesha ubangiji ka jibanci lamurran mu. Ameen ya amsa yana mikewa ya tsaye yace "zanje in dawo. Mamy tace "Yanzu Sadeeq haka zaka dinga fita ko kuwa zaka dinga sanya Rawanin? Shuru yayi yana nazri saikuma yace" Bari in maida wayan cen kayan kawai inkuma sanya rawani inyaso gaba in naga sun aminta dani sai in daina sawa. Cikin Amincewa tamai fatan ALKHAIRI da kuma fatan nasara a'rayuwar shi. Ameen ya amsa yana juyowa ya shafi Fuskar Hamrat ya ficce. Sauri -sauri ya sanya kayan da basu gama bushewa ba ya naÉ—a Rawanin tare da fitowa yana duba lokaci yaga biyar da rabi, Cikin sauri yamata bankwana ya fita tare da tare Machine ya faÉ—amai inda zai kai shi. Tinda suk shigo layin yaga babba J5 yason aiken su aka kawo shiyasa ta nemeshi. Siririn tsaki ya saki tare da karasawa wajen ya sallami mai machine É—in. Ana ya gansu tsaitsaye yakarasa tare da cema Mamy" Barka da marece Hajiya. Tace yawwa Habu ko kaifa, Naji daÉ—in zuwanka yanzu ga kaya nan ashigo dasu asasu inda yan uwansu suke zuwa gobe za afara rabasu zansa akawoma mota. Kai ya jinjina tare da cema Iro daya saki baki yana kallon shi "kashigo da motar ciki. Bakaniken yace ai ta garejin muce bari ashigo da ita. Wangale musu get din Habu yayi cikin kuzari suka shigo da motar ya nunamus inda zayyi parking dinta kusa da D'AKIN. Anan sukayi kam cikin jarumta ya fara kwasar kayan akafaÄar shi yana shiga dasu. Cikakken mint talatin baiba ya tsauna su cikin Äakin. Iro ya saki ihu tare da fad'in Hokai jarumi Jarunaj wallahi dole Bab yayi misir (Missing)dinka saboda samun jarumi yanzu kamarka babban aikine ,wallahi Allah yasa inyi K'arfi irin naka. Baice komi ba haka kuma bai amsa ba. Ita kanta Amal ya masifar burgeta dan ta yaba da zaÉ“en Mamy tasu da tace tanaso yazamana mai aikin gidan su... Bayan sun gama mamy ta cema su Iro zasu iya tafiya ta gode. Bankwana sukai sukaja motacin sukayi gaba .. Wata kyakyawar Bukka da akayita saboda hutawa tace ya biyota. Binta yayi har zuwa wajen inda ta samu wuri ta zauna shikuma yayi tsaye kanshi a sunkuye... "Ina son ganin fuskarka Habu saboda inson da wa nike zaune, in'yaso daga yau saika cigaba da lullube abunka ba damuwata bace mamy tafad'a cikin natsuwa... Baitsaya gardama ba ko wani fargaba a'hankali ya since rawani.. Tin kamin yagama amal ta mike tsaye jikinta na rawa tana nunashi da yatsa...... 5/18/22, 09:33 - MY MTN 2: D'AN DAKO 🌹 MALLAKI 🌹 UMMY AYSHA 🌹 🅿ï¸7ï¸âƒ£&8ï¸âƒ£ """Fitunannu idon shi ya watsamata tare da kauda kanshi gefe yana sakin Æ™aramin tsaki. Cikin tsanani ruÉ—u Amal tace" da gaske kake kai ÆŠan Dako ne? Kai ya jin-jinamata batare da ya kalle ta ba. Ita kanta Mamy saida taji zuciyar ta ta buga da karfi ganin kyakyawan saurayi kamar shi wanda som babu alamun da suka nuna yayi kama da ÆŠan Dako , Dan ko kayan sa fess suke babu wata lalacewa babu kuma faci jiki... Amal zatai magana Mamy tace zauna ya isa haka kaima zaka iya zama. Cikin girmamawa Yace" Aa Hajiya basai na zaunaba ina sauraran ki dai... Mamy tace shikenan. "Dama inaso gobe zansa akawoma mota zan haÉ—aka dasu Amal ku kaimun kaya cen gidan mahaifiyata, Zaka tsaya ta lissafamaka duk wanda za'aba ,zaka É—auka ka kaima mutane, Bayan angama inaso ka dawo gidan nan da zama kana É—an kama ma Baba Madu aikin bude get din cen , Naga ya fara manyanta, Sannan yan aike -aike da suka dace zaka dinga zuwa kana muna, Wannan shine kawai aikin ka, inaso ka haÉ—o kayan ka ka dawo gidan nan ,ga É—aki cen daka tsauna kaya idan ka kwashe zaka sanya naka a'ciki, Ina fatan tsarin yamaka haka? "Bai manba Hajiya. Ya bata amasa cikin Natsuwa.. Kallon mamaki suke binshi dashi ganin irin gatan da akaimai amma babu wata shakka yace tsarin baimai ba. "Komi yasa kace haka "? Mamy ta furta. Saboda ina da mahaifiya da Æ™anwa da nine jigonsu, Ni suke gani suji daÉ—i, Ni mike zama muyi fira dasu in maye musu kewar mahafina! Wannan shine kawai. Murmushi Mamy ta saki tare da cewa indai wannan ne karka damu zaka iya maidosu gidan nan da rayuwa suyi zaman su ,Nidai na aminta dakai, Bana tinani wata cutarwa daga gareka, In ma mahaifiyar taka zata iya sai ta É—an dinga kamamun wasu aikace -aikacen nan part É—ina. Wani kallo ya mata da yasata shan jinin jikinta, ta rasa miyasa take shakka yaron da baifi shekara 30 ko Da 31 ba, Yana masifar yimata kwarjini tana jinshi kamar É—an da ta haifa.. Cikin fushin da yatasomai murya a'kausashe yace mahifiyata bazatai aiki ko inaba,In hakane haihuwata batai mata rana ba kenan,Ayanzu data ajiye kamata tafi bukatar hutawa fiye da da,in dai har zanfita ta fita to menen ribar haihuwar tawa ma Hajiya? Ina son Ammi na bana fatan ace wai tayi wani aikin wahala Dan zata samu abunda zataci,Nidai da nike namiji Zan iya iya aikin karfi wanda yafi Dako wahala dan sama mata farin ciki, In zaki amince ma zuwana karfe 8 na safe in tafi bayan isha to shikenan, In kuma bazaki yarda ba to gaskiya asamu wani saboda nima inaso in samu lokacin da zan tattauna da mahaifiyata inji matsalarta data Ƙanwata data ragemun,Dan nine garkuwan su . Ya faÉ—a cikin gaskiyar shi tare da tsuke baki dan ya daÉ—e bayyi irin wannan dogon sharhin da wani ba sai da mahaifiyar shi ko sst shi.... "KAIFI ÆŠAYA"Mamy ta furta ,Dan ta fahimci yana da tsatstsauran ra'ayi sosai.. Tace shikenan na amince ma hakan, Ina fatan ka rike amana shiga da ficen gidan nan .sannan miyasa kake son rufe fuska? Ko buzayene ku.. KafaÉ—ar shi ya É—aga. Tare da faÉ—in ko É—aya, kawai Bakowa ke yarda dani ba idan yaga fuskana shiyasa,Suna ganin kamar zanzama É—an leken Ashirin su.. Amal da ta ke binshi da ido cike da burgewa tace. "Ai kana da kyau sosai Wallahi kamafi Aunty Amnah kyau ba kaÉ—an ba Shiyasa ake kin yarda.. Kallonta yayi tare da kauda kanshi gefe. Mamy tace sunan ka Habu ko? Yalwatacciyar sumar shi ya murza tare da cewa. "Sadeeq ne sunana, Tsohon da nike aiki dashi yasamun Habu, Saboda bazai iya faÉ—in sadeeq ba. Mamy tace shikenan daga yau zamuna kiran ka Sadeeq dan yafi daÉ—i. Amal tace yamafi dacewa dashi. Wayar shi ya zaro tare da cewa zan je Sallah Hajiya.. Mamy tace akwai masallaci a'kofar gidan nan kaje ka dawo zan baka sako. Yace ok tare da nufar wajen mai gadi ya gaisheshi amutunce tare da fita daga gidan . Harya fara tafiya ya juyo tare da cewa Baba ba zaka Sallah bane? Baba Habu ya rike baki yace "Yaro Hajiya Amnah tazo bana nan aini nason dubu hamsin din da suke bani zatabi Ruwa, Anan nike kayana.. Cikin Æ™anÆ™antar da ido yace akan duniya Baba da shekarunka zakayi gudun zuwa masallaci dan kar ka É“atama wata rai?Wai miyasa mutane ke É—aukar raini akan wasu yan canji da ake basu,Danmi zaka saÉ“ama mahalicci ka Akan abokin halittar ka,Baba kasamu kwaÉ—o kasanya kawuce muje sallah ,Sallah cikin jam'i tafi lada, Baba kaji tsoron Allah kaida ka fara manyanta ma ... Jikin Baba yayi lakwas kamar an'watsama kaza gishiri. Yace shikenan yaro bari in rufe.mutafi Nagode da tinatarar wa. Ido Sadeeq ya lumshe batare da yacekomi ba. Baba ya ÆŠakko kwado ya dannama gidan tare da faÉ—in muje. Fita sukai suna fita saiga masallacin jere da gidan. Sadeeq yace kenan ma masallacin na gidan ne kawai fita ne bakayi. Baba Madu Yace_ Wallahi" Yaro ina tsananin tsoron Yarin ya abun har mamaki yake ba'n, Dan Akwai Hannatu jikata na tabbata ta girmeta, sai dai in nayi duba da kasansu nike sai inga wajibine in mata biyayya. Hanci Sadeeq ya hura tare da cika baki shi da iska, Tura hannayen shi yayi cikin aljihu tare da fadin muje. Shiga sukai sukai sallah ana sallamewa Baba yafara kyarma tashi. Sadeeq ya kamo hannushi Yace" Karka tashi mana Baba, Ya kamata ka nemi gafara Allah, kayi karatu koda aya gomane, in san samune ma katsaya ayi Isha kana ka koma,Saboda Lahiraka tafi duniyar ka faÉ—i.. Baba Madu ya koma ya zauna dan yasha alwashin gyara goben shi kodan samun rabauta, kwara yasama ranshi zamanshi da Æ™orar shi duk Allah ne zai tsara su acikin Æ™undun Æ™addara shi. Suna zaune suna lazumi har akayi isha kana suka fito. Suna fitowa suka koma gidan ya buÉ—e masu suka shiga su duka suka zauna akan bencin dake wajen. Baba ya'ce" yaro ya sunan ka. "Sadeeq" ya bashi amsa atakaice tare da danna ma Mamy kira yace" na dawo. Amal ce ta fito da kayan abinci niki -niki tayo wajensu tarr da cewa "Yah Sadeeq ga abinci inji Mamy. Da sauri ya kalleta yana mamakin sunan da ta kirashi da shi ''Yayah'' yasake mai maitawa tare da taÉ“e baki . Atakaice yace ki mayar nako shi Alhamdulillah, Sai dai ko Baba amma ni kamin in fito naci Abinci wajen Ammi nah.. Cikin langwabar da kai a:lamun bataji daÉ—in yanda yamata ba tace. "Dan Allah kaci wallahi saboda kai na girkashi fa Takarasa cikin yanayin shagwaÉ“a... Kasa yayi da kanshi akaro na farko yace. "Amalll banajin yunwa nace ki mayar ba. Wani sanyi dadi ya ziyarce ta jin yanda yakira sunan ta da wani kala jan baki da bata taba jiba, Ita batamason sunan ta yana da daÉ—i ba sai yau da tajishi abakin ÆŠAN DAKO Gidan su. Baba dake kallonsu Murmushi yasaki ba tare da yace komi.ba. Amal tace shikenan. Mamy tace kashiga ciki. Ta faÉ—a tana ajiye tiren wa Baba madu. Tashi yayi yace "muje. Tafiya ta fara yana biye da ita har suka Æ™araso palon da Sallama, Inda suka iske Mamy zaune cikin kwalliya . Cikin yan second ni ya karema palon kallo tare da samin kujera dake nesa da ita kaÉ—an ya zauna. Kai ta ÆŠago ta kalleshi tare da sakin murmushi dan gabatar shi na burgeta da alama bayason raini,Koda kasancewar shi talakka Annabi bai yarda mutunci da Allah yayi Mashi ba ya zube, Da wanine ta tabbata zai zauna akasan kujera in yaga tana sama. Barka da dare yakatse mata tinaninta tare da TurÉ“une fuska dan bayasan acika kallon shi ana nazari abun na sosa ranshi... Tace yawwa "Sadeeq Zaka iya tafiya yanzu Baba sai ya dinga kwana gobe da safe zakazo kamar yanda kacemun karfe takwas . Yace baki da matsala indai wannan ne insha Allah. Mikewa tayi sai gata da wasu ledoji manya guda biyu da ta zuba Kaji, kifi ,Naman rago. Cikin É—aya'n kuma kayan fruit ne ta zuba akai tace ka kaima Ammin ka ina gaisheta sosai wannan kuma albashin kane na farko ta Damkamai dubu dari da hamsin. Ledar ya karaba tare da cewa Allah ya Æ™ara arziki Nagode sosai, Amma albashin dubu dari kikace naga nan kuma akwai karin hamsin?. Murmushi tayi tace'' saboda zaka sha wahala sosai ne wajan raba kayan abinci shiyasa namaka Æ™ari, Kuma akwai bukatar kasai kaya masu kyau dan ni ba matsayin bawa nikeson rikeka agidan nan ba inajinka ne kamar kanena, Kana ga Amanar Amnah da Amal nan ka kula da lafiyansu da kuma tarbiyyan su, Mahaifin du bai kasance ma'aboci zaman gida ba,inaso katayani saka ido ga tarbiyya yarana saboda shi namiki jigone agida. Kanshi ya jinjina cike da tsare gida da kamun kai yace "shike nan na amince , Allah ya sadamu da alkhairi natafi nagode Allah ya amfana. Sosai taji dadi dan harga Allah ta aminta dashi tace" Nagode Sadeeq Nima. Yace ba komi tare da mikewa. Amal tace yah sadeeq agaida Ammi da kanwar mu. Murmushin gefen baki yasaki tare da furta" insha Allah yasa kai ya ficce. Yana fitowa yaga Baba madu nata kwasar gara tare da Æ™ulla wani ga leda. Sallama yamai ya wuce. Fitar shi bada jimawa ba Amnah ta fito cikin wasu mahaukatan riga da wando da suka masifar yinata kyau kasancewar su read color, kanta ko É—an kwali babu sai parking din da tayi tsakiya ta tufkeshi da read din bant ta sakeshi yana Lilo,,Kunnata toshe da read din Bluetooth don da ya haska farar fatar ta. Bakinta ta turo tare da kallon Mamy da som hankalinta bai kanta. Cikin shagwaba tace "Mamy ina Namana ? Kallonta mamyy tayi batare da race komi.ba sai tashi datayi ta haye sama tana latsa waya dan tana so taga Amnah ta gyara halin ta. Amal ta kallah tana lumshe ido kamar mai jin Bacci. Da hannu Amal É—in ta mata nuni dakan dinning da aka ajiyemata . Cikin natsuwar tafiyar mai jan hankali ta mike tana juya.manyan hips dinta wanda wasu suke tinanin tsabar gayune kesata haka , Amma som ba hakaba ne yanayin tane haka. Fridge ta Bud'a ta Äauki Hollondia yoghurt tare da karasa wa wajen dining ta zauna. Naman ta zuba kaÄan Ta tsakure shi ta zuba yoghurt din taci tare da mikewa tsaye ta nufi hanyar d'akin ta. Kallo Amal ta bita dashi tare da cewa "Aunty Amnah wai kinga wannan mutumin ashe mahaukacin kyau ne dashi, Wallahi kamar Balarabe, Allah kika ganshi sai ya ruÉ—aki, bakiji yanda naji ina son shi ba, kema Wallahi inkin ganshi zakice kina son yazama YaÆ´an ki, nidai daga yau yazama Yayana kema... "Ya isa!!! Takatseta cikin daka tsawa. Ke in'banda kina wawiya talakka har kyaune dashi, shashasha, insoshi!insoshi kike faÉ—a!! To bakin banzanki ya faÉ—a miki, Amma nida wancen talakkan sai na azabatar da shi wallahi, ai naji duk kullin da kukai na kawoshi gidan nan, kuma hakan yamun daÉ—i, kana da kanshi da kafarshi zai bar gidan nan, Tinda har yayi sanadin da aka mare ni ni yar gidan .mtsss ta watsama Amal yawu ta haye sama.. Kukan takaici Amal din tasa tare da diddire kafa tace Wallahi nidai ina sonshi wallahi.. Rai aÉ“ace amal ta haye sama itama.. Æangaran sadeeq kuwa yana fita yasamu acaÉ“a ya hau tare d kaishi unguwar su da shatara ta Arziki ,Sosai ya yaba da karramawar matar dakuma halaccinta gareshi. Yana shiga gida da sallama ya iske Ammi da Hamrat waje sun shinfiÉ—a Tabarma suna shan iska , ga kuma karamar fitila data haska gidan maici da battery. Oyoyo Babyyyy.. Hamrat tace cikin ihu tare dayo wajenshi ta faÉ—a kanshi. Da sauri ya ajiye ledojin hannunshi tare da cewa oyoyo Baby'n Babyyyyy. ya faÉ—a yana rungumeta tare da daygata sama yana juyi da ita cikin tsanain farin ciki. Dariya suke sosai cike da shauki . Ammi tace nishikenan bakwa tani ko? Sauke Hamrat yai tare da sumbatar hannunta ita kuma ta sumbaci goshin shi. Tare da cemai i miss you so much Baby. Yave.mee too Baby'n Baby. Tashi tayi tsaye tayi cikin jindaÉ—i ta nufi É—akinsu tana ta dan tsalle tsallanta da rigar jikinta mai kyau sosai. Kallo ya bita dashi har ta shiga kana ya maido hankalinshi ga Ammi Ya gaisheta yana sakin murmushi.. Hararashi tayi tare da cewa bana amsawa sadeeq kaga Hamrat mantawa kake dani dan haka nayi fushi.. Kyakkyawa sumar shi ya turamata tare da faÉ—in" kaina bisa wuya Ammi nah, Lefa ta daban ce, kinson dole muyi kewar juna yau banganta da rana ba. Sumarshi ta shafa mai tsananin taushi da yawa tace hakane "ina jin daÉ—in AlaÆ™arku Allah ya dora da zumuncin ku har jikoki. Ameen-Ameen ya amsa tare da janye ledojin da yazo dasu wanda baiso ko na miye ba . "yace gashi hajiya tace akawo maki kana ya kwashe komi yanda sukai ya fad'amata.. Hamrat ta.fito tare da wani dan cup mai kyau ta bude Randarsu mai sanyi ta ÆŠebomai ruwa tace Baby gashi kasha ruwa. ƘarÉ“a yayi yace yawwa Baby'n Baby Allah yabar k'auna. Idonta ta juyamai masu kama da nashi "tace Amin tana bashi hannu suka kashe .. Yana gama shan ruwan ya juyo ya fuskanci Ammi tare da buÉ—e ledojin yace "Ammi kinga ashe Nama ne ma bansani ba ga kuma fruit. Godiya da Addu'a tashiga yima Allah da kuma Mamy data kyautata musu yau daya taÉ“asu abunda suka kwana biyu basu ciba. Kudin da aka bashi ya fiddo ya gwadamata tare da faÉ—in Mamy inaga silar warakamu tazo yakamata muyi amfani da damar muyi.abunda mike buÆ™ata inaga zansiyo muna fridge D'an madai daici dan mudinga samun abun sanyi,kinga Zafi ake sai kuma in siyo kayan abinci masu yawa a ajiye in sai miki gas ki huta kunna icce ko Garwashi. Idonta dake cike da hawaye ta ÆŠago tace hakan yayi sadeeq ubangiji Allah yamaka albarka yabaka lada yasa kagama da duniya lafiya. Ameen ya amsa tare dashafar kan Hamrat yace 'Baby zanje indawo mizan siyo miki? Cikin jin dadi tace ka siyomun Baru(Tantabara) Sai ka siyomun sweet mai daÉ—i... Dariya ya saki daba koda yaushe yake yin taba yace insha Allah" wai miyasa kikeson Tantabara ne? Murmusi tayi tare da cewa Baby ya sayyadi ke cemuna muna karatu in mundawo gida? Sai muce "eh." Sai yace muzama masu cika Al'kawari muyi halin tantabaru, Dansu akwai amana da cika Al'kawari, wanan dalilin ne yasa nike sonta Baby. Kanta yashafa yace angama zan siyo miki Amnah sai gobe insha Allah Ihu ta saki tare da rungumeshi. Fita yayi sai gashi da kayan masu yawa ya siyomusu fridge madaidaici buhun shinkafa taliya.maca kus- kus semo da yan kaya masu sauki ya siyoma kanshi. Farin ciki sosai ya bayyana ga Ammi tai tamai Addu'a tare dacewa naga mutun cin matar nan Sadeeq, Daka bari nima na dinga mata aikin in tana da bukatar hakan.. Take fara'a fuskarshi ta Äauke yace ""Ammi na ke zakiyi aiki da raina da lafiyana zan barki kihi aikatau? hmm Allah ya kiyaye kima daina wannan tinanin keda akaima... Ya isa sadeeq jekayi wanka ka huta. ta katseshi da hanzari akan magana da yakeson yi.. Shuru yayi tare da leka ÆŠakin ta ya ajiyema Hamrat kayan da ya siyo mata gefen ta ganin tayi bacci. Kai tsaye yashige nashi É—akin bayan ya fito ya shirya cikin wasu kayan bacci farare sol masu tsanani taushi da kyau. Babbar jikkashi ya bude tare da fiddo wata computer mai kyau ya fara dudduba wasu sakwanni na abubuwa da sauri. Tare da É—aga wayar shi yafara kofe wasu number da banson na minene ba. Yana gamawa yasaki wani mahaukacin tsaki tare da jinjina kai. Take jijiyar kan shi ta mimmike idon shi ya canza launi. Cikin sautin dake bayyana bacin rai yace Rana DUBU TA BARAWO DAYA TAK TA MAI KAYA... 5/18/22, 09:33 - MY MTN 2: D'AN DAKO 🌹 MALLAKI 🌹 UMMY AYSHA 🌹 9ï¸âƒ£&🔟 ""Cikin yanayin na fushi ya rintse hannushi tare da kaima jikka dake kusa dashi duka. Saida ya kwashe sama da awa biyu kana ya jonata charge yatashi yayi addu'a ya kwanta. Bacci ya Æ™oso ya zomai amman yakasayi ,saboda tinanin inda rayuwa tamayar dashi ayau daya ya tashi daga ÆŠan Dako ya koma mai gadi, koda yake bazaice hakan ba tinda cenma DAK'ON zai dinga musu. Tsaki ya saki yana taune jajayen lips É—in shi. Ahanka bacci ya yi nasara kwashe shi. Washe gari da asuba ya tashi tare da walwatsa ruwa dan garin akwai zafi, Yana fitowa yayi shiri cikin farar tattausa jallabiya data mishi kyau sosai ta fiddo zatin shi kamar wani balarabe.. Masallaci yaje yayi Sallah. Bai shigo gidan ba sai Bakwai, yana shigowa ya iske Ammi kiching tana mishi breakfast dan tason da wuri zai fita . Suna gaisawa ya shige dÉ—akin shi tare da cire kayan jikinshi ya É—aura haramin shi yafito yayi wanka. Yana fitowa yazo yashafa mai tare da fesa tiraren E collection mai daÉ—in kam shi da sanyaya rai. Wasu riga da wandone Black masu ratsin white ya É—akko ya sakama jikinshi tare da murza turare a'hannun shi yasake mulke kan shi take wani daddaÉ—an kamshi ya fara tashi daga É—akin. Tattasau sumar shi ya gyara tare da É—aukar wata Black p-cap yasama kanshi ya É—auki bakin maks ya mannama dogon hancin shi. Madubi ya kalla tare da lumshe ido dan shi kan shi ya yaba da shigar tashi duk da duka kayan jikin nashi ko 5k basu kai ba amma yayi masifar kyan da wanda yakashe 100k bazai yi kwatankwacin kyan shi ba, dan kyau ajinin shi yake. Da sauri ya fito yana kallon agwogo ganin yaci four mint acikin awa É—aya kuma baya fatan karya alkawarin dan ba fatan shi bane kuma baya cikin tsarin shi. Ammi ya iske zaune tana fiffita mishi tea'n data haÉ—a mai . Zama yayi ya Æ™arÉ“i tea yasha tare da É“allar bread da kwan data soyamai kaÉ—an yakai baki. KaÉ—an yaci ya aje sai tea daya shanye. Kallan shi tayi cikin fuskar damuwa tace wai miyasa sadeeq bakason cin abinci ne?kana aikin karfi kana wahala zafi inuwa Æ™una amma baka da lokacin cikin ka miyasa? Takarasa cikin raunin murya. Kallon ta yayi sosai yana murmushi tare da riko hannunta yace "karki damu Ammi nah kinson duk sadda ka cika cikin ka lokacin rauni da kasala ke kawoma ziyara . Nikuma bana fatan abunda zai dakushemun kuzarina da rashin cika muradina dare da Rana . Shiyasa nama kaina wannan sabon kuma yabi jikina . Amma Ammi kidaina damuwa dan ni ba yaro bane duk sadda naji yunwa zan nemi abinda zanci na barki lfy . Tsororo tayi tana kallon shi dan tabbas maganar shi akwai kamshin gaskiya. Addu'a ta mishi dafatan nasara kana ya shiga É—akin ta ya shafa kan Hamrat kana ya ficce da sauri. Takwas saura minti biyu ya isa kofar tafkeken get din gidansu Amnah. Bayan ya shiga sun gaisa da baba madu ya É—aga waya yama Mamy waya akan ya iso. Dadi taji sosai tare da faÉ—in "akwai sabuwar mota na nan compound ka karbi key wajen Baba Madu ka fara shirya kayan aciki kamun su Amnah su gama shiri saiku wuce. To yace tare da latse wayar. Key ya Æ™arba tare da nufar motar ya jata har wajen kofar É—akin kana yafara sungumo kayan cikin tsantsar jarumta yana shiryawa. Cikin kankanan lokaci ya take bayan motar taf da kaya,Kana yakoma wajen Baba madu yana sauke ajiyar zuciya dan cikin kwanakin'nan da yayi aiki da yawa sai yaji Æ™asan zuciyar shi namai masifar ciwo da bayan shi,Daure wa kawai yake dan baya fatan yaba gangar jikinshi muhallin hutu har sai ranar da burun shi ya cika. Kimanin awa É—aya suna zaune saiga Amal cikin shirinta na atamfa tasanya hijjob madaidaiciya tafito da Æ™aton basket a'hannunta shake da kayayyaki. Kai tsaye ta iso wajensu tana doka murmushi tare da ajiye kayan gaban shi ta tsugunna tana dafe kumatunta ta zubamai ido cikin narkakka murya tace "yah Sadeeq ina kwana, kana lafiya yasu Ammi da sst Hamrat.? Alhamdulillah ya bata amsa agajarce yana kallon gefe. Tace yawwa" Ammi tace ga breakfast ka farayi kamin Aunty Amnah ta gama shiri. "Yace ayyah kimayar kice ngd naci agida kamin inzo Naci. Kallan shi tayi tana kwabe fuska tare da faÉ—in "Dan Allah kaci mana miyasa duk sadda zamu baka abu bakaci ko kana tinanin zamu cutar da kaine ? Murmushi ya saki da bai shiryaba yayi ganin yanda tayi magana kamar zatai kuka . Yace "A'a ko É—aya kawai naci abinci agida Amma bani ruwa. Ruwa ya Æ™arba yasha kaÉ—an ya rike sauran ahannun shi. Baba madu ta turama sauran takoma ciki cikin rashin jin DaÉ—i. Saida suka shafe kusan awa É—aya sannan suka fito su duka. Mamy Amnah Amal. Kai tsaye wajen motar su Amnah ta nufa yayin da Amal da Mamy sukayo wajen shi suka sake gaisawa tare da fad'amai yanda takeso ayi tsarin abun dan washe gari ake sanya ran ganin wata. Kai ya jinjina tare da mikewa cikin kuzari ya isa ga motar ya ajiye ruwan tare da shiga ya zauna yana lumshe ido tare da wasa da hannunshi daya rike styarin ... Tada motar yayi dai-dai lokacin da Amnah ma ta tada tata tayo hanyar get. Shima hanyar get É—in ya nufo tare da kashe motar ya fito ya tura get É—in da hannu daya kan ya koma mota yadosi get din. Sosai Amnah ta sheko da gudu asan ta samu ta rigashi fita. Cikin kwarewa ya kaucema motar ta tare da fita yayi parking ya fito . Cikin bacin rai ta fito tana sanye da maroum din Abaya mai duwatsu kota ina tasha kwalliya data mata mugun kyau. Wajenshi ta nufo cikin gadara tana zuba yauki kamar sabuwar Æ™ubewa "Uban waye ubanka dazan fito kafito bazaka jurema fitana ba kamin kafita É—an talakawa marar tarbiyya? miye ai'kinka inba takemun bayaba ka rikemun jikka amatsayinka na ÆŠan Dako uhum nace waye ubanka? Wata firgitacciyar tsawa ya dakamata data sata daka tsalle ta koma gefe. Afusace ya zare hular kanshi kyakyawan gashin shi ya bazu tare da cizge maks din da yasama fuskar shi ya cilla gefe. Jajayen idanuwan shi da suka cika da É“acin rai ya dago ya zubamata Tare da nuna kanshi da yatsa cikin É“arin da jikin shi keyi yace. " Ni tsaran kine?ke wace irin wawiyar yarin yace marar hankali da tinani,Natabbat nabaki shekara goma a haihuwa,Saboda bakida wadatacciyar tarbiyya ko?ko Dan kinganni agidanku akacemiki kisamu damar wulakantani!To bazan É—aukaba, bazan jureba, tinjiya naga take taken nothing kanki akwance suke. To Wallahi ni Sadeeq S Sadeeq zan iya saita ki yanzunnan kimatsa kibani waje kamin inmiki abunda baki taÉ“a tinani ba dakikiya kawai ko AnfaÉ—amiki kyauta za'asallameni ba sai nayi aikiba, bana tinanin cewa hakana za'kuna É—aukar kuÉ—i kubani kyauta, Yajarasa yana sakin siririn tsaki tare da kifa hularshi ya fita cikin kasaita da cikar zati. Duk abunda ya faru akan idon Mamy da Amal Sosai abunda yayi ya burge mamy ganin irin furgici da tashin hankali da tsawar shi kadai ya jefa Amnah. Murmushi tasaki batare da tace komi ba sai ciki data koma waya makale akunnanta cikin farin ciki taci gaba da magana da Æ™awar ta Hajiya Turai. Amal takarasa wajenta cikin rashin jin daÉ—in abunda aka mata ta kama hannunta tace. Auntu Amnah kiyi hakuri muje kinji ko. Fuzge hannuta tayi idanuwanta sun cika da kwallah amma taki basu damar zuba dan kar ya gani ya rainata. Cikin rawar murya tace "agaban Mamy akaiman haka amma tashige ciki tana doka murmushi, D'an Dako yafi dan gida, nida gidan ubana, anya mamy na sona, kodai ba Mamy ta haifeni ba,? TaÆ™arasa tana yarfe hannu tare da kutsa kanta cikin mota ta kifa kanta da styari tana sauke ajiyar zuciya, ga mamy ta mata shamaki da kai Æ™arartaa wajen Abban ta,kuma tason babu wanda zai goyi bayan ta sai shi. Amma tayi alkawari koyama wannan baÆ™auyen hankali. Tada motar tayi tawani fizgeta da Æ™arfi tare da fita daga gidan. Tsaki yaja tare da taÉ“e baki ya kunna tashi yabi bayansu. Duk yanda take tsula gudu bisa titin dan tabashi wahala ta hanyar bacce mai amma abun ya gagara. Dan yanunamata namiji namiji ne mace kuma macace. Tafiya mai É—an tazara suka karaso unguwar su Nene. Unguwace dake da yawan mutane mabuÆ™ata da almajirai, Dan ta tara makarantun allo da dama . Parking tayi awani gida mai babban get black da yasha fentin lemon green Hon tayi wani saurayi hannushi rike da Radio ya keto da gudu ya É—an buÉ—e yana faÉ—in. "Yau sain tsulamaku bulalai yan iska masu kawunan Agwagwa shikenan baku barina in huta masu gida basuce in buÉ—eba saiku yan banza duk ruwan da aka fidda muku waje amma saikun karbi na cikin gida saboda hassada, Nace uwaku ya saki daÆ™uwa dai -dai lokacin da idon shi ya sauka kan na Amnah data tsareshi da lumsassun idonta fuska a tsuke.. Salati ya saki yana yankowa da gudu ya zube Æ™asa tare da cewa "Dan Allah kiyi hakuri Hajiya Amuna wallahi banyi tinanin ke bace naga jiya kikazo. Afusace tace zaka buÉ—emun get kosai nabi ta bisa bakaken yatsunka masu kama dana gizo- gizo na wuce?.. Hannunshi ya kalla kana ya tashi da gudu yashiga ya bud'É—e get É—in yana cillama bayan motar harara tare da "fadin wannan mai kama da manja Allah yamamu maganinki fitinaniya ga kyau kamar zoben zinari amma kafurar zuciya gareta kamar ta haÉ—a iri da sheÉ—an.. Yana kokarin rufewa sadeeq ya dallo tashi ciki. Wait !wait !!! ya ciga da cewa amm ko tsayawa baiba saidai ya samu wuri kusa da motar Amnah yayi parkin tare da zamanshi yana latsa wayarshi hankali kwance batare da yace komi ba. Su Amnah Fita sukayi suka faÉ—a cikin gidan inda Suka iske wata dattijuwa da a'Æ™alla takai shekaru sittin da biyar tanata faÉ—a da mai lallaÉ“e mata kai. "Haba zulfa sai shafar mun kai kike kamar kwartuwa nace ko dad'i kikeji?Dan masifa kingama kitsemun tin É—azu amma bazaki barni inje inyi walha ba dan dai kisa inmakara ko? Miyasa wai baki da imani da tausayin wanda ya kwana biyu. Mai kitson tayi murmushi tace" Haba Hajiya Nene tattare miki nike dan karya dameki kin tsufa amma har yanzu kanki masifar yawa ga tsantsi dole sai an tufkeshi gudun karya warware. Baki ta murguÉ—a tace tubarkallah kali kuss mai bakin banza sala kija ma'askin dare yamun aski tinda kincikani da baki, ni sakeni in sammaki nama dan in banbaki ba nason ba ci kike ba kuma karshenta bala'in bakinki kan kyakyawan gashina zai kare, Duk inkinmun kitso saikinyimun baki. Dariya makitsiya ta tuntsure da ita harda kwallah tanason Nene sosai shiyasa take jure abunda take mata. Amal dake tsaye fuskarta cike da murmuahi yayin da Amnah ta zauna ta É—ora É—aya kan É—aya tana kallon mai kitson cike da takaici irin yanda ta samu damar zama tana yanda take so . Amal tace "Nene mu!. Afurgice ta É—ago ta kalleta tare da mikewa tana kokarin gudu wa. Dariya Amal tasa tace ga faÉ—a ga masifar tsoro to nice. Dariya Nene ta saki tana mikewa ta Æ™araso wajensu ta cire kallabinta ta yarfama Amal din afuska tare da cewa "ja'ira na É—auka aljannu zulfa ne suka tashi kinson suke gareta kusan buhu goma akai. Dariya suka sanya Amal da zulfa inda zulfan ta tashi tana faÉ—in Nene bari in wuce sai da daddare nazo inci tuwo mai sulbinnan in kintuÆ™a selonita kike cemai komi? Baki Nene ta saki tace kai kedai wannan kanki kamar na Zabo wlh bakya rabawa" semovita" akecewa wannan tsamin bakin naki yana kasheki da yawa. Dan ma Allah ya rufamiki asiri bakinki baya wari da babu ni.babu ke kinson ni nafison É—an gayun mutum koya yake kuwa. Dariya tayi tace shikenn bari inwuce sai nazo. Tsaidata tayi tashiga ta shakomata kula da naman da fura mai sanyi tabata tare fa sabullan wanka dana wanki dan Nene akwai kyauta. Godiya zulfa tayi taryr da fita dan atsorace take da irin kallon da Amnah kemata. Tana fita Nene ta juyo wajen Amnah tare da sanya kafarta ta noshi ta amnah datake kaÉ—awa cike da Æ™asaita. Da sauri ta É—ago idonta tazubama Nene su. Cikin bacin rai tace ta sannu hakima!wadda gaba É—aya zuri'arku babu wanda akaba koda sarauta kwasar kashi ce, Amma in akaga kina abu sai ayi tinani dai- dai da Æ™udan gidanku sarkine minafuka. Kinsha wasu jajayen kayan banza kamar yar shan jini Amnah ki kiyayi duniya wallahi, zulfa ba tsara uwarki bace da ba zaki gaisheta ba ,sai ma hararata da kike kika furgitata kika hanata zama. Fuska ta yatsina tare da faÉ—in nifa kin cikamun kunne da hayani dan Allah kibarni Nene Ko infita inbar gidan ki. Haba safiyar fari a cikama kunne da faÉ—a,kina da masifar hayaniya. Ido Nene ta murza saiga hawaye tace shikenan Amina kici gaba da zagina kina wulaÆ™antani jiyama kamin kibar gidan nan saida kika kwashemun albarka tass daga kiranki yimakai abun arzi to kisani daga yau babu ni babu ke, Allah kuma ya isa zagina da kikai. Amalulu muje kici dambun shinkafa yasha kayan dad'i wlh . Amal tayi murmushi tace to kishare hawayenki kana muna tare da ÆŠan Dako ne zai sauke kaya. Mamy tace danki samu sauki zai rabamiki iyaka kifita kibashi umarnin inda zai kaisu. Baki Nene ta washe Tare da faÉ—in kai Allah yama fulanina Albarka ya É—aya tilo mai share ma iyayen ta kuka Allah yajikan Bashari da É—an uwanta,da yana nan da yaga yanda duniya takeyi damu wayyo Allah na mijina ta kece da wani irin kuka zuwa cen kuma ta saki dariya tare da gyara zani tace muje muje Amalulun Nene. Fita sukai suka doso harabar tsakar gida inda suka iske sadeeq zaune akan motar. Yana ganin sun fito da yar farar dattijuwar ya tashi tsaye tare da zame hular kanshi . Daga nesa Nene ke kallonshi tare da É—an lallekawa dan san sanin ina yan uwanshi suke. Suna gab da zuwa taja wani wawan burki tare da cewa ubnmi akaimka zakazo kaiman tsaye kamar bishiya Dabino, wato shine daga campany suka turoka kenan to maza kabar gidan nan wallahi tin kamin in dakko barkono da mai in laftamaka ga fuska,Dan iskanci banace bana so ba. Ahankali ya É—ago Æ™anshi dan yaga dawa take. Karaf idon shi ya faÉ—a cikin nata hakan yasa Nene daka tsalle takoma bayan Amal tare da Daga hannu tace Sukusmie(excuse me) tana dagamai hannu alamun yabata waje. Kallonta yayi sosai tare da sakin murmushi dan yana tinanin shigr da yayi yasa take ganin shi kamar Dan sanda. Ƙarasawa yayi wajenta tare da duÆ™awa yace" ina kwana. Gabaki É—aya idanuwanta ta fiddo tana kallon yanda yayi hausa raÉ—am a'bakinshi. Amal tace nene gaisheki fa yake shine kuma yakawo kayan daga gidan mu . Mamy ta sameshi zai dingamata aikace- aikace fa. Wani irin Æ™anÆ™ance ido Nene tayi can ciki tare da fitowa daga bayan Amal tace kina nufin wannan ne Dan Dako? Mike damun Saudat da zata É—auki wannan saurayin aiki?Lalli kune ya rufema ido amma ninan Nene babu shegen dazaiman rufa ido dagani turoshi akai gidan ku dan ya sace ku, Mussaman waccen mai girman kan bala'i dam ansan in an É—auketa za akwashi kudi. Duk maganar da take yana jinta babu abunda yake sai murmushi tare da jingina da motar ya harde kafarshi hannunshi kuma daya sai gilgiza key din yake.. Nene ta matso wajenshi tace kai tsakanin ka da Allah wazaka sace? wa akace kasace kaji tsoron Allah ka fadamun gaskiya? wa akabaka kongila daga acikin zuria ta? '"Kece'' Yabata amsa agajarce fuskarshi Daure tamau kamar bashi ke sakin Murmushi ba.. 5/18/22, 09:33 - MY MTN 2: 🌹 ÆŠan Dako Mallaki🌹 Ummy Aysha🌹 🅿ï¸1ï¸âƒ£1ï¸âƒ£&1ï¸âƒ£2ï¸âƒ£ "" Duk da zuciyar Nene ta buga amma cikin jarumta ta daka tsalle ta iso gaban shi, tare da "faÉ—in kai uban Turajima yayi kaÉ—an balle kai, barganinka da kirar samudawa Bashari ya tsumani kamin ya Mace, Dan haka daga yau bana son Æ™ara ganin ka cikin zuri'a ta, saboda ban'yarda dakai ba. Yo inbama haukaba irin na Saude taya zata iya zama gida É—aya dakai jibifa nan inka. Takaima faffaÉ—an kirjin shi naushi. Idon shi ya lumshe tare da sakin fuskar shi da yalwataccem murmushi yarasa dalilin da yasa tsohuwa ke masifar burgeshi, yana tsananin sonta lokaci guda acikin ranshi. Ido a lumshe ya fara magana cikin sanyin murya "Nainahh yaja sunan da wani sauti mai masifar daÉ—i wanda yasa Amal rintse idonta da karfi tare da buÉ—esu lokaci guda ta saukesu akan pink lips dinshi dake motsi A'hankali. "Nainah bantaÉ“a cutar waba,duk da ni ancuceni amma kuma hakurina yafi gaban zuciyana,banshigo zuri'a kiba dan cuta saboda bana fatan cutar da Dabba mai tafiya a hanya balle ÆŠan Adam da Allah ya karrama, Abu É—aya nasani tabbas ni ÆŠAN DAKO ne ,a kasuwa suka ganni nakaimusu kaya mahaifiyar su ta amince dani.... Atakaice yabata labari duk abunda ya faru cikin natsuwa. Nainah ni maraya ne Baban ya rasu kana ina da Æ™anwa da mahaifiya, wayanda sune gatana na duniya kuma nima duk kan wahala da zanyi dan farin ciki'n sune. Banji haushin kiba dan kin haÉ—ani da mai sace mutane gaskiyan ki saboda rayuwan babu amana aciki. Amma kisani bawai dan kibarni inyi aiki gidan y'arki ba aa ! Gaskiya ta zanfaÉ—amiki banacin amana amma kuma ina hukunta wanda yaci tawa. Ya rage naki ki amincemun ko karki amincemun duk É—aya ne awajena, Saboda ita kofofin rahma ta Allah yawa garesu , Kisani ranar da nakai kaya gidansu Amall aranar wanda nikema aiki ya koreni , Muna tsaka da magana yanda zan samu wani aikin da zan kula da mu da mahaifiyata naji kiran y'arki. Zaki iya kiranta yanzu kimata magana kin hanani dan bazan iya tinkarar taÉ“a gaskiya. Yakarasa yana É—ago fararan idanuwan shi ya saukesu akan Nene da tinda ya ambaci Maraya ne shi ta É—ora kanta akan motar ta fara kuka marar sauti. Gaban shi ya faÉ—i sosai har baison sadda ya Æ™arasa wajenta ya É—agota tare da zube gwiwoyin shi Æ™asa yace nine ko? Kimin hakuri bazan sake ba kiyi hkuri na tafi. ya faÉ—a yan juyawa . Da wani irin gudu da kuka shaÉ“e -shaÉ“e Nene ta kamo hannun shi tare da rikewa gam tace" wallahi kai ba maraya bane, kana dani kana da mahaifiyar ka, Yaro ina sonka zanzamemak a gata kamar yanda allah ya zamemamu a'sadda muma mukayi rashin jigon mu, Dan haka i lovulu wallahi. Baison sadda dariya ta kwacemai ba sosai yake dariya harda wasu kwallah da suka masifar mai kyau. Nena ma dariya tayi tana jin tsananin tausayinshi har cikin zuciyar ta. Tace muje palo na kaci abinci, ya sunan ka? "Sadeeq" yabata amsa atakaice. Hannu ta tafa tace sunan Æ´aÆ´an Saudat Wallahi shine ya É“ata tin yana karami ta faÉ—a tana share hawaye. Cikin jimami ya mata jaje tare da faÉ—in ina za asauke kayan. Mai gadinta takira tare da cewa" ÆŠan larai kama mashi mana ya saukesu. Da" to" ya amsa ya samu ya kinkimo buhu guda ya ajiye yana mayar da numfashi. Sadeeq ya tattare hannayen rigarshi ya fara saÉ“osu akafaÉ—a yana direwa gaban Nene, sadda ya kusa gamawa kana ÆŠan Larai ya ajiye buhu ukku. Tsaki Nene tayi tare da cewa" Huhulahun banza huhulahun wofi, Duk uban abincin da kake ci amma ji abinda kayi . Cikin nishi yace "Hajiya Nene kowa fa da aikinsa yafi kwarewa, Dan haka aikina buÉ—e get bawai DAKO ba, shikuma aikin sane karshenta kiga inzai bude get har kuka sai ya fashe dashi. Murmushi kawai sadeeq yayi yana gamawa ya hango pampo ya karasa ya wanke fuskar shi tare da zama kasan wata bishiya Mango dake gidan yayi shuru. Nene tace to ai yayi mai wuyar dan haka É—akko Baro kazo ka kaima kowa tinda kason inda ake kaiwa shiÉ—in ya kula da get din. To yace yana sakin mika. Nene ta koma ga sadeeq ta tsuramai ido cikin tausayi tace" Sadidi in'kawomaka abinci anan . Kallonta yayi tare da kaÉ—a kai alamar aa. Amal tace Nene bayacin abincin ko inafa wallahi saina Ammin sa,Ban sani ba ko yana zargin zamu masa wani abune. Cikin tausasa murya yace babu wanda ya isa yayi sai da yarda Allah, ni bana zargin ku sam kawai ra'ayinane haka,nason duk inda Ammi na take yanzu tanacen tana bukatar taga tamun abinda zanyi farin ciki, to nafito kuma nacika ciki waje kinga bazataji daÉ—i ba taga na koma nace banaci ko? Yakare magana awahalce dan matsanancin ciwon da yakeji a Æ™asan zuciyar shi. Nene tace" kai Saddi wallahi na fita iya girki, Sala katafi kana tsinemin albarka da zagina akan namaka tayin rowa ko? Amalulu É—eboman abinci kihaÉ—o da ruwa da kaina zanbashi. Da sauri ya É—ago kai ya kalleta tare da kawar dakai gefe yana motsa baki. Cikin hanzari Amal takoma ta jero komi ta kawoma Nene . Nene tayi zaman dirshan gabashi tare da cewa kadaiga ni "Tsohuwace inka wahala dani allayh zai Sakaman Saddi kaci ko in baka.? Ganin mutuncin Tsohuwa da kulawa da take nunamai yasashi Æ™arba cokalin yayi Bissimillah yafara ci cikin natsuwa. Ido ya lumshe danjin yanda Danbun da yasha zogala da kayan lambu ya ratsa bakin shi. Bai an'kareba saida yaci rabin flat kana yaji ya koshi. Nene ya kallah tare da É—an fiddo ido yace shikenan" Nainah yau babu ni babu cin abincin Ammi nah, kincikamun ciki da girkinki mai daÉ—i ya yfada yana lumshe ido. Dariya jin DaÉ—i Nene tayi tace" kai nifa gwanace a girki dan shekarun baya har Matar Masari saida taso É—aukata aiki saboda yanda nike baÉ—e kofofin hancinta da kamshi da kuma labarin iya girkina da Bashari ke bata . Cikin rashin fahimta inda ta dosa ya kaÉ—a kai baice komi ba. Nene tace to taso muje ciki. Yace aa zanje in É—akko sauran indawo. Tace yawwa Saddi maza. Tashi yayi cikin jin kwarin jiki yafaÉ—a mota ya fita. Me gadin Nene yadawo da almajirai sunkai talatin. Azabure Nene ta mike tana faÉ—in Æ™udira sama Liman da wawan zama, ÆŠan Larai uban minene haka? mizasuman .? Yana nishi yakaima kirjin wani dake kusa dashi naushi yace kingansu nan kullim da kinkawoman abinci zakigansu kamar jamfa a jos sun taso suna buÉ—e hancina kamar kofar guga, Suna ya bayin Allah, Minafukan Allah dan suja in'masu rowa Allah yakamani tinda sungani. To abun yazamemasu jiki kullim saina basu loma É—aya shiyasa da naga zanyi wannan aikin wahala naje na gayyatosu dan karsuci banza , dan haka kowane shege shi zai É—auki na gidajen da ake kaiwa. Nene tace kamun dai _dai dan Larai wani lokacin fa akwaika da hankali , Dan haka basu suci gaba da kaiwa kana tsaremin get. Ahaka duk suka karar dana wajen yayin da Nene ta koma ciki. Anan suka iske Amnah zaune cikin wasu riga da wando gabaki É—aya'n su pink sunmata kyau sosai tayi parking É—in dogo'n gashinta tsakiya ,ta kunna kayan kallon tasa kida mai taushi yana tashi ahankli sai kaÉ—a kafa take tana latsa waya. Koda suka shigo basu kalletaba itama bata kalle suba. Saida sukai alwallah sukai sallah Nene" tace amalulu waccen kota hada iri da kafuraine da bata sallah. Amal tace aa Nene yau batayi fa. Fusk Nene ta yamutsa tare da cewa kazamar banza kawai dole taita shiga jajayen kaya ashe cikin jini take. Dariya Amal tayi ta linke abun Sallah tare da mikewa tace" Nene wallahi yunwa. Tace kije kici abinci ni banaso tuwo zanyi. Zuwa tai ta zuba abinci ta dawo palo tace" Aunty Amnah in zubo miki!. Akasalance ta kalleta tana lumshe ido kamar yar maye dan Abinda take gani awayata yana masifa tayar mata da hankali. Kai ta kaÉ—a mata tare da faÉ—in naci nawa kuna waje. Nene ta kalleta tace ke" Amina ubanwa ya baki izinin zuba Abincina, ke waima tsaya ke zuwafa yanzu yakamata a'miki aure naga sai wani iskanci kike kina ganin mutane É—ai-É—ai. Cikin natsuwa ta muskuta ta gyara zamanta tare da fuskantar Nene. Cikin taushi murya tace "Nima inason kumun auran amma kaf faÉ—in katsina banga wanda yadace da rayuwata ba, Saboda ni inason saurayi mai kuÉ—i mai masifar kudi fa Nene bawai kaÉ—an ba, kana É—an gidan Sarauta maiji da jinin mulki,in ma so samune ya Æ™asance sarkine,kana fari kyakyawa mi yalwataccem saje, kana karfaffa bawai soko ba, ina so in son samune ya kasance Soja ko Likita, cikin biyun nan dai, Dan bana da ra'ayin auran É—an kasuwa saboda masifar matsolanci dabin Æ™a'ida. Cikin ta fasa zuciya da takaici Nene tace dan ubaki in sai dashi ake kije kisiyo mana kana da ba'ason asalin anguluba sai muce daga Æ™asar masar take, ke nan har zaki zaÉ“i mijin da ke zaki lissafashi,to in saukin samu garai kije kisiyo,Shiyasa ko É“era baita É“a sallama dake ba. Murmushi ta saki tace wallahi Nene in bansamu wanda na lissafamiki ba banayin Aure, Muddum mijina bai fito daga gidan sarauta ba bana sanshi, ko satin nan kamal É—an gidan Gwamna Sani Baba yazo nemana, Amma karkiso kiga yanda namasa, saboda fatana in'samu masu takemun baya da kamar masu kudinsa kona tsohon sa, Dan bazan É—auki talakaba dan som baison daraja mutane ba, kidubamun wancen wawan ÆŠAN DAKO, Yau É—aya ya É“atamun rai amm yakasa zuwa ya bani Hakuri. Kuka Nene ta fashe dashi na takaici tare da tashi ta haye sama tana faÉ—in" na zauna wajen wannan yarin ya wallahi zuciyana bugawa zatai inma fulani na asara. Amal tace Gaskiya " Aunty Amnah bakya kyutawa,Æ™o fa babu komi ya girmeki kana ba ayiwa Allah haka, kedai ki nemi zaÉ“in Allah. Shutt up kika sakemin magana zan wankamiki mari tsarar kice ni? tashi kiban waje. Cikin É“acin rai Amal ta tashi tayi É—akin su dake nan gidan Nene tayi kwanciyar ta tana tinanin sadeeq , ita tarasa dalili tin jiya yaki barin zuciyar ta, koda wane lokaci tinani wani abun nashi take, yakan sata É“ata fuska ko tayi murmushi, A'hankali tace Ga aji, ga kyau ,ga Æ™asaita, ga rashin son Raini ,wallahi yah sadeeq kayi Allah yabani Mai irin halinka. Jin Æ™arar buÉ—e get ya sata tashi da sauri ta fito palo tare da leÆ™a wa anan ta hango shi ya danno hancin mota ya shigo. ÆŠan Larai namai magana saikuma yaga al'majiran nan suntaso sunfara kwasar kayan da sauri. Gefe ya koma ya naÉ—e hannuwa yana lumshe ido dan dama bayajin daÉ—i som. Da sauri Amal ta nufi dakin Nene ta iske ta fito wanka . Nan ta faÉ—amata ya dawo. Da suri Nene ta canza kaya tace muje suka fito Tare. Suna fitowa Nene ta kamo hannunshi tace" muje ciki Sadiq ka huta,yanaji hannunka da zafi ko baka lafiy ne.? Kai ya gilgizamata tare da faÉ—in" Nainah lfyna fa kawai dai. Kawai mi ? Nene tace. Kai ya sosa yace muje inga É—akin naki ta yanda zansanu saukin kwasheki da daddare. Dariya tayi tace haba dai yaro mukwashe juna dai ni ai da dare yayi nikeyin layar É“ata in bacce É“at.. Kallonta yayi yasaki Murmushi har suk isa ciki. Suna shiga ta nuna mai saitin kujera da Amnah take anan ya zauna danshi baima lura da ita ba kamar yanda batason sunshigoba hanklinta na ga abunda take kallo. Fira Nene kemai yana É—an amsawa sama- sama daga baya yace mata zai koma . Tace amma zaka dinga zuwa nan ko. Yace" Azumi fa za afara, na daizo karÉ“a barka da sallah na. Nene tace shikenan Allah ya nunamuna. Ameen yace yana mikewa da sassar fa yayo hanyar fita, cikin akasi Amanah ta mike tsaye da sauri duk tinaninta Nene ce ke son leÆ™o ta. Bam kakeji ta faÉ—a cikin kirjinshi. Lumshe ido tayi jin wani irin sassanyan kamshin daya mamaye hancinta, kwakumeshi tasakeyi kasancewar cikin yanayi take wanda ita kanta batason miyakawo mata hakan ba. Wata irin faÉ—uwar gaba ta kawomai ziyara jin yadda ta af'komai bisa kirji, kuma saitin zuciyan shi dakemai ciwo. A fusace ya fisge ta tare da dannata bisa kujera yasaki tsaki ya wuce. Ido ta É—ago cikin wani irin tashin hankali dajin tsanar kanta ta kalli bayan shi, Dan ko alama batason shibane, to taya tazo jikin shi? innalilli yanzu shikenan ya sake rainata. Jikinta ta kallah tare da sinsunawa taji yssbon kamshin ma take akan nata, Amma dan sharri fuska ta yamutsa tare da faÉ—in ta yama zakaÆ™i hamami da wari kana aikin Dako , Dole in'sake wanka . Nene ta kallah da Amal wand som hanklin su naga kallon da suke basu lura da abinda ya faru ba. Da sauri ta mike ta shige toilet tayo wanka ta fito. Koda ta fito ta shirya kanta tare da faÉ—awa kan gado ta fara tinanin abunda ya faru ,tsaki kawai take jerawa wani bayan wani. Abangaran Sadeeq kuwa yana fita ya fara kakkaÉ“e jikinshi yana yatsina fuska, tare da faÉ—in Æ™azama shashasha, marar kirki, wadda batason daraja mutane ba ,kawai kinfamamun ciwo hakanan kawai Makauniya. Gidan Mamy ya koma ya faÉ—amata duk an'kammala ! Taita samai albarka tare da gashi wani sabon key na machine tace'' gashi kaima ka dinga hawa ka huta da zirga -zirga zuwa da komawa, kana akwai buhu shinkafa ,masara, gero, dawa ,alkama, sugar, taliya ,macaroni, indomie, ka kaima Ammin ka . Kace ga kayan Azuminan ina gaidata, amma kyanshi ka fara kaisu a'mota suna store kason bazasu É—akku a machine ba . Tsororo yayi yana kallonta cikin wani yanayi yace" Hajiya kintina kuÉ—in da kika bani jiya ,ga nama, wallahi kibar abinki nagode Allah ya saka da Alkhairi.. Mamy tace" sadeeq bakayi islamiya bane.? Ido ya zaro tare da cewa nayi Hajiya mikika gani.? "Tace to minene ribar abaka sadaka kace bakaso, ko rainawa kayi ne Sadeeq ?banaso daga yau in nabaka abu kanunamun yayi yawa ko kuma kuna dasu. Yanzu in'ka kai mata wannan ai na tabbqta tana da yan uwa da makwafta da abokan arziki ko? ta ai'zata rabamasu kuma duk tarayya zamuyi cikin lada, dan haka ka kwashe kawai duk rabon azumine kuma kason Allah naso ka kyautatama mabukata a cikin azumi ta hanyar ciyar wa, kana ni ina jinka ajikina wallahi ba É—auka É—an aiki nikema ba,Aa jinka nake kamar jinina,ina jinka kamar babban É—ana wanda na haifa, ka É—auka Allah ne ya haÉ—amu dan mu Æ™aru da juna, wannn bakomi bane zaka iya tafiya.ta faÉ—a tana faÉ—awa É—aki ta bashshi sake da baki. Fitowa yayi jiki babu lakka ya Æ™arasa store din da tace ya kwashe kayan, Anan yaga hadda jarkar Mai. Kwashe su yayi ya tura a'mota tare da fita yayi gidan su yana tinanin maizaicema ammiyn shi dan abun ya fara bashi tsoro. Yana isa gidan ya sakko daga motar anan ya fara.kwasar kayan ya saukesu tare da kammalasu soron gidan lana ya rufe motar ya fita Kofar y atura da sallama yafara kai kayan . Ammi ta fito tana faÉ—in ikon Allah sadeeq lafiya'n ka kuwa? wayannn kayan fa, bayan wayanda ka kawomana jiya?. Saida ya kammala kana ya zauna ya koramata bayani tare fa faÉ—in" nifa Ammi banaje gidan su dan aita kashemun kuÉ—i ba ,,aa subani iya hakkina ya isa abun fa y isheni. Murmushi Ammi tayi tace karka manta kila zakka Azumice, kaga kenan muma Allah yaci damu, dan haka muma bazamuci mu cinyeba zamu kyautatama wanda suke cikin yanayi, duk da bama shiga harkar kowa unguwar nan kuma babu mai shiga tamu, hasalima tsoronmu ake to amma zamu kyautata iya iyawar mu da yarda Allah. Kai ya jinjina tare da faÉ—in in Baby? Tace tana ciki ka sonta da bacci tinda mukai sallah Æ™arfe É—aya take bacci. Yace shikenan tare da zaro wayar shi yace" bari in'kirata kimata godiya ko. Ammi tace eh kirata kuwa kayi hangen nesa. Mamy ya dan nama kira cikin lokaci ta É—auka. Cikin natsuwa yace" Ammina zata miki godiya. To Mamy tace tana sakin Murmushi. Karba Mamy tayi suka gaisa a'mutunce a inda taita godiy da Addu'a buÉ—in Alkhairi. Mamy taji daÉ—i ta amsa da ganan sukai sallama. Abinci Ammi tamai tayi yace" yaci gidan Nene anan yabata labarin Tsohowa taita dariya itama tare da faÉ—in ai tsaffi akwai daÉ—in zama. Gab da la'asar yace mata zaije masallaci daganan zai wuce, misuke buÆ™ata na sahur dan ana sanya ran É—aukar azumi yau. Tace babu komi sai dai ko fura inzai dawo. To" yace tare da fita. Gab da sallah mangariba suna fira da baba madu su Amal suka dawo. Anan take shedamusu da anga wata saudiyya. Ido y lumshe tare da faÉ—in Allah yabamu ikon kyautata halshen mu da zukatan mu. Ameen ta amsa ta wuce... Bayan sun dawo isha yama Mamy sallah ma ya wuce. Sai da ya tsaya ya saima Ammi fura mai kyau da yoghurt yayi ma Hamrat tsaraba kan ya kom gida da sabon machine É—insa. Yana isa gida anan ya shiga da abin shi. Da gudu Hamrat ta taso tayo wajen shi tana "oyoyo ga Baby yayi sabon machine zai kaini yawo'n sallah. Da sauri ya gyara parking kana ya kama hannunta suka Æ™arasa wajen Æ™ofa yana"oyoyo Baby acici harta Æ™agara sallah tazo, to mikika tanadar mata?.. Tsalle tayi tace "Baby ice cream ,kadaiga wannan karan kana da machine bazaka ki Æ™aini ba ko? Rufe gidan yayi kana ya kamota suka dawo har gaban Ammi bayan sungaisa ya shedamata anga wata. Addua tayi tare da fatan farawa cikin sa'a. Hamrat tace baby baka bani amsaba?. Murmushi yayi yace" insha Allah baby'n baby zamuje duk inda kike so, saboda banda wanda yafiki kedai kishirya kawai Allah ya nuna muna wannan lokacin. Ameen ta amsa tana karba abinda yabata da godiya.. Da wuri suka rabu inda ya koma É—akinshi ya fara bincike a sistem É—insa saida ya daÉ—e kana ya kwanta. 3:30 ya tashi yafara nafilfulu har sai karfe 4:30 kan yayi sahur da tea da Ammi ta bashi, yana gamawa yayi raka'atul fijr kana ya wuce masallaci,bayan yayi sallah yayi azkar yayi karatu sai bakwai da rabi ya doso gida. Cikin sauri ya shirya kanshi cikin wasu kaya dogon wando brown da yellow riga sunmishu masifar kyau. Sallama yama Ammi tace mai da yamma ya dawo ya kai abincin masallaci lokacin ta kammala. Yace insha Allah ya fita. Bayan yaje gidan Mamy sun gaisa ta bashi ya karÉ“o musu kaji da yan ciki yana dawowa" tace shikenan zai iya zuwa ya kwanta. Carfet ya É—auka yatafi lambu Æ™ason bishiyar Mango ya kwanta ,sai azahar ya tashi. Sallah yayi sai masallaci, bai fitoba sai biyar na yamma dan karatu ya yini yi. Bayan ya fito ya É—auki mashin sai gidan su, anan ya iske Ammi ta cika manyan kuloli da waina da ruwa mai sanyi sosai. DaÉ—i yaji ya kwasa ya kai masallaci biyu ya dawo, ta Zubamai kayan buÉ—a baki ya É—auka ya tafi. Yana isa Amal na zuwa da kaya masu yawa ta bashi. badan kar taga kamar wani Abuba ya karba Yamata godiya. Ana kiran Sallah yaci Dabino da kankana ya tashi yatafi masallaci. Bayan ya dawo sukayi buÉ—a baki awadace, ana sallah ya tafi masallaci sai tara na dare ya dosyi gidan su. Haka sukaita rayuwa yayin da Azumi keta tsula gudu dan har yakai goma sha biyar suna ta rayuwa mai daÉ—i. Aranar da aka É—auki na sha shidda yana zuwa Mamy ta shedamai zai kai su Amal kasuwa. "Yace shikenan. Bayan sun fito Amal ta shiga gaba Amnah ta zauna a baya. Suna É—aukar hanya Amnah ta fara sakin tsaki mai Æ™arfi. Amal tace mike damunki Aunty amnah? Hancinta ta toshe da yatsunta tare da fiffita da gudan hannu tace" Amal bakyajin wani masifataccen wari da Æ™arni kamar na jaÉ“a.? Nifa bazan juri yawo da Gardiba wallahi saboda yana cutata,haka kawai n Mamu ta HaÉ—amu da, masifa ,ni bazan jureba yazama dole Abba in yadawo a sallami wannan gardin ,yayi ale-ale cikin mota kamar ta tsohon sa..... Wani wawan burki yaja daya tada hankalin mutane dake kan titin dana su Amnah. Afusace tace kai talakka motar Uban nawa ka keso kamun asara? Harda neman bugama wani wawa gwame kawai babu abinda ka iya sai warin talauci. Kanshi y dafe da masifar karfi yace Amalllll fi...t..ttah ya faÉ—a cikin ihu da in ina. Hankali tashe tace ina zani Yah dadeeq. Tsawa ya Sakar mata mai mugun tada hankali batason sadda ta buÉ—e ta ficce ba da sauri. Belt ya sanya tare da tada motar da wni mahaukacin gudu. Salati mutanan wajen suk saki ganin yanda motar ta wu....âœï¸ 5/18/22, 09:34 - MY MTN 2: ÆŠAN DAKO 🌹 🌹MALLAKI UMMY AYSHA 🌹 🅿ï¸1ï¸âƒ£3ï¸âƒ£&1ï¸âƒ£4ï¸âƒ£ ""Salati Mutanan wajen sukai ta saki ganin yanda motar ta wullah saman titi har wani tsalle take saboda azabar gudu. Wasu na faÉ—in É—an shaye- shaye ne wasu na faÉ—in Azumi ake kila motar ke janshi ,kowa da abinda yake faÉ—a dai. Amal kam hannu ta É—ora akai ta saki wani siririn kuka. To mizaima yar uwar ta?kodai da gaskiyar Nene Amnah akeso ya sace? innalillahi wa inna ilaihi Raji'un. Ya zatace da Mamy? miyasa bai tattarasu suka tafi baki É—aya ba?Ta yarda da magana Nene abinda babba ya hango yaro bazai taÉ“a hango sa ba. Abangaran sadeeq kam wani mahaukacin gudu yake ido rufe , Da kuma hannu É—aya, ga baki É—ayan idanuwan shi sun'mai duhu, har Yaji- Yaji, kwallah- kwallah yakeji masu tsananin Zafi a cikin idon sa, ga kanshi ga baki É—aya saramai yake, fatan shi ya buÉ—e baki yayi magana amma yason in ina dake kawomai ziyara duk sadda yake cikin É“acin rai bazata barshi ba . Afusace ya tura hannunshi cikin yalwatacciyar sumar shi ya dinga bazata kota ina. Amnah ga baki É—aya jikinta rawa yake ganin har sun fita daga garin Katsina sun naushi hanyar Dutsama. Cikin Daure tsoron ta tace" kai ina zaka dani baka da hankaline.? Kamar jira yake ya Æ™arama motar gudu jikake fiiit -fiit yana wuce yan tsurarun motoci'n dake tafiya da dawowa. Saida ya nausa da ita wani É—an daji mai yawan duwatsu kama yayi parking. Afusace yafito ya buÉ—e inda take tare da buÉ—e idon shi dakyal ya watsasu bisa fuskar ta data zubami ido, A karo na farko kenan da suka tsaya sukaima juna kallon Æ™urullah. Abangaran Amnah kallon mamaki takemai dama haka yake.? Shikuwa zallar tsanace afuskar shi tare da tinano irin fansar da zai É—auka akan iskancin da take mai harda zagin mahaifinshi dake kwance cikin kasa. Cikin ihu da in ina yace" Fii..t.toooo. Gabaki É—ayan jikinta ya saki jajayen idanuwanta ta É—ago ta yarfamai tare da faÉ—in" ina zaka kaini.? Gi..dan uban..kiii... Ya bata amsa a wahalce. Ido ta zaro tare da fitowa tace'' kai ni kake zag... Kanta Æ™arasa ya bata wasu kyawawan maruka guda ukku wanda ya sata tintsurawa cikin wasu manyan Duwatsu. Cikin wata tafiya ta Namiji duniya ya Æ™arasa wajenta tare dasa Æ™afarshi ya take yatsun hannunta da masifar Æ™arfi ,wanda yasata sakin ihu da karfi tare da kallon shi da sauri.. "Bani da ra'ayin zalintar kowa, bakuma niso azalinceni, yau in namiji ne É—an uwana yamun abunda kikamun Wallahi Wallahi ina mai shedamiki saina É“atamai fuska ,ta yanda uwar da ta haifeshi bazata gane shi ba. Kirike azziÆ™in Æ™i da iskancin ki. Nima kuma kikayale ni, in rike talaucina da mutuncin kaina. Amma in kinÆ™iya ko gaban uwar kine zan casaki kamar gero, wawiya daÆ™iÆ™iya. Wallahi billahi daga rana mai kamar ta yau kika sake zagina ko kuma ki kira mahaifina da baya raye saina É“atar dake a faÉ—in duniya, daÆ™iÆ™iya jahila,tinda kika zama mai wannan halin ni ina da tantama akan asalinki wallahi. Duk wanda yayo gadon Azziki baya iskanci da tinkaho, saboda abin a jininsa yake. Dan haka kije kiyo binciken Asalinki karshenta ke agolace agidan da kike takama na ubanki ne, dan ita yar uwarki ina tinanin itace yar gidan da yake ita gadon azziki tayi ba haye ba gashinan ta rike mutuncinta tason daraja mutane. Tashi muje jaka kawai. yadaka mata tsawa. Gabaki É—aya'n doguwar magana da yayi cikin in ina yake yinta wadda ta kara shagalar da ita wajen kallon pink lips dinshi dake motsi ahankali ga idon shi da suka canza kala kamar wanda ke tsaka da buÆ™atuwa. Bata fara fahimtar miyake faÉ—a ba har saida taji ya fara Ai banta asalinta kana tafarajin faduwar gaba da wasu kwallah masu tsananin zafi. Akaro na farko ta nuna kanta jikinta na rawa tace "ÆŠAN DAKO nikakema sharri? Nizaka aibantama Asali? Wallahi wannan magana Taka sai kayi dana sani? Court zata rabani dakai koda abinda na mallaka zai Æ™are. Tsaki yayi ya juya yayi gaba abinshi cikin Æ™unar zuciya da bacin rai. tabbas yau sai ya ajiye aiki agidan su bazai jure Æ™arama yarinya namai wulaÆ™anci ba. Ganin yayi nisa yasata tashi duk jikinta ya lalace da Æ™asa ga hannunta har yayi fushi. Dakyal ta taso ta gangaro ta faÉ—a motar da kyal , Duk tsorace take dashi ga faÉ—uwar gaban da takeji in ta tino furucin shi. Gudu da yake yafi wanda yazo dashi gaba É—aya hankalinta atashe yake, tana ganin tayi bankwana da gidan su kawai. Cikin mintina Æ™alilin ya isa inda ya sauke Amal, anan ya isketa zaune tayi zaman Dirshan tana ta kuka . Som ta kasa kiran Mamy batason wane yanayi zata shigaba, gata da hawan jini. Tana ganin mota ta tsaya gabanta da sauri ta tashi ta faÉ—a baya tare da tallabo Amnah tace. "Aunty minene ya miki, ina yakaiku, dukanki yayi? Takarasa cikin kuka. Kai Amnah ta gilgizamata tare da maida kanta cen gefe ta fara nazari Magan-ganu shi. Hanyar kasuwa yayi Amal tace kabar ayhi ka maidamu gida. Tsaki ya saki tare da juyawa ya doshi unguwar su. Yana shiga ya buÉ—e motar ya fita tare da isa kofar palon Mamy cikin sassarfa. Wayar shi ya É—auka ya kirata . É—auka tayi cikin faÉ—uwar gaba tare da fadin sadeeq lafiya? Alhamdulillah yace cikin kasa da murya tare da cewa "gani nan kofar palon ki. Da sauri ta kashe wayar tare da fitowa ta buÉ—e. dai- dai lokacin da Amal ta kamo hannu Amnah suka doso wajen. Mamy na buÉ—ewa ta zubamusu ido cikin barin jiki tace "miya sameku.? Amal tace" Mamy muje ciki babu komi fa. Hanya ta basu suka wuce ta maida hankalinta ga sadeeq tace" ina jinka. Hannushi ya tura cikin sumar shi tare da turata baya duka, har lokacin kuma muryar shi bata fita sosai. Da kyal yace'' na ajiye aiki ga key dinki na gode da hidima da kikamun. Innalillahi wa inna ilaihi Raji'un, Hazbunallahu wani imal wakim," sadeeq minai maka ? Babu abinda kikamun Hajiya. Amma gaskiya bazan iya zama Æ™alÆ™ashin inuwa É—aya da yarki ba,Saboda bata kauna haÉ—a jini da talaka,kana tana muzantani,Anan yafaÉ—amata abinda ya mata da wanda ta mashi. Daga karshe ya ajiye key É—in ya juya abin shi.. Hankali tashe take kiranshi Amma yakasa juyowa . Afusace tashig palon cikin matsanan cin fushi ta zari wayar charger tafara tsulama Amnah ajiki, Abinda bata taba yiba. Ihu Amnah keyi sosai tana neman É—auki amma Mamy ido ya rufe bataji bata gani. Amal ma kuka take tana neman agaji akan yar uwar ta , Amma babu wanda zai iya jiyota ,saida mamyy tayi mata RuÉ—u-RuÉ—u kana ta koma gefe tana sauke numfashi. Dakyal Amnah ta mike ta haye sama tare da faÉ—awa toilet tayi wanka tana kuka sosai ta fito daga iya sai Æ™aramin towel tayi kwanciyar ta, tana kara jin tsanar Sadeeq aranta sosai, duk da wani sashin na zuciyar ta na hasasomata yana masifar kama da irin mijin da take fatan samu. Tsaki tayi a fili tace'' aiko nafasa bazan taÉ“a auran mai kama da talaka ba,Kuma ÆŠan Dako. Anan palo kam Amal ta Rarrafa ta rike Æ™afar Mamy ta fara bata hakuri, sanin Mamy batada isashiyar lafiya tinda takasa magana abun ya dameta sosai. "Mamy dan zatin Allah kiyi hakuri kar halin Aunty Amnah ya dameki,kibar wa Allah kitayata da Addua, ni kaina banajin daÉ—in abinda take . Ajiyar zuciya Mamy ta sauke tace" Amal taya zan iya samun mai amana kamar sadeeq, nasha auna shi da bashi kudin da suka zarce da niyyar wani abu amma haka zai maidomun canji,ga natsuwa ,uwa uba ilimi, kinafa jin shi kullum cikin Lambu yana raira karatun Alkur'ani,baya wasa da sallah ko kaÉ—an, taya zanji natsuwa da farin ciki in irinshi ya kufcemun? Wallahi Amnah bata kyutamun ba som,Tinda taje US ta dawo iskancin ta ya Æ™aru, ya zama dole ana gama sallah in É—auki mataki a kanta, saboda lamarinta kullum gaba yakeyi ba baya ba. Hakuri Amal taci gaba da bata har saida taga ta sakko. Tace Mamy kibani number yah Sadeeq inje gidan Nene! Na son suna shiri sosai dan ko cikin azumin nan yana yawan zuwa tacemun, in'haÉ—asu nason zata lallaso miki shi. Cikin farin ciki dajin daÉ—i ta bata. Ita kuma batayi sanya ba ta fita ta hu mota sai gidan Nene. Anan ta kora mata bayani saiga Nene na kuka tana tsinema Amnah. Cikin kuka tace'' latsoman shi dan Allah, inji awane hali yake , Allah yasama bayyi zuciya ba ya hau saman titi ya kwanta yace mota tabi tasaman shi,Koda yake Æ™atone bazai ji ciwo sosai ba. Sai kuma ta kwaÉ“e bakinta tare da faÉ—in'' wannan ai fatar banzace ina azumi yan Ameen su amsa in'cuci maraya nima walakiri Yaci man uwa. Arikice ta kwace wayar tan halo- halo Saddi dan Allah ka É—auka kar in'maka baki . Abangaran Sadeeq kuwa yana fita masallacin dake kofar gidan ya shige yayo alwallah tare da É—aukar Ƙur'ani ya fara karatu. Take yaji zuciyar shi ta fara sanyi. Jin Æ™arar wayar shi ne yasa shi É—auka da sallama. Nene najin ya É—auka tasaki shewa tare da amsawa tace" yawwa Abubakari kwandon sukari, Dan Allah kayi Hakuri kaje ga fulanina, Wallahi fulani kullum ceman take ita dai I lovulu to saddi , Amma kaga wannan yal banzar da batada kunya ta ganka Ƙato ita kuma tayi zubi da Buta lamba 2 tace zatama rashin kunya , Wallahi na baka dama duk in ta kuma kasanya makwal-kwasa ka fiddama shegiya rabin hakori,kai saddi kaji tsoron Allah rabi fa ba É—aya ba, A'a toh karka maidata kamar kofar Rijiya, inki samun Dan jikallan da zai sota. Nainah dama kina sya number nah amma baki taÉ“a kirana ba? Yakatse Nene da keta zuba. Nene tace "Eh mana kwandon sukari ina da number ka. Kai wallahi karya haramun ina azumina yanzu Amalulu ta sanyaman , Uwar ta Fulani ta turota akan tazo ta ÆŠaukeni mufita gantalin nemanka, cikin rana da kishi, shine nace naga kason mutunci nah kuma kaga ina kyautatama , Nason kamun alfarma ka koma ko? Shuru yayi yana murmushi jin yanda take rattafo zance. Da kyal Nene tasha kanshi yace zaikoma yanzu insha Allah. Dadi taji tace' um muah saddina, kason munyi zama da laraba ko Tusa É—ansu yayi sai sunyima Takashin yaron suu sunba,Suga Tantabaru iyayen kauna ,haba inama amfani wannan ai Iskancine da Æ™azanta,Saddi kason nataÉ“a ganin wani Balarabe zaima matar shi a laɓɓ... . Dariya ta bashi da sauri ya kashe wayar yana gilgiza kai. Saida yayi Sallah kana ya koma gidan Mamy anan takara bashi hakuri yace mata ya wuce. Ahankali kwanikka keta shudewa yau harya zamana sallah saura kwana ukku ko biyu . inda kafatanin al'umar musulmi kowa shiri yake dan ganin ya kerema sa'a . AÉ“angaran sadeeq kuwa gabaki É—aya cikin damuwa yake ta Rashin abinda zaima Ammin sa da Hamrat koda shi baisamu ba , Amma yason lokacin biyan sa baiba dole sai ranar Daran Sallah. Bayan ya kammala komi kamar yanda ya saba ya shiga yima Mamy sallama anan ta tsai dashi ta shiga sai gata da manya ledoji guda biyu ,dakyal ta jawosu tace yawwa "sadeeq ga kayan sallah ku mai ÆŠinki kane yabani matsala shiyasa ba a kammala da wuri ba, akwai na ÆŠiyata Hamrat dana Ammi duka dai baki É—aya, kana ina neman alfarma akawoman Hamrat ranar Sallah, kason gidan namu na cike da kewar Æ™ananun yara. Kallon ledar yake yana kallon Mamy wai shi da minene zai sakama matar nan, yanzu kayan sallah tami shi kenan? Wani irin girma da darajata yaji sun lunku a cikin zuciyar shi ,yana rokon Allah ya bashi abinda zai faranta ranta kamar yanda take faranta nashi dana Ahalin shi. Karba yayi ya mata godiya da addu'a da ganan sukai sallama yayo gida cikin farin ciki. Koda ya iso ya shigo da kayan tsakar gida tare da komawa ya shigo da machine dinsa ya rufe gidan. Sallama yayi ya shigo inda ya iske Ammi zaune tanata shafa kan Hamrat dake neman yin bacci. Amsawa Tayi tana mai sannu da zuwa, tare da matsawa gefe ya zauna yana mai jan yatsun Hamrat yace'' Baby'n Baby tashi kiga abunda nakawomiki. Da sauri ta tashi tana murza ido tare da turo baki tace ''baby munÉ“ata yanzu baka da lokacina. Dariya ya sanya sosai yana ganin yanda takeyi kamar budurwa. Ammi ma cikin dariya tace" To ke Hamrat bakyaso Yayan naki yaje aikine yasamo miki abunda zakici? Inso Ammi amma inason mudunga tafiya tare sai in ragemai wata wahala ko. Dariya sukayi su duka yayin da ya fara buÉ—e ledojin da keta zuba kamshin da yarasa kona minene yana jin kamar ya son Æ™amshin. Lumshe ido Ammi tayi jin wani kamshi daya daki hancinta wanda ya sata tinawa da lokuttan baya,take jikinta ya fara bari ,wanda ya sata jingina da bango tana Addu'a dan samun sauki. Saida yagama fiddo komi kana ya kalleta wanda hakan ya sashi faÉ—uwar gaba. Da sauri ya ture kayan tare da kamo hannunta yace ''Ammi nah mike damunki ,ko bakya farin ciki da kayan, kinson bafa nina sayaba, Anan ya faÉ—amata abunda ya faru. Ajiyar zuciya ta sauke tace" Dee ka tino wannan kamshin kuwa? Nazari yashiga kamin ya shiga jijjigamata kai cikin cikowar hawaye yace'' Ammi nah natina, wallahi natina Ammi nah, Amma babu damuwa Allah yakai Damo ga harawa ko baici ba zayyi wawaso,Gaba kaÉ—an gaskiya zatai halinta,lokaci kaÉ—an yarage zaki yayi ciki da Kura Dan magance handamar ta,kimanta baya Ammi na mu fuskanci goben mu. Kai ta gilgizamai tare da faÉ—in insha Allah" Dee . Wasu tsadadun lace da atamfa ya daga masu kyau sunsha ÆŠinki ya ajiye gabanta yace "Ammi ga wannan nakine ,ga mayafi da takalma duk nakine . Cikin murna da sa albarka ta gwada komi taga cif- cif da jikinta taita godiya. Wasu zafafan dogayen riguna na yaran yan gayu masu tsananin kyau ya É—aga guda ukku masu masifar kyau. Pink ,blue, milk sai sheki suke ya damkama Hamrat yace ''eyye Baby tayi kayan yan gayu. Hawaye ya zuboma Ammi tace Allah sarki rayuwa! Hamrat É—ita tazama yar gayu, bana bazata sanya atamfa roba ba taÆ™arasa cikin hawaye. Kai ya gilgiza cikin damuwa yace ''Ammi nifa som kayan nan sunfita raina,Duk Irin kyautar da za'aman wadda zata saki shiga wani yanayi inaji kwara Abar ta. Kan shi ta shafa tace'' kayi hakuri sadeeq bamu da bakin magana wa baiwar Allah nan sai dai godiya. Cigaba yayi da fiddo kayan hadda takalma, Hamrat kuma dai -dai kafarta guda ukku kalar riguna ta masu kyau da tsada , Sai kit na kayan make up da tiraruka,Daga Æ™asa yaga wata Farar kwalba mai kyau , Anan ya fiddota yaji wani mahaukacin kamshi , Da sauri ya mikama Ammi yace to hasashen mu ya zama gaskiya. Hannuta har kyarma yake ta karbi kwalbar tare da kwaÆ™umeta ta fashe da kuka gwanin tausayi , sai da tayi ta gaji sukabata baki kana tayi shuru. Gudar ledar ya buÉ—e inda yaga wasu shaddodi É—inka ku masu masifar kyau angoge an'sanya a leda yar ciki da babba rigace guda ukku na shadda masu tsada sai wasu boyel da a kaima tazarce guda biyu. A takaice kayan sunyi kyau,sai hular su zanna mai kalar kayan, sai takalma taki biyar da agwago da wani glass mai masifar kyau. Farin ciki sosai yaji ya kawomai ziyara Lokacin da yaga kayan mutunci da aka haÉ—a mai. Murna sukaitayi shi da Ammi,daga karshe suka kira Mamy suka mata godiya da Æ™udirin ranar sallah tare zai kaisu Sumata godiya ita da Hamrat. Washe gari ta kama Daran Sallah kuma anasa ran ganin wata. Hakan yasa a keta hada- hada , na shige da fice. Abangaran sadeeq ma yana tashi bayan yaje gidan Mamy ta bashi kuÉ—i yayo musu cefane da kaji masu yawa tace'' ya raba biyu ya kaima Ammi shi rabi. Da" to "ya amsa yaje yakai ya dawo suka cigaba da Abinda ya dace. Amnah ce kwance É—aki tana waya da wata Æ™awarta da sukai karatu US wadda ke shedamata tana Najeria ranar sallah zata kawo mata ziyara ita da cousin din ta . Murna tai tayi dajin daÉ—i dan ta son Billy babba yarinyace, shiyasama tasu tazo É—aya ko a makaranta batada tamkar ta, Dan yar babba gidace duk da batason gidan suba Amma ta shedamata Nijeriya take karatune ya kaita cen.. Karfe goma na dare sukaji Æ™arar bindiga daga masarautar katsina tabbacin ganin wata. Hakan yasa gari ya rikice da murna yakoma tamkar ba dare ba. Haka yake wajen sadeeq wani irin farin cikin da baison daliliba yaji yana saukar mai, sai goma yakoma gida bayan ya Æ™arbi Albashin sa yayo sayayya abun buÆ™ata. Anan ya iske Ammi nata aiki ya cire kaya tare dasa Æ™ananu yaci gaba da kamamata aiki sai sha biyu suka kwanta. Washe gari take Sallah Babbar rana zuciyar kowa cike da farin ciki, Duk Yanda rai yakai ga baci farin cikin wannan ranar kan goge damuwa da takaici kowane bawa . Karfe bakwai Sadeeq ya faÉ—a wanka ya jima sosai kana yavfito yanata zuba kamshin sabulun lemon Safe guard . Cikin kuzari ya faÉ—a É—akin shi tare da maida kyauran ya rufe. Wani tsadddan maine ya fiddo da ya saya daran jiya ya shafama fatar shi. Body spray na Tiraran Deal ya É—auka ya mulkama farar fatar shi. Tare da É—aukar wata farar vest da wando ya sanya . Kayan da Mamy tamai ya buÉ—a dan zaÉ“ar kala da zaisa,Anan yaga da Royal Blue , sai Brown, da Ash sune keda babba riga. Sai boyel Blue Black da milk. Royal blue din ya ÆŠauka tare da Addu'a saka kaya ya sanya wando da yar ciki ,hular data haÉ—amai da ita ta Æ™ayan ya sanya tare da fesama jikinshi tiraran Arabia oud mai sanyi, ya Æ™ara da Burmi oud ya murje jikinshi tare da murzama babba rigar daya baza bisa gado. Wani ni'imtaccen kamshi mai sanyi ya mamaye ÆŠakin. Ahankli ya É—auki rigar ya zirama jikinshi tare da kafa hula da agogo ya zura takalma. Masha Allah bi'ahsani khalik,shine Abinda Ammi tace sadda ta buÉ—e Æ™ofar tashigo, dan tinda taji kamshi ta tabbata yagama sanya kayan shi,Cikin tsanin so take kallon tilon yaron nata da yayi mata masifar kyau, kamar shi da mahaifin shi ta fito sosai.. Cikin murmushi yana zura links É—in hannu shi ya isa wajenta tare da kamo hannunta ya sumbata yace" Ammi nah Takabbalalahu minnah wa minkum. Kanshi ta shafa tace shukran laka . kaga yanda kayi kuwa Sadeeq É—ina , Yau Dee Appy nane ya fito kamar Ango, sadeeq dama rayuwa kanjuyawa , kaganka kuwa, bantaba sha'awar zamanka da iyali ba sai yau Dee da kayi wannan shigar, wallahi ka dace da zama magidanci sadeeq, ka taimakamun ka samoman yar da zata haifaman jikokina ingansu tin kamin rai yayi halin sa. Gabaki É—aya kunya yaji takama shi wane irin aure kuma, abun ma harda jikoki, kai Ammi yafada cikin Æ™asa da murya tare da sakin murmushi. Murmushin tayi tace to bari inje in'shiryama Hamrat itama kuwa blue zansamata kuyi iri É—aya ko? Kai ya jinjina mata yana kallon gefe dan wani nawie yaji ya saukar mai da tayi mai magana aure, Dan shi bashi da ra'ayi aure ,baya kuma kawoma rayuwar shi , to damai zai rike matar, ga baki É—aya albashin shi a tsare yake da hidimar ahlin shi, to in yayi aure kuma yazata kaya, wama wama zata so shi.? Ganin lokaci na tafiya ya sashi gyara sajen shi tare da fesa wani spray, take yakara kwanciya yayi shar -shar ga fuskar shi. Cikin tako na isa da wadatacciyar lafiya ya doso kofa É—akin Ammi ,a inda yashiga ya iske tama Hamrat kwalliya tayi masifar kyau, yarinya kamanni shi da ita sun fito sosai , Ga tulin gashinta na fulanin Asali yasha parking É—in Tsakiya, an'samata rigar mai hade da Bandana tsakiyar kanta. Tirare ya É—auka gefe yaci gaba da fesamata yana yaba kyan da tayi itama tana yaba nashi. Ammi ma tayi wankanta cikin lace din da aka bata tayi kyu sosai. Lokaci guda yaji sha'awar rike babbar waya da yanzu sai yamusu photo kodan tarihi.. Agulguje suka fito ya fitar da machine dinsa, Hamrat ta hau sai masallacin G.R.A na unguwar su Mamy kenan. Amma babban masallaci na Idi. Sahun farko suka samu dan karfe tara ake fara sallah sukuma sun iso tin 8:50. Sallah sukayi tare da addu'a kana aka fara watsewa inda kowa ya dinga fitowa masu photo nayi ma mutane,wasu nayi a waya, sai su karÉ“i number ka su turoma. Wani mai photo ne yana ganin ya fito da gudu ya doso shi yace" Yallabai dan Allah ka tsaya kaida ÆŠiyar ka inmaka Photo kyauta, wallahi kunyi kyau Allah ya horemaka kyau da zati. Murmushi yayi tare da gyarawa ya musu photo masu kyau shida Hamrat har ukku, kana ya Æ™arbi number shi tare da cewa zai Turo mai ta waya. A takaice "Yace bana da waya" . Cikin mamaki mai photo ya kalleshi zai magana ya wuce batare da yace komi ba. Cikin natsuwa yake tafiya shida Hamrat suna Dan labari. Assalamu Alaikum . Yaji wata murya tamai sallama cikin sanyi......âœï¸ 5/18/22, 09:34 - MY MTN 2: 🌹ƊAN DAKO MALLAKI🌹 🌹UMMY AYSHA 🌹 1ï¸âƒ£5ï¸âƒ£&1ï¸âƒ£6ï¸âƒ£ """Shuru yayi dan yanajin kamar ba dashi ake ba. Sallama ya sakeji a karo na biyu hakan yasa ya dakata da tafiya ba tare da ya juya ba. "Yallabai girmankane dan kazama mai shariya, Amma karka manta ita sallama Allah mai girma ya umarcemu da am'sata a duk sadda akamuna,Dan haka Assalamu Alaikum tasake mai maitawa . Ahankli ya juyo dan tabbatar wa kanshi dashi ake ko-ko? Wata mummuna faÉ—uwa yaji gabanshi yayi da mugun Æ™arfi lokacin da idanuwan shi suka sauka akan fuskar kyakyawar budurwa dake gaban shida. Ta kasance wanka TarwaÉ—a ce ,Amma tana da kyau sosai, tana sanye cikin Abaya Black sai sheki take ,ta yane kanta da mayafi tayi fess da ita hannuta riÆ™e da Iphone É—inta. Tsayuwar shi ya gyara sosai batare da yabari fuskar shi ta tona asirin zuciyar shiba,Na É—imuwar da ya shiga da ganin ta. Murmushi ta saki tace "Uncle Dee Dama zuciyana bata taÉ“a Amincewa da mutuwar kaba Wallahi ,bantaba tinani samunka cikin garin katsina ba,Saboda . Ya isa Bily,ya isheki, kisani yanzu ba da bace, kana zanmanta da alÆ™awarin dake tsakanina dake zan miki wanki babban bargo , kikama kanki fiye da yanda na kama kaina , Dan yazu ta canza zani... Murmushi ta saki sosai tace "Dee kenan! nason dole a wannan karan kaji ka tsani kowa, Dan duniya tamaka hankali ,Amma wallahi billahi ni Bily rayuwata cike take da tausayin ka, da Æ™udirin taya ka cimma burinka, fatana kabani dama kawai. Shekeke ya kalleta tare da fincikar hannu Hamrat suka tafi. Kai Bily ta dafe tare da faÉ—in allah ya taimakeka akan abinda kasa gaba Dee, ina nan ina bibiyar lamurranka har sai na tayaka cimma burinka.. Waya ta zaro tare da magana ,sai kuma naga tayi gaba cikin sauri tare da tsayawa da mai photo nan ta bashi Damen kuÉ—i ta wuce abinta ta faÉ—a cikin mota. Wani matashin Saurayine zaune fari kal dashi tace" maza Abul khairi kaini gidan su Amnah, na mata Alkawari zuwa. Kai ya jinjina tare da tada motar suna tafiya suna fira cikin nishaÉ—i. AÉ“angaran sadeeq kuwa takaici da kuma É“acin ran ganin Bily cikin rayuwar shi lokacin da baya sa buÆ™atar kowa.Hakan yasa ya fasa zuwa gidan Mamy kai tsaye ya fara yawa da mashin kota ina cikin katsina, har inda baitaÉ“a takawaba kusan tsawon shekara takwas da zamanshi saida yaje. Tin hamrat na murna yana yawi da ita har tagaji tafara rihimar ya mayar da ita gida. Tafiya yake yana waiwaye saida ya Tabbatar babu mai binshi kana ya fara bin lunguna, har saida ya cimma unguwarsu kana ya sauke ajiyar zuciya. Abanza ta sashi karya alkawarin,da yason da haÉ—uwar su mizai kaishi masallaci g.r.a ,da wani zaije tinda akwaisu da yawa. Gida suka koma Ammi na tamai faÉ—a akan Baizo ya kaima Mamy abinci ba , Dan tayi sinasir da alkubus da miyar kajin da takaimasu, da yawa tazuba akuloli manya ta aje da niyyar ya kaimasu. Hakuri yabata tare da faÉ—in tabari sai bayan sallah la'asar ya kai. Wanka sukayi sukaci abinci suka fara fira cikin jin daÉ—i. AÉ“angaran Bily kuwa tana zuwa gidan su Amnah bayan sunshiga get din ta ma Amnah waya akan Ta shigo. Da sauri Amnah da tasha wata kafurar kwalliya cikin wani skit da riga na lace Royal Blue ta fito cikin tako da yauki ko ina na jinki na juyawa, bakajin komi sai kamshin da take zubawa. Ƙasa ta sakko tace Mamy nayi baÆ™i zan'shigo dasu. Baki many ta taÉ“e dan har lokacin bata sakar mata fuska sosai. Tashi tayi ta haye sama abinta. Asanyaye ta fita daga gidan tana tafiya cike da natsuwa . Masha Allah itace kalmar da Abul khairi ya furta lokacin da yayi tozali da ita kamin ta Æ™araso yace" Bily wannan mai zafin fa.? Murmushi tayi tace'' ka rufama kanka asiri wallahi ita É—an sarkine burinta , Dan batason koda dan gomna ne,Tafiso tana tafiya ana mata kirari . Yace Abu mai sauki mu yan duniya har an'fadamana Tako! tsaya kiga Ya wani sha mur tare da kishin giÉ—awa ya fiddo dalleliyar wayar shi yana chart din bogi. A'hankali ta Æ™araso wajen tare da buÉ—e bayan motar tashiga ba tare da ta rufe ba. Bily ta jiyo cikin murmushi ta bata hannu suka gaisa. Tare da cewa" na sameki lafiya?.. Cikin isa da Aji na ya mace tace" lfy kefa.? Alhamdulillah ta amsa tana murmushi . Tace muje ciki ko?.. Bily tace Amnah baki gaisa da Prince ba... Wata irin faÉ—uwar taji gabanta yayi batare da tace komi ba ta buÉ—e motar ta fita. Da ido ya bita ganin yanda take tafiya albarkacin halitun ta nata juyawa. A rikice yace dan Allah Bily karki yarda ki fito saida zuciyar ta ahannu, ni kuma zan saya ko nawa ne dan Allah,Wallahi son gaske nike mata auran ta zanyi. Kai ta Æ™adamai tare da fita tabi bayanta har palon Mamy. Hannu Amnah ta kama sukayi sama É—akinta ta fara kawomata abinci da drink anan suka fara fira yaushe gamo. Amnah tace Bily ya naga duk kincanza kinÆ™ara kyau fa?.. Murmushi tayi tace" ai'kedai aka bari baya, nayi- nayi kizo inÉ—oraki ahanya kinÆ™iya ,Kullum sai dai ki kawana da takaici kibi maza subaki mazajen kudi, ki zauna gida kiga abun da ya samu.. Amnah tace Bily ina masifar tsoro wallahi, ni dai kamar bazan iya ba. Tsaki tayi t afara tsaramata yanda zasu kasance. Bily tace kinga wannan cousin É—inane É—an gidan Abdul mutallab ne sarki maici yanzu, shine babbn É—ansa amma baya da buÆ™atar hawan sallah, shiyasama na samu dakyal ya biyoni dan sauran yan uwansu duk suna bisa dawakai yanzu haka, Amma shikam duk ya É—auki abin bidia,gashi Babban likitam kwalwa Amnah, Gaya baya ko magana Saboda jinin Sarauta dake yawo jikin sa. Murmushi Amnah tayi tace" kinson duk yanda namiji yakai ga aji ni ya mace nazarce shi, dan haka koda yaÉ—an hada wasu abubuwan amma ba duka ba bazan iya tunkarar saba , Dan haka kibarshi kawai indai har lafiyayye ne to zai kawo kanshi... Dariya Bily tayi tare da faÉ—in shegiya Æ™awata kingano inda na dosa kenan, kina wuta ,wato ashe kinama sane da tarkon ki ya kama kurciya kenan, to wallahi kintafi da bawan Allah, Dan ba kiji yanda yake gamani da Allah akan inzo in karÉ“i number kiba. Amnah tayi Murmushi tace wlalhi duk da kinfadaman Prince ne amma som baiman ba, sai dai zanyi malege da shi, shima fa dan Aure ne da nike so. Tsaki Bily tayi tace" tin school nike fama Dake akan ki fara harka kisamu kudin da zaki magancema wani matsala shi bama Taki ba,bawai kullum gida kice abani dubu dari biyar ba Abaki ukku ace kiyi hakuri wallahi Amnah yaci ace wayewar ki ta zarce wannan gida dancin da kike,mene ma matsala daga shan mint?. Harara Amnah ta zubamata tace Wallahi ko abinda kike turomun inajin daÉ—i ne a lokacin da nike kallo, amma da lokacin ya shiÉ—e ina fadawa duniyar dake cike da tashin hankali, abun baza ace komi ba Bily, kawai iyayena su taimakamin suman aure, danshi Abba babban burin shi da ya dawo yasamoman aiki infara zuwa Asibitin shikenan. Amma ke kanki kinson yanda nike da ajin nan mijina ya ganni a banzace aiko ajin ya tashi a banza. Bily tace "to yanzu kina da masu zafi ko in turomiki? Amnah tayi shuru sai kuma tace kituroman amma wallahi Bily. Dariya Bily tayi tace" bari intashi in wuce yana jira na. Da sauri Mamy dake tsaye jikin kyaure ta zarce ÆŠakin Amal hankali tashe tana yarfe hannu. Illahirin jikinta rawa yake dan Ta sauka falo taga wayar bily anata kira shiyasa ta haura takaimata, ashe rabon zataji mummunan zance. nashiga ukku kardai ace Amnah halin mahaifinta gareta, Innalillahi. innalillahi wa inna ilaihi Raji'un, Ya Allah. Da sauri ta É—auki wayar ta ta kira Hajiya Turai ta fashe da kuka tana bata labari. Ciki Æ™aÉ—uwa tace ta tsaya ga tanan zuwa. **** AÉ“angaran sadeeq kuwa bacci sukayi su duka gidan, sai da la'asar ya tashi yayi wanka ya maida shadda shi. "Yace ma Ammi ta shiryama Baby ya kaita wajen Mamy. Da to ta amsa ta shirya Hamrat tare da fiddo masu kulolun data zubama Mamy abinci tace yakai mata. Yana dawowa suka É—akko hanyar har gidan Mamy . Suna ajiye machine Hamrat tace ''Baby kalli bishiyar mango Dan Allah ka kaini in tsinko. Yace aa Baby ba nawa bane ,babu kyau kinji sai ka tambaya. Kai ta É—aga mai tana bin mango din da kallo. Hanun ta ya kama suka Æ™arasa bakin kofar. Bayan ya kwan-kwasa kofar Mamy dake zaune idonta ya kumbura dan kuka . Tasowa tayi ta buÉ—emai duk tinaninta Hajiya Turai ce ta Æ™araso. Gaisawa sukai ta kama hannu Hamrat ta rike tana mai tambayar lafiya Ammi. Gaisheta Hamrat tayi tana faÉ—in lfy klau tana gaidaki gashi tace akawomiki. Kulolin ta karba tai ta godiya tare da cewa" Sadeeq kayi kyau sosai Amma Autata tafika kyau, kushigo ciki kuci abincina nima mana. Yace A'a Hajiya zan jirata inta fito mutafi. a koshe muke yanzu mukaci abinci. Mamy tace ta shikenan Hamrat ina barkana da sallah ? Baki ta rike tace "kai ai Baby ya hanani karÉ“a, saboda yankema mutum hannu ake ,kinga aka yankeman hannu dami zanci Abincin ammi nah. TaÆ™arasa cikin Alhini tare da duba yatsun ta. Dariya tayi tace hakane Babu ma wanda ya isa ya yanke miki hannu insha Allah, zaki kwana wajena?.. Kai ta gigiza da sauri tace" A'a Hajiya bazan iyaba gaskiya Baby muje gida. Dariya many tayi sosai ta rungumota jikinta tace karki damu bazaki kwanaba amma wani lokacin zakizo ko. Kai Hamrat ta Daga mata . Mamy ta É—ago ido ta kalleshi dai -dai lokacin da ya kalleta yaji gaban shi ya faÉ—i. Ganin yanda idonta yayi sasur . Da suri yace Hajiya lafiya dai naga kamar kinyi kuka Allah yasa dai bawani abu ke damunki ba.? Murmushi tayi tace "aa karka danu Sadeeq babu komi. Yace shikenan allah ya qarware miji matsalolinki kamar yanda kike warware na mutane . Ameen Ameen ta amsa cikin jin daÉ—i.. Yace Hamrat shiga kifito muje gidan Nene ko. Mamy tace aa bazatajeba gaskiya, kai kaje inka dawo kwatafi. Fita yayi yana dagamata hannu suka rufe palon Mamy ta zaunar da ita akan kujera suna fira. Yana fitowa ya nufi wajen machine dinshi dai -dai lokacin da motar su Hajiya Turai ta turo kai cikin gidan , sukai parkin kusa da machine dinsa. Fitowa tayi tana kallon shi kallo na rashin sani . Gaishe ta yayi tare da tada abinshi yayi gaba. Cikin gidan ta shiga tare da tadda mamyy zaune tana shafa kan Hamrat dake cinyar ta ,dan har tasoma sakin hamma dan Hamrat badai bacci ba.. Bayan ta zauna sun gaisa take tamabayar waye yafita a machine.? Mamy ta bata Labarin alakar su har zuwa kawomata Hamrat da akayi yanzu. Kai ta jinjina tana faÉ—in yanzu ya ake ciki game da lamarin Amnah? ,ya zama dole fa a aurar da ita cikin Æ™anÆ™anan lokaci,inba hakaba matsala da zata kunno nan gaba wallahi sai tafi ta baya,kana in son samune abata wanda baida yawan Ahli, Amma akai kuskuran kaita gidan sarauta toke kanki sai zaman Katsina ya gagareki,Kana a lokacin ne mahasada zasuyi tsalle suyi shewa ,Alokacin ne zasu nunamiki ikon da kike faÉ—in kina dashi akan y'arki ya tashi abanza, Dan haka shawara ki fita ki nema ma Amnah miji. Cikin damuwa Mamy tace nashiga ukku ni Saudat,Inaji kamar in aura mata ALMAJIRIN GIDA NA da ina dashi,koda kuwa yaro ne cen sutafi suyi AUREN YARINTA,Saboda kullum maganata ita gada wanda ta CANCANTA,Hajiya turai ina tsoron É—iya ta ta fara mu Amullah da Æ™awaye yan ZAMAN TASHA,kwara nidai in tafi koda masallacine in samo ko liman ne in auramata, da tarbiyyata ta lalace kwara ace tana AURAN USTAZ ,duk da nason halinta nason dole hankalin ta ya tashi, to Amma da in kasance kullum cikin magana TAYA ZAN GANE Wanda ya lalata Rayuwar Yata kwara ko ÆŠAN DAKO Na samu In bashi. Hajiya Turai tace" wannan magana taki haka take, Dan Wallahi kyan Amnah tasamu dan gida wanda zai tausayamata ya riketa da mutunci , Wallahi Hajiya fulani da ina da Yaro saurayi dana haÉ—asu aure, Amma Allah bai bani ba sai Sudais kuma kinga ko shekara goma bai kai ba. Mamy tace nasani wallahi ,nason fiye da haka zakimun, tashi tayi tare da É—aukar Hamrat tace bari in kaita É—akin Amnah nan Æ™asa nason tana ciki. Hajiya turai tace kifa kula da yawan kebb kanta da take Wallahi, Tinda har tafara faÉ—in aure takeso to kijawota jiki kiji wanda takeso kuma ki fahimci yanayin da take tafiyar da Rayuwar ta.. Mamy tace'' insha Allah tare da tura kofar ta shiga cen ta hango Amrah cikin É—akin tana waya bakajin koda abinda take cewa. Tana ganin Mamy tayi saurin katse wayar tare da mikewa tana zare ido. Kwantar da Hamrat tayi ta juya ga Amnah tace'' mikike É—akine ke É—aya? kinki zuwa ki gaida uwata kuma kinyi zaune kamar mai jego ,to bani wayar ki nan in ita ke saki kebe kanki daga gareni. Wani irin kyar ma jikinta ya É—auka tace Dan Allah kiyi hakuri bazan sakeba Yayan Bily ne ya kirani Wallahi. Tsawa Mamy ta dakamata tace babu ke babu wannan yar iskar yarinyar, dan bataiman ba, bani nace. Cikin É“arin jiki ta mikamata tare da dafe kirjinta tason shikenan tashiga ukku ta lalace, gashi bata sama waya security balle ta samu saukin wani abu . Fita Mamy tayi tare da kama hannun Hajiya Turai suka haura sama É—akin ta. Tace dole yau in'son ma dawa take mu'amullah, yarin ya kullum waya a hannu.. Anan ta fara bincikawa contact taga number ukku ne , Daga ta Bily, saita Æ™awar ta Dr fatima Bello, sai wata Khairy Barno duk Æ™awayen ta ne. Message ta shiga taga babu komi . Har zata ajiye wayar takuma shiga gallary. Hankali tashe ta mike tana murza ido tace" Hazbunallahu wani imal wakim, A gidana, yar dana Haifa ,Nayi sakacin da na barta tana kallon wayan nan yan iskan Vidio, kuka ta saki tana miÆ™ama Hajiya turai wayar. Kallo tayi taga BF ne sunkai É—ari cikin wayar gasunan babu tsari. Hankali tashe tace Fulani in har kika bar Amnah ta Æ™ara wata É—aya cikin gidan nan wallahi akwai matsala,Kuma kema zaki samu rabonki awajen Allah, kawai kinson gadon masifa tayi dan haka cikar mutun cinki da nata ki miÆ™ata É—akinta, ki samu kowayema indai kin yarda da tarbiyyar shi toki auramai kamar yanda musulunci yace. Cikin kuka Mamy tace insha Allah daga nan suka shiga tattauna yanda zasu bulloma lamarin. Abangaran Amnah kuwa safa da marwa kawai take cikin É—akin hankali tashe, tana tinanin ya zatayi in Mamy taga abunda take Ai katawa. Tinowa da Hajiya Turai na cikin gidan ya sata sauke ajiyar zuciya dan ta tabbata magana suke, zatayi amfani da damar ta É—auke wayar ta goge komi kana ta mayar mata. Da wannan gurguwar shawara ta samu natsuwa. Wajen shidda saura Hamrat ta tashi tana faÉ—in zanyi fitsari Hajiya akaini Fitsari Dan Allah. Kallonta Amnah tayi tace masha Allah, Allah yasa in na hauhu in'haifi irin wannan kyakywar yarinya, ko ina Hajiya turai ta samota. Azahyure Hamrat tace wayyo babu zaimun duka Dan Allah zanyi fitsari. Amnah ta tashi da sauri takamata tashiga toilet tayi ta gyara ta kana suka fito. Suna fitowa ta kalleta tayi Murmushi tare da shafa dogo'n gashinta tace Baby ya sunan ki? "Sunna Hamrat.* Tabata amsa. Amnah ta jinjina kai tana kallon tsadaddun kayan jikinta kai da gani kason iyayanta sun jiÆ™u da nera,Haka takeson taga yara yan gayu. Hamrat tace "Aunty dan Allah ki kiramun Baby ya maida ni gida ,na gaji inaso inga Ammi nah fa. Cikin mamaki take kallonta tace waye Baby? To kiyi hakuri sugama za kutafi kinji ko ,zakici Abinci ne? Hamrat tace aa nagode. Amnah tace to mikike so? Cikin yarinta tace wallahi Mango Amma Baby ya cemun bakyau ka É—auka saika tambaya, nikuma ina so. Amnah tayi Murmushi tace to "muje in tsinko miki. Da sauri ta taso ta biyota tana murna. Hannuta cikin nata suka fito har cikin lambun gidan. Suna isa Amnah tayi tsalle Amma takasa kamowa dan yayi sama. Tsalle ta Æ™ara dakawa amma bata kamo ba. Hamrat tace Wallahi Aunty zanyi kuka, kiyi girma irin na Baby mana(TantaÉ—o) Dariya tayi tana faÉ—in karki damu zakisha kinji sweety nah. Dai-dai lokacin Sadeeq ya shigo gidan Amma bada machine din saba, Dan yabar shi waje dan kar ya yita wahala shiga da fita, Tin da Hamrat zai mayar gida.. Tsalle Amnah ta daka sai gata ta ciro wani danye, dariya ta saki Hamrat kuma tayi ihun murna. Hannu Amnah ta bata suka kashe tace" Bari in sakeyin wani tsallan sai in baki wancen Æ™aton ko? Cikin jin daÉ—i Hamrat ta É—agamata kai. Ihun ta yasa shi kai duban shi wajen . Anan ya hangosu Amnah nata daka tsalle. A gabanshi ta sake wani wahallan tsallan dayasa rigar ta mikewa farar fatar cikin ta ta bayyana, Yayin da Albarkacin kirjin tama suka daka tsalle. Faduwa yaji gaban shi yayi sosai . Siririn tsaki ya saki tare da nufar wajan su cikin takon isa da Æ™asaita. Baitsaya komi ba yayi sama da Hamrat tare da fadin Baby tsinko . Cikin ihu tasa hannu ta É—akko biyu tana faÉ—in" sai Baby. Afurgice Amnah ta kalleshi shima ita yake kallo . dai -dai lokacin da Mamy da Hajiya Turai suka fito da niyyar yimata rakiya. Ido suka zubamasu suna kallo ....âœï¸ 5/18/22, 09:34 - MY MTN 2: 🌹ƊAN DAKO MALLAKI 🌹 🌹UMMY AYSHA 🅿ï¸1ï¸âƒ£7ï¸âƒ£&1ï¸âƒ£8ï¸âƒ£ """Wani Murmushi Hajiya Turai ta saki tace "Ƙawata ashe kina da Nama har gida amma kike fama da maita, to mukoma na fasa tafiyar sai nayi Sallah. Cikin Rashin fahimtar inda magan'ganun ta suka dosa Mamy ta bita suka shiga. Hannuta Hajiya Turai ta kama har ÆŠakin Amnah na Æ™asa ,inda ta isa da ita wajen window ta zuge labulan tace" kina ganin abinda nike gani kuwa? kwalwarki na faÉ—amiki cancanta da sukayi da juna kamar yanda tawa ta nuna man? Fulani Allah ne yakawo miki Dama har gida shiyasa ya samiki soyayyar yaron da bakison ko waye shiba, Fulani yanzu kika gama ceman zaki iya ba ALMAJIRIN GIDA'nki Amnah,To tinda baki dashi amma ga ÆŠAN DAKO ko? Dan haka kinga shine kawai zai rike mutunci y'arki, Tinda kin yaba da halayyar shi ,kuma kin yarda ba macuci bane, Tinda har yataÉ“a É—aukar ta suka wulla wani wuri yakuma yimata Hukunci akan Abinda tamai ya maidomiki abinki,Abu na biyu kuma ga shi baya É—aukar raini ,Na tabbata bazai yarda Amnah ta dinga mai abinda take so ba ya kyale ta. Darasi na ukku da zata É—auka shine zama da talakka. Tason daraja shi ta kuma haÆ™ura da buÆ™atin shi dole ,saboda da ganin sa bazai yarda da Halayyata ba. Kinga kin jefi Tsuntsu biyu da dutsi É—aya kenan fulani. Na farko kin kaita inda za'akula da ita. Na biyu kin kaita inda rayuwa zata koyamata darasin girmama É—an Adam, da kuma sanin daraja talakka tin kamin Duniyata ta bankaÉ—o tsohon Sirrin dake binne cikin Æ™asa ... Wani irin tsuma jikin Mamy ya É—auka sai kai da komo take tana yarfe hannu, tana ta Auna magana Hajiya Turai a mizani daya dace, tabbas ta yarda da maganata,To amma waye shi ,Ina dangin sa shima sadeeq din, koda bata tambayeshi ba bata taÉ“ajin yamata wata magana ba,Karfa suyi Abinda zasuyi dana sani. Cikin jimami tace'' shawarar ki haka take Aminiyata , Amma kina ganin zai amince? Nasha faÉ—amiki baya jire raini wayo, kar zuciyar shi tabashi kamar dan in haÉ—a shi da Amnah nike kyautata mai, bayan bayan ni Wallahi billahi dan Allah nayi. Murmushi Hajiya Turai tayi tace A'a bana tinanin hakan daga gare shi insha Allah. Amma kamin nan yana da kyau muyi istakhara dan neman zaÉ“in Allah, duk abinda kika natsu dashi to ki dunfareshi kai tsaye, Allah zai warware komi ,mudai mafita muke nema. Kai Mamy ta jinjina cikin gamsuwa tare da Æ™ara zubama Windon ido inda ta gansu Amnah namai magana da hannu tana jawo Hamrat shikuma sai binta da ida yake yana nuna ta da yatsa kai kace magana soyayya suke . "Tsananin dace wa fa sunyi Fulani, jibi kayan jikinsu wallahi ni in'bama idona gizo yakemun ba kama suke sosai. Hajiya Turai da ta dafa kafaÉ—ar Mamy ta faÉ—a cikin zakuwa. Mamy tace "magana ki dutsi, inshaah zanyi yanda kika ce. AÉ“angaran su Amnah kuwa cikin sanyi tace" ka sauketa mana, ya daga ganin yar mutane zakayi sama da ita ka ajiyeta fa. Shareta yayi ya sakko Hamrat ya kama hannuta da niyyar tafiya. Da sauri Amnah ta rike hannu Hamrat tana mai zubamai ido tana tabe baki. yayi da shikuma yake mata kallon sama da kasa na ganin raini wayon da takemai . Afusace yace bazaki sake ta ba muwuce. Itama cikin fusata tace" bafa tsoronka nike ba, karkaga inama magana cikin sanyi kayi tinanin wai tsoro nikeji, A'a ina gudun fushin mahaifiyata ne ,daga ganin yarinya saika fita da ita, wannan dacewa ce ko tarbiyya ce? kabani amsa mana. ta faÉ—a cikin ihu tana yarfe hannu. Cikin takaici yace Ƙanwar kice ko Æ™anwa ta? Babu ko É—aya amma kaima miye matsayinka wajen ta, ina kai ina wannan yarinya. Bar ganin kasha wasu kayan aronka cen kazo ka rainamun hankali fa. Hamrat tace "Aunty Baby nefa kikema ihu . Baby kayi hakuri kema Aunty kiyi Hakuri babu kyau manya na faÉ—a ko Baby? muje gida inga Ammi nah.. Tsororo Amnah tayi dan sai yanzu ta lura da masifar kamar da suke, kenan Æ™anwar sace take ta lallaÉ“awa haka,. Waji shegen tsaki ta saki tana juyawa cike da takaicin kanta,Jibi.yanda tazage tana mata hidima. Shima tsakin yayi yana faÉ—in mahaukaciya kawai. ya kama hannu Hamrat suka tafi. Da sauri Mamy ta zuge glass din window ta kwala mishi kira. tsayawa yayi tare da juyowa yana kallon saitin da take. Da sauri ta cemai ina zuwa tashiga É—akinta ta É—akko wani Æ™aramin akwati ta fara loda kayan yara da take saidawa kala- kala aciki, Masu kyau dana wasanni ta haÉ—a da sabbin kudi dubu ashirin ta tura ciki, kana ta jawo ta fito fuskar ta asasure da kumburi. Hajiya turai tace kwara kiÆ™ara lafkacewa tin yanzu ya gano kina cikin tsananin damuwa, in ya tambayeki fashe masa da kuka. Murmushi Mamy tayi ta fita. Cikin sanyi tace" Sadeeq da tafiya zakuyi babu ko sallama . Kallonta yayi cikin tausayawa yace" Hajiya yau fa naga kamar bakyajin daÉ—i, kuma kar a barta ta isheki da surutu, kwara mu wuce kawai. Gefe Mamy tayi da kai cikin damuwa tace" katayani da addu'a sadeeq , Allah ya sauÆ™aÆ™a lamarina, ya kuma kawoman komi cikin sauki. Ameen yace yana gyara tsayuwar shi yace. ' "Hajiya in kinson zan iya taimakamiki kifaÉ—aman Amma bawai tilasti bane, Wallahi billahi kullum Addu'a ta Allah ya kawo ranar da zaki nemi alfarma wajena kowace irice na miki Alkawari zan miki ,in kinson zan iya shiga hurumin abin kifaÉ—amun duk girman HaÉ—arin sa, in'kuma kinson ba hurumina bane to zantayaki da Addu'a Allah ya warware miki matsalaki . Ya Æ™arasa yana zubamata idanuwa.. Cikin lokaci hawaye suka fara gudana Acikin idonta. Tace Sadeeq kamun alÆ™awarin magancemun matsalata ? Cike da kwarin gwiwa yace insha Allah indai bata saÉ“ama Addini na ba. Murmushi tayi tace'' shikenan nagode inka samu lokaci gobe Kashigo da wuri sai ka kaini gidan Nene . Kai ya ÆŠagamata tare da faÉ—in insha Allah. Hannu Hamarat ta kama ta turamata É—an madai-daicin akwatin tace Autata ga kayan wasa .ai kina wasa ko? Da sauri ta kaÉ—a kai tace" inayi ,shikenan ma nasamu abun wasa bazan sake bacci ba ko Baby?. Kai ya ÆŠagamata tare da yi ma Mamy Godiya . Tace yawwa bama sai ka dawo ba kayi zamanka gida sai gobe insha Allah. Godiya yamata suka wuce. Bayan sun isa gida Hamrat taita yaba kirkin Mamy da Aunty Mai kirki' tana ba Ammi labari. Farin ciki sosai tayi tace'' lallai Aunty Mai kirki wato har kinmata suna kenan. Sadeeq ya taÉ“e baki batare da yace komi ba. Cikin damuwa yake faÉ—ima Ammi halin da yake ganin Mamy yau ciki kamar ba bikin Sallah a keba som batada walwala. Ita kanta duk sai taji bataji daÉ—i ba saboda kyautatawa ta garesu tafi gaban ace tana cikin damuwa suyi burus.. Cikin sanyi tace musata Addu'a Sadeeq. Daga nan yaje masallaci,sai da aka gama isha kana ya dawo gida yayi wanka da wuri yama Ammi sallama yashige É—aki. Itama É—akinta ta kama Hamrat suka shige abinsu. Yana shiga É—akin yahi ya cire haramin sa tare da É—aukar wani Æ™aramin towel milk ya É—aura ma kugun sa . Wajen wani babban madubi dake É—akin wanda ke like da bango yaihi tsaye ya tsirama faffaÉ—an kirjin shi ido Ko kyaftawa ba yayi. Ahankali yasa fararan dogayen yatsun shi ya fara Zagaye wani babban tabo dake kasan zuciyar shi wanda yayi kama da halbi bindiga. Lotsa wurin yayi da Æ™arfi baison sadda yayi Æ™aramin ihu ba yace ashhh. Jajayen idanuwan shi suka kaÉ—a sukayi jawur. Da sauri yake lailaya wurin yana cije leÉ“e . Afusace yace "kamar yanda nike jin zafin nan haka nike fatan ku Æ™are rayuwar ku cikin zafi da bakin ciki, Baku Raunata banza ba, ina nan dawowa gareka bada jimawa ba. Alkawari nayima rayuwata duk ranar da wani wanda ya sanni ya ganni to tabbas zaki zai koma Dawa. Wata daya.. Wata biyu... Wata ukku.. Kacal na É—ibar ma rayuwa Ahalin dake zaune daram akan kwaraga zalinci. Zan yanke maku farin ciki kamar yanda kuka yanke nawa,Kukasa Kasata ta gagareni zama, haka zan koreku da rarrafe kubar iyalan ku. Daga nan Kurar da ta daÉ—e da yunwa zata fara fatattaka naman jikin ku dana Ahlin ku. Daga nan ne angulu zatayi dirar mikiya gidanta na tsamiya. Cikin wata irin fuskar da bantaÉ“a ganin shi ba ya juya ya faÉ—a kan katifar shi, tare da É—akko sistem dinshi ya fara aiki yanayi yana latsa waya, tare da magana da banajin miyake faÉ—a dan cikin wani bahagon yare yake magana. Sama da awa É—aya kana ya ajiye ya kwanta. Washe gari kamar yanda ya saba bayan yaje masallaci ya dawo yayi shiri cikin boyel din da Mamy tamai wanda yayi masifar yimai kyau, ya kashe hula tare da feshe jikinshi da turare . Break Ammi ta haÉ—amai yaci ya koshi kana yamata sallama ya tafi. Hamrat tayo mai rakiya tana faÉ—in ya gaida mata Aunty mai kirki. Banza yayi da ita ya kyale tare da fita da machine É—insa. Kai tsaye gidan Mamy ya nufa . Waya ya mata akan ya iso. Tace "to sadeeq gamunan fitowa. Shuru yayi yana mamakin to wai daga Dan Dako driver ya koma kokuwa? tinda yaga in'zata gidan Nene ita kekai kanta ko Æ´aran ta, toshi minene nashi? KafaÉ—a ya idaga irin ko ajikin shi yaci gaba da zaman jiranta. Bayan 30mnt ta fito cikin shiri har lokacin fuskar ta akwai fushi kaÉ—an, suka sake gaisawa, saiga Amnah ta fito cikin wata dakekiyar shadda pich da tasha kwalliya Royal blue, komi na jikinta royal blue ne. Ganin idon Ammi ya sata cemai "ina kwana." Sarai yajita amma ya shareta sai motar da ya faÉ—a . Bayan Mamy ta shiga tace ma Amnah shiga gaba. Kallon Mamy tayi sai kuma tayi saurin buÉ—ewa tashiga tana turo baki ganin yanda Mamy ta dallamata harara. Cikin natsuwa yake murza sityarin ya É—auki hanyar gidan Nene. Dai-dai Rowl É—in Lada wapa traffic ya tsaida su. Anan ya maida hankalin shi akan mutumin daketa binshi akan machine. Gaba ki É—aya'n Hankalin shi ya maida kan tukinshi ganin anbasu hanya, yanayi yana kallon mutumin ta mirrow kamar ya taÉ“a ganin sa. Suna É—aukar hanya gidan Nene yajuya kan mota zuwa wata hanyar ta daban. Mamy tace Sadeeq lafiya kayi wannan zagayen. Arikice yana kallon mutumin yace Affuwan Hajiya zanyi abune. Shuru tayi yayin da Amnah keta zuba mai harara. Wata kwana ya gani ya bulla ta ciki yayin da ya fado ta hagu inda yaci gaban mai machine É—in ya rufeshi ruf dan babu wata hanyar da zata fitar dakai . Da sauri ya tsaida motar tare da fitowa a fusace hannushi rike da sit belt din da ya ciro . Mai machine na ganin ya fito cikin tashin hankali ya fara neman hanyar da zai bulla, dan sadeeq ya riga da ya datse hanyar baki É—aya. Da sauri ya fara Æ™oÆ™arin tada machine É—in dan juyawa amma karfen bature bashi da tabbas yaki tashi. Ganin da gaske ya Dumfaroshi yasshi aje mashine din ya fara Æ™oÆ™arin guduwa. Cikin zafin nama Sadeeq din yayi taku biyu ya taÉ—emishi Æ™afa sai gashi ya faÉ—i. Hankali tashe Mamy ke kallon shi yayin da Amnah ke kallon ikon Allah" to miyami shi?. Hular kanshi ya tura baya yayin da yalwatacciyar sumar shi ta zubo saman goshin sa, tare da sanya Æ™afar shi dake sanye da takalma cover ya take yatsin mutumin. Cikin ta fasa zuciya dawata irin murya yace" waya turoka wajena?. Waye kai? Minaimaka?. Zan kasheka har lahira in kaima wanda ya turo ka kasheni gawar ka. Afurgice mutumin yace" Wallahi wata ce bansonta ba, Dan Allah kayi Hakuri. Cikin nazari yace" bakaine kamun photo ba jiya ?waya turoka.? Cikin rawar jiki yace" itace Yallabai, Dan Allah kaÉ—agamun yatsu zasu cire. Tsawa ya dakamai tare da faÉ—in wacece ita? kuma miyasa take bibiya na.? Nima bansani ba Yallabai, Dan Allah kayi Hakuri . To uban mi tace kabiyoni kamun yanzu? Cewa tayi inbika inga masaukin ka. Yabashi amsa cikin rawar baki. Murmushin mugunta ya saki tare da kwantar da mutumin ya danne mai duka yatsun shi na hannuwa ,Tare da riko Æ™afafuwan shi, zaro belt din yayi ya fara tsulama Æ™ugun shi. Ihu mutumin yake yana bazan Æ™araba Yallabai, Wallahi bazan Æ™araba, Dan girman Allah kayi hakuri ,ga wayatama ka rike bazan sake bibiyar kaba ,wallahi dan Allah kabari ,wayyo mazaunaina . Saida yamai bulala jamsin a Æ™ugunshi kana ya É—ago yana sharce zufa ,Æ™afar shi yasa ya halbi mutumin kana ya É—auke wayar shi ya dawo motar cikin murtuke fuska... Da fari Hankalin Mamy dana Amnah a tashe yake musamman da sukaga ya rufesu babu damar su buÉ—e su fita. Lokacin kuma daya naÉ—e mutumin yafara dukan mazaunans hi yasa Amnah bushewa da wata kafurar dariya cike da mugunta take dariya. Ganin yanda mutumin ke shure shuru. Ganin yanda ya dumfaro motar ne cike da sassarfa yasata binshi da kallo. Akaro na farko a rayuwar ta da taji jarumtar shi ta burgeta . Agaskiya tanason jarimin namiji, som bata muradin lusari, jibi yanda ya hukunta mutumin da basuson miya mai ba. Motar ya buÉ—e ya shigo tare da É—aukar tissue ya goge zufar data zubomai ga fuska . Mamy ta sauke ajiyar zuciya tace" Sadeeq baimaka komi ba dai ko? kuma miyamaka kamai wannan dukan? Motar ya tada tare da faÉ—in kibarshi Hajiya. Irin yan iskan nan ne da akeba kuÉ—i suna shiga unguwanni masu kuÉ—i suna ganin shige da ficcen su, Dan asamu damar kidnapping din Mutane, Tinda muk fito yake binmu kinga yanzu sai yakoma ma wanda ya turoshi ya kaishi Asibiti... Cikin tsoro da tashin hankali tace" Sadeeq kuma bugun nashi bazai zama aibuba, yanzu abunda mukeji cen wani garuruwan har yana neman ya shafemu. Zufar data cika sajen shi ya yarfe sai bisa fuskar Amnah. Da sauri ta kalleshi dai- dai lokacin da shim ya juyo ya kalleta. Batace komi ba kuma bata goge ba. Cikin Æ™asa da murya yace" Affuwan tare da mikamata Tissue. Ƙarba tayi amma bata goge ba , Dan sosai take jin yana burgeta da irin kasadar da yayi. A É“angare É—aya kuma tsoro yakamata tare da kudirin bazata sake fita ita É—aya ba, dole asama mata driver, Mussaman da take shirin fara aiki. Godiya Mamy tamai sosai da jajir cewa. * yace bakomi yiwa kaine. Bayan sunje gidan Nene ya sauka kan Mamy ma ta fito ya buÉ—e mata kofar tare da juyawa ya shige cikin palon Nene. Da ido Mamy ta bishi tana kissima abubuwa da dama aranta. Yana shiga Nene" tace oyoyo my lot oyoyo. Fuska ya yatsina yace"" gaskiya Nainah kidaina cemun my lot,Infa matata taji bazataji daÉ—i ba kina cemun masoyin ki. Nene tace yo daga abun arziki Allah ya kashe yabakani saddi ,Harma zaka raina. Yace to banaso kibani ruwa in'tashi in fita ga Hajiya nan . Nene tace yo Fulani micece! daga ganin ta saika tashi katafi dama dan ita kake zawa gidan ne ?. Yace hmm tare da duba gefen da yaji Ajikin shi kamar ana kallon shi. Karaf ko idon shi ya faÉ—a cikin na Amnah da tayi tsaye ta zubamai idanuwa . Fuskar shi ya É—aure sosai tare da mikewa ya buÉ—e fridge din Nene ya É—akko ruwa mai sanyi ya rufe . Ya daga murya yace" Nainah na wuce fa. Da gudu ta rugo tana haba" Kwandon Sukari sauran kaÉ—an kaja infaÉ—a cikin a kurkin tumatarina dan sauri, fura fa na ajiye maka naje É—akkowa. Mamy da ta shigo ta gansu sosai abun ya burgeta, kenan ya saba da Nene amma ita ko magana inba ta dole ba baya mata. Cikin zaulaya tace oniii Sadeeq! Wato nice ka kasa sakin jiki dani sai Nene ko. Cikin kunya ya sosa kanshi tare da kallon Nene ta gefen ido data saki baki tana kallon Mamy. Afusace tace ni dake matsayinmu É—aya, nima my lot É—ina ne. Da sauri yabar palon dan yaga Nene na neman sashi kunya. Abinci da ta haÉ—amai taba Amnah tace ke fitsarariya maza je ki mikamai, sala kigaya mai magana. Fuskarta ta yatsuna tare da Æ™arba ta fita ta iskeshi zaune Æ™asan bishiya yana ta latsa wayar wanda ya zane. Cikin isa da yanga ta Æ™arasa wajenshi ta ajiye tiren, kamar ta juya sai kuma tace Nene tace gashi. Sanin rashin cin magana zai jawomi wajanta yasa ya É—aga kai kawai. Harara ta zubamai tare da faydin sai isa shi ba kowa ba. AÉ“angaran Mamy kuwa f ÆŠakin Nene sukashiga anan ta koramata bayanin komi. Inda Nene tasa kuka tana fadin shikenan "Asirin mu zai tonu, maza shirya muje gidan mahaifiyar sa ayi komi yanzu,su su Amal din abarsu Anan. Mamy tace shikenan tare da miÆ™ewa suka fito. Suna fitowa ta iske shi tsaye yana waya. Sallama tamai ya ajiye waya tare da cewa mutafine.? Kaka tace ''Aa zamuje mugaida maman kane, muje ka kaimu a ida sanin juna. Gaba shi yaji ya wani buga da Æ™arfi, haka nan yaji bai samu natsuwa da zuwan nasu ba. Kanshi ya sosa yace" miyasa bazaku bari in É—akko maku ita ba.? Nene tace ai anzama É—aya. Yace shikenan muje. Hawa wukai sai unguwar Tudun wada. Sosai mamy ke kallon hanyar har suka Æ™araso Dan kofar gidan nasu. Tindaga bakin kofar zaka tabbatar da tsaftar masu gida'n. Fita yayi tare da musu nuni da gidan ya rufe Motar yace" Bissimillah. Da sauri Nene tayi gaba tana faÉ—in wai kuyi ta rangwaÉ—a saman Æ™asa. Ƙuda za'atausa ciki, ai'kwarama kayi sukuwa kayi yanda kakeso tin kamin ita ta dafe ka. Su dukansu Murmushi sukai suna bin bayan ta. Sallama ta rafka da Æ™arfi cikin gidan. Da sauri Ammi data gama girki tafito cikin shigarta ta kamala cikin daya daga kayan da Mamy ta mata ta amsa tana fadin sannu ku da zuwa ganin su da Sadeeq. Yawwa Nene tace tana faÉ—in in shigo . Mamy tace Bissimillah. Sadeeq da Mamy sukai sallama suka shigo. Fara'a fuskar Ammi ta Æ™aru tace marhababukum lale da zuwan ku. Sadeeq dama kana tafe da baÆ™i bazaka faÉ—aman ba. Yace Mamy banson da zuwan suba sai yanzu. Wannan itace Hajiya ya nuna Mamy. Wannan kuma Nainah . Nene tace kai tsaya my lot, Wallahi Æ™arya kake kace Nene ce ni kawai duk da kana gyara man sunan,Bari kaji Naira 1000 naje makka in'faÉ—amaka tin Duniya na zaune kalau, har zakaceman Nene babu Hajiya ba komi dan ragemun matsayi , kabar haka dan Allah. . Dariya yayi kadan yace to Hajiya Naina na dai na. Tace" yawwa kwandon sukari ko kaifa. Yace wai dan Allah miysa kike cemun haka? nifa ba yaro bane. Afusace tace na cema kwandon sukari daka buga tusa sai sukari... Da sauri ya faÉ—a dakin shi yana murmushi. Dariya Ammi ta tuntsure da ita tace "dole yake yawan maganaki ashe chapter kuke. Mamy tace" lallai kam, ni kaina banson haka suke ba sai yau, ta karsa tana kallon Bakin Ammi dake sanye da hakorin makka tabbacin har saudiyya ta taÉ“a zuwa kenan . Fira sukayi cikin mutuntawa ta zubo musu abinci ita da Mamy. Na Nene kuma daban. Duk da basajin yunwa Amma zama sukai sukaci sosai suka gode. Bayan sungama cin abincinne Nene tace dama magana mukazo yimiki da kuma neman alfarwa dan Allah Hajiya badan muba. Bakuma dan halin muba, sai dan rufuwar asirin mu, da kuma taimako da zakima baiwar Allah nan da batada wadatacciyar lafiya. Cikin mamki Ammi tace alfarma kuma Nene? To nikam mizaku nema ku rasa daga garemu bayan kunmana komi,Ai dan dai sada zumunci da nace bama sai kunzoba ,ta waya kaÉ—ai zamu iya magana. Nene ta share hawayen ta tace "mudai ya can-canci muzo. Ammi tace Nene ke uwace in kina mun kuka wallahi hankalina na masifar tashi , Dan Allah kifaÉ—amun mikike so kai tsaye, ko aiki kuke so in maku ?indai wannan ne babu komi zanyi wallahi. Mamy tace aa ba aiki bane. Nene tace kai tsaye alfarma muke nema ta haÉ—a É—anki sadeeq da Aminatu É—iyar Fulani Aure... Dam-Dam haka zuciyar Ammi tayi wani mugun bugu . A furgice ta mike tsaye tana ja baya tare da kaÉ—a kai .... 5/18/22, 09:34 - MY MTN 2: 🌹 ÆŠAN DAKO MALLAKI🌹 🌹UMMY AYSHA 🅿ï¸1ï¸âƒ£9ï¸âƒ£&2ï¸âƒ£0ï¸âƒ£ ""Wasu kwallah masu tsananin zafi suka fara ambaliya a kan fuskar ta. Cikin kuka tace'' Dan zatin Allah Hajiya Nene ku daina wannan magana inba so kuke kufamamun tsohon miin dake zuciyata ba,Tayama Sadeeq zai auri yarki, Bayan shida bashi da kowa,taya zayyi aure babu magabata,Hajiya ina son yarona yayi aure amma gudun tonuwar wani sirri mu na kyaleshi har zuwa yanzu da yake cikin shekara ta 32, Jiya jiyan nan nagama mishi magana aure , Sai bayan yatafi kuma naga hakan ma kuskurene,kwara muyita zaman mu haka cikin guntun farin cikin da yafara ratsa zukatanmu,shigowa da bare azaman takewar mu babban haÉ—arine, Shi ba kowa ba, ba komi ba Hajiya, Baidace kuyi tinanin hada yarki da Sadeeq aure ba. taÆ™arasa cikin wani irin kuka mai cin zuciya. Nenema hawayen take.Da kyal ta share tace "shikenan É—anki ne bazamu miki dole ba. Mamy kam kuka ta saki tare da durÆ™usawa akan gwiwoyinta tace" Dan zatin Allah Ammi ki taimaki rayuwata data yata dake cikin haÉ—ari da Æ™alubale, Wallahi bandamu da sanin kosuwaye kuba,nidai rokona gareku ku aminceman sadeeq ya auri Amnah saboda nagar tashi,Hajiya zuciyata namun radaÉ—in da take gaf da kaini Æ™asa,a wannan karan muddum nayi kuskuran da maÆ™iya suka samu galaba akaina to tabbas zansha kunya da kalaman dana furta abaya, kuma Wallahi zaman Katsina sai ya gagareni,dan zatin Allah kitaimakamun,.. Ammi tace" taya zan'taimakamiki wai? Yar taki muni ne da ita da kike neman mararaba da ita komi? Wannan wane irin bahagon zancene kike Mun? Taya mace zysta zo neman aure namiji haka al'ada ta tsara mana ne hayjiya? Indai kina ganin aikin da yake gidan kine zaisaki tilastamu akan abinda bamu da buÆ™ata to kiyi hakuri sadeeq ya daina zuwa... Wani irin kuka mai cin zuciya maganganun Ammi suka sanya Mamy,Cikin lokaci kam magana tayi sanadin tashin ciwon ta, cikin lokaci tafara wani irin tari tana dafe saitin zuciyar ta. Kuka Nene ta saki tana cire mayafinta ta ajiye gefe tare da tallabo Mamy data durkushe tana ta tari akan sawunta.. Ihu Nene ta saki ganin wani uban jini dake bin hancin Mamy da bakinta, lokaci guda idanuwan ta sunfara juyewa.. Ihu Ammi ta saki da yasa Sadeeq dake aiki da sistem nashi ajiyewa ya yanko da gudu ya faÉ—o É—akin. Cikin rawar baki yace" minene? mi akaimata Nainah? Ya Æ™arasa a rikice hankali tashe. Nene dake kuka ta ciccibo mai fuskar Mamy tace sadeeq kagani. Ciwon ta na zuciya yatashi, Wallahi Sadeeq itama zata mutu ta kyaleni, ina son Fulani sadeeq tinda yarin tatta tashiga matsaloli na rayuwa sosai ,wanda suka sakar mata da babban ciwo na zuciya,Sadeeq ka kamaman ita in kaita Asibiti, inda rabon ta tashi Allah ya rayamana, in kuma babu to Allah shi yason yanda zayyi dani. Nene ta faÉ—a cikin kuka sosai gwanin tausayi... Ammi dake gefe kuka kawai take baki É—ayan hannayenta akanta ,jitake inama babu wata alaÆ™a tsakanin sadeeq da su Mamy, inama ba Katsina suka yada zango ba inama ace Æ™auye'n Æ™ayau suka sauka,inda babu mutane . Wato shi Æ™alubale rayuwa duk inda kake sai ya iskeka kenan ,Æata taÉ“a tinanin zata sake fuskantar wani tashin hankali ba ayanzu da suka keÉ“e kansu da kowa ba,bata da buÆ™atar kowa yason su suwaye ,to amma shi lamarin aure akwaishi da bankaÉ—o sirrin É“oye. Da karfi sadeeq ya gilgiza Ammi yace "Ammi minene haka? Ammi dami zanji , Hajiya bata lafiya ke kuma bakya cikin hauyacinki , Nainah na kuka . Dan Allah ku Tausayamun . Nene tace "Sadeeq kasata mota muwuce Asibiti. Tinanin ta yanda zai fara É—aukar matar mutane yake . hakan yasa shi cikin in ina shi da tashin hankali ke tasomai yace Nai..nah baniii...da...hurumin É—aukar ta ..ya Æ™are magana a wahalce. Nene ta tallabo Mamy da bata motsi tace shikenan- shikenan ni Amina nashiga ukku na lalace .. Cikin É“arin baki sadeeq yace Ammi kinafa gani dan mi bazakiyi wani abu akai ba? Lfy tane fa . Da gudu ta tashi ta shiga dakinta sai gata da wata babba jikka anan ta zazzage duk kayan duba marasa lafiyane masu kyau sabbi daganin su zasuyi kudi sosai. Da sauri ta iso ga Mamy tare da fara du bata cikin hanzari tanayi tana tausasamata wasu abubuwa masu kama da dutsin guga a kirji. Cikin Æ™anÆ™anan lokaci Mamy ta fara kawo ajiyar zuciya. Ammi ta duba Bp É—inta anan taga yayi muguwar hawa. Kai ta gilgiza tare da bata taimakon gaggawa. Mamy na falfaÉ—owa ta tsare Ammi da ido ko kyaftawa batayi. Yayin da Sadeeq ya fita tsakar gida dan basu waje . ÆŠakin sa yashiga ya fara kai komo. To miya janyo haka? ita kuma Ammi shi kukan minene take? Amsa da baya da ita. Saida Ammi taga komi ya tsaya kana ta É—akko takadda ta fara wani shegen rubutu irin na likitoci tace'' Sadeeq ga shi ka nemo maza. Da sauri ya karyba ya fita dan yana da kuÉ—i A hannu. Yana fita Mamy ta tashi tana cije baki. Bakinta ta buÉ—e da niyyar magana sai kuma ta fara bleeding. Ammi cikin tausayi tace" ki kwantar da hankalin ki kinji . Na amince indai wannan ne damuwar ki, kana ki daina Æ™oÆ™arin magana har sai namiki allurar da zata tsaida jinin ,ina fatan kingane?. Wata irin guÉ—a Nene ta saki tare da tashi ta fara rawa tana gilgiza kirjinta mai kama da slipas . Mamy fuskar ta tacika da annuri tana É—a gama Ammi hannu Alamun godiya. Murmushi itama ta mata tana jin faÉ—uwar gaba. Cikin 20mnt ya dawo ya kai mata allura ya fito. Anan ta yima Mamy tare da É—oramata leda ruwa guda danjin kwarin jikinta. ta samata ita da É—an gudu dan ta kare . Bayan awa biyu Mamy ta tashi ba laifi jikin da dama . Anan ta fara jerama Ammi godiya. Ammi tace Hajiya wani hanzari ba guduba. kana akwai sharaÉ—i. Mamy tace'' minene sharaÉ—in. Ammi tace". Kin amince ki aurama sadeeq yarki bakison ko waye shiba, kana bana da buÆ™atar ki sani, kin yarda? Da sauri Mamy ta kaÉ—a kai tace" na yarda Hajiya dan dama itama burinta karkowa yason wanda ya auri Amnah. Mamy tace" Masha Allah. abyu na biyu y'arki zata iya zama da Sadeeq a cikin halin da yake ciki, bayan ita bata saba da irin wannan rayuwar ba?. Mamy tace "na Amince dan ina buÆ™atar inda za a killaceta, abata sabuwar tarbiyya, da koyar da ita darasin Rayuwa. Ammi tace abu na ukku Hajiya kin amince da babu dangin Sadeeq a auran nan, saidai aje ga liman yazama waliyyin shi ko kuwa ? Cikin faduwar gaba Mamy tace "to ina ah'linshi?. Murmushi Ammi tayi tace" indai kin Amince ahaka babu damuwa, in kuma saida ahli gaskiya kiyi hakuri dan nima bana buÆ™atar jin komi daga wani ahlin yarki, dan na fahimci akwai lauje cikin naÉ—i, dan dan haka kawai wannan auran yazamana auran taimakekeniya. Mamy tace" shikenan insha Allah zansamu wanda zai zamemai waliyyi . Daganan sukamata godiya suka fito. Sadeeq ya fito ya mata sannu suka shiga mota ya maidasu gidan Nene. Suna isa Mamy tace zai iya komawa gida da daddare yazo ya É—auketa. Yace shikenan ba damuwa. Yana isa gidan su yayi tsinke É—akin Ammi ya isketa zaune ita da Hamrat ta na shafa kanta amma som hankalinta na wani wuri. Sallama ya sakeyi a'karo na biyu. A furgice ta kalleshi tana yaÆ™en dole tace ''Dee ka dawo? Yace eh Ammi tare da zama kusa da ita ya tankwashe Æ™afar shi "yace Ammi miya faru É—azu hankalina ya tashi fa,Daga zuwan ta abu harda tashin ciwo.?.. Kuka tasamai tare da riko hannu shi tace" ka yafeni Sadeeq, ka yafeni dan girman Allah, Nason zakaga kamar cutar da kai nayi,zakaga na yanke hukunci ba tare da shawaraka bayan bani da wanda ya fika, to Wallahi ba hakabane sadeeq ka kyautatama wanda ya kyautatamaka, kamata wannan alfarma kamar yanda ta buÆ™ata. Anan ta kwashe duk maganar da sukayi da Mamy ta faÉ—amai... Gabaki dayan jiki shi ya É—auki bari wata zufa mai masifar zafi ta fara ketomai. Hular kanshi ya cire yana fiffita da ita tare da miÆ™ewa ya fara zirga- zirga cikin É—akin. Kimanin 30mnt yakasa cewa komi sai zarya yake. Dakyal ya É—aga jajayen idanuwan shi ya sauke su ga Ammi da ke binshi da kallo tana share hawaye. Hamrat ma kukan take. "Ban amince ba ,kana na bar aiki agidanta , bakin da Allah ya halitta bazai hanashi abinda zai ciba. Ammi yana da kyau ki haÉ—a kayanki dana haynrat yanzu insamo mai sayen gidan nan Abani abunda ya samu. kwara in dumfari Æ™asata koda babu kayan yaÆ™i. in yaso komi zai faru ya faru. Da in zauna inda ake juyi da rayuwata kamar Ball. "Aure" ni za ama aure. Lallai na yarda talakka gatanshi Allah ,wato inbaka dashi kenan rayuwama tsaramaka ake, To ban amince ba, kuma bazan ba, kayan duk datamana tm zanje in mayar mata da abinta. ana dole ,Banaso. ya Æ™arasa cikin wata razananniyar ihun dayasa Hamrat daka tsalle ta rungume Ammi tana sakin kuka. Cikin tashin hankalin Ammi ta tashi ta rikoshi dan taga yana Æ™okarin fita. Rungumoshi tsami tayi jikinta ta fara shafa bayanshi. kamar wani Æ™aramin yaro haka ya zage yana sauke ajiyar zuciya . Hannushi Ammi ta kama suka zauna tace "Sadeeq inaso ka fahimceni ka fahimci uwa bazatama É—anta abinda zai cuceshi ba, Sadeeq matar nan nada ciwon zuciya abu kaÉ—an zai iyasa zuciyar ta bugawa,baivkamata muna da hanyar magance matsalata ba amma ace munkasa , Duk kan kyautatawar ta garemu mu sai mumata butulci? Ta karÉ“eka hannu biyu tana mutuntaka Sadeeq tana kyautata mun, muna da damuwa kuma muna fatan ganin karshenta da izinin Allah,haka itama tana da tata muke mata fatan ganin karshen tata da izinin Allah,to ita tata mai saukice tinda har zata iya bayyana buÆ™atar ta, to danmi bazamu taimaka mata ba? Kana Auran naku duka na Taimakekeniya ne fa babu tsaurara bincike. Ina mai baka umarni da ka karbeshi hannu biyu ka kuma tsaya ka sauke hakkin yarinya dake kanka ,kaji tsoron Allah shine kawai abinda zakmun ,daga nan taci gaba da lalashin shi tanamai nasiha. Kai ya jinjina ma Ammi yace" shikenan na Amince. ya tashi yabar É—akin da sauri dan inya zauna yana iya saÉ“ama umarnin mahaifiyar shi abinda baya fata. Cikin tsananin jin daÉ—i ta bishi da sanya Albarka tare da kwanciya gefen Hamrat tafara tinanin wani kuma rayuwa zasuyi a'sadda suka tashi daga su ukku zuwa hudu . shine yarinya zata iya zaunawa dasu Ahalin da suke ciki,shin tanama son É—an nata ko kuwa?Ya hayyu ya qayyum ka kawoman agaji da mafita, Allah in haÉ—in nan alkhairi ne Allah ya tabbatar, in kuma ba Alkhairi bane Allah kai kason yanda zakayi damu. AÉ“angaran Mamy kuwa tinda ta koma gidan Nene ta samu gado ta kwanta. Haka nan take yawan jin faÉ—uwar gaba wadda tarasa ko ta minene, Yanzu babbar Damuwar ta Sadeeq da Abban Amnah, ya zai É—auki maganata, shin zai fushine dan tayi gaggawa yanke hukun ci ko-ko zai fahimci manufar ta. Nene da tashigo hannuta rike da kofin fura mai sanyi dai madai-daicin flat data shaÆ™oshi da felfesun yan ciki sai kamshi yake. Tace ma Mamy" Fulani tashi kici abinci dan Allah kiyi sallah kifaÉ—ama Allah damuwarki danshi zai maki maganin komi. Mamy ta tashi tace Nene damuwata Abba Amnah. Nene ta taÉ“e baÆ™i tace ''ke nifa nafarama gajiya da wannan gantalallan auran naku Wallahi. Na taÉ“a ganin miji kamar naki ace kayi tafiya neman kudin ka sama da shekara biyu bakazo ga iyali ba, wannan ai wulakanci ne da rashin sanin hakkin Aure. Murmushi kawai Mamy tayi tare da karÉ“a furar ta shanye tass tace" na koshi da yan cikin sai anjima. Nene tace" shikenan ki kwanta kihuta zuwa anjima . Abangaran Amnah kuwa suna fita ta faÉ—a É—akin Amal anan taganta kwance tana bacci . Da sauri ta É—auki wayar ta da tasa charge ta lallasa number Bily. Bugu buyu ta É—auka cukin kasa da murya tace" inaji. Tsaki Amnah tayi tace ke akwaifa damuwa Bily wallahi ,kinson mene ya faru kuwa? Da sauri Bily dake kwance kusa da Prince ta mike tana gyara zaman É—aurin kirjin da tayi jin murya Amnah" tace'' A'a sai kinfaÉ—a minene? Amnah tace waya ta Mamy ta Æ™arba Bily, ina cikin tashin hankali kar ta fahimci wani abu. Bily ta kalli Prince ya É—agamata gira da sauri tace" tamiki magana? Amnah tace aa batace mun komi ba, kana komi bai canza ba. Bily ta sauke ajiyar zuciya Tare da cewa haba karki wani damu babu komi kinson tin jiya mutumin ki ke nemanki. Amnah Wallahi Prince na masifar sonki, kinson wanda baitaÉ“a soba inya afka abin na bashi matsala. takarasa tana kaimai duka. Amnah tace Allah sarki ina gaidashi. Bily tace yanzu taya zan iya kawo miki wata waya ki É“oyeta ya zamana ta sirrin kice ko Amal karki bari ta sani. Cikin matuÆ™ar jin daÉ—i Amnah tace'' yawwa hakan ma yayi, amma ina da kuÉ—i bari inje in siyo, in nadawo nayi miki magana. ta faÉ—a tana datse kiran. Dariya Bily ta tuntsire da ita tace waini su Abul khairi an'zama prince. Sajenshi yaja yana kashe ido yace "dole komi ma inzama akan Baby nan tayi fa da kyal na yi bacci fa. Bily tace "to yanzu in iyayenka zasuje gareta yaza'ayi? Yace" ke kika sansu na bogi zan'samu ins'akar musu Æ´aÆ´an banki kawai suje suyi abinda za'ayi. Cike da gamsuwa ta É—agamai kai tana Murmushi.. Sadeeq kuwa tinda yashiga É—aki yaji wani masifaffan ciwon kai na kawomai ziyara , Wanda bai rasa nasa ba da tashin hankalin da yake ciki ya tabbata. Yanzu shida ke burin barin Katsina cikin wata ukku an'mishi aure to ina zaije da yar mutane ?som bayajin son koma wacece a'cikin yaran ta, Dan ba auran zaiba shi minene ma zayyi da mace , Bayan Aikin da yasama gaba wanda ko iyayen shi sai ya musu nisan kiwo . AÉ“angaran Mamy kuwa zaune take tana nazari yanda Sadeeq zai É—auki magana su,da fahimtar bayanin ta, sam takasa natsuwa tana tinanin an sanar masa ko-ko. Waya ta É—auka ta danna mishi kira dan samun natsuwa ta . Kwance yake rigin-gine ya faÉ—a Duniyar nazari wai shi zaiyi Aure, To mi ake acikin Aure,Mizai iyama mace shikam. Yana tsaka da tinani yaji wayar shi na ring. Yana duba wa yaga Mamy ce harya juya kafaÉ—a kuma ya tina da abinda Ammin shi tace. wayar ya jawo ya É—auka cikin sallama. Ajiyar zuciya Mamy ta sauke tace am "Sadeeq ina wuni . taÆ™arasa cikin rikicewar murya. Kamar yanda ya saba ya mayar mata da gaisuwar. Tare da cewa kingama ne mutafi? Tace aa ina daiso kazo gidan Nene ne yanzu zan aikeka gidan Hajiya Turai kaida Amal. Kai ya jin-jina tare da cewa" ina zuwa ya kashe wayar. tare da sakin tsaki. Amnah kuwa ganin babu kowa palo yasa cikin sanÉ—a ta fito daga ita sai Yar jikka ta fita da sauri daga gidan Nene. Sama ta kalla ganin wani irin hadari da yayiwa saman kawanya. Cikin sauri ta fara tattakawa dan Æ™arasawa bakin hanya dan tasamu ta hau napep tayi sauri. Abinda bata taÉ“a yi ba. Napep ta tsare" ta mai kwatancen inda zai kaita. Yace "maza shige Hajiya kinga hadarin nan ya kwacema mutum waje akwai damuwa. Shiga tayi suka É—auki hanya. Dai -dai lokacin da garin ya kara rinewa. Tace'' Malam bara in Æ™arbo Abu ka mayar dani . Yace ohk maza. Da sauri ta shiga ta dauko dalleliyar waya tare da sim cart ,ta Musu transfer ta fito. Napep É—in ta faÉ—a suka É—auki hanya. Wani gagarumin iska ya taso mai tsananin Æ™arfi wanda yasa mai napep É—in samun wuri yace. "Gaskiya bazan iya tafiya cikin wannan iskan ba, Hajiya tafiya cikin iska haÉ—ari ne. Fada ta rufeshi dashi akan yaje a'haka zata bashi ko nawane. Yace ba kuÉ—in ki nike soba lafiyana nike mawa, dan haka sallamani kawa i dama kusa da gida nike. 1k tazaro ta jefamai tare da fita ta fara tafiya tana kama mayafinta da iska keta son janyewa. Sadeeq kam saida ya mila yasha iska kana ya tashi ya watsa ruwa yace ma Ammi zaije ya dawo. Tace to Dan Allah kabi A'hankali kaga iska da alama ruwa zamu samu,kuma karka nuna mata komi ko a fuska kamun wannan alfarmai. Yace shikenan insha Allah. Fita yayi da machine din ya É—auki hanyar gidan Nene. Ganin wani irin iska da ake ya sashi zaro glass ya toshe idon shi dashi tare da fara tafiya cikin natsuwa. Cikin tashin hankali Amnah ke É—agama masu abun hawa hannu Amma kamar an'hanasu tsayawa, kowa sauri yake, sai masu mashina ita kuma bata iya hawa ba. Innalillahi wa inna ilaihi Raji'un tace lokacin da ta doso ta wani titin da babu yawan mutane akai Ta fara tafiya . Sadeeq kam ganin yayyafin da ake ya sashi Æ™arama machine dinsa gudu ,yana gab da cimma unguwar su Nene ya ga wata babba mota ta tare hanya da alama matsala tasamu ga mutane nata jira sai faÉ—ace -faÉ—ace ake. Tsaki yayi ganin yanda ruwa yaketa Æ™ara karfi duk yajike. Kawai ya karya wani lungu ya fara sheka gudu duk da yason yayi dogon zagaye. Amnah kuwa tashin hankalin da take ciki ba a magana, ga wayar ta a hannu, ga rashin abin hawa, ga rashin mutane, a titin, ga rashin faÉ—ama iyayenta, hakan ya sata dana sanin fita. Cikin sauri take tafiya ruwa nata jiÆ™a jikinta yayin da shadda jikinta tabi shape É—inta ta lafe har shatin pant É—inta kana gani, saboda bata sanya ondie. Wata motace fara ta sheko da gudu har ta wuce kuma tayo baya da gudu tasha gaban Amnah. Wasu matasane guda biyu da ganinsu babu tarbiyya ko Æ™adan a tattare dasu duba da shigar da sukayi da kuma askin dake kansu. Cikin muytya yan iska É—aya yace haba "Baby mai kayan daÉ—i bai dace kamarki kina yawo da Æ™afa ba ,haka ai sai duniya ta tsinemuna mu bayin mata, Dan Allah ki an'taya motana in wullah dake duk inda kike so. Cikin faÉ—an da yazama halinta na rashin ganin kowa da kirki yasa ta fara musu masifa . "Ubanwa zaku É—auka da wannan gwarama motar taku yan iska , Sai wari kukeyi, kudai kam daganin ku yayan matsiyatane ,inba Akuyanci ba daga ganin mace sai kufara binta? É“accemun da gani ko in laftamaka mari , Da Wata shegiyar fuska taka Æ™atuwa Kamar giginya. Cikin bakin ciki da takaici É—aya yace Bashow an:tayama shegiya a yau zakison kin faÉ—o hannu mai fuska giginya, zakison komi namu ma siffar giginya gareshi yar iska. Tsaki tayi tacigaba da tafiya cikin sauri. Da sauri suka rufe motar su suka fara binta, É—aya yasa hannu ya jawo mayafinta data rufe jikin ta. Tashin hankali wanda ba'asamasa rana tashiga lokacin da taji hannu É—aya bisa mazaunan ta. Ihu ta saki tare da cire takalmanta ta fara kwasar gudu. Baya suka rufamata suna tika gudu cikin ruwa. Tana shawo wata kwana taji tayi Æ™aro da wani katon dutsi,take ta faÉ—i a wajen Æ™afar ta tayi wani mahaukacin buguwa. Dariya suka saki suna biyota tare da gyara wandunan su É—aya harda cire belt É—in shi. Innalillahi wa inna ilaihi Raji'un tace lokacin da tayi Æ™oÆ™arin tashi amma ta kasa, haka ta fara jan Æ™ugunta tana matsawa suna binta tare da wata shedaniya dariya da suke saki. Daga nesa ta cikin farin glass É—in shi yake hango abinda ke faruwa duk da baigane ko wacece ba. Ganin yanda suketa binta yasa ya ajiye machine É—ina sa tare da takowa a hankali cikin ta fasa zuciya da kuma bacin ran da yake ciki dana abinda mazan zamani suke aikatawa mata wato fyade. Hannaye Amnah ta haÉ—e waje guda tana rokon su akan su barta zata basii duk abin da suke so. Dariya É—aya yayi yace ga abinda muke so nan. ya faÉ—a yana nuna jikinta tare da riko rigar ta daga Æ™asa. Cikin ta fasa zuciya sadeeq ya lallaÉ“a ta bayansu tare da musu wata kafurar shaÆ™a. Cikin tashin hankali sukeso su juya dan ganin wake masu wannan abun amma kamin sukai ga ganin fuskar shi ya gwara kansu, ihu suke sosai dan gabaki É—aya kawunan su juyawa suke. Amnah ganin Allah ya kawo mai cetonta duk da batason ko waye ba hakan yasa ta lallaÉ“a ta mike A'hankali tana É—an gyasa Æ™afa, ta É—auki kwalin wayar ta da yasha ruwa ta ciro wayar tasa a leda da sim É—in tasa a rigar ta tare da zubar da kwalin. Mayafinta ta fara sawa tana tafiya tana jan Æ™afar da takejin kamar zata cire. Saida ya basu Azaba son ranshi yaga sun jigata ba tare da sun ganshi ba, kana cikin zafin rai da Æ™unar da zuciyar shi kemai ya jasu keeee har zuwa cikin wata Æ™atuwar kwalbatin da keta ambaliyar ruwan da akai . Cikin É“acin rai ya tausa kawunan su ciki sosai sai da ya tabbatar da sun sume kana ya sakesu ya juya.. Cikin É“acin rai yake tafiya yana sakin tsaki. Ta gaban Amnah yabi ya wuce cikin sauri. Wani irin faduwar gaba taji ta saukar mata lokacin da ya shayata ya wuce. Har ya hau machine ya tada zai juya kuma ya juyo da fuskar shi dan yimata gargadi. Karaf idonsu ya sarÆ™e dana juna lokaci guda bugun zuciyoyinsu ya Æ™aru. Baki ya buÉ—e zai magana kuma ya fasa yana cije lips É—inshi. Amnah ganin yana Æ™okarin juyawa yasa cikin sauri tace ÆŠAN DAKO. banza yayi da ita ya kyale tare da tada machine É—insa ya fara tafiya. zuciyar shi na fad'amai bai kyautama mahaifiyar taba in yabar mata É—iya a wannan yanayin duk halaccin da tamai bata can-canta ba, uwa uba yaran da keson keta mata haddi duk da baisani ba ko suncimma buri ma oho. Afusace ya juya machine É—in har zuwa inda Amnah take tsaye ,dan tsayawar da tayi da niyyar mai magana Æ™afar ta kasa motsa wa. Hawaye ta share tason yau ita kashinta ya bushe. Afusace ya tsaya gaban ta cikin tsawa yace "wuce muje. Sosai ta samu kanta da shakkar shi cikin sanyin murya ta nunamai Æ™afar taa da tayi sasur tace" bana iya tafiya. Wallahi zan tafi in barki duk abunda zasu miki su miki, Tinda kafiya ne dake ,wato kin iya biyo Centre da ba mutane amma baki iya Æ™are kanki ba ,to ki wuce mu tafi. Da sauri ta cira Æ™afar ta É—aya mai lafiya, tazo cira mai raunin ji kake tim tayi wata mahaukaciyar faÉ—uwa. Ihu ta saki tana yar fe hannu. Kallonta yayi ganin da gaske dai take bata iyawa. Wajen yabi da kallo ganin babu alamun abun hawa gashi in yatafi baison yazai bar taba tinda amana suke hannushi, hakan yasa ya cije baki tareda fadin kizo ki hau machine É—in nan. Da kyal ta dafa kasa ta mike tace "wallahi ban iya ba kaji na rantsema bantaÉ“a hawa ba. Tsawa ya da kamata tare da cewa wallahi tallahi zantafi dana kilga ukku. ukku biyu... Wani irin tsalle ta daka ta faÉ—a kanshi tare da cimamiyoshi da mugun Æ™arfi . Azabure ya kalleta itama shi take kallo ga ruwa na dukan su. Kallon juna suke sosai babu ko kyaftawa kuma kowan ne da tinnin dake ranshi. Cikin mutuwar jiki da sanyin murya" yace zaki taka nan zaki hau. Da sauri tayi yanda yace Amma mai makon tayi zamanta hakanan kawai tasa fararan yatsunta ta sargafo dasu ta wajen cikin shi ta rike gam tare da kwantar da kanta a bayan shi dan in'tace ta kalli hanya zata na ganin jiri. Innalilli wa inna ilaihi Raji'un yace lokacin da yaji..... Alhamdulillah nagama free. Maiso ya 300 ne kacal. Hmm karku bari abaku labari. Ku tuntubeni ta wannan number dan neman Æ™arin bayani 07038-4234-51 Akwai lagwada cakwakiya🥰 Zallar soyayya da babu algus. Wayyo dad'i 😅😅🥰🥰🥰 5/18/22, 09:34 - MY MTN 2: *Littafin🌹DAN DAKO🌹 na kudi ne biya ki karanta cikin Aminci. Biya 300kacal to 0006454115 Amina Dahiru jaiz bank,or MTN card to this number 09165832002. then send the evidence of payment via 07038423451* ðŸ¤ðŸ™ðŸ¤² 🌹ƊAN DAKO 🅿ï¸2ï¸âƒ£1ï¸âƒ£&2ï¸âƒ£2ï¸âƒ£ "" Saukar Tagwayen ta akan bayan shi. Wani yanayi ya samu kanshi wanda shi tinda yake a rayuwa bai taÉ“a jinsa a haka ba. Da sauri yace" Dan Allah ki sauka mu tafi Æ™asa. Amnah da keta maida numfashi tare da jin wata natsuwa ta mussaman ta saukar mata lokacin da tayima kanta masauki a jikinshi , Cikin wata irin murya mai matuÆ™ar sanyi tace "Dan allah muje a haka zansha wahalane Æ™afana ya goce ne. In ina ya fara yana faÉ—in tayaa...zan..É—aukeki ..haka kina kwance a bayana!. Shuru tayi sai murmushi data saki tana sake sanya yatsunta ta kara kama Æ™ugunsa sosai. Ganin tana neman sa ya faÉ—i yasa A'hankali ya tada machine din yana mai tsananin jin kunya suka fara tafiya. Wash ! tace'da Æ™arfi tare da Æ™oÆ™arin faduwa baya dan hakanan ta buÉ—e ido sai ga jiri ya kawomata ziyara. Da sauri yasa hannu sa guda yana sakin tsaki ya riko nata ya rike . Wani irin yanayi suka tsunci kansu ciki mai wuyar fassarawa. Cikin wata shagwabar da batason ta iyaba tace" Dan Allah Dan Dako kafana namun ciwo in na dorata anan ko zaka rikemun kamun DAKO'nta? Tsawa ya dakamata ganin Abu nata ya fara zama iskanci. yace wallahi hannukk zan saki cen kifadi ki fashe kai mene nawa. bazan rike ba ya fada afusace yana yarfe hannuta. Da sauri ta sake cimamiyashi tayi luf ajikin shi. Ahaka Allah ya taimakeshi har kofar gidan Nene ga ruwa ya tsananta sai hon yake ba'aji. Ki sauka " Yace da ita. Tace bana iyawa ". Tsaki yayi tare da kafar da machine din yasa hannushi É—aya ya janyo kafar ta tare da sakko da ita A'hankali, dan yaga tayi wani irin fushi sai kuma ta dafa bayan shi ta dire tare da jan Æ™afar kaÉ—an- kaÉ—an ta matsa wajen wata rumfa dake kofar gidan Nene tana É—ingisawa. Shikam yana ganin ta sauka ya bita da harara tare da hawa saman machine din yayi zaune ruwa na bugu nshi batare da ya damu ba. Wata irin Æ™anÆ™ara tafara sakkowa kwar-kwar tana feshi ko ina. Amnah da take kallon shi ganin irin Æ™anÆ™arun da ke sakkowa manya yasa ta kalleshi ta kalli yanda suke faÉ—owa gefen ta. Harara ta zubamai tace" sai isar banza shi ba kowa ba, Allah yasa ta makeke sai inga yanda zakai, ita dai da mutum bace balle ka ce zaka rama kai ga mai Æ™arfi. Shikam jin Æ™anÆ™arun na sakkowa yasa ya sauka daga machine É—in ya iso rumfar da take tare da komawa gefe yayi tsaye. A takaice nan suka tsaya har saida aka fara kiran mangariba kana ruwa ya É—auke suka shiga ciki. Yayi alwallah ya hau machine dan komawa gida ya canza kaya. Yayin da Amnah kuma ta shige É—akin Nene tana É—ingisa Æ™afa ganin ba kowa yasa tayi É—akin su, Anan Amal ke tambayar ta inda taje ? Tace sweet naje siya wasu suka biyoni na faÉ—i. Sosai Amal ta rikice da mata sannu cikin tausayawa ganin yanda Æ™afar tayi fushi sosai. Bayan sallah mangariba Amnah da tasha wanka cikin wasu ash din riga da wando,saman rigar nada faÉ—i kana hango Black din ta ciki, ga wata kwalliya mai gashi- gashi da taima saman wuyan Æ™awanya, kuma kakkaura saboda sanyin da ake. Anan Mamy da Nene suka sakko suka zubamata ido. Nene'' tace ke gidan ubanwa kika je.? Cikin rawar murya tace. "Nene naje siyo chocolate ne JIFATU, anan na haÉ—u da wasu yan iska suna bina, Garin in gudu na faÉ—i, to wannan ÆŠAN DAKO ma ya korasu ya maidoni gida. Nene tace agidan ubanwa kikaga ÆŠan dako'n. Anan ta basu labari suna tsaka da magana yayi sallama ya shigo, Yana sanyw cikin Æ™ananun kaya farare masu kyau sosai ,sun haska farar fatar shi sai kamshi yake. Kujera ya zauna ya gaida su Nene tare da tsuke fuska yana kallon gefe guda. Nene tace "Kwandon sukari in kawoma ka Abinci?. Yace A'a Nainah na gode. Amal ta gaishe shi tare da cewa Nene" wannan ai tayin rowane kawai ki zubomasa. Yace A'a nagode in kuma kina da ruwan Lipton mai kayan yaji kibani Nainah. Nene tace akwai Saddi bari in kawoma ka. Anan ta kawomai yasha ya kalli Mamy yace" gani Hajiya . Som ta kasa kallon shi sai rawa da bakin ta ya fara. Nene tace ma su Amnah kuje É—aki. Tashi sukayi Amnah na tsaki suka shiga cikin É—akin. Mamy ta sakko Æ™asa tare da rarrafowa wajen shi. Wani shegen tsalle ya daka ya mike tsaye cikin rawar baki ya doshi hanya yana kaÉ—a mata kai, dan baya son irin wannn rokon som. Nene tace dawo sadeeq Dan girman Allah, da manzon sa, ka dawo nace. Dawowa yayi tare da neman waje Æ™asa ya zauna ya sadda kanshi kasa. Mamy ta fara hawaye tace'' sadeeq na tabbata kaji abinda yafaru daga bakin mahaifiya ka, Sadeeq nason zakaima maganata mummuna fahimta,zakaga ina da son kai ,wallahi billahi bani da burin cutar ka Sadeeq, ina rikon Allah ya dauki raina da inga ranar da zan cuceka koma waninka, sadeeq na yaba da nagar taka tin a ranar farko na samu natsuwa kai,Na Amince da kalaman Aminiyata na haÉ—aka Aure da Amnah, Sadeeq ka amincema buÆ™atata Dan Allah cikin kyakyawar fahim ta. Kai ya jinjina yana nazari. "Amnah" kuma a furgice ya kalleta yace" Amnah fa kikace Hajiya? Amnah? ina ita ina takala irina, yarinya da bata shiri da matalauci , Hajiya kibani koma wacece amma Amnah bazan iya da ita ba. Nene tace A'a" Sadeeq kaine kawai zaka iya saita rayuwar Amnah, dan haka dan Allah ka amince . Bakinshi ya cije yace na Amince Hajiya! na amince ya faÉ—a yana tashi da sauri ya fita. Ya fara zarya cikin gidan Nene. Wayar Mamy tayi ring ta zaro taga number Abbah ta Nigeria, wani irin faÉ—uwa gaban ta yayi, cikin sauri ta É—auka da sallama. Daga É“angaran shi kam cikin jin daÉ—i da walwala yace gani cikin Palon ki ina tattare da Æ™ishirwa ganin ki da Yarana. Amma kin shanyani baki dawo ba. Da sauri ta mike tsaye tace'' wai da gaske kake .? Yace tabbas kuwa tin la'asar ina gida. Tace ganinan zuwa ta datse kiran tana kallo Nene dake taÉ“e baki. Kayanta duk ta kammala ta mata sallama tare da kiran su Amal suka fito. Anan ta iske Sadeeq yanata yawo tace mai" muje gida sadeeq inka ajiyeni dan Allah ka kaita othopedic Aduba Æ™afar ta. Yace ohk "tare da shiga mota suka shiga ya tada ya ficce. Mamy suka ajiye suka wuce dan tama manta bata sanar dasu Abba su ya dawo ba. Tana shiga mai gadin ya budemata anan taga manya- manya motocin mijin nata guda ukku jere ras tabbacin yana gidan kenan. Maimakon ta samu kanta cikin farin ciki saita samu kanta dajin shakku dawowar ta sa. Tana tura kofar palon tashiga da sallama tana waigen ta inda zata ganshi. Cak taji anyi sama da ita ana juyi da ita cike da soyayya yake faÉ—in "oyoyo Sweetheart. Kallon shi take cikin tsananin jin daÉ—i da kewar shi, tare da cewa" Hayatee ka saukeni hakanan, munfa girma bakajin ina da nawi?. Akan gujera ya saukar da ita yace "soyayya bata tsufa Saudat sai dai masoyan su tsufa, sonki kawai nike ,kewar ki kawai nike ,Dumin jikinki kawai nike da buÆ™ata matata ,shiyasa na kasa control É—in kaina, Mafari na shammaceki na watsar da komi nazo ga halaliyata, insha Allah zanmiki wata biyar kamin in'koma.. Cikin Wani irin farin ciki ta rungumeshi tana Alhamdulillah Allah nagodema daka juyo da hankalin mijina gareni, Alhamdulillah. Murmushi yayi yana shafa goshinta yace" kiyi hakuri nason bana kyautamiki , Amma Fulani bani da yanda zanyine , amma insha Allah zan maido da wasu harkokin nan nawa dan in'samu zama kusa daku! ina yarana?. Anan take fad'amai Amnah ce tayi rauni zasuje Asibiti. Arikice ya mike tsaye yana zarar key din mota tare da faÉ—in" miyasa ba asanar dani ba? maza tashi mubi bayan su. Kallon shi take cikin so da Æ™auna. Cikin natsuwa ta tashi ta rungumoshi ta saita bakin ta cikin nashi ta faramai wani salo na Mussaman da ya sashi sakin key É—in mota. Ahankali takai hannuta ga jallabiyar jikinshi tayi Æ™asa da zif din kan wuya shi ta fara shafa galgasar dake kwance akan kirjinshi, tare da murza nipple É—insa. Wasu zafafan ajiyar zuciya ya fara saukewa cikin sauri -sauri yana jinshi a wata duniya ta mussaman. Cikin low voice yace" fulani na, matata, kibani agajin gaggawa tin kamin nunfashina ya É—auke . Ahankali ta kama hannushi yafara binta idon shi ko buÉ—uwa basayi. ÆŠakinta suka shiga shape_ shape tayi wanka tana cikin murza kwalacca ya taso yajawota jikin shi. Abangaran su sadeeq kuwa bayan sunje aka basu suyo x-ray bayan sunyi sun dawo aka tabbatar musu da Amnah ta samu gocewa a Æ™afa, dole agyaramata amata É—auri. Amal ta fara kuka Amnah kuma sai zare.ido take gani wasu manyan likitoci nayo É—akin da take , tare da warware wasu Æ™arafa da bandege. Koda tana nursing amma saida zuciyarta ta buga da karfi lokacin da taga sun dumfarota. Wani mahaukacin ihu ta saki sadda taga an'rikemata Æ™afa. Da sauri babban Dr yace" a kira Æ´aÆ´anta da ya kawosu ya riketa ko mijintane? Cikin rikicewa Amal tace" mijintane wallahi Yayan tane, ta faÉ—a ciki É—imuwa dan akwaita da tausayi. Sadeeq suka kira dake zaune É—an reception É—in yana kallon tv wanda som hankalinshi ba a wajen yake ba. Tashi yayi yana tsaki ya shiga É—akin. Anan suka umarce shi da ya rike matar shi zasu gyaramata. Zai tsaya magana Annabin ta wani cizgo shi jikinta tana jijjigawa cikin tashin hankali tana sakin siririn kuka. Ke anafa kallonki yace da ita cikin Æ™asa da murya. Ganin tana ta ihu gasu sunason yin ai'kinsu yasa ya rungomata jikin shi tsam tare da rike hannuwata ya fara goga dogon hancin shi akan nata, tare da hura mata iskan bakin shi a wuyanta da keta fitar da zufa. Kyarma jikinta ya É—auka sosai gana azaba gana mamakin abinda yake mata. Shikam duk aganin shi taimkone yake mata dan daraja mahaifiyar ta badan halinta ba. Sunkai 30mnt kana aka gama . Da sauri ta tsareshi da ido tare da sakar mai wata harara tana goge bakin ta. Da sauri cike da takaicin kanshi ya fita daka É—akin tare da faÉ—awa mota ya zauna yana tinanin mima ya kaishi ?mai makon da yaje yasa igiya ya É—aurema shashashu hannuwan ta, sai yasa hannayen sa,mtss kamar zasu kasheta, duk iskancinta ashe raguwace. Magunguna aka basu Amal ta biya kana suka fito tana dingisawa yashiga mota suka tafi. Suna shigowa gidan ya fita da sauri tare daba Amal key din ya haye machine dinsa ya tafi, Dan dama.wata irin ciwon kai da zazzaÉ“i yake ji , Kuma yason bai rasa nasa ba da ruwan daya zane shi da damuwar da yake ciki. Tafiya yace cikin dauriya yayin da kanshi keta kara É—aukar zafi da jikin sa . Dakyal ya isa gida lafiya yana shiga sama -sama suka yi magana da Ammi ya faÉ—a É—aki ya kwanta. Wani masifaffan sanyi ke kawomai ziyara yayin da hakoran shi keta gamuwa dana juna suna cijewa. Haraminsa ya É—akko ya rufe jikin shi da wani Æ™aramin barko wanda som babu kauri a jikin sa. Innalilli wa inna ilaihi Raji'un yace sadda yaji kan na sake mai wani wahallalan ciwo kamar zai fita. Mamy ce tsaye gaban mirro tayi wanka ta zira wata doguwar rigar bacci doguwa white nd pink sai hula ma pink tayi kyau sai kamshi take. Abba ne ya shigo É—akin yanata zuba murmushi tare da janyo hannuta yace Allah ya miki albarka fulanina, ya Æ™ara miki lafiya, ya bani ikon Æ™ara kyautata miki kinji. Ameen Mamy tace tare da cewa muje Æ™asa in'sama maka abinda zakaci . Suna sakkowa sukaji tsayuwar motar su Amal. Ai da sauri ya mike ya buÉ—e palon dai -dai lokacin da suka shigo. Wata irin rungum@ yayi musu cikin tsananin so da Æ™auna irin ta uban dake ji da yaran sa. Mamy ta kallesu tana zuba Murmushi tare da yin hanyar kiching.. Duk tsanani ciwon da Amnah keji lokaci guda ta nemesa ta rasa , Dan ganin mahaifinta ya dakushemata komi sai zallar farin ciki. Cikin tausayawa ya kamota ya zaunar da ita bisa É—aya daga cikin kujerun palon . Cikin tausayawa ya zame saman carfet ya riko kafar ta tare da cewa Amnah nah sannu kinji! Allah ya baki lafiya ya kikejin Æ™afar. Cikin shagwaÉ“a tace" Abbah na da sauki, ganin ka yasa na warke.. Ya shafa kansu cikin nishaÉ—i yana samasu albarka. Amal tacgaidashi ta tashi dan tason in'tana kusa haushi kawai zata shaÆ™a, dan baya ta tata kamar yanda yake ta Amnah. Suna zaune suna fira Mamy ta shiryo mai juluf din taliya da tasha kayan lambu da kifi sai kamshi take ta ajiye gaban shi. Anan suka zageye su duka sukaci suka Æ™oshi. Tace ma Amal ta kama Amnah su haye sama. To tace tana kama hannu ta ta ajiye É—akinta ta shige nata. Amnah ta sama É—akin key tare da fiddo wayar ta tasata charge ta shiga wanka, Bayan ta fito ta kwanta tana tinano yanayin da suka kasance da Sadeeq. Kai ta gilgiza tare da faÉ—in babu É—an laifi. Wayar ta ta jawo ta kira bily akan ta turomata number Abul khairi. Bayan ta tura mata ta kirashi . Anan ya fara faÉ—amata irin yanda yayi kewarta tare da neman izinin son ganinta gobe . Hakuri ta bashi akan zata fitar da wani lokaci Abban ta na gida. Yace shikenan Gimbiya. daga nan ya fara mata fira dake tattare da zallar Æ™auna da kuma daÉ—aÉ—an kalamai. Abunka ga mace dan danan taji ya samu babban gurbi azuciyar ta. Washe gari suna zaune palo Abbah ya fiddo wata takadda yace ma Amnah ga offer nan ta aikin ki. insha Allah kinsamu aiki a babba Asibitin . Rungumeshi tayi sosai tana murna. Wasu kyawawan SarÆ™oÆ™i iri É—aya guda ukku ya zaro ya basu yace" kin ga wa'yannan da kaina na zanasu gasunan keda yaranki ya mikama Mamy.. Murna sukaitayi da godiya. Daganan ya rabamusu tsaraba su kowa ya tashi ya tafi É—aki. Ahankali ya jawo Mamy jikinshi yace wai Fulani na tin jiya ina lura dake kamar kina cikin damuwa ko? Lokaci guda tasa masa kuka dan tason shine abinda ke saurin karya da zuciyar sa. Arikice yace'' innalillahi wa inna ilaihi Raji'un. Fulani minai miki ,mike damunki ,ko bakyajin daÉ—i?. Tace lafiya' na Æ™alau lamarin Amnah ne ke bani tsoro . Anan take fad'amai irin abinda tagani a wayar ta Amma bata nuna mata ba sai abinda yace kana. Azabure ya mike tsaye ya fara kai komo tare da kwalama Amnah kira da masifar karfi cikin bacin rai da tashin hankali. Da sauri ta fito hannuta rike da wata Sanda ta silba. Amal ta fito itama ya dakamata tsawa tare da cewa ta É“acce mai da gani. Aguje ta taahi tayi sama tafaÉ—a É—akinta. Amnah na zama ya kalleta fuska a É—aure yace akwai wanda kike so ne? Agigoce ta kalle shi ta fara zancen zuci, mi hakan ke nufi? ko aure zaimata? toko Mamy ta faÉ—amai.? Kai bata tinanin haka. Tsawar da ya sakar mata yasa azabure ta saki kuka tana É—aga kai cikin gigicewa . Mamy tace Alhamdulillah ki shirya bikin ki nan da wata É—aya ,insha Allah zamu badaki ga wanda ya dace.. Tsaye ta mike tana raba ido tace'' Mamy nii ni za ama aure? to waima da wa? Afusace tace da Sadeeq ÆŠAN DAKO gidan nan insha Allah....... 5/18/22, 09:34 - MY MTN 2: *Littafin🌹DAN DAKO🌹 na kudi ne biya ki karanta cikin Aminci. Biya 300kacal to 0006454115 Amina Dahiru jaiz bank,or MTN card to this number 09165832002. then send the evidence of payment via 07038423451* ðŸ¤ðŸ™ðŸ¤² 🅿ï¸2ï¸âƒ£3ï¸âƒ£&2ï¸âƒ£4ï¸âƒ£ """ Wata dariya Amnah ta saki mai haÉ—e da kuka tana nuna kanta tace . Ni ! Haba Mamy nayi kama da matar talakka, Abba nah kana fa jinta waini zata ba ÆŠAN DAKO, nifa Abba! Amnah ka fa, kace wani abu mana. ta Æ™arasa a tsawace cikin gushewar hankali. Wasu maruka masu zafi Mamy ta yarfa mata tare da faÉ—in wallahi !wallahi!! baki da mijin daya wuce sadeeq,mijin nawa kike fad6ama magana? Tsaranki ne ?to kifara shiri inma zaki fara yar iska yarinya , Wato so kike in'barki kina kallon iskanci kenan ko, ta yanda nan gaba zaki fara fita gantali ko, ko kinyi tinanin bansani ba dan nasa miki ido?. Rawa sosai jikinta ya É—auka da wata matsananciyar kunya data rufeta, yanzu shikenan iyayenta sunga abinda take aikatawa ,To taji kunyarsu inaga ta mahaliccinta, Astagfirullahu lathi la ilaha illahuwa hayyu qayyum wa atubu ilaik tafara fada Cikin kuka tare da zubewa akan sahunta ta fara basu hakuri.. Abba yace" ta tashi ta tafi ta kwanta zai magana da Mamy. Bayan ta mikene tanajin wani irin jiri ta tafi É—akinta ta faÉ—a akan gado ta fashe da kuka . Ina zankaishi,talaka ne,ya Æ™awaye na zasuji duk ranar da akacemusu ÆŠAN DAKO, na aura. Duniya zatamun dariya, kana shima zai raina ajina ,kuka ta sake saki dai -dai lokacin da taji wayar ta na ring. Da sauri ta jawota ta É—auka tare da sakin wani marayan kuka. Afurgice Abul khairi ya mike tsaye daga jikin wata budurwa da suke kwance yace" Matata waya taÉ“aki, mike damunki, waya taba rayuwata yanzu inturo fadawa su kwasheshi? Cikin kuka tace. *Zasu rabamu Prince, sunyi kyautata wa mai aikin gidan mu, Prince ÆŠAN DAKO ne fa suka bashi ni, wallahi bana sonsa, bana Æ™aunar sa, Prince kai ne rayuwata, I love You so much, kwanamu biyu dakai Amma inajin sonka da Æ™aunarka na zagaye dukkan wata kafa ta jinin jikina, Abul khairi kaine Alkhairi zuciyata ,in na rasaka bazan iya rayuwa dakai ba , Abul come back to meeee tasaki wani marayan kuka. Wani halbi na fitar hankali yacsakar ma karuwar dake kusa dashi, da ta nemi jawo hannushi da niyyar taÉ“ashi. Ihu ta buÉ—e baki zatayi ya tausama fuskar ta pilo. Cikin rawar murya yace . Bazai taÉ“a yiyuwa ba, bantaba so ba Amnah, sai akanki ,kuma a kanki nike fatan karewa, ko É—azu muna tare da mai martaba ina bashi labarin ki ,na faÉ—amishi ko sarauta bazan iya karÉ“aba dan kula dake da yaran da zamu haifa, akan me ,mene kikai da hakan zata kasance, to ni Abul khairi bazan iya barwa kowa keba, inko har an'tsananta zan kwasheki mubar Æ™asar, mu tafi wata muje muyi rayuwar farin cikin mu. Tace karmi haka maisona, zamuson yanda zamuyi insha Allah ta kashe wayar tare da fadawa duniyar kuka da tinani. AÉ“angaran Mamy kuwa tana ganin Amnah ta fita ta sakko Æ™asa tare da kama gwiwar Abba tace. Mijina kazauna mufahimci juna dan zatin Allah ,kana ina rokon kamun kyakyawar fahimta kamar yanda kasabaman a lokutta da dama. Hannuta ya kama suka haura sama É—akinshi. Zama yayi akan gado tare da fuskantar ta yace. Ina jinki fulani waye ÆŠAN DAKO da kikama kyautar yarinyata batare da nasani ba? Anan takwashe komi ta faÉ—amai, har irin taimakon da ya musu sadda ake bibiyar su, da na maido Amnah gida. Tsaye ya mike ya na zagaye yace" Wannan ba hujja bace Fulani, bazai yiyuba gaskiya, kwara a'samu mutum mai nagar ta da cikakken family, ba wanda ba Muson asalin sa ba. Kuka ta samai tana sakin nishi mai zafi tace kafa duba Amnah har yau batason wacece ita ba. Yana da kyau ta fara rayuwar da zata koyi darasi a cikinta, inba haka ba to kawai boyayyan sirrin dake kulle zanje in'warware yanzu Wallahi, bazan iyaba, kason duniya zata zagen,i za amun kallon wadda ta gaza daga kurarin da tayi. Rungumota jikinshi yayi yace. Ki kwantar da hankalin ki kinga numfashinki ya fara canzawa, na yarda na amince da kalamanki, insha Allah gobe zanga yaron. Cikin tsananin jin daÉ—i ta amince mai dan danan ta wartsa ke ta fara rikitashi da zafaffan wasanni. cikin lokaci kadan suka afka duniyar jin daÉ—i. Sadeeq kam som idon shi baiga bacci ba, Saboda azabar da yakeji, ga sanyi da yarasa mizaimai maganinsa. Har akai Asuba ya kasa tashi. Æ™arfe bakwai Mamy ta shigo palon dan bataji motsin saba. Salati ta saki datagan shi yanata rawar sanyi. Da gudu ta Æ™arasa wajen shi ta tallaboshi tana faÉ—in" sadeeq! Dee nah! ka tashi Dan Allah karkamun haka haba sadeeq . Ajigace ya É—ago fuskar shi da tayi wani irin ja ya zubama Ammi ido ko kyaftawa ba yayi. Yana zuwa zai fara magana numfashin shi ya wani irin ja da Æ™arfin tsiya. Sanadin da yasa idanuwan shi Lumshewa kenan baki daya ko motsi baisake yiba ya saki... Sadeeq! Sadeeq!! Dee!!! Ammi tace arikice tana Dukan kumatun shi. Cikin matsanancin kuka ta tattaro shi baki É—aya jikinta ta saki wani mahaukacin kuka tana fadin shima na rasashi, shikenan Sadeeq, miyasameka ?miyasa kamun haka baka faÉ—amun ba, ko akan umarnin da na bakane ya saka HaÉ—iye zuciya .. Wayar shi dake gefe ta shiga ring. Cikin matsanancin kuka Ammi ta É—auka tare da sakin sabon kuka. Dan Abbah yace a'kirasa su tattauna dan zai fita. Afurgice mamy ta mike tsaye tana faÉ—in minene, miya faru daku, Ammi ina sadeeq ,miyasamu sadeeq É—in? Sadeeq ya tafi ya barni Hajiya shima na rasashu, ya tafi da burin É—aukar fansa ran mahaifin shi da na yar uwar sa, Hajiya narasa kowa Ammi ta Æ™arasa cikin matsanancin kuka... DaÉ“as Mamy ta faÉ—i Æ™asa tare da kecewa da wani kukan da yafi na Ammi Æ™arfi tana dafe zuciyar ta.. Cikin tashin hankali abba ya É—auki wayar anan Ammi tamai bayani ,ya nemi jin kwatancen unguwar da suke dan suzo. Ammi tamai tana kashe waya tana jijjiga Sadeeq. Da sauri ya sama Mamy hijjob inta tare da mikar da ita suka fita tanata kuka. Da kanshi ya tuÆ™a motar har unguwarsu Ammi. Da hannu Mamy ta nuna mai har gidan su. Suna zuwa suka afka gidan Tare. Inda suka jiyo kuka Ammi anan suka shiga. Dai -dai lokacin da Ammi ta É—ago kanta cikin kuka dan ganin waye... A É—imauce cikin rawar baki ta mike tana nuna Abba da hannu tace Alh isa dama kana raye? Dama kaine mijin ta? innalillahi wa inna ilaihi Raji'un. Cikin rawaa baki Abba yace" ina nan Doctor wallahi ina nan. Mamy data kasa fahimtar kalamansu hankalin ta naga sadeeq tace . Kufa kamashi mukai shi a dubashi yafi wannan surutun kila ba mutuwa yayi ba. Da sauri Abba ya fara Æ™oÆ™arin É—aukar sadeeq amma ya kasa ,saboda ingarman namijin gaskene. Cikin sauke numfashi yace" ranki ya daÉ—e kiyi hakuri ki danne damuwarki dan Allah ki duba sa . Ita sai lokacin ma ta tino da kayan aikinta . Da gudu ta isa É—akinta ta kwasosu taci gaba da duba shi . Cikin awa É—aya numfashin sa ya kawo. Hamdala ga Allah Ammi ta fara tana dariya da kuka. Cikin myutya marasa lafiya yace "Ammi zanyi wanka in Sallah . Tace" to sadeeq kana iya tashi ko kabari ka karajin sauki. Kai ya gilgizamata alamar A'a. Su Mamy ya kallah tare da zubama Abbah dake kallon shi ido kamar ya son shi. Cikin kulawa Abba yace sannu yarona. Kai ya É—agamai yana duban mamy dake jeramai sannu cikin zallar tausayawa. Itama kan ya gilgizamata tare da tashi cikin dauriya . ÆŠakin Ammi suka zauna inda Ammi ta kalli Abbah tace yarinya kace kenan sadeeq zai aura, na amincema airyan koda nan da sati biyu ne . Abba zai magana ta É—agamai hannu tare da cewa . Ka adana kalamanka nan gaba samana rana ,aje a fara shiri, koma meye ya biyo baya. Godiya ya hau jeramata wadda taba Mamy mamaki. Cikin kwana biyu cikin ikon Allah sadeeq ya warke ya koma bakin aiki. Yayin da Amnah ta hana kanta walwala kullum tana cikin É—aki tana waya da Abul khairi , Dan shine kawai ke sata jin sauki, ko abinci tadaina ci duk ta rame,ga Bily bata Æ™asar, hakan yasa ta rasa wazata fuskanta da damuwar ta, dan sauran Æ™awayen ta tana ganin abun kunya ne suji magana su kuma rike sirrinta ,bayan sunson Æ™udirinta.. Washe gari aka sanya biki wata É—ay.. Mamy ta zage ta fara gyaran Amnah duk da tana gardamamata saita hada da faÉ—a kana suke dai -dai tawa. Amal kuwa ranar da ta samu labari har jinya tayi, Dan tin ranar farko take DAKON son Sadeeq amma ta fawwalama Allah komi , tare da rokon ya ciremata sonsa ya bata wanda zai fishi. Ta É“angaran Amnah kuwa Abul khairi ya kwantar mata da hankali akan tayi hakuri tayi auran, Tin da ba son mijin take ba anan ne zasu mafi samun damar sakewa su mulki soyayyar su son rai. Hakan yasa ta É—an saki kaÉ—an har tana cin abinci, Amma zuciyar ta fall take da nau'in azabar da zata gana mai , Dan da kanshi zai saketa ta tafi ta auri zaÉ“in ta. Dan ita talaucin shine kawai kesata kinsa amma da da azzikinsa da tafi kowa murna saboda ya haÉ—a komi. Biki na ragewa saura sati É—aya Nene ta dawo gida da zama tare da fara yima Annabin wankan lallai kullum , Da bata wasu magunguna irin nasu na mutanan da sai tace na tsarin jiki ne, haka take tausa mata Magungunan da take bata dakyal suke barin ta bacci, Dan sai tayi download din kayan baÉ—alata kana take rarragewa ,wani yanayi na buÆ™atuwa kawai take jinta a ciki.. A É“angaran Sadeeq kuwa ko ajikinsa, tin ma ranar da sukai mai magana ya watsar da magana harka gaban shi kawai yake. Saura kwana ukku biki Ammi tace Sadeeq kayan lefe ya zamuyi dasu kana Sadakifa? KafaÉ—arshi ya É—aga" yace banda su" . Ammi tayi jim tana wani nazari zuwa cen kuma ta saki murmushi tace jiya ka kwashi albashinka ka zaro 20k abasu . 10k kayan sawa 5k tayi hidima biki, 5k sadaki . Yace"shikenan tare da zuwa É—akinta ya dakko ya bata . Waya tama Abba cikin kankanan lokaci sai gashi yazo. Anan ta zaro kudin ta bashi ta fadamai duk abinda ta keso. Kai ya jinjinamata cikin gamsuwa tare da mata sallama ya tafi. Bayan yaje gida ya nunama Mamy abinda suka bada taita godiya . Yace fulani kodai in Æ™ara akai ?wallahi abin nan na É—agamun hankli banson halin da Amnah zata shiga ba. Murmushi Mamy tayi tace'' A'a Hayatee zasuga mun raina mu da sukama Alfarma, Allah ya amfana ,kuma wannan ma ai ya na É—aya daga cikin darasin da nikeso rayuwa ta koyamata ko. Yace shikenan tare da fara waya wa Abokansa ya sanar dasu ÆŠaurin auran Yarsa, da gidajen Radio ko ina dai. Da yamma Hajiya Turai tazo ita da wata mata da ganinta ba cikakiyar bahausa bace tafi kama da shuwa'arab. Tace ma Mamy ta kawota ne dan ta gyara jikin amarya. Mamy tayi na'am da hakan tare da zama suka fara tsara yanda abun zai kasance. Cikin kwana biyu gidan Mamy ya rikice da mutane wayan da aka gayyata da wayan da ba agayyata ba, kide -kide kawai ake. Agefe ga yan unguwar su Nene Æ™awayen ta tsaffi sunata buga kwarya sunyi layi da ankon su na sallah da Nene ta rabamusu. Nene ce ta iso da sauri tasha kwalliya da uwaye gwala gwalai tace'' haba kukam anyi masu busashen hannu ,Yo ko zafi bakwaji,sai dukan kwarya kuke ,haba ku ajiye kuje kuyi wanka sai wari kuke muje É—akina kuci abinci ,inba haka ba wallahi baku shigar shi sai dai in buÉ—e maku wani. Tashi sukai suna faÉ—in da wankan mu kwara kibamu muci anan. Aiko ta tafi tana rausayawa ta kyalesu. Washe gari da safe ta kama juma'a ranar É—aurin aure kenan. Sosai gidan Mamy ake hada_ hada tana zaune palo ita da Hajiya Turai tasha wanka da wasu Æ™awayan su sunsha kwalliya sai kyalli suke, fuskar su cike da farin ciki. A É“angaran amarya kuwa tana kwance É—aki ko wanka ta kiyi sai waya take inda abul khairi ke bata shawara akan in taga zata shiga damuwa zai bata wani magani Bacci masu yawa ko gidan taje ta yawaita shan su dan tasamu hutu ta rage tinani . Sosai ta yi na'am da shawara sa dan Haka taji daÉ—i haduywa dashi dakuma shawara Bily da ta bata akan tayi wayar sirri da yanzu an'dakushe farin cikin ta.. Matar dake mata gyara ce ta kwan-kwaso kofar. Amnah ta boye wayar ta tashi ta budemata. Fuska a É—aure ta shigo da wani sabulu tace" muje toilet. Cikin bacin rai tace ke nifa na gaji kinji, an turoki wani sangam -sangam to banaso bazan ba . Mikike faÉ—a Amnah Mamy tace'' data shigo. Aguje ta shige toilet din tana kuka. Matar ta bita ciki anan ta gwada mata yanda zatayi amfani dasu kana ta juya baya dan ta samu tayi. Wankan tayi tayi kyau sosai fatar sai sheki take. Suna fitowa ta tsantsaramata kwalliya tare da bata wani dakeken lace silver color mai tsada aka shirya ta. Ana sakkowa daga masallacin juma'a suka farajin kida da busa cikin gidan . Yayin da Amnah ta Æ™araso wajen window tana karema zugar mutanan da suka halacci ÆŠaurin aure ta. Ga unguwar ta cika. Kwafa tayi tace da kanka zaka maidoni talakka. Karaf ta farajin maroka na faÉ—in an ÆŠaura auran Aminatu Isa mai zinari Da Sadeeq ÆŠAN DAKO akan Sadaki naira dubu biyar lakadan ba ajalan ba.... Ihu ta saki tana dafe kirjinta da yayi wani mahaukacin bugu. Da gudu Hajiya turai ta turo kofar ta shigo Mamy na biye da ita ta janyo hannu Amnah tace" muje palo ga mijin ki nan ya iso.... 5/18/22, 09:34 - MY MTN 2: *Littafin🌹DAN DAKO🌹 na kudi ne biya ki karanta cikin Aminci. Biya 300kacal to 0006454115 Amina Dahiru jaiz bank,or MTN card to this number 09165832002. then send the evidence of payment via 07038423451* ðŸ¤ðŸ™ðŸ¤² 🅿ï¸2ï¸âƒ£5ï¸âƒ£&2ï¸âƒ£6ï¸âƒ£ "" Kallon su tayi ta saki wani siririn kuka tana kallon kanta a madubi. Tace'' ni ! Nice aka bada sadakina dai- dai da kudin kazar da nike ci kullum a rana ,ni aka saya da masifar arha 5k kudin gyaran kaina, 5k Æ™arama kyautata ga wanda na raina ,Ni Amnah Mai Zinari akama haka, ni akama sayan tsuntsaye , Mamy inaso kifaÉ—aman wacece mahaifiyata, Dan ban yarda ke kika haifeni ba , Duk kan uwa fatan ta yar ta taje gidan da zata huta, Amnah banson minai miki ba kikamun haka ,kika bani wanda ba kullum ma yake samuba sai karshen wata ,to mizan dinga ci Mamy,miyasa baki tambaya ra'ayina ba kamin ki yanke hukun ci?. Tsawa Mamy ta dakamata cikin fitar kwallah tausayi Amnah dake zuboma ta. Cikin kuka ta kama hannu Annabin ta rike tace . Amnah bazaki gane gata na miki ba sai nan gaba, bansani ba lokacin zai iskeni da rayuwata ko akasin haka, Wallahi Amnah uwa bata yarda takai É—iyarta wajen da zata cutu,da kike zancen mahaifiyar ki ni É—in nan daice na haifeki cikin yanayi na Æ™asÆ™anci da tausayawa na rashin gata. Amnah ana dukana na haifeki , Amnah akan kwalta titi uwarki ta biya , Amnah ! Amnah ta saki kuka sosai mai ban tausayi ta kasa Æ™arasawa. Galala haka Amnah ke kallonta cikin tsananin tashin hankali, to mitake nufi?. Da gudu ta karasa wajenta ta faÉ—a jikinta tana fadin Mamy wai minene kike boyewane ga rayuwata ,wacece ni? suwaye suka dukeki, ina Abbah na A lokacin. Hajiya Turai dake kuka sosai ta share hawaye ta tace Fulani miyasa zaki É“ata farin cikin ki,Miyasa zaki fara sakin zance cikin gushewar hankali. Amnah tace "Momy Turai mike faruwane. Mamy ta riko hannu Amnah tace kimin alÆ™awarin zama gidan sadeeq , kimai biyayya Amnah, ki kyautatama sa, kirike sirrin sa, kidaina mai abinda kikaga dama , Dan na tabbata yafiki gata nesa ba kusa ba, nan da 12- 1-2023 na miki alkawarin zan sanar dake tarihin rayuwata , Amma kimin alkawarin kyautata rayuwarki agidan auranki, ina mai miki nasiha da kiji tsoron Allah Amnah, kiso sadeeq dan Allah badan yana da azziki ko bashi da shi ba, Azziki na Allah ne, wata kil in Allah yaso kizama Abokiyar azzikinsa, kana ki so uwar sa da Æ™anwarsa dan sune kawai farin cikin sa, in'kinmin wannan alfarma ina rokon Allah ya lulluÉ“eki da rahma, yasa ki farin ciki har karshen rayuwaki, in'kuma kinÉ“ataman Amnah zaki gani , ni dai nason na sauke nawin ki dake kaina, na miki tarbiyya dai-dai iyawa na. Dole ta sani miki aure saboda halin da naga kina neman sa kanki na halaka, kuma saida muka sauke hakkin ki kikace baki da kowa. A irin rayuwar da kika fara yanzu Amnah Aure shine mafitar mu,kuma rufuwar asirina, kitashi muje nace ta faÉ—a tana share hawayen ta. Cikin sanyi jiki Amnah ta mike ta bita tana share hawayen ta, Tare da alÆ™awarin kyautatama umarnin mahaifiyar ta in zata iya insha Allah, sai dai ko sha'awar duniya zata kasheta bazata yarda sadeeq ya raÉ“eta ba , Saboda bashine burin rayuwar ta ba, Abul khairi ta yima wannan tanajin ,dan nlshine ke sonta shi zai tarai-rayeta ko bayan ya mallaketa, shikam wannan baya so ba taso da muguntama zai iya haÆ™emata ya yaga banza. Hajiya Turai ta Æ™ara gyaramata fuskan ta sosai tare da kamo hannuta kanta akasa suka fito. Anan Æ™awayen Mamy suka fara guda Nene ma ta yo kanta da zugar abokanta da yan fans É—in group É—in ÆŠAN DAKO ga baki É—ayan su sunma Nene Æ™ara , Nene na taji dasu saboda tasan mutanan Azzikine ga haÉ—in kai da son juna. Suna kawowa palo Sadeeq yayi sallama ya shigo shida Abbah . Sanye yake cikin wani yadi yellow mai masifar saukin kuÉ—i wanda a'Æ™alla duk yadi bai kai 500 ba, Sai hular shi taÉ“ani kaji hadith daya sanya hannu shi rike da casbaha. Cikin murna Mamy ta tarebeshi tana nunama Æ™awayenta ga surikin ta, ga sadeeq mijin Amnah. Lokaci guda gulma ta ciwo mutane aka fara gwara kawuna kowa da abinda yake faÉ—a. Shikam Sadeeq murmushi kawai yake dokawa yana binsu da kallo ta Æ™asan ido.. Hajiya tuyrai ta cema Annabin ga mijinki kije a muku photo na tarihi ko? Ahankali ta É—ago idanuwanta ta zubasu a cikin nashi da ya tsareta da ido.. Hajiya tyiurai tace. "Affuwan na tino ganin mu bazaisa su iya ba, Dan Allah sadeeq kamata kuje palon sama, ke Amnah maza kuje sama na turo muku mai photo a cen. Kamin ma ta rufe baki ya iso wajenta tare da cafkar hannuta ya fara janta A'hankali inda suka nuna musu. Kamar rakuma haka take binshi som hankalinta ya gushe, tinaninta na neman barin ganga jikinta,wannan ne zata aura.. Suna bi ta step É—in karshe ya hango haÉ—aÉ—É—an palon da yafi na kasa tsaruwa. Hannuta ya saki tare da samun kujera yayi zamanshi yana mai dora kafa daya akan daya yayi shuru.. Kwas !kwas !! kwas!!! ya fara jin sautin takowar ta da tsinin takal manta. Gaban shi tazo bata tsaya komi ba ta durkushe kasa tare da kifa kanta akan kujera da yake ta saki kuka sosai. Baice komi ba dan shima da da dama kukan zaimusu. Sai da tayi dan kanta fuskar ta duk ta É“aci da hawaye, majina, tayi kaca- kaca. Ahankali ta É—ago fuskar ta tace. Na rokeka da Allah ÆŠAN DAKO kayi hakuri ka sawwakemun ,na maka alÆ™awarin kudi mai masifar yawa da zasu isheka gina rayuwar ka. Kai kason som babu dacewa tsakanin ni dakai. Ka kalleni ka kalli zubinka katsan wutsiyar rakumi tayi nisa da kasa. Tindaga kan sadakina na Tabbatar da zaka aureni ne dan wulakanta rayuwata, ni zaka bada sadakina 5k kudin wannan koÉ—aÉ—É—an yadin na jikin ka ,ka taimaka ka sawwakemun Dan Allah . Baki ya taÉ“e tare da mikewa tsaye . Ahankali ya taso da ita ya sanya duka hannayen shi ya dafa kafaÉ—arta, ido cikin ido suke kallon juna. "Yace Amnah bana sonki som, Saboda ke baki da tarbiyya, kana bakiyi kala da macen da nike soba,farace ke nikuma bakar fata nike so,ke yar masu kudice nikuma talakka nikeso Yar uwata,banson wacece keba nikuma mai asali nike so,ki iya bakinki wannan auran auran taimako sunan sa. Saboda darajata da son a taimaka miki har gaban mahaifiyata akaje neman auranki, kinga kam tabbas ni mai tsadane. Da yanzu wayan da sukaje nema miki aure zasu dawo suce a sawwaÆ™emaki Wallahi cike da farin ciki zan sallameki, sabosa bana sonki, Ke daga irin shigar danayi kinson cewa ba auranki ne gabana ba. Duk talaucina bazan iya sanya wannan yadin ba. Shiyasa ko da naje kasuwa nace abani yadi mafi sauki, mafi kuma muni , Saboda ni yau ba ranar farin ciki na bace. Ni ba ustaz ba ,ba liman ba, amma kinga hular danasa saboda in nunama duniya duk tsadar da kike faÉ—in kina da ita to ga a inda kika kare, ita duniya budurwa wawace. Albishir na karshe ina miki murna shigowa gidan ÆŠAN DAKO nan da kike cewa, nan da mint talatin ki shirya Mai adaidaita zaizo ya É—aukeki, dan dan ban amince ki shiga motar kowa ba. Kana karki kuskura kisama ranki zaki tafi da takaddun aiki dan bazan fita kifita ba ban lamunce ba. Hancinta ya lakace yana fadin sai munhaÉ—e yam mata ya ficce cike da Æ™asaita batare da anyi photo ba... Kwaraf ta faÉ—a akan kujera tacigaba da kukan ta tana faÉ—in kagama dani ka cuceni wallahi ka cuci rayuwa ta.. Bayan fitar shi su momy sukazo sukace taje taci abinci sunkusa tafiya. Sadeeq kam cikin jin daÉ—i da nishadin takaicin da ya tusamata yafita ya zare kayan ya badasu wa Baba masu . Ya zira wata farar shadda da Abbah ya bashi suka ficce sai gidan Ammi shida Abbah bayan ya sallami Abokansa. Cikin farin cikk sosai fuskar ta cike da annuri, tasa wata atamfa mai kyau tana ta zuba murmushi. Sallama sukai suka zauna. . Ammi tace "Sannu Alh Isa da kokari, an'samu muhallin zaman kuwa? Kai ya jinjina mata fuskar shi babu yabo ba fallasa, yace an'samu Doctor! Amma miyasa kika kafe akan Bazai karÉ“i gidan dana mallaka musu ba?. Tace'' saboda nayi magana sirri da mahaifiyar ta , Dan haka abar ta hakanan kawai. Kai ya jinjina yace ''to wanda dai muka samu mai kyau Mai haske yanzu, ÆŠaki daya ne tal , sai tsakar gida da baifi zaman mutum biyu ba, sai kiching da toilet ajere, kinji fa tsarin gida . Tace ya ishesu Allah ya am'fana. Yace Ameen tare da tashi ya tafi jiki a'sanyayye. Bayan ya tafi suka fara tattauna magana da banajin mi suke faÉ—a. na daiga sadeeq É—in ya natsu sai gilgiza kai yake. Tace ka tashi kasamu mai napep kaje ku dauketa, Nason zuwa yanzu sunkammala aikin da zasuyi ,am ban tambayeka ba ya sunan unguwar da zaku zauna?. Kai ya shafa danshi kunyama yakeji ace dagashi sai mace cikin gida kamar wani kwarto. Yace cen sabon layi ne. ''Ta gilgiza kai cikin gamsuwa tare da cewa. "Sadeeq kaji tsoron Allah kayi aiki da hankalin ka karka cuci yar mutane, Daka cuta kwara a ciceka, Sadeeq dan girman Allah karkayi amfani da karfinka da ikon hakkin dake kanka nata ka juya musu É—iya kadai son irin halaccin da suka mana ko? ko ka bata wahala, A'a ina umartaka da duk abinda zakayi kayi wanda bai saÉ“ama sharia ba kaji,Kana ayanzu dole kana mata uzuri koda zaginka zatai,na baka umarnin kabata wata biyar in ta sauya Alhamdulillah, daganan sai ka fara aikin ka,in kuma bata canzaba to sadeeq ina mai baka umarni ka rabu da ita saboda ba macen aure bace kasamu wadda ta kwanta ma... Yace'' insha Allah tare da tashi ya canza kaya zuwa na wayan da ta fara ganin shi da su ranar farko na Buzaye ya fita, tare da tare Napep yayi gidan Mamy. Yana zuwa ya zaro wayar shi ya kira Mamy . Bayan ta É—auka tace . Ya samesu palon Abbah. Sallama yayi ya shiga tare da samun wuri Æ™asa ya zauna. Anan Hajiya Turai ta fito da Amnah dake sanye da wata Atamfa mai masifar kyau Ash, an'samata Alkyabba silver sai kamshin take aka zaunar da ita kusa da Sadeeq. Abba da idanuwa'nsa sukayi jawur ya É—ago ya zubama Amnah da kanta ke kasa ta nata kuka ido. Anan ya fara musu nasiha mai ratsa zuciya. Daganan ya janyo 5k din sadakinta ya dam Æ™amata. Yace" gashi Amnah sadakinki ne, ki rike abinki zasumiki amfani. Magana ta karshe Amnah ana nemana wajen aiki dole gobe zan koma ,kuma wannan karan da mahaifiyar ki zantafi da yar uwarki saboda ta kammala karatun ta acen. Ina fatan in harhaÉ—a dukiyar kasuwancina indawo kasata nima. Dan haka yanzu duniya baki da wani makusanci sai Sadeeq. Ina miki fatan Alkhairi da fatan nasara a'cikin sabuwar rayuwar da zaki tsinci kankk,ina fatan Allah ya baki ikon cin jarabawa da ya É—ora miki. Sakacinki yasa Mamy ki dauke gwala-gwalan ki dan karkiyi wasa dasu zata ajiye miki,kana takaddun makarantaki suma za a ajiye, magana aiki kuma yace bai amince ba ,dan haka kiyi hakuri ki fuskanci buÆ™atar mijin ki. Sako na nan na ajiye miki acikin Dakin ki cikin lakar gadon ki dake Æ™asa, Allah ya baku zaman lafiya da zuria dayyiba. Ya zaro Æ™arama waya ya bata yace "gashi zamuna waya insha Allah gobe zamubi jirgin safe.. In akwai abunda kike buÆ™ata ga Momy Turai nan ki faÉ—amata, ko Nene, duk zasu miki maganin matsalaki insha Allah, sadeeq ku tashi ku tafi. Kuka Amnah take kamar ta HaÉ—iye zuciya ,Tanaji da taga wannan bak'ar rayuwar kwara mutuwar ta. Kam ta kama Abbah ta rike tana kuka tana bazani ba bazanje ba, Wallahi nadaina abunda bakwa so,Bazan sake ba dan Allah karku badani wa ÆŠAN DAKO. Da sauri Abbah ya kwace daga rikon da tamai ya faÉ—a É—akin shi . Duk dauriya ta namiji wani irin kuka ya saki yana faÉ—in why! why!! Doctor, Miyasa Fulani, Nene miyasa kuka zaÉ“i wannan rayuwar wa Æ™arama yarin ya. Mamy ma kuka take Amal kam gefe ta koma tana kallon sadeeq tana kuka tana kuma tausayin Amnah da rayuwar da taji ana tsara zatai. Lokaci guda tsannin tausayin su ya mamaye zuciyar sa . Tashi yayi tsaye baison sadda ya jawo Amnah jikinshi ba yace" kiyi hakuri Aminatu muje. Turjewa take tana kuka akan bazata ba ,amma cak ya É—agata yana rike da akwatin ta suka fita. su Mamy suka bita suna ÆŠagamata hannu suna share hawaye. Ganin sunshiga napep yasa Mamy dawowa palo tasaki wani mahaukacin kuka tana faÉ—in Amnah dole tasa, inaso kizama mai zuciyar tausayi,inaso kifahimci rayuwa ,inaso kisan daraja Dan Adam tin kamin kiji ko wacece ke,ya Allah ka cikamun burina, kasa wannn auran yazama Alkhairi ga ahlina da kuma dawwama farin ciki na. Ameen Amal tace suna komawa ciki. Anan sukaga Nene tana kwance ykasa sai burgima take tana kuka, idonta yayi mahaukacin kumburi kamar fitila besfa. Shikam Sadeeq tinda suka tafi take ihu tana kururuwa tare da kiran sunan Abba, Dan ta riga ta yardama kanta ba Mamy ce Maman ta ba. Ganin duk inda suka wuce tana tara mai mutane hakan yasa da karfi ya riko hannayenta. Tare da tausa halshensa cikin bakinta ya danne mata halshe. Hakan yasa ta waro idanuwa akan nashi tana gilgizamai kai alamar ya barta. Banza yayi da ita dan in ya kyaleta kowa sai ya kalleshi. Ajiyar zuciya taita sauke har suka kawo Sabon layi Mai Napep ya tsaya basu saniba sai da ya juyo yace" am Malam ina.. Kan ya karasa yayi Saurin juyawa yana" haba Yallabai, ya kake haka? mu gwauraye ai sai muyi sama da yan matan titi.. Akasalance ya juyo ga baki É—ayan idanuwancshi sunyi jawur, da hannu ya nunamai wani Æ™aramin gida da yasha sabon penti milk. Saukesu yayi ya sallame shi i yace ta fito. Cikin masifa tace bazan fito ba, wallahi babu inda zani sai ka maidani gidan ubana, É“arawon banza barawon wofi. Kanshi ya gilgiza tare da jawo hannuta ya saÉ“a a kafaÉ—a kamar buhun gero, hannu guda kuma ya ja akwatin har Æ™ofar gidan . Ajiye akwatin yayi tare da sanya key ya buÉ—e gidan . Bayan ya shiga ya rufe tare da jera Addu'a kana ya direta yace" kishiga da Æ™afar dama. Da karfi ta taka bakin kofar da Æ™afar Hagu tana murzawa tace nashigo da hagu nashiga, kayi duk abinda zakayi ,Albarka nike nema a auran naka akacema?kuma bazan kwana agidan nan ba shegen gida kamar kabarin sheÉ—ani ,ni zaka kawo gidan da ko Tsuntsuwa bazan iya ajiye wa ba, wallahi sai ka sakeni taci kwalar shi da Æ™arfi. Akwatin ya ajiye gefe tare da kama duka hannayenta yace "Amnah ni É—ane, kana na halak, mai kuma burin faranta ran iyayen shi ta hanyar yi musu biyayya, zansake maimaitamiki wallahi bana sonki som, bakya cikin ra'ayim matan da nike so,Amma na karbi kyautar ki bisa ga umarnin da iyayena suka bani. Cikin kuka tace ba dole ka karÉ“a ba ,makwaÉ—aici kaida iyayen naka, banzaye wanda baida uba,talakan Æ™auye kawai,Wayan da babu abunda suka ajiye sai maula, daga karshe kayi kulle- kullen ku na yan iskan kauye ka auroni, to baka isa in'zauna da kaiba, in'kau harka matsa to ba shakka zanyi auran Ƙauna akan Auran ka..... 5/18/22, 09:34 - MY MTN 2: *Littafin🌹DAN DAKO🌹 na kudi ne biya ki karanta cikin Aminci. Biya 300kacal to 0006454115 Amina Dahiru jaiz bank,or MTN card to this number 09165832002. then send the evidence of payment via 07038423451* ðŸ¤ðŸ™ðŸ¤² 2ï¸âƒ£7ï¸âƒ£&2ï¸âƒ£8ï¸âƒ£ ""Sakin hannuta yayi ya matsa gefe tare da jawo wata Æ™arama kujera ya zauna ya zubamata ido yana mai jin zafin yanda take surfamai zagi da iyayen sa, Amma yayi alkawarin kyaleta zai bata wata biyar kamar yanda mahaifiyar shi tace ,saboda ya tara laifikan da tamai dan yasamu hujja rabuwa da ita. "Cikin natsuwa yace'" Dan kinyi aure akan aurena ni ba damuwata bane ,kana bani da hukuncin da zanmiki, amma wanda ya yiki ya yini zakiga yanda zayyi da rayuwar ki ,Ruwanki ne kishigo ko kibi ta sama kifita . yayi tsaki ya shige É—akinta. Masha Allah É—aki É—ayane tal ba laifi yayi kyau amma ko bedroom babu aciki, a kasamata Italian bed fari sol mai kwalliyar pink mai masifar kyau, sai wadrob da sauransu, sai sai wata kujera mai masifar kyau irin ta hutawar nan kwara É—aya . Dakin babu Ac amma akwai fanka. Kallon É—akin yayi ba tarry da ya ce komi ba ya sakko kasa ya zaman shi yana latsa waya. AÉ“angaran Amnah kuwa rai bace ta zare alkyabbar jikinta tare da banka kyauran da take tinanin kichin ne, anan taga É—an karamin toilet amma yayi kyau, kuma an Æ™awatashi da kayan zamani. Gudan kyauran ta tura taga kiching ne babu wasu tarkace sai abun amfani ,sai kam kayan abinci jibge babuce kawai babu wajen. Tsaki tayi sosai tare da share hawayen ta ta Samu wuri tayi zamanta tare da fiddo wayar ta ta fara chart tana kuka. Abul khairi yace . Baby har an kaiki an É—aura miki nawin wani kato akanki ko , Dan Allah kimin alkawarin killace kanki kar kiba wani wawa damar ko da rabar inda kike😭😭😭ya nuna alamar kuka. Kuka take sosai tace. Kai ne muradina Abul! babu shegen da zan iya bari ya raÉ“eni ,wallahi kai nike so. Daganan sukaita fira ya kwantar mata da hankali akan ta saki jikinta. an'jima tasha maganin da ya turo mai gadin ayu ya kawomata. Tinowa da hakan yasa cikin jin daÉ—i tace nagode masoyi ,tare da datse wayar ta É“oye taci gaba da zamanta nan har aka fara kiran salla mangariba yazo yayi alwallah tare da cewa kitashi kiyi sallah. Tace" bazan ba kabarin ka daban nawa daban.. Kyaleta yayi yana gamawa ya juya baya yana tafiya. Kallo ta bishi dashi na harara daga sama har kasa tana sakin tsaki! Da faÉ—in namiji har namiji amma jibi shigar shi wawa kawai ,Dama dan ya samu aurena ga Sallah yay ta kashe kala, aiko zaka gane kuran ka, duk sai na toya kayan ka in'yaso ka zauna tsirara . Murmushi ya saki dan duk kan abinda ta faÉ—a yaji. fita yayi daga gidan tare da samai key, yana zuwa masallaci yayi sallah, bayan angama ya zauna har saida yayi isha'i, tare da zama waje É—aya ya fara kwararo Addu'a shirya wa Amnah, da kuma neman Allah yabashi dan gana ya taushe zuciyar shi dagaji da ganin mumman abinda zatamai, ko ta faÉ—amai. Wayar shi ta shiga ring . Fitowa yayi tare da É—aukar . Anan yaga Mamy ce. Bayan ya É—auka ya gaisheta tace mai in yana kusa dan Allah ya zo ya Æ™arbi sako. Yace gashinan zuwa. Mashine ya tsaida sai gidan su. Bayan ta fito ta mikamai wasu manyan kuloli tace gashinan sadeeq abinci ne, ga kuma key É—in machine din ka. Karba yayi ya mata godiya sosai tare da fatan nasara a tafiyar da zasuyi . Hakuri taita bashi game da abinda Amnah za tamai, daga nan ta mikamai wata leda mai girma da keta masifaffan kamshi, tace'' gashi kabata sai yanzu aka kawo. Yace shikenan mungode ya hau machine dinsa ya biya gidan Ammi tare da buÉ—e foodflaks É—in dake cike da kaji ya É—ibar musu dai -dai yanda zasu ishesu ,kana ya mata sallama ya fito kamar yayi kuka, wai shine yau zai raba makwanci da iyayen shi , Allah gamu gareka yace. Ammi ta biyoshi ta rufe gidan ta koma. Kai tsaye gidan shi ya nufa bayan yaje ya shiga da machine soron gidan ya Rufee gidan tare da sallama ciki. Itakam Amnah tinda ta shiga É—akin taji wani kafurin zafi ,hakan yasa ta cire duka kayanta ta daura wani towel tayi kwanciyarta ta É—au waya dan dama ba sallah take ba. Akaro na biyu da yayi sallama bata amsaba ya sanya kai. Sosai yake jin yanda take waya wadda ya kasa tantance dawa take, dan muryarta baya ko fita. Ita kuwa ganin shi som baisa ta katse ba taci gaba da soyayyar ta tana samun saukin zuciya. Gefe ya koma har saida ya kwashe wajen awa daya kana ta katse wayar tayi shuru. Yace ga abinci nan inji mamanki kichi. Da sauri ta duro dan dama masifar yunwa takeji. Kiching din da tagani taje ta É—akko flat ta buÉ—e fridge ta dakko ruwan sanyi da lemon chi exotic ta dawo ta zuba nama sosai ta koma gefen gado taci nama,saida ta koshi ta ajiye gefe, tare da tashi daga ita sai towel ,sai kam gashinta da yasha gyrata ta sakeshi sai yawo yake ta fita. Da ido ya bita yana mamakin rashin kunyar ta, daga zuwa gidan miji sai hunce wa, lallai wannan som ba tada kunya ,dan koni bazan iya haka ba. Bakinta ta wanko tare da kunna pampon deke tsakar gidan ta cire towel din ta tarba babban boket ta fara kwarara ma jikinta, hankali kwance take wanka, dan tayi alkawarin gana mai azaba da dakan shi zai sallame ta. Fitowa yayi da niyyar É—aukar flat É—in da zaici abinci. Anan ya ganta tsaye duk da tsakar gidan babu haske amma akwai na farin wata, hakan ya sashi zaro ido tare da komawa da masifar karfi yana dafe saitin zuciyar shi, dan shi bai taÉ“a ganin babba mace tsirarra ba inba Amnah ba. Tinani ya fara anya ba akwai wata a'Æ™asaba da aka bashi wannan yarinya ?shi ya taÉ“a gani ko jin sabuwar amarya haka ,anya yarinya nan cikakiyar budurwace kuwa? Innalillahi wa inna ilaihi Raji'un yace yana jingina da bango. Itakam hankali kwance ta gama duk Abinda zatayi kana tayo É—akin tana tako... Hanya ya bata ta shige tare da fitowa. Anan ya dauki flat din ya zuba kaÉ—an ya dawo waje yaci. Yana gamawa yaje yayi wanka ya dawo da kayanshi ya mayar a jikka sa ,ya É—auki wasu Æ™ananu yasa ya koma kan sopa ya kwanta. Amnah kuwa chart tai tayo sai É—aya na dare ta kwanta. Washe gari bayan ya dawo Sallah Asuba ya shigo tare da cewa" kina lafiya? Banza tayi dashi ta kyale sai wayar ta da ta daina jin shakkun boyewa. Shima shareta yayi ya son dai Alhamdulillah yafita hakkin ta. Mamy ta kirashi tamai bankwana suka tafi ,yana mai kara jin girmanta har cikin ranshi, dan som bata nemi yar data haifaba takashe wayar. Daga haka bacci ya kwashe shi. Karfe goma ya tashi ya kalli inda take kwance tana bacci. Ƙarasawa wajenta yayi yana kallon fuskar ta ,tsaf irin ta Mamy, dan dai zuciyar ba É—aya ba. Bakin gadon ya É—an kaima duka kaÉ—an . Cikin magagin bacci ta bude idonta ta zuba ma fuskar shi ido, tare da shafo sajen shi tace ina sonka Abul khairi, babu wanda ya isa ya mallakeni sai kai ,kaine burin raina, kai naiwa tanajin rayuwata,karike alkawarin mu,dan kai nike fatan bama makullin sirri nah... Idon shi ya lumshe tare da janye hannuwata yace. " Miza'asiyo miki wanda zakiyi amfani da shi?. Cikin wani irin zafin nama ta mike tana watsam@i harara tace. "Miye Haka, ina mafalkina zakazo kamun wani tukus gabana, ba'aso, waye zaimaka girkin ,aiko sai dai kayi duk abinda zakayi mtsss . Baice komi ba sai zuciyar shi da ya farajin tana mai zafi kan yanda take mai magana son ranta,da sauri ya bar É—akin ya faÉ—a toilet ya zuba wanka ,yazo ya É—auki wata dakekiyar shadda ya sanya, kana ya dawo ya zauna yana latsa karamar wayar shi. Tsaki ta jera sosai tana faÉ—in" aci kayan aro aita buÉ—awa. Bai ko kalleta ba yana gama abinda zayyi ya fita. Gidan Ammi yaje bayan sun gaisa take cemai ya Amnah?. Yace Alhamdulillah. Tace to ya zaman naku badai matsala ko?. Jim yayi sai kuma yace. "Alhamdulillah. Hamrat ta fito bayan sun gaisa ya tashi ya tafi gidan Nene. Anan ya yini yaci abinci ya koshi sai bayan la'asar ya koma gidan shi. Anan ya isketa tsakar gidan tasha wanka cikin wasu mahaukatan kaya tana Video a Tik tok tana ta juya jiki... Shafata yayi ya wuce ya shige É—aki. Atakaice haka suke ta rayuwa ba wata shakuwa kowa har karshi yake waya kam kullum tana hannu ta tana soyayya,Shikuma baitaÉ“a fahimta ba yana ganin da Æ™awayen ta kawai take mu'amullah ko yan uwan ta. Suna samun wata É—aya Amnah ta fara girki. Amma na dai -dai cikin ta shikam ko oho. Gashi Kuma ya samu kanshi da kasa faÉ—ama Ammi,ko tace yazo yaci zaice Alhamdulillah. Sai dai yaje gidan Nene yaci Abinci wani lokacin kuma ya siya tasha yaci, gashi kuma baya aikin komi, ga zara bata barin dami, da kaÉ—an kaÉ—an kudin shi sunfara karewa. Bayan wata É—aya. Amnah ce kwance dan yanzu ta saba da zaman gidan kuma tanajin daÉ—in zaman ,saboda tana sakewa tayi soyayyar ta da Abul khairi , Dan yanzu har Vidio call suke. agefe kuma ga kallo BF dinta sai abinda yaci gaba, Kullum da ciwon mara take kwana, danma tana kwan-kwaÉ—a maganin da Abul khairi ya bata tana rage damuwar ta sosai ta hanyar yawaita bacci. Sadeeq ne ya fita kasuwa dan samun abinda zai É—anyi dan ya samu ya rarrage , Amma haka ya karaci yawan shi ya dawo. Haka yake fita kusan kwana ukku amma sai dai ya dawo a wahalce. Shawwara ya yanke akan zai Sayar da machine É—in sa akwai shago kofar gidan shi sai ya bude ko kayan provition ne Bayan yayi shawara da Nene da Ammi suka goyamai baya. Hakan ya sashi fara neman takardun machine É—insa amma duk inda ya duba bai gani ba , Hakan yasa ya rikice har yazo cikin bedsite . Anan yaga kwalabe kayan shaye- shaye sun kai hamsin. Ido ya zaro jikin shi ya É—auki rawa , wake shan wayan nan abun, Innalillahi wa inna ilaihi Raji'un yace lokacin da ya kalli Amnah yaga yanda tayi muguwar rama,Dama ya lura kullum bacci take, dan ko abinci batacika ciba. Kanshi ya dafe tare da faÉ—in duk tsananin kiyayya ce yasaki jefa kanki cikin wannan mummuna halin ,yah Allah ka kawoman mafita ya fada yana kwashe kwalaben tass ya fita dasu yasa a machine, kana ya dawo dakyale ya gansu yaje yakai kasuwa suka bashi kudin shi ya shiga kasuwa yayo sayayya abinda zai buÆ™ata, Anan yazo ya shirya shagon shi. Agajiye cikin yunwa ya shiga gidan ya iske Amnah ta tashi sai layi take. Da sauri ta faÉ—a jikincshi cikin tsananin maye ta fara mai magana tana fadin ina sonka Abul khairi, kasoni kaima kaji, inajin yunwa ka bani Abinci,l Abul, ta faÉ—a tana fadawa jikinshi tare da tura yatsunta cikin rigashi tafara shafa kwantaccen galgasar dake saman kirjin sa. Innalillahi wa inna ilaihi Raji'un yace yana faÉ—in" Amnah kidaina ,Amnah dalili na kika faÉ—a wannan yanayin ,insha Allah zansamamiki farin ciki,zan haÉ—aki da wanda kike so nan da watanni ukku. Fuskar ta ta É—ago tana zuba mai ido tace da gaske? Ta faÉ—a tana kokarin sanya bakin ta cikin nashi. Kanshi ya juya gefe tare da janta bisa gado ya kwantar da ita ,yazo mikewa ta jawo shi jikin ta da masifar Æ™arfi, tare da hayewa saman ruwan cikin shi ya zamana suna fuskanta juna. Tace zan'hora ka fa sosai,ashe ba abul bane kaine,to zan hayeka sai gobe zan É—agaka ,kamin nan ka mace in huta,ta faÉ—a cikin gushewar hankali .. Baison sadda kwallah tausayinta suka zubomai ba, baitaba tinanin jin tausayin Amnah ba sai a Wannan lokacin. Cikin murmushi yace na yarda indai zaki hakura Amnah, hakan zai saki huce ko? Kai ta É—agamai tana sakeyin luff bisa jikin shi take bacci ya kara dauketa. Sai da ya tabbatar tayi bacci kana ya murgina da ita gefe yactashi ya fito kiching dinta akaro na farko da yasanya kafarshi da niyyar yin girki . Fridge din ta guda da aka loda nama aciki wanda ya cika da kankara da gani bakomi take dafawa ba,kwalin indomie dake gefe ya kalla shine yaga taci daya da rabi tabbacin shine kawai abinda take ci. Kai ya gilgiza dan shi yanzu tausayima take bashi. Kaza guda ya É—akko a fridge da kyal ya É“allo To ya yayyankata ya wanke tare da sanya albasa mai yawa ya jajjaga tafarnuwa da citta ya zuba curry ya kunna gas ya É—ora. Sabuwar tukunya ya É—akko ya wanke ya tarba ruwa. Bayan suncika ya dora a gudan gas É—in. Lokaci guda kamshi ya fara kewaye gidan kota ina. Kayan miya ya fita ya siyo dan basu da su. Bayan ya dawo ya gyra ya wanke yayi greating É—in su shape- shape ya markade su ya ajiye gefe. Mai ya zuba ya soya kaji sosai kana ya juye markaÉ—an a'ciki, miyar ya hada saida ta kusa soyuwa ya zuba naman duka a'ciki, kana ya tsane shinkafar da ya dafa. Amnah kuwa cikin Bacci ta farajin wata masifatacciyar yunwa,ga wani kamshi wanda yasata jin wata irin murÉ—awa tare da hautsinawa ciki, da sauri ta mike ta fito daga ita sai kananun kayan dake jikinta na bacci, wandon kamar pant sai Vest din da bata ida kai cikin taba ammata gidan Bra ,kayan Dark blue ne sun haska farar fatar ta, fitowa tayi tana miÆ™a! karaf idonta ya sauka akan shi yana zaune cikin kiching. Kallon shi tayi sosai ganin yanda yayi wani irin fari tass ta kalli kanta ta madubin window taga duk tayi baki ta rame. Kallonta yayi yace kintashi lafiya? Samun kanta tayi da É—agamai kai hakanan taji ya burgeta ya kuma bata tausayi,gashi zaune yana girki ita tana bacci.. Wanka ta shiga ta fito da towel ta giftashi ta wuce. Yana gama abinci ya zubo mata ga flat, ya É—auko pure water yaje har daki yace Amnah taso kici abinci ina so muyi magana. Sosai kamshin girkin ke rikita Yawun ta.. Karba tayi ta faraci shima ya zubo nashi yaci. Yana gamawa ya fada wanka ,bayan yayi ya dawo ya zauna tare da sanya wani ash din wando da Black din singlet data haska farar fatar shi. Kallon ta yayi sosai tare da cewa" ke Amanar mahaifiyar kice a'hannuna, miyasa kika zaÉ“i rayuwa shaye -shaye? bakison zai miki illah ba? zai illata lafiyanki? kinga yanda gabaki daya kikayi baÆ™i kikayi rama ?sai uban hanci, miyasaki haka?. Tace "wallahi auranka ne kawai banaso ,Fatana ka sawakemun in'koma ga Abul khairi. Yace shikenan na Amince miki , Amnah, zan kuma sawwaÆ™e miki, amma alfarma É—aya nike nema daga gareki anan shine kisaki jiki dani saboda zamanki cikin kaÉ—aici kansaki jefa kanki halaka ,kana kidaina shan duk wani abunda baidace ba, nikuma namiki alkawari nan da wata ukku zan baki takaddar ki, Amma wallahi kika sanya rashin kunya cikin lamarin sai dai ki dawwama a haka . Kai ta jinjina cikin gamsuwa tare da fadin na Amince ni kuma. Yace yawwa ngd da fahimta. Kai ta gilgizamai batare da tace komi ba. Washe gari da safe yana dawowa asuba ya farajin motsi a kiching. Shiga yayi ya iske Amnah tsaye tana dafa indomie sai kamshi ke tashi. Har yasa kai zai juya yaji tace" ina kwana. Cikin mamaki ya kalleta yace lafiya !kina lafiya ! . Tace um'' tare da maida hankali ga girkin . shape- shape ta gama ta sanya tata taci ta ajiye sauran a kula. Bayan yayi wanka ya shirya zai fita tace ga abinci nan a kula. Yace to nagode ya É—auka yaci kana ya fita ya buÉ—e shagon shi. Alhamdulillah ya kau samu azziki dan cikin Lokaci kowa sai yace ya tafi shagon É—an fulani sayayya dan ya saki kayan cikin farashi mai sauki. Karfe biyu ya shigo cikin fara'a yace Amnah mikikeso asiyo miki? . A mamakin shi tace lafiya kake ta doka murmushi ,ko kasamu wani aikin DAKO'n ne. Yace aa nadai buÉ—e shago ne kuma Allah ya sama abun Albarka Tace ohk" tattasai kawai nike so akwai komi. A nan ya fita ya siyo Ya kawomata. Babu laifi cikin sati daya suka samu shakuwa dan tana mai magana mai daÉ—i duk da basa wani fira Amma babu zagi babu cin mutunci,kuma zata mai girki yaci . Su Mamy kuwa fushi take dasu sosai ko son tinowa dasu bata yi. Ranar wata juma'a da yamma kwance take tana latsa wayar ta. Ahankali take jin yanayinta na sauyawa ga marata nata mata ciwo kadan -kaÉ—an sai juyi take ,ta rasa ya zatayi, dan kallon sabbin Vidio tayi wayan da suka Hautsina mata tinani . Da sallama ya shigo cikin gidan yana sanye da farar shadda, anan ya shiga É—akinta yace Amnah Hamrat tace zatazo ta gaisheki bari inje in É—akko ta. Shiru tayi duk da taso yimai magana amma ta kasa , Dan wata kafurar sha'awa takeji wadda ta sata jin kullewar mara sosai. ÆŠakin ya shiga yana daga labule yace wai bacci kike ashe. Har zai juya yaji dogon nishin ta. Da sauri ya juyo tare da isa wajenta ya kamo hannuwata yace . "Ke minene , Amnah minene? . Tace ashhh da karfintsiya tare da damke cikin ta. Arikice yace cikin ki ke miki ciwo? Kai ta É—agamai tana kara matsewa da haÉ—e cinyoyin ta waje É—aya. Yace kinci wani abune? Tace A'a, wayyo Allah nah ta saki wani wahalallan kuka. Kanshi ya dafe cikin tashin hankali da tausayi yace" sannu yanzu bari inje insamo Napep muje asibiti a dubaki. Kam ta rike shi tana yarfe hannu, tare da kama hannuwan shi ta Aza bisa marata tana kuka. Cikin kuka tace karka tafi, inka fita mutuwa zanyi, Dan Allah ka danna mun Sadeeq. Yace taya kina amana wajena zanganki cikin ciwon bazan nema miki magani ba? ya fada arikice. Itama a rikicen t asake damke hannushi tare da mikewa azabure tawani turashi akan gado tare da hayewa bisa jikin shi ta fara murzashi da masifar Æ™arfi take murza kirjinta akan nashi tana sakin wani dogon nishi da ya kasa fahimta na miye saima ruÉ—ani daya shiga. Murzashi take sosai jikinta na rawa tana fidda sauti Washhhhh, ahhh, yesssaa ,Ahhhahhhhh sai wata zufa take haÉ—awa. Cikin wani yanayi da ta jefashi ya turata Æ™asa tare da hayewa saman ruwan cikin ta ya É—aga rigar ya fara danna fararan yatsu shi bisa cikinta yana lumshe ido A'hankali. Jin ya kusa zuwa wajen marata yasa da karfi ta É—aura hannuwanta akan nashi ta nautsa wajen tana fadin "Dee nan ne, Innalillahi ciwo cikina zan mutu wallahi marana zai fita, Tsinkemun zayyi, wayyo Dee ka danna mun ta fada tana juya kai. Ga baki É—ayan jikin shi rawa yake dan duk maganar da take cikin kunna shi take,sai huramai Hucin numfashinta take. 5/18/22, 09:34 - MY MTN 2: *Littafin🌹DAN DAKO🌹 na kudi ne biya ki karanta cikin Aminci. Biya 300kacal to 0006454115 Amina Dahiru jaiz bank,or MTN card to this number 09165832002. then send the evidence of payment via 07038423451* ðŸ¤ðŸ™ðŸ¤² 2ï¸âƒ£9ï¸âƒ£&3ï¸âƒ£0ï¸âƒ£ Washh Amnah dan Allah ki daina, karkisani cikin wani yanayi na gushewar Hankali,inaso in aura dake da cikar kamalaki ko dan daraja mamanki, ki daina Amnah ahhh ya saki wani nishi mai masifar zafi. Ita kam hankalin ta ya fara gushewa. Hannuwanta kawai take tausawa a'cikin sumar kanshi tana faÉ—in Danna'min sosai Dee, ka danna ka cakamin yatsunka, ka zura ciki sosai fa ahhh Dee.... Sake matseta yayi jikinshi sosai yana huramata iskan bakin shi, ga wani Azababban zafi da jikinta ya É—auka, tabbacin zazzaÉ“i ya fara saukar mata. A'hankali ta fara rarumo babbar yatsar shi ta tausa Abakinta tare da fara mai wani tsotsa kamar ta sabon jaririn da ya samu mama, shan Yatsan take sosai tana jujjuyashi tare da sauke numfashi mai zafi.. Shikuwa galala haka yake kallonta idanuwan shi sunyi wani irin ja har kwallah suke fitar wa. Ba tare da ya janye hannushi daga nata ba yace "Amnah tashi muje in kaiki Asibiti,baki da lafiya sosai. KafaÉ—a ta maÆ™ale tabbacin bata zuwa. Ganin haka yasa ya zame daga jikinta da sauri. Wani marayan kuka ta saki tana kifiwa ga kyarma da jikin ta ya É—auka . Kallon jikin shi yayi lokaci guda ya rintse ido. Dan abinda bai taÉ“a faruwa dashi bane ya gani a kanshi,Dan kuwa Dee É—insace tayi sambal sai dukan iska take, kai ka rantse baisa komi jikinsa ba. Wani irin faÉ—uwa gaban shi yayi danshi zai iya rantsuwa da hankalin sa ko mafalki bai taÉ“a yi da wata mace ba wadda zai kaishi ga haka ,to wai dama haka yake ne,yanzu taya zai fita haka, towai mike damunta take mai wannan abun dake neman sashi cikin yanayi. Wanka ya faÉ—a ya fito ya canza kaya tare da saurin fita ya tsaido Napep ya dawo gida, ya canzamata kaya tare da samata hijjob cak ya É—akkota a kafaÉ—a ya kulle gidan . Napep suka fada ya faÉ—amai Asibiti da zai kaisu. Kai tsaye Emagency suka nufa . Agaggauce aka Æ™arÉ“eta bayan sun shiga sukace yaje ya yanko kati. Da sauri yayi komi ya gama ya dawo ya zauna yafara zancen zuci. Anyaa Amnah ba wani Abu taci ya É“atamata ciki ,Kai anya,shifa kar yar mutane ta mace a hannusa ta jamai masifa,tsaki ya saki yana faÉ—in illar auran dole kenan, da wanda take so akaba ta bazatai haka ba, kilama ulcer ce takama ta,haka yayyata zancen zuci yana kaiwa yana komowa. Wani likitane ya fito yana sharce zufa yace "muje office ko Abokina. Kai Sadeeq ya É—agamai daganan yabi bayan sa. Suna shiga Doctor ya zare safar hannu shi tare da wanke hannuwan sa, kana ya zauna , Ya fuskanci Sadeeq. Yace am nace ya kuke da marar lafiya ne? Sadeeq yace Ƙanwata ce. Kai ya jinjina cikin gamsuwa yace "to gaskiya magana Yallabai kason kowa da yanda Allah ke halitar bawan sa ko? Sadeeq daya matsu yaji miye yace "Dan Allah na sani kamun dalla -dallah mana. Yace ohk'' to gaskiya Æ™anwar ka na cikin layin mata masu tsananin sha'awa, saboda haka yana da kyau ku gaggauta aurar da ita tinkamin spam din da ya taru mata a mara ya mata illah , Saboda ko yanzu shine ke sata wannan fitinanna ciwon cikin, Amma yanzu ga magunguna zaka siyamata,kana zata kwana da safe sai ku wuce... Shuru yayi yana nazari. Likitan yace" Ya dai Abokina?. Yake ya saki yace" am bakomi nagode, ya tashi ya fita ya biya kudin kaf na hannushi saida suka Æ™are. ÆŠakin da aka kaita ya dawo ya zauna ya tasata gaba yana kallo. Saima yanzu yabm fahimci dalilin aurar da ita da akai kenan. dana jarababba ce shiyasa aka bashi ke nan,aiko sun cuceni,ya zasu haÉ—ani da Harija mace,in tamun fyade fa,gaskiya magana bazan iyaba ,dan ni mai saukine ,bana iya wannan jarabar. Sai Æ™arfe biyu na dare ta falka ta gan shi zaune ya zubamata ido sai kallo yake ,yana zancen zuciya. Ganin ta motsa ya sashi janye idon shi yace" ya jikin, Dan shi tsoron tama yaji yanaji kar tamai fyade Tsakiyar dare... Da sauki ta bashi amsa tana karema ÆŠakin kallo, tare da tino abinda ya faru, Murmushi kawai ta saki tana lumshe ido. hawaye suka biyo mata da fuska, da kyal tace mike damuna? Kame- kame ya fara tace" ya isa Sadeeq. Na tabbata kason abinda ke damuna. Kason dai bazan iya zama da kaiba ko? Dan Allah ayau din nan ka sawwakemun in kama gabana, in auri mai sona, jarumin maza dai-dai dani... Duk da kalamanta sunyi mai tsauri hakan yasa ya tashi ya fita baki É—aya daga É—akin, ya koma waje har akai Asuba, bayan yayi sallah kana ya dawo ya iske tana bacci. Zama yayi akan kujera bacci na fuzgar shi. Gefen gadon ya samu ya kwanta da kan shi, take bacci yayi awon gaba dashi. Sai takwas ya falka azabure ya ganta zaune ana ciremata ruwan da aka É—oramata sai kallon shi take ido lumshe. Da sauri ya janye idon shi yana mai faÉ—in bari in Æ™arbo Miki takadda mu wuce. Batace komi ba shima baisa ran amsawar ta ba. Koda ya kammala komi haka ya É—akko mata takalma ya kamo hannuta suka fito. Zaunar da ita yayi ya taro musu napep ya sata yashiga kana suka É—auki hanya.. Suna isa unguwar suka karya kwanar layinsu anan sukaga Dandazon mutane anata salati . Da sauri ya suka yana kutsawa cikin mutane, dan yaga kamar kofry gidan sane. Innalillahi wa inna ilaihi Raji'un yace lokacin da yaga yanda shagon shi yayi Æ™urmis babu komi a ciki. Wasu suka fara faÉ—in yawwa ga D'an Fulani nan gobara muma mukaga shagon nayi, da yake sun maido wuta mai karfi to kuma muna kiran ka dan kuma fito ashe bakwa nan. Baice komi ba sai shagon da yabi da kallo yanda komi ya zama toka ga ruwa an'samai. Anan yace da yan unguwar ya gode da suka Taimaka baikai gidan sa ba, iyalin sa yaje kaiwa Asibiti.. Tausayi sosai ya basu sukamai jaje suka watse.. Dawowa yayi cikin napep É—in yace ma Amnah fito." Tace lafiya wai? Yace shagona ne ya Æ™one, komi babu, ni ban mason ya zamuyi da mai napep É—in nan ba. Mai napep najin haka yace haba É—an uwa aikai yanzu abin tausayine, Allah ya tsare gaba ya mai da maka Alkhairi. Yace ameen ya masa godiya suka fito.. Sosai take Æ™arema shagon kallo ynda komi ya cinye , kyauran kanshi yayi wuluk. Gidan ya buÉ—e suka shiga ,anan ta faÉ—a É—akinta ta kwanta ,shima shiga yayi ya zaun ya buga tagumi. Kallon shi tayi a karo na farko da taji ya bata tausayi tace. to miyakawo haka? Anan yake faÉ—amata yanda sukace. Shiru tayi tare da juyawa ta É—auki wayarta ta fara chart. Har azahar bai rintsaba baikuma tashi ba. Tace kai nifa yunwa nikeji . Yace bari a dafamiki indomie. Tace bazanciba zafi ya tasoman ,kayi cefane ka hado da nama tinda namu ya kare... Kallonta yayi sosai baiga wani alamun jajantawa a tattare da itaba. Yace yanzu Annabin bakya tausayamun, bakya ganin bani da ko naira biyar ,wane cefane zan miki,Dami zanji da ÆŠawai niyar ki kota Mahaifiyata da Æ™anwa na da suka dogara da Allah suka dogara dani. Shuru tayi tana ganin bata kyauta ba, jibi jiya Yanda duk.ya rikice da yaganta cikin hali, ga kudin shi tasan sun Æ™are Asibiti... Cikin sanyi murya tace kayi Hakuri Sadeeq Allah zai baka wani. Yace nagode . Tashi tayi ta shiga kiching anan taga suna da kayan abinci Amma babu mahaÉ—i. Ta dawo tace mai ko zaka É—auki shinkafa ka sayar ka saimana kayan buÆ™ata?. Yace kar in'kwashe miki abinci fa. Tace babu komi ai amfani kainane. Ya tashi ya É—auka ya siyar ya dawo ya bata kudin. Kilgawa tayi ta bashi na abinda zai siyomasu ta koma ta kwanta.. Bayan ya siyo da kanshi yashiga ya musu girki ya dawo ya kawomata. Bayan Wata Biyu. Wata irin wahalla Rayuwa sadeeq ya shiga, dan komi nasu ya kare, babu abinda suke da shi. Sai ya fita ya wuni ya dawo baisamo ba,Ga bashi da isashiya lafiya.. Rayuwa ta juyama Amnah baya sosai hakan yasa duk ta fara fita hayyacinta ta fara laushi. Saboda babu mayuka masu kyau, babu cima mai kyau, babu -babu... Ajigace ya shigo gidan yana tangaÉ—i tare da rike saitin zuciyar shi. Amnah dake zaune tsakar gida yunwa na bugunta basu da komi sai rabin buhun shinkafa, babu gas ,babu magi ,ba komi ,da kyal take chart din da take. Ganin shi a haka ya sata mikewa da sauri ta isa gareshi tare da cewa. kai miye haka, lafiya, mi kasha? Kasa magana yayi sai wuri da ya samu ya zauna yana sauke numfashi. Yace Amnah mi kikaci?. Yakare magana a wahalce. Tace banci komi ba kai kuma mike damunka. Yace Æ™asan zuciyana ke ciwo , Dan Allah kiyi hakuri bansamu komi ba, wallahi yanzu haka su Ammi ma basu da komi gidan su. Kai ta jinjina mai tare da cewa karka damu ,yanzu ya zamuyi kenan, ga suma su Ammi suna jin yunwa. Yace Annabin wallahi tinda na fita bansamu ba . Tace shikenan tare da tashi ta shiga É—akinta ta fara binciken kudin da aybbah ya bata Na Sadakinta . Da kyal ta gansu bayan tasha wahala,bata son sadda ta fara kwallah ba. wai yau itace keda 5k take murna, innalillahi wa inna ilaihi Raji'un, talauci masifane, talauci bala'ine. Fitowa tayi da niyyar ta bashi ta ganshi kwance babu ko Lumfashi ajikin sa ,hannu shi kuma bisa saitin zuciyar sa. Da sauri tayi kan sa tace. Sadeeq! kai ÆŠAN DAKO!! Dee!!! tashi mana, miye haka ,karkamun wasa mana ,baka gani dagani sai kaine ,ko yunwa kakeji ,tashi ga kudi ka samo muna abinda zamuci Dan Allah ka tashi. yaÆ™i wani motsi da zai tabbata mata da yana da rai . Rawa jikinta ya É—auka cikin tashin hankali . Hannushi ta ture tare da ÆŠaga rigar shi da kyal. Anan taga wani babban tambari wanda bata da tantama na halbin bindiga ne,wanda yayi wani irin malolo har wani tsulbi fatar wajen keyi. kuma ya kumbura.. Ido ta zaro da karfin tsiya dan tana da tabbacin bindiga ce ,to waya wannan mutumin ,kuma waye ya halbeshi ,wani irin tsoro da tashin hankali suka kawomata xyuyara. Da gudu ta shiga kiching ta É—ebo ruwa ta yayyafa mishi amma shuru. Kuka tasa tana mai kifa kanta a kanshi tace. Dan Allah ka tashi sadeeq ,ka tausayaman kar tashin hankali duniya ya karni ,bani da kowa a,wannan duniyar dake cike da kalubale sai kai, ka tashi sadeeq dan Allah, kar ace ni na kashe ka, ka tashi namaka alkawarin daina duk abinda nike, bazam sake ba wallahi ,bazan sake maka ba, wayama bazan sakeyi da kowa ba, ka tashi dan Allah . Ganin bai ko motsa ba hakan yasa ta kara buÉ—e rigar sa ta sanya hannuta ta danna ramin da É—an karfi. Wata irin zabura yayi da Æ™arfi batare da ya bude ido ba. Yayin da ita kuma taji wani É“ull kamar kwanciyar ruwa cikin abin. Ganin ya motsa yasa da sauri ta Æ™arasa wajen bakin shi bata saya komi ba ta dinga huramai iskan bakinta da masifar Æ™arfi. Wata irin ajiyar ziciya ya sauke yana bude idon shi kadan da suka Æ™anÆ™ance sukayi ja.. Tace sannu Sadeeq! kanaji ba, ko in fita in É—an samo maka maganin da zai ragemaka raÉ—aÉ—in ciwon. Ido kawai yake binta dashi yanajin wani irin radadi a ciwon sa. Da sauri ta mike ta shiga É—akinta hijjob inta ta sallah ta É—akko tasa. A karo na biyu kenan ta fita tinda tazo gidan. Tana fitowa taga Wata budurwa da ta É—akko icce zata shiga gidan dake kusa da nasu. Da kallo ta bita kamar zatai magana kuma ta kyaleta ta tare Napep tamai kwatancem sulhu pharmacy. Yana kaita tace ya jirata. Bayan ta shiga ta faÉ—i mishi abinda takeso bayan sun bata suk mta list É—in 4100 . Sosai taji gabancta ya faÉ—i dan ya kama saura 900 kenan ,ga mai Napep. Haka ta karba ta fito. Bayan ta fito ta shiga ya maidota ya Æ™arbi 300 . 600 din hannuta tabi da kallo wasu hawaye masu zafi suka zubomata. Ya kamata ace kamin yasha magani ta bashi wani abu yaci, dan tin jiya baici komi ba. Da kafa ta Æ™arasa wata rumfa mai shayi dake kusa da gidan da take Ta mika duk Æ™udin tace abata madara da sugar da bread sai a bata ruwan Lipton tinda bata da gas babu kuma wuta. Mai shagon yace haba Hajiya wai duk cikin dari 600, toko madara yanzu 300 ,kinga kudin bazai isaba ko. Shuru tayi tana kallon yanda ya balbaka wuta da itatuwa yanda suke ci sosai a Murhu. Yace Hajiya ina magana fa. Tace ka bani na É—ari ukku ka bani ciko, amma kamun hadin shan mutum É—aya dan yayi kauri sosai. Yace angama aiki nane. Bayan ya bata tace dan Allah ina ake saida wannan iccen, kana yazan kunna shi yaci sosai. Shekeke yake kallonta irin kallon kinma raina mutane. Afusace yac order sa nayo daga chaina. in'kinaso kawo ayo miki... Murmushi kawai ta saki dan yanzu ita ta riga ta dawo rakiya rayuwa, som babu tabbas ga rayuwa, wai yau itace ke zullimin fidda kudi. Tace kayi hakuri Malam. ta faÉ—a tana juyawa da Sauri ta shiga gidan ta rufe.... 5/18/22, 09:34 - MY MTN 2: *Littafin🌹DAN DAKO🌹 na kudi ne biya ki karanta cikin Aminci. Biya 300kacal to 0006454115 Amina Dahiru jaiz bank,or MTN card to this number 09165832002. then send the evidence of payment via 07038423451* ðŸ¤ðŸ™ðŸ¤² 🅿ï¸3ï¸âƒ£1ï¸âƒ£&3ï¸âƒ£2ï¸âƒ£ ""Da Sallama tasa Æ™afar ta tare da saurin Æ™arasawa inda yake . Anan ta ganshi yanda yake, Amma ko numfashin kirki bayayi, idon shi kuma duk sun juye sunyi jawur. Gilgizashi tayi sosai tare da cewa . Sadeeq! ka tashi ka sha Tea in'baka magani , Dan Allah. Shuru yayi dan yana son yayi magana amma yakasa, yanajin ciwon dake damun shi kamar zayyi sanadin tafiyar sa lahira ,ya kuma hana shi cika Burin shi .. Hijjob in jikinta ta cire ta É—akko cup kiching tare da Æ™arasowa wajen shi tasa hannu da kyal ta É—ago kanshi ta É—ora a cinyar ta. Saida ta tabbatar ta dai& dai yanda zaisha batare da matsala ba kana ta É—agoshi dakyal tana numfashi ta kafamai cup É—in bakin shi. Kanshi ya gilgizamata alamar bazaisha ba. Tace'' Dan Allah karkamun haka mana, kasha zanbaka magani, zaka ji sauki insha Allah, ta Æ™ara kafamai kasancewar yanajin yunwa yasa ya É—an sha kadan ya kauda kai tare da Æ™oÆ™arin tashi Amma ya kasa. Wayar ta dake gefe ta shiga ring. Da sauri ta duba ganin Abul khairi ne yasata jan tsaki. Haka nan ta samu kanta da datse kiran. Kusan so biyar yana kiranta tana kashewa, Tare da sanya wayar airplane mode... Kallon ta yake sosai yana mamakin abinda ya hanata É—auka . Ido ta É—ago karaf ya faÉ—a cikin nashi. Kallo- kallo suke ma juna kowanne da abinda yake tinani . Ita tana tinanin waya halbeshi har wajen yamai wannan mummun illah. Yayin da shikum yake tinanin wai yau Amnah ce ta fara sanyi haka ,har take É—ora talakka bisa kafarta lallai Duniya juyin Æ™osai. Idonta ta janye tare da mikomai magani da ruwan pampon data Tara dan yanzu sune ruwan shan su. Bakin shi ya buÉ—e ta bashi tare da kwantar da kanshi bisa hijjob inta ta tashi tana miÆ™ar gajiya, dan Sadeeq in'garman namiji ne. Drip din da ta siyo ta sargafa ga wata Æ™aramar igiyar da yake musu wanki ta É—ora akai , Tare da duÆ™awa ta kama hannu shi ta sanya wata siririyar roba ta É—ora mishi , tare da É—an dukan saman hannu kadan-kadan . Tana gani ta samu jijiyar da take buÆ™ata ta zaro Allura tare da kallon shi. Idon shi fess akanta yana kallon yanda take Abu cike da sanin makamar aiki. In maka mai zafi ta faÉ—a fuska a É—aure.. Kai ya ji jinamata yana lumshe ido dan zaton shi da gaske mai zafin zatamai.. Bakinta takai saitin jijiyar hannu ta kafa tana É—an zuko wurin KaÉ—an -kaÉ—an tana danna mishi yawun bakin ta. Ido ya lumshe tare dajin tsigar jikin shi na tashi. Sai da takai 5mnt kana tasa Tissue ta goge anan jijiyoyin sukai raÉ—a -raÉ—a. Allura ta É—akko tare da lumshe idonta tana cije baki ta soka masa kaÉ—an- kaÉ—an har ta shige baki É—aya ,kana ta sauke ajiyar zuciya. Kallon ta yayi yana mamakin miyasata wannan lallamin bayan yayi tinanin da mugunta zata mishi. Tana gamawa tace" sannu zaka iya magana. Kai ya ÆŠagamata. Tace to kace wani abu mana . ta faÉ—a cikin shagwabar da batason ta iyaba. Murmushi yayi yana juya kanshi gefe dan shima yana fatan ace ya samu bakin magana ko godiya ya mata saboda Sosai yakejin raÉ—aÉ—in na Æ™asa.. Tea'n dake gefen shi ya nuna mata alamun tasha. Tace aa zaka buÆ™ata dan akwai Allura dana maka cikin ruwa zakaji yunwa sosai , kuma babu komi gidan. Wayar shi ya É—auka ya fara rubutu kamar haka. "Dan Allah kisha mana ambah ,Hakkin ci dake yana kaina, amma bana iya fita samo miki wani abu,kisha ba damuwa ni bazanji yunwa ba insha Allah. Ya mikamata wayar. Tana gama karantawa batason sadda wani irin tausayin shi ya dirar mata azuciya ba. Wato bayaso Amnah yana son ya tsare hakkinta kenan, lallai yason daraja aure. Astagfirullahu lathi la ilaha illahuwal hayyu qayyum wa atubu ilaik ta fara jerowa cikin zuciyar ta ,tare da dana sanin ruÉ—un da shaidan yamata,duk da bataso bai kamata tayi wasa da igiyoyin auran sa dake kanta ba. Tace bari in dafa Abinci. Wayar ya karba yasake rubuta. " Babu Wani mahaÉ—i ga abincin ki barshi.. Tace karka damu bari in É—an fita Æ™aÉ—an. Kanma yayi magana ta ficce tare da shiga gidan dake kusa da nasu, inda taga yarin yar nan ta shiga. Sallama tayi tare dayin tsaye tana Æ™arema gidan kallo komi tsaf ga girki suna tayi da icce. Sallama ta sakeyi aykaro na biyu. Wata matashiyar mata ta fitito da shekarunta sunkai 30 ta girmema Amnah. Da fara'a ta ce sannu da zuwa baÆ™uwa mukayi shigo mana. Amnah ta É—an shiga Æ™aÉ—an tare da cewa "ina wuni. Tace lafiya lau sai dai ban waye kiba?. Shuru tayi tama rasa mizatace. Wannan budurwa da zatakai shekara 15 ta fito tare da cewa" laaa Mama wannan ai Amaryar ÆŠan Fulani mai shago ce , nima É—azu naga ta fito gidan.. Cikin fara'a doysai matar tace "kai Dan Allah Fatimah, aiko bata taÉ“a shigowa ba muma bamujeba, sannu da zuwa Amaryar. ta nunamata kujera tace zauna.". Amnah tace "ba zama zanba , Dan Allah yanda zan kunna wuta nikeso ingani zanyi girki ne. Tsororo matar ke kallonta tace" iccen ne baki iyaba ko-ko ? Ba nan garin kike bane.. Amnah tace "eh gas É—ina ne ya Æ™are, to yanda zataci kamar naki nike so.. Matar tace tofa ikon Allah, inkana da rai kasha kallo, to ga Fatima nan ta biki ta haÉ—amiki ko.. Amnah tace" aiko nagode, amma banda wannan. ta nuna murhu. Mamaki ya Æ™ara kashe matar tace" to ina zuwa. ÆŠaki ta shiga sai gata da sabon Murhu ta bata tace gashi, Sabone bai siyo , nawa sun farayin Æ™asa .. Amnah tace ngd zan maido in nagama. Da suri tace "aa haba Dan kama makwafcin ka abu babu komi Wallahi. Fita sukai fatima na biye da ita . Suna shiga gidan ambah ta juyo da niyyar mata magana.. Anan taga ga baki É—ayan hankalin fatima naga sadeeq da yake bacci cikin rashin jin DaÉ—i. Wani irin takaici da haushi ya kama Amnah har batason sadda tace" ke ki fara abinda ya kawoki mana. Yarin ya tayi furgigit tare da cewa" ai babu icce. Amnah tace ina ake sayar wa, kuma nawa? Tace wajen baban mu, Mai sayar da shayi, naira É—ari . Amnah ta zara ta bata ta fita sai gata ta dawo tace'' Aunty gashi harma da ashana na Æ™arÉ“o. Tace to.. Nan ta fara haÉ—a mata dan -danan wuta takama. Tace Aunty Abada tukunyar da za'aÉ—ora. Amnah ta shiga kiching sai gata da tukunya mai masifar kyau nata da aka samata. Yarinya tabi tukunyar da kallo tace" aka sata zata lalace, Bari in É—ebo toka gidan mu. Amnah bata fahimci mitake nufi ba, ta dai É—agamata kai kawai tana mai rufama sadeeq wani bedsheet marar nawi a jiki.... Da sallama fatima tashigo tare da Æ™arasawa wajen pampon ta zuba tokar Æ™asa tare da zazzaga kill ta kwaba ta murje tukunyar tass ,kana ta tarba ruwa ta É—ora tana mai iza wutar Ganin tanaci sosai tace" Aunty mizaki dafa? Amnah tace "shinkafa.. Fatima tace A'a kikawo asiyo miki wake da mangyaÉ—a da tashi in'dakamiki na iya sosai, muma ita zamuyi, harma da salat. Tace zan kashe nawa?. Tace 150. Ido Amnah ta zaro ganin in'tabada saura 50 naira kenan ," Ya Allah" tace tanajin idonta na cikowa da kwallah... Tace karaÉ“a kisiyo Man Ƙulin mai yawa ,ki kashe kuÉ—in duka. Fatima ta É—agamata kai tare da ficcewa. Bata jimaba sai gashi ta dawo saura cikin Naira biyar ta ba Amnah. "Tace rike shi ,wannan yazan masa. Yarinya ta zauna ta gyara waken tsaf ta wanke ta zuba , tare da wanke salat din ta yayyanka shi tare da tumatur da albasa. Bayan ta gama ta dakama Amnah yaji mai daÉ—i, irin wanda mamanta ke dakawa. Tana ganin waken ya Nuna tace "Aunty ki zuba shinkafar fa. Amnah ta debo mai yawa ta wanke ta zuba tanajin hayakin har cikin kwalwarta, ga jikinta duk ya É—auki Æ™auri, kai innalilli tace tana sakin kuka. Da ido yarinya ta bita tare da cewa "Aunty mai akaimaki, ko hiyaki ke akwai?.. Kai kawai Amnah ta ÆŠagamata. Fataima tayi dariya tace'' niko munsaba shiyasa ba maji. Amnah batace komi ba sai gishiri da ta É—ibo ta zuba akai. Ta tashi da niyyar É—akko mataci tsanewa taga idon Sadeeq akanta alamun ya tashi kenan. Da sauri ta Æ™arasa wajen shi tace" sannu! acire ya Æ™are ko,ya saukin jikin naka? bakajin komi? yunwa kake ji ko ?ingama girki kaci? zakaci ko.? ta faÉ—a cikin rikicewa dan duk batajin daÉ—i itama. Cikin Æ™asa da murya ya fara magana . *Amina kece da hura wuta ,waya koya miki? miyasa zakiba kanki wahala, kiciremun in tashi in'fita insamo miki abinda zakici.. Kai ta gilgizamai tace'' bazaka iyaba Sadeeq, wannan wajen akwai wata matsala na tabbata,kayi addua ALLAH ya baka lafiya, amma zanso muje Asibiti kar ya zamemaka wata illah. Yace" banda komi baki da komi Asibiti kuma sai kana da kuÉ—i. Kallon wayar hannuta tayi taga aÆ™allah zatakai dubu dari da wani abu, Dan ko sadda ta sayeta kusan 200k . Tace karka damu bari in'Æ™arasa dai... Kai ya jinjina mata yanajin tausayinta har cikin ranshi, lallai duniya juyi -juyi, rayuwa babu tabbas. Bayan ta tsane abinci fatima ta kashe itatuwan tare da mayar da murhun gefe ta dora itatuwan akai, ta gyaramata wajen tace na tafi. Amnah tace zokici abinci. Kai ta gilgiza tace A'a Aunty shine mukayi na tafi. Amnah tace Dan Allah karkice haka, duk wahala da kikasha?. Fatima tayi murmushi tace wallahi bazan ciba, ta faÉ—a tana sanya ki ta fita tana mai jan Æ™ofar. Amnah ta shig kiching ta É—akko kuloli ta zub abinci mai yawa, tare da zubawa akula madaidaiciya ta aje gefe, kana ta juye sauran awata kula. ÆŠakinta ta shiga ta cire kayanta tasa a wadrob da ta cika da kayyaki babu kudin sabulun da zasu wanke. . Babban towel ta É—akko ta É—aura tare da É—ira hijjob akai, kana ta fito tashig wanka. Bayan ta fito ta zare mai ruwan , Tare da ta dashi dakyale ta jinginar dashi ga bango ,ta zubomai ruwa a buta tace kayi al'awallah, daga nan sai kayi Sallah. .Yace wanka nike buÆ™ata yi.. Ta zaro ido tace to wazai iya daukar ka, kana kato da kai.. Murmushi ya saki a hankli yace kece mana.. Harara shi tayi tace bazan iyaba ,bayan duk kajama na gaji. Yace "uhm" Tare da Æ™oÆ™arin dafa Æ™asa ya tashi amma ina ya kasa. Yace Amnah ki kamani Dan Allah . Amnah tace to" tare da zuwa ta rike hannuwan shi taja baya sosai da niyyar ta kamoshi ya mike. Wani irin jigif taji yayi kuma ko motsi bai ba. Tace wayyo Allah kashin bayana, Dee ka taso man. Cikin dauriya ya kama ya mike dakyal yana dukewa, dan baya iya mikewa tsaye sosai. Wani irin jiri ya kawomai ziyara, hakan yasa yayi baya zai faÉ—i. Aguje Amnah tayi kanshi ta rungumoshi jikinta sosai . Anan suka fara layin faduwa dan yamata nawiem Arikice take kallon shi tana kallon yanda zaisha Æ™asa, karshentama kan shi zai bugu ta fara tinani. Cikin hanzari ta wullo filo da Æ™afarya tare da durkushewa dashi har towel din jikinta na cirewa. Wash tace da karfi dan gwiwoyinta sun bugu sosai. Numfashi ya fesar tare da juya da kanshi kanta yace" Allah yasaka da Alkhairi nagode . Itakam hannu kawai take yarfewa dan gwiwar ta zafi. Baison sadda yasa hannushi ya jawota jikinshi ba suna fuskanta juna. Yace Sorry Ragguwa yarinya ,Nine ko? Pink lips dinta ta turo tace wallahi nawie kamar buhun masara ,duk kaine kasa kayi wannan nawin da kake É—aukar kaya masu nawi. Murmushi kawai ya saki yana Æ™ara lafewa cikin jikin ta. Amnah ki debomun ruwan anan sai inyi wanka na yace.. Ido ta zaro tace kai baka da kunya ne? Yace zama da kene ya kawo hakan. Tace yo ai na daina bazakayi ba, ka hakura da wankan dama ai sanyi- sanyi ake. Yace uhm yana gyara kwanciyar shi , Yana tinanin mahaifiyar shi da Æ™anwar shi ,shine kawai garkuwan su gashi kuma abubuwa na neman kwantar dashi. Akaro na biyu yayi Æ™oÆ™arin tashi Allah ya taimakamai ya mike amma baya iya tsayuwa sosai, sai ya rankwafa. Ahankali yake bin hanya har ya shiga toilet. Amnah ta bishi da kallon tausayi dan ta fahimci akwai matsala ga raunin nashi sosai , Tinda ya fara irin wannan tafiyar. Tana nan zaune ya fito dagashi sai jallabiya ya isa É—aki ya sanya kaya marasa nawie ya fito a dudduÆ™e ya zauna yayi alwallah ,yana gamawa yayi sallah daga zaune. Itama Sallah tayi bayan ta gama ta sanyo wata atamfa riga da skit sun mata masifar kyau ta fito waje ,tare da shiga kiching ta zubomai abinci takawomai da ruwan pampo ,dan basu da ko pure water ,kuma babu kudi hannu ta balle ta siya. Kai ya kaÉ—amata alamar ya koshi. Tace Dan Allah kaci. Yace ke kika fi dace wa da kici Amnah, ina lura dake baki ci komi ba, kinaso ciwo ya kamaki, ke kwance ni kwance? Kai ta gilgiza alamar aa. Yace to matso muci wannan, amma kar kisamun yaji sosai. Kai ta É—agamai tana ci tana bashi Ahankali, Duk a takure take dan dai kawai baya lafiya ,bayan sungama ta tashi ta É—akko sabon gyale cikin kayanta tace am nace kamun kwatancen gidan su Ammi sai inje in kaimusu, kaga kar suyita jin yunwa ko. Cikin mamaki yake kallonta,tinda tazo gidan bata taÉ“a mai magana maman shi ba. Da wani irin zallar farin cikin da yakasa É“oyuwa a fuskar shi yace "Amnah taya kikayi abinci dasu, ina kika samu kuÉ—in?. Tace Allah ne ya bani. ta fada tana murgudamai baki. Yace to kina da na Napep din da zakije?. Tace ga napep É—ina nan. ta nuna Æ™afar ta. Ido ya zaro yace" A'a kibari inje kawai akwai tafiya fa. Tace aa kayi kwanciyar ka, kamun kwatance zanje. Anan ya kwatantamata tace to natafi sai dare zandawo. Yace wai dagaske tafiya zakiyi ki barni ? tace'' eh sai nadawo ta ficce. Ahankali take tafiya hannuta rike da kula sai tambaya take ana nuna mata hanyoyi, har sai wajen ukku ta isa ta masifar gaji ,duk ta jigata,Æ™afar takam duk tayi fushi. . Wani yaro ta tambaya gidan su Sadeeq anan tamai kwatancen shi. Yace gyisan da ba a shiga?. Kai tsaye ta É—agamai kai. Anan ya nuna mata ta sanya kai da sallama tana nishi. Ammi dake zaune hannuta rike da alkur'an sai Hamrat dake kan cinyoyinta tana Bacci ta É—ago kai cikin mamaki tana amsa sallama ... Kallo É—aya Amnah tamata ta ta janye kanta gefe , dan hakanan ta samu kanta da jin nawin matar Da ke amsa sunan sirikata. Cikin fara'a sosai Ammi tace sannu da zuwa. Amnah tace yawwa tare da zama cen gefe kanta a Æ™asa tace" Ammi ina wuni . Ta faÉ—a cikin sanyi da kuma sakkowar zazzafan zazzaÉ“i da ya mata sallama.. Ammi ta amsa tana mata kallon rashin sani. Kular gabanta ta ajiye kusa da ita tace ga abinci nan yace A kawomiki, Hamrat bacci take?... Salati Ammi ta saki tana tafa hannu tace'' wai dama É—iyatace bansani ba , Allah sarki sannu dazuwa, tare kuke ne? Ai sai yanzu nagane danaga kamanni Mamy ki. Kai ta gilgiza alamar A'a batasake cewa komi ba. Ammi ta karemata kallo tare da zancen zuci ita bataga wata isa da gadara da akace yarinya nada ita ba. Amnah ta tashi tsaye tace" ina kiching in É—akko miki flat. Cikin jin dadi Ammi ta gwadamata. Anan ta shiga ta É—akko taga komi a tsaftace tabbacin Ammi yar gayuce kenan . Tana zuwa ta DuÆ™a ta zubama Ammi, tare da tashi ta isa wajen jerin butoci da ke jere ta wanke Æ™afarta da fuskar ta da tasha zufa ,kana ta dawo ta zauna. Ahankali ammi ta fara janta da labari tare da nunamata ta saki jiki ita bata da matsala ,kuma sirikata ai yartace.. Tace hakane Ammi. Karfe hudu nayi tayi sallah tace ma Ammi zata tafi. Tace wai tin yanzu? na dauka sai anjima zaizo ku wuce. Tace aa zanje da kaina dai. Ammi ta mata godiya sosai tare da cewa Hamrat Kasa taki tashi balle ku gaisa. Amnah tace" ba komi ai gobema zandawo. Da haka sukai sallama ta fito da sauri take tafiya. Dan hakanan taji ta kasa natsuwa da barinshi shi kaÉ—ai, Kamar bata kyautaba,Sadda yan iska suka tare ta shiya taimaka mata ,gaskiya bai can-canci haka ba. Cikin awa É—aya ta isa gidan, tana isa ta tarar da shi zaune yana nazari da tinani. Cikin mamaki yake kallonta tare da kallon kafafuwanta da duk sukayi kura ,Siket dintama duk ya lalace da Æ™asa. Har kin dawo yace. Tace eh tare da É—aukar kula guda ta mika gidan su fatima tayi godiya ta fito suna kiran ta bata tsaya ba. Kayanta ta cire tare da saurin shigewa É—akinta ta kwanta bisa gado, Dan wani masifar zazzaÉ“i da ciwon kai take ji. Ganin har mangariba bata fitoba ya sashi shiga É—akin tare da cewa. Amnah ki tashi kiyi sallah fa.. Jin tayi shuru yasa shi taÉ“a kanta. Anan yaji zafi sosai ga jikinta ma ko ina zafi. Cikin tausayawa yason aikin wahala da tasha ne yau ya saukar mata da zazzabi, Halan ya sashi fara lalubar aljihunan sa babu komi, balle ya siyo mata magani. Dakyal yasamu ta tashi sukai sallah mangariba da isha, babu wanda ya kara cin komi ta koma bisa gado ta kwanta ta fara Æari. Ganin yanda takene yasa shi tashi ya koma bisa gadon, tare da zare rigar jikinshi Ahankali ya haura gadon ya jawota cikin faffaÉ—an kirjinshi. Wasu irin ajiyar zuciya suka dinga saukewa a jajjere. Lokaci guda bacci mai masifar daÉ—i yayi gaba dasu wanda sun daÉ—e basuyi irin saba. Washe gari ma haka ta tashi jikinta babu daÉ—i amma ta daure ta É—imama musi abincin daya kwana ta koma gefe tana kuka , Dan data kai loma É—aya da kyal take hadiyewa, dan baya mata daÉ—i, duk da babu Abinda yayi ,hasalima cikon fridge yasa musu shi... Cikin tausayi yace Annabin kiyi hakuri kinji, yau ina lissafi sati uklu ya ragemaki zama dani, zan barki kije ki auri zaÉ“in ranki , Dan Allah kiyi hakuri kinji. Ko kina buÆ™atar tafiya yanzu?. ya faÉ—a yana zubamata idon sa..... 5/18/22, 09:34 - MY MTN 2: *Littafin🌹DAN DAKO🌹 na kudi ne biya ki karanta cikin Aminci. Biya 300kacal to 0006454115 Amina Dahiru jaiz bank,or MTN card to this number 09165832002. then send the evidence of payment via 07038423451* ðŸ¤ðŸ™ðŸ¤² Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Yan uwana mata ina kuke ku malmatso ga wanni sirri da nike son baku, ita ya mace sai da kamshi, ina macen da take ganin izgili da wulakanci da ake cewa maza nada shi, hmmm yar uwa to inkin kasance a haka da alama akwai ayar tambaya akanki. Tambaya ta ta farko gareki da wane irin turare kike amfani a jikin ki ?,da wane irin turare kike turara gidan ki,shin dawane irin turare kike Zukunni, hmmm to matso kusa kiji yar uwata. Shi kamshi Annabi muma ya faÉ—a abin sone,kuma Abune mai sanya natsuwa da girmama ma'aboci shi , Da Yawon son kusantar sa. Duk kan wulakanci da izgilanci na maza akwai turaran da zai miki maganin sa da izinin Allah,ba boka ba malam,wanda zai karkato da hankalin mijinki akan ki ku samu fahimtar juna. Ko kin son kamshi na dakusar da fitinar É—a namiji yar uwa? kigarzayo ki kwashi rabonki ga shaharariyar yar mai Dugurin nan mai suna UMSAD INCENSE ,Mace mai kishin mata da son Fiddo martaba mu. Nayi Amfani da turaranta naji masifar daÉ—in da yasa nakasa barwa raina. Nace bari in yaÉ—amuku dan kowa ya mallaki nashi cikin farashi mai sauki. Da fari bari in zayyano muku su kamar haka.👇 Maleek Al'oud Royal kush Cous-cous Kajiji Original sandal Sandal flex Sandal bange VIP mix Hawi Al'oud Kindikay Danal banat Darot Habil Gaf-Gaf Sirrun nisaa'i Sandal chips Kwalacca Humra black and body milk Attractive humra. Yar uwa zanmiki Dallah- Dallah. Akwai turaran da zaki sanyama kayanki . Misali! kisa kabasa kiturare kayanki . Akwai humra da bazaki sataba sai zaki turaka. Akwai turaran kaya ,na jiki, Dakuma na É—aki. Akwai kwallaca sirri, amma bama badata gaskiya sai ga wanda baida kishiya , Dan muddum kina amfani da ita tofa gabaki dayan hankalin mijinki akanki zai dawo,Dan yana juyo da hankalin namiji akanki baki É—aya ,zaki zama shalele Baby, Akwai sirrin nisaa'i. hmmm Dagajin sunan kason na dabanne,na baki sati É—aya ki gwada ki gani Hajiya ta, tsugunno ake akai ga mai buÆ™ata ya tunÉ“e mu ta wannan layin 08028827241 karku manta UMSAD INCENSE mune na É—aya. Muna aika kayan mu duk inda kuke. Kamshin jiki martaba mutum.... 🅿ï¸3ï¸âƒ£3ï¸âƒ£&3ï¸âƒ£4ï¸âƒ£ ""Kanta ta kawar gefe tare da mikewa tsaye. Saikuma ta juyo gare shi tace "kabari adadi ya cika kana . Tana faÉ—in haka ta faÉ—a É—aki tare da faÉ—awa akan gado ta fara sakin wani irin kuka mai tafe da Æ™unar zuciya, inama amfanin kaso duniya, kaba duniya amanar kanka, cikin lokaci guda ta juyamaka baya,Wai itace ke cin ÆŠumame. Wayar ta tashiga ring ta É—auka afusace ta kanga avkunne tare da" faÉ—in kai Dallah Abul khairi ka shafamun lafiya kaji, ka rabu dani ka fita harkata, karka sake kirana. Saboda som abunda muke bai dace ba.. Afusace yace Dallah yimun shuru kinji shashasha , Wato ya ÆŠanÉ—anamiki zumar sa shiyasa kika fara juyamun baya ko? Dama mayaudariyace ke? maciya Amana, Duk cen da bakison binda muke babu kyau sai yanzu ,to ni dama amfaÉ—amiki auranki zanyi jaka kawai, kina da aure kina waya dani ,nima nason na aureki zakiyi da wani. Allah ya Æ™ara dawwamar da rayuwar ki cikin kunci da bakinci ki da talauci marar yankewa, banza kawai ashe dama wahala da naita sha akanki na kiranki kina Æ™in É—agawa kinacen manne ga matalaucin mijinki, fakiri da ko sisi bashi dashi, to kije kici shi ya ciki shikenan kuzauna lafiya jarabba kawai, dama ubanwa zai iya Dake inaba matalaucin da bashi da aiki ba AYU kawai ya kashe wayar yana sakin tsaki takaici. Innalillahi wa inna ilaihi Raji'un tace jikinta na É“ari ,ga wasu kwallah masu zafi suna zubomata ,yau ita Abul khairi ke da tsama magana haka, babu kunya babu shayi dan yason Sirrin zaman takewar ta, daga ta fadamai gaskiya ,wai mike faruwa da rayuwanane da komi yake son juyamun baya. Duk kan abinda nasa gaba sai ya Dakushe mun ya zamemun Æ™arangiya arayuwa na. Æ™ara kifa kanta tayi a filo taci gaba da kuka. Shikam Sadeeq daga waje bayan yagama cin abinci ya zauna yana nazarin taya zai iya fita yaje yaga mahaifiyar shi, Dan bayason tason bai lafiya, Baison ya zataji baz Baison halin da zata kasance ba ,har zai mike kuma ya dawo ya kwanta yana tinanin kila Amnah tayi bacci. Yana zaune yaga azahar ta kunno kai amma bata fito ba. Dakyal ya dafa bango ya mike ya isa É—akin. Yana zuwa yacganta kwance tana ta shasheka kuka . Yace subhanallahi Aminatu kiyi hakuri kinji, nima na son kinyi Æ™oÆ™ari. A'hankali ya Æ™arasa wajen jikkar kayan shi ya duka ya fara bincike, sai gashi ya É—akko farar takarda da biro da kyal ya mike yana cije baki ya karaso wajenta. "Yace share hawayen'ki Amnah, tashi ki fara haÉ—a kayanki sauran in naji sauki na kawomiki gida Nainah . Jin abinda yace" da kuma motsin takarda da taji ya sata dago kai da sauri tana kallon shi. Hannushi É—aya yasa ya dafe kirjinshi , É—ayan kuma ya dora akan takarda ya fara rubutu kamar haka. Ni Sadeeq S Sadeen na yan..... Da karfi ta kwace biron ta zubamai idonta da suke tsiyayar hawaye. Kallonta yake cikin mamaki abinda tayi , Dan yayi tinanin zatafi kowa farin ciki da jin dadi. Ahankali cikin bugun zuciya yace Amnah miye haka ? Kamar jira take ta duro daga kan gadon da karfi, bata tsaya komi ba ta rungumeshi ta saki kuka sosai hade da shashe ka. Cikin natsuwa yake buga bayanta ahankali har ta fara sauke ajiyar zuciya. Yace mikikeso? mikuma ke damunki. ko har yanzu jikin? Kai ta gilgizamai tare da dago idonta da suka kumbura sukayi jawur tace "Sadeeq Bazan iya rabuwa dakai ba awannan duniyar da muke ciki,Na dawo daga rakiyar rayuwa, duniya bata da tabbas,Ina son mukasance a haka har karshen rayuwata,kayi hakuri Dan zatin Allah da dukkan abinda namaka, Saboda wanda na É—auki akala rayuwata na bashi tini ya juyaman baya,Ada ina ganin zai zamoman Ma'ajin sirri na amma ina tini ya gaza,Inaso son mugina sabuwar rayuwa mu manta da wadda ta shude,A shirye nike dayin duk kan abinda kake buÆ™ata,kuma ashirye nike da zama dakai ahaka har karshen rayuwata,Alfarmata gareka ta karshe karka kara zancen saki , Dan zatin Allah,bani da kowa bani da komi ayanzu sai kai ,dakai na saba dakai kuma nike so na Æ™afa tarihin sabuwar Rayuwa ta. TaÆ™arasa tana faÉ—awa jikinshi ta rungume shi sosai.. Idon shi Alumshe yake jin zantikan ta wayanda suka zamemai kamar Almara. Shafa kanta yayi yana É—an murmurazata jikin shi . Ahankali ya É—ago kanta tare da rike habar ta yace". Amnah zaki iya rayuwa dani Ahalin talaucin da nike ciki yanzu ?wanda ko abinda zamuci bandashi, bankuma da lafiyar nemowa? Da sauri ta É—agamai kai tace"Zan Rayu dakai sadeeq ,ashirye nike kuma da faÉ—awa gwagwarmaya rayuwa dan ingata taka, kana inaso kabani dama ta fanni nema maka lafiya. Kai ya gilgizamata yace Amnah wannan Ciwon kibarvshi kawai ,ki tayani da Addu'a, kana nagode da kikamun wannan halaccin, Allah ya bani abinda zan sakamiki kinji Æ™anwata. ya jawota jikinshi ya rungume tare da kissing goshinta. Iso ta lumshe tana sake maÆ™alewa cikin kirjin shi. Sun daÉ—e a haka kana tace Mai "Dan Allah kabani izinin zanje in siyar da waya ta in dawo . Yace" Amnah karki rabu da abinki, ba tana debe miki kewar su Mamy ba? in suka kiraki sukaji bakya akan layi fa, ba zasuji dadi ba(dan baitaÉ“a tinanin bata waya da suba.) Kuka ta saki tace kayafeni "DEE" Ka yafeni, ina mai tsananin jin kunyar ka da tsoron tashi agaban ubangijina da hakkin ka mai girma dana É—auka na banzatar da igiyoyin auranka danayi har naba shaiÉ—an damar shiga rayuwata yadinga sarrafa ruhina da zuciyana yanda yake so,Daga karshe gori nasha sakayya da Akamun kenan. kayafeni dan zatin Allah. Ba tare da ya fahimce ta ba dan cikin kuka take magana. Yace babu komi Amnah duk kan abinda kikamun nayafe miki ,nima kuma ki yafemin. Tace bakamun komi ba, hasalima nina kasance mai yawan cuta agareka, tin daga ranar farko da muka hadu nafara É“ata ranka,Waya kuma zan siya Æ™arama. Yace shikenan Amnah nagode in nawar ke na fara aiki zan biyaki insha Allah. Wani irin farin ciki da sukunin zuciya ya kawomata ziyara, hakan yasa batason sadda ta daÆ™a tsalle ta sumbaci bakin shi ba. Tare da daukar dogon hijjob ta sanya tace zanshiga makwaf'tana muje da yarinya jiya. Kai ya É—agamata ta fita tana dagamai hannu shima hannu ya dagamata yana murmushi .oh Allah mai sauya bawa arana É—aya yafada. Amnah kam tana fita ta wanke fuskar ta tare da bude gidan ta fita tare da jan Æ™ofar. Gidan su Fatima ta shiga da fara'a sosai afuskar ta tayi Sallama tare da cewa Maman Fatima na nan kuwa.? Da sauri Maman Fatima ta fito tana Daura É—an kwali tace ''oyoyo ga Amaryar, sannu da zuwa, to yau dai kishiga ciki ko ina zuwa mugaisa. Amnah tace "to" tare da bude labulan palon ta shiga ta iskeshi fess ba datti ba komi dan Maman fatima akwai tsafta. Da sallama Maman fatima ta shigo, bayan sun gaisa Amnah ke cewa nazo aron fatima ne ta rakani wani wuri. Maman fatima tace'' to babu damuwa, bari tazo Baban ta ya aiketa Æ™arbo muna kaÉ—in taliya, jiya sai ga hidima ta abinci Allah yasaka da Alkhairi . Amnah tayi murmushi batace komi ba. Suna zaune fatima tashigo tsaf da it ta gaida Amnah, daga nan Mamanta ta faÉ—ama Babanta dake cikin É—aki ya bata izini suka fita. Kai tsaye inda suka sayi wayar suka nufa. Bayan sunje ta siyar da utya a mutunce sukabata 150k taita murna. Ahaka ta tsaya ta sai musu kayan miya da nama da wasu abubuwan buÆ™ata na gida,Irin su Mai, shinkafa, fulawa, wake , da sauransu, Dufa ta kashe 40k kana suka nufi gida da kaya niki- niki. Da sallama ta shiga ta iskeshi zaune yana waya, yana ganinta ya datse kiran tare da cewa" sannu Ƙanwata kin dawo?. Ashagwabe tace" kason mene ?nagaji fa wallahi, Yau dole kamun tausa ,au namanta babbane kai, kamun karyani zakai, ta faÉ—a tana zaro ido. Sosai abinda tayi yaji ya mai kyau, hakan yasa shi sakin Murmushi yace" ni da bani da lafiya taya zankai ki nawie inba sharri ba Amnah. Tace hmm ai'ka kusa warkewa insha Allah. Yace Allah ya amince nima zanso haka kodan in kul daku. Fatima ta fara shigowa dakaya ita da wasu almajirai suna ajiye wa. Sosai yake kallon kayayyakin yana mamakin yanda tayo sayayya mai yawa haka. Cikin jimami yace" Amnah duka kaÉ—in kika kashe? Ido ta kashemai tace" Saura na Lafiyan ka kawai ,gobe sai Asibiti insha Allah, medical center zamuje dan tafi kwararrin likitoci, Ban yarda da babba Asibitin ba... Godiya ya mata sosai da karamcin data nuna agare shi. Dubu biyar taba fatima da wani almajirin dake aiki gidansu suka É—auki gas dinta suka ciko mata . Bayan sundawo ta É—ora girki cikin nishadi take komi ,lallai ta yarda inma ka kauce hanyar Allah kunci da takaici da rashin walwala ke cika zuciyar ka. Girki tama su mai rai da lafiya,bayan ta gama tayi wanka ta zuba ta kai gidan su fatima ta zuba musu a flat daya, ta zuba nasu Ammi ta ajiye gefe. Ahankai take diba tana bashi yana ci yana Æ™arba yana bata har suka gama. Ta kalle shi cikin zaulaya tace" To matar na tafi, ki kula da gidan, sai na dawo kinji... Ido ya zaro tare da faÉ—in" Au hakama zakice ,Bari in'kamaki ya fara Æ™oÆ™arin tashi. Dariya Ta saki da sauri ta dauki foodflaks É—in ta fita fana É—agamai hannu. shima yamata fatan dawowa lafiya tare da zamewa yakwanta yana lumshe ido.... Tana fita ta tsaida napep har unguwar su Ammi. Bayan ta sallame shi tashiga gidan da sallama. Anan taga Ammi zaune ta rafka tagumi tana tinanin abinda ya hana yaronta zuwa gareta . Da fara ta amsa Sallama. Hamrat ta fito daga É—aki da gudu ta rungume Amnah tana faÉ—in "oyoyo aunty mai kirki, Sannu dazuwa, ina tacema Baby ya kaini wajen ki ya kiya, shima kuma yanzu kwana haka banganshi ba . ta nuna yatsa É—aya alamar kwana É—aya. Amnah ta durkusa ta rungumeta sosai cikin tausayin su, ta son shine jigon su. Tace "Hamrat kima Baby Addu'a bayada lafiya kinji . Kuka ta fashe dashi tace inaso in gan shi. Amnah ta share hawayenta tace zaki ganshi insha Allah . Ammi dake gefe jin abinda sukace yasa jikinta daukar rawa tace. "ÆŠiyata mijin nakine bashi da lafiya ban sani ba? Ta Æ™arasa cikin rauni da rawar murya. Amnah ta isa wajenta ta zauna ta gaidata tare da cewa" eh Ammi! Amma da sauki ,kasancewar in ya mike yana wahalane yasa nace mai karya fito zan fita in kawomiki ,gobe insha Allah zamuje Asibiti. Cikin rashin natsuwa Ammi tace" Amnah muje gidan naku in gansa, sadeeq shine jigona, shine cikon farin cikin rayuwar mu ,mune kaÉ—ai gareshi, baya da kowa sai mu. Dan Allah muje ta faÉ—a tana share hawaye. Itama Amnah hawaye'n tausayin su ta share tare da mikewa tace "muje Ammi. Atare suka fita akaro na farko da Ammi ta fito daga gidan, kimanin shekaru bakwai tana zaune ko kofar gida bata taÉ“a takawoba ,Tin ranar da suka shigo katsina. Gidan ta rufe tabi bayan Amnah dake rike da hannu Hamrat. Adai-daita suka shiga har unguwar su. Suna isa suka sallame shi suka faÉ—a gidan da sallama. Kwance yake idon shi asama yana tinanin Ammi . shi yason dole hankalinta ya kasa natsuwa da Rashin ganin sa kwana biyu. Jin sallama yasahi É—ago kai da sauri ya saukesu fes akan Ammi da Hamrat dake tsaye. Da sauri ya fara Æ™oÆ™arin tashi amma ya kasa. Da gudu Amnah ta isa kanshi ta kamo shi kana yanÉ—ago A'hankali. Sannu tamai ta shiga É—aki ta fiddo wani carfet ta shimfiÉ—a ma kusa da shi. Tace'' Bissimillah Ammi. Zama Ammi tayi idonta har sun canza launi. Yayin da Annabin kuma ta tashi ta shige É—akinta ta saki labule dan basu wuri su gana. Ahankali cikin tsananin rauni Ammi tace "Dee nah baka da lafiya ne dama shiyasa ka hukuntani da rashin ganin ka,yanzu da haka kaso kabar ni cikin yanayi batare da kasanar da niba?. Yace Ammi dan Allah Kiyi hakuri , wannan damuwar da zaki shiga itace sanadin da yasa nakasa yarda in sanar miki, Ammi rayuwata zata sake tsanani Ina nagan ki cikin damuwa,Gashi komi ya tsaya Ammi,Rayuwa ta muna tsanani, har takai ga bani da Abinda zan kai miki ,muma bamu da Abinda zamusa acikin bakin mu. Jiya da baccin yarinyar nan kila Ammi da bazaku samu komi ba ,kuma nima karshenta zankasance cikin halin da yafi wannan danike akai. Anan ya bata Labarin abinda Amnah tayi jiya har girki da icce, da siyar da wayar ta da tayi, da magana sakin data hana yamata, da alkawarin zama da shi akowane yanayi... Kai kawai Ammi ke jinjinawa a zuciyar ta kuma hamdala amkawai take ga Allah, tare da faÉ—in Alhamdulillah burin mu ya fara cika, Alhamdulillah Allah ya Æ™ara hada kansu , yasa suzama abin kwatance aduniya da lahira. Sadeeq da yaga tayi shuru yace" tinanin mikike Ammi?.. Murmushin karfin hali tayi tace "babu komi sadeeq, Allah yabaka Lafiya . yanzu muga ciwon naka. Ahankali ya nannaÉ—e rigar jikkin shi tare da nunamata babban tabon da ya cika da wani irin ruwa daya linka na jiya girma... Ido ta runtse da karfi tare da toshe bakinta. Kuka na kwacemata tace" maza -maza Sadeeq muje Asibiti kar abun nan ya fashe maka, Sadeeq munyi gan-gan ci wallahi. ta faÉ—a jikinta na daukar rawa. Shima Hankalin shi ya tashi yace" Ammi akwai matsala kenan.? Mikewa tsaye tayi tace" Babba Sadeeq . Amnah da ta jiyo kukan Hamrat da suka kyaleta tsaye gefe guda suna zance yasa ta fitowa da sauri tana faÉ—in lafiya Hamrat?. Anan taga Ammi tsaye. A rikice tace Ammi lafiya? Ammi ta share hawayenta tace "zoki gani yata, kema ai nursing ce ko ?zokigani. Da Sauri ta Æ™arasa wajen shi anan ammi ta É—agamata rigar shi taga wajen yayi wani mugun tukulluma da tafi tajiya. Kuka ta saki tana faÉ—in" Dee dama haka yamaka baka faÉ—amin ba?. Aguje takoma É—aki sai gata da hijjoba da Æ™aramar jikka ta tsargafo tace ma Ammi ina zuwa. Fita tayi ta samo mai napep ya iso har Æ™ofar gidan. Da gudu tacshigo gidan tace "Dee tashi mutafi. Shuru yayi yana mai jin rauni azuciyar shi, yanzu in ya mutu shikenan haka zasu shiga tashi hankali, Ya Allah ka araman tsawon ran zama da iyalina. Ahankali ya dafata suka kakkamashi ya mike a duke yake tafiya kamar tsoho suka fita... Suna isa kofar gidan Ammi ta fara shiga kana mai napep ya taimakamai ya shiga. Amnah ta rufe gidan tashiga gidan su fatima tace musu zasu Asibiti mijinta babu lafiya. Sosai Maman fatima ta jajantamata da addu'a Allah yakara lafiya mai amfani.. Fitowa tayi suka faÉ—a Napep din suka doshi hanyar Asibiti. Suna zuwa kai tsaye Emagency suka nufa. Kudin farko da aka fara cazata 20k dan sun lura ciwon nashi mai girmane. Fada suka fara akan ba akawoshi da wuri ba. Anan Ammi ta musu magana akan basu son da raunin ba su ma. Anan suka rubuta takarda da zasumai aiki washe gari da safe dan sai yasha magani. kana suka miÆ™a musu. KarÉ“a Ammi tayi ta duba batason sadda Æ™afafuwanta suka fara rawa ba. Amnah mah Æ™arba tayi ta kalla . kuka tasaki tare da buga kanta ga Bangon É—akin ta fara salati... Ina zasu samu wananna maÆ™udan Æ™udin da suka kai daraja Million É—aya da dubu É—ari biyu ,innalillahi wa inna ilaihi Raji'un tace tana sake karfin kukan ta. Agaggauce ta fito daga asibitin tare da samun Napep tayi gidan ta . Tana zuwa bata shiga ba ta fada gidan su fatima, tare da faÉ—in tana neman Alfarma a haÉ—ata da masu sayen kayan daki. Maman fatima kam batayi kasa a gwiwaba ta hadata da wata Yayar ta dake dillancin kayan ÆŠaki. Cikin lokaci matar tazo da wasu samari. inda Amnah ta É—aure fuska tare da faÉ—in bata yarda su shiga É—akin taba su tsaya ta fito. Anan sukayi tsaye waje. Itakuma ta buÉ—e Gidan suka shiga ta rufe. ÆŠakinta suka Æ™arasa anan matar ta saki baki tana kallon hamshakan kayan da aka É—ora ma wannan É—an gidan. . Amnah tace haba Hajiya kinyi tsaye uzurifa garan, dan Allah kiyi abinda ya kawoki. Matar tace "to nace nawa zaki sai dasu''?. Amnah tace dan Allah ba wannan ne gabana ba kibani ko nawane. Ganin banza ta samu yasa Hajiya cewa" zanbaki dubu É—ari takwas yayi. Amnah tace "eh bani ." Tace ai sai dai in'miki transfer gaskiya ban fito da kash ba ,kana dole akwance kayan kinga banamu bane na nan... 5/18/22, 09:34 - MY MTN 2: *Littafin🌹DAN DAKO🌹 na kudi ne biya ki karanta cikin Aminci. Biya 300kacal to 0006454115 Amina Dahiru jaiz bank,or MTN card to this number 09165832002. then send the evidence of payment via 07038423451* ðŸ¤ðŸ™ðŸ¤² Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Yan uwana mata ina kuke ku malmatso ga wanni sirri da nike son baku, ita ya mace sai da kamshi, ina macen da take ganin izgili da wulakanci da ake cewa maza nada shi, hmmm yar uwa to inkin kasance a haka da alama akwai ayar tambaya akanki. Tambaya ta ta farko gareki da wane irin turare kike amfani a jikin ki ?,da wane irin turare kike turara gidan ki,shin dawane irin turare kike Zukunni, hmmm to matso kusa kiji yar uwata. Shi kamshi Annabi muma ya faÉ—a abin sone,kuma Abune mai sanya natsuwa da girmama ma'aboci shi , Da Yawon son kusantar sa. Duk kan wulakanci da izgilanci na maza akwai turaran da zai miki maganin sa da izinin Allah,ba boka ba malam,wanda zai karkato da hankalin mijinki akan ki ku samu fahimtar juna. Ko kin son kamshi na dakusar da fitinar É—a namiji yar uwa? kigarzayo ki kwashi rabonki ga shaharariyar yar mai Dugurin nan mai suna UMSAD INCENSE ,Mace mai kishin mata da son Fiddo martaba mu. Nayi Amfani da turaranta naji masifar daÉ—in da yasa nakasa barwa raina. Nace bari in yaÉ—amuku dan kowa ya mallaki nashi cikin farashi mai sauki. Da fari bari in zayyano muku su kamar haka.👇 Maleek Al'oud Royal kush Cous-cous Kajiji Original sandal Sandal flex Sandal bange VIP mix Hawi Al'oud Kindikay Danal banat Darot Habil Gaf-Gaf Sirrun nisaa'i Sandal chips Kwalacca Humra black and body milk Attractive humra. Yar uwa zanmiki Dallah- Dallah. Akwai turaran da zaki sanyama kayanki . Misali! kisa kabasa kiturare kayanki . Akwai humra da bazaki sataba sai zaki turaka. Akwai turaran kaya ,na jiki, Dakuma na É—aki. Akwai kwallaca sirri, amma bama badata gaskiya sai ga wanda baida kishiya , Dan muddum kina amfani da ita tofa gabaki dayan hankalin mijinki akanki zai dawo,Dan yana juyo da hankalin namiji akanki baki É—aya ,zaki zama shalele Baby, Akwai sirrin nisaa'i. hmmm Dagajin sunan kason na dabanne,na baki sati É—aya ki gwada ki gani Hajiya ta, tsugunno ake akai ga mai buÆ™ata ya tunÉ“e mu ta wannan layin 08028827241 karku manta UMSAD INCENSE mune na É—aya. Muna aika kayan mu duk inda kuke. Kamshin jiki martaba mutum.... 🅿ï¸3ï¸âƒ£5ï¸âƒ£&3ï¸âƒ£6ï¸âƒ£ Amnah tace" ba damuwa zan'biki gidan ki yanzu in Æ™arba, amma kayan kibari gobe da yamma kana na dawo sai akwance, akwai buÆ™atar in kwashe kayan dake ciki. Cikin murna sosai Matar tace "baki da matsala, zanma iya barmiki su har nan da sati biyu ko wata É—aya. Amnah ta hau godiya. daga nan suka rufe gidan suka fita.. Bayan sun isa Amnah ta tsayar da napep É—in ta shiga, matar ta Æ™ilgomata chip ta bata. Godiya ta mata Sosai kamar ta bata kyauta. Aguje ta fita ta faÉ—a napep din sukayi Asibiti. Anan Æ™ofar É—akin da yake taga Ammi zaune waya a hannuta sai kangawa take akunne tana saukewa cikin damuwa. Da sauri cikin sassarfa ta isa wajenta tace" Ammi sannu ,ya mai jikin? Hawayenta ta share tace" Da sauki Amnah. Amnah tace" ko zan iya ganin Doctor da zaimai aikin?. Da hannu Ammi ta nunamata office É—in likitan daya duba shi. Da sauri ta tashi ta shiga ta gaisheshi , Tare da neman alfarma afara karba kudin hannuta gobe zata ciko sauran. Kasancewar sa dattijo kuma mai kirki yasa ya Amince. Anan ya faÉ—amata inda zata kai . Bayan taje takai suka bata Takada shedar biya ta dawo, ta dafa gwiwar Ammi tace'' Dan Allah Ammi mu ki share hawayen ki ,ki É—auka Amma Dee aiki angama, yanzu nariga da na biya dubu dari takwas insha Allah gobe zamu cika sauran.. Cike da mamaki Ammi ta mike tsaye tace'' Amnah kina nufin kinbiya kudin Aiki? Kai ta jinjina tace "eh saura dubu dari hudu suma insha Allah zanbiya gobe. Wata irin Runguma Ammi ta mata ta na sakin kuka tace'' Allah kenan! in yayika makaho sai ya baka É—an jagora, Daya kwantar da garkuwan mu sai ya bamu jaruma, Allah ya miki albarka ya Miki tukuici da aljanna , Amma Amnah ina kika samu wayan nan kuÉ—aÉ—an masu yawa bayan ya faÉ—aman Halin da kuke ciki?. Amnah tace "Wallahi kayan É—akina na siyar. Ido Ammi ta zaro tace anyi haka Amnah, to ke da mizakuyi Amfani?. Cikin natsuwa tana murza yatsun hannuta tace" haba Ammi, komi namu zai kare ai zamu iya sadaukar dashi dan lafiyar sa,in Allah yasa gaba ya tashi ya samu sai ya mayar muna ko. Cikin yabawa da maganar ta Ammi ta ÆŠagamata kai tare da dafa kanta tace" Amnah kin cika yar Halak,Allah ya Miki albarka ,ya baki abinda kike SO duniya da lahira... "Ameen" Amnah tace " Tare da miÆ™ewa ta tura dakin da yake , Anan ta ganshi kwance sanÉ“al idon shi sama yana kallon fanka. Da sauri ta Æ™arasa wajen shi ta zauna bakin gadon tare da riko duka hannayen shi ta rike tace'' Sannu Dee, ya jikin naka? Juyowa yayi gareta da murmushi akan fuskar shi yace "Alhamdulillah Æ™anwata ,ya kinci abinci kuwa? Ta É—agamai kai alamar taci. Cikin damuwa yace'' Amnah aiki zasumun, kuma da sassafe, Tinma yanzu sun hanani cin komi ,Babba damuwata bamu da komi ,kuma nason dole aikin yayi tsada ko... Murmushi tayi cikin son kwantar mai da hankali tace" kasan mene Dee? nima nayi tinanin aikin zayyi tsada, to duka abinda zamu kashe 25k, kuma kaga Alhamdulillah ina dasu , Dan haka ka kwantar da hankalin ka kaji ? Fatana Allah ya fiddoka lafiya mu rayu cikin Aminci.. Cikin jin daÉ—in lafazinta ya ÆŠagamata gira guda yana lumshe ido da sakin yalwataccen Murmushi mai tafe da ma'anoni da yawa... Ahankali suke fira har mangari ta kawo kai ,ta mai Alwallah ya tada sallah daga kwancen da yake . Itama Sallah tayi kana tafito. Tazo tace ma "Ammi ta shiga ciki zataje ta É—akko carfet da abinda za suci. Kai Ammi ta ÆŠagamata tana yabawa da kulawarta akan su... Bayan taje gida taga abincin su daya rage babu yawa, hakan yasa ta biya gidan Ammi dan dama key É—inta na wajenta ,ta É—akko wanda takai musu basu ciba ta nufi Asibiti. Bayan taje ta samu ta zubama su Ammi abinci sukaci suduka sukayo Sallah isha.. Ammi tace" Amnah ki koma gida in kwana dashi nan. Ido ta zaro tace "Ammi mizanyi agida, A'a kwara mukwana anan mufa kadai gareshi, babu abinda zanyi da safe naje. Ahaka sukayo zamansu suna É—an fira sama- sama. Karfe ukku na dare Amnah ta tashi tayo alwallah ta fara Sallah, Tana neman Allah yataimaka musu a mishi aikin cikin nasara, yasa a shiga lafiya a fito lafiya . Addu'a take sosai tana kuka tare da neman gafara Allah da yafiyar sa akan watsi da tayi da marta ba mijin ta. Jin shasheka kuka'n ta yasa Ammi ta tashi itama tayi alwallah suka zo suka hau Sallah. Tin daga sadda ta tashi yake kallonta, dama shi ba bacci yayi ba. Sosai abinda tayi ya burgeshi hakan ya Ƙara mata matsayi sosai acikin zuciyar sa... Suna zaune a haka har akayi sallah Asuba, sukayi sallah suka fara azkar. Karfe shidda wasu nursing maza suka shigo É—akin da wani gado na daukar marar lafiya. Sosai jikin Amnah ya É—auki rawa , Mussaman da taga ya zubamata ido ko kyaftawa bayayi, ga wata rama da yayi sai wani irin hanci zir kamar kuÉ“ewa dan tsawo . Ganin wani nursing zai samai riga yasa da sauri ta Æ™arasa wajen ta karÉ“a tare da faÉ—in" ku bamu waje mu mishi Addu'a ko. Fita sukayi Ammi ta matso ta mishi Addu'a sosai da fatan nasara kana ta fita. Hamrat ta miÆ™o mai hannu tace "Baby Allah yabaka lafiya . Kai ya ÆŠagamata ahankali yace "Ameen Baby'n Baby. Fita tayi tana É—agamai hannu. Hakan ya karyar mai da zuciya baison sadda hawaye suka zobomai ba,yana ganin wata kil bazai tashiba,shikenan yayi bankwana da ahlin sa. Amnah mah kuka ta saki ganin yanda yarinya Æ™arama jikinta yayi sanyi. A'hankali ta rufe É—akin tare da zama gefen shi ta kama hannu shi ta rike, tare da ÆŠaura kanta bisa hannu ta fashe da kuka sosai. Tace "Abokin faÉ—a, Abokin sabuwar rayuwa, Abokin mutuwa insha Allah... Cikin Æ™arfin hali yake jinjinamata kai ,siraran hawaye na bin gefen kumatunsa.. Amnah tace" in rokon Allah Mai rayawa mai kashewa ya fitomun da mijina Lafiya, Allah yasa yanda aka shiga da kai lafiya a fito dakai Lafiya,ina rokon Allah da yabani aran rai da lafiya na kula da ragamar rayuwar ka Dee har karshen numfashi na. Ameen -Ameen yace natare da Æ™ara haÉ—a hannuwan su ya matse Sosai. Kwankwaso kofar akai haka yasa A'hankali ta É—ago da kan shi ta sa mai rigar. Bata tsaya komi ba ta kai bakinta wajen na shi, tare da Tura halshenta ciki ta fara bashi wani irin zazzafan kiss mai tsayawa azuciya. Sosai take juya halshenta a cikin nashi tare da gangarowa kan Laɓɓan shi masu tsanani taushi ta tsotsa sosai. Cikin mutuwar jiki ta zare bakinta ta sumbci goshin sa, da sauri ta juya baya tace" A fito Lafiya Baby ,tana faÉ—in haka ta ficce tana share kwallah.. Yah ALLAH yace lokacin da tafita, yaso yana da Æ™afar da zai samu damar rikota, Sosai abinda tamai ya tsaya mai A rai,Abun ya masa masifar daÉ—i,Wani irin nishaÉ—i yaji yana tsintar kanshi ciki. Ahankli wayan da zasu tafi dashi suka shigo, suka azashi akan gadon suka fito dashi Ta gaban su Ammi suka wuce dashi yana É—aga musu hannu sun É—aga mai, har suka shige wata Æ™ofa dake nesa da É—akin da aka ajiye shi Sosai.. Amnah naganin sun shige ta rushe da kuka tare da rugawa É—akin ta daura Alwallah ta fara Sallah tana kai kukan ta ga Allah, a kan ya tada Dee É—insu lafiya. Suna zaune su duka babu wanda ya sama bakin shi wani abu, har karfe tara ba'afito da shiba. Iya tashin hankali sunshiga sai wajen 10 kana sukaga an nufo É—akin dashi yana kwance kamar gawa akan gado. Da wani irin gudu Amnah ta Æ™arasa wajen tare da tare gadon tana kallon shi . Shikam bacci kawai yake bai masom duniyar da yake ba. Suna shiga É—akin Ammi ta shigo tana faÉ—in ya'ya Doctor da fatan anyi aiki cikin nasara? Cikin fara'a sosai yace" Alhamdulillah Hajiya, Duk da aikin yaso bada matsala Amma Allah ya magance ta ,Anyi cikin Sa'a, sai fatan falfaÉ—owar sa lafiya insha Allah. Inaso daya tashi A kirani. Kai Ammi ta É—agamai suka ja gadon suka fita. Duk rurrufe shi sukai suna kallon yanda yake bacci hankali kwance, amma daka kalli fuskar shi kason yaji jiki. Ammi tace ma" Amnah taje gida tayi wanka, sai ta haÉ—omai Tea in ya tashi ya sha. Kai ta jinjina mata kana tafita tana rike da hannu Hamrat suka hau napep. Bayan sunje gidan ta dafa musu indomie suka ci ,kana ta É—ora ruwan tea da yasha kayan kamshi. Bayan ta gama ta juye a Flak's mai kyau, ta silalamu su taliya ,dama tana da sauran miyar jiya hakan yasa bata daÉ—e ba ta haÉ—a komi ta yima Hamrat wanka suka tafi. Suna isa suka iske Ammi zaune ta buga tagumi, ganin har karfe É—aya amma ko motsi bai ba. Amnah ta zauna tare da haÉ—ama Ammi tea mai kauri ta bata tasha . Sallah sukayi suka samu wuri suka zauna suna Addu'a tashin shi lafiya. Basu jima da zama ba ya fara motsa kafar sa, hakan yasa har rige -rige suke wajen isa inda yake. A hankali yake buÉ—e jajayen idanuwan shi har ya budesu fess akan ahalin sa. Kallon su yake É—aya bayan É—aya. Cikin sauri ya fara yunÆ™urin tashi. Hakan yasa Amnah saurin dafe kafaÉ—un shi tana gilgizamai kai tace" A'a Baby Dee! ka kwanta Dan Allah, kaga yanzu suka fito dakai. Ahankali yake motsa bakin shi yana jin Æ™afafuwan shi da kugunshi kamar ba ajikinshi suke ba. Yace Amnah an'mun aikin ne? Murmushi ta saki sosai tace" an maka cikin ma nasara kuwa Alhamdulillah. Idon shi ya lumshe bacci na fizgar shi.. Amnah ta fita daga É—akin ta faÉ—a office É—in likitan ta fadamai ya tashi. Atare suka shigo anan su Amnah suka fita . Sai da ya dubashi ya tabbatar da komi lafiya kana ya basu umarnin su bashi tea yasha. Da sauri Amnah ta shiga haÉ—a mai. GIDAN HAJIYA NENE. Zaune take palonta sai kaÉ—a kafa take cikin tsananin bacin rai, tare da É—aukar waya ta fara kangawa a kunne. Tanajin an É—auka ta fashe da kuka tare da faÉ—in Fulani! Fulani!! nace Fulani so nawa na kiraki? Kasancewar wayar speaker take yasa Mamy sauke ajiyar zuciya tace'' Nene ina wuni? Nene tace bansan shi ba, bansan gidan uban da yayi ba, Saude. Yau ko kinki ko kinso sai jia karya dokar ki, inkuma kikace kikawoman Æ™abali da'ba'adi wallahi zankwashe miki albarka. Yo in'bama wulakanci na yaran zamani ba ni dana haifeki kike bani umarni, kin hanani zuwa ga jikata. Kwana na nawa banga Kwandon Sukari ba,ke kinson tinda ya É—auke kafarsa daga gareni kila fushi yayi dani , Dan haka natafi yanzu zani ÆŠAN Larai ya kaini.. Ajiyar zuciya Mamy ta sauke tace bakiji ba Nene. Afusace tace bani ba Æ™araji kam har abada, munafuka kina nan Æ™asar waje kinata cika kina tumbatsa, amma kin watsar da rayuwar tilon yarki ,Kin rabani dasu inata rayuwa ni kaÉ—ai kamar mayya,to hukuncin yaci ubansa. Ta datse kiran tare da tashi ta É—akko mayafi ta sanya takalma, taja Æ™ofar palonta ta rufe. Tana gama rufewa ta yanko da gudu harabar gidan hannuta bisa kai tana ihu tana na shiga ukku ÆŠAN Larai, tashi ka kaini unguwa . Tim kakejin ya faÉ—o daga saman table É—in da yake kai yana bacci. Nene tahau yarfa hannuwa tace" Yanzu dama aikin da aka kawoka kenan kayi ,shege ka barman gida awatse sala yara suzo su tsinkemun yan shukoki ,to tashi mutafi nace... Cikin yanayi na mai bacci yace "wallahi Nene kiji tsoron Allah, ina bacci zakizo dawani mahaukacin gudu ki tashe ni ,nasama wuta ta tashi É—ak.... Wani irin mahaukacin bugu taima bakin shi da takalman ta. Tace munafuki É—akin uwarka wuta zata tashi, ba dai nawa ba, tsoron Allah kuma ai'nafi ubanka wallahi ,hauka kuma kaine zakayi shi tuburan ma kuwa,shege da baki kamar motar icce... Tashi tsaye yayi yana Æ™okarin nufar mota. Ta dakamai tsawa tace" maza zoka wanke wannan kodaddar fuskar taka da take ta maiko kamar sabon k Ƙuli ,ka kuma durje Æ™aton bakin ka kar kasama mutane cuta. Kan shi ya taho yana gilgizawa ya wanke fuskar shi, kana ya tashi yanufi Æ™ofar still yana gilgiza kai. Nene tace yo Æ™adangarema da abun yake halittar shi yayi yagama sai kai da kayi haye,shegen kai É—an mitsitsi kamar furar naira goma, Allah yasa ya cire sai kason ka ari halin Æ™adangaru... Dariya ya saki yace naji dai. Shiga motar tayi suka fita ya rufe gidan suka É—auki hanya. Ahankali take kallon hanya har taga masu saida zogala da Æ™uli -Æ™uli tace'' kai tsaya insai ma yar jikallena in naje in kwaÉ—amusu ita da kwandon Sukari, Allah sarki kwandon sukari I milisu Wallahi (I miss u) Dariya ÆŠan Larai ya saki yace" Nenes ina sonki zan turaki kabari Wallahi. Banza tayi dashi ta kyale dan zuciyar ta bugawa take. Bayan sun saya ya É—auki hanya har korar gidan Amnah. Anan sukaga gidan rufe. Nene tace ikon Allah, Ƙudurar sama liman da Wawan zama ni Aminatu ina yar nan ta tafi?... Fatima ta yanko da gudu zata shiga gida taga Nene da Æ™aton dutsi tana kiran kwandon sukari ku buÉ—eman na kawomaku zogala. Fatima tace "Inna ai basa nan suna Asibiti mijin ne bai lafiya . Wata irin juwa ta fara Æ™oÆ™arin kada Nene, da sauri ÆŠan Larai ya tareta tare da buÉ—e mota ta shiga. Cikin kallon Ruwa bebie tace "uban mi kikace yarinya?... Dariya fatima ta saki ganin yanda Nene ta juya idonta tace "ÆŠan fulanine baya da lafiya ,shine suka tafi Asibiti, batama jima da tafiya ba tazo ta É—auki kayan Abinci. Kururuwa Nene tasa ta É—akko wayar ta tana latsawa, hawaye suncika Mata ido ko gani batayi. Ta sake turo idon gaba amma ta kasa gano number da take so ta kira... ÆŠan larai dake tsaye ya rike marfin motar yana kallon wani waje . Nene takaima mahaukacin bugu a kirjin shi tace "kana gani ina ta wahala, munafuki bazaka iya kama man ba, amma kai kam anyi É—an asara wallahi.. Yace wai nenye yau sai kwasheman albarka kike minai maki? Tace ubanka kamun! Æ™arba ka kiraman Saude. Ya karbi wayar yakiramata dai- dai lokacin da motar yan nepa tayi parking Æ™ofar gidan. 5/18/22, 10:22 - Ummi Tandama😇: *Littafin🌹DAN DAKO🌹 na kudi ne biya ki karanta cikin Aminci. Biya 300kacal to 0006454115 Amina Dahiru jaiz bank,or MTN card to this number 09165832002. then send the evidence of payment via 07038423451* ðŸ¤ðŸ™ðŸ¤² Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Yan uwana mata ina kuke ku malmatso ga wanni sirri da nike son baku, ita ya mace sai da kamshi, ina macen da take ganin izgili da wulakanci da ake cewa maza nada shi, hmmm yar uwa to inkin kasance a haka da alama akwai ayar tambaya akanki. Tambaya ta ta farko gareki da wane irin turare kike amfani a jikin ki ?,da wane irin turare kike turara gidan ki,shin dawane irin turare kike Zukunni, hmmm to matso kusa kiji yar uwata. Shi kamshi Annabi muma ya faÉ—a abin sone,kuma Abune mai sanya natsuwa da girmama ma'aboci shi , Da Yawon son kusantar sa. Duk kan wulakanci da izgilanci na maza akwai turaran da zai miki maganin sa da izinin Allah,ba boka ba malam,wanda zai karkato da hankalin mijinki akan ki ku samu fahimtar juna. Ko kin son kamshi na dakusar da fitinar É—a namiji yar uwa? kigarzayo ki kwashi rabonki ga shaharariyar yar mai Dugurin nan mai suna UMSAD INCENSE ,Mace mai kishin mata da son Fiddo martaba mu. Nayi Amfani da turaranta naji masifar daÉ—in da yasa nakasa barwa raina. Nace bari in yaÉ—amuku dan kowa ya mallaki nashi cikin farashi mai sauki. Da fari bari in zayyano muku su kamar haka.👇 Maleek Al'oud Royal kush Cous-cous Kajiji Original sandal Sandal flex Sandal bange VIP mix Hawi Al'oud Kindikay Danal banat Darot Habil Gaf-Gaf Sirrun nisaa'i Sandal chips Kwalacca Humra black and body milk Attractive humra. Yar uwa zanmiki Dallah- Dallah. Akwai turaran da zaki sanyama kayanki . Misali! kisa kabasa kiturare kayanki . Akwai humra da bazaki sataba sai zaki turaka. Akwai turaran kaya ,na jiki, Dakuma na É—aki. Akwai kwallaca sirri, amma bama badata gaskiya sai ga wanda baida kishiya , Dan muddum kina amfani da ita tofa gabaki dayan hankalin mijinki akanki zai dawo,Dan yana juyo da hankalin namiji akanki baki É—aya ,zaki zama shalele Baby, Akwai sirrin nisaa'i. hmmm Dagajin sunan kason na dabanne,na baki sati É—aya ki gwada ki gani Hajiya ta, tsugunno ake akai ga mai buÆ™ata ya tunÉ“e mu ta wannan layin 08028827241 karku manta UMSAD INCENSE mune na É—aya. Muna aika kayan mu duk inda kuke. Kamshin jiki martaba mutum.... 🅿ï¸3ï¸âƒ£7ï¸âƒ£&3ï¸âƒ£8ï¸âƒ£ "" Wani Æ™aton mutum ne BakiÆ™irin dashi luti- luti yazo kofar su ya fara duka. Nene ta datse wayar hannuta ta tsaya tana kallon shi a Æ™ufule. Sosai yake buga gidan. ÆŠan Larai yace "Yallabai basanan fa. Afusace yace ''Aiko yau zan sheke wutar gidan nan, Munafukai kusan wata biyu basu biya ba, in zafi yaci ubansu sunje su biya. Nene tayi kwafa tare da ziro kafarta ta fito tana hura hanci. Tsani da aka ajiye mishi ya fara takawa yana kaÉ—a kanshi da yayi kwal da sabon aski. Sai da Nene ta bari yakusa kaiwa kana tazo da gudu ta gilgiza Tsanin tana sosa kanta, tare da fashewa da dariya -dariya mai haÉ—e da kuka- kuka. Gabaki É—aya ta rikice sai susa kai take tana gilgiza tsani. Jikin É—an lukutin nan ya É—auki rawa ya fara sakin salati yana kallon sama yana kallon Æ™asa, Ganin in ya faÉ—o mummu na illa zayyi,inkuma ya tsaya bai son ya zata kaye ba,.. Cikin ihu yace" Su Badamasi kuna kallon mahaukaciya zata watsoni da Æ™asa fa kunyi shuru. Jin abinda yace yasa yan uwan shi sakkowa daga saman mota sukayo wajen da sauri. Kamin su Æ™araso Nene ta watse hannuwata tana gilgiza musu kai, tana faÉ—in "uwaku -uwaku nace yan kwal uba, kamosu nan ta bisu da gidu tana mai É—ibar Æ™asa a hannu. Karcet sukayi wajen mota jikin su na É“ari. Yayin da ÆŠan Larai ya shige cikin mota yana kwasar dariya harda rike ciki. Nene ta dawo wajen tsani ta tsake gilgizawa. Ihu ya saki yace "Dan zatin Allah ki wuce kuma ki kyaleni. Cikin Susar kai tace'' kai Mai kan Sulba nan fa gida nane sai ka hanani ganin haske. kamoshi nan ya faÉ—o Æ™asa ya dagargaje. ta sake gilgizowa. Ihu ya saki ya Æ™ara Æ™anÆ™ame falwaya sosai. Cikin dariya tace "to maza ka Sakko na kara ganin Æ™afar ka sauy na cirewa wandon ka namaka shayi ,eh kanason shayi ko?... Cikin tashin hankali yake É—aga kanshi yace "A'a Tsohuwa an man wallahi. Dan matsawa tayi gefe tana tsintar duwatsu. Ganin haka yasa ya sakko da sauri ko tsanin bai É—aukaba ya ruga da da gudu. Aguje ta bishi tana faÉ—in taho ga aska nan ta nuna duwatsun hannuwan ta. Baiko tsayaba itama ta juya tana tsaki. Da sauri Dan Larai ya fito idon shi fal hawayen dariya yace "Nene kina wuta, cikin sauki kin korasu. Bugu takaimai ya kauce. Wani É—an nepa ne yazo da sauri ya dayuki tsanin ya ruga. Nene ta shiga gidan su fatima tace "abata kwatancen Asibitin da suke. Anan Maman Fatima ta faÉ—amata ta mata godiya suka fito ta shiga mota ta faÉ—amai inda zai kaisu. Bayan sunje da kwatance da ake musu suka samu suka gano inda suke... Amnah na zaune gefen shi bisa kujera, yayin da Ammi ke Æ™asa bisa tabarma ,shikuma sadeeq na bacci. Da sallama Nene ta tura kofar tana Æ™oÆ™arin magana ta hangosu. Da sauri ta Æ™arasa wajen ta saki kuka tana cire mayafinta ta aje gefe. Atare Ammi da Amnah suka muke tsaye suna kallon ta dan basu taÉ“a zato ko tsammani ba na ganin ta. Nene bata kallesu ba ta Æ™arasa wajen Sadeeq ta shafa kan shi sosai tana bin jikin shi da kallo, Tinda babu riga akai ,sai ciwon shi dake lulluÉ“e da bandeji. Amnah kam rawa jikinta ya É—auka hakan tasa ta koma gefe ta lafe bayan Ammi, Dan hakanan taji wani irin nawin ganin Nene, taji kamar bata kyauta ba ,ga shakka Nene da taji ya shigeta.... Nene ta zauna akan kujera saida tasha kuka ta gaji kana ta kallo Ammi da keta gaida ta bata amsa ba. Ammi ta sake gaisawa da Nene. Fuska a'ÆŠaure ta amsa tana sakin tsaki. Ammi ta taso tazo wajen Nene tace" Nene wake sanar dake bashi da lafiya'".?. Kuka tasa tace'' ai dama ni nason baku É—aukeni da mahimman ciba shiyasa aka kasa faÉ—aman Kwandon sukari baya lafiya, Fisabilillahi yaron da ke kula dani ya samu wannn mummunan ciwon da yakaishi ga aiki amma ace baza asanar da ni ba. Sai in ya tashi ya fara gaba dani ,yace naki zuwa ganin shi, to Allah yamun sakayya ... Ido Ammi ta zaro tace Dan Allah kiyi hakuri Nene, yau akai aikin wallahi jiya da yamma aka kawoshi, hankalin ba kwanceba . Anan ta faÉ—amata yanda sukai da kawo shi .. Hawayenta ta share ta kalli Amnah da duk tayi duhu tayi rama sosai . Cikin sanyin murya Amnah tace'' Nene ina wuni. Kai Nene ta jinjina tace" Lafiya klau ya mai jiki. Tace Alhamdulillah tana sadda kanta Æ™asa. Nan suka shiga fira Amnah taga rana tayi tace zanje inyo girki in dawo. Nene tace shikenan sai kindawo. Hannu Hamrat ta kama suka fita . Napep ta tare musu suka isa unguwar su. Bayan sun shiga gidan anan ta fara tinanin ina zata haÉ—a masu kudin su. Kujerata ta kalla da katifarta tace "ya kamata in rabu daku kuma. Da sauri tace ma Hamrat ta tsaya ta shiga gidan su fatima ta fito. "Tace to Aunty." Shiga tayi bata zaunaba ta nemi da akiramata Dillaliya. Ganin banza ta sake samuwa yasa tace gatanan. Amnah ta dawo gida ta fara girkin abinci shape- shape ta dafa ta juye musu ,kasancewar jallop ce tayi na kus-kus, shiyasa tayi saurin gamawa. Tana Æ™oÆ™arin shiga wanka aka bugo gidan. Dillaliya ce tashigo da katuwar jikka fuskarta fal da fara'a. Bayan sun gaisa Amnah tace'' Dan Allah katifana nikeso kisiya da kujerana. Ido tavzaro tace "wannan kujera ta Æ™asar wajace fa itama. Amnah ta É—aure fuska tace "zaki siya?. Da sauri ta É—aga kai alamar" eh." Nan ta shiga ta musu kudi dubu É—ari da Ashirin. Amnah ta gilgiza kai, tason bazasu kai ko rabi ba, Ya Allah , ina zata samu sauran. Wadrof É—inta ta shiga watsowa dan tasamu ko kayanta ne ta siyar sabbi. Sosai ta rikice tana watso kayan ciki gabaki É—aya É—akin ko ina ya cika. Wadrof gudace taki buÉ—uwa hakan ya sata fara neman key É—inta. Anan taga wata Laka dake É—akin Æ™asan gadon ta. BuÉ—ewa tayi da sauri . Wata katuwar jikka ta gani, da sauri ta jawota tana fatan Allah ya sanya key É—in na ciki. BuÉ—ewa tayi tare da zazzage jikka Æ™asa. Ihu ta saki ganin kuÉ—aÉ—e masu masifar yawa. (Amnah sako na nan na ajiye miki a cikin locar dake Æ™asan gadonki). Maganar Abban ta ta faÉ—omata a rai. Wani irin runguma tama kudin ta saki mahaukacin kuka cikin masifar jin daÉ—i da tsananin farin ciki tace"Ajiya maganin wata rana. Adanasu tayi ta fito taga Dillaliya na kallon kiching É—inta. Tace "am na fasa saidawa,zaki iya tafiya. Ido ta zaro tace kai" yar uwa yanzu dama kinson ba siyarwa zakiyi ba kikaja na kwaso Æ™afa nazo? Amnah tace" eh." Dillaliya tace" shikenan, ni da hadda ma wasu kuloli nagani nace kozan iya baki dubu dari da hamsin kibani su? Amnah tace "A'a bana da buÆ™ata, kawai ina ga gobe war haka kizo ma akwance miki wayan nan kayan ki wuce dasu'' . Tace "shikenan! ta fita jikinta a sanyaye. Amnah kam wanka tayi ta shirya ,anan taje ta kilga kuÉ—in taga Million É—aya ne chip -chip. 400k ta zara kana ta rufe gidan suka tafi, ta tsaya bakin Asibiti ta sayi fruit masu kyau ta shiga dasu, cikin kuzari da nishaÉ—i take tafiya har suka Æ™araso.. Suna shiga suka iske Sadeeq an dan tado gadon shi haka kamar ya zauna Ammi na bashi Tea. Kallo -kallo sukaima juna. lokaci daya ya saki murmushi yana juya kanshi gefe. Sosai Amnah tajj daÉ—i ya mamaye zuciyar ta ganin ya samu sauki. Gefen shi ta koma tayi tsaye tana kallon ledar ruwan da ake Æ™aramai. Tace" Dee ina wuni ya jikinka..? Yace lafiya kalau Alhamdulillah nama warke. Murmushi tayi tana kallon Nene dake kallon su cikin zallar mamaki da farin ciki ganin suna magana lami lafiya ba tsangwama kamar handa Amnah ta saba. Tace Nene" ina gajiya. Tace bani tare da ita, tinda gani ga Kwandon Sukari nah.. Amnah ta sakarmata Harara tana komawa gefe. Yana ganin abinda tayi Ammi ma haka. Farin ciki ya mamaye zuciyar shi yanaji inama ace su kadaine a É—akin,duk da bayajin zai iya wata magana da ita kamar yanda yake da sha'awa yi amma ya kasa. Nene ta mike tsaye tace" inaji ajikina akwai zukatan dake tsinemun albarka ,tashi mutafi waje Mamasu Kwandon Sukari, shin waike baki da suna ne sai Ammi? kins on dai baki haifeni ba ban kiran ki da sunan da yara ke maki A'ato. Dariya su Ammi sukayi tace "Nene sunana Maryam. Nene tace "Allahu Akubar kabiran, suna mai daÉ—i kuwa. Amnah tace am" nace ba! ko ku zauna inje in fara kai cikon kuÉ—in in dawo... Da mamaki Ammi ke kallonta shima sadeeq din mamaki yake na cikon mi? bayan 25k ne . Ammi ta jinjina mata kai tana mamakin minene kuma ta sake sayar wa. Da sauri ta fita taje ta bada ta dawo. Suna ganin ta suka fita. taja kujera ta zauna hannuta rike da Banana tana É“arewa. Bakajin ciwo yanzu? ta faÉ—a idonta akan ðŸŒ. Yace na fiki lafiyan jiki Amnah.. Bakinta ta turo tace "kai Baby Dee. Yace au hakama zakicemun, Baby kuma? Ta É—agamai kai tana zubamai narkakun idanuwanta. Tare da gusawa kusa dashi ta turamai 🌠a baki tace" haaa Baby. Yace "in kikacemun Baby sai inji wani iri". Tace nida Hamrat wayafi da cewa ya kiraka Baby?ita in takiraka kanajin wani abune? Shuri yayi yana sakin murmushi . Ta mike tsaye ta É—ago kanshi ta watsa idon ta cikin nashi "tace wayafi dacewa ya kiraka da wannan sunan?. Yace "Amnah aini bankai matsayin da zaki kirani da Baby bafa,itama tsananin yarintace, bata son ma mi hakan ke nufi ba. Idonta ta sadda Æ™asa gabanta na faduwa ,ta naji kamar bai manta duk abinda tamai ba kenan. Ahankali ya sanya hannu shi cikin nata ya murza, tare da cewa" Ya dai sst?. Ta É—ago idonta dake cike da kwallah tace" Dee na tabbata kana rike dani a zuciyar ka har yanzu, wallahi billahi Amnah da ba itace yanzu ba. Kayar da dani ,ni ina son Alakar mu inason muyi zama na har abada, wanda mutuwa zata rabamu, ka daure kabani dama mallakamaka sirrin zuciyana, Wallahi INA...SON...KA. ta faÉ—a cikin rawar murya Azabure ya É—ago idon shi ya zubamata yana mata wani kallo mai ma'anoni da dama ,cikin wani yanayin na zallar farin cikky yake kyafkyafta idon shi, tare da cewa kikace? Ya faÉ—a cikin son sake tabbatar wa.. Tace" yes na son kaji, amma zan sake mai maita maka ,Tinda ba abin kunya bane mijina ne kai,I LOVE YOU SO MUCH DEE . Banson Lokacin da sonka ya shammaceni yamun shigar sauri ba, na dai wayi gari da son kasancewa dakai har abada ,kaine jarumina, kuma kaine ka daceel da rayuwana ,kana kaine malamina daya fara bani darasin sabuwar rayuwa,Zan rayu dakai, da fatan samun farin ciki daga gareka . Cikin shauki ya sanya hannushi ya jawota jikinshi ta gefen hagun shi inda babu rauni. A'hankali ya fara sanya Laɓɓan shi yana zagaye karamin bakinta, tare da kissing fuykar ta, kanta, baki daya daya dau,bakajin komi sai sautin um muah! um muah !! Da ke tashi... Daga karshe ya gangaro da halshen shi ya fara mata wata kyakyawar sumba, yana danna halshen shi sosai cikin nata. Cike da buÆ™atuwa ta cafke tana lumshe ido. Sunkai 5mnt a haka kana ya zare daga gareta ya koma gefe yana sauke numfashi ztare da jinshi cikin wani yanayi wanda tinda yazo duniya bai taÉ“a jiba. Yace" Amnah akwai magana da zanmiki amma sai nasamu sauki, akwai godiya ta Mussaman da nike son nunawa gareki amma hakan bazai samuba sai nasamu sauki ,akwai amsa da nike son baki itama bazata samu yanzuba sai na warke, Sakona gareki na karshe I LOVE YOU TOO MY WIFE .... Wani irin tsalle ta daka tare da zubewa ta fara sujjada godiyar ta ga Allah. Kallon mamaki yake mata mai tattare da farin ciki. Jinya babu daÉ—i, amma shi yaji daÉ—in tashi, Dan gashi ta zame mai silar magancewar matsaloli da dama ,fatan shi Allah ya bashi lafiya ya dumfari aikinsa na gaba. BAYAN SATI ÆŠAYA. Wata irin shakuwa ce da soyayya ta shiga tsakanin su, wadda ta sasu nuna ma juna kulawa ko agaban waye. Yayin da É—aya baya iya juriyar rashin ganin É—an uwansa na tsawo wasu awanni.. Kimanin karfe biyu na rana suna zaune suna fira , Amnah ta zame ta tafi officer din Dr. Bayan sun gaisa ta fara kame -kame. Yace yadai Ƙanwata? mikike sone? Tace am" Nace Bazaka sallamemu mu koma gida ba, naga jikin da sauki. Yace da bari nayi ya kara warkewa saboda muna kulawa da ciwon. Tace ka faÉ—aman yanda zanyi zankula dashi gida . Ganin da gaske take yasa ya mata bayanin komi, kuma ta fahimta. Anan ya rubutamata magani tare da basu sati biyu sucdawo. Cikin murna tana rike da takarda tayo É—akin. Nene dake zaune bisa kujera tana cin dafafiya masara tace" ke mikike ta washema baki. Takadda ta nunamata tace" Ansallame mu. Nene tace kai Alhamdulillah yau kwandon sukari sai gidan Nana Maryama. Da sauri ya É—ago ido ya kalleta itama Amnah ita take kallo. Nene tace" Dole ya koma gaban uwar shi tayi jinyar shi, ke kuma kiwuce muje gida. Amnah ta kama hannu shi ta ruke sosai tace" Wallahi babu inda zani, kai kaji Nene, wake da Alhakin kulawa dashi inba niba, to bazanje ba, nida kika watsar da rayuwata kuma sai yanzu dan iyayi zakice wani yan! yan!! yan!!! to banzuwa.... Sosai yake zuba murmushi yana lumshe ido . Ammi kam cikin jin daÉ—in son da taga tana nunama yaron ta tace" da gaskiyar ki ÆŠiyata, ku wuce gidan ku, ke ma ai kin karanci lamarin jinya nan,na tabbata zaki kula da ciwon sosai. Nene tace "ke Maryama yaran yanzu basu da ta ido, Aa to ku bassu cikin gida su kaÉ—ai suyi abinda sukaga dama, ciwo yaki ci yaki cinyewa ,nidai na faÉ—amuku, kar azo ana kuka dani. Ammi ta sanya takalmanta ta fita cike da kunyar kalaman Nene. Shikam ido ya zubama Amnah yana kallo . Itama cikin nawin kalaman Nene ta saci kallon shi. Karaf idonta ya fada cikin nashi, kuma ta gaza janyewa. Halshen shi ya fiddo sosai tare da lankwasashi ya lashe lips din saman bakin shi ,kana ya huromata wani sassanya kiss. Cikin jin daÉ—i. Ta lumshe idonta tare da kama hannuwata ta matse a kirjinta sosai.... Nene na juyowa taga abinda suke . Da sauri ta mike tana rike zananta da yakusa faÉ—uwa , ta fita tana fada ita dai tason halin jikanyar ta, in tai mai fyade babu ruwan ta.. Da yamma ÆŠAN Larai yazo ya kwashesu suduka suka tafi gidan kwandon sukari.. Bayan sunshiga tayi saurin fiddo Æ™atuwar carfet ta shimfiÉ—a musu tsakar gida dan batasoma Nene ta shiga É—akinta balle taga babu gadon ta, dan tini an'kwance shi ta bada, sai tulin kaya dake gefe.. Zama sukayi suna fira. Amnah tace "Nene aroman wayar ki dan Allah . Nene ta zaro tabata. ÆŠaki ta shiga tana kallon Sadeeq dake binta da ido. Bayan taje ta zauna akan kati farta tare da latso number Mamy. Dan Hakan taji tana masifar kewar ta,musamman da taga Nene, lallai ta tabbatar da tayi babban kukure ,su iyaye ba'ayin fushi dasu, ko bakomi ya kamata ta kira su taji lafiyan su. Ahalin da take ciki ita bata bukatar kudin kowa, kuma bata bukatar asan Sirrin zaman takewar su, kawai tana dai fatan gyara Alakar ta da iyayen ta,Da duk wani makusan cinta... Number ta danna ma kira. Saida ta katse kana Mamy ta kira ta É—auka tayi shiru. Da sallama tace Nene kin huce kenan? Mamy nah ina wuni, ya gida ya Abba nah ,ya Amal ,fatan duk kuna lafiya.. Dam! Dam!! Mamy taji gabanta na faduwa, cikin rawar baki tace "Amnah kece , Amnah dama da rankai da lafiyanki kika sharemu Amnah?. Rawa jikinta ya É—auka lokaci daya hawaye ya sakko mata , tace" Dan Allah koma mi namiki kiyi hakuri ki yafemun, kuma bazan sake ba insha Allahu.. Cikin jin daÉ—i'n sauyin da aka samu Ammi tace" shikenan na hakura , Kowa lafiya ,basa nan ni kaÉ—aice, Amnah nayi kewar ki ,ina Sadeeq? kwana biyu bamu gaisa ba. Tace" yana lafiya Mamy. Mamy tace ina wayar da Abban ki ya baki ranar da zaki tare? Ido ta zaro tare da mikewa tsaye tace'' wallahi Ammi na mance da ita? 5/20/22, 09:13 - MY MTN 2: *Littafin🌹DAN DAKO🌹 na kudi ne biya ki karanta cikin Aminci. Biya 300kacal to 0006454115 Amina Dahiru jaiz bank,or MTN card to this number 09165832002. then send the evidence of payment via 07038423451* ðŸ¤ðŸ™ðŸ¤² Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Yan uwana mata ina kuke ku malmatso ga wanni sirri da nike son baku, ita ya mace sai da kamshi, ina macen da take ganin izgili da wulakanci da ake cewa maza nada shi, hmmm yar uwa to inkin kasance a haka da alama akwai ayar tambaya akanki. Tambaya ta ta farko gareki da wane irin turare kike amfani a jikin ki ?,da wane irin turare kike turara gidan ki,shin dawane irin turare kike Zukunni, hmmm to matso kusa kiji yar uwata. Shi kamshi Annabi muma ya faÉ—a abin sone,kuma Abune mai sanya natsuwa da girmama ma'aboci shi , Da Yawon son kusantar sa. Duk kan wulakanci da izgilanci na maza akwai turaran da zai miki maganin sa da izinin Allah,ba boka ba malam,wanda zai karkato da hankalin mijinki akan ki ku samu fahimtar juna. Ko kin son kamshi na dakusar da fitinar É—a namiji yar uwa? kigarzayo ki kwashi rabonki ga shaharariyar yar mai Dugurin nan mai suna UMSAD INCENSE ,Mace mai kishin mata da son Fiddo martaba mu. Nayi Amfani da turaranta naji masifar daÉ—in da yasa nakasa barwa raina. Nace bari in yaÉ—amuku dan kowa ya mallaki nashi cikin farashi mai sauki. Da fari bari in zayyano muku su kamar haka.👇 Maleek Al'oud Royal kush Cous-cous Kajiji Original sandal Sandal flex Sandal bange VIP mix Hawi Al'oud Kindikay Danal banat Darot Habil Gaf-Gaf Sirrun nisaa'i Sandal chips Kwalacca Humra black and body milk Attractive humra. Yar uwa zanmiki Dallah- Dallah. Akwai turaran da zaki sanyama kayanki . Misali! kisa kabasa kiturare kayanki . Akwai humra da bazaki sataba sai zaki turaka. Akwai turaran kaya ,na jiki, Dakuma na É—aki. Akwai kwallaca sirri, amma bama badata gaskiya sai ga wanda baida kishiya , Dan muddum kina amfani da ita tofa gabaki dayan hankalin mijinki akanki zai dawo,Dan yana juyo da hankalin namiji akanki baki É—aya ,zaki zama shalele Baby, Akwai sirrin nisaa'i. hmmm Dagajin sunan kason na dabanne,na baki sati É—aya ki gwada ki gani Hajiya ta, tsugunno ake akai ga mai buÆ™ata ya tunÉ“e mu ta wannan layin 08028827241 karku manta UMSAD INCENSE mune na É—aya. Muna aika kayan mu duk inda kuke. Kamshin jiki martaba mutum.... 🅿ï¸3ï¸âƒ£9ï¸âƒ£&4ï¸âƒ£0ï¸âƒ£ """Mamy ta saki salati tace" Amnah kina nufin kayan kamshin ma dana kashe miki makudan kuÉ—aÉ—e baki taÉ“a amfani dasu ba Amnah??? Cikin kame -kame tace. "zanyi" . Tace to maza -maza kifara saboda komi na nan arubuce,Akwai na sha, na gyaran jiki, dana kamshi . Tace shikenan nagode. Amma yaushe zaku dawo.? Tace " sai nan da wata bakwai. Kai ta jinjina tace" shikenan in na É—auki wayar zankiraki anjima. Tace kiba Sadeeq wayar. Tace "anjima zankira ki in'baki, suna tare da Nene da Ammin sa. Tace" Lafiya dai ko ?ko wani abun kikai masa da aka taru? Tace" A'a bashi da lafiyane Mamy ,harma aiki aka masa. Azabure tace" innalillahi wa inna ilaihi Raji'un, Amma kika kasa sanar dani Amnah?.. Tace"nidai nace kiyi hakuri Mamy da komi da namiki. Tace'' shikenan Allah ya bada lafiya. Ameen ta amsa tana mata sallama suka ajiye wayar. Girki ta fito ta É—ora, duk inda tayi idon shi akanta, dan doguwar rigace jikinta baÆ™a, tamata kyau sosai ,duk da babu kwalliya afuskar amma tayi masifar kyau. Bayan ta gama zata zubama Ammi tace "A'a ta gode tafiya zatayi. Nene tace" ita kam bazata ciba , cikinta cike yake. Ana mangari ba ÆŠAN Larai yazo daukar Nene. Nene tace ma Ammi ta tashi su sauke su gida. Anan suka musu bankwana. Amnah ta musu rakiya hannuta rike da kula data zubamu Abinci. Bayan ta karÉ“a tayi godiya, Hamrat na É—agamata hannu suka wuce. Gidan ta rufe ta dawo fuskarta fal da murmushi ta karaso wajen shi tace" sannu Baby Dee. Yace hmm "nida kika share tin É—azu kina girki kin barni tsakankanin taffi sai kewar ki nike. Murmushi tayi tana shafa sajen shi tace. Ai'gani yanzu dagani sai kai ,ko wasan Danbe zamuyi zan maka duka in kadaka ,inma ligif bazaka iya komi ba.. Kai ya jinjina yana murmushi" yace hakane jarumata,Bari in Æ™arasa warkewa sai mugwada ko?.. Dariya tayi ta tashi ta zubo mai ruwan Alwallah, bayan yayi itama tayi suka tada sallah .. Suna gamawa sukayi karatu har Isha . Bayan sungama kana suka fara fira . Sai tara suka tashi jin mazajen sauro na kawo musu ziyara,ga babu wuta. Tashi tayi ta taimaka mai suka nufi É—aki. Suna shiga ya zaro ido tare da kallonta ,ya Æ™ara kallon É—akin yace" Amnah ina kayan ÆŠakin ki? Tace sunbi lafiya. Cikin diriricewa yace" ban'fahimceki ba, minene kike nufi da sunbi lafiya, Amnah kardai kicemun sata aka miki bayan bama nan, innalillahi wa inna ilaihi Raji'un ,ya faÉ—a cikin damuwa. Hannushi ta kama ta É—orashi akan kujera takoma gefe ta zauna tace . Dee ka daina damuwa. Ita kaddara nada DaÉ—i, saboda akwai ranar da zatazo baka da ko sisi, to aranar kake sanin darajats, in Allah yasa kana da abin kuÉ—i sai ka magance matsalaka ranar da babu cash hannu. Aikin da aka maka gaskiya yana da kudi shiyasa ni kuma naga bamu da komi, kuma ina da abun siyarwa sai ince sai nabi mutane ina a taimakamana ?wannan rayuwar da ake ciki. Shiyasa nayi amfani da damata na siyar na nemi lafiyar ka. Wallahi tallahi ko Nene bata sani ba ,kuma har abada bazata sani ba. Duk ranar da Allah ya baka iko in'kasamu abinyi zaka mayar mun ko. Kai kawai yake jinjinawa yana jin tsananin tausayinta da wani mahaukacin son ta da yaji yana sake huda kowace Huda ta jikin shi. A'hankali ya jawota jikinshi yace "Nagode sakhallahu khairan matar sirri, insha Allah zakiyi alfahari da mijinki nan gaba . Tace kulawar ka da soyayya nafi buÆ™ata ba dattin duniya ba.... Yace inshan' Allah kimin Addu'a samun sauki da bakinki mai albarka. Tace Allah ya horema mijina lafiya. Yace" Ameen matata Nagode, amma inajin zafi ko zaki taimakamun inyi wanka? Tace sosaima ko in'maka. TaÆ™arasa tana kashe mai ido. Da sauri ya Daga kai yana faÉ—in" Sosai ma, dama kince ke kikafi can-canta da jinya. Dariya tayi ta mike tsaye tace "taya zanma babba wanka kamar ka, ai zakace bani da kunya ko. Yace" ai dama ba ason mace najin kunyar mijinta, in akace ta haka za atafiyar da rayuwar tofa za acutar da juna. Fita tayi tana mai jin daÉ—in kalaman shi. Cikin wata babba roba ta zubamai ruwan tare da ajiyemai kujera tsakar gidan ,kana taje tamai magana. Yace to sannu. Ahankali ta É—agoshi ta ciremai dogon wandon, tare da cewa to kaje kayi ko. Ya kwabe fuska yace" miyasa bazakimun ba, kamar yanda kikasamun rai. Idonta ta rufe tace" Dan Allah karkasa in nutsefa. Dariya yayi kaÉ—an ta kamashi yafita, saida taga ya zauna kana ta dawo ta fara lalubar jikkar shi dan son samomai kaya marasa nawi da zaisa Ganin duk manyan kayane yasata zazzageta bisa katifar ta tana tinanin ko suna Æ™asa. Wani irin ihu ta saki wanda yasa Sadeeq mikewa da sauri ya sheka ruwa ya É—aro towel karami a'kugun shi yashigi arikice yake faÉ—in Amnah lafia kuwa? Kuka take sosai tana lafewa ga bango jikinta na É—aukar rawa.. Yace innalillahi wa inna ilaihi Raji'un, Amnah minene, yanzufa na... karaf idon shi ya sauka akan bindigar dake gefe wadda yana da tabbacin itace silar shiga furgicin ta. Kan shi ya dafe tare da Æ™oÆ™arin isa wajenta. Da sauri ta mike tsaye tana sake lafewa ga bango jikinta nasake É—aukar kyarma.. Cak ya tsaya yaki Æ™arasawa,Dago kai yayi ya kalleta yace "Amnah Dan Allah karki hora rayuwar da muka gina da tsoro ko shakku, ki yarda dani kizama mai amince wa da mijinki ,ganin bindiga ajikkata karya saki shakku ko mamaki, ko tinanin zan iya cutar dake ko wani. Wallahi billahi bantaÉ“a cutaba Amnah, hasalima ni aka cuta, aka kashema rayuwa ,amma kiyi hakuri kiba lokaci damansa da sannu zai bayyana miki komi kinji ,wallahi ni ba abinda kike tinani bane. Cikin rawar jiki tace"" nifa bana Tinanin ka da komi , kawai na tsoratane, wallahi banason bindiga som, kuma miyakawota cikin kayan ka.? Yayi murmushi yace "aiki. Tace" Aikin mi sadeeq? nifa kasani a duhu. Ƙarasawa yayi wajenta ya rungumota tare da mannata da kirjin shi. Yace" kirabu da wayan nan tambayoyi marasa amfani kinji ,na faÉ—amiki lokaci zai bayyana komi, kimayar da ita inda kika ganta kawai ,kidaina taÉ“awa..... Cikin yarda da kalaman shi ta fiddomai kaya marasa nawie kana ta mayar hannu na kyarma. Nan taga harda sistem É—inshi mai masifar kyau da tsada. Kallon shi ta sakeyi akaro na biyu . Da sauri ya juya ya fita dakin yasamu wuri tsakar gidan ya zauna . Dan bayason yawan tambayoyi lokacin da baishirya bada amsasu ba.... Bayan ta gama komi ta shirya duk kan kayayyakin su saman kujera anan taga Æ™atuwar ledar turarukan da Mamy ta aiko mata da jikkar wayar ta. Cikin jin dadi ta buÉ—e kwalin wayar ta fiddota ta ajiye gefe, Æ™aramace amma mai kyau mai tsada. Katifar ta gyara musu tare da gyara É—akin fess kana ta fito ta shiga wanka. Bayan ta fito taga kwalaben turarukan ta duk sun Æ™are.. Tsaki tayi tana faÉ—in dole inje kasuwa kodan siyo muna fanka da kayan buÆ™ata. Ledar da kamshinta keta dakar mata hanci ta fiddo. Wani irin lumshe ido tayi dan kamshin ya masifar mata daÉ—i da sata natsuwa... Ahankali ta fara fiddo manyan kwalaben tana ajiyewa gefe . gabaki É—aya akwai rubutun dake tabbatar da amfanin su da bayanin su. Wata yar siririyar kwalba da duk tafisu Æ™aranta ciki ta tafi da hankalinta, dan tindaga kwalba zakason cewa koma miye na ciki mai kyau ne,ga uwa uba wani masifaffan Æ™amshi da ke tashi ciki. Anan ta fara duba rubun da akai jiki kamar haka. (Amnah Dan Allah kitaimaka karkimun wasa da wannan damar,Humra sirrice ta UMSAD INCENSE da kyal tayoman ita cikin wata É—aya, dan na kashe makudan kuÉ—i wajen ganin an'yomana ita da yawa nidake, ki tabbatar in zakiyi amfani da ita ko zaure bazaki takaba, kadan zaki diga ga hannuwanki ki murje illahirin jikinki da bayan kunnuwanki ,Saman mararki duk dai wata gaba da zatakai sako jikin ki ki shafe ta, Allah ya zaunar daku lafiya.) Tace to fa wannan yar abun keda wannan dogon bayanin. Sosai ta É—ibeta ta fara murza jikinta kamar ta samu mai. Ita kanta kamshin masifar dadi yake mata,wasu fararan kaya ta É—auka yan kananu rigar dai- dai saman cibin ta, sai wandon ko gwiwa bai kai ba . Bayan ta gama ta É—akko fitilata ta fito tana zuba makirin kamshi. Da Sallama ta karaso wajen shi inda ta ganshi zaune ya buga tagumi. Amsawa yayi yana mai sake bude hanci jin tana zuba wani masifataccen kamshi mai tada tsigar jiki. Idon shi ya É—ago yaga yanda tayi kyau sosai. Hannu guda yasa ya tarota tare da faÉ—in oyoyo kinbarni zaune tindazu kina tsorona ko? Fitilan ta ajiye gefe tare da Æ™arasowa wajen shi ta zauna gefe tace "wallahi koda kaine SHEƘAU zan iya zama dakai saboda son da nike ma, kawai bindigar ne banaso . Yace" to aiko dole kisaba da ita ,ya faÉ—a yana lumshe ido. A'hankali ta É—ora kanta bisa cinyar shi da har lokacin towel kaÉ—ai garai. Tace miyasa bakasa kayan da na fiddomaka ba. Yace ina shakkun shiga É—akin ne ,ki Æ™ara furgita, nabar zuciyar ki ta samu natsuwa ne A'hankali, gashi yanzu kin iso da kanki ko? Ya faÉ—a yana shafa hannushi bisa fatar ta. Tace uhm hakane. shiru yayi yana jin wani irin yanayi illahirin tsigar jikin shi mikewa take. A'hankali! A'hankali!! yake jin yanayi da yake ciki yana sauyawa,ga wani masifaffan kasala da ta fara sauka illahirin jikin shi. Wanda sanadin hakan ne yasa Amnah dake kwance kan cinyoyin shi saurin tashi ta kalleshi, ta kalli Dee dinsa dake wani irin numfashi daga cikin towel É—insa. Sosai shima ya zubama towel din dake manne ga jikin shi ido, ganin yanda yake ta huruwa yana sama sosai kamar wata mesa.. Wata masifaffar kunya takawo mai ziyara ,sai matse kafa yake amma ina abun yaki bashi hadin kai tsalle kawai yake yana dukan iska. Amnah kam som ta kasa janye idonta daga kanshi, hakan yasata kara kankance ido tana karemai baiwar da Allah yamai kallo ,wato ashe da jarumi take tare yan iskan da take kallo matsayin jikokin sane,Yau gata ga uban ubansu ,wayyo Allah na ta saki wata kafurar miÆ™a.... Sadeeq kam sosai marar shi ke hautsinawa, yanajin jikin shi nata É—aukar rawa.... Da sauri ya mike yama manta da ciwon jikin shi, ya jawo Amnah suka mike tsaye ,tare da kama hannuta suka nufi ÆŠakin su da yayi durum... Wani zazzafan numfashi ya saki tare da rungumeta sosai yana lumshe ido, Ga Dee É—insa nata cakin ta. Cikin in ina sa ya fara magana . Amnah ..menene.. ki ..kayi ..amfani dashi.Amnah wane kalar turaren kika shafa, Amnah inajin son kasan cewa dake, Amnah kinsani yanayin da bantaÉ“a shigaba, Amnah kibani kanki ,Ina masifar son Kamshin ki,in kika hanani zan iya shiga tashin hankali , Ahhhahhhhh Amnahhhh ... Wani irin tsalle ta daka ta koma gefe. Cikin lalube ko gani bayayi ido cike da wutar jaraba ya isa inda take. Da karfi ya jawota tare da lalubo bakin ta ya tausa nashin a'ciki. Gabaki É—aya hannayen sa ya sanya ya yaga rigar jikinta cikin gushewar Hankali. Cikin kyarma sosai da jikinta keyi tace "Dee miye haka, Dan Allah ka daina ,ka gafa karka fama raunin ka. Som baiji mi take cewa ba, Hasalima jiyayi kamar tana cewa" Dee kayi komi kake so ni takace. Sosai ya'sake haukacemata har ya kaishi ga manna bakin shi akan twins É—in ta. Wasu irin zafafan ajiyar zuciya suka sauke a tare... Ahankali kafafauwanta suka fara rawa jin abinda yake mata. Da sauri ta kwace daga gareshi ta haye saman katifa ta kwanta tana sauke numshafi, tare da haÉ—e kafafuwanta waje guda ta matse da Æ™arfi... Shikam still lalube ya cigaba dayi dan som Idon shi sunki buÉ—uwa.. Saman katifar da yakejin saukar numfashinta ya dira ,tare da jawota jikinshi ya fara mata wasanni masu zafi, inda ta haukace ta fara sambatu tana shafa kanshi da fuskar shi.. Shikam jin abun babu sauki yasa ya saki kuka , yana faÉ—in karki hanani, jijiyana zata tsinke, kitsayamun Dan Allah,Karki barni Amnah da DAKO Sha'awar ki .... Amnah hankalinta ya fara dawowa jikinta, Dan shape ta manta da raunin shi . Da sauri ta mike tsaye tana turashi gefe tayo tsakar gida aguje tana sauke numfashi. fitilar ta ta É—auka aguje ta sake komawa É—akin. Anan ta ganshi kwance kuma har lokacin towel É—in shi daure ajikin shi kana ganin tsayuwar sandar girmansa... Kanshi ta Æ™arasa da Sauri tare da cewa "Dee are You okay? Kai kawai yake juyawa yanajin wata azababiyar sha'awa. Amnah ta saki kuka tace" Dan Allah kayi magana, ko ciwonka ka fama?.. Hawaye suka silalomai yace ""Amnah ke nike buÆ™ata, amma kina hanani abunda ya halatta agareni,kina gudu na, in'bansamu daga gareki ba gawa zan samu ,dan Allah kibani dama ,in' kum bazaki bani ba Amnah ki tashi kije kiyi wanka ,ki raba kanki da wannan masifaffan kamshin dake neman kaini lahira, Dan Allah Amnah ki tashi naceee... Da sauri ta mike tana tinanin to miye haÉ—in kamshinta da shine . Toilet ta shiga tayi wanka sosai ta wanke gashinta kana ta fito. Dakin ta Æ™araso yana kwance har lokacin tsaye yake kyam babu alamun kwanciya ajikinshi. Itakam tana so ta rikeshi tanajin tsoro, tana kuma jin kunya, hakan yasa ta koma gefe tayi zaune tana zubamai ido. Ganin goma tayi na dare babu sauran sassauci daga yanayin da yake ya sanya yace "Amnah zoki kwanta inji ÆŠuminki , Dan Allah karki hanani kasancewa dake yau daya,Namiki Rantsuwa da Allah bazan miki komi ba... Da sauri ta Æ™arasa wajen shi ta shige cikin jikinshi sosai ta lafe. A'hankali ya zame daga gareta ya fara wasanni da ita sosai, wayan da som hankali da tinani bazai baka ya iyasu ba. Sosai take sakin wani nishi wanda shi kanshi yanasane dana buÆ™atane, amma taki amince mai. Daga karshe haka ya tura Mamanta guda abaki yana tsotsa har bacci yayi gaba dasu. Asubar fari ta fara buÉ—e ido jin anata kiraye kirayen Sallah.. Ido ta zaro sosai ganin Mamanta cikin bakinshi yana tsotsa ,hankali kwance kuma bacci yake. Wata masifaffiya kunya ta kamata, wadda ta sata sauri rufe ido, tare da kama Mamanta tana Æ™oÆ™arin jaa A'hankali Dan zugi yake mata . Da sauri yasake cafkowa yana Æ™ara karfin tsotsar shi gare ta. A'hankali tace washhhhh Dee_ zafifa.. Jin maganar ta yasa ya fara buÉ—e ido akanta A'hankali yana kallon fuskarta ,wadda itama shitake kallo. Ganin ya buÉ—e idon shi duka fes akanta yasa tayi saurin rintse nata. . Ganin yanda tayi baisa ya cire bakin shi ba, saima Idon shi daya lumshe yaci gaba da tsosta. Cikin shagwaÉ“a ido rufe tace gaskiya ka saki karka tsinkamin Mamana fa ,kai ko kunya bakaji.. Ahankali ya saki yana mai juyo da ita yace" Amnah buÉ—e idonki muyi magana?.. Tace "um um ina jinka a haka. Yace da gaske nikefa magana zamuyi. Kadan -kadan ta fara budesu tass ta waresu a kanshi . Ido ya zubamata Sosai yace "Amnah tin daga ranar da kika furta kalmar so gareni nasama kaina son in'fara rayuwa aure dake , Amma na tabbata banda wannan dama sai na warke. Hakan yasa na killace kaina har sai jiya da kika tsokanoni. Wallahi Amnah Ajiya naso mallakar ki yanda bakiyi tinani ba. Amma kika kasa bani wanna damar ,,keda kikace kina so na, to miye auren inba wannan ba , Amnah wallahi duk ranar da kika Sanni na sanki ni natabbata daga ranar shakuwa da soyayya mu zata daÉ—a hauhawa, To Dan mi zaki hana, kinson Allah na fushi da macen dake kauracema mijinta miyasa zakiyi hanani halak ÆŠina dake kanki ?. Cikin rawar murya tace" kayi hakuri Dee, Wallahi ba hanaka nayi ba. Ka duba ciwon ka a lulluÉ“e yake, kuma in'kace wani abu ya shiga tsakanin mu akwai buÆ™atar kayi wanka ,shin zakayi wankan ne Batare da ka zubama inda aka toshema ruwa ba? Ya saki Mulmushi tare da mikewa Ahankali, batai aune ba sai gani tayi ya cire towel É—in baki É—aya, ya mata tsaye Haihuwar gyatima. Ihu ta kurma jikinta yana Bari, ta koma gefe tana salati... Yace kin'yarda ke sirrinace ,ki ture zancen kunya wallahi ayanzu babu abinda bazan iyayi gabanki ba, kinzama ni,nazama ke, kin yarda abunda baikai hakaba zai iyasani wanka a kanki, Wallahi Amnah tin kamin inshigo dÉ—aki dake jiya wanka ya tabbata kaina. Kasa juyowa tayi sai tsoro mai tsanani da taji ya Dirar mata. Murmushi kawai ya saki ya fita jin ana kiran Sallah. Tana ganin ya fita ta juyo tare da dafe kirjinta tace" wow zan ciyu Wallahi, nacsamu dai -dai dani wanda zai gamsar da buÆ™atata, ta tashi tana taka rawa...... 5/20/22, 09:13 - MY MTN 2: *Littafin🌹DAN DAKO🌹 na kudi ne biya ki karanta cikin Aminci. Biya 300kacal to 0006454115 Amina Dahiru jaiz bank,or MTN card to this number 09165832002. then send the evidence of payment via 07038423451* ðŸ¤ðŸ™ðŸ¤² Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Yan uwana mata ina kuke ku malmatso ga wanni sirri da nike son baku, ita ya mace sai da kamshi, ina macen da take ganin izgili da wulakanci da ake cewa maza nada shi, hmmm yar uwa to inkin kasance a haka da alama akwai ayar tambaya akanki. Tambaya ta ta farko gareki da wane irin turare kike amfani a jikin ki ?,da wane irin turare kike turara gidan ki,shin dawane irin turare kike Zukunni, hmmm to matso kusa kiji yar uwata. Shi kamshi Annabi muma ya faÉ—a abin sone,kuma Abune mai sanya natsuwa da girmama ma'aboci shi , Da Yawon son kusantar sa. Duk kan wulakanci da izgilanci na maza akwai turaran da zai miki maganin sa da izinin Allah,ba boka ba malam,wanda zai karkato da hankalin mijinki akan ki ku samu fahimtar juna. Ko kin son kamshi na dakusar da fitinar É—a namiji yar uwa? kigarzayo ki kwashi rabonki ga shaharariyar yar mai Dugurin nan mai suna UMSAD INCENSE ,Mace mai kishin mata da son Fiddo martaba mu. Nayi Amfani da turaranta naji masifar daÉ—in da yasa nakasa barwa raina. Nace bari in yaÉ—amuku dan kowa ya mallaki nashi cikin farashi mai sauki. Da fari bari in zayyano muku su kamar haka.👇 Maleek Al'oud Royal kush Cous-cous Kajiji Original sandal Sandal flex Sandal bange VIP mix Hawi Al'oud Kindikay Danal banat Darot Habil Gaf-Gaf Sirrun nisaa'i Sandal chips Kwalacca Humra black and body milk Attractive humra. Yar uwa zanmiki Dallah- Dallah. Akwai turaran da zaki sanyama kayanki . Misali! kisa kabasa kiturare kayanki . Akwai humra da bazaki sataba sai zaki turaka. Akwai turaran kaya ,na jiki, Dakuma na É—aki. Akwai kwallaca sirri, amma bama badata gaskiya sai ga wanda baida kishiya , Dan muddum kina amfani da ita tofa gabaki dayan hankalin mijinki akanki zai dawo,Dan yana juyo da hankalin namiji akanki baki É—aya ,zaki zama shalele Baby, Akwai sirrin nisaa'i. hmmm Dagajin sunan kason na dabanne,na baki sati É—aya ki gwada ki gani Hajiya ta, tsugunno ake akai ga mai buÆ™ata ya tunÉ“e mu ta wannan layin 08028827241 karku manta UMSAD INCENSE mune na É—aya. Muna aika kayan mu duk inda kuke. Kamshin jiki martaba mutum.... 🅿ï¸4ï¸âƒ£1ï¸âƒ£&4ï¸âƒ£2ï¸âƒ£ ""Wanka yayi kana ya É—auro alwallah ya dawo yace taje tayi. Bayan tayi sukayi Sallah kana ya jata jikin shi suka kwanta. Sai karfe goma ta falka ta samu ta zare jikinta daga nashi, ta hau gyaran gidan. Bayan ta gama ta haÉ—amusu breakfast mai sauki kana ta faÉ—a wanka. Bayan ta fito ta zauna tayi kwalliya dai -dai misali ta sanya riga da wando masu masifar kyau da suka fiddo shape É—inta sosai. Humrata ta É—auka zata sa sai kuma ta fasa ,sai kawai ta murza kwalacca UMSAD INCENSE mai daÉ—i kamshi ,kana ta Æ™arasa wajen shi tayi tsaye tana kallon yanda ya rungume pilo yana bacci cikin natsuwa... A'hankali ta haye katifar tare da zare pilon ta maye gurbin shi da ita. Sassanya kamshin da take ne ya kaima hancin shi duka. Wanda hakan yasa cikin sauri ya fara baÉ—e idanuwan shi. Murmushi ta sakar mai tana shafa sajen shi dake masifar burgeta. Tace "good morning Yaya Dee. Hannu shi yakai kan lallausan gashin goshin ta da yayi luf-luf yace" kintashi lafiya Dear ,shine kikamun wayo ko, kika tashi kika barni. Tace nafi buÆ™atar hutunka sosai saboda kayi saurin warkewa. Yace in na warke mi zakibani?. Ido ta juya tace "Sweet. Yace hamm matsoraciya. Idonta ta lumshe tana juyawa gefe cikin kunya. Yace Amnah. . Ta juyo tace "Na'am Yah Dee. Ido ya lumshe yace" ina masifar sonki. Tace "nima haka, na mafi Sonka fiye da yanda kake Sona. Yace "Hmm ,Na tabbata zakiyi mamaki idan nace miki tin ranar da na fara É—ora idona akanki sonki yamin dirar mikiya ,na hadu da mata kala +kala ammah bantaba jin wadda na damu da damuwarta ba sai ke, sai dai matsala É—aya banason rauni mafari bantaÉ“a baki fuskar kikawoman raini ba,Aranar danaga wasu yan iska na neman keta miki haddi wallahi bantaba jin zallar bakin ciki da takaici ba kamar ranar,ke ko wannan halbin bindiga dake jikina banji zafinshi ba kamar yanda naji zafin ganin ki da wani, Amnah saida na kwana biyu bani da lafiya, kuma duk saboda fargaba abinda suka so miki da banzo ba,ban fahimci sonki ni keba inaganin kawai Amanar mahaifiyar kice da ta bani nike karewa,har sai ranar É—aurin auran mu bayan munzo gidan nan tare ,ganin halin da kike ciki yasani damuwa , anan nagane duk kan jinki da nike araina so ne. Amma saboda naga som hankalinki ba akaina yake ba nakama kaina, A'hankali na fara janye zuciyata daga shiga hurumin ki,nayi burin kyautata miki da son samiki ran kiyi biyayya da umarnin iyaye amma kika kasa, sai gashi lokaci guda Allah ya amshi Addu'a nah ya juyoman da hankalinki,Duk da AURAN namu dama sharaÉ—ine dashi, in kin fara sona mu zauna tare, inkuma wata biyar ,ko shekara É—aya ta cika babu canji dole nayi alkawari sauwaÆ™e maki ,kije kisamu zabin ranki. Amnah kece zabin raina ina fatan ko Aljannah mu kasance atare. Ahankali ta faÉ—a jikinshi ta saki siririn kuka tace. " Nima kaine zabin raina, amma wani ruÉ—un duniya yasa na kasa gasgatawa. Saboda wani shirme na cen marar amfani,, Duk sadda zan tinano yanda Nikeson wanda zan aura ya kasance Wallahi kaine ke faÉ—omaun arai ,amma rashin hankalina yasa nakasa gane cewa kai din nan dai kaine zaÉ“ina, Amma nagode Allah da Auran ka ya zamemin sanadin canza rayuwata... Yaca Alhamdulillah burin farko ya cika saura na biyu insha Allah. "Tace mungode Allah". Daganan ta taimaka mai yayi wanka bayan ya fito ta bashi kaya marasa nawie yasa sukayi break kana suka shimfiÉ—a carpet ta zauna ya kwanta bisa cinyar ta suna fira. Karfe 12 Amnah tace "My love ko kana so kaje gidan Ammi? Kai ya ÆŠagamata da sauri . Tace "to É—agani in tsaido mana abin hawa sai muje , Dan Allah kabani dama inje kasuwa in samo muna abun buÆ™ata. Yace na baki Amnah Allah ya saka da Alkhairi da Æ™oÆ™ari.. Tace Ameen ya Allah kana ta mike ta sanyo babban hijjob har Æ™asa, kana tazo gareshi ta sumbaci goshin shi ta fita . Bata jima ba sai gata ta dawo. Anan ta kama shi ta É—auki ledar maganin shi kana ta taimka ya shiga Napep... Gidan ta dawo ta É—auki dubu dari ukku ta ajiye sauran ta fito ta rufe ko ina, kana ta shiga Napep din suka tafi suna fira cikin nishaÉ—i. Bayan sun je ta sallame shi ta kamoshi hannuta É—aya rike da jikkar maganin shi sukayi sallama... Ammi dake zaune tana tinanin yanda zata ganshi dan da kunya taita zara ta ji kamar sallama su. Da sauri ta É—ago kanta tare da miÆ™ewa cikin zallar farin ciki da ya kasa É“oyuwa tace'' oyoyo ga ÆŠiyata, wallahi yanzu nike ta tinanin ku ,ga wayata babu kati balle inkira inji lafiyan ku. Amnah na rike da hannushi tace" Ammi muma tinda mukaji Æ™arfe 12 yayi baki ba Nene nace muzo nan mu yini dan zanje kasuwa.. Cikin jin daÉ—i tace "aiko kin kyauta É—iyata Allah ya kaÉ—e fitina yaÆ™aracsanya shakuwa da kusanci a tsakanin ku. Amnah tayi murmushi tana sunkuyar da kai . Yayin da shikuma yace Ameen ya Allah Yana turo baki... Ammi ta kalleshi tace" Dee nah yau da Ammi naka kake fushi hadda turo baki? Ashagwabe yace shikenan Mamy daga kinga Sweety tah sai ki kasa bi takaina ko ki ji ya jikina dole inyi fushi kin canza sabuwar Ya.. Murmushi sosai ya bayyana ga fuskar ta, Yayin da Amnah taji kunya sunan da ya kira ta da shi ta shige É—aki tana kiran Hamrat. Ammi ta dafashi tace" Sannu Dee nah, na son kasamu sauki tinda kana kalkashin kulawa matar ka ko. Kai ya É—aga mata alamar "eh. Hannushi takama ya zauna suka fara fira . Amnah ta fito da Hamrat da tasha wanka cikin riga da wando tace" Ammi tin kamin in zauna in kasa tafiya bari inje kasuwa in dawo. Ammi tace "shikenan saikin dawo, Allah ya kiyaye. Ameen tace tana satar kallon Sadeeq tare da É—agamai hannu. Murmushi yayi "yace bakiji ba Dear." Juyowa tayi ta kalleshi yace" Allah ya kiyaye ya tsareki daga sharrin masu sharri, Allah ya miki albarka mar'atu saliha. Cikin tsananin jin daÉ—i tace "Ameen Yah dear, nagode Ammi na tafi. Fatan dawowa lafiya tamata suka fita... Ammi ta juyo gare shi cikin tsananin jin daÉ—i tace "Kaga ribar biyayya ko sadeeq ,Naji daÉ—i sosai da Allah ya dai-dai ta tsakanin ku da Amnah wallahi ,Yarin yar nan tana da hankali da natsuwa, sadeeq som banga abunda ake faÉ—a akanta ba, Sadeeq ko kason Million É—aya da dubu dari hudu aka maka aikin ka, kuma wallahi duka ita tabiya. Anan ta faÉ—amai duk yanda sukayo da Amnah, da kuma kudin da Abba ta ya ajiye mata. Tace Sadeeq" lokaci yayi da Yakamata kaba matar ka tarihin rayuwar ka. Saboda ta cacanta da zama ma'ajin sirrin ka. Kana banaso muwuce wata biyu bamu doshi kasar mu ba. Kai ya jinjina yace" Insha Allah Ammi, nima ba na Aminta da ita sosai wallahi, kuma darajata ta linku sosai a idona. Wayar shi data kwana biyu ajiye ta shiga ring. Bayan ya fiddo yaga Mamy ce. Cikin girmamawa ya daga suka gaisa ta mai ya jiki ,da jajantawa akan bata saniba, Nene tayi fushi da ita taki faÉ—amata. Murmushi yayi yace" naji sauki munama gidan Ammi. Tace" ina Amnah na kira wayar ta bata shiga?. Yace taje kasuwa ita da Hamrat, Na son babu charge, jiya bamu samu wuta ba. Cikin tausayawa da halin da suke ciki tace" shikenan nagode Sadeeq, ka gaida Ammi taka ,kace mata muna dawowa kusa insha Allah, Amma karta faÉ—ama Amnah. Yace insha Allah, Allah ya maidoku lafiya . Tace" Ameen sukayi sallama. Suna cikin magana sukaji tsayuwar mota. Dai -dai lokacin ne kuma Nene ta sanyo Kafa da sallama tana faÉ—in kwandon Sukari dama kana nan, wai miyasa kuketa juyi da rayuwata ne, Dan wulaÆ™anci kamar kun samu kwallo. Bayan kason zanje ganin ka shine ka kwaso kafa kadawo nan. Wannan ai cin mutuncine da son sani gudawa. Saboda na É—auka Wallahi halin naku na yaran zamani kukayi kirjin ya É—aÉ—e aka koma Asibiti ayi sabon Aiki, Bakaji yanda Yan cikina suke kiran Zuzuzuzu ba , Yo daga tsyayawa yi maku girki sai ku kulle gida ku kwaso Æ™afafuwa kamar sandar rake ka dawo gida ,to yau babu inda zaka nan zaka kwana, som banyar da da komawar ka gidan nan daga kai sai ja'irar yarin ya nan ba. Ammi kam wata masifar kunya ce tasa taita motsi tanajin kamar ta yanka da gudu. Yayin da Sadeeq ya kafe Nene da ido yanata auna maganata ,wai kodai suma sunson Amnah mabukaciya yace? tabbas sun sani tinda har sukayi gaggawa aura mai ita,to Amma taya?abin nan na masifar dauremai kai?to kodai suma Asibitin sukaje sukaji daga garesu. Ohhh Allah Nainah na Æ™oÆ™arin fassara mai mata A idon duniya... Yace" Naiha munfa gaji da zama gidan mukaÉ—ai. Shiyasa mukayi nan. Ido ta zaro tana kwalkwal da ido alamar zatai kuka tace "Yanzu Kwandon sukari duk yanda nikejinka araina amma ka nunaman kafi buÆ™atar ganin uwarka dani ko? To shikenan, babu komi,Bani babu kai na gayama. Ammi ta taso tana dariya ta gaidata. Neje ta amsa tace "shine kika basu wuri suka zauna kikaÆ™i cewa suje su gaidani , dan baki É—aukeni da mahimman ciba , Bayan har yanzu Æ™afata,Bayana,kwankwaso na ciwo suke, Saboda zaryar goyashi da Nike ina kaishi banÉ—aki sadda baya hayyacin shi. Ido Ammi ta zaro shima idon ya zaro yace" Nainah wallahi kiji tsoron Allah. A yaushe na fita hayyacina da zaki goyani? Ta matse kwallah tace" ni dai nason anyi haka, Amma kila mafalki nayi... Dariya yake sosai yana faÉ—in" sorry my lot... Tace" to nayi Surri É—in... Wayar ta ta É—auka ta kanga akunne tana hura hanci. Bayan an É—auka tace" hala namomin danama bawan Allah girki dasu Dan ya samu ya tada komaÉ—a kasamun busashen hannu ka kake tsincewa ko? Wallahi an'dayyi asara dan ubanka ,ka kawo kayan nace wai mutum yason aikinshi amma saika faÉ—amai.... Sadeeq yace "Nainah kayan dad'i kikamun ne? Tace" eh mana dan in'samu wannan kirjin naka Ƙato ya ciko da wuri ,wallahi Saddi kanamun kama da samudawa ko kuma irin yan cikin fim din nan na indiyawa . Yama sunan su ta kalli Ammi. Cikin dariya tace" banson wanda kike nufiba Hajiya Nene.. Nene tace'' Rafto ake cemai ko buss ,mai dai kashe mutane....... Dariya sosai ya sanya yana dafe ciwon shi yace" Allah ya barmu da Nene yar boko. ÆŠan Larai yayi sallama ya shigo hannushi rike da manyan kuloli ya gaida Ammi tare dama sadeeq sannu da jiki ya ajiye. Nene ta bishi da harara. Kayan abinci ya fara kawowa da lemuka masu kyau ya ajiye kana ya fita. Ammi tace" Nene wannan uwar hidima haka. Tace to _Maryama inban makuba wazai maku, Kwandon sukari dai babu lafiya, kuma baku da wani abu , dole aÉ—an taÉ“a da wannan Allah yabada lafiya . Godiya Sadeeq yamata sosai yanajin girmanta na daÉ—a hauhawa cikin ran shi. Suna zaune har karfe ukku kana Amnah ta dawo hannuta rike da manyan ledoji sai yaro ya biyota da kwalaye guda biyu.. Ganin Nene yasa ta shiga É—aki dasu tare da fito da wata ta kayan marmari ta gaishesu kana ta zaune gefe tana Ajiye su gaban Sadeeq. Nene tace Amnah mikika siyo? Tace kayan make up ne. Kai ta jinjina sukayi zaune har akai la'asar. Nene tayi alwallah tashiga É—akin Ammi yin sallah. Anan ta buÉ—e ledar taga yawanci duk kayan tea ne , sai kayan data soyamai Æ™anana, sai turaruka da man shafa da sabulun wanka dana wanki sai killing,Sai kwalayen da tayo pieces É—in kayan abinci kala- kala tinda suna da wasu.. Hawaye ta share tace" Aminatu kinyi Hankali, kinga Rayuwa tabbas .... "Bayan wata É—aya.* Zaune suke a harabar Asibitin shida Amnah, hannu su sargafe dana juna, yana sanye cikin wasu riga da wando Black da suka masifar yi mai.kyau, ita kuma Amnah na sanye da abaya mai duwatsu Black sai sheki take, tayi kyau sosai farinta ya sake fitowa, ta cika sosai alamar kwanciyar Hankali . Ahankali yakai bakin shi akunnata yace "Sweety yau in aka tabbatar miki dana warke zaki yarda? Ido ta zaro tana faÉ—in" Allah My love masifar tsoronka nike, nifa gani nike zan iya mutuwa wallahi in'kasamun ... Murmushi yayi yace" ai'shine girman da mutun ci na ko ,kin fiso muyita kwana da ciwon mara kullum, sai dai romance amma Babu sex balle mu rarrage ,ai kinga anyi ba'ayi ba ko . Ta rufe idonta tace" Dan Allah kayi shuru ,karma aita kiranmu bamu jiba. Tana rufe baki wani yafito yakirasu. Bayan sunshiga Dr ya sake duba Sadeeq yamai murna sosai dan ciwo ya warke sumul.. Sosai suka shiga farin ciki . Cikin masifar jin daÉ—i" yace Zan'iya komawa ga Iyalina? Amnah tace" laaa tare da tashi ta fita da sauri tana yaba Rashin kunyar Dee É—inta. Shikam likita dariya yayi sosai yace" babu abinda bazakai ba Abokina ko ince Æ™anena,Gama wasu magani nan da nike amfani dashi nida iyalina,Insha Allah zakaji daÉ—i sosai ,. Anan ya bashi wasu chocolate manya masu masifar kyau yace "to ga nawa gudummuwar, wannan mai gold din kwalin shine naka, wannan kuma na madam ne ,sai muce araya sunna na Lafiya, Allah ya kawo rabo mai amfani... Farin ciki sosai ya kaimai ziyara baison sadda ya mike ya rungumeshi ba. Yace" nagode Doctor kason sabon aure nayi shiyasa nike cikin shaukin abun.. Cikin mamaki yace "Sabon aure ne kai, to gaskiya kayi hakuri nakuma jinjina ma da har ciwon nan ya warke lami lafiya, Allah yabaku zaman lafiya, bani number ka. Sadeeq ya bashi shima ya É—auki tashi suka tafi. Yana fitowa yaga Amnah tsaye gefe tana latsa wayar ta. Cikin sauri yayo kanta ya bata wata irin Runguma, cikin Shauki yace '' KOMI ZANYI Sweetheart . Kugunshi ta kama tarike tana jujjuyawa da shi tace" Alhamdulillah baby mu ya warke sai shagali . Yace kidaina fada.my wife muje gidan Nainah yau acen zamu yini... Napep ya tsaidamusu suka shiga sai gidan Nene. Cike da farin ciki ta tarbesu tana faÉ—in ga laila da majnuni.... Ido ya zaro yace "majnuni kuma?Aljanifa kenan . Tace yo ki nason yanda ake cewa ne . Yace to kice ga miji da mata so simple. Tace bazan ceba. Anan suka fara fira sai dare suka mata bankwana. Tamasu godiya da yini cike da farin cikin warkewar sa... Suna isa kofar gidan sukayha wata dalleliyar mota. Sallama mai Napep Amnah tayi ta doshi Æ™ofar. Hy Æ™awata kece a adai-daita sahu?. Taji an faÉ—a abayanta. Arazane ta jiyo idon ta ya sauka ga Billy da tasha wani mahaukacin wanka. Amnah tace"Laa kece agari Billy, Sannu da zuwa, waye ya maku kwatance ne.? Ta juyo da niyyar magana kenan idonta ya sauka ga sadeeq da ya doso inda suke hannushi rike da canji daya Æ™arba. Azabure tace" Uncle Dee. Da sauri Amnah ta kalle shi shikum ya zubama Bily ido. Cikin mamaki Amnah tace kinson miji nane? Wani irin Salle ta daka ta koma gefe hannuwanta na kyarma take nuna shi tana nuna Amnah. Cikin yanayi na zafi da zallar bakin ciki tace" kina nufin ke kika auremin shi? .... 5/21/22, 16:51 - Ummi Tandama😇: *Littafin🌹DAN DAKO🌹 na kudi ne biya ki karanta cikin Aminci. Biya 300kacal to 0006454115 Amina Dahiru jaiz bank,or MTN card to this number 09165832002. then send the evidence of payment via 07038423451* ðŸ¤ðŸ™ðŸ¤² Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Yan uwana mata ina kuke ku malmatso ga wanni sirri da nike son baku, ita ya mace sai da kamshi, ina macen da take ganin izgili da wulakanci da ake cewa maza nada shi, hmmm yar uwa to inkin kasance a haka da alama akwai ayar tambaya akanki. Tambaya ta ta farko gareki da wane irin turare kike amfani a jikin ki ?,da wane irin turare kike turara gidan ki,shin dawane irin turare kike Zukunni, hmmm to matso kusa kiji yar uwata. Shi kamshi Annabi muma ya faÉ—a abin sone,kuma Abune mai sanya natsuwa da girmama ma'aboci shi , Da Yawon son kusantar sa. Duk kan wulakanci da izgilanci na maza akwai turaran da zai miki maganin sa da izinin Allah,ba boka ba malam,wanda zai karkato da hankalin mijinki akan ki ku samu fahimtar juna. Ko kin son kamshi na dakusar da fitinar É—a namiji yar uwa? kigarzayo ki kwashi rabonki ga shaharariyar yar mai Dugurin nan mai suna UMSAD INCENSE ,Mace mai kishin mata da son Fiddo martaba mu. Nayi Amfani da turaranta naji masifar daÉ—in da yasa nakasa barwa raina. Nace bari in yaÉ—amuku dan kowa ya mallaki nashi cikin farashi mai sauki. Da fari bari in zayyano muku su kamar haka.👇 Maleek Al'oud Royal kush Cous-cous Kajiji Original sandal Sandal flex Sandal bange VIP mix Hawi Al'oud Kindikay Danal banat Darot Habil Gaf-Gaf Sirrun nisaa'i Sandal chips Kwalacca Humra black and body milk Attractive humra. Yar uwa zanmiki Dallah- Dallah. Akwai turaran da zaki sanyama kayanki . Misali! kisa kabasa kiturare kayanki . Akwai humra da bazaki sataba sai zaki turaka. Akwai turaran kaya ,na jiki, Dakuma na É—aki. Akwai kwallaca sirri, amma bama badata gaskiya sai ga wanda baida kishiya , Dan muddum kina amfani da ita tofa gabaki dayan hankalin mijinki akanki zai dawo,Dan yana juyo da hankalin namiji akanki baki É—aya ,zaki zama shalele Baby, Akwai sirrin nisaa'i. hmmm Dagajin sunan kason na dabanne,na baki sati É—aya ki gwada ki gani Hajiya ta, tsugunno ake akai ga mai buÆ™ata ya tunÉ“e mu ta wannan layin 08028827241 karku manta UMSAD INCENSE mune na É—aya. Muna aika kayan mu duk inda kuke. Kamshin jiki martaba mutum.... 🅿ï¸4ï¸âƒ£3ï¸âƒ£&4ï¸âƒ£4ï¸âƒ£ """"Kaf!kaf kaf jikin Amnah ya fara rawa . Cikin zaro ido da zallar kishi take kallon Bily tace" kina da hankali kuwa, mijin nawa kikema jajajen na aure miki shi? Bily ta cire siririn mayafinta ta É—aura a kugu tace "Wallahi zanyi dambe dake ,zankuma tona miki asiri ,kana shima in tona nashi, dan bansamu ba keÉ—in banza kice kisamo ki zauna lafiya. Cikin tsananin fushi ya dakamata tsawa tare da nunata da yatsa yace. Matar tawa kike faÉ—ama magana , Banza , Dabba, kiwuce kibani wuri inba hakaba wallahi zanfara ta kanki, shashasha mahaukaciya kawai... Cikin ihu ta fara tsalle- tsalle tare da zaro wayarta ta lallatsa ta kanga a kunne . Tsaye yayi yana kallon mizatayi,bai ankaraba yaji ta sake fashewa da kuka tace "Daddy naga D.... Wani mahaukacin tsalle ya daka ya murÉ—e hannuwanta ,Tare da matse baki ta. Afusace ya É—auki wayar illahirin jikinshi na rawa ya kanga a kunne. Daga cen bangaran yaji murya wani dattijo cikin tashin hankali yake fadin Bily kina lafiya dai ko,waye kika gani? Jajayen lips É—in shi yama wata tauna ta tashin hankali cikin kakkausar murya yace. "Tana hannu, fansar ranta Million É—ari biyu. yana gama faÉ—in haka ya kashe wayar, tare da karance number tass kana ya fasa wayar ya jefata cikin kwalbati, tare da cema Amnah budemun gidan. ya faÉ—a hannushi É—aya na shake da wuyan Bily..... Jikin Amnah ya É—auki rawa tace'' mi..mi zakayi da ita cikin gidan Dee.? Tsawa ya dakamata yana zaro idon shi dake Æ™oÆ™arin yin aman wuta. Yace" kibude Nace". Aguje ta Æ™arasa ta buÉ—e gidan . Yace maza shiga!. Shiga tayi shima yaja Bily keeee har cikin gidan kana yasa kafa ya tura kyauran ya Æ™arbi key ya rufe gidan kana ya saketa. Amnah tayi tsaye wajen pampo idonta na zubar da kwalla tace" Dee dan Allah miye haka, miye AlaÆ™ar ka da bily, miyasa kakeson yin garkuwa da ita, bana son ka É—asama zuciyana zarginka fa... Cikin rawar murya ya hankaÉ—ar da Bily gefe kana ya matso wajen Amnah jiki na rawa, Ido na tsiyayyar da kwallah. Yace "Amnah wannan ita da ahalinta sune silar tarwatsewar farin ciki nah, Amnah bazan taÉ“a yafewa mahaifin yarin yar nan ba,Agabana- agabana fa ........ Ya saki kuka mai cin rai tare da faÉ—awa jikin Amnah yana mai kasa Æ™arasa magana da ya fara... Hankali tashe take Æ™oÆ™arin É—ago kanshi dan ganin da gaske kukan yake ko-ko,Miya faru da rayuwar jarumin mijin nata dake kokarin sashi kuka haka, innalillahi wa inna ilaihi Raji'un. Bily kau dake gefe sai wulwula ido take dan san samun hanyar fita . Amnah ta shafa Bayan shi cikin tattausar murya tace". Duk tsanani yana tare da sauki,Haka kuma mai hakuri yakan dafa dutsi har yasha romansa ya more,Duk kan sadda zuciya zatai nawi innalillahi wa inna ilaihi Raji'un, Hazbunallahu wani imal wakim ,kan sanyayya zuciya da samaka natsuwa ,Kunci, da bakinci, in'suka kawoma rayuwa ziyara maganin su Alkur'ani mai girma,Shin mijina tinda muna dashi acikin gidan nan akan mene zaisaka zubar hawaye. Dan Allah dan Annabi karka É“ata farin cikin da muke murna samuwar shi yau na rokeka,muje muyi Alwallah mukai kukan mu ga Allah,ku mu É—auki Alkur'ani mu karanta musamu saukin zukatan mu... Bily tace" Wallahi Dee zan kashe kaina agidan nan ,Kwara ka buÉ—emun infita cikin salama,ganin ka ahaka kaida kawata kan baÆ™anta raina , tinkamin inyi muku aika- aika ka sakeni in tafi. Cikin sauri ya tashi daga jikin ambah tare da dosar wajen da take cikin sassarfa ya fara wullamata maruka masu masifar zafi. Cikin in ina shi yace" Kika kara magana kina sona wallahi billahi sai na halbi Æ™afarki,Na tsaneki na tsani ahlin ki ,Babu ni babu ku,Tsakanina daku babban yaki ne wanda ko in kashe ko akasheni, kamar yanda Akai ma mahaifina da yar uwata Agaban ido na nima zanyi fiye da haka... Da gudu ya shiga É—akin Amnah ya É—akko jikkar shi baki daya ya fito da ita ya zazzzage. Anan bindigar shi ta fado ya É—auka ya ÆŠuramata bullet tare da gyara wandon shi ya dan nata aljihu baya. Kana ya dakko sistem din shi ya rike ahannu. Wayar shi ya zaro ya fara latsawa, Cikin minti na Æ™alilan yaji an'É—auka. Yace''" Sultan Kazo gidana yanzu, kana kazo da adai-daita sahu zanbaka aiki. Yace ok" Yallabai yana kashe wayar. Kasa ya Zauna ya fara caccaka computer cikin kwarewa . Bily tasa kuka tace "Dan Allah uncle Dee kayi hakuri, kar laifin da banmaka ba ya shafeni wallahi -wallahi ... Tsawa ya dakamata tare da faÉ—in takara magana daya sai yafasa kanta... Amnah kam waje ta samu tayi zaune zuciya ba daÉ—i sai hawaye take, ganin lokaci guda ya canza ya dawomata wanda tasani ranar da ya É—auketa sukayi hanyar Dutsama, ranar daya murje yatsunta da kasa . Sosai yake aiki har yaji wayar shi na ring. Bayan ya É—auka yace ok. tare da mikewa ya fita. Minti kaÉ—an ya dawo gidan tare da dakama Bily tsawa yace ta tashi. Cikin sauri ta mike tana kallon Amnah dake kuka sosai... Yace zaki fita ko bazaki ba. Fita sukayi tare yayin da ya tausa ta cikin motar da tazo da ita. Wani murtukeke kato ya fito tare da sarama Sadeeq yace'' Allah ya huci zuciyar Yallabai Wannan ce.. Sadeeq baice komi ba sai kai da ya É—aga mai ya koma ciki. Bayan yashiga yaga Amnah ta sanya kanta cikin gwiwa tana kuka sosai da tinanin" wata aura.... Ahankali ya isa gareta ya sanya hannuwan shi ya É—agota. Azabure ta mike jikinta na rawa tayi Æ™asa da kanta... Jawota jikin shi yayi yacei" Aminatu fatana ki yarda dani shine Abinda nike fata, wallahi Amnah ni ba abinda kike tinani bane ,bana kisa bana garkuwa da yaran mutane,Damuwar ki zatasa in kasa control É—in kaina. Kimin affuwa dan yanzune lokacin da zaki fara gani canje- canje, amma komi zaki fahimta insha Allah Amnah. Kai ta É—agamai cikin gamsuwa da magana shi. Murya na rawa tace. " Yanzu bazan sake samun kulawa ko sakin fuska daga gareka ba har sai ka kammala aikin ka kenan? Murmushi ya saki yace" Amnah ni kuma in na kuntata rayuwar ki taya zan iya samun damar yin aiki bayan kina cikin damuwa , Tinda bamu gina tubalin rayuwar mu akan haka ba,Amnah matar kirki itace mai Æ™oÆ™arin faranta ran mijinta aduk sadda tagan shi cikin É“acin rai ,dan haka aiki na'gareki ko ki kyaleni cikin damuwa ,ko kuma ki mantar dani.... Aiko kamar jira take cikin kuzari ta mike tare da shagwabe fuska tace'' to ka zare bindigar mana. Hannu shi ya ÆŠagamata "alamar babu".. Wayar ta ta zaro ta haska fuskar shi, taga yanda har lokacin idon shi ke a rikeda har sunÉ—anyi fushi kaÉ—an... Tace" muna tsaka da farin ciki wata banza tazo ta batamuna rai,wallahi nayi dana sanin haÉ—uwa da Bily.. Yace tinda tabar gidan nan hasken Annurin ki ya dusashe duhu data sakarma zuciya na. Amnah na baki muÆ™amin ragamar rayuwata, kisarrafata yanda kike so cikin awa shidda ,kiyi Æ™oÆ™arin dawo da farin cikin damuka wayi gari dashi har zuwa marece..... Sosai take É—agamai kai tanajin gabanta na bugawa, to ita kam mizatamai dan dawo da walwalashi da farin cikin? Ohhh yah Allah, ko in'bashi abinda yake muradi? ina noo ba yanzu ba, kar yamun illah, yana cikin fushi, to Amma asadda yake cikin yanayin nan abinda zanmai kenan ya dawo da walwalar sa saboda shine abinda yake fatan samu ba dare ba Rana..... ÆŠagata yayi daga jikin shi ya nufi hanyar É—aki. Da sauri ta bishi suka isa tare. Suna shiga ta fitar da kunya ta taimaka mai ya cire kayan shi baki É—aya itama ta since nata. Hannu na kyarma ta jefa nata cikin nashi. Ajiyar zuciya ya sauke batare da yace komi ba. Amnah kam ganin cikin duhu ne yasa tace''My love muje muyi wanka ko?ko kanaso na maka. Yace "duk yanda kikace d zanyi biyayya da umarni ki my wife. Tace shikenn muje. Babban towel É—in su dake saman kyauren kofar ta jawo tace "Baby kafini tsawo ka rufamuna mana. . Ƙarba yayi ya maidota gaban shi ya dauro towel É—in ta bayan sa ya sargafo dashi har samar kirjinta. Jin tudun kirjinta ya sashi sauke ajiyar zuciya, tare da tausa hannuwan shi wajen muradin ranshi ya kwantar da kanshi bisa kafaÉ—unta yana sauke ajiyar zuciya da sauri- sauri .. Sannu- Sannu yanayin shi ya fara sauyawa, wanda yasa Amnah zaro ido jin kamar yana turata. Casu jikin ta ya É—auka hakan yasa tace" Baby Dee ko In barmaka wannan towel din naga kamar ya mana kaÉ—an ko?Karya takuraman kai. Um -um yace cikin wata fitinanniyar murya. Ahankali ta fara tafiya yana biye da ita kamar sun hau machine😜 Suna isa toilet ya since musu towel din tare da sargafa shi akan kyauran. Yace" Sweetheart bana ganin kifa ,ya kamata kibamu fitila dan inga kayana da kyau. Amnh tace "wallahi Baby idan da fitila bazan iya ba, inajin kunya. Murmushi ya sai yana mannata cikin kirjinshi. Yace"Amnah ya kamata ace tsawon wata biyu mun rayuwa jin daÉ—i, kinganni na ganki, amma kice wai har yau kunya na kike ji,to kodai dan har yau bakiji na ratsa kiba shiyasa kike haka ko?.. Tace" laaa kadaina Baby haba .. Jawota yayi jikin shi kawai ya sakar musu shower ., Wanka suke sosai yana murzata Tin cikin toilet É—in hankali sa yafara neman gushewa.. Ganin yanda yake yamutsata yana Æ™okarin ratsa jikinta daga tsaye yasa ta saki ihu tana neman guda wa. Da sauri ya cafkota ya rufe kofar yace "kiyi Alwallah Amnah. Tace banayi sallah ba.? Yace" yana da kyau inzaka kwanta kayi alwallah ai. Tace" to duk a tsorace ta fara alwallah . Bayan ta gama shima ya duÆ™a ya tsarkake kanshi kana yayi, yana miÆ™ewa tsaye suna dallo nepa. Tana Ƙallon shi taga yanda yake ta saki ihu ta faÉ—a kanshi. Towel din ya É—akko ya É—oramusu suka fito. fuskar shi na bayyana Annurin, duk damuwar shi kashi 90 ta sauka. Suna shiga É—aki yace" sanya kayan ki muyi sallah. Doguwa riga ta zura. shima yasa jallabiya sukayi sallah. Bayan sungama ya mata tambayoyi akan Addinin ta ta bashi amsa dai-dai. Kai ya jinjina daga nan yace "mukwanta ko ,dan mutashi da wuri. Tace "to tana mikewa tsaye ta isa ga mirro ta É—akko Humra UMSAD INCENSE da bata taba amfani da ita ba ta mulkama jikinta, haÉ—e da bude cinyoyinta ta shafe su tas. Kana ta koma saman mararta ta murje tas. Wani spray ta É—auka na kai ta fesa kana ta zura farar riga Æ™arama, ta isa inda yake tare da kunna fitilar wayar ta , Dan ta kashe glove din ta dallashi da fitila da niyyar tace mai ya tashi ya sanya kaya. Anan ta ganshi kwance Haihuwar gyatima yana kallon saitin da take... Da sauri ta taushe fitila cikin cinyoyinta tace "wai Baby yau miye haka, kana fa sake furgitani. Cikin damuwa yace Amnah ina son kasancewa dake, Dan Allah karki hanani, Amnah gobe zan doshi mahaifata da kudiri biyu,ko indawo a raye, ko in'dawo amace,kibar ni inji ÆŠuminki inda rabo insamu wanda ko bana raye yamun Addu'a,banason kusantar ki batare da izinin kiba,zan miki ahankali ta yanda bazakiji rauni ko zafifa ba, Amnah yanda kike budurwa bakison kowa ba, nima haka nike,kin ga yanda zamu kasance farkon shiga akwai bukatar muduka mu muyi komi A'hankali gudun raunata kan mu. Cikin sanyin jiki da kalaman shi tace" Baby dama ba katsina kake ba? to wane gari kake? Kai tasaye yace" eh Abuja". Ido ta zaro tace" miyakawoka nan.? Yace "Amnah Dan Allah ki daina, kar ki É“atamun farin cikina. Hawayen ta ta share tare dayin jifa da rigarta cikin kwarin gwiwa ta isa gareshi , Bai aune ba sai ji yayi ta hayeshi, cikin rawar murya tace . "gani mijina nazo gareka ka sarrafa akala rayuwata duk kan yanda kake so, indai har hakan zai É—orar da farin cikin ka ... Kamar mayunwacin zaki haka ya mike da sauri tare da mayar da ita Æ™asa ya fara bata wasanni masu masifar zafi. Kimanin awa É—aya suna abu daya duk kansu basa hayyacin su. Amnah sai surutu take tana fadin" karya barta, zata tagayyara ,kayi Baby karka sauka ,Karka fasa ,inka fara karka daina sai mutuwa, ahhh babyyyyyyy taja da karfi cikin gushewar hankali. A'hankali ya fara Addu'a ziyarta wa iyali kana ya saita alkalamin shi a kanta. Ihu ta saki mai haÉ—e da salati tana Æ™oÆ™arin tashi.. Cikin son cimma buri da rawar jiki ya kama hannuwanta ya rike ya saki kuka sosai yana faÉ—in. karki fitar ,karki hana Amnah, wallahi mutuwa zanyi in'kika hanani. Sosai yake Æ™oÆ™arin shigar ta amma ya kasa samun dama. Kuka ya saki sosai tare da danna kanshi jikinta da masifar karfi yana wani irin gilgiza hade da kururuwa kamar wanda yake filin yaÆ™i. Lokaci guda kaji wani futtt kamar anfasa abu. Ihu ta kwallah mai masifar karfi jin ya samata abu kamar rodi cikin jikin ta. Cikin gushewar Hankali da tsunduma sabuwar duniya ya fara sukuwar in'garman Doki a'kanta..... Kuka take sosai tana bashi hakuri, tare da Yakushi amma baison tanayi ba.. Sama -sama takejin magana shi yana faÉ—in. Ki soni ,karki barni,Karki bari in bar zumar ki,kibar ni in shekara ina morewa ta. Duk duniya babu mace tamkar ki. In gaki bana kallon zuma, saboda kinfi zumar zaki, Dan Allah karki barni ,kika barni zanyi hauka ,KarÆ™ata kaf dukiyana Amnah na mallakasu gareki, na baki mukamina da matsayin da ,nike dashi awajen aiki aaaa ,wowwwwww, Amnah so sweet,Daure-Daure Amnah tahhhhhhhhhhhhhhhh. Sosai yake sukuwa a kanta ita kuma tana kuka ,tin tana gane abinda yake faÉ—a har yazo ta kasa koda motsa Æ™afar ta. Kimanin awa biyu yana abu É—aya kana taji ya matse kanta, ya saki wani Gigitaccen ihu yayi flat akanta yana sauke numfashi. Ga bugun zuciyar shi da ha sauya yana fita da masifar Æ™arfi.... Kimanin 10mnt yana kwance kanta kana ya sauka ya kom gefe yana suke wani irin numfashi, cikin lokaci kuma ya saki kuka sosai yana matse marar shi. Amnah kau data rasa gane duniya da take ko ido bata iya buÉ—ewa sosai ,Sama-Sama ta kejin kukan shi. Sai da yayi dan kan shi kana ya murgino gareta . TaÉ“ata yayi yaji ga dai tanan bata ko motsin kirki. Salati ya saki yana mai kunna glove din ÆŠakin... Ido ya zaro ganin ta kwance magashiyan sai sauke numfashi take A'hankali tana raba ido. Da karfi ya gilgizata yana dora kanshi kan tudun kirjinta Yace" Amnah, Matata, DaÉ—i nah , Dan Alla karkimun haka kitashi Amnah muyi murna cikar muradin mu. ya gilgizata da masifar Æ™arfi.. Ajiyar zuciya ta shiga saukewa da karfi kana ta saki kuka tana faÉ—in" Yah Dee ka samun barkono, ina masifar jin zafi, kamun da karfi , Bayan alkawarin dakai, miyasa ka saÉ“a ,miyasa? ina neman agaji ka kasa tallafamun ,miyasa ka kasa cemun baka hakura da abinda namaka shekara É—aya data wuce ba, sai yau zaka fanshe ,Na tabbata kamayar dani gurguwa, bazan sake Tafiya ba. Nason ko fitsari bazan sakeba ,saboda ka Æarani ,Ni nason ma kila na samu yoyon fitsari, haka zan dinga tafiya inayin sa kamar Shanuwa ,wayyo ni Amnah, ashema abin zafine dashi ba daÉ—i ba,Bazan sake yarda kamun ba..... Sosai yakejin kukan ta har cikin ranshi.. ga kanshi dake mai masifar ciwo ,yanajin kamar zayyi zazzaÉ“i. Jawota jikin shi yayi ya fara hura kunnata. Yace" Amnah kowace mace na tabbata miki da hakan ta fara ,indai ta tsare mutuncin kanta. Wallahi Amnah zallah farin ciki da nishaÉ—i, natsuwa ta mussamn cikar kamala duk yau ina jinsu akaina, inajin nakai wani,kusantar ki takaraman Æ™aimi, da karsashin dumfara makiyana ,ba tare da wani lauye -lauye ba. Ya Allah kasani ina son baiwar nan taka mai yawan ibada Allah ka sota,ya Allah ina fatan zaman lafiya azaman takewar mu Allah ka dawwamar muna,Ya Allah kayi alkawarin duk kan macen da tasamu yarda mijinta ta kyautata mishi tamai É—a'a da abinda kayi Umarni Aljannah zata. Ya Allah ga Aminatu baiwarka ,ni mijin Aminatu na É—agamata duka kafafuwana Allah kabata ikon wucewa cikin Aminci. Ya Allah ko a Aljannah kabani Amina ta, Amnah kinmin komi arayuwa, kin mallekini kin mallaki dukkan gangar jiki da ruhina. Tabbas ke ma'ajin sirrinacez kuma da gake an kulle, kece ta farko kece ta karshe. Amnah tinani na BaitaÉ“a bani bayan rasa iyayena akwai wani farin ciki ba sai ayau dana kasance dake,BantaÉ“a tinanin wannan abun mai tsada zan iya bayyana shi ga kowace mace ba har in'koma ga mahallicina sai gaya lokaci ya bayyana shi gareki saboda ke É—in mai sa'ace.. I love You so much My Wife .... Sosai kalaman sa suka mata daÉ—i, hakan yasa tace nagode mijina Allah ya bani ikon biyayya ga umarnin ka, Allah kuma ya cikamaka burin ka na Alkhairi. Goshinta ya sumbata yace Ameen" Sweety tah... Tashi yayi yaje toilet yayi wanka bayan ya dawo ya fara tinanin taya zai gasa ta, tinda babu Kwamin wanka a toilet É—in. Goshin shi ya dafe yace. "Zakiji daÉ—i Minah ta, zakiji daÉ—i sosai insha Allah ,zaki zama abinda Duniya zatai alfahari dake ,kin hakura kinzauna dani ,,kinsoni Ahalin jinya ,kin min É—awainiya alokacin da bani dashi,kin kula dani lokacin da nike buÆ™atar kulawar ki. Nikuma insha Allah zan kare rayuwata wajen kula dake da mahaifanki da duk kan wanda ya shafeki har Æ™arshen numfashina... Kiching ya shiga ya dakko wata babba roba ya zo ya cikata da ruwan daya É—ora a gas ya sirkamata kana ya shiga É—akin ya ganta yanda ya barta. Cikin tausayawa ya É—akkota . Ido ya zaro ganin illahirin wajen da take ya lalace. Da sauri ya ajiyeta gefe jiki na É“ari yace" haka na miki Sweety, sannu dan Allah kiyi hakuri , Wallahi bansani ba, bazan taba burin wani ya cuceki ba balle ni, Amnah ke É—ince ta daban, DaÉ—in ki gigita kwakwal wana yayi wallahi, ko yanzu ina so in.... Da sauri ta kalleshi tana zaro ido. Ido ya kashemata yana sungumata. Saida ya tabbatar daya gasata sosai tana tamai shagwaba, kana ya dawo da ita É—akin ya yaye zanan katifar ya fita dashi ya jika aroba kana yayi wanka yazo ya rungumeta ,a haka bacci ya kwashe su... Washe gari tinda Asuba ya tashi yana ta zuba murmushi fuskar shi fal da fara'a yace" Honey Tah.. Ido ta zaro tace "yau kuma sunan da nasamu kenan?. Yace yees ke dince kin zama zumata wadda nike fatan inta lasar ta har Æ™arshen numfashi... Murmushi tayi kawai tana kallon shi . Yace tashi kimun Tatata inga in da sauki ,inkuma sai A'hankali muje Asibiti. A'hankali ta yinkura tare da cemai zan iya My love, mazane kawai naji, amma kwana biyu zan koma dai- dai ,zan kula da kaina Insha Allah. Kanta ya shafa yace" Masha Allah sweety nah ALLAH yabar mu tare. Tace" Ameen Baby. Bacci suka koma sai goma na safe ya tashi. yana tashi ya sake sungumar ta ya gasata sosai kana ya maidota d ÆŠaki. Bayan ya mai dota yaje yayi wanka ya haÉ—a musu tea suka sha suka koshi ko bread babu. Zama yayi kusa da ita yana jawota jikinshi Yace" Matata zanyi tafiya,inaso kimin Addu'a nasara,Daga karshe kuma karki manta dani Dan Allah, Amnah ki kulamun da kanki, Na baki Amanar kanki data Baby nah in ALLAH ya bamu rabo,Ki zamema su Ammi garkuwa da zata maye gurbina kinji ,na so mallakarki tin kamin wannan ranar dan zama inyi jinyar É“arnar danayi,to amma nayi alkawrin duk ranar dawani nawa ya son muhallina ko inda nike to ya zama dole indoshi Kasata. Da a iskeni kwara in iske ... Hawayenta ta share tace" taya zan iya kwana babu kai,bani da fili sai hannuka ,Kirjinka shine katifana,taya zaka barni adaidai lokacin da muka zama abu daya muke buÆ™atar zama Æ™alÆ™ashin inuwa É—aya? Yace na sani Amnah nima bawai tabbacin bazan dawo gareki ne bani dashi ba a'a kawai dai .. Tace kawai mi ,wallahi ni bazan iya zama ni É—aya ba. Yace shikenan tashi muje gidan Ammi. Cikin kuka tace yanzu yau rabuwa zamuyi?... Yace ganga jikin ce kawai zasu rabu Amma ruhin da zuciyar a'tare Allah ya halicce su kinji. Kai ta É—agamai ya É—akko mata wata riga milk ya bata ta sha,tare da bata maroom din hijjob tasa. Kana ya miÆ™ar da ita tare da sata cikin kirjin shi haka ya rufe É—akin. A'hankali take takawa har suka fito soron gidan. Anan ya É—akko Æ™aramar kujera yace "ta zauna yana zuwa, zai tsaido Napep. Kai ta É—agamai tana sakin kuka sosai tare da lallatsa wayar ta. Kangawa tayi taji bata shiga kamar ma layin Æ™asa yake. Tsaki ta saki, ta sake kiran wani. Sai ga murya Nene RaÉ—au tana faÉ—in" ja'ira kinji uwarki tazo shine harda mun waya ko... Cikin rauni batare da ta fahimci mitace ba tasa kuka tace" Nene wai kinga zai koma mahaifar sa zai barni , Dan Allah Nene kice yaje dani, wallahi bazan iya rayuwa ko kwana babu shiba,kana Nene ina tsoron wani abu ya sameshi, Nene zuciya na bazata jure ba.. Da sauri ya shigo ya tallabota ita kuma wayar na akunnata tanajin Nene na salati. Kuka ta sake sawa tac"e yanzu gida Ammi zamuje Nene. Nene tace to" muhaÉ—u cen mu duka ta kashe wayar. Tsaye yayi yace" Amnah bazaki daina kuka ba, bakyaso inyi abunda ya kaini. kedawa ke waya.? Tace Nene ce mana . Murmushi yayi kawai ya sata a Napep din tare da jawota jiki , kana yaci gaba dalallashi har suka isa gidan Ammi. Anan sukaga motoci manya -manya sun kai guda goma, wayanda ke cike da Sodoji ko wanne na rike da bindiga suna mazurai, fuskar nan babu rahma ga unguwar ta cika da mutane sunata kllonsu . Azabure tace Baby miyafaru Dan Allah, mi akayi naga sodoji kofar gidan Ammi?. Murmushi yayi yace lafiya Æ™alau my wife. Sauka sukayi suka sallami mai Napep da jikin shi keta rawa. Sadeeq ya fito hannu shi rike da Amnah, yana mai sake rungumeta cikin jikin shi. Ganin sun doshi inda suke wani soja É—aya ya ganshi hakan yasa da sauri ya É—akko wata sarewa ya fara busa mai daÉ—i. Hakan yasa suka fara É—irkowa daga kan mota jif -jif suna jera layi gwanain sha'awa. Da sauri wani babban mutum ya fito daga gaban mota fuskar shi cike da Annuri. Sadeeq na ganin shi ya É—aga hannuwan shi guda ya saramai tare da sadda kanshi Æ™asa.... Da sauri mutumin ya Æ™arasa wajenshi cikin tsananin farin ciki yace" Conal ya dawo bakin aiki, Alhamdulillah Gwarzo mu, jajir taccen jarumin mu yau Allah ya haÉ—amu dashi... Sadeeq ya É—ago kai yace" Yallabai ga matata . A'hankali Amnah da mamaki keson kasheta tace . Good Morning sir. Cikin farin ciki suka gaisa ya mikama Sadeeq wata leda tare da faÉ—in zamuje Ran gadi mudawo, munbaka awa biyu kamun mu wuce. Yace tnx u sir... Matsawa yayi inda sauran suke fuskar shi da sassanya murmushi ya É—aga musu hannu. Ji kake taf -taf suna sarawa tare da doka kafafuwan su Æ™asa. Daganan busa ta tashi ta murna dawowa shi bakin aiki...... 5/23/22, 10:31 - MY MTN 2: *Littafin🌹DAN DAKO🌹 na kudi ne biya ki karanta cikin Aminci. Biya 300kacal to 0006454115 Amina Dahiru jaiz bank,or MTN card to this number 09165832002. then send the evidence of payment via 07038423451* ðŸ¤ðŸ™ðŸ¤² Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Yan uwana mata ina kuke ku malmatso ga wanni sirri da nike son baku, ita ya mace sai da kamshi, ina macen da take ganin izgili da wulakanci da ake cewa maza nada shi, hmmm yar uwa to inkin kasance a haka da alama akwai ayar tambaya akanki. Tambaya ta ta farko gareki da wane irin turare kike amfani a jikin ki ?,da wane irin turare kike turara gidan ki,shin dawane irin turare kike Zukunni, hmmm to matso kusa kiji yar uwata. Shi kamshi Annabi muma ya faÉ—a abin sone,kuma Abune mai sanya natsuwa da girmama ma'aboci shi , Da Yawon son kusantar sa. Duk kan wulakanci da izgilanci na maza akwai turaran da zai miki maganin sa da izinin Allah,ba boka ba malam,wanda zai karkato da hankalin mijinki akan ki ku samu fahimtar juna. Ko kin son kamshi na dakusar da fitinar É—a namiji yar uwa? kigarzayo ki kwashi rabonki ga shaharariyar yar mai Dugurin nan mai suna UMSAD INCENSE ,Mace mai kishin mata da son Fiddo martaba mu. Nayi Amfani da turaranta naji masifar daÉ—in da yasa nakasa barwa raina. Nace bari in yaÉ—amuku dan kowa ya mallaki nashi cikin farashi mai sauki. Da fari bari in zayyano muku su kamar haka.👇 Maleek Al'oud Royal kush Cous-cous Kajiji Original sandal Sandal flex Sandal bange VIP mix Hawi Al'oud Kindikay Danal banat Darot Habil Gaf-Gaf Sirrun nisaa'i Sandal chips Kwalacca Humra black and body milk Attractive humra. Yar uwa zanmiki Dallah- Dallah. Akwai turaran da zaki sanyama kayanki . Misali! kisa kabasa kiturare kayanki . Akwai humra da bazaki sataba sai zaki turaka. Akwai turaran kaya ,na jiki, Dakuma na É—aki. Akwai kwallaca sirri, amma bama badata gaskiya sai ga wanda baida kishiya , Dan muddum kina amfani da ita tofa gabaki dayan hankalin mijinki akanki zai dawo,Dan yana juyo da hankalin namiji akanki baki É—aya ,zaki zama shalele Baby, Akwai sirrin nisaa'i. hmmm Dagajin sunan kason na dabanne,na baki sati É—aya ki gwada ki gani Hajiya ta, tsugunno ake akai ga mai buÆ™ata ya tunÉ“e mu ta wannan layin 08028827241 karku manta UMSAD INCENSE mune na É—aya. Muna aika kayan mu duk inda kuke. Kamshin jiki martaba mutum.... 🅿ï¸4ï¸âƒ£5ï¸âƒ£&5ï¸âƒ£6ï¸âƒ£ """Sunkai 10mnt kana suka fara sara mai suna juyawa cikin tsari suka shiga mitocin su suka tafi.. Amnah kau sai lafeeay take cikin jikin shi dan mamaki abinda ta gani. Motocin na karya kwana motar su Nene na shigowa layin. Yayin da Abbah ke tukin motar Mamy kusa dashi, Nene da Amal a baya... Afurgice Nene tace "kai Isa minene haka ake cikin wannna unguwar, ko kisa akai?.. Abba shima cikin mamaki yace" A'a Hajiya bana tinani nima bansani ba gaskiya. Suna isa kofar gidan amymi sukaga Amnah da Sadeeq tsaye yana mata magana. Cikin farin ciki Amal ta bude kofar ta fito ,tana isowa wajen Amnah da gudu ta faÉ—a kanta .. Da sauri Sadeeq ya tallabota yana kallon Amal yace "Sst bata da lafiya fa, Kimin A'hankali da ita. Asukwane Amal tayi baya tana sake kallon Amnah data lafe jikin shi. tace''" Aunty Amnah baki da karfi jikine, kuma bakya nurna dawowa na ko? Amnah tayi murmushi tana mai jawo hannu Amal tace "A'a Amal ina murna dawowar ki sosai. Su Abba da ma6my suka fito motar su duka ido suka zubamusu, dan sun masifar dace da juna, daka gansu kason akwai shakuwa da soyayya mai girma a tsakanin su... Ahankali Amnah ta zame daga gare shi ta nufi wajen Mamy tana tafiya A'hankali ta faÉ—a jikinta, kana ta juyo ga Abbah. Haka nan taji tanajin kunyar rungumar shi kamar yanda suka saba, da kyal ta É—an sunkuya ta gaida shi. Da sauri yace" tashi Amnah basai kin duÆ™a ba muje ciki. Ahankali ta mike tana tafiya tana cije baki... Nene kam ta kasa motsi sai kallon Amnah take har saida Mamy tace muje ciki ko Hajiya Nene. Kana Nene tace" to" ta rufe motar. Sadeeq kam sosai yakejin kunyar su, haka nan yake musu sannu da dawowa kai a Æ™asa. Da sallama suka fara shiga gidan inda sukaga Ammi zaune cikin shiga ta kamala fuskar ta cike da Annuri. Da sallama suka shiga ta tashi ta É—akko musu tabarma babba ta shimfidamu su, Dan babu wuta kuma É—akin akwai zafi... Su duka suka zauna aka shiga gaisawa... Nene kam hankalinta naga Amnah ta naso tayi magan tanakuma jin nawin sirikinta... Ammi tace" Nene ina fatan jikan naki yaje miki sallama yau zaije Abuja? ... Nene tace "ya za'ayi yaje Maryama baccin naga yana ta tarbo Amnah, kila cinyoyinta ke ciwo ko. Hala sune suka hanaka zuwa ko kwandon sukari na sani.... Ƙasa yayi da kan shi yana doka Murmushi. Duk kansu babu wanda ya fahimci zancen ta ,sai shi da Amnah. Wayar shi ta shiga ring da sauri ya tashi ya tura É—akin da yake ya shiga ya rufe. Yana gama wayar ya dauki ledar da ogan shi ya bashi ya zazzage. Sabbin kaya ne na Kakin soja. Kallon kayan yayi sosai tare da rungumesu ya fashe da kuka sosai yana faÉ—in "Allah sarki Abba nahhhhh. Saida ya gaji dan Æ™anshi kana ya sanya su jikin shi, Ya dakko bindiga Æ™arama ya soka ga aljihunshi na gaba, ba tare daya sanya hular ba ya isa ga madubi. . Masha Allah ya furta shi da kanshi, Dan ganin yanda kayan suka masifar yi mishi kyau, suka fiddo da kwarjinin sa suka haska farar fatar shi. Tattausan sajen shi ya shafa yana sakin murmushi , tinowa da daransu na jiya. "A'hankali yace" ka É“arani, ka samun barkono,Ashema babu daÉ—i sai masifar zafiiiiii.... Idon shi dake lumshe ya bude ya zubasu ga madubi,inda yaga lokaci guda har sun canza launi. Da sauri ya fesa turare kana ya fito .. Kamin kowa ya mike Nene ta mike tana zuba salati ta shige kiching É—in su tare da maida Æ™ofar ta rufe, jikinta na É—aukar rawa.... Amnah kam tsaye ta mike ta zubamai ido, yayin da shima ita yake kallo cikin so da Æ™auna ya ware mata hannayen shi. Cikin sassarfa ta isa gareshi ta faÉ—a cikin jikinshi tare da sakin kuka. A'Hankali yake murza bayanta yana ambata sorry ,sorry my life ,am so sorry kinji Sweety... Mamy, Amal, Abbah, ga baki É—aya tsaye suka mike suna kallon shi cikin tsananin mamaki. Ammi kam sai cewa take masha Allahu. Alhamdulillah! Alhamdulillah!!!.... Daga cikin kiching suka farajin wani irin bugu kamar ana fasa bango. Da Sauri Sadeeq ya zaunar da Amnah cikin natsuwa, kana cikin sauri yayi wajen yace" Nainah ki fito mana nine fa... Kuka tasaki tace" wallahi bazan fito ba, bango zan huda infita, ka cuceni, ashe kason kai É—an Sanda ne kake zama dani, bayan kason ina tsoron ku, Wallahi Kwandon Sukari babu ni babu ku, kuma sai ka saki jikata. ta kara dan nama wajen turmi ita da tsiya dashi zatayi Æ™ofar da zata fita. Da sauri ya leÆ™a ta window yaga sai zufa take zanan ta na gefe daga ita sai ÆŠan kamfai.. Da sauri ya ja baya tare da banka kofar da kafa É—aya take ta buÉ—e . Ihu Nene ta daka da sauri yayi wajen ta yana mai riko hannuta yace "Dan Allah Nainah ki natsu nine fa. Ammi tazo ta kama hannuwanta tace" Nene ku zauna inbaku tarihin rayuwar mu ,a gulgije dan Sadeeq yanzu zai tafi gida. Gabaki É—aya suka zauna suka zubamata ido. Shikam Sadeeq gefe ya zauna yana jawo Amnah jikin shi ya rike hannuwata yana É—an murzawa kaÉ—an. Ammi tace. ""Kamar yanda kuka sani ni sunana Maryam haifafiyar garin sudan ce,Acen nayi karatuna har nataka matsayin babba likita, Mun haÉ—u da mahaifin Sadeeq a Æ™asar mu da yaje sarin kaya, daga nan shaÆ™uwa ta shiga tsakanin mu har iyaye suka shiga tsakani, daga nan aka bashi ni ya kawoni Gidan shi dake Abuja. Su ukku ne agidan su,akwai Musbahu shine babba Æ´aÆ´an shi, Sai Sadeeq kana Jidda autar su. Na iske Musbahu da sabuwar Amaryar sa mai suna Rabi'a... Cikin ikon Allah muka fara zaman lafiya dasu kasancewar muduka gida daya muke harda iyayen su, sai dai kowanne da part in'sa, sai kaso zakaje inda wani yake. Soyayya da Æ™auna zalla ina ganin wajen mijina, kullum fatan shi in zayyi tafiya ya sani gaba muje duk inda zaya,Saboda ya hanani aiki,Yason ni Æ™adai zan zauna,gashi babu dangi,Dama mahaifiyata ta rasu kuma ni Æ™adai Allah ya basu. Kimanin shekara É—aya da Auran mu amma babu ciki babu alamun shi , Hasalima ko É“atan wata bantaba yi ba. Daga nan ne Mahaifiyar Sadeeq mai suna Hajiya Suwaiba na É—an fara ganin canjin fuska daga Gare ta. Akwai wata tafiya daya shirya muna zuwa Dubai, yaje gaidata da daddare shine take cewa. "Ta fara nunama sa in'zaya waje wurin aikin sa dole ne sai yatafi dani, kamar inya barni cikin su zasuman wani abu , Bayan ga matar É—an uwan shi nan shima ai yana tafiya ko sai shi na Mamajo mayen Juyar macen da bata haihuwa .. Kai ya gilgizamata tare da bata hakuri akan bazai sake ba. Asanyaye ya dawo da jikinsa part É—ina" yace mun tafiyar da zamuyi inyi hakuri in zauna yaje ya dawo.. Kuka nasa mai dan baitaÉ“amun haka ba , Anan yake faÉ—amun Umma su ce batajin daÉ—i, tana ganin kamar bai yarda dasu bane. Bani da yanda zanyi haka na hakura inaji ina gani yayi tafiyar sa. Alokacinne kuma matar dan uwanshi Musbahu dake da yaro dan kimanin wata hudu na fara ganin canji daga gareta , Saboda ko yaron ta nazo É—auka zata dauke abinta tana nunaman bazata bada ba, inyi zuciya in haihu amma na tsaya soyayya da miji. Banacemata komi saboda ba tashin hankali nike so ba .. Tafiyar nan da yayi saida naji dama Mahaifana kusa suke, inkoma garesu saboda zama nike cikin kunci da baÆ™in ciki ,som abinda basamun suka Fara mun, Duk inda naje Hantarata suke, har Umma su da batamun haka. Alokacin ne kuma yayi daÉ—ewar da bai taÉ“ayi ba, Dan saida ya kwashe wata ukku kamin ya dawo. Zo kaga murna da farin ciki ranar da ya zo gida. Aranar ne kuma nasha mamaki, dan umma da matar Musbahu sukaita lallaÉ“ani suna tarairaya tare da nuna mai kewarsa tasa duk na rame ko abinci banaci. Murmushi yayi yana mai sunkuyar da kanshi dan Sadeeq akwai kunya. Bayan mundawo party in mu Yake cemun" mike damuna ,in faÉ—amasa gaskiya ko akwai damuwa?. Kai na gilgiza mai ina faÉ—in duk kewar sace. Atakaice dai haka muka fara sabuwar rayuwa cikin jin daÉ—i, koda wane lokaci muna tare bai taÉ“aman zancen rashin haihuwa na na damun sa ba. Kwatsam Allah maji rokon bawa ya bani ciki wanda bana laulayi, ni kaina banson da shi ba sai da yakai wata huÉ—u na fara jin motsi . Alokacin ne na fad'amai mukaje Asibiti aka tabbatar mun da ciki ne da ni wata huÉ—u. Zo kaga murna wajen mu, anan na nemi alfarma da kar kowa ya sani ina jin kunya. Ya amince mun dan yanason abin da nike so. Haka naita rayuwata da ciki na babu mai zuwa part É—ina nima bana fita sai da daddare in'zuba doguwar hijjob inje gaida Umma sa , Dan mahaifin shi ba mazauni bane... Ciki na nada wata takwas naje gaida Umma. Sadda na mike zan dawo naji ta kurma ihu da salati tana faÉ—in mi zata gani haka?. Cikin jin kunya nayi saurin fitowa bansake komawa part din ta ba dan naji kunya sosai .... Ashe takaici da bakin ciki suka cika zuciyar ta, wanda hakan yasa har jinya tayi. Ciki na nada wata tara na haifo yarona santalele mai masifar kyau ,da yayi kyau na dana mahaifin shi , Dan som mahaifin shi baikama da yan uwanshi ,dan yafi su ke sosai yafi kala da buzaye ko fulani...... Ahaka muketa rayuwa da yaron mu mai shiga rai, wanda tinda na haifeshi na matsama mahaifinshi akan ya sa mai Sadeeq . Yace shi Sadeeq, Baby shi Sadeeq, abun yayi yawa. Nace aini naga ranar sadeeq ya samai ina so . Haka kau ya samai ,anan ma saida umma ta tada hankalin sa ... Bayan Shekara hudu Allah ya sake bani wani cikin, a nan na haifo ya mace mai kyau sosai kamar Dee. Ranar suna aka samata Halimatu muna kiranta da Sady. Haka na kammala Yarana biyu inata ji da su, Daga nan kuma haihuwar ta tsayamun cak, babu wanda ya damu Acikin mu ,tinda munhaÉ—a jinsu biyu da muke fatan Allah yasa musu Albarka... A É“angaran Umma kuwa bata kaunar yarana Som, tafison Ƙaseem da Æ™anwar sa dake zanan goyo mai suna Bilkisu suna cemata Bily,.... Duk ranar da tsautsayi ya fidda Sadeeq ko Sady Tofa sai sunshigo da kuka, Dan Umma duka take musu bana wasa ba. A haka muketa taÆ™arÆ™ara rayuwar ,in mijina na nan munajin daÉ—i, in kai baya nan sai azaba, da wahala. Sadeeq nada shekara goma mahaifin su Abban su ya rasu. Munyi kukan rashin sa dan mutumin kirki ne. Bayan Sadaka Bakwai da rasuwar sa Akazo zancen rabon gado . "Tofa anan ake yinta.'' Bayan lauyoyin sa sun bada duk kan wani Ƙundun kaddarasa zasu fara bayani. Umma ta fara magana cikin fushi tace" to ranar wanka ba a'boyen cibiya. Mai haÉ—awa dai yanzu ta raba, Dan haka kai Sadeeq dama bani na haifeka ba ga yara na nan daga Musbahu sai Jidda, Dan haka maza tashi ka tattara tsummanka ka tafi neman yan uwa da abokan arziki , Dan nikam ko kaÉ—an banson waye kai ba, na dai raine ka ne dan daraja mijina, yanzu kuma baya nan sai ka tashi ka kama gaban ka, abar yan gida Æ™aÉ—ai suyi magana..... Arazane ya tashi tsaye inda muma mu duka muka tashi muna kallonta, Dan munji maganar kamar saukar aradu. Tace kwaraiko maza ka ficcemuna daga gida. Dariya sosai Musbahu keyi yana nuna Sadeeq da yatsa yace" Wato anyi luf akwashi dukiya aÆ™ara cikin wadda ake kwamushewa ko ,to ita kanta duk muna nan zamu kwace babu kai babu ita... Hawaye Sadeeq ya fara yace" Umma to waye ni? kuma ina kuka samoni?.. Tace" A kano muka sameka, kana Tafiya tabbacin baccewa kayi, kana kuka Alokacin bakafi sheara biyu ba aduniya. Amma Allah ya baka bakin iya faÉ—in Sadeeq, Saudat ,sune kawai abinda ka iya ,in ance yasunan ka kace Sadeeq Saudat... Azabure Nene ta tashi jikinta na rawa tace'' kikace a kano aka tsince shi? Innalillahi wa inna ilaihi Raji'un ,wallahi billahi É—ana ne , Dan girman Allah ku kaini inganshi na shig ukku, dama Sadeeq ina yana Abuja, yanzu wanna dama jikanane , Ni nason ba banzaba nikejin Sadeeq a raina wallahi,ashe jika nane, ga yar uwar sanan itace Saudat É—in, Dan Allah kutashi mutafi..... Kuka Ammi da sadeeq suka sanya a tare sukace Musbahu ya kashe shi.. Ihu nenyw ta kwallah sai gata Æ™asa a sume Azabure Sadeeq ya É—akko ruwa ya yayyafamata ta tashi tana sauke Ajiyar zuciya tace . Maryam sun kashemun yaro, minene ya musa? Ammi tace'' Nene bayan sungama rabon gado muna gefe muda Sadeeq muna kuka. Sai lauyan ya buÉ—e wani shafi yace to" Alhamdulillah Alhaji ya bar wasiyya, kuma dasa hannu yace" Duka dukiyar shi dake hannu sadeeq ya bar masa ita halak malak yaci gaba da juyata. Kamin mu an'kara Umma ta faÉ—o daga kan kujera. faÉ—owar da tayi silar shanyewar É“arin jikinta.. Bayan anje Asibiti aka tabbatar musu da abinda ya faru yasa ta kamu da ciwon shanyewar É“argo. Anan Musbahu yama Sadeeq kallon tsana yace" wallahi tallahi saika sani, kuma saika maidomana dukiya mu. Afusace ya ja Bily dake hannu shi tana kuka tana kallon sadeeq tana faÉ—in banzuwa wajen mijina zan zauna dan tana son Dee dan ma iyayen su basa barin su shigowa part É—in mu. Sadeeq baice komi ba sai gida da muka dawo ya fara haÉ—amana kayan mu, anan muka kwashe komi. Washe gari da safe muka doshi wani tamfatsetsen gida Dani kaina banson yana gina shi ba,Zagaye yake da ma'aikata maza masu yawa. Bayan munje muka iske komi Ashirye, anan yake shedaman nashine daya gina, dan haka muyi zaman mu a ciki babu wansa ya son dashi... A'hankali Muke sabuwar rayuwar Mu cikin farin ciki da jin daÉ—i da walwala, har muka samu shekara biyar Biyar a ciki, Alokacin Sadeeq nada shekara Ashirin, inda ya matsama uban akan ya kaishi aikin soja ,Dan shi soja zaizama fatan shi kenan.. Kasancewar shi mai son cika muradin yaran shi yasa yamai hanya har aka samu.. Dee Na Tafiya da wata biyu wata rana Abban su yazo gida a gigice ,ya fara haÉ—a wasu takaddun tare da kuÉ—aÉ—e masu yawa ya É—aga kason gado na ,anan naga wata Æ™oface karama da ba kowa yason da ita ba, anan ya fara tura duk kan Ƙadda rasa.. Kamar zan mai magana na kyale, saida aka samu kusan wata daya kana Yake faÉ—aman shima yana ganin rayuwar shi tazo karshe, Dan bilhakki Musbahu ranshi yake nema , Bayan fadamai maganganu da yayi, da kuma turowa da yake ana bibiyar sa basu mai ba . ya fahimci yana so yaga ya tagayyara .. Jikina yayi sanyi Anan nabashi kwarin gwiwa akan babu wanda ya isa ya masa wani abu.... Bayan shekara 3. Sadeeq ne ya mana Dirar Bazata, inda yake sanye cikin kayansu na Sodoji yayi kyau sosai ,ya Æ™ara zama namiji Saboda illahirin jikinshi abuÉ—e yake, Dama gashi da, tsawo da kuma kwari kamar kirar Baban sa. Anan mukaita murna inda Sady taita haba-haba dashi. Cikin zaulaya take fadamai tayi saurayi wanda mu kanmu bamu sani ba. Cikin muskilancin shi ya jinjin mata kai tare da faÉ—in" zaigan shi.. Dariya tayi tace mai kamar wani babba. Kanta ya dungure yana tashi ya shiga É—akin shi, Anan Abban shi ya bishi suka fara tattauna magana, wadda ni kaina banson mi suka faÉ—a ba. Washe gari muna zaune mukaji sallama ta Ƙaseem da Bily da Alhaji Musbahu. Kujera ya samu ya zauna yana zaro jajayen idanuwan shi rai a É“ace yace "ka gama guje- gujen? gani gaka yau a tsakiyar Katafaran Palon ka, Dan haka bani kuÉ—unmu kawai ... Abba Sadeeq yace'' gaskiya tinda bani na roka ba aka bani bazan maidosu ba Yaya ,kayi hakuri kata shi ka tafi... Afusace ya mike yana faÉ—in na baka kwana ukku, in ka bada katafiyar da rayuwar ka dai -dai, in'kuma ka Æ™iya to anan zakayi bankwana da duniya baki É—aya.. Azabure Dee ya mike cikin tsananin fushi yana fiddo bindiga yace" ka sake gayama mahaifina magana sai na fasa koÆ™on kanka, ware nace kaida kutaren yaranka ya fada cikin ihu da motsuwar Allura su ta sodoji... Mahaifinshi bai tsaya komi ba ya fara yanka mai mari akan ya faÉ—ama dan uwan shi magana. Alhaji Musbahu kau Kwafa yayi ya tafi yana mai jan hannu Bily dake kuka tana fadin ita bazataba tana son Uncle Dee shine mijinta .. Saida Musbahu ya kwadamata mari kana ta bishi suka tafi. Anan nake cema Abban su ya bashi kuÉ—aÉ—an muzauna da rawayuwa mu lafiya. Murmushi yayi Yace bazai bada ba, in kyale su kawai... Haka muke ta zama AÉ—arare har kwana ukku , akayi sat,i har sati na biyu ya shiga, Aranar da DEE ke shirin komawa bakin aikin su dan hutun su ya kare har ya fita ya dawo yace" ya fasa tafiya sai washe gari da safe, Dan Saurayin Sady yace zaizo su gaisa . Dariya mukai tamai muna jinjina son girma da gabata irin nasa. Kimanin biyu da rabi na dare muna kwance É—aki muka fara jin kamar motsi. Da sauri na mike daga É—akin Abbah da nike na leka window, anan naga wasu mutane sunkai su hamsin palon mu sanye da bakaken kaya. Agigice na buÉ—e kofar dazan iya ganin harabar gidan. Anan naga ma'aikatan mu duk kwankwance Æ™asa kamar sun mutu.... Kyarma jikina ya É—auka da kyal na tada Abban Sadeeq nace" ya tashi ga É“arayi nan.. Murmushi kawai yayi yana kallona, idon shi na zubar da hawaye yace" muyi maza mukira su Sady suzo, akwai kofar sirri tanan ciki muÉ“uya ko mu gudu. Azabure na kalle shi nace" kaifa?... Yace" in baiga na barmishi duniyar ba duk inda zani zai bini maryam.. Kuka nasa na faÉ—a kanshi, ina faÉ—in karyamun haka mana, ya son muna da bukatar shi A rayuwa bamu da kowa sai shi.. Murmushi yayi ya buÉ—e Æ™ofar, dai-dai lokacin da wani murtukeken kato ya banko kofar ya shigo, tare da É—ora mai bindiga akai yace" muje palo.. Cikin rawar jiki muka fita palo, anan naga sun fito da Sady sun kwantar da ita. Cikin kuka na Æ™arasa inda take na É—agota naga jikinta sai rawa yake tana kuka.... Dee ne ya fito da wani kato yasamai bindiga akai, ya taso keyar sa gaba. Suna isowa ogan su ya dakamai tsawa da umarnin ya sauke bindigar shi ko ya halbi iyayen shi, ganin da gaske zai iya abinda yace yasa ya sauke jiki shi na É“ari zuciyar sa ta motsa,Cikin bakin ciki yake bin iyayen nashi da kallo da aka zagaye su gashi babu damar yayi wani abu. Kason kujer ogan ya Wullah bindigar Dee tare da nuna Abban Sadeeq da ita yace bamu kaddarori ko ranka. Abba zai magana Nace" wallahi nason inda suke, aje ÆŠaki na aÉ—aukko suna kason gado.. Tana gama faÉ—an haka suka tada mutum biyu, anan sukaje sai gasu da kaya niki -niki suna nishi... Kuka Abban su yasa yace" inaji ina gani rayuwar ku zata tagayyara . Kamin ya rufe baki wani ya É—auke shi da mari. Sanadin hakan ne yasa zuciyar sadeeq motsawa yayi tsalle ya fara Dukansu da hannu yana fatan yayi magana amma ya kasa,Saboda Dee Nah tsananin É“acin Rai kan sashi in ina ya kasa magana in yana cikin fushi. Bindiga suka dora akan Sady, Nace ma Dee yayi hakuri ya daina karsu kasheman miji. kana y zauna yana numfashi sama- sama... Waya É—aya Ya É—auka yana faÉ—in "komi ya kammala.. Munajin murya Musbahu na dariya sosai yace" to ku karshi, kamin ya Wullah kuma kumai abinda zuciyar sa zata buga, yaji bakin cikin danaji da yayi ta wahalar mun da Rayuwa .... Cikin dariya iskanci suka amsa suna kashe wayar. Wata Æ™atuwar igiya ya tillama wani dake kusa da Dee,cikin shammata suka kamashi kuson su ashirin suka fara daureshi kamar goro. Sai da sukamai É—aurin da ko motsi bayayi sosai. Abban shi damu muna ta kuka. Dariya suka sanya tare da daure hannu na dana Abban su wajen guda. Kana sukazo suka ja sady da karfi suka fara since mata kaya. Kuka su Ammi keyi sosai tana ganin kamar lokacin abun ke faruwa. Gabaki É—ayan su suma kukan suka sa, sai Abba Amnah ne kawai ke hawaye..... Dakyal taci gaba tace" A gaban idona da mahaifinta da É—an uwanta suka mata tsirara kana É—aya ya maidota gaban mu Agabana yama É—iyata fyade, Agabana Mutum ashirin yama Sady fyade, hakan bai masuba suna ganin tana numfashi sama -sama amma suka É—auki bindiga suka Halbeta a'ciki ,kamin mu an'kara sun halbi Abban su akai take ya faÉ—i shikenan... Daga nan ne banson minene ya sake faruwa ba, nadai ganni wani dan karamin É—aki nida Sadeeq yana gefe yana kuka.... Cikin kuka da tashin hankali nike kallon Sadeeq ina tambayar shi ina suke ,in mafalki Nike ya ta dani, ina ahlina, Dan Allah karya tabbatar mun da mafalkina.... Kuka yasa yana mai sake bani hakuri tare da faÉ—in"Ammi sun kashemana farin cikin mu, bamu da kowa bamu da komi, Mamy yau kwanan mu bakwai kauyen nan, bayan sun kashe Abba sukaman wata Allura ni dake kana suka barmu. Sai washe gari da yamma Na falka, bayan gawar Abba data Sady har sunfara canzawa,.... Da yan kuÉ—aÉ—ena na samu wata mota ta kawomu kauyen nan aka musu sallah aka binne su,Saboda koda na tashi banga wani ma'aikaci ko É—aya ba gidan mu wanda zai kama man,Gashi ke kuma har lokacin baki dawo hayyacinki ba. Cikin kuka yace"Ammi mun rasasu, suna cen gidan su na gaskiya. Cikin kuka sosai Nace "to miyasanya ka kawomu nan.? Tace fansar ran Abba da Sady zan ÆŠauka, kema bana fatan a sake kashemin ke shiyass na É“oye ki nan inda babu wanda zai sani. Kuka nayi sosai daga nan na fara kwarara amai baji ba gani. Wata matace sanye da kayan buzaye ta shigo cikin É—akin, ganina zaune yasa ta rug da gudu sai gashi ta shigo da wani Dattijo.... Bayan ya mun ya jiki kana ya jiÆ™a magani a kwarya ya bani, sukamuna sannu suka tafi. A takaice wata biyu na samu wannan kauyen dagani sai Sadeeq muke rayuwa bama cin wani abun kirki saboda damuwa . Akuma lokacin ne muka fahimci ciki ne jikina, wanda nake Tinanin ya kai wata biyar. Bani da abin so da Æ™auna sama da cikin nan . Lokacin daya cika wata tara Sadeeq ya zauna gabana yana kuka tare da faÉ—in dole muje gidan mu, akwai sakon da Abban sa ya bashi. Nace mai bazanje ba babu ni babu gidan.. Anan yake nausar dani fa'idar zuwan saboda akwai kudade da kaddarorinsa dan dama duk kan takaddun da wayan nan mutanen suka É—auka na bogine, kudin ma dake hannu su na bogine. Banyi wata murna ba saboda wanda ya tara su nafi bukatar kasancewa dashi akan kudin, sai dai kuma lallurina yafi gaban ace haka . Dattijon da muke gidan sa mai suna Baba Lawandi "Yace yaro kaje da kanka, ina ga zaifi, saboda it halin da take ciki kar wani abu ya tada hankalinta ,kason mace da rauni.. Cikin yarda da sgyawarar shi Sadeeq yasa kai ya tafi.. Anan ne na farajin wani irin faÉ—uwar gaba da nadama akan barin shi da nayi ya tafi. Atakaice kusan awa ukku muna jira shuru, Hankalina ya tashi da na Baba. Muna tsaitsaye sai gashi mun hango yana isowa da manyan jikkunoni guda biyu hannu sa. Da sauri na nufi inda yake, Dai-dai lokacin da mukaji halbin bindiga tah! tah !!tah !!!har ukku, inda cikin tsautsayi É—aya ya samu Sadeeq a Æ™ason kirjin sa, take kuwa awajen ya faÉ—i ba rai. Ihu muka sanya nayi kanshi ina gilgizashi cikin tashin hankali, lokaci guda kuma ciki na yayi wata murÉ—awa wadda ta sanya ni matse cikina da karfi jin dan cikin nawa na Æ™oÆ™arin fitowa duniya ,bayan baya da ko pant din da zanmasa Amfani da shi... Baba Lawandi ya tashi abunka ga mazauna kauye sunson sirrin hatsabibanci ya fiddo wata powder ko toka zance bazan iya ganewa ba , Ya fara faffesamuna yana fesama gefe da gegen mu. Ashe gani yayi sundo so inda muke dan kare rayukan mu yasa yayi wannan siddabarun, sai gashi wajen ya koma Jeji mai tsananin duhu da ban tsoro , Da kuka'n manya -manya namin Daji, hakan yasan ya wayanda suka biyo Sadeeq rugawa da gudu.. Yayin da ya kira matar shi ta jani É—aki ,shikuma ya isa ga Sadeeq banson mi suka mai ba.. Cikin ikon Allah lokaci kankane na haifo yar kyakyawar É—iyata mai tsananin kama da sadeeq. Ina samu ta faÉ—o Duniya banbi ta kantaba ko kallon ta banba, Saboda bata ita nike ba, aguje na fito É—akin anan naga Baba da sadeeq da baya hayyacin shi bakin wata bishiya duk ya ÆŠaÉ—É—aura ma kirjinshi Bedi, Da wasu ganyayyakin da banson kona minene ba. Da gudu naje gunshi nace" miyasamu Yaro na, ko sun kashe shi? Yace mun "A'a yana da rai. Haka muka fara jinya shi ina kuma jegon ÆŠiyata da ko Pant sai da Baba ya birni ya siyomata. Ranar data cika bakwai nace ayan kamata Rago ayi sadaka muka ba da kudin wa Baba Lawandi. Ya bukaci sunan ta nace ya samata Sady. Kuka sadeeq yasa yana gigiza kai. Nace to Asamata sunan ya É—aga kai dan baya magana. Watan mu É—aya kana Sadeeq ya É—an maro, Cikin ikon Allah jikin shi yayi sauki sosai babu laifi,Amma in zai tafiya sai kaga yana dudduÆ™ewa. Aranar daya cika wata biyu da tashi Baba yace" akwai matsala muyi maza mubar shiyyasu, inba haka ba tom abu marar dadi zai biyo baya... Aiko cikin hanzari na goya ÆŠiyata suka nuna muna Æarauniyar hanya muka taho da manya jikkunan mu muna musu Godiya da Alkawari dawowa duk ranar da komi ya lafa.... Fuskar mu a kulle muke tafiya , Yayin da sukuma mutane suke binmu da kallo. Muna shigowa cikin gari Sadeeq ke cemun Umma nan fa gold ne, akwai hadari shiga motar haya dashi. Jin haka yasa nace mai muje shagon Alhaji Isa mai gold dan munyi school É—aya da shi kuma ina yawan sayan gold wajen shi. Muna zuwa bakin shagon Anan na cema Sadeeq ya samo muna abinda zamu ci,yana tafiya na shiga ciki na bashi Ajiya ,sama -sama nafara mai magana tare da faÉ—in zanzo in karba , Ita kuma gudar jikka muka buÉ—esu kaÉ—aÉ—ene da yawa sai uwaye takaddu. To kudin ne Na dibo da yawa sosai, kana na bashi ajiya sauran yana ta so inmai karin bayani amma ina agulguje na fito ganin Sadeeq ya doso wajen mukayi Tasha. Anan mukaji ana Am'batar motar Katsina, bamu tsaya komi ba muka Haye sai Katsina, muda bamu taba zuwan ta ba. Bayan munzo munsha wahala babu wanda muke neman alfarma daga gareshi ya taimakamuna ,kowa kallon mugaye ake muna, ganin yanda muke a jigace.. Dakyal muka samu wani mutum ya taimaka muna Muka sayi gidan da muke ciki. Amma abun damuwa som yan unguwar basa yarda damu, Hakan yasa bama shiga harkar kowa, mukaÉ—ai ke rayuwar mu. Yan sauran canjin mu mukasayi abin buÆ™ata, Irin su Kayan Abinci dana sawa, Dan namu duk suna gida. Haka mukaita rayuwa a Æ™untace , Sadeeq yana warkewa sosai ya fara shiga kasuwa yana neman Aiki ,amma babu mai bashi har Allah ya hadashi da Wannan Dattijo daya Bashi Aikin DAKO , Bayan ya rabu da shine kuma Allah ya haÉ—aku. Ahaka muke rayuwa inda shakuwa mai karfi ke tsakanin shi da Hamrat, duk abinda ya samu ita yake fatan kashemawa. Shekara mu biyu kunci da tsada rayuwa tasa in Sadeeq yayi Aiki sai inga kudin basa isarmu, dan aikin ba kullum ake samu ba ,Kunson DAKO'N Hatsi. Hakan yasa na yanke shawarar turashi wajen Alhaji Isa ya karbo kudaden mu ya kawo muna. Bayan yaje ya dawo a sanyayye tare da Nunamin shagon ma an mayar dashi garejin manyan motoci, an tabbatar mai da tashin sa sama da shekara É—aya ba ason inda ya koma ba.... 5/23/22, 11:03 - MY MTN 2: *Littafin🌹DAN DAKO🌹 na kudi ne biya ki karanta cikin Aminci. Biya 300kacal to 0006454115 Amina Dahiru jaiz bank,or MTN card to this number 09165832002. then send the evidence of payment via 07038423451* ðŸ¤ðŸ™ðŸ¤² Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Yan uwana mata ina kuke ku malmatso ga wanni sirri da nike son baku, ita ya mace sai da kamshi, ina macen da take ganin izgili da wulakanci da ake cewa maza nada shi, hmmm yar uwa to inkin kasance a haka da alama akwai ayar tambaya akanki. Tambaya ta ta farko gareki da wane irin turare kike amfani a jikin ki ?,da wane irin turare kike turara gidan ki,shin dawane irin turare kike Zukunni, hmmm to matso kusa kiji yar uwata. Shi kamshi Annabi muma ya faÉ—a abin sone,kuma Abune mai sanya natsuwa da girmama ma'aboci shi , Da Yawon son kusantar sa. Duk kan wulakanci da izgilanci na maza akwai turaran da zai miki maganin sa da izinin Allah,ba boka ba malam,wanda zai karkato da hankalin mijinki akan ki ku samu fahimtar juna. Ko kin son kamshi na dakusar da fitinar É—a namiji yar uwa? kigarzayo ki kwashi rabonki ga shaharariyar yar mai Dugurin nan mai suna UMSAD INCENSE ,Mace mai kishin mata da son Fiddo martaba mu. Nayi Amfani da turaranta naji masifar daÉ—in da yasa nakasa barwa raina. Nace bari in yaÉ—amuku dan kowa ya mallaki nashi cikin farashi mai sauki. Da fari bari in zayyano muku su kamar haka.👇 Maleek Al'oud Royal kush Cous-cous Kajiji Original sandal Sandal flex Sandal bange VIP mix Hawi Al'oud Kindikay Danal banat Darot Habil Gaf-Gaf Sirrun nisaa'i Sandal chips Kwalacca Humra black and body milk Attractive humra. Yar uwa zanmiki Dallah- Dallah. Akwai turaran da zaki sanyama kayanki . Misali! kisa kabasa kiturare kayanki . Akwai humra da bazaki sataba sai zaki turaka. Akwai turaran kaya ,na jiki, Dakuma na É—aki. Akwai kwallaca sirri, amma bama badata gaskiya sai ga wanda baida kishiya , Dan muddum kina amfani da ita tofa gabaki dayan hankalin mijinki akanki zai dawo,Dan yana juyo da hankalin namiji akanki baki É—aya ,zaki zama shalele Baby, Akwai sirrin nisaa'i. hmmm Dagajin sunan kason na dabanne,na baki sati É—aya ki gwada ki gani Hajiya ta, tsugunno ake akai ga mai buÆ™ata ya tunÉ“e mu ta wannan layin 08028827241 karku manta UMSAD INCENSE mune na É—aya. Muna aika kayan mu duk inda kuke. Kamshin jiki martaba mutum.... 🅿ï¸4ï¸âƒ£7ï¸âƒ£&4ï¸âƒ£8ï¸âƒ£ """"Kuka Nene take sosai kamar zata shiÉ—e, Dan mutuwar É—anta ta daketa sosai ,ta motsa mata tsumin kaunar gudan jinin nata. Da rarrafe Mamy dake kuka sosai ta rungume Nene tana faÉ—in kiyi Hakuri Nene mu , Dan zatin Allah ki bishi da Addu'a, Dan a yanzu ita yafi buÆ™ata daga bakin ki mai Albarka, Nene Allah yamana gata daya haÉ—amu da iyalin shi .... Abba ya sunkuyar da kanshi yace" Tin daga ranar da kika kaiman maÆ™udan kuÉ—aÉ—e da Gold din nan naku nike cikin mamaki da kuma jiran zuwan ki. Ahaka lokaci yayita ja har na samu shekara É—aya babu ke babu labari, Alokacin ne kuma azzikina ya fara durkushewa, sakamakon sata da akaje gidana akamun, Bayan naje Dubai nayo sabon sari. Allah ya taÆ™aita man banda kuÉ—un ku. Saboda dama tin ranar da kika bani kudin ki na kaisu banki na ajiye. Gold din kuma naje nayi rami na binne su lambun gidana dake Abuja. Ina tsaka da tinanin yanda zanyi in sameki in nemi alfarma juya kudin ku dan zaman hakanan babu babba harka ya ishe ni. Kwatsam matata ,Allah ya mata cikawa sakamakon ciwon ciki na dare daya da tayi. Nayi kuka sosai na takaicin rabuwa da ita. Hakan yasa zaman Abuja ya gagareni na sayar da komi nawa nasamu kudi masu kauri na haÉ—a da naki kawai na fara fita kasashe ina harkalla ta. Kasancewata maraya ba uwa ba uba yasa nasanu shago acen ina harkata, in kuma na samu Abokan Sana'ata na nan ina zuwa inbasu kan farashi mai sauki ,su biyani inkoma. A takaice ko nazo Æ™asata bana jimawa nike komawa saboda bani da kowa... Akwana a tashi na hadu da wani mutum mai suna Alhaji Hamza mai Zinarai, amma shi Katsina yake yana zuwa sarin kaya. Kunson komi haÉ—uwar jini ce . Jinin mu ya hadu sosai hakan yasa muka kullah zumunta mai girma. Munkai shekara biyu dashi wata rana ya gayyace ni ÆŠauri auran yarsa da za'ayi. Aiko dan nunamai muhimman cinshi na ajiye komi na sanu halatta É—aurin auran , Ashe kaddara HaÉ—uwata da Fulani ta kawoni... Da sauri su Amnah suka É—ago kai. Yayin da Mamy tace" kwarai kam kaci gaba, kuma ka faÉ—i komi yanda yake ,bana bukatar asaya wani abuuu.. Yayi Æ™asa da kanshi yace" Bayan angama daurin aure munata gaisawa da mutane wayata ta shiga ring.. Zamewa nayi daga wajen mutanan ina É—an tafiya nesa dasu , Dan samun saukin hayaniya da ake . Ahankali nike taku ina jefa Æ™afana inda bansani ba, sai wayata nike cikin kwanciyar hankali... Kamar saukar aradu haka naji an kwalloman katon abu akaina ta saman guntuwar Æ™atangar gidan da nike tsaye ina waya.. A É—imauce na juya dan duk tinanina bangone yaman saukar bazata aka.. Wata kyakyawa tsohuwace hannuta rike da jaririya tanata tsallara kuka. Wasu garada ne su kusan biyar sai bankosu waje suke suna faÉ—in sai sunbar gidan ,tinda bana ubansu bane... Cikin rawar murya Tsohuwa tace" zamu tafi amma kudaina watsamana kayan mu Dan Allah, Kun ga kayan wanka yarin ya Nan duk kun kashe su fa kuma Wallahi dakyal na siya. Daya ya dakamata tsawa tare da faÉ—in" ta ware. Wani matsanan cin fushi ya taso mata inda naji afusace tace" Fulani fito kibar musu matsiyaci gidan su ,wankan jegon banza wanka wofi yasa sunta tozar tamu. Tana rufe baki naga wata kyakyawar matashiya da bazata wuce 18yr ba, ta fito kanta a Æ™asa tana share kwallah, ta kallesu tace Dan Allah kuyi hakuri kubar ni ingama wanka sai in Fita insa mo muku kuÉ—in.. Afusace daya daga ciki ya yankamata Mari, wanda hakan yasa Tsohuwa sakin ihu ta kwantar da Baby Æ™asa ta kwashi wani katon dutsi tayi kan wanda ya mari yarta, Jikake kaf ta É“auremai kai,Take ya faÉ—i yana ihu jini ya wanke wurin. Kamin inyi wani yunkuri naga daya yayo kanta yana faÉ—in babu ruwan sa da tsufa ta sai ya ramama É—an uwan sa. Ganin yana Æ™okarin bi ta saman Baby dake ta Tsan yara kuka yasa da sauri na É—auketa, yayin da ita kuma Tsohuwa ta cika hannayen ta da kasa ta watsamasu su duka tana faÉ—in su za'ama iskanci suda sukayi hadda yanda ake zama da yan iska.. Gyaran murya nayi nace" Mama dan Allah kiyi hakuri , miya haÉ—aku.. Tsawa ta dakaman tana faÉ—in bansani ba ,karka kara ceman Mama, sunana nene Murmushi nayi dan hakanan Naji ta Burgeni da ta iya kwatar kanta hannu mugaye. Daya daga cikin su ya mike zayyo kanta ina dakamai tsawa amma yakiji ,ashe ta lura da sauri tayi flat Æ™asa ta kwaso kafafuwan shi sai gashi yayi suka ya shige cikin ramin babba kwatar dake lungun... Dariya ta saki tana Æ™arsawa wajen shi ta dauki siririn icce ta fara zane mazaunan shi ,dole azaba tasa ya ida shigewa baki É—ayan shi ciki .... Baby dake hannuna na kalla yarinya mai masifar kyau fara sol, sai Dan bakinta mai kyau ga hanci,sai tsotsar babban yatsanta take tana sauke ajiyar zuciya, tana kallo na. Farat daya so da kaunar É—iya ya shiga raina, dan dama ni bantaÉ“a haihuwa ba. Cikin natsuwa nike tafiya ina kallon Baby har na karaso wajen da nike tinanin Tsohuwace da niyyar in mikamata ita. Sai naga matashiyar budurwa dake matse Kwallah ta mikoman hannu cikin natsuwa take fadin mungode da taimako da yanzu sunkashe ta... Tsaye nayi ina kallonta dan hakanan naji ta burgeni, kuma ina buÆ™atar shiga rayuwar su dan basu taimako daga halin dana fahimci suna ciki. MiÆ™amata nayi tayi godiya tana juyawa taba Nene dake Taunar goro tana hura hanci. Karba tayi tace'' Duk kwaso muna sauran kayan mu mutafi ko Saman rowl ne muzauna, ba shikenan ba, cen in na uban mutum ne sai ya tadamu, in'zamuyi buÆ™ata akwai na haya ashirin ko goma bazata gagaraba, Allah ya iyama kowa ta faÉ—a tana matse kwallah... Sosai tausayinta ya tsargani hakan yasa da sauri na Æ™arasa wajenta na gaidata ta amsa a mutunce tana mikewa tsaye tace''kayi hakuri É—azu raina ya É“aci ne kaji jya dakama tsawa. Anan nace ba komi. Nace" Inna ni abokin makwafcinki ne Alhaji Hamza, in ba damuwa ina so in taimaka muku, kuma kizama mahaifiya a gareni ,saboda bani da kowa. Kuka tasa sosai har ta bani tausayi tana faÉ—in Allah ya jikan Sadeee nah yau ga wani na samu. . Tace ashha, Abokan juna kaida Hamza wargaji? Amma hali ya banbanta, Alhaji hamza baya iya taimakon kowa sai cikin shi dana yaran shi, amma kau na gode ni ko aikine ka É—auke ni.. Nace "A'a Nene, yanzu muje mota nima ba nan nike ba , dole sai na samu yan gari sun faÉ—aman yanda tsarin garin naku yake .. Ba shakka ba tsoro gareta tace" to dama na Allah muke nema ,muje nidai ko aikin guga ne zanyi ita kuma Saude ko kaya sai ta wanke. Cikin tausayinsu muka fito daga lungu inda na umarceta da ta bar kayan su duka basai ta É—auka ba. Haka muka fito mukabar zaratan maza kwance cukin hali.. Bayan mun fito na buÉ—e kuysu motana da dama kamin inzo na sayi abina. Shiga sukai ni kuma naje nayi sallama da Alhaji hamza inda na tambaye shi inda zan samu gida tsaye zan saya. Cikin mamaki yake tambaysr abinda zanyi da shi? Anan na fad'amai taimako nike so Zanyi dashi. Baice komi ba yayi waya sai gashi an'cemai ansamu tsaye kam. Abinka da kudi nan danan na siya na basu kudun su. Anan ya haÉ—ani da wani mutum muka tafi tare muka shiga motar har unguwar da Nene take yanzu.. Bayan munje gidan yamun kuma suma sukaita murna, amma yarta batacewa komi ,sai dai tayi Æ™asa da kanta akai-akai tana share Kwallah... Nene tai ta gidiyay tanasaman albarka da taimako su da nayi. tace'' ta yarda dani ta son Allah ne y haÉ—a mu, shiyasa na taimake su.. Murmushi nayi nace mata to zan bada kayan buÆ™ata akawo masu, gobe zan koma wajen aiki na ,amma yanzu tinda inada ita zandinga zuwa . Taita godiya harda yoman rakiya... Da yamma na bada kayan abinci aka kaimusu aka kuma basu kudi da wayar da zamu dunga gaisawa. Haka rayuwa tai ta gudu har saida na samu shekara biyu ban lekosu ba, amma ina musu aike kuma muna waya, ina yawan cema Nene "kince wannan anya mai gaskiyane, ya ajemu ya kama gaban shi. Sai tayai dariya tace" yo mizaka muna wanda Allah baimuna ba, kaganni nan nasha tabara na'sha yaseen, Babu bakin da zai kamani.... Murmushi kawai nike muyi sallama. Bayan wayar mu da kwana Biyu na shiryama tafiya Nijeriya. Bayan na sauka Kano na hau mota ta kawoni Katsina, kai tsaye gidan Nene nayi dan ko motana anan na ajeta dama kamin in tafi, saÉ“anin da da nike ajiyeta gidan Alhaji Hamza... Zo kaga murna wajen Nene da ta ganni kamar ta goyani sai haba- haba take dani... Muna zaune nida ita sai ga Saudat ta fito cikin shiga ta kamala ,Yarinya badai natsuwa ba kuma babu hayaniya a yanayin ta. A'hankali ta koma gefe damu ta zuÆ™unna ta gaishe ni.. Amsawa nayi cikin sakin fuska tare da kallonta. Ni dai hakanan tana burgeni, natsuwar ta nakaraman jinta azuciya ... Tana zaune bata tashi ba nima kuma banjanye ido daga gareta ba naga yar yarinya ta fito daga É—aki dakwal -dakwal tana kuka tana murza ido. Masha Allah nace dan yarinya tayi kyau sosai ... Anan na kalli Nene cikin mamaki Nace" wannan Baby ce wai ta koma haka? Tace'' eh mana itace gatanan Amnah ba..... Azabure Amnah ta mike tsaye tana kallonsu bakinta na rawa jikin ta na É“ari take nuna kanta da yatsa tace "Ni! nikuma? dama Abba. kamin ta Æ™arasa tayi baya luuuuuuuuu. Da sauri Sadeeq ya duke ta faido kan shi ba Lumfashi. Arikice yake tura bakin shi cikin nata yana danna mata iska yana yarfe hannu tare da kiran sunan ta da karfi cikin tashin hankali Amma bata motsi.. Mamy kau gefe ta koma ta tura kanta cikin cinyoyinta ta saki kuka... Iya gigicewa sadeeq ya É—imauce, yama rasa Mizai mata, kawai ya jata gefe ya dora kanshi kanta ya saki kuka kamar mace.... Ammi ta share hawayen ta ta" mike ta fara bata taimakon gaggawa. Cikin ikon Allah ta falfado . Anan ta hada ido da Sadeeq. Fuskar shi ta shafa cikin kasa da murya tace "Baby Dee kai din nan mai gaskiyane ,kana mai hangen nesa,tabbas kataba faÉ—aman in binciki asalina na gaskiya, kenan dama hakane ?, Wanda yayi gadon arziki baya abinda nayi. Ka ya jinjina mata idon shi na fidda hawaye yace" Dan Allah dan girman Allah kidaina fadin haka, Amnah wallahi dan inÉ“ata miki rai nayi ,amma bawai da niyyaba, in baki mantaba mahaifina kika zaga, Dan Allah karki É—ora maganata a mizanin da bata da ceba, Amnah wallahi ko baki da iyaye ba ason asalinki ba ina sonki ina kaunar ki, ina sonki bazan barki b,ina tare dake har abada,Domin kece Rayuwa ta. Murmushi mai ciwo ta saki tare da miÆ™ewa zaune tana cije baki. Ido ta zubama Mamy tana kallo!Cikin Æ™asa da murya tace "wanene Baba nah Mamy?..... 5/30/22, 07:39 - Ummi Tandama😇: *Littafin🌹DAN DAKO🌹 na kudi ne biya ki karanta cikin Aminci. Biya 300kacal to 0006454115 Amina Dahiru jaiz bank,or MTN card to this number 09165832002. then send the evidence of payment via 07038423451* ðŸ¤ðŸ™ðŸ¤² Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Yan uwana mata ina kuke ku malmatso ga wanni sirri da nike son baku, ita ya mace sai da kamshi, ina macen da take ganin izgili da wulakanci da ake cewa maza nada shi, hmmm yar uwa to inkin kasance a haka da alama akwai ayar tambaya akanki. Tambaya ta ta farko gareki da wane irin turare kike amfani a jikin ki ?,da wane irin turare kike turara gidan ki,shin dawane irin turare kike Zukunni, hmmm to matso kusa kiji yar uwata. Shi kamshi Annabi muma ya faÉ—a abin sone,kuma Abune mai sanya natsuwa da girmama ma'aboci shi , Da Yawon son kusantar sa. Duk kan wulakanci da izgilanci na maza akwai turaran da zai miki maganin sa da izinin Allah,ba boka ba malam,wanda zai karkato da hankalin mijinki akan ki ku samu fahimtar juna. Ko kin son kamshi na dakusar da fitinar É—a namiji yar uwa? kigarzayo ki kwashi rabonki ga shaharariyar yar mai Dugurin nan mai suna UMSAD INCENSE ,Mace mai kishin mata da son Fiddo martaba mu. Nayi Amfani da turaranta naji masifar daÉ—in da yasa nakasa barwa raina. Nace bari in yaÉ—amuku dan kowa ya mallaki nashi cikin farashi mai sauki. Da fari bari in zayyano muku su kamar haka.👇 Maleek Al'oud Royal kush Cous-cous Kajiji Original sandal Sandal flex Sandal bange VIP mix Hawi Al'oud Kindikay Danal banat Darot Habil Gaf-Gaf Sirrun nisaa'i Sandal chips Kwalacca Humra black and body milk Attractive humra. Yar uwa zanmiki Dallah- Dallah. Akwai turaran da zaki sanyama kayanki . Misali! kisa kabasa kiturare kayanki . Akwai humra da bazaki sataba sai zaki turaka. Akwai turaran kaya ,na jiki, Dakuma na É—aki. Akwai kwallaca sirri, amma bama badata gaskiya sai ga wanda baida kishiya , Dan muddum kina amfani da ita tofa gabaki dayan hankalin mijinki akanki zai dawo,Dan yana juyo da hankalin namiji akanki baki É—aya ,zaki zama shalele Baby, Akwai sirrin nisaa'i. hmmm Dagajin sunan kason na dabanne,na baki sati É—aya ki gwada ki gani Hajiya ta, tsugunno ake akai ga mai buÆ™ata ya tunÉ“e mu ta wannan layin 08028827241 karku manta UMSAD INCENSE mune na É—aya. Muna aika kayan mu duk inda kuke. Kamshin jiki martaba mutum.... 🅿ï¸4ï¸âƒ£9ï¸âƒ£&5ï¸âƒ£0ï¸âƒ£ "" Abba Yace" Baban ki na nan da ransa da lafiyar sa , Amma kwara mubi abun dalla- dalla kinji... Batace komi ba sai kanta data dora saman kafaÉ—ar Sadeeq, Yayi da shikuma ya fara mata magana Æ™asa -Æ™asa da banajin miyake FaÉ—a.. Ammi ta kalli Sadeeq tace' Dee kafadama ogan ka abar tafiyar Nan Sai gobe insha Allah da safe,Saboda nima ina so in'bika. Dansauri Nene tace itama zataje. Anan suka aje magana akan suma duk suna son zuwa. Waya ya É—auka ya kira shi cikin ladabi ya masa bayani kuma ya gamsu. Hakan yasa ya tashi ya shiga É—akin shi ya cire uniform din ,ya sanyo wasu ya fito. Abba yaci gaba da cewa" Cikin Mamaki Nike kallon yarinya ,tana ganina taita murmushi aguje tayi kaina ,kan in an'kara ta fado kaina tana wasa da sajen fuskana tana dariya. Wasa na shiga mata damin naji ina sonta. Nace" Nene wai basun gama wanka ba Tini,miyasa bazasu koma gidan su ba? Hawaye ta share tace" ai har abada babu Saude babu Mai malmala Wallahi. Cikin mamaki nace ban fahimci abinda kike nufi ba?. Tace "Isa mu buzayen agadas ne ,Yanayin yaki da rashin zaman lafiya yasa duk muka watsu da ahlinmu kowa ya kama gaban shi, nima iyayena suka É“accema ganina, kusan sama da wata biyar. Nayi neman na gaji daga baya Kuma yan Æ™ungiyar da muke suka fara kawoman farmaki, hakan yasa nima na gudu ni kaÉ—ai na share kwanikka kamin Allah ya fito dani Dajin na fado garin jibiya. Anan na samu nayi bara na samu kudina na hau mota na dawo katsina. Nan na fara gantali ina neman muhalli da abinda zanci ,amma bana samu saboda akan ce yan gudun hijira yawanci duk mayune shiyasa ake tsiron mu. Kwasam wata rana ina tafiya cikin galabaita nasha yunwa nagaji banson na kawo titi ba, Sai ji nayi ankwasheni da machine , BanÆ™ara sanin inda nike ba sai dai na falka na ganni wani É—aki bakomi ciki , Amma ashafe yake, ni kuma ina saman wata yar katifa irin ta yara ta makaran ta, kafana da hannuna guda a É—aure, alamar dai karaya na samu. Kuka na saki saiga wani mutum ya shigo da gudu. Tsoro ya kamani na fara Æ™oÆ™arin tashi. Da sauri ya fara magana yace" Dan Allah yam9 Mata karki tashi ,kinsamu karaya, wallahi bada gan-gan na tureki ba, faÉ—owa kikayi gaba na. Shuri nayi ina kallon shi cikin kuka nace mai ni toilet zan shiga. Anan ya fara salati yana fadin shine kadai gidan matar shi sun rabu, saboda baya haihuwa, yanzu ya zayyi dani? ya son bai dace ya taÉ“ani ba, Tinda ni ba muharrama sa bace. Kuka nasa sosai ina fadin zanyi fa anan... Kai ya jinjinaman cikin tausayi yace" kiyi anan kamin in sami wadda zata gyara ki. Cikin yarinta nace to kai bakamun. Yace a'a bai kamata ba tinda ba auranki nike ba. Nace to ka aureni mana. Murmushi yayi dan ya manyanta, amma yaji ina ya aureni yar yarinya dani. Da yamma ya samo wata makwafciya Shi ta gyarani tsaf, ya sallame ta ta tafi. Daga baya yazo yacemun na amince ya aureni ? Nace" eh "nida bani da kowa na Amince. Yace shikenan da yamma sai gashi da Dabino wai an'muna aure. Aiko daga ranar yake kulawa dani har na warke sumul. Bayan na warke ne kuma na maye gurbin matar shi. Bansamu wata daya ba gidan na samu ciki, zo kaga murna wajen Malam Bishir ,Yayi ta jin dadi yana ma yan uwan shi dake kano waya yana faÉ—amusu. Bayan wata tara na haifo yarona jajur mai tsanani kama dani ,sati na zagayowa akasamasa Sadeeq. Yana da shekara daya na sake Haihuwar Saudat. Bayan Saudat tayi shekara muka shirya tafiya Kano wajen dangin Baban su, bayan munje muka biya gidan yayan shi da akai haihuwa, Anan Sadeeq É—ina ya É“acce, na nema kamar wasa sama da sati daya muna neman yaro amma shuru , hakan yasa zuciya na ciwo sosai nayi kuka har na barwa Allah, mahaifinshi kuma É“atan yaron ya sanya hawan jini yimai mummuna kamu saboda akwai soyayya mai girma a tsakanin su, cikin wata biyu yace ga garin ku nan. Na shiga tashin hankali da É—imuwa na rashin jigona, Daga baya na rungumi ÆŠiyata muna rayuwa maraicu, Sadeeq kam yana yawan faÉ—oman arai na son baiko iya magana ba, Daga sunan shi saina Saude ya iya, amma ko mama baya cewa... Bayan shekara sha biyu muna cikin hali, gashi lokacin saudat ta tasa sosai, Hakan yasa muke zuwa cen wajen kasan layin mu wajen makaranta Allo wani Malami da akecema Mai malmala muna saida Æ™osai. Duk sadda zamuje zai buÆ™aci akawomai Æ™osai, kuma Saudat nike ba ta kai mai. Da haka yayi amfani da damar shi ashe sonta yake ko ince sha'awa. yayi siddabaru ya rufe muna baki yazo da magana Aure. Hakan yasa na kasa magana amma ita Saudat kuka tasa tana fadin ya zatayi da Tsoho?. Cikin kwana biyu yaje garin su mahaifinta ya nemo auranta, bayan suma ya rufemu su baki, Dan tsohon mutum ne ko Lokacin ya kai shekara hamsin. Basu jaba sukazo washe gari aka ÆŠaura aure. Inda Saude taita kuka nima inayi. Inaji ina gani aka É—auke man ya É—aya tak aka kaita gidan wannan tsohon. Tinda ta tare. Duk kan dare na Allah zai kaima Saude ziyara, amma bata amince mai, da duka yakushi bugu take hanashi, daga bayama sai ta dunga rufe Æ™ofa. Hakan ya fusata shi dama yana da mata hudu ganin Saude ne yasa ya saki É—aya, Ya maye gurbinta da Saude,ga babba matsala duk wani siddabaru yayi amma abanza baya kama . Gidan shi dake da yawan yara kwatsa-kwatsa ya tara dukkan mutan gida, hadda saude data buÉ—e kofa ganin gari ya waye ta fito cikin taron... Anan yake faÉ—in daga ranar ya hutar da kowa aiki a gidan Saude zata dinga mai, Dan bata da É—a'a da ladabi. Sanin halin shi ne yasa suka amince mai tinda dai ba kwana ya hanasu ba. Daga ranar take wahala tuka tuwan gidan ma kadai aikine, sai dai tayi tukunya ukku tinda ba iya da yawa zatai ba. Cikin sati biyu ta fara fita hayyacinta, yarin yata mai garin jiki amma duk ta bushe , Gashi duk sadda nayi niyyar zuwa gidan sai in kasa. haka Saude taita rayuwa har ta cika shekara ukku. ya kama shekarata sha biyar ,babu abinda ya shiga tsakanin ta da Mai malmala, saboda har lokacin rufe Æ™ofa take da mangari ba tayi. Ranar da ta manta bata rufe kofar ba bacci ya kwasheta aranar Allah ya kaddara da rabon yarin yar nan, saboda ranar ya hakemata yamata illah mafi muni dan har yoyon fitsari ta kamu dashi kuma ya kore ta, saida nayi bara kana muka samu mukaita zarya Asibiti,kudi da yawa aka samana hakan yasa gidan da nike ciki na sai dashi dan in samu kuÉ—in magani ta , Da sauran muka kama haya inda ka ganni. Cikin ikon Allah abun ya tsaya aka sallamo mu muka dawo gida. Kwana ta ukku da dawowar saiga Mai Malmala a fusace ya shigo gidan nan, kamin in'magana yaja hannuta suka tafi tana turjewa,suna isa gida ya É—auketa ya watsa ga gado ya shaga biyan bukatar shi. Daga ranar ya maidata jaka koda wane lokaci yana hake da ita, kasancewar shi harijine shiyasa mafi yawan mata basa zama dashi Saboda suna cutuwa.. Sosai Saudat ke shan azaba duk ta rame ta fita hayyacinta ,ga shigar ciki da laulayi amma baya ÆŠagamata kafa, ga matan shi sun fara matsamata ,suna ganin baya kwana wajen su kulkum yana like da ita . Ahaka cikin rayuwa wahala cikin ta ya mika, yafito sosai su kuma daga lokacin suka dauki aniyar dukanta ,Duka km bana wasa ba, Dan sunga bata da kowa daya fita makaranta allon shi zasu hadu su mata shegen duka, Cikin fatan su cutar da cikin amma ina Allah bai nufa ba . Gashi ya hanani zuwa ingañta, dana doshi gidan zanta ganin wasu abubuwa dole nike komawa, itama baya Barinta fita dan kar ta gudu.. Wata safiyar litinin ce ana ruwan sama kamar da bakin kwarya, Saude ta fara Nakuda . Mijinta dake Makaranta ya tada Almajiran sa ya taso ya shigo gida abuÆ™ace ya afka É—akin ta. Tana gani shi ta fashe da kuka . Bai tsaya komi ba yayi kanta anan yayi yanda yakeso sama da awa biyu gashi dama cikin nakuda take , Dole nakuda ta sake tashi amma ba tausayi babu jin kai ya shareta tanata wahala shi kam yana bacci. Addu'a ta farati tana kuka akan Allah ya kuÉ“utar da ita daga gidan dan ta gaji. Cikin ikon Allah bacci mai nawie ya kwashe shi. Hakan yasa ta fara rarrafowa tana Æ™oÆ™arin fitowa É—akin ta . Saiga uwar gidanta da gudu wai ta tashi ta doramusu ruwan koko yaran su naji yunwa. Saude tace bata iyawa . Anan ta fara jibgarta kamar ta samu jaka, ga bugu ga nakuda ahaka taita rarrafawa tana kuka. Uwar gidan na jawota tana fadin babu inda zata tana dukan ta. Cikin ikon Allah Saude ta tureta ta fito daga gidan da sauri har ta kawo bakin Titi haihuwa ta tashi rigi- rigi ,ga karfin ruwa nata karuwa Suna sauka akan ta. Anan saman kwalta ta duke tana kuka tana nishi har Allah ya bata sa'a taji Baby ta faÉ—o cikin zanan ta. Kasa tashi tayi kuma ta kasa motsi ,saboda halin da take ciki garuwa na dukanta. Wata motace ta yanko da gudu anan taja burki. A'rikice wata mata tafi to dan jinin da taga yanabin kasan Saude É—in ne ya sata tsayawa. " tace'' ke lafiya?. Saude ta kasa motsi matar ta iso kanta da lema hannuta ta É—an matsar da ita dan taga tushe abu. Anan taga Baby nata billayi kasa ga cibi ba ayanke ba. Salati ta saki ta watsar da lema ta dakko kayan aiki cikin mota ta yankemata cibiya, kana ta sa Baby a gyalan ta ta naÉ—e kana ta sata a'mota,A gulguje ta É—an bama Saude taimako kana ta dakkosu ta buÆ™aci sanun inda suke. Anan ta faÉ—amata har sukazo gidana suka shigo taman bayani ita Likita ce sunan ta Turai, anan ta ajiyemuna kudi tace zata dawo. Daga lokacin ne muka fara sabuwar rayuwa ta kunci. Watan ta daya Mai malmala ya turo da takarda sakinta da zagi kala- kala. Aranar ne nikuma Allah ya budemun bakina na fara jin takaicin abubuwan da yama ta. Da kaina naje na siyo barkono na daka shi haka nan na hura icce na dafa ruwan zafi na juye yajin ciki kana na fita na nufi makaran ta shi. Yana kwance yana bacci na koma gefe na fara mai wanka tindaga saman fuskar shi ,kai ,har cikin wandon shi., Ihu yake yana kari amma baison waya mai ba na fita hankali kwance ba tare da kowa ya ganni ba. . To bayan kwana ukku ne kaganmu Acikin wannan yanayin na rashin kudin haya..... Hawaye na share naji tausayin Saude ya shiga raina, Gaskiya an'kashe rayuwarta ,shiya sa bata ko son magana. Anan na nemi alfarma magana da ita Nene ta amince. Bayan munkeÉ“e nike mata magana son zama miji a gareta. Da fari taku amincewa saida naita lallashinta tare Da Bayyana da alÆ™awarin zamema É—iyarta uba kana ta yarda. Alokacin ne kuma kwasam Mai malmala yasamu labarin Auran ta har ya gano gidan. sai gashi shida yan uwansa wai abasu É—iyar su zai tashi daga katsina ya koma kauyen ÆŠAN ÆŠagoro, anan yake so ya fara sana'a saida hatsi. Aiko anan Saude ta nuna mai ba Mai hakuri bai iya fushi ba, Ranar hadda mari ta rafkama tsoho nan, Da nuna mai itace uwa da uban yarta ,bata fatan har abada É—iyar ta tason shine ya haifeta. Rigima sosai akayi inda yace "ya barmata amma ta sani duk ranar da aka tashi auran ta to bata da uba ,kuma in dai har yasani to Babu mai auranta. Tace mai taji tana turashi waje ya fice gida. Shekara na zagayowa muka angwance, muka tafi da Amnah ina mata duk kan wani gata. Har saida ta cika shekara biyar kana Allah ya bamu cikin Amal. Nayi murna nina zanga gudun jinina, amma na fiso da shakuwa da Amnah sama da wadda na haifa wannan shine tarihin mu. Wani irin kuka Amnah keyi yanzu itace aka haifa cikin gararin rayuwa, Lallai ita bai dace data tsani jinin talakaba har saita fara zuwa taga mazaunin ta.. Mikewa tayi tsaye tana fadin "abata address din gidan mahaifinta. Nene tace muma bamu sani ba sai dai muje unguwar da muka bari a tambaya ,amma ki bari aje Abuja adawo. Shuru tayi badan taso hakan ba. Sadeeq ya kama hannuta yace" muje ki huta kinga bakyajin daÉ—i. Mikewa tayi dan tana buÆ™atar hakan suka tafi É—aki shi ya rufe. Hijjob inta ya cire tare da zame mata rigar ta ya cirar nashi kana ya jata jikinshi suka kwanta. Take ta fara sauke ajiyar zuciya, cikin lokaci baccin yayi gaba da ita. Saida ya tabbatar tayi nisa kana ya tashi ya maida kayan shi ya fito . ya fita waje tare da tsaida machine ya doshi goruba roud. Bayan yaje ya sauka wani faskeken gida,take wani soja yazo ya buÉ—emai yana mai saramai. Shiga yayi yana tafiya cikin Æ™asaita har zuwa wani kofar palon dake farko ya tura ya shiga. Anan yaga Bily zaune tana kuka. Dukawa yayi kusa da ita yana mai zaro sabuwar waya da sim card sabo ya bata yace" samun number ÆŠan Akuyan ubanki. Kallon shi tayi tace "Uncle Dee.harda cin mutunci, ni dake buÆ™atar taimaka ma. Mari ya kaimata yace" zakisa ko sai na sanya karnuka sun yaga naman jikin ki. Da sauri ta sanya ta bashi. Shikuma Ya danna mai kira. Bayan an'É—auka ya saki Murmushi mai ciwo. Daga cen bangaran Alhaji Musbahu yace" wanene akan layi...? Sadeeq yace "DEE S.S" Azabure ya mike yana faÉ—in kana nufin Sadeeq S Sadeeq ,ubanwa ya baka number nah, kuma dama da ranku,Aiko zakuci uban ku .. Cikin natsuwa yace "ai'kagama cinshi tinda har ka karshi, yanzu kuma nine zanci naka agabanka, baka kuma da abinda zakai. Da fari ga karyar yarinyaka nan hannu na,Kason ka tarbiyyan tar damu da son kuÉ—i, Dan haka fansar ranta million dari biyu ne,Ma'ana kudin da Abbana ya Sanya ajikkar da kuka kwasa sama wanda Æ™asa ya samaku na bogi... Cikin ihu yace" wallahi wallahi ka taÉ“a mun ya saina kasheka har lahira, bayan yaudara da kukamun kaida matsiyacin ubanka zakamun wata kai ga maye mai gadon Asara ko?. Afusace Sadeeq ya zaro bindiga ya saki halbi saman kujera daya gigita Bily ta saki ihu sosai, Yayin da jikin Alhaji Musbahu ya dauki rawa ya fara faÉ—in" ba dai kasheman ya kaiba, kai kana da hankali ,yar tawa data ragemun, Ƙaseem mafa ya mutu , Dan Allah Dee kar kamun haka, dan Allah ita kadai garan.. Yace kayi maza ka bada kudin fansarta ciki 3hr, Niku ma in sanya acire bullet din Kafar ta, in'kuma kaÆ™i to dan ubanka zaka zo katarar da gawarta ta kumbura ko inba karnuka su cita.. Salati ya É—auka yana faÉ—in" Dee zan hadaka fa da hukuma. Yace karka manta nima hukuman kainane, sai na jika kill ya kashe wayar tare da mikewa ya fita.. Washe gari da sassafe suka dayuki hanya harda Bily, Bayan su kau zugar motocine sunfi a kilga sai jiniya suke... Zuwa azahar suka shiga garin Abuja . Kamin su isa Sadeeq yayi waya da mahaifinta inda ya tabbatar mai da ya biya kudin... Murmushi yayi yana jawo wayar shi ya kira wani mutum yace" sako yazo. Yace" eh Yallabai sunzo kuma mun kilga sun cika .. Kashe wayar yayi yana doka Murmushi... Suna isa kwanar yaga gidan mahaifin shi ne, Bazai taÉ“a mantawa ba, Wato shine aka gyara kenan suke ciki ,hooooo É—an nmadam kenan Ya kashe mai abu ya mallaki gida. Jiniyar suka kashe sadda suka isa. Bayan sunje suka fara fitowa wasu suka zagaye gidan, wasu kuma suka nufi get din gidan gadan- gadan ,ciki kuwa harda Nene dasu Abba sai uban gayya da Ammi.. Kwan-kwasa wa sukai mai gadin ya fito yana faÉ—in" waye ? Sadeeq yace" ka bude yar Alhaji muka kawo. Da sauri ya buÉ—e suka turashi suka fara shiga gidan zuga guda . Salati mai gadin yasa Amma ganin iyayen shi ne a iskanci yasa ya koma gefe yana kyarma dan yason soja ba mutunci... Wani Bakin glass sadeeq ya dauka ya toshe idon shi daya fara jin hawaye na neman zubomai tinowa da rayuwar da sukayi da Uban su agidan da yar uwar shi. Bindigar hannu shi ya gyara tare da sumba tar goshin Amnah yace". kikoma wajen su Nainah. Tace to tana mai É—agamai Hannu. Cikin kuzari ya isa gaba tare sa kutsa kai baban palon da yasha kayan Alatu.. Tsaye yayi yana kare ma palon kallo ,komi na more rayuwa akwai ciki na zamani. Zama yayi akan kujera tare da É—ora daya kan É—aya yana gilgizawa, fuskar nan babu rahama som. Ganin babu kowa yasa ya É—aga bindiga sama ya halba jikake "dammm.. " Kamar saukar aradu Alhaji Musbahu da Matar shi suka ji abin nan suna tsaka da zaman jiran ganin yarsu. Aguje su kayo palo inda suka ga Sadeeq hakimce duk da ya Æ™ara girma ya kara cika da kyau hakan bai boye musu fuskar shi ba dake kama data baban shi... Wani mahaukacin tsoro ya Dirar ma Alhaji Musbahu musamman dayaga Sodoji dakin cike suka zare ido. Take jikin shi ya dauki rawa ya fara Æ™oÆ™arin koma daki .. Kan ya Æ™arasa yaji saukar bindiga a kafar shi.. Ihu ya Kwallah tare da murginowa daga kan step din da yake sai gashi tam gaban Dee.. Bindigar shi ya gyara yana mai taka ruwan cikin shi yace" yama karin maganar nan da gayusawa kece wa? . shiru Musbahu yayi sai jikinshi dake kyarma yana fidda hawayen azaba... Sadeeq yace'' nason bazaka amsamin ba, to rana daya ta É“arawo daya tak ta mai kaya , Dan haka gani gaka, yau sai mugwada kwanji muga wazai nasara. Kamar haka ne shekara goma data wuce kasa aka taramu palon nan, aka muna cin mutunci da illah babba, daga karshe aka kashemun Abba nah da sst na mafi siyuwa agare ni, to yau kaima agaban ka zankashe kowa naka kamin in dawo kanka.... Kuka sukaji irin na tsofafi daga gefe. Sadeeq ya waiwaya yaga Umma ce tanata jan kugu tana sauri, Duk tayi mugun tsufa ta lalace... Tana Æ™arasowa wajen su ta kallesu tana kuka tana buÆ™atar tayi magana amma ta kasa. Sadeeq ya toshe hanci yace "dama da ranki, to Alhamdulillah, yanzu in kinga mutuwar su ina fatan taki ta kawomaki ziyara, kamin nan Ammi, Nainah, My Wife, Amal, Abba kuje waje dan Allah zamuyi magana.. Suna Æ™oÆ™arin fita Nene tace "wallahi saina ramama É—ana zalinci da kuka mai. Ta dawo da gudu ta cire takalman Amal masu tsini har ta kusan ya data ta nufi wajen Alhaji musba dake kwance cikin jini. Takalman ta rike duka hannayen ta ta fara kwalama Alhaji Musbahu a fuska tana kaimai mari dasu. Ihu yasa sosai Yayin da Sadeeq ke tafi yana faÉ—in kaga kakar soja, Allah yaja da ranki Nainah. Kamar ya Æ™aramata kuzari taci gaba da marin shi, sai da taga ko in ta tashi fuska tayi sumfut kamin ta gaji ta mike ta kaimai naushi tace" Matsiyaci nice nan uwar Sadeeq,m dan ubanka ta Æ™arasa tana nishi tare da nufar wajen Umma. Tan ida da karfi ta shureta tare da kai mata mari ta fizge hular kanta ta kwalamata takalman tana fadin kafura la'ananna mai zuciyar azzalumai, ashe ki kaita cutar yarona, kina zalintar sa , Dan bake kika haifeshi ba, to dama ina ke ina haihuwar yarona fari mai farar aniya , Amma ke kam kafurar daga ganin ki baki da mutunci munafuka sai kukan kyankyasai kike mana .. Kuka Umma tasa tana gilgiza kai kamar zata shiÉ—e. Nene ta fita tana tsogwami da faÉ—in zata kara mata wani. Suna fita Sadeeq yasa aka rufe Æ™ofar, tare da mikewa ya juya baya ya cema yaran shi ku kwantar da yar shi gatanan kuyi Abinda kuke so wanda kamin ya wullah lahira zai tafi da bakin ciki ,ni nace kuyi abinda kuke so.. Hifufuuuuuuuuu zakuna sunga nama ,har rige rige suke wajen doso inda Bily take. Ihu mamanta tasa da Babanta yana faÉ—in noooo Sadeeq, kwara ka kasheni daka sa aketa mutuncin yarinyata gabana..... 5/30/22, 10:15 - Ummi Tandama😇: *Littafin🌹DAN DAKO🌹 na kudi ne biya ki karanta cikin Aminci. Biya 300kacal to 0006454115 Amina Dahiru jaiz bank,or MTN card to this number 09165832002. then send the evidence of payment via 07038423451* ðŸ¤ðŸ™ðŸ¤² Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Yan uwana mata ina kuke ku malmatso ga wanni sirri da nike son baku, ita ya mace sai da kamshi, ina macen da take ganin izgili da wulakanci da ake cewa maza nada shi, hmmm yar uwa to inkin kasance a haka da alama akwai ayar tambaya akanki. Tambaya ta ta farko gareki da wane irin turare kike amfani a jikin ki ?,da wane irin turare kike turara gidan ki,shin dawane irin turare kike Zukunni, hmmm to matso kusa kiji yar uwata. Shi kamshi Annabi muma ya faÉ—a abin sone,kuma Abune mai sanya natsuwa da girmama ma'aboci shi , Da Yawon son kusantar sa. Duk kan wulakanci da izgilanci na maza akwai turaran da zai miki maganin sa da izinin Allah,ba boka ba malam,wanda zai karkato da hankalin mijinki akan ki ku samu fahimtar juna. Ko kin son kamshi na dakusar da fitinar É—a namiji yar uwa? kigarzayo ki kwashi rabonki ga shaharariyar yar mai Dugurin nan mai suna UMSAD INCENSE ,Mace mai kishin mata da son Fiddo martaba mu. Nayi Amfani da turaranta naji masifar daÉ—in da yasa nakasa barwa raina. Nace bari in yaÉ—amuku dan kowa ya mallaki nashi cikin farashi mai sauki. Da fari bari in zayyano muku su kamar haka.👇 Maleek Al'oud Royal kush Cous-cous Kajiji Original sandal Sandal flex Sandal bange VIP mix Hawi Al'oud Kindikay Danal banat Darot Habil Gaf-Gaf Sirrun nisaa'i Sandal chips Kwalacca Humra black and body milk Attractive humra. Yar uwa zanmiki Dallah- Dallah. Akwai turaran da zaki sanyama kayanki . Misali! kisa kabasa kiturare kayanki . Akwai humra da bazaki sataba sai zaki turaka. Akwai turaran kaya ,na jiki, Dakuma na É—aki. Akwai kwallaca sirri, amma bama badata gaskiya sai ga wanda baida kishiya , Dan muddum kina amfani da ita tofa gabaki dayan hankalin mijinki akanki zai dawo,Dan yana juyo da hankalin namiji akanki baki É—aya ,zaki zama shalele Baby, Akwai sirrin nisaa'i. hmmm Dagajin sunan kason na dabanne,na baki sati É—aya ki gwada ki gani Hajiya ta, tsugunno ake akai ga mai buÆ™ata ya tunÉ“e mu ta wannan layin 08028827241 karku manta UMSAD INCENSE mune na É—aya. Muna aika kayan mu duk inda kuke. Kamshin jiki martaba mutum.... 5ï¸âƒ£1ï¸âƒ£&5ï¸âƒ£2ï¸âƒ£ """Banza Sadeeq yayi dashi sai window da yake kallo yana É—an jijjigawa, Tare da goge kwalla da suka zubo mai saboda tinowa da yanayin da suka tsinci kansu kamar haka sadda suke neman taimako daga garesu ,amma saida suka cimma buri . Ihu Bily ke kurmawa yayin da wani basamuden kato ya kaimata ziyara, Tason tayi iskanci kala -kala amma bata taÉ“a haÉ—uwa da Jibgegen gardi ba kamar wannan kasurgumin ba. Cikin kururuwar su ta Arna yake ihu har saida ya cimma buru kana ya koma gefe yana sauke numfashi. Ahaka sukaita ratsa jikinta one bye one tin tana ihu har ta kasa, Saboda sumewar da tayi. Yayin da jinin azaba ke gangarowa daga jikinta yana lailayowa har wajen fuskar Alhaji Musbahu dake kwance kamar ruwa yana kallon yanda ake casu da É—iyar shi. Ita kam Umma sai karta kai take tana siririn kuka, Dan Nene duk ta kwankwashe mata Æ™eya. A Æ™alllah awa biyu suka samu ana musayar Bily wa katti, Wannan ya É—auka yaba wannan ,kana Sadeeq yace'' musu ya isa zasu iya maidota gaban iyayen ta, Dan shi bazai iya yarda yayi kisan kai ba kamar jahili... Kamar tsohuwar mota haka suka jawota gaban uban ta dake kuka kamar ranshi zai fita. Magana yake burin yi amma bakin shi ya kasa buÉ—uwa. Itakam Mamanta tini ta sume. Cikin natsuwa Sadeeq ya jiyo tare da zama akan kujera da yake yace" Wannan kadai na maka dan kaji zafi,Kaji kwatankwacin wanda naji. Cikin awa biyu ina so ka tattara uwar ka da matar ka da yar iska yarka kubar mun gidana . Inko kunÆ™iya zansa a rushe gidan gaba É—aya, kuma wallahi zanbada umarnin a hada daku É—an iska tsoho kawai. Gidan da mahaifina ya gina kuka zauna kuka kwantar da hankali kuna saÉ“on Allah, to kaje Allah yamaka yanda kamun, bazan kashe kaba, bazan kuma kashe kowa naka ba, sai dai nabar wanda yayi ka yayi ni da yamun sakayya, ku tashi ku tafi kubar mun gida ya fada cikin in inaaa Sosai.... Cikin matsananci kuka Alhaji Musbahu yace" kayiman rai Sadeeq, taya zan iya tashi ka gurgunta ni,ina kake so inje bayan komi nawa ka kwace, wallahi kwanannan na rasa duk kan wasu shagunan dana bude,Wayan nan kuÉ—aÉ—an daka karba sune wayanda nike fatan fita dasu inyo sabuwar sayayya. Ina kake so in'koma? bayan bani da komi, kamin rai, kamain halacci Dan Allah Dee ko dan rike ubanka da uwata tayi.... Tsawa sosai ya dakamai jikinshi narawa yace" Sadda kake bibiyar ubana kamar ÆŠan Akuya katina hakuri da yake baka, to ina da labarin komi,kasani wallahi baka ba sake kwana gida na,Kuma uwarka rikon da tamaka tama uban nawa,shegiya tana fama da banzan kanta kwal kamar Toch light. Cikin ihu ya fara basu umarnin a fitar dasu. Da gudu sodojin nan suka fara sungumar Alhaji Musbahu da umma, da bily da Mamanta suka sanya a wata mota, wadda ita kadai ta rage musu wadda yake hawa,haka suka sanya su ciki wani bisa wani kamar awakai. Umarni ya bada da akwashen duk kayan su duka a fita dasu, A kaisu cen wajen gari a ajiyesu da kayan nasu. Cikin lokaci suka fara kwale kayan ÆŠakin, kan kace mi sunma gidan tumÉ“ur. Haka aka kwashesu da kayansu aka nufi cen wajen gari aka sauke su, aka bar musu motar da kayansu jibgi guda suka juya... Alhaji Musbahu tashin hankali ya sashi sumewa, bai Æ™ara sanin inda kanshi yake ba. Bayan komi ya lafa . Sadeeq ya fito yana share hawaye, yayi wajen su Nene. Da sauri Nene ta cimmashi tana mai rungumeshi ta fashe da kuka. Ammi ma kukan take sosai tana tino rayuwar su. Amnah kau zazzaÉ“i mai zafi takeji da ciwon kai wanda ko ido bata iya buÉ—ewa sosai.... Sadeeq ya mike daga jikin Nene yayi inda take zaune. Durkusawa yayi kusa da ita yana mai É—ago haÉ“ar ta yace "my wife minene? kina lafiya ? ko karar bindiga ta tsoratamun ke,, kiyi hakuri kinji matata, kisa ba kinji, inkuma bakyaso kifaÉ—amun aikin da kikso in fara sai in nema. Kai ta gilgizamai tana kuka tace" waye Baba na, shine nike so ingani, wane irin mahaifi ne Allah ya bani mai zalintar iyalin sa... Sadeeq yace Kiyi hakuri yau zamu koma insha Allah, na riga nima dana gama da Abuja har abada yanzu haka takadda transfer nah zanje Æ™arba, na fiso a mayar dani Break din katsina bata kaduna ba, kinga sai musiya gida acen ko bakyaso? Kai ta É—agamai tana faÉ—awa jikin shi. Cikin Æ™asa da murya yace. " Yadai wajen ya daina ciwo ko yanayi ,muje hotel in sake gasaki ko? Cikin jin kunya da.maganshi tayi Æ™asa da kanta. Yace "ok tashi mutafi in_gani.. Mikewa tayi A'hankali tana matse baki... Nene dake kallon su tayi tsaki tace "Saddi ashe kai É—in nan ma jarabbabe ne, ina ganin Amnah zata kadaga amma dan rashin mutunci sai gashi ka É—auketa ka lafta da Æ™asa, wannan ai cutane ,muje ka kaita Asibiti nasan ÆŠinke yal banza zasuyi kamar kwarya... Kan shi ya sosa yace". Taya mace zata kada namiji . Naina dan Allah ki rage sanya ido ,miye ruwanki da har ka mata da miji. Su Mamy kam lokacin nema suka farga da abinda ya faru. Cikin tsananin farin ciki da jin daÉ—i take kallon su, Duk damuwar ta taji ta sauka, Alhamdulillah kawai take faÉ—a da Allah ya hadamata kansu... Waya akama Sadeeq akan takardar shi ta fito . Da murna suka shiga mota zuga guda sukayi wani hadaddan gidan Abinci, Bayan sunci suka É—auki hanya har Kaduna inda da ya fara aiki, Bayan yashiga suka tayashi murna yayi cike- ciken shi na tabbacin dawowar shi aiki kana suka wuce..... Karfe tara na dare suka sauka Katsina ajigace likis dan ma suna tsula gudu. Anan Ammi tace ma Mamy" A wuce da Amnah gobe tinda safe sai suje cen kauyen su. Cikin tsananin jin dadi Mamy tayi godiya. Sadeeq daya anso mota ya taho cikin jin daÉ—i yace "my wife muje gida ki huta ko... Kallon shi tayi ta kwabe fuska tace "Ba Ammi ta hana ba. Ido ya zaro yace mita hana? Tace "wai batare zamu kwana ba,a gidan Mamy zan kwana. Yace" innalillahi wa inna ilaihi Raji'un ,Minai musu,miyasa bazasu faÉ—amun laifina ba in basu hakuri,miyasa zasu horani da rabani dake.?.. Shuru tayi tanayin Æ™asa da kanta , Dan ita komi ma baya mata daÉ—i... Motar ya rufe ya isa ga su Mamy. Kan su an'kara ya duke Æ™asa tare da yin Æ™asa da kanshi yace" iyayena kuyi hakuri Dan Allah, in akwai abinda na muku to akan kuskurene,Amma Dan Allah karku hora zukatan mu ta hanyar raba ganga jikin mu,kubarni da matata mana zan bata kulawar da ta dace.. Nene'' Dake shan Æ™aton mangwaro tace "na shiga ukku ni Aminatu,wai mike damun yaran zamanine,Anya shegiyar allura nan da kuke kaisu ta bbc (BCJ)ake cemata komi ba allura rashin kunya da fitsara bace?. Cikin ta fasa zuciya ya juyo gareta yace'' Nainah Wallahi babu wata kunya da zanji, saboda dukkan su iyayena ne,Babu wani kunya da zanji tunda matata ce ,in'kin son ba sawa zakiyi abani ba to dan Allah Nainah kiyi shuru.. Nene tace'' Bazan ba Kwandon Sukari, dama tinda kaga yau an'baka muÆ™amin soja naga kanata hura hanci, kana Æ™oÆ™arin duka na ,to babu inda zaka da ita sai ta warke, ko-ko so kake abaka ita kaje ka Æ™ara jimata rauni. Ka bari ta warke sumul sai abaka ita salin alun, itama anan zata gwadama jinin su na Gado Daga Mai Malmala shege mai kan gyaÉ—a. Amnah ta saki kuka tace" Nene duk fa lalacewar sa Baba na ne. Tace "oho" ni da yaso ya lalataman É—iya, da yanzu ke kanki yanda yaso maidata wallahi bazaki so kice uwar kibace, wanda ya fasamata mahaifa yasa tana tafiya tana shatato fitsari kamar RaÆ™uma ,aiko kinga ni dashi sai danyen duka shege nason yana nan ya kara kwamushe wa. Amnah ta fashe da kuka sosai jin yanda akwme watsa ubanta tinkan ta ganshi.. Da sauri ya mike ya jawota jikin shi yace" Haba Nainah miye haka? babu fa daÉ—i. Tace kai dakataman fatan ta É—auki darasin rayuwa ,haka taimaka taima dubun ka talakawa ... Yace "Dan Allah kidaina tina baya kowa yason ta canza Wallahi,Matata ta dabance yanzu... Baki ta taÉ“e tana faÉ—in wallahi babu inda zaka da ita , Duk kagama goyen bayan nata kai koma kai kadai. Isa ja muje inga yanda zayyi. Mamy cikin kulawa tace" kayi hakuri my Son kaji muje gida zata dawo kusa insha Allah... Kai ya jinjina yana faÉ—in shikenan tare da É—agamusu hannu suka hau mota, Abba yazo ya tuÆ™a suka wuce ,shima yace Ammi zaibi bazai iya kwana shi kaÉ—ai ba suka tafi.. Kai tsaye gidan Ammi suka wuce, bayan sunje take cemai Sadeeq kaga yanda rayuwa tayi damu ko? Yace eh Ammi amma yanzu komi ya wuce Insha Allah, rayuwa farin ciki zamuyi . Tace shikenan Allah yasa. Yace Ameen ya tashi ya tafi ÆŠakin shi ya É—an lalatsa computer shi kuma ya kwanta, Yayita juyi ya kasa Bacci, dole ya kira Amnah suka kashe dare, saida yaji tayi tsit ya son bacci tayi kana ya ajiye ya rungume pilo ya kwanta... A gidan Mamy kuwa suna isa gida ta shiga toilet tayi wanka mai kyau ta fito, cikin natsuwa ta fara shafe jikinta da kwalacca UMSAD INCENSE mai masifar kyau da kama jiki ,kana ta zuba humra ta shafe jikinta tass ta zira riga marar nawi ta fita, kai tsaye É—akin amnah tashiga ta ganta jwance akan gado tayi shuru. Cikin tsanani tausayi na ÆŠiya da uwa ta kamo hannuta tace "Amnah nason wannan rayuwar zata zo gareki shiyasa naita nausar dake, lokaci ne kike ganin kamar bana sonki, to wallahi baso ne bana miki ba,Aa inaso ne kifahimci rayuwa kamin ranar da zakiyi nadama. Babban jin dadina da kamin ranar tazo kika fara sanyi , Tinda har kinson kirike sirrin gidanki ,kuma baki taba nema daga garemu ba duk da Æ™addarorin ki da muka karÉ“a kika kama mutuncin ki ,kika rungumi zabin da muke maki , Wanda ba akai ko ina ba kingane hakan Alkhairi ne, tinda gashina kun amince da junan ku, kuma kungano yan uwan juna ne ku, ina fata kuskuran da kikayi Abaya Allah ya yafemiki, kana ki tashi mushiga toilet ki gasa kanki. Kisani Amnah kinkai wani matsayi wanda kike da buÆ™atar bama kanki kulawa ta musamman da kanki ,Bawai sai na miki dalla- dalla ba, A'a nason kinsani kin karanta, hasalima É“angaran lafiya mace kika karanta, Dan haka ki tashi muje ki duba kanki ,in kinsamu rauni muje Asibiti, kana zan bada a miki haÉ—i na mussaman, kin son ni bandamu da kai tashan garuruka ba wanda baka son ya aka haÉ—asu ba, Kayan itatuwa sun isheki, tsumin kuma inada mai kyau zan zubamiki galan guda, amma yanzu dole mune mo Yar Barno UMSAD INCENS dan itace kawai zatamun abinda nike so ,akwai Zaujatunoor ta kwalacca da zata haÉ—amana,Amma fa Amnah kiji tsoron Allah, karkiga miji ya rikice akanki kiyi yanda kikeso, inaso ne kisan cewa shi amfani kayanan dan samun zaman lafiya ne, Da rage faÉ—ace- faÉ—ace tsakanin ma'aurata, wanda bana fatan ace kina yinshi, Duba dani da mahaifinki baki taba ji ko gani daga gareni ba , Dan haka ina fatan kiyi koyi dani kinji,Ba wai nace bamayi ba aa munayi amma anan muke dai-dai ta kanmu saboda akwai kyakywar fahimta a tsakanin mu.... Tace to Mamy insha Allah, Amma bansamu matsala ba, kawai dai banajina dai-dai. Tace babu damuwa maza jeki toilet ki gyara jikinki ki gasa kanki da ruwa masu ÆŠumi sosai kinji. Tace to ta tashi a'sanyayye taje ta gama ta dawo lokacin Mamy ta ajiyemata indomie da kwai da tea mai kauri ta ficce wajen mijinta . Bayan taci kaÉ—an tasha tea da yawa suka dora waya da Sadeeq, har bacci ya kwashe ta. Washe gari ta tashi jikinta da sauki sosai Cikin sauri tayi shiri tsaf tayi kyau. Tana gamawa ta kirashi waya anan suka hau fira so da Æ™auna cikin mutuntawa. Bayan ta fito palo ta iske su Mamy ashirye tsab cikin shiga ta kamala. Bayan sun gaisa Abba yace "Amnah muje yanzu ko kamin rana tayi mudawo. Tace to Abba, ta É—auki mayafinta tasa suka tafi zuciyar ta na dukan goma -goma.. Kai tsaye gidan Ammi suka nufa,, inda sukaga motar sodoji Guda ukku sai wata mai masifar kyau Black sai sheki take ... Abba ya musu sallama. a mutunce suka gaishe shi kana suka sanya kai ciki. Suna shiga suka iske Sadeeq tsaye cikin wata dakekiyar shadda mai masifar kyau ash,ya sanya ta kalma ash masu kwalliyar Black, ya zuba hularshi Black data sake fiddo ai'nafin kyan farar fatar shi... Suna shiga da sallama Annabin tayi tsaye tana karemai kallo, ganin rana guda ya canzamata... Shima ganin ta yasa da sauri ya buÉ—e hannuwanshi yace oyoyo my wife yana Linshe ido. Bata an karaba tsumin kaunar shi ya jata take ta fada jikinshi tana mai mantuwa da iyayen su dake kusa . Luf ya maida hannuwan shi ya rufe yana limshe ido jin yanda taketa tashin sassanyan kamshi ... Abba yasaki gyran murya, Mamy kau kai ta kauda gefe tana murmushi.. Sadeeq ya É—agota ya sumbaceta yace muje kiyi kalaci ko. Tace nayi Baby ina Hamrat?. Yace tana ciki ina ga. Wajen ammi ta karasa suka gaisa kana suka fito da niyyar biyawa gidan Nene a É—auketa. Haka suka rufe gidan yan unguwa nata mamakin shiga da ficen da ake da sodoji. Shiga sukayi motar Abba farko wadda shida Mamy da Amal da Ammi ne, , Sai Black din da sadeeq da Amnah sai Hamrat gaba ita da driver dake tuÆ™asu . Sunyi wani masifar kyau sosai, Daga ganin su kason hutu ya fara sallama. Kai tsaye gidan Nene sukaje sukace ta fito. Tace" Babu motar da zata bi, kwara ta shiga tata Mai Malmala ya ganta da azzikin ta.. Haka ta shiga motar da tasha wanki, ÆŠAN Larai ya tuka suka tafi gwanin kyau. Nene ta nuna tsohuwar unguwar su , Bayan sunje aka musu kwatance. " inda tace ta gane suka nufi karamin kauyen . Da tambaya suka gano gida'n. ƘarÆ™atakaf yan kauyen sai leke suke, wasu kuma na guduwa suna ganin kamar anzo kamasu ne, ko wani balai ya kawo musu masu kaki. Su Sadeeq kM GabaÉ—ayan su suka fito cikin kamala da waye wa. Sadeeq ya tausa hannushi cikin na Amnah ya kalleta yana sakin murmushi. Itakam wata irin kunya ta kamata ganin inda aka kawosu gidan agurgure katangar kamar ta kaji. Nene ta fito tana mai É—aukar bakin glass da babu wanda yason ina ta sameshi ta sanyama idonta, tare da É—ago kallabinta tayi ture kaga tsiya, farin gashinta mai yalwa duk ya sakko Æ™asa. Tace zaku iya biyoni in kungama tsayuwar. Da sallama tashi ga gidan tana faÉ—in gafaran ku dai .... Wani dattijo ne ya tsufa sosai ta hango cen saman buzu yanata kilga kudi. Sallama ta sake rafkawa da karfi. Da sauri ya tausa kudin kasan buzun yana faÉ—in". "haba Lami, ban'hanaki wannan iskancin ba, na zoman gaba gadi gandan- gandan kamar Kafura. Nene tace kai mai malmala kallani nan nafi karfin sunan daka kirani dashi . ta faÉ—a tana zare ido. Su Amnah kau jin sautin Nene yasa sukabi bayan ta da sauri... Turusss sadeeq yaja burki ganin tsohon uban gidan sa tsaye da Nene dake nunashi da yatsa. Cikin tsananin mamaki yace" Baba!. Dama kana nan?. Nainah karkicemun dai Baba da nama dakon hatsi shine mahaifin matata?... Sa dauri Amnah ta kalli tsohon da bazata manta fuskar shiba . Ta kalli Nene da hannu ta nuna shi tace "Nene kina nufin wannan shine ubana.? Nene tace yess shine nan ba. Shikam Mai Malmala ido rass yake kallon Annabin yana kallon Nene da Mamy dake baya kusa da Abba. Nene tace Wallahi kana Æ™aremamu kallo sai na kaima shegen kirjin nan naka duka, ka faÉ—i ka mace kowa ya huta, ai'nason ka sanni sarai bakin cikine ke neman saka macewa ko.... Cikin mamaki ya sake kallon Sadeeq yace yaro! ko ba Habu bane nike gani? Sadeeq yace'' nine Baba!. Nene tace shine kuma mijin diyarka ba Aminatu. Affuwan Babu editing 5/30/22, 10:16 - Ummi Tandama😇: *Littafin🌹DAN DAKO🌹 na kudi ne biya ki karanta cikin Aminci. Biya 300kacal to 0006454115 Amina Dahiru jaiz bank,or MTN card to this number 09165832002. then send the evidence of payment via 07038423451* ðŸ¤ðŸ™ðŸ¤² Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Yan uwana mata ina kuke ku malmatso ga wanni sirri da nike son baku, ita ya mace sai da kamshi, ina macen da take ganin izgili da wulakanci da ake cewa maza nada shi, hmmm yar uwa to inkin kasance a haka da alama akwai ayar tambaya akanki. Tambaya ta ta farko gareki da wane irin turare kike amfani a jikin ki ?,da wane irin turare kike turara gidan ki,shin dawane irin turare kike Zukunni, hmmm to matso kusa kiji yar uwata. Shi kamshi Annabi muma ya faÉ—a abin sone,kuma Abune mai sanya natsuwa da girmama ma'aboci shi , Da Yawon son kusantar sa. Duk kan wulakanci da izgilanci na maza akwai turaran da zai miki maganin sa da izinin Allah,ba boka ba malam,wanda zai karkato da hankalin mijinki akan ki ku samu fahimtar juna. Ko kin son kamshi na dakusar da fitinar É—a namiji yar uwa? kigarzayo ki kwashi rabonki ga shaharariyar yar mai Dugurin nan mai suna UMSAD INCENSE ,Mace mai kishin mata da son Fiddo martaba mu. Nayi Amfani da turaranta naji masifar daÉ—in da yasa nakasa barwa raina. Nace bari in yaÉ—amuku dan kowa ya mallaki nashi cikin farashi mai sauki. Da fari bari in zayyano muku su kamar haka.👇 Maleek Al'oud Royal kush Cous-cous Kajiji Original sandal Sandal flex Sandal bange VIP mix Hawi Al'oud Kindikay Danal banat Darot Habil Gaf-Gaf Sirrun nisaa'i Sandal chips Kwalacca Humra black and body milk Attractive humra. Yar uwa zanmiki Dallah- Dallah. Akwai turaran da zaki sanyama kayanki . Misali! kisa kabasa kiturare kayanki . Akwai humra da bazaki sataba sai zaki turaka. Akwai turaran kaya ,na jiki, Dakuma na É—aki. Akwai kwallaca sirri, amma bama badata gaskiya sai ga wanda baida kishiya , Dan muddum kina amfani da ita tofa gabaki dayan hankalin mijinki akanki zai dawo,Dan yana juyo da hankalin namiji akanki baki É—aya ,zaki zama shalele Baby, Akwai sirrin nisaa'i. hmmm Dagajin sunan kason na dabanne,na baki sati É—aya ki gwada ki gani Hajiya ta, tsugunno ake akai ga mai buÆ™ata ya tunÉ“e mu ta wannan layin 08028827241 karku manta UMSAD INCENSE mune na É—aya. Muna aika kayan mu duk inda kuke. Kamshin jiki martaba mutum.... 5ï¸âƒ£3ï¸âƒ£&5ï¸âƒ£4ï¸âƒ£ ""Hankali kwance Mai Malmala yace" Yo ni É—iya gareni Aminatu,, Ai ban haifi Amina ba , Dan haka kuwuce kubani waje, dangin marasa mutunci... Nene ta dakamai tsawa tace kai tsaya jarababban tsoho ubanwa zakama korar kare ,to ba'ayika ba, tsaya kagani . Ma'aikata,! Ta fara kwala ma sodojin Sadeeq kira. Da sauri wani murtikeken kato ya shigo fuska adaure hannushi rike da bindiga. Mai malmala yace Æ™alu Subhanaka la'ilma lana ila ma'alamtana ! Haba jama'a, mi yakai ku zuwa da kufurai makiya Allah, Wayan da basuson Tsoho ko Tsohuwa ba... Nene tace'' Sun kau sani, Amma in dai tsoho na azziki ne ko Tsohuwa azziki, in kau É—an iskane sucimasu uwa dai- dai da dukan da zasuma É—an shekara 20 sabon jini, ai naga zakamana iskancine yanzu zanbashi umarnin fasa É—an kanka mai kama da kofin yara, Dan haka zauna muyi magana. Zama yayi yayin da aka kawo masu tabar ma daga ciki... Nene tace to Alhamdulillah bayan wulaÆ™antamin yarin ya da kayi, kaci mana mutunci, to ga abunda Allah ya baka, kuma ta girma cikin tarbiyya da soyayya uban kwarai, kana bana fatan ka sota wannan ruwanka ne. Yarinya taji tarihin rayuwarta ta matsa akan saitazo taga ubanta, shine muka kawo ta dan kawar da kokonto akan rashin Asalin ta. Wannan kuma da kake gani sunan shi Abubakar Sadeeq ,Sojane, kuma jikanane, kana mijine ga Amina. Dan haka mu zamu juya ke kuma kinga ratattakaken ubanki ko, to ta kuka ta kare tinda kin fahimci ba daga sama kika faÉ—oba, kutashi mutafi muyi abinda zamuyi.... Amnah ta rarrafa wajen Baba'nta ta sanya hannuwanta cikin nashi ta saki kuka tace "Baba baka sona har yanzu kenan ? Shuru yayi baice komi ba sai zuciyar shi dake bugawa. Ta sake matsawa kusa dashi tace baba intafi ?baka sona ?har yanzu ne ?in ka fitar dani daga yaranka Baba sai inkoma inda na fito... Kuka ya saki yace ina sonki Wallahi ÆŠiyata, ina sonki ,ni dama tin ranar da naga kinzo sayen gero Wallahi naji ajikina kedin nan jini nace. A'hankali ya tashi ya isa wajen Mamy ya duka kasa yace" Saude dan Allah, Dan zatin Allah kimin hakuri ,ki'yafeni, wallahi nason na cutar dake ,ban baki kulawa da ta dace ba matsayin ki na Æ™aramar yarin ya mai Æ™ananun shekaru... Nene" tace kai nima zonan ka bani hakuri, ni dama kafi cuta ka taushemun baki,bana um bana uhm uhm... Hakuri ya shiga bata harda hawaye, Amnah kau farin ciki taji sosai ko bakomi duk lalacewar iyayen ka nakane ,kuma baka da kamar su A duniyar ka... Ya koma ga Sadeeq yace" Habu Allah ya maka Albarka, Allah kuma ya hada kanku, ashe Habu dama dai kai mai kudine shiyasa akaÆ™i yarda da kai ko? Sadeeq yace" ai'kai ka yarda dani Baba, Nagode Allah ya Æ™ara tsawon rai, bazan taÉ“a manta Alkhairi ka gareni ba, Saboda ba Dan korar da kamun ba bazan ga Ahlina ba,Da matsayina na da baidawo ga reni ba,Ga kyakyawar mata daka haifamun tsakanina da kai sai godiya... Yace "Ameen yana mai jin kunyar abinda ya masa. Nene tace'' ka sake mai godiya da rokon ya rike jinin ka hannu biyu, Dan gabaki daya jarabaka yarin ya nan ta kwaso, ina tsoron jikan ya koma tsololo Wallahi ta shanyeman shi kadai ganshi kakkaura kirar Æ™arfi... Mai Malmala yace "Kuyi hakuri Hajiya Nene , Nima Wallahi lalurine da kuma halitta. Nene tace oho dai ,Allah ya kwaci ÆŠiyata, da yanzu fallan zani sai yafita kyan gani.. Gaba É—aya kunya ta kamasu ,amma ita ko ajikinta ... Ahankali Mai Malmala ya mike yace" Bari in É—akko mata magani, insha Allahu zata dawo dai- dai da halittar mijinta ,babu cuta ba cutar wa a tsakanin su.. Wani irin faÉ—uwa Sadeeq yaji gaban shi yayi, shida ke fatan kasan cewa da ita akaro na biyu kuma amai wannan sagegeduwa, ya fara raba idanuwa yana gudu amasa illah da bayajin zai jure... Kai a Æ™asa yayi gyaran murya tare da cewa" Nace Baba da ka barshi, duk jinsun mu É—aya ne Wallahi... Azabure Nene ta cire glass dinta, yayin da ta kalleshi sama da Æ™asa tace" Na shiga ukku, na bani na lalace, yanzu ta gidan uban wa ka gane bayan Karan ku É—aya,Taya zaka tantance yanzu ,Daga haÉ—a alaÆ™a so É—aya zakacemun haka Dan kajaman sharri. Ta saki kuka tare da cewa Wallahi Dan sujaman sharri , Kuma ni harna Æ™are rayuwata ma tsoron Bashari nike ,inajin kamar in hau tsani in kwana saman katanga saboda kunya, Amma ku kau yan iska jarababbu har faÉ—amana kuke . Kai dawo ka zauna mu muntashi ma taÆ™arasa a fusace. Mai Malmala ya zauna yana murmushi yace ma Amnah. Aminatu ina so kimana sati biyu ko ukku dan ki saba da dangin ki ko? Ya ilahil alamina Amnah tace, tana mai jin tsananin faÉ—uwar gaba. taya zata iya rayuwar gidan da ko kyaure babu, sai tsohon zani da a kasa aka rufe Æ™ofar.... Sadeeq yace "am Baba Dan Allah kayi hakuri, zan maidota da kaina insha Allah,Saboda yanzu batajin daÉ—i, kuma akwai buÆ™atar kulawa ta mussaman daga gareni... Kai Baba'n ta ya jin-jina yace" shikenan tare da zaro tsohuwar naira Hamsin ya miÆ™amata, yace'' ungo kisha ruwa da alawa. Dariya mai haÉ—e da hawaye tayi kana ta karÉ“a ta mai godiya. Yayin da ya É—auki naira goma yaba Amal yace" ungo ke ma. Nene tace kadaiji kunya matsolon banza matsolon wofi, uban yarin ya nan baitaÉ“a ban-banta taka da tashi ba ,Hasalim yafi yima taka gata sama da tashi, Amma ji abinda kaba yarshi ,kai kumaida mai Dan ubanku ko in zubamaku mari ta faÉ—a a fusace. Baban Amnah yace" tsaya fa Tsohuwa Sirikata, babu ta yanda zanyi in'saki kudi ina almubazaranci da su, Bayan naga yara tula- tula alamun babu abinda suka rasa, tomi zasu siyama in na basu da yawa? Nene ta mike tana gyara glass dinta tace" ku tashi muje kar takaici ya Æ™arasani. Shima Baban Amnah ya mike yace "Dan Allah ku biyoni ciki in'gwadamusu ga ÆŠiyata ta dawo gareni ... Ba suce komi ba ya fara tafiya sukabi bayan shi har tsakar gidan da yake kaca -kaca da kwanikka, ga awakai da kaji ,ga yara gasunan dai kwatsa-kwatsa kamar Æeraye, Ƙananu kuma sai rarafe suke ,wasu atsaye fuska ta kwaÉ“e babu kyan gani. Wani irin masifaffan amai ya kawoma Amnah ziyara lokacin da taga yanda komi yake a wulakance. Da sauri Sadeeq ya jawo ta jikincshi yana É—an shafa bayanta yace" ki!daina Sweety kinji, karsuga kamar akwai cin fuska. Shuru tayi suna shiga yar rumfar dake gefe. Mai Malmala yace "kai ga diyata tazo da Æ™afarta nemana Saboda tason daraja uba,Kukau Munafukan sai kallonta kuke kunga baturiya ,To albishirin ku Soja take aure, Duk É—an iskan daya tanka yanzu zaiga kwalwarshi a watse tsakar gida nan .. Da gudu uwar gidan shi ta shiga É—aki ta dakko tabarma ta shimfiÉ—a musu. Nene ta taÉ“e baki tace" bazamu zauna ba, gaskiya wucewa zamuyi, ga yar uwarku nan ankawo maku ,in kuna son ganin ta kuyi wanka mai kyau kuje ku ganta.. Aiko Æ´aran da sunkai talatin da wani abu suka zo suka fara maÆ™alÆ™ale Amnah suna tsalle, wasu nason taÉ“ota sai jujjuyawa take, Dan gabaki É—aya sunÉ“ata mata kaya da datti. Wani ÆŠan saurayine da yakai shekara shabiyar ya daka tsalle ya hayota da karfi yana faÉ—in" Bani biyar Yaya. Kuka ta saki tana faÉ—awa jikin Sadeeq tace muje Dan Allah Baby bazan iya ba. Kudi masu yawa Abba ya basu suka ficce suna toshe hanci. Mai malmala yayi sufa ya kwashe kuÉ—in ya fito yana washe baki . Yace" su sauka lafiya ya Dawowar sa ciki. Bayan sun tafi Abba dake gaba ya É—auki hanyar Goruba roud. Sadeeq kam cikin mamaki suke binshi badan sunson inda zaya ba. Saida yazo wani Katafaran gida mai masifar kyau tindaga Æ™an get É—in zakason cewa lallai an kashe maÆ™udan kuÉ—aÉ—e wajen aiki sa. Wani kyakyawan remote ya fiddo ya latsa take get É—in yayi sama suka fara shiga ciki. Bayan duk sun shiga ya maida ya rufe, Fuskar Abba cike da murmushi ya karaso wajen Sadeeq ya mikamai hannu , Tare da bashi wani key yace my Son ga gida'n ku..... Cikin mamaki suke kallon shi , yayin da Nene kuma tace kushigo in nuna muku. Shiga sukai wani tafkeken palon daya linka na gidan Mamy so Biyu girma da kyau, ga wasu mahaukatan kujeru milk da Brown dake sanye cikin leda, Da labulaye komi dai na palon yaji dan yayi masifar kyau . Cikin Mamaki Ammi tace" Alhaji isa kunsani a duhu fa?. Yace" Doctor tin ranar da na dauki kudin ki na fara juyawa na fadama Nene ya zanyi da rivar da ake samu, gashi bangankuba. Tace da aita ta rata kwara ace ansai abu mai amfani ana ajiye wa, Duk ranar da Allah ya bayyanaku sai indamÆ™amuku a bunku, yanzu Doctor ribar kudinki ne ya gina miki wannan gidan , Harma da katafaran masallacin da kika gani waje wanda shidama tuni nayi karambani buÉ—eshi ina fata ya zama sadaÆ™atul jariya wa mahaifin Sadeeq da Hamrat... Gwal inki kuma suna nan an'miki sabbi na zamani, an baki ribar wancen da kika samu , Dan haka yanzu muje sama komi naku na nan a ajiye, kuma part biyu ne kinga saiki baro cen ku dawo nan dazama ya isheku ko?.. Nene tace tabbas kuwa ya wadatar,kuma zatana kula da lamarin yaran nan dake son cinye juna.. Cikin tsananin murna da farin ciki irin rikon Amana da ya masu Ammi tayi sujjada godiya ga Allah, ta fara masa godiya da kirarin baiwar da ya musu,Bayan ta gama ta hau godiya ga Abbah ... Yace mata babu komi dukiyar su gabaki É—aya ya haÉ—ata zuwan da sukayi ya tattaro komi, kuma shima ya dawo kusa da iyalin shi dan sunfiye mai zama cen nesa. Farin ciki sosai Sadeeq yaji lokacin da aka mikomasu kuÉ—in. Amnah kau sosai jikinta yayi sanyi , Allah ya rufamata asiri da yanzu tason sadeeq korata zayyi Da bata gyara halinta ba.. Murna sukayi sosai suka tashi tafiya. Sadeeq yace'' Sweety zauna in rakasu in dawo. Ammi tace ai ba yau zamu dawo ba, sai anma gidan Saukar Alkur'ani kana ,ko nan da sati biyu haka..... Ido shi ya zaro yace" Ammi Dan zatin Allah kubarni da matata,hab har yaufa bansamu damar keÉ“ewa da ita ba fa tin jiya da safe, bafa ta da lafiya na faÉ—amuku taya zakuna rabamu bayan banji daga gareta yanayin jikin nata ba. Nene tace'' kai Wallahi gidansu zata, sai ta warke zata dawo,muma aimun fahimci bata da lafiya rasa kunya É“eran tanka,basai ka fadamuna ka santa ta sanka ba ... Yace shikenan Nainah gatanan ku wuce. ya fada yana fita cikin fushi ya faÉ—a mota suka hau suka tafi... Nene tace kadawo É—an banza, Tinda yanzu kaga kafara canza sutura zuwa ta kakin soja ai'kwara kafara mana baÆ™in hali ,Amnah bazata koma ba sai taji sauki sumul .... 5/30/22, 10:57 - Ummi Tandama😇: *Littafin🌹DAN DAKO🌹 na kudi ne biya ki karanta cikin Aminci. Biya 300kacal to 0006454115 Amina Dahiru jaiz bank,or MTN card to this number 09165832002. then send the evidence of payment via 07038423451* ðŸ¤ðŸ™ðŸ¤² Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Yan uwana mata ina kuke ku malmatso ga wanni sirri da nike son baku, ita ya mace sai da kamshi, ina macen da take ganin izgili da wulakanci da ake cewa maza nada shi, hmmm yar uwa to inkin kasance a haka da alama akwai ayar tambaya akanki. Tambaya ta ta farko gareki da wane irin turare kike amfani a jikin ki ?,da wane irin turare kike turara gidan ki,shin dawane irin turare kike Zukunni, hmmm to matso kusa kiji yar uwata. Shi kamshi Annabi muma ya faÉ—a abin sone,kuma Abune mai sanya natsuwa da girmama ma'aboci shi , Da Yawon son kusantar sa. Duk kan wulakanci da izgilanci na maza akwai turaran da zai miki maganin sa da izinin Allah,ba boka ba malam,wanda zai karkato da hankalin mijinki akan ki ku samu fahimtar juna. Ko kin son kamshi na dakusar da fitinar É—a namiji yar uwa? kigarzayo ki kwashi rabonki ga shaharariyar yar mai Dugurin nan mai suna UMSAD INCENSE ,Mace mai kishin mata da son Fiddo martaba mu. Nayi Amfani da turaranta naji masifar daÉ—in da yasa nakasa barwa raina. Nace bari in yaÉ—amuku dan kowa ya mallaki nashi cikin farashi mai sauki. Da fari bari in zayyano muku su kamar haka.👇 Maleek Al'oud Royal kush Cous-cous Kajiji Original sandal Sandal flex Sandal bange VIP mix Hawi Al'oud Kindikay Danal banat Darot Habil Gaf-Gaf Sirrun nisaa'i Sandal chips Kwalacca Humra black and body milk Attractive humra. Yar uwa zanmiki Dallah- Dallah. Akwai turaran da zaki sanyama kayanki . Misali! kisa kabasa kiturare kayanki . Akwai humra da bazaki sataba sai zaki turaka. Akwai turaran kaya ,na jiki, Dakuma na É—aki. Akwai kwallaca sirri, amma bama badata gaskiya sai ga wanda baida kishiya , Dan muddum kina amfani da ita tofa gabaki dayan hankalin mijinki akanki zai dawo,Dan yana juyo da hankalin namiji akanki baki É—aya ,zaki zama shalele Baby, Akwai sirrin nisaa'i. hmmm Dagajin sunan kason na dabanne,na baki sati É—aya ki gwada ki gani Hajiya ta, tsugunno ake akai ga mai buÆ™ata ya tunÉ“e mu ta wannan layin 08028827241 karku manta UMSAD INCENSE mune na É—aya. Muna aika kayan mu duk inda kuke. Kamshin jiki martaba mutum.... 5ï¸âƒ£5ï¸âƒ£&5ï¸âƒ£6ï¸âƒ£ Mamy tace'' Nene wannan bai kamata ba, yazo ya É—auketa sutafi kawai. Ammi tace "barshi kuje gida kawai . Haka sukatafi Amnah kuma batace komi ba, Dan jikinta yayi sanyi matuÆ™a.... Sadeeq kam bayan fitar shi kai tsaye wajen saida motoci suka nufa, ya siyo wasu dallah- dallah guda biyu nashi wayanda zai dinga fita dasu , Sai guda É—aya wadda tafi tashi sada mai masifar kyau. Daga nan ya badasu aka kaisu gidan da zasu koma suka wuce. Kai tsaye Army Break suka nufa. Bayan sunje aka gwalgwadamishi mutanan da zasuna kulawa da lafiyan sa, da wayanda zai ajiye gidan shi , Da haÉ—É—an office din shi mai masifar kyau... Farin ciki sosai yaji ya mamaye ranshi. Anan wani matashin Saurayi da shekarun su bazai wuce daya ba ,mai kyau sosai ya iso wajen shi ya saramai yace" Yallabai ina matuÆ™ar sonka ,ambani tarihin jarumtar ka inaso inyi koyi da kai,in'babu damuwa ina so muzama Abokin ni sunana Abbas. Lokaci guda Sadeeq ya samu aminci dashi ya mikamai hannu suka gaisa a mutunce, kana yaÉ—au hanya da niyyar sai monday zaifara fita aiki ,Dan muna Thursday. Bayan suntafi kai tsaye gidan Ammi ya isa yana kumbura baki. Ammi tace'' zonan Dee. Bayan ya isa tace'' Dee nah kasan mene yasa nace ta koma gidan su? Kai ya gilgizamata yana sadda kanshi Æ™asa. Tace Saboda yakamata ace mun haÉ—a gagarumar walima ,Mu mata lefe muma da kayan kece raini saboda ta haihu Yar halak,tinda Allah ya kawo muna wadata kwara itama ta sheda. Inaso ka shiryamun tafiya Dubai yau ko gebe . Ga Hamrat nan ka É—auketa ka kaita gidan Nene ,Kacemata tazo mata sati daya kaji ko,Karka faÉ—a mata zanyi tafiya ba... Kai ya gilgiza cikin gamsuwa da bayanan ta yace''shikenan. Fita ya sakeyi yama rasa wazai kira, dan shi duk ya manta wasu abubuwan. Abbas ya faÉ—omai arai, bayan sunyi waya yace'' Aboki kana ina ? Ammi nah zatayi tafiya inaso inganka. Cikin tsananin jin dadi Abbas yace "ganinan zuwa yallabai , Bani mint kadan kuma ka turoman address din gida'n. Dee yace shikenan sai kazo yana mai kashe wayar ya turamai, yayi n da yayi zaman shi bisa mota yana mai latso number Amnah. Bayan ta É—auka tace" Baby ya kake. Yace babu lafiya sweety.. Azabure ta mike tana fadin minene! mike damunka? kana ina haka? . Yace masifar zazzabi nike da ciwon zuciya, Amnah ina buÆ™atar ganin ki yau ko gobe, in kau har kika hanani zaki tsinci gawana.. Kuka tasa tace'' haba Dan allah kadaina fadamun haka, yanzu kana ina ,kazo gidan Mamy yanzu inganka wallahi bata barina fitowa. Da sauri ya diro daga motar yace shikenan anjima zanzo ya kashe wayar yana Sakin huci mai zafi .. Yana tsaye saiga Abbas da motar shi , Bayan yazo suka gaisa kamar sun daÉ—e da sanin juna, anan ya nunamai yanda zayyi komi ta online hankali kwance cikin É—akin ka. Cikin lokaci akama Ammi komi zata hau jirgi daga kano zuwa Abuja, daga Abuja zai cala dasu. Godiya ya mashi sosai kana ya wuce. Sadeeq ya koma ciki ya mata bayani, Taji daÉ—i sosai hakan yasa ta haÉ—ama Hamrat kayan ta tace" ya wuce da ita tinda yamma. Hamrat kau taita murna zata wajen Nene. Bayan ya isa gidan ya shiga har palon ta kai tsaye. Inda ya iske Nene zaune tasha wanka tana taunar naman kaza, daga gefe kuma ga sassanya fura mai sanyi sosai tana korawa. Zama yayi fuska a É—aure . Da sauri Nene ta mike tana fadin oyoyo ga Hamami kike ko ÆŠoyi? Hamrat ta fashe da dariya yayin da tace" ke Aunty Nainah Hamrat fa. Nene ta rike baki tace" minikeji haka yarinya, ni kike cema Aunty, Dan ki wulakantani, to kar inkumaji, Nene sunana, ko kice Hajiya Nene, Dan isa ya kaini makka so biyu. Hamrat tayi Murmushi tace "Nene to zankwana anan inji Ammi. Nene tace "Alhamdulillah kaga yanzu nason nayi jikanya, su kau wayan cen in'sunzo kwana biyu suke su koma, aiko bazaki sake komawaba tinda ina da hakki mai girma kanki ko Hamta. . Cikin dariya Hamrat tace" eh tana kallon sadeeq daya É—aure fuska. Nene kam ta shiga labari da Hamrat tayi shuru ta kyale Sadeeq. Yace'' nainah bakison ina fushi dake ba? Tace ikon Allah Bashir mi naimaka?. Cikin mamaki yake kallonta yace'' Bashir kuma? Tace ta yo eh mana, naji kana bani wani umarni irin kamar kai ka haifeni, ko kuma Æ™asan igiyoyin auran ka nike ,to wallahi ba ayika ba sanholo kawai ,ka É—auka tsoronka zanji. Sakkowa yayi Æ™asa cikin lallashi Yace" to Nainah naji kiyi hakuri bazan sake ba , Amma dan Allah ki taimakamun kicema Mamy Amnah tazo nan ,ina kunyar ta wallahi, Dan Allah ta dawo nan gidan da jinya, wallahi Nainah bazan É“oyemiki ba ina kewar matata ,ina tsoron faÉ—awa halaka ta rashin ganinta kusa dani ,Nainah Dan Allah. ya karasa kamar yayi kuka. Dariya sosai Nene tasa tace'' shegiya mace mai maida soja É—an daudu. To kayi hakuri mana har saita warke. Yace shikenan Nainah ga Hamrat nan, ni na wuce. Tace ok sauka lafiya. Cikin takaici ya DuÆ™a ya kwashe kajin da furar tanacen tanama Hamrat magana ,akan ta kai kayanta É—akin su Amal ya ficce. Bayan ya shiga mota ya tada ya fita. Kai tsaye wani Katafaran shago yaje yasiyo wayoyi masu kyau guda biyu, ya fito yaje gidan Ammi. Bayan yaje suka É—an tattauna kana ya shige dakin shi ya jona charge. Ana gama mangariba yaji wanka mai kyau ya dakko waya É—aya ya saki murmushi ya fita. Anan ya iske wani gandareren kato shida Abbas tsaye. Cikin mamaki suka gaisa yace "bakamun waya ba Aboki zaka zo. Abbas yace "Yallabai Wallahi jirgin da Ammi zatabine tashin asuba zayyi, to shine kawai nazo da aminataccen driver da aka baka kan ya kaita , Dan kaima oga Ali na nemanka da safe balle mumata rakiya. Yace "shikenn ya shiga ya faÉ—ama Ammi. Cikin jin dadi ta tashi ta É—auki yan abubuwan buÆ™ata suka fito yanatamata Addu'a. itama tana mishi. Motar David ta shiga suka dauki hanyar kano. Yayin da ya rufe gidan suka shiga Motar Abbas suka É—auki hanya gidan su Amnah yana nuna mishi har suka isa. Bayan sun isa ya gaisa da Baba madu a mutunce suka kutsa kai. Abbas yace" Yallabai ni juyawa zanyi. Sadeeq ya kalle shi yace" Abbas lokaci guda naji na amince da tayin Abotar da kamun , Dan haka babu zancen Yallabai, muddum ba wajen aiki mukeba, ka kirani da Aboki ko sadeeq kawai zanfi jin daÉ—i. Yace insha Allah Aboki. Yace yawa nan gidan su matata ne kuma cousin muke da ita, zanshiga in'zakaje muje. Yace ''A'a Aboki watarana zanje, zan tafi gida wajen Umma nah tana jirana . Sallama sukayi ya fita da motar shi... Da sallama ya shiga gidan inda ya iske su zaune su duka , Amnah ce kawai babu. Amal tace Yah Dee ina wuni ya gajiya? Yace lafiya klau Sister ya kike?. Tace Alhamdulillah. Bayan sungaisa dasu Mamy yayi shuru yana motsa baki. Many ta taÉ“o Abba ta gwadamai shi da ido. ya saki murmushi yana mata alamun sutaimakamai su bashi abinshi. Kan tayi magana sukaji Sadeeq yace Mamy ya Amnah da jiki ,ga waya na siyo mata tata ta faÉ—a ruwa yafaÉ—a yana raba ido dan baya son karya, Shiyasa in yayi zakaga yanata wiki- wiki da ido . Da sauri Abba Yace" tashi ka shiga ka bata da kanka tana ciki. Kanma su Æ™arasa aguje ya mike yana tura É—akinta ya shiga, sai jin Æ™arar key sukai. Da sauri Abba ya mike Mamy tace ma Amal kije ÆŠaki ki kwanta ki huta gajiya. Amal tayi murmushi ta mike ta haura sama. Mamy kam bayan Abba tabi a ai'nda ta iskeshi bakin kofar É—akin shi yana tsaye. Tana isowa ya buÉ—emata hannu ta fada jikinshi. Yace" Dear Ke kadai kikeso kiji dadi banda yaran namu ne. Tace" ba haka bane inaso ne taji sauki dan nafahimci taji rauni. Yace ai sunmayi hakuri fa, sama da wata biyar kuma kana lafiyayye ga mace a gida, taya zan iya wannan sagegeduwar. Dariya Mamy tayi tace" Kai Hubby. Yace Allah shiyasa na rufama kaina asiri na gudo wajen matana. Ciki sukayi suna dariya. Sadeeq kam yana shiga ya rufe kyauran. Anan yaga Annabin kwance akan gado daga ita sai wani É—an karamin wando da vest duka orange, sun haska farar fatar ta ,sai black din hula tayi masifar kyau. Da mamaki take kallon shi dan yace mata baya lafiya. Yayinda shikuma yayi tsaye ya harde hanneyen shi duka ya zubamata ido yana ganin har wata rama taÉ—anyi kaÉ—an, sai uban fari kamar ta fashe jini ya zubo.. A'hankali ta taso ta iso gareshi tace" Baby ka Huce?. Yace Amnah bana fatan Allah ya Nunamin ranar da zanyi fushi dake, kawai Nainah ce ta É“atamun rai . Jikinshi ta fada tace" nayi missing dinka sosai baby wallahi. A'hankali ya sanya hannuwashi ya rike mazaunanta yana mai É—ago kyakywar fuskarta ya danna bakin shi cikin nata , cikin tsananin bukatuwa yake tsotsar sirara Laɓɓan bakinta yana sauke ajiyar zuciya. Sosai jikin Amnah ya É—auki rawa ganin haka yasa ya jata har bisa gado,ya kwantar da ita yana mai zama bakin gadon Yace"My wife ki barni in samu gamsuwa daga gareki,wannan kyarma banaso kinayinta in kinganni Amnah, zafin farkone kawai zakiji, amma duka sauran rayuwar ki dadi ne zai dinga kawomiki ziyara kinji. Kai ta É—agamai. hakan ya sa Ahankali ya cire riga,rshi ya ajiye gefe tare da cizge dogon wandon ya bar karami ya jawota jikinshi.. Ajiyar zuciya ya hau saukewa, tare da fara wasanni da ita masu zafi . Sai da taga yana Æ™okarin zarce lagos ta sakamai kuka, tana faÉ—in Baby akwai fa zafi har yanzu, dan Allah ka daina agidan Mamy fa muke.. Yace Amnah babu ruwa na ,ni dai nason halaliyata nike nema, kibarni Dan Allah inji É—umin jikin ki kawai. Kuka tasa mai sosai tana fadin ka daina Dee . Gefe ya kom yana sauke numfashi , tare da matse marar shi sosai yanajin kamar ya saki ihu.. Da sauri kuma ya mike ya shiga sanya kayan shi, yana gamawa yace ga waya nan na siyo miki nagode ya ficce da sauri yana sake gyara zaman rigar shi. DaÉ—i yaji sosai da yaga ba kowa Palon, hakan yasa har gudu -gudu yake ya ficce da sauri . Amnah kau cikin tashin hankali ta mike tana kwalamai kira amma kamin tazo har Ya ficce. Wayar shi ta fara kira, Ganin haka yasa ya datse tare da kasheta baki É—aya. Yana isa bakin Titi ya hau machine ya nufi gidan da suka zauna da ita. Bayan ya isa ya buÉ—e gidan ya shiga ya rufe. Ahaukace yayi ÆŠakin yana fitar da wata zufa mai zafi, sai hura baki yake. Inda kayanta suke lode bisa kujera ya kalla. Rigar data kwana da ita ranar da ya Æ™arbi Budurcinta , Ya É—auka ya ajiye gefe. Tare da sunce kayan shi duka ya faÉ—a wanka. Bayan ya gama yazo ya fesa turare. Tare da É—aukar rigar ya É—akko pilo É—aya ya sama rigar Amnah. Kwanciya yayi ya jawo shi jikinshi a rikice Yace" Matata in samu natsuwa dake ko? nason ke zaki amincemun , Nason bakyamun rowa ,kece kaÉ—an zan raÉ“a inji gamsuwa ta Mussaman. Ahankali ya fara shafa pilon yana jinshi kamar Annabawa saboda gabaki daya kamshin jikinta yake. Lokaci guda ya ficce hayyacin shi ya fara sambatu yana ihu saboda rikitatta Humra UMSAD INCENSE da ta dake tsumuwa da kamshi, Baisamu sukuni ba sai da yaji ya samu gamsuwa kana ya koma gefe yan sauke numfashi fuskar shi cike da annuri. Bayan ya huta ya tsaftace jikinshi ya jawo pilon jikinshi ya kwanta yana mai tsananin jin daÉ—i yace''Allah ya miki albarka My wife. Ahaka bacci ya kwasheshi cike da gamsuwa . ********** Asubar fari Amnah ta shirya tare da mikewa ta fito palo ta gaida Mamy da Abba. Bayan sun amsa tace" Mamy zan wuce gida na, jiya fushi yayi ya tafi wallahi. Tsororo sukai suna kallonta , Mamy ta dakamata tsawa tace. " Baki wucewa kiban wuri, koma ciki. Cikin kuka takoma tana diddire Æ™afa, Dan som bata samu bacci ba, ganin ranshi É“ace ya fita batason wani yanayi zai shiga ba. Sadeeq kam yana tsananin son yaji muryar ta, amma ya kyaleta, Dan yanaso ta fahimci yaji zafi daya nemeta ta hana,Bayan tason bayada wata sai ita. Bayan sati É—aya. Mamy sosai take gyara Amnah da kayayyaki masu inganci, mussman É“angaran kamshi mai sirri da yawa na UMSAD INCENSE Da batajin zata iya amfani da wani kayan in ba nata ba,Shiyasa duk in suka giftaka sai ka kallesu.. Har lokacin kuma Sadeeq bai kara zuwa ko yimata waya ba. Dan har aikima ya koma, kuma sosai sukejin daÉ—in aiki dashi, Dan akwai gaskiya da amana, a gefe guda kuma makale yake da son Amnah, amma ya fiso randa zasu kasance dashi takasa gardama ma buÆ™atun sa,tinda ta fajimci baya so. Washe gari Ammi tayi saukar yamma da kaya niki -niki . Da daddare suka zauna suka gani, farin ciki kamar mi, Dan hada manya- manya sarka na gold aka sama Amnah kaya masu kyau da inganci som babu tarkace. Anan suka fiddo akwatina set ukku suka shirya kayan gwanin sha'awa. Washe gari Sadeeq ya É—akko motarm da ya saima Amnah suka shirya kayan tsaf a motar kana Devid ya shiga. Yayin da Sadeeq ya É—akko É—ayar mai kyau yacema Ammi ta shiga ciki. Shiga tayi baya shikuma ya tuka suka fita. sunyi masifar kyau cikin shiga ta kamala. Anan suka doshi gidan Mamy kai tsaye. Bayan sun sauka Sadeeq yace da David ya fara kwasar kayan ya kai bakin Æ™ofa Mamy da yamai nuni da hannu.. Kwasa yayi duka ya ajiye. Sadeeq ya ÆŠan kwan-kwasa kofar kaÉ—an ya tsaya abasu izini. Amnah dake zaune palo tana ta gwada wayar shi ta taso ta buÉ—e. Cikin tsananin mamaki da farin ciki take kallon shi,Bata taÉ“a zato ko tsammani ba... Murmushi ya sakar mata yana É—aga gira. Mamy ta fito daga Palon ta tana faÉ—in" Amnah waye ya shigo da mo... Ganin su tsaye suna kallon juna yasa da sauri ta isa tace A'a wai dama Sadeeq ne ,to shigo mana. Kanshi ya sosa yace mamy ina wuni. Tace lafiya klau shigo. Yace ga Ammi nan da kaya zasu iya shigowa dasu.. Cikin tsananin farin ciki tace sannu da zuwa Aunty nah shigo ciki manaj . Mamy ta shigo hannuta rike da karamin akwatin da gold din ke ciki. Sadeeq ya tsaya yaba Devid umarnin ashiga dasu ciki. Shiga ya farayi dasu cikin kuzari, saida yagama tsaf ya bashi key din motar. Amnah kau kamar ta mace Dan mamaki ,taga bai koyi murna da ita ba. Key din ya mikama Ammi kana ya fito yaga har lokacin Amnah na tsaye takasa motsi... Kumatunta ya É—an ja kadan yace "koma ciki ni zan wuce Yam mata yafada yana mai shafata ya gifta yana sakin Murmushi. Ganin ya shiga mota yasa da sauri ta biyo bayan shi........ 5/30/22, 21:13 - Ummi Tandama😇: *Littafin🌹DAN DAKO🌹 na kudi ne biya ki karanta cikin Aminci. Biya 300kacal to 0006454115 Amina Dahiru jaiz bank,or MTN card to this number 09165832002. then send the evidence of payment via 07038423451* ðŸ¤ðŸ™ðŸ¤² Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Yan uwana mata ina kuke ku malmatso ga wanni sirri da nike son baku, ita ya mace sai da kamshi, ina macen da take ganin izgili da wulakanci da ake cewa maza nada shi, hmmm yar uwa to inkin kasance a haka da alama akwai ayar tambaya akanki. Tambaya ta ta farko gareki da wane irin turare kike amfani a jikin ki ?,da wane irin turare kike turara gidan ki,shin dawane irin turare kike Zukunni, hmmm to matso kusa kiji yar uwata. Shi kamshi Annabi muma ya faÉ—a abin sone,kuma Abune mai sanya natsuwa da girmama ma'aboci shi , Da Yawon son kusantar sa. Duk kan wulakanci da izgilanci na maza akwai turaran da zai miki maganin sa da izinin Allah,ba boka ba malam,wanda zai karkato da hankalin mijinki akan ki ku samu fahimtar juna. Ko kin son kamshi na dakusar da fitinar É—a namiji yar uwa? kigarzayo ki kwashi rabonki ga shaharariyar yar mai Dugurin nan mai suna UMSAD INCENSE ,Mace mai kishin mata da son Fiddo martaba mu. Nayi Amfani da turaranta naji masifar daÉ—in da yasa nakasa barwa raina. Nace bari in yaÉ—amuku dan kowa ya mallaki nashi cikin farashi mai sauki. Da fari bari in zayyano muku su kamar haka.👇 Maleek Al'oud Royal kush Cous-cous Kajiji Original sandal Sandal flex Sandal bange VIP mix Hawi Al'oud Kindikay Danal banat Darot Habil Gaf-Gaf Sirrun nisaa'i Sandal chips Kwalacca Humra black and body milk Attractive humra. Yar uwa zanmiki Dallah- Dallah. Akwai turaran da zaki sanyama kayanki . Misali! kisa kabasa kiturare kayanki . Akwai humra da bazaki sataba sai zaki turaka. Akwai turaran kaya ,na jiki, Dakuma na É—aki. Akwai kwallaca sirri, amma bama badata gaskiya sai ga wanda baida kishiya , Dan muddum kina amfani da ita tofa gabaki dayan hankalin mijinki akanki zai dawo,Dan yana juyo da hankalin namiji akanki baki É—aya ,zaki zama shalele Baby, Akwai sirrin nisaa'i. hmmm Dagajin sunan kason na dabanne,na baki sati É—aya ki gwada ki gani Hajiya ta, tsugunno ake akai ga mai buÆ™ata ya tunÉ“e mu ta wannan layin 08028827241 karku manta UMSAD INCENSE mune na É—aya. Muna aika kayan mu duk inda kuke. Kamshin jiki martaba mutum.... 5ï¸âƒ£7ï¸âƒ£&5ï¸âƒ£8ï¸âƒ£ ----------- Tinda yaga yanda ta tafo a furgice yake sakin muskilin Murmushi. Tana Æ™arasawo ta buÉ—e kofar baya inda yake ta shiga . Yace da David"bamu wuri. Yace ok sir yana fita waje. Juyowa yayi ga Amnah yace ya dai Sweety nah.? Kuka ta samai tace" minai maka, Duk ka canzamun, ba haka ka sabamun ba, babu oyoyo babu komi, babu nuna kayi missing É—ina kamar yanda nayi naka, babu magana sai Æ™oÆ™arin katafi ,kenan bakason kasancewa dani, miyasa ka kashe wayar ka, laifin minaima ka.?... Kyakyawan sajenshi ya shafa yace "ko É—aya my wife, ke ai bakya laifi wallahi ,kawai nabar ki kisamu natsuwa ta mussaman, Saboda kina ganin zan iya cutamiki ko, zan kuma raÉ“eki in matsamiki ko, shiyasa na baki sarari ki huta sosai, saboda ina son abinda kike so Amnah, ki koma ciki ni zan wuce .. Kuka ta sake samai tana faÉ—awa jikinshi tare da fara É“alle mai maÉ“allan rigar shi ,ta tausa Hannuwan ta ciki tana shafa lallausan gashin da yama faffaÉ—an kirjin sa Æ™awanya. tace'' wallahi Baby cike nike da buÆ™atar ka da kewar ka, kai ka kasa fahimta nane, amma wallahi nafi fifita buÆ™atar ka sama da tawa, kawai dai umarnin su Ammi ne nike bi, Amma dan banda yanda zanyi na Æ™aurace ma umarnin ka. Yace "shikenan kibi umarnin su nikuma ki saÉ“amun,amma kisani hakkina yafi girma akan nasu Wallahi,haba Amnah, bantaÉ“a tinanin haka daga gareki ba, inzo har gidan ku dan ke kaÉ—ai gareni , Amma ace ki hanani samun natsuwa dake,wallahi kin shayar dani mamaki ,amma babu komi na miki uzuru, wallahi Amnah na tabbata da ace banje abuja ba babu ta yanda za'ayi arabamu ,amma daga sungano ko waye ni sai surabamu,maimakon sadda ma basusan asalina ba su rabamu ba sai yanzu da yakamata ace mu kasance tare,saida kika ÆŠan É—anaman zuma abaki kana zaki barni ,na hakura na baki shekara daya kizauna su kula dake, in akwai abinda kike buÆ™ata ki faÉ—aman,kuma ki kulaman da kanki sosai. Ya Æ™arasa yana hura mata kunne da iskan bakin shi mai masifar zafi , Dan takaicine fal zuciyar shi.... Tace baby in'kamun haka sai inga kamar Dan kana da azziki shiyasa kakeso ka buÆ™aci inyi nisa da kai har na tsawon shekara É—aya,ka nuna man kanaso inyi nisa da rayuwar ka.. Yace kull Amnah! kull! ki daina man wannan magana, Saboda ni kece azzikina wallahi, a banike yafiyeman dukkan wani dattin duniya da zansamu anan in barshi,ke kau ina fatan har aljannah mukasance dake, to amma yazanyi tinda sai abinda sukace. Takasa magana ta son da gaskiyar shi ,sai jikinshi data lafe . Yace kishiga in wuce zanje wani wuri. Tace inah.? Yace wani wuri. Tace "Baby zanbika muje gidan yanzu ina da buk... Shuru tayi tana mai yin Æ™asa dakai. Kanta ya shafa yace" nafayi hakuri sweety,Mikike da buÆ™ata? Ya faÉ—a cikin jin daÉ—i. Tace" kawai. Yace shikenan kawai ki koma ciki, zamuyi walima jibi insha Allah, zanturo miki invitation card kirabama kyawayen ki kinji.? Tace ''A'a bana dasu, na rabu da kowa. Yace shikenan Amal fa.? Tace sai dai ko ita. Cikin kulawa yace'' tom shikenan yanzu kin shirya dawowa gareni.? Tace eh mana nidama ai kullum ina tare dakai. Yace hmm ke ketare dani koni ke tare dake. Fira suka shigayi sai da aka kira azahar kana sukayi bankwana cike da shaukin ganin juna. Amnah na shiga ciki tabi kayan dake baje da kallo. . Mamy kau cikin tsananin jimami tace" Annabin wai kinga Sadeeq uban kayan lefen daya miki kamar baza'a Mutu ba. Kanta ta sadda Æ™asa tana wasa da yatsun hannuwan ta, aranta kMi masifar daÉ—i da kauna shi ke linkuwa cikin zuciyar ta . ÆŠakinta ta wuce cikin sauri tayi tsalle ta faÉ—a bisa gado, tana ihun murna. Mamy kau fira sukashigayi da Ammi ta walimar da zasuyi. Mamy ta É—akko waya tafara kiran Æ™awayenta dasu Hajiya Turai akan suzo Suga lefe , Akwai kuma walima da zasuyi. Abinka ga yan ganin kwaf cikin lokaci gidan ya fara cika, akaita É—umi ana son barka... Bayan mangariba Hajiya Turai data rage kaÉ—ai ta kalli Mamy tace" Æ™awata kinga abinda na faÉ—amiki ko ,to yanzu kuma zamu shirya gagarumar dinner party wadda za asha shagli kowa sai ya yaba. Mamy kau ta amince washe gari akayo musu invitation card suka dinga rabama mutane . Amal kau tafi kowa farin ciki dan akwaita da son party, baki daya Æ™awayenta ta dinga zuwa tana kaimusu. Amnah kau bayan magariba ta tsarama Sadeeq text mai masifar daÉ—i na godiya da tulin kayan da yakawomata harda mota. Bayan kwana ukku gidan ya rikice kamar bikin farko, haka akayima Amnah lallai mai masifar kyau da wasu Æ™ananun kitso da aka yarfamata na maraÉ—awa. Da daddare tana kwance É—aki suna waya da Sadeeq yace''. Sweety nah ina kewarki fa ,ina son kasancewa da É—umin jikin ki. Tace shikenan bara muyi Vidio call ,nima inaso inga zaÉ“ina.. Cikin shauki dajin daÉ—i suka buÉ—e data suka fara Vidio call cike da soyayya da kauna, sai rawa take mau tana gilgizamai dukiyar ta. Gabaki É—aya ya É—inauce ko gani sosai bayayi ido dishi -dishi yake kallon ta. Ganin babu sauki Sukayi sallama ya rungume pilon da yakema canjin kaya dana baccin ta yana rarragewa. Gagarumar walima aka shirya wadda ta Æ™awatar sosai, kuma tsakanin Ango da Amarya akayita da abokan su, inda Abbas ya taka rawar ganin sosai dan yayi gayya ta ban mamaki, Yan gun aikunsu ma sunyi mai kara sosai, duk inda ka gifta mutane. a'haka akayi aka tashi da kyaututuka masu girma. Washe gari yan gun aikinsu suka shirya mai kwarywa- kwarya party, da zasuyi tsakanin su , sai amarya da Æ™awayen ta.. Aiko ansha kyau cikin shigar kakin sa itama tasanya riga da wando na kakin soja sai wata kimono green da tasa sunyi kyau, cikin tsari sukayi suka watse inda suka samu kyaututuka da dama.. Ranar Friday da yamma aka fara shirin Dinner, kuma aranar Amnah zata tare sabon gidanta daya jiku da kayan more rayuwa amma sadeeq bai sani b. Sunayin sallah mangariba da isha aka fara tsantsarama Amnah kwalliya mai masifar kyau, da tasata fitowa kamar aljana saboda kyau, kowa masha Allah yake faÉ—a. Kawayen Amal suka É—auki ihu suke Dinga photo da ita dan tayi kyau dole kaso RaÉ“ar ta. Mamy ta shigo É—akin tace " Dan Allah kubani wuri. Fiya sukayi daga ita sai Amnah suka rage tace''. Amnah zare wannan rigar fara É—aura wannan jigidar a kugunki,Sai da safe sai ki mayar da ita a kwalbar ta dake da ruwan tmTurare a'ciki, Kisani da anyi mangariba ki dinga ÆŠaurata , Allah ya bada zaman lafiya. Tace" to Mamy Ameen. Daga haka suka Æ™arasa shiryawa , sai karfe tara suka fito fess, iyaye da ya'ya, ga Æ™awayen Amal suncika wuri.... Motoci suka fara zuwa cikin tsari, kuma dukkansu abokan aikin Sadeeq ne, sai kau na Abokan Abbas. Abbas yazo da wata fara dalleliya sai sheki take, Sadeeq na baya hakimce sai baza idon ganin ta inda Tauraruwa tashi zata É“ullo.. Hajiya Turai da Amal suka kamo hannu Amnah suka fito da ita suka sanyata aciki kusa da Sadeeq. Amal tayi murmushi tace" Yah Dee kunyi kyau sosai kundace da juna, fatan Alkhairi, Allah ya bada zuria É—ayyiba ta fada cikin yalwataccen murmushin dake bayyana natsuwar ta. A'hankali ya kalleta yana jinjina mata kai, tare da faÉ—in Ameen sst nagode Allah ya baki miji nagari. Abbas daya mace da kallonta yace" am nace bakiji ba Dear. Cikin natsuwa ta juyo tace" sorry Abokin Yayah ina wuni. Yace lfy Dan Allah kizo muwuce anan mana. Tace" da motana, zanje da Æ™awaye na. Fita yayi ya samar ma Æ™awayen nata wasu motocin kana ya dawo yayi tsaye gabanta yace. na sama musu Æ™anwata, muje inaso kizama Æ™asan kulawata kinji?. Murmushi ta saki kana ta buÉ—e gaba suka tafi... Tinda suka tafi yake kallonta, yanajin masifar daÉ—i, Dan yana fata ya malleketa cikin lokaci Æ™alilan, wayar shi ya zaro ya kanga ga kunne. Yace" Hajiyata addu'a ki taci. Allah ya kai damo ga harawa ,gashinan sai Æ™oÆ™arin wawaso yake, asake mun wata addu'a ya faÉ—a yana satar kallon Amal da batason wainar da ake toyawa ba. AÉ“angaran oga Sadeeq kam tinda Amnah ta shiga ya farajin wani yanayi mai wahalar bayyanawa , Dan wani tsuma da karkarwa jikin shi keyi, sakamakon Kamshin da jikinta ke fiddawa. Cikin natsuwa yasa hannuwan shi ya janye mata kyakyawan net din da aka rufe fuskar ta dashi. .ahankili ta dago idanuwanta ta Zubamai su tana murmushi... Innalillahi wa inna ilaihi Raji'un. Sweety yanzu haka zamu shiga mutane duniya ta kallemun sirrina.. Murmushi tayi batace komi ba. Bayan sun Æ™arasa Abbas ya'fito ya buÉ—e sashen da yake ,Amal kuma ta buÉ—e sashen da Amnah take. Anan sukaga kawayensu suka sasu tsakiya hannusu cikin na juna suka isa cikin katafaran hol É—in. Mc ya gabatar da isowar ango da amarya, bayan ya saki kida mai taushi da sanyi. Kyakyawar kujera da aka kawata da kayan ado suka zauna cikin natsuwa. Su Mamy da Ammi da Hajiya Turai kam sunyi shiga iri É—aya ta kamala, baka ganin komi ajikinsu sai kyallin gold, sunsha make up sunyi kyau over. Bayan gabatar da godiya ga Allah da kuma taya amarya da ango murna mallaka junan su aka fara casu. Inda Abbas ya zage yadinga ma Amal liki da 1k itama ta dakko nata ta fara yayyafami su cike da shauki . Sadeeq kam bayan an'basu wuri suka fito a kace dole su taka rawa, saboda ranar farin cikin ne. Kida aka sakar musu na amarya da ango. .cikin farin ciki ya kamo hips dinta dayaji sun sake cika ya rike yana sauke ajiyar zuciya. Lumshe ido yayi yana kai bakinshi saitin kunna ta yace" wash Sweet yaushe kika zama haka, Anya zan haÆ™ura a tashi kuwa, kincanza Wallahi kinÆ™ara zama Æ™atuwa kayana sunyi fom-fom. Yace wayyo daÉ—i ya karasa magana cikin kunna ta. Ihu wajen ya É—auka dan zaka dauka wani salon soyayya ne yake mata. Bayan anci ansha aka rufe taro da addua karfe goma kowa ya tashi. Mamy da Ammi da Hajiya Turai sukazo aka fara zubamusu photo, bayan angama sukamusu nasiha zaman lafiya tare da cewa zasu iya wucewa. Wayyo dad'i ga Dee ba'a magana. kamin taron ya Æ™arasa watsewa ya sungumi Amnah yayi waje da ita sunatamai dariya .. Yana zuwa sukaga Amal da Abbas cikin mota da alama an'samu fahimta juna. Sadeeq yace wai kai mikake nufi, naga tinÉ—azufa sai wani kame- kame kake?. Abbas yace ai an:wuce wajen oga Sadeeq, sai shirin angon cewa. Cikin farin ciki suka musu fatan Alkhairi . Sadeeq yace Amal fita kuje dasu Momy . . Abbas yace "Dan Allah Yallabai ka barta tamun rakiya man, in na ajiye ku sai muwuce da ita. Yace "a8a Abbas muje dai ,kaima kasake hakuri. Yanaji yana gani ta wuce suka shiga baya suka wuce. Tin a motar yake wasanni da jikinta itakuma sai murmushi take zubamai dan zallar zalama take gani agareshi. Mansho Suya suka tsaya yasai musu kaji da abubuwan buÆ™ata kana suka wuce. Abbas na ajiyesu yace "to maza gida ka gaida Hajiya. Fuska ya kwabe yace. "Yallabai ka rabani da tawa kuma kai zakayi wuff da taka yanzu. Ido ya kashemai yana danna remote É—in get din yayi sama Abbas ya fita. ya kuma rufewa tare da kama hannu Amnah sukayi ciki. Bayan sunje yace" Yau dai Allah ya cikamun burina ,gani ga matata bayan sati biyu da aka hanani ganin ta, anga dama Ambani yanzu, Bayan an'wahalar da zukatan mu, An'raba gan-gar jikin mu daga ji da ganin juna , To yanzufa, gani gaki, Amnah bana tinanin ko haihuwa kikayi zanbar ki komawa gida , dan bazanyi Abinda zai raba zukatan mu ba, ina fata ALLAH ya zaunar damu lafiya Matata, ya kuma bamu Yara masu albarka,Amnah bazan É“oye miki ba ina masifar son yara , Wallahi in'kika haifaman su kinbiyani Matata, Allah yasa albarka a tarayya da zamuyi a daran yau ya bamu Baby ,Ya bani jarumtar jefa miki Biyu ko huÉ—u haka yaÆ™arasa yana kashe mata ido É—aya. Murmushi tayi tana kallonshi tace" Æ™ari kake nema ne koya? Cikin rashin fahimtar maganar ta yace" bangane Æ™ari ba Dear?. Idonta ta rufe tace'' ai tin ranar da ka halba kwallo na farko ya faÉ—a raga ,ina nufin akwai ajiyarka anan ta nuna cikin ta... Arikice ya mike tsaye yana kama hannuta bakin shi na rawa, ga baki dyaya idon shi ya zazzaro cikin in ina farin ciki yace "Dan Allah Amnah karki faÉ—amun famalki nike , Dan Allah karki fadamun zaulayana kike, Dan Allah karkicemun ba da gaske kike ba... Cikin zallar shauki da jin daÉ—i ta mike tsaye Tare da cire mayafinta ta zuge zif É—in rigata tayi Æ™asa da ita. Anan twins É—inta suka bayyana sunyi tuma- tuma gwanin kyau ,sai shining suke suna tsole idon Dee. A É—imauce ya Æ™arasa gareta yana hadiyar wani yawun jaraba yace" . tabbas my wife na yarda, wannan cikar da kikayi bata banza bace. Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Allah ngd maka dakamun babban gata kabani abinda nike so ,wayyo dad'i nikam mima zanmiki in faranta miki ,ya faÉ—a yana yin sama da Amnah ,yana jiyu da ita cikin zallar farin ciki sai dariya take. Saida ya gaji dan kanshi kanan ya sauketa ya cire babbar rigarshi ya É—akko flat kiching din su yazo ya zazzage naman kajin da keta turiri. Kat -kat haka yawunta suka fara tsinkewa. Da sauri ya fara bata tanaci tana bashi, sai da suka koshi kana ya haÉ—e goshin su waje É—aya yace "Matar Aljannah a daran farkon ki ,mijinki bashi da ko si-si, bai ciyar dake da kazan nan ta al'ada ba ,Amma ke baki damuba, saima ke dakikamai babbar kyauta, ta hanyar ciyar dashi da abu mai tsananin tsada da ya siya only 5k, Amnah kinyi a rayuwa , kinbiyani, ina fatan Allah yabani ikon kyautata miki da faranta ran duk kan wanda kikeso kinji. Tace" Ameen mijina nima ina fatan Allah ya bani ikon biyayya ga umarnin ka,kana Allah ya baka damar dauwamar da soyayya da kakeman har abada. Ameen Yace" tare da tattare wurin ya kamata suka nufi sama. Masha Allah tace lokacin da taga kayan alatun dake sama Fiye dana Æ™asa . Tace Baby" kayi Æ™oÆ™ari, Allah ya linka azziÆ™in ka, yasa albarka a Aikinka, ya tsareka daga haram, ya baka ikon kyautatama wanda bayadashi , Allah yadawwamar da albarka a halaliyar ka... Cikin farin ciki yace" Ameen- Ameen matata uwar É—ana ko yata, Allah yabani yaro ko yarinya mai tsananin kama dake, Amnah ina sonki banÆ™i duk kan yarana su biyoki ba wallahi ,saboda bana gajiya da ganin ki. Tace" nikuma wallahi nafiso subiyoka ,kaga koda kana wajen aiki nasamu photo coppy ka.. Hancinta yaja yace" kina tinanin zantafi aiki ne inbarki gida? nooo kidaina wannan zancen, anacen officer É—ina an'kafaman gadona mai masifar kyau, wanda zamuna hutawa dake ko, na sonki sarai bazaki jure rashin daÉ—in ki a kusa dake ba, kinga danayi aiki kaÉ—an sai muje mu huta, in ciyar dake in shayar dake ,kema kimun sai indawo bakin aiki , aÆ™allah musamu kusanci arana koda so goma ne kamin mu dawo gida. Ido ta zaro tace wayyo Baby kason mene kake fada kuwa? Yace" yess Harija da Hariji ,sai ahaÉ—u aita Harijanciii ya Æ™arasa cikin shauki da matse hannuwan shi yana lumshe ido. Duka ta kaimai a kirji ta ruga yabi bayanta yana maida kofar ya rufe, Dan daga É—akinta zaka iya fadawa nashi ,dana yara da aka fidda.. 6/1/22, 20:25 - Ummi Tandama😇: *Littafin🌹DAN DAKO🌹 na kudi ne biya ki karanta cikin Aminci. Biya 300kacal to 0006454115 Amina Dahiru jaiz bank,or MTN card to this number 09165832002. then send the evidence of payment via 07038423451* ðŸ¤ðŸ™ðŸ¤² Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Yan uwana mata ina kuke ku malmatso ga wanni sirri da nike son baku, ita ya mace sai da kamshi, ina macen da take ganin izgili da wulakanci da ake cewa maza nada shi, hmmm yar uwa to inkin kasance a haka da alama akwai ayar tambaya akanki. Tambaya ta ta farko gareki da wane irin turare kike amfani a jikin ki ?,da wane irin turare kike turara gidan ki,shin dawane irin turare kike Zukunni, hmmm to matso kusa kiji yar uwata. Shi kamshi Annabi muma ya faÉ—a abin sone,kuma Abune mai sanya natsuwa da girmama ma'aboci shi , Da Yawon son kusantar sa. Duk kan wulakanci da izgilanci na maza akwai turaran da zai miki maganin sa da izinin Allah,ba boka ba malam,wanda zai karkato da hankalin mijinki akan ki ku samu fahimtar juna. Ko kin son kamshi na dakusar da fitinar É—a namiji yar uwa? kigarzayo ki kwashi rabonki ga shaharariyar yar mai Dugurin nan mai suna UMSAD INCENSE ,Mace mai kishin mata da son Fiddo martaba mu. Nayi Amfani da turaranta naji masifar daÉ—in da yasa nakasa barwa raina. Nace bari in yaÉ—amuku dan kowa ya mallaki nashi cikin farashi mai sauki. Da fari bari in zayyano muku su kamar haka.👇 Maleek Al'oud Royal kush Cous-cous Kajiji Original sandal Sandal flex Sandal bange VIP mix Hawi Al'oud Kindikay Danal banat Darot Habil Gaf-Gaf Sirrun nisaa'i Sandal chips Kwalacca Humra black and body milk Attractive humra. Yar uwa zanmiki Dallah- Dallah. Akwai turaran da zaki sanyama kayanki . Misali! kisa kabasa kiturare kayanki . Akwai humra da bazaki sataba sai zaki turaka. Akwai turaran kaya ,na jiki, Dakuma na É—aki. Akwai kwallaca sirri, amma bama badata gaskiya sai ga wanda baida kishiya , Dan muddum kina amfani da ita tofa gabaki dayan hankalin mijinki akanki zai dawo,Dan yana juyo da hankalin namiji akanki baki É—aya ,zaki zama shalele Baby, Akwai sirrin nisaa'i. hmmm Dagajin sunan kason na dabanne,na baki sati É—aya ki gwada ki gani Hajiya ta, tsugunno ake akai ga mai buÆ™ata ya tunÉ“e mu ta wannan layin 08028827241 karku manta UMSAD INCENSE mune na É—aya. Muna aika kayan mu duk inda kuke. Kamshin jiki martaba mutum.... 5ï¸âƒ£9ï¸âƒ£&6ï¸âƒ£0ï¸âƒ£ ""Cikin sassarfa yayi taku ukku ya kamo Æ™ugunta ya rike gam! Yace" koda zaki barni badai yauba, saboda yau cike nike da begenki da farin cikin dasa gudan jinina da nayi a mahaifarki... Tace" nima bazan barka ba, saboda ina tare da kewarka. Goshin ta ya shafa yana sakin Murmushi yace. "Allah ya miki Albarka, bara nayi wanka, ko tare zamuyi?. Tace "A'a ba yauba sai gobe. Yace shikenan sai na fito. Tana ganin ya shiga ta tashi da sauri ta É—akko babban Flak's Dake cike da ruwan kanun fari ,da aluf kaÉ—an, da ganyen magarya ,da bagaruwa, sai miski kaÉ—an da Hajiya Turai tace ta ajiye mata, ta shiga dasu toilet tinda tamata bayanin su. Bayan ta since towel É—in ta É—auka ta fara kama ruwa dashi ,tana yarfama gabanta tana tausa gumin yana ratsata. (Yar uwa ki kiyayi zaman cikin roba , Wallahi lalata mace yake ,watsa ruwa shike hadeki gam babu wanda ya isa ya kawomiki raini, ko haihuwa kikai karkice zaki raÉ“e- raÉ“e cikin roba buÉ—ewa É—inki keyi, inko kikasamu abu kika zauna kina zubasu da guminsu kinfi gasuwa ki haÉ—e gam ko kisa towel inkin matse sai ki tausa ,Dan Allah basai mun haihuba aa hakanan ma kidingayi.) Sosai takejin daÉ—in ruwan , a haka tai tayi har suka Æ™are, kana ta É—ebi ruwa mai kyau masu ÆŠumi kaÉ—an tayi wanka da sabulun UMSAD INCENSE na gyaran fata maisa ta tayi glowing ta fita tanata zuba kamshi kamar tayi wankan turare.. Tattausan jikinta ta goge tass kana ta murza kwalcca zaujatul noor ajikinta, tabi da humra da turare mai sanyi,Take ÆŠakin ya É—auki masifat Æ™amshi . Tana cikin neman kayan bacci ya murda Kofar ya shigo da sallama. Da sauri ta juyo tana amsawa, tare da sunkuyar da kanta Dan daga ita sai Æ™aramin towel. Bakin kofar yayi tsaye yana Æ™aremata kallo cikin fitinannu idanun shi da lokaci guda suka canza launi ko buÉ—ewa basayi sosai.. ÆŠagowa tayi cikin shagwaÉ“a tana turo Æ™aramin bakinta tace" Baby ka gama?. Cikin mutuwar jiki ya ÆŠagamata kai ,tare da fara takowa inda take cikin wata tafiya mai masifar burgewa ta ingarma Namiji. Kallo shi tayi taga yana sanye da wasu fitinannun kayan bacci farare sol, masu masifar kyau da taushi , illahirin surar da Allah ya mishi kana gani. Cikin rawar murya tace" Baby kayi kyau.. Yace "kema kimmin kyau a haka matuÆ™a. Ido ta zaro tace" Babu kaya fa a jikina ina kyau? Yace'' a wajen mutane ne-ne ma'aurata basa kyau haka, amma tsakanin Ma'aurata hakan yafi kyau ,kaga komi! komi ya ganka. Murmushi tayi batace komi ba. Jikin shi ya jawo ta ya Æ™arasa gaban wadrof É—inta ya É—akko wata leda mai masifar kyau , A'hankali ya zazzage ta a kan gado. Wasu kayane masu kyau da tsananin taushi suka faÉ—o. Zaunar da ita yayi akan gadon ya isa ga kayan yace" Sweety nah bara na zabi dai-dai da tsarina. Fara É—agasu yayi duk ciki babu na mutunci, wasu irin kayane dasu kwara babu. Wasu pink masu ratsin fari ya É—akko mata yace" yawwa Sweety tashi insamiki wannan. Tace" Habu wayan nan na jarirai fa Baby? Yace" jaririyace ke mana awajena ,kin mafi jaririyar,Ki É—auka babu kowa aduniyar. Cikin jin kunya ta tashi ya samata su ,sukamata D'ass gwanin kyau kai kace domin ta aka yisu. Ihu ya saki yana kashe glove É—in ÆŠakin suka faÉ—a kan gado. Cikin lokaci wasan ya fara canzawa, bakajin komi sai tsananin ihun da yake da shashekar kuka Amnah, sama da awa biyu yana ziyar Tata kana ya koma gefen ta yana sauke ajiyar zuciya. A'hankali ya rungumota jikinshi yace "Sweety babu zafiii.? Hawayenta ta share tace" Baby akwaifa, amma bakamar na rannan ba. Yace'' yawwa anjima in zanÆ™ara bazakiji ba. Ido ta zaro tace "ka Æ™ara mene? Baby awa biyu fa ?. Yace" yess bakyason daÉ—i ne .? Kina da masifar daÉ—i. Bana fatan ingaji da ziyara ki wife. Tace'' inaso !amma sai bayan sati biyu. Yace'' hmm kina dai so ne a wayi gari aga namace ,ya ina da zuÆ™eÆ™iyar mace kamar ki in'tasaki gaba ina kallo, wanda ma mukayi farko takaici naji Wallahi matuÆ™a. Tace''Hmm Banda tina baya muje muyi wanka. Tashi yayi suka nufi toilet É—in suka fara wanka cikin so da Æ™aunar juna, daga nan kuma Sadeeq ya fara burkice mata, yana wasanni da sassan jikinta , Mussaman twins É—inta dake masifar sashi wani yanayi. Suna zaune cikin kwamin wanka ya buÉ—e kafar ta yana matsawa sosai gareta suka samu kusanci,tare da cewa Please Amnah ki bani koda 30mnt ne , Dan Allah Namiki alkawari babu zafi, kinga abun ki na kuka fa yafaÉ—a yana nunamata AlÆ™alaminsa da ido. Kuka'n shagwaÉ“a tasa mai tace'" nidai gaskiya Baby ina tsoro Wallahi." Cikin gushewar Hankali yace" Babu komi, bazakiji komi ba, sai tsananin daÉ—i kinji Halaliya nah.. Kai ta É—agamai cikin salo da kwarewa ya fara ziyartar ta daga zaunan da suke. Ajiye zuciya kawai suke saukewa da sauti numfashinsu dale fita da sauri ,cikin tsananin jin daÉ—i , dan Amnah tama fishi jin daÉ—i saboda Irin salon da yake mata, sai motsi take tanajin kamar zata suma saboda azabar daÉ—i. Kusan awa É—aya kana ya matseta jikin shi ,bayan sun huta sukayi wanka suka fito. Amnah zata sanya kaya yace" gaskiya Sweety ban'yarda ba, bazaki samun komi ba , Saboda inaso duk sadda zan jiki ajikina inji komi a bayyane wallahi. Murmushi tayi tana kallon shi. Ƙarasawa yayi gareta ya jata bisa gadon , Tare da rufamusu bargo ,ya jata jikinshi sosai yana wasanni da Dukiyar fulanin ta har suka fara bacci. Misalin karfe 3 ta farajin hannushi na yawo a sassan jikinta, tare da sauyawar numfashin sa. Cikin tsananin Mamaki take buÉ—e ido tana kallon shi , tace'' Baby yane?. Murya na rawa yace" ki barni in'samu natsuwa matata , Wallahi na kasa bacci ,ina son kasancewa dake, wallahi masifaffan feeling nikeji na kasa kwanciya, Amnah marana zai tsinke.... Kuka ta samai tace'' Baby inafajin zafi , Dan Allah kabar Baby mu ya huta matso kaji in'baka Mama zakasha ko. Ta faÉ—a cikin lallashi dan mantar dashi daga Æ™udurin sa.. Cikin shagwaÉ“a ya ÆŠagamata kai yana faÉ—in" ba lafiya sa zamu inganta ba? Tace" ai ya ginu da É—umin Daddy sa, ya wadatar dashi Baby kaji?ko kanaso ya samu matsala.. Cikin gamsuwa ya gilgizamata kai, Tare da faÉ—in bana fata Sweety nah saboda jinin jikinane. Ace yawwa my â¤ï¸ ta Æ™arasa tana zaro Mamanta dake cike fal ta tausa mai baki. Cikin sauri cike da buÆ™atuwa ya cafke ya fara tsotsa kamar sabon jariri, yanayi yana matseta jikin shi,a haka bacci yayi gaba dasu. Ita kam Amnah bawani baccin kirki take ba, sai kafa da take ta matseqy saboda irin zuÆ™ar dayakemata ,sai taji dama bata hanashi cimma burinsa ba. A'hankali tazo zarewa da sauri ya sake cafkewa, yaci gaba da tsotsa hankali kwance ido rufe.. Karfe huÉ—u nayi ta fara murza tattausan jikin shi, duk inda tason sakonta zaikai mai cikin Sauri,haka ta fara tattausamai tana É—an murzawa. Kan ta an'kara yayi sukuwa ya haye kanta Sai biyar na Asuba ya sararamata, ya tashi yaje ÆŠakin shi yayi wanka, yazo ya tada ta ya iske ta fito tana tsane gashin ta Kyakyawan Murmushi mai bayyana tsantsar jin daÉ—i su sukama juna, inda ya sumbaci goshinta tare da faÉ—in na wuce Masallaci. Tace "To Baby Allah ya tsare ya kiyaye, ya karamana jin daÉ—in juna . Ameen Yace yana huro mata kiss, Ya sauka da sauri Dan inya tsaya Alwallah shi zata kare. Bayan ta gama Sallah tayi azkar ,kanan ta fara karatun Alkur'ani cikin sassanya muryarta, sai takwas ta gama ta ajiye tana buga hamma, Dan baccine jikinta. Dai-dai lokacin da shima ya shigo ya cire kayan shi ya cire mata nata ya jata kan gado suka kwanta.. Karfe sha biyu wayarshi ta fara ring . Cikin murya bacci yace" ina ji. Ammi tace" Dee ga breakfast nan na ajiye muku, ni na wuce Aiki, (Sahoda Abbah ya sama mata aiki babba Asibitin) inka tashi kazo ka É—auka, agaidamun É—iyata bye takashe wayar. Tattausan murmushi ya saki yace" Ammi na kenan,Tason bana iya magana ina tsaka da jin daÉ—i. A'hankali ya zame Amnah daga jikin shi dan yasamu damar zuwa gaisheta kamin ta wuce, ya mike ya sanya jallabiyar shi ya fita. Bayan ya fita ya shiga part din Ammi, anan ya iske har ta fito hannuta rike da key din mota. zama tayi fuskarta cike da fara'a tace 'na tasoka ko? Ai da kunyi bacci kun huta in nadawo magaisa. Murmushi ya saki kanshi Æ™asa Yace"wai Nainah tana nufin bazata maido Baby'n Baby bah. Tace eh tace sai zata aurar da ita. Ido ya zaro yace "Ammi kinji dogon guri ko, ita tana tinanin zatakai, kai Nainah akwai son duniya kamar bata daÉ—e ba. Dariya tayi sosai ta tashi tace "zan wuce. Rakiya ya mata yana faÉ—in zan samamiki driver insha Allah, sunma matsa akawo ma'aikata amma naki yarda , Ammi banaso acikamun gida da garada wallahi, ko David nan kusa gidan gona nan nace ya dinga tsayawa banso ya shigo,Masu bina ma Banaso Wlh. Tace to yazakayi tinda haka aikin ku yake, Allah ya zaÉ“a Alkhairi. Yace "Ameen yana mai ÆŠagamata hannu har ta fita, ya rufe kana ya dawo ciki da kulolin ya shiryasu a dining table kana ya haura sama. Wayam yaga gadon batanan, hakan ya tabbatar mai ta tashi my be tana toilet. Shima É—aki shi ya shiga ya murza wanka ya fito yanata zuba murmushi, kamar wanda akawa kyauta.. Bayan ya gam ya fito ya iske smnah zaune kan gado tasha wanka tayi masifar kyau. Hannayenta ya kama ya rungumeta yace" bana gajiya da ganin kyakyawar Fuskar ki, bana gajiya da jin É—umin jikinki, domin natsuwata tana.tattare.da mallakar komi naki. Tace" nima bana gajiya daji da ganin ka, domin kaine garkuwa ta. Yace "muje Æ™asa muyi break ko, sai mutafi office. Tace "wai Baby da gaske dani zakana tafiya?. Yace" sosai makuwa, in'babuke akusa bazan iya komi ba. Tace yo aikin gidan fa. Yace sai muyi kafin mutafi.. DaÉ—i ya kamata tace" shikenan i love you. Yace "me too noorul khalbi. Shape -shaoe sukai Break kana ya haura sama ya shirya ,cikin uniform din shi dake haska farar fatar shi ,yayi masifar kyau ya sakko cikin sassarfa data sake fiddo asalin jarumtar shi da kwarjini sa. Mukewa tayi tare da saramai. Kyakyawan murmushi ya saki yana rungumeta yace "aike kika dace in sara miki Gimbiya ta,Dan kece daÉ—i nah wallahi,dole inyi biyayya konasamu zuwa inyi noma anji ma. Dariya ta saki tace kai Bab bakaji. Yace Hmm. Cikin Sauri suka fita suka shiga mota. Bakin get ya tsaya yayi ma Devid waya ,sai gashi cikin shiri ya fito, bayan sun gaisa ya fiddo motar suka wuce. Amnah dashi na baya sai soyayya suke. Bayan sun isa break din yana riÆ™e da hannuta suka shiga ciki.... Da gudu David ya buÉ—e mai officer din ya shiga, ya nunama Amnah wani kyakyawan gado yana sakin murmushi. Cikin mamaki tace "wai dama Baby da gaske kake.? Yace" eh mana nason darajar shine ,anan ya budemata shi É—an medium mai masifar kyau yace" wannan gadon na sirrine, ba kowa yason da shiba Amnah, yanzu ki zauna ki huta,zan gaida oganni na in'dawo. Zama tayi tana mishi a dawo lafiya. Bayan yafita yaba David kudi ya siyo musu ice cream da samosa kana ya wuce. Duk natsuwar shi na tare da matar shi, shape- shape yaje ya dawo ya isketa tana bacci hankali kwance. Hannuta ya kama da sukayi tass suka cika ya sumbata kana ya fara aikin shi dan ya barta ta huta. Sai azahar ta falka sukayi sallah ,ya bata ice cream tasha yace mukwanta muhuta ko Baby?. Tace eh mana?. Rungumeta yayi suka kwanta abinsu sai shidda sukayi gida. Haka rayuwa taita gudu suna cikin farin ciki, Yayin da sadeeq azzikin shi keta haɓɓaka, Dan ya buÉ—e katafaran shagon saida motoci . Yayin da ya buÉ—ema Amnah botic da wajen saloon da henna, make up din Amare babu abunda basayi, akasamata ma'aikata kwararri dandanan wajen ya samu karÉ“uwa ,dan komi anayinsa bisa tsari da kuma sauki . Bayan wata biyar. Cikin Amnah yayi girma sosai, yayin da yake shan gata kota ina ,kamar kanta aka fara haihuwa, dan uban gayya kam ya kasa ya tsare ,kullum yana cikin aikin gina gudan jinin shi. Amnah kau takan bada hadin kai dan inma bayanan takan kirashi, Dan Nene ta hanasu tafiya office tare ,tace. "Bazasu mata asara É—aba ko É—iya, tinda ta fahimci dukan su basu da sauki wajen Bauta... Wata Alhamis dunya zaune ya dawo daga office. "Amnah tace Baby ya kamata fa inje Æ™auye mu, nama Baba na alÆ™awarin zuwa. Yace" karki damu love ina sane, Amma ki bani nan da sati daya sai muje tare ranar da ba office. Tace to "amma nida ke so in kwana ,kar'suga kamar ina kyamatar asalina. Yace "ba damuwa, sai mutafi Friday mudawo Sunday yayi?. Ta zaro ido tace" hadda kai ?. yace" tabbas, taya zan iya bacci bakya kusa dani. Murmushi jin daÉ—i tayi tana shafa sajen shi. MiÆ™a ya saki yace "muje ko. Ido daya ta kashemai tana faÉ—in yeah . Cikin jin daÉ—i ya cicciÉ“eta suka nufi É—aki, sukasha soyayya daganan aka raya Sunnah... Sati na zagayowa suka fara shirin tafiya gidan su Amnah. Inda ya É—auketa sukaje gidan Nene sukamata bankwana, ta bata goro guda ukku tace takaima ubanta badan halin saba. Karba tayi tana murmushi suka tafi. Bayan sunbiya gidan Mamy sunmata bankwana ta musu fatan Alkhairi. Hanya suka É—auka inda Amnah keta kalle- kallen titi, tana faÉ—in yasaimata kaza ,yasai mata kaza . Cikin ihu tace Baby ga agwalima asiya itama. Parking yayi yana mai zuge glass din window, yace'' Malam bani ta 2k. Da sauri mai Agwaluma dake jera ta ya juyo yana faÉ—in Yallabai 200k aiko..... Cikin rawar murya yake nuna Amnah da itama ido ta zubamai tana mitsitsika ido sosai ta nunashi da yatsa tace Abul khairi!. Dama kana nan?. Kodai idona ne?. Agwaluma ka dawo saidawa.. Kuka ya sanya yace" Amnah kece ,kikace man rayuwa ta juya miki.baya,to ko kinfito gidan wancen matsiyacin kin auri mai kuÉ—i kenan, Amnah Bily ta cuceni. Ta kwasheman komi. Bayan bansonta ba haÉ—uwar online ne kawai. Cikin Mamaki tace'' kai Prince banason iskanci, kana nufin karya dama tamun tace É—an uwanta ne ka?i. Yace "eh wallahi ni nan ma gidan marayu nike, bayan na girma wani mai kudi ya daukeni basu taÉ“a haihuwa ba,shine ya ingata rayuwata, daga baya ya buÉ—e gidan Mai yabani manager ,to duk kan abunda nike da kuÉ—in sane saboda baya Æ™asa,bayan ya gano ya koreni nikuma na tattra abinda ke garai na gudu. Yarda da Aminci yasa na fad'amai Bily, sai gata kwatsam batama da lafiya Æ™afa tazo, Amma muguwa ta hada kayana tayi gaba dasu, ganin zan mutu babu mai taimakaman yasa na fara wannan sana'a. Sadeeq kam kallon su kawai yake ranshi na Æ™una. Amnah kau tace" Alhamdulillah Allah na gode maka, dakamun sakayya tin aduniya, azzalumi maÆ™etaci, wannan shine dai mijina, Dan Dakon gidan mu, shine ya dawo mijina mai dakon zuciya na, bayan na gane tarayya dakai bashi da amfani. 6/1/22, 20:30 - Ummi Tandama😇: *Littafin🌹DAN DAKO🌹 na kudi ne biya ki karanta cikin Aminci. Biya 300kacal to 0006454115 Amina Dahiru jaiz bank,or MTN card to this number 09165832002. then send the evidence of payment via 07038423451* ðŸ¤ðŸ™ðŸ¤² Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Yan uwana mata ina kuke ku malmatso ga wanni sirri da nike son baku, ita ya mace sai da kamshi, ina macen da take ganin izgili da wulakanci da ake cewa maza nada shi, hmmm yar uwa to inkin kasance a haka da alama akwai ayar tambaya akanki. Tambaya ta ta farko gareki da wane irin turare kike amfani a jikin ki ?,da wane irin turare kike turara gidan ki,shin dawane irin turare kike Zukunni, hmmm to matso kusa kiji yar uwata. Shi kamshi Annabi muma ya faÉ—a abin sone,kuma Abune mai sanya natsuwa da girmama ma'aboci shi , Da Yawon son kusantar sa. Duk kan wulakanci da izgilanci na maza akwai turaran da zai miki maganin sa da izinin Allah,ba boka ba malam,wanda zai karkato da hankalin mijinki akan ki ku samu fahimtar juna. Ko kin son kamshi na dakusar da fitinar É—a namiji yar uwa? kigarzayo ki kwashi rabonki ga shaharariyar yar mai Dugurin nan mai suna UMSAD INCENSE ,Mace mai kishin mata da son Fiddo martaba mu. Nayi Amfani da turaranta naji masifar daÉ—in da yasa nakasa barwa raina. Nace bari in yaÉ—amuku dan kowa ya mallaki nashi cikin farashi mai sauki. Da fari bari in zayyano muku su kamar haka.👇 Maleek Al'oud Royal kush Cous-cous Kajiji Original sandal Sandal flex Sandal bange VIP mix Hawi Al'oud Kindikay Danal banat Darot Habil Gaf-Gaf Sirrun nisaa'i Sandal chips Kwalacca Humra black and body milk Attractive humra. Yar uwa zanmiki Dallah- Dallah. Akwai turaran da zaki sanyama kayanki . Misali! kisa kabasa kiturare kayanki . Akwai humra da bazaki sataba sai zaki turaka. Akwai turaran kaya ,na jiki, Dakuma na É—aki. Akwai kwallaca sirri, amma bama badata gaskiya sai ga wanda baida kishiya , Dan muddum kina amfani da ita tofa gabaki dayan hankalin mijinki akanki zai dawo,Dan yana juyo da hankalin namiji akanki baki É—aya ,zaki zama shalele Baby, Akwai sirrin nisaa'i. hmmm Dagajin sunan kason na dabanne,na baki sati É—aya ki gwada ki gani Hajiya ta, tsugunno ake akai ga mai buÆ™ata ya tunÉ“e mu ta wannan layin 08028827241 karku manta UMSAD INCENSE mune na É—aya. Muna aika kayan mu duk inda kuke. Kamshin jiki martaba mutum.... 6ï¸âƒ£1ï¸âƒ£&6ï¸âƒ£2ï¸âƒ£ ""Ido Abul khairi ya zaro yace" Kai Dan Allah damine kayi azziki haka lokaci guda? kaga motar ka kuwa,kodai ka fara yankan Maman matane kana saidawa? Kamar jira Dee yake ya fito afusace ya mishi wata mummuna shaÆ™a, sai da ya tabbatar da ya bashi wahala sosai ,ya ganamai azaba kana ya watsar dashi asume kana ya dawo yaja motar a fusace... Hankalin Amnah ya masifar tashi , Dan tama kasa magana, sai binshi da ido take ganin yanda yake tsula gudu kamar zai tashi sama, idon shi yayi jawur yakasa magana sai kwafa yake... Cikin murya lallashi tace" Dan zatin Allah Baby kayi Hakuri, Wallahi duk kan abinda zaisaka É“acin rai bana fatan bin hanyar shi,sama da wata nawa muna cikin rayuwar farin ciki ,karkaba É“acin rai damar Æ™utse ciki wasu yan sakanni ya É“ata jin dadin da ya daÉ—e azukatan mu. Kasani koma miye ya faru ne abaya ne, Alokacin da kuruciya na É—ibana, lokacin da ni kaina bansan wacece ba,lokacin da akala rayuwans take agantale babu makwaÉ“i Babj mahani,haka nan ka É“atamun hannuka da dukan kazamin mutum irin wancen,karka manta da sonka aka halicceni, kuma dashi nike fatan inbar duniya nan,kayi hakuri kayi mijina dan Allah, karka canzamun fuska, ban sababa, zuciyana bazata É—auka ba,Bana da juriya akan canjin da zan gani daga gareka Please... Ajiyar zuciya ya sauke Batare da yace komi ba. Ta É—an rankwafo kaÉ—an tace" Baby bakace komi ba fa? Yace'' Amnah bazan iya fushi dake ba, nakasa control kainane bawai dan zagin da ya munba ko aibantawa, A'a idon shine dake yawa asassan jikin ki shine ya fusata ni, Amnah da a kallamun ke wallahi kwara amun dukan tsiya zaifiyemun sauki,banhaÉ—aki da kowa ba, saboda ma'ajin sirrinace ke ,bana so kowa ya raÉ“eki inba niba sai wanda ya can-canta . Amma mine zaisani fushi dake to in rungumi wa? Idonta ta lumshe tace" Naji daÉ—i da Allah ya bani Miji mai tsananin kishi na da fahimta lamari na, da ace duk kan mazaje kamar ka suke da bana tinani aure ko É—aya zai mutu,rashin fahimtar juna kan kawo cikas azaman takewar auran mu. Yace'' aikema da duk kan mataye kamar ki suke masu control É—in fushin mazajen su wallahi bana tinanin za'asamu saÉ“ani, Allah ya barni dake matata har aljannah. Tace "Ameen ya rabbi tana sakar mai kiss a hannu. Cikin Æ™anÆ™a nan lokaci suka Æ™arasa wani tafkeken gida mai masifar kyau ,ga wani katon get babba dukkan kauyen ko gidan mai garin babu wanda yakai kwatar shi kyau da tsari kamar a a Birni. Cikin mamaki take kallon shi tace'' Baby ina ne nan ka kawo mu? Yace" muje kigani. Gaba É—aya suka fito yazagayo ya rufe kofar tare da kama hannuwan ta suka shiga kai tsaye da sallama. Baban Amnah dake zaune cikin shiga ta Alfarma bisa carfet yasha farar shadda da babba riga sai hula sun mai kyau ,kamala shi ta Dattijo ta sake fitowa sosai , Ya taso hannushi rike da Æ™arama sanda ta silver yace" Masha Allahu ga Habu, Tin É—azu naÆ™i shiga ina jiranku marhaba'bukum. Cikin mamaki Amnah ke kallon Baban ta, ta kalli gidan ,ta kalli Dee da alamar tambaya sai dai ya kashe mata ido É—aya kawai. Amnah ta duÆ™a da kyal tana matse baki ta fara gaidashi . Da sauri ya kamo kafaÉ—unta yace "maza tashi Amina , Allah ya miki Albarka, ya saukeki lafiya, bantaÉ“a haihuwar yaron azziki ba Amina irinki, keda na watsar da rayuwarki nike ga baki da ranar da zakimun sai gashi ta dalilin ki kiga yanda mijinki ya maidaman gidana , Irin na shugaban Æ™asa fane Amina hadda gut(get). Dariya suka sanya su duka inda yace" to kushiga ciki kuhuta ko, sai muÆ™arasa ciki kuci abinci ko insa akawo maku. Amnah tace to" Baba tare da cewa ina yaran gidan?. Yace mijinki ya buÉ—e islamiya nan gangare kuma ya sasu ,yasamo malammai birni suna koyawa yana biyan su,kai Amina Habu fa yamu rana yakarasa yana sakin kuka... Sadeeq ya rikemai hannu yace" Dan Allah Baba kayi shuru haba, karka manta nimafa É—ankane, Wallahi bani da abinda zan sakama saboda ka taimakamun alokacin da nike da buÆ™ata, daga karshe kamun kyauta mafi girma, ka haifaman mata da babu irin ta,to inban kyautata maka ba mizan maka?. Yace "Nagode Allah ya saukeki lafiya, yasama rayuwarki albarka data abinda zaki haifa. Dee yace'' Ameen Baba. Baba ya zaro wani key Yace,, gashi Habu. Karba yayi suka nufi wata Æ™ofa dake harabar gidan, anan ya bude Saiga gida fess mai masifar kyau É—an karami Yasha tiles kota ina. Cikin kamaki Amnah tace" wai Baby nan fa,yau kanata bani mamaki.. Yace'' kinson sonki bazai barni injure nesa da keba, dan haka duk kan inda nason zaki iya zuwa ki kwana to yazama dole musamu muhalli mu, inda zamu shaÆ™ata ko musha Æ™auna ya Æ™arasa yana kashe mata ido. Cikin tsananin jin dadi ta rungumeshi ta saki kuka tana faÉ—in " ni banmason da mene zan sakamaka ba ,baby ka gamamun komi arayuwa wallahi, Allah ya Æ™aramaka lafiya ya bani ikon sake kyautata maka . Yace "Ameen sweety nah muje ciki. Ciki suka shiga suka iske ÆŠaki na alfarma mai masifar kyau yasha kayan alatu harda kiching aciki komi dai a wadace. Kayanta ya shiryamata yafito sukayi wanka, a haukace suka fito suka fada gado sai da sukayi ibada kana suka mike sukayi wanka. Suna fitowa sukaji ana buga gida. Jallabiya yasa ya fito ya buÉ—e. Anan yaga wata yar budurwa ta gaisheshi cikin ladabi tace "Yayah ga abincin ku kaida Aunty Amnah, anjima zandawo ingaishe ta. Karba yayi yace" Nagode ya sunan ki? Tace "Sunan khadija. Yace" ok tom mungode. Anan yashiga ciki ya bude kulolin masu tsananin kyau komi a tsaftace, yaga tuwon shinkafane da miyar agushi yaji naman kaji sai kamshi yake . Dayar kula kuma naman rago ne yasha suya sai kamshi yake zubawa. Yawu Amnah ta haÉ—iye ko kaya bata saba ta diro ta zauna bisa shi ya fara bata , Yana tsokanarta dan yana ganin yanda cikinya ke tsananta halbawa alamun a buÆ™ace take data faraci.. Kwanan su biyu sun samu kyakyawan kulawa suna zauna lafiya da kowa ,yayin da tarbiyya yaran gidan duk ta canza dan an'wadatasu da komi da ilimin zamani da Arabic, kuma shima Baba yaga ba a baÆ™in ciki yanzu yasaki hannu, gidan shi komi awadace, Da Amnah zata dawo rago aka yankamta aka soye mata ,aka basu suka taho dasu ,da manshanu, kwan zabbi, zabbin kansu saida aka yanka aka zubamusu akwali suyi tsaraba. a takaice sunga kulawa mussaman wajen yayyun ta maza, cike da kewa suka dawo gida suka rarraba tsaraba suka adana sauran gida. Bayan sati biyu tana zaune palo tana waya da khadija da jinin su yazo daya da Amnah, suna mutunci sosai. Wayar Mamy ta shigo wayar ta hakan yasa sukayi sallama ta kira Mamy. Bayan ta É—auka tace" Amnah yaudai an'sanya bikin Amal da Abbas wata hudu masu zuwa saboda haihuwar ki kana hankali ya kwanta. Ihu ta saki tafara murna, Tace Mamy kuma baki fadaman ba da banzo ba. Tace" Amnah nifa cikin nan tsoro yake bani, sai inga kamar yafi wata biyar. Murmushi tayi tace'' Mamy ni damuwata ma kayana basamun yanzu, danma jiya Baby ya siyomun dogayen riguna marasa nawaie ,mamy kodai mutuwa zanyi ta karasa cikin rauni. Mamy tace "A'a Annabin dama duk inkana da ciki abinda kake gani kenan, Insha Allah lafiya klau zaki haihu, Allah ya rabaki lafiya kinji, daganan sukai sallama ta kira Amal akan ta kyauta da bata faÉ—amata ba. Tace "Maman yan ukku zanzo ina school ,in na'tashi zanbiyo in miki yini ta kashe wayar. Murna tai'tayi Da kyal ta mike ta shiga kiching ta É—an fara girkin abunda bashi da nawi da zata tari yar uwar ta dashi. Karar buÉ—e get taji ta tabbatar Sadeeq ne dan Ammi mafiya lokutta gidan Nene take wucewa tayi zaman ta sai dare ta dawo, hakan yasata sakin murmushi tace" Baby yadawo dole in kashe girki. Tana kokarin fitowa kiching din sai gashi ya shigo cikin tashin hankali daya kasa É“oyuwa a fuskar shi. Æari jikinta ya kama da hannu take mai magana akan mene dan bakinta ya kasa magana. Control É—in kanshi yayi kadan yana rungumota yace" kwantar da hankalin ki kinji Sweetheart. Cikin rawar murya tace" miyasamu farin cikina ne, Dan Allah ka sanar mun tinkamin numfashina yabar ganga jikina.. ÆŠagota yayi suka zubama junan su ido. yace'' Amnah aiki za'aturani cen Barno, a Æ™alllah zanyo wata biyar kamin indawo , Amnah da in rasa kusanci dake ko lokacin da zan kula dake kwara in ajiye aikin nan in fadama kasuwancina, ta yama zantafi inbarki a haka bazan iyaba gaskiya.. Sosai gabanta ya faÉ—i Amma bata nuna mai ba, sai ma murmushi Æ™issa data saki tana mai jan hannu shi palo ta zaunar dashi , tare da Æ™arasawa wajen fridge ta É—akko mai ruwa mai sanyi sosai ta kawomai , Tare da tsiyayami a cup, saida ya shanye tass ta Æ™aramai ,ya shanye kana ta karba ta ajiye gefe. Zama tayi tana cije baki. Hannu shi ta kamo ta É—an murza tattusan hannuta kadan ciki kana tace'' Daddy Saleem!.. Da sauri ya kalleta tare da washe baki. Murmushi ta saki ganin tarkonta na neman kamawa. Tace" yaushe ne tafiyan? Yace "nan da wata É—aya? Tace wata nawa zaka yi? yace'' 5 Tace "Baby so da kaunar tallafawa Æ™asar ka da kare rayukan al'umma koda kai zaka rasa naka yasaka aiki hakane? Kai ya jinjinamata yace tabbas". Tace to danmi kuma a'yanzu zaka bijiro da wannan son kan,ka nuna kafison naka da aikin da kake kare dubbani mutane dashi , Baby wallahi na fika jin zafi da raÉ—aÉ—in rabuwar da zamuyi,to amma in natino da halak dinka zaka nema da taimako sai inji natsuwa, tare da kwarin gwiwar binka da Addu'a da fatan nasara, Dan haka Dan Allah da manzon sa karka ajiye Baby, kana tare da Addu'a iyayenka da matarka da izinin Allah zakayi nasar akan cikar burin ka, fatan ka kulaman da kanka ka rikemun amanar kanka, Baby Dan Allah! ta karasa hawaye na sakko mata. Gabaki daya jijiyoyin kanshi sun'mike, maganata ta kashemai jiki, kuma ta kulle shi da mukullin da bazai iya buÉ—ewa ba. Jikin shi ya jawota yace" Amnah in na tafi waye zaibani makwanci mai kyau? Ma'ana damtsen hannuki da yazama makwancina filo na sama da watanni biyar.? Waye zai dinga shayar dani har inyi bacci. Ma'ana Maman da kike bani kana bacci ya dauki ni?. Amnah wazai tadani da sassanyan kamshi irin na jikin ki.? Ma'ana tadawo da kikemun cike da salon So da kauna gangar jikin ki akaina kina huraman Dadda É—an iskan bakin ki mai saukar da natsuwa. Amnah zanrasa komi baki daya, ganin ki ,jinki, girkin ki ,uwa uba jikin ki. Hawaye ta share tace" kayi hakuri Baby Dan Allah, muyi addua Allah ya bamu dangana, wallahi duk kan abinda kakeji inajin fiye da haka, to amma yazanyi dole in daure in baka kwarin kwarin gwiwa shine cikar so.... Kai ya jinjina yana dafe kanshi da yaji yana sarami saboda tsananin bacyin rai... Cikin son taga ya saki jiki tafaramai abinda yake so ta hanyar fara bud'É—e butter din gaban rigar shi, tare da tausa hannuwanta akan kwantacen galgasa dake jikin shi . Ajiyar zuciya ya fara saukewa tare da juyota gaban shi sosai. Tsaye ta mike tana diddire Æ™afa da turo baki dan son faranta mishi tace "nidai gaskiya yunwa nikeji kuma ga goyo ina so kamun. Yacei to muje kici abinci sai ingoyaki amma taya? Tace "gashi ba, ta faÉ—a tana nuna kanshi. Ido ya zaro tare da sakin dariya farin ciki gabaki daya ya sungumeta suka haura sama, cikin lokacin ta mantar dashi sunan sa sai gashi bayan shiÉ—ewar wani lokaci sun sakko suna ta sakin fara'a. Rakiya tamai ya fita dai-dai lokacin da Amal ta shigo, bayan sungaisa ta wuto ciki Amnah kau saida taga ya fita kana ta dawo fuskarta cike da Annuri. Sosai sukasha fira sai dare Amal ta tafi bayan suncikata da kayan azziki.. Bayan wata daya suna zaune akan gado sai ihu suke suna kwasar garaÉ“asa ,ihu kawai sadeeq keyi yayi'n da Amnah kena azaba, Dan iya galabaita tagaji ga katon ciki amma haka yake haÆ™arta baji ba gani. Saida wayar shi ta shiga ring kana ya sarara mata ya mike yana haÉ—a hanya yashiga toilet , bayan ya tsarkake jikinshi ya fito fuskar shi som babu annuri ya fito asalin sojan shi. Amnah da tayo wanka É—akin shi ta shigo tana kallon shi, tayi Æ™asa dakai tare da share hawayen ta dan bataso ya gani. Wayar shi da aka sake kira ya É—auka afusace. Abbas yace Yallabai munafanan airport kaikawai muke jira. Tsaki yayi yana kashe wayar... Amnah ta Æ™araso wajen shi da kyal ta É—an tattaimakamai yasanya kayanshi, Dama jikka shi ta shirya mai ita, ta É—akko ta tayi tsaye tana kallon shi.. Kallonta yayi yace "kema bakyaso Sweety amma kin tirsasa ,bayan inada sana'a da zata rikemu. Wannan tafiyar ma ni bana da tabbacin dawowana ko akasin haka,amma bani da yanda zanyi tinda Nasa ba tafiya na tattare da kwarin gwiwarki.. rungumeshi tayi ta fara jeromai Addu'a tsari da kariya daga Allah Subhanahu wata'ala.. SundaÉ—e a haka kana sukayi sallama ta yomai rakiya yanata shafa cikin ta. Abakin Æ™ofa sukaga Ammi sukayi mai bankwana yana dagama su hannu suna dagamai, har suka ficce idon shi fess akan Amnah daketa hawaye tana É—agamai hannu... Kamar kar yatafi amma ya daure suka fita cike da kewar ahlin shi. Amnah kau na ganin ya fita ta rushe da kuka. Ammi ta kamota tafara aallashi akaron farko tajata suka nufi part É—in su Amnah anan suka zauna tashiga bata baki. Suna a haka saiga Nene da Hamrat da Amal da katuwar jikka . Nene tace'' a'a ikon rabbi. Yar kwal uba kamar ba itace kecewa bataso ba, to miyasa kike kuka, dan baya nan kawai?ke kaji É—iya, inya zauna Uban mi zakimai,m da wannan tuÆ™eÆ™en cikin naki kamar mai girmana zaki haiho.. Cikin kuka Amnah tace tubarkallah Bissimillah. Hamrat kau da sauri ta isa wajen Amnah tana shafa cikinta tace" Aunty da gaske zaki haifo muna Baby ,To mai kama dake ko mai kama da Baby?. Cikin murmushi ta share hawaye tace" insha Allah mai kama da Baby zamu haifo Baby'n Baby kinji?.. Kai Hamrat ta É—aga cikin gamsuwa da farin ciki. Amal dake waya tana yar kwallah ta kalli suka haÉ—a ido da Amnah... Harara Amnah ta sakarmata hakan yasa ta mike tayi É—akin Amnah tana tama Abbas kuka shagwaÉ“a duk ta rikitashi. Amnah ta shigo É—akin hannuta rike dana Hamrat ta zauna bakin gado. Amal tamai bankwana ta kalle Amnah. Amnah tace saboda baki da kunya saurayin ma zakima kuka, toni da mijina ya tafi nace mene? Amal tace" Aunty bazaki gane ba, Abbas yayi arayuwa ,bashi da hayaniya som , Abinda yasani kuka bikin mu da suka aiko aka Æ™ara É—agashi an'maidashi wata shida, sai bayan yadawo da wata daya kinga kuwa dole inyi kuka,Ina son Abbas bana fatan yaga wadda ta fini ya koma mata. Zatai magana sukaji Nene na salati tana faÉ—in" Allah ya tona muku asiri munafukan Allah....? 6/1/22, 20:33 - Ummi Tandama😇: *Littafin🌹DAN DAKO🌹 na kudi ne biya ki karanta cikin Aminci. Biya 300kacal to 0006454115 Amina Dahiru jaiz bank,or MTN card to this number 09165832002. then send the evidence of payment via 07038423451* ðŸ¤ðŸ™ðŸ¤² Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Yan uwana mata ina kuke ku malmatso ga wanni sirri da nike son baku, ita ya mace sai da kamshi, ina macen da take ganin izgili da wulakanci da ake cewa maza nada shi, hmmm yar uwa to inkin kasance a haka da alama akwai ayar tambaya akanki. Tambaya ta ta farko gareki da wane irin turare kike amfani a jikin ki ?,da wane irin turare kike turara gidan ki,shin dawane irin turare kike Zukunni, hmmm to matso kusa kiji yar uwata. Shi kamshi Annabi muma ya faÉ—a abin sone,kuma Abune mai sanya natsuwa da girmama ma'aboci shi , Da Yawon son kusantar sa. Duk kan wulakanci da izgilanci na maza akwai turaran da zai miki maganin sa da izinin Allah,ba boka ba malam,wanda zai karkato da hankalin mijinki akan ki ku samu fahimtar juna. Ko kin son kamshi na dakusar da fitinar É—a namiji yar uwa? kigarzayo ki kwashi rabonki ga shaharariyar yar mai Dugurin nan mai suna UMSAD INCENSE ,Mace mai kishin mata da son Fiddo martaba mu. Nayi Amfani da turaranta naji masifar daÉ—in da yasa nakasa barwa raina. Nace bari in yaÉ—amuku dan kowa ya mallaki nashi cikin farashi mai sauki. Da fari bari in zayyano muku su kamar haka.👇 Maleek Al'oud Royal kush Cous-cous Kajiji Original sandal Sandal flex Sandal bange VIP mix Hawi Al'oud Kindikay Danal banat Darot Habil Gaf-Gaf Sirrun nisaa'i Sandal chips Kwalacca Humra black and body milk Attractive humra. Yar uwa zanmiki Dallah- Dallah. Akwai turaran da zaki sanyama kayanki . Misali! kisa kabasa kiturare kayanki . Akwai humra da bazaki sataba sai zaki turaka. Akwai turaran kaya ,na jiki, Dakuma na É—aki. Akwai kwallaca sirri, amma bama badata gaskiya sai ga wanda baida kishiya , Dan muddum kina amfani da ita tofa gabaki dayan hankalin mijinki akanki zai dawo,Dan yana juyo da hankalin namiji akanki baki É—aya ,zaki zama shalele Baby, Akwai sirrin nisaa'i. hmmm Dagajin sunan kason na dabanne,na baki sati É—aya ki gwada ki gani Hajiya ta, tsugunno ake akai ga mai buÆ™ata ya tunÉ“e mu ta wannan layin 08028827241 karku manta UMSAD INCENSE mune na É—aya. Muna aika kayan mu duk inda kuke. Kamshin jiki martaba mutum.... 6ï¸âƒ£3ï¸âƒ£&6ï¸âƒ£4ï¸âƒ£ The end. Alhamdulillah Allah na gode maka daka bani aron rai da lafiya na kammala wannan littafi nawa mai taken ÆŠAN DAKO, kuskuran danayi Allah ya gafartaman,Naga so da kauna a masoyan littafin nan, bana da bakin magana gareku dan kun nunamun so da kauna, zallar kulawa da babu algus, kyautatawa da darattawa , Nagode- nagode over, ina yinku fans É—in DAN DAKO, dama duk kan wasu mabiyan sa, da masu sata duk inayinku kuma nagode sai munhaÉ—u Asabo mai zuwa nan kusa insha Allah mai suna ÆŠIYAR SHEKH, Hmm fans karkubari ayi baku ,farin cikin ku shine nawa, kaÉ—an daga cikin labarin É—iyar Shekh zaizo muku kasan page nan nagode.... -------""Amnah ta kalleta cikin mamaki tace mene mukai miki Nainah kike cemana haka.? Nene ta sake tafa hannu tace "shegiya soyayya, harda sunan da mijin ta ke kirana dashi ta koya, to ai gani nayi kunzama yan iska kuna labarin Samari,. Amnah tace "Nene iskancine ? bayan begen mijina nike , Wallahi nidama banbashi shawarar ya tafi ba tafada tana turo baki. Dariya Nene tayi tace" ke taso yar jikanyata kinji ko, ga KwanÉ—on zagale cen namiki, nizan zauna dake in'kula dake harki haihu, kinga harda sabuwar reza nazo da ita dan Bansani ba kar tashin hankali rashin miji yasa ki haifi Biyar ni Bama bakwai ni ba. Dariya Amnah tasa tace" Allah ya kiyaye Nene, Taranni na zan haifa insha Allah. Dariya suka sanya suka sakko Æ™asa,Anan suka iske Ammi ta shirya musu dinning. Bayan sunci suka fara lallaÉ“a Amnah,Dan ko motsi tayi zasu tambayeta ya'ya? Zatace bakomi agefe guda kuma kewar mijinta ne sosai a ranta. Bayan wata ukku. Rayuwa Amnah keyi mai daÉ—i da Ah'linta, da Maman Dee, dan dai akwai kewar mijinta sosai ga rashin waya da basayi sosai, dan aiki suke sosai ga Dajin da yake babu network, hakan yasa tinda yaje so ukku sukayi waya, sosai kuma hakan ya damu Amnah har rama tayi, dan ma su Nene na iyakar Æ™oÆ™arin su wajen ganin sun inganta kulawarsu akanta ,da Baby'n ta, Dan har awo take zuwa itada Amal suje sudawo . Lokacin da cikin ta yakai wata tara dole Amnah tabaka tausayi, Dan dukkan halittunta sun canza, ta fita hayyacinta ga kewar Miji kullum sai tayi kuka,ga zullimi haihuwa ,ga cikin yayi masifar girma hakan yasa wata rana Nene sai ta sata gaba ,ta buga tagumi tana kuka . "tana faÉ—in nidai Allah yasa ki iya haihuwar wannan ciki, Kamar an'maki ciko da tankin ruwa , Amnah abun nan na bani tsoro Wallahi, kodai an'maji jifane ciki kar ace harda jinjirin jaki ciki kamar yanda naga Amma wata mata ,sai sufashe da kuka baki daya har sai Ammi ta shigo ta lallahe su kana su daina. Wata safiyar talata suna waya da Sadeeq, sai murna take hakan yasa yacemata yana kan dutsi tayi maza ta nunamai Baby shi zaikoma bakin aiki, wasu É“arayi ne suka kaima farmaki. Cikin sauri ta mike tsaye ta yaye Æ™aramar rigar dake jikinta tana gwadamai ,sai sakin murmushi yake yana fadin Saleem ga Daddy'n ka ,kamun Addu'a nasara kaji, ka daina bama Mommy wahala kaji ? . Amnah zatai magana taga wani ya lallaÉ“o ta Bayan sadeeq ya bugamai sanda. Ihu ta kwallah cikin tsananin tashin hankali dai-dai da faÉ—uwar wayar tashi komi ya dauke sai duhu. Kuka ta fashe dashi sosai tana faÉ—in. "Allahumma a'jirni fi masibati, wa ak'lifni khairan minha. Hazbunallahu wani imal wakil, la'ilaha illah anta subhanaka inni kuntu mina zalimin. Ya rabbi ,ya hayyu, ya Æ™ayyum,kar kaba magauta damar sukar Mijina, ya Allah kaji tausayina, kaji tausayin abinda yake fatan gani dare da rana, Ya Allah! ta fashe da kuka tare da kasa Æ™arasawa lokaci guda kuma cikinta yayi wani mugun murÉ—awa. Hannu ta yarfe tana mai Æ™oÆ™arin sakkowa daga kan gadon ,ta cike baki ta sakko Æ™asa tana salati, tare da Æ™oÆ™arin jawo wayar ta dake kan mirrow amma ta kasa. Sosai takejin cikinta na yamutsawa, Æ™ugunta,da bayanta sun wani irin rike sai neman cirewa suke. Koda batason haihuwa ba ta tabbata haihuwa zatai Tinda ta karanta, Hakan yasa ta fara kwalama Nene kira. Amma da yake cikin Muryar galabaita ne babu wanda yajita, dan zaune suke palo taga kiran Sadeeq ta haura sama, har Nene nacemata kilbabba tace bata iya tashi amma da miji ya kira ta mike... Kimanin awa É—aya Amnah na wajen tin tanajin dai-dai har ta fara fita hayyacinta. Hankalinta in'yayi dubu tashe yake, ta tabbata itama mutuwa zatai, gashi bata son makomar halin da mijinta yake ba. Cikin kuka tace" Allah ka fitar mun dashi da karfi tanajin wani abu na turomata, Hakan yasa da sauri ta Dauki bargo ta shimfaÉ—a ta haye sama, tafara sakin dogon nishi dakesa taji kamar ranta zai fita. Ciki ikon Allah tana sake wani nishi taji Kan yaro, hakan yasa cikin jarumta ta sake dafe gadon ta tafara sakin nishi da masifar Æ™arfi tana rintse ido. Gabaki daya yaron ya faÉ—o bisa bedsheet yana Yan-yara kuka . Ajiyar zuciya ta sauke cikin Tsananin galabaita, tare da fara yunkurin tashin dan É—akko akwatin gaggawa, amma ta kasa jin wani masifaffan ciwo ya sake tunkarota, tare da dannowar wani Baby gabaki É—aya. Ido ta zaro tana sakin kuka tare da yarfe hannu tace "Shikenan Nene, mutuwa zanyi kun kyaleni ,na shiga ukku, zan haifo yan cikina ta karasa tana yarfe hannu tare da sakin nishi, sai ga Baby ta fado tana canyara ihu mai masifar Æ™ara, da alama akwai zajin murya.. Ajiyar zuciya ta sauke ganin uwa ta biya, hakan yasa ta dora kanta akan gado tana sauke ajiyar zuciya ,tare da bin yaran da kallo cikin tsananin galabaita... Kamar wasa Nene tazo daukar abinci ta kaima Amnah taga taki sakkowa sama da awa biyu taji kamar kukan jariri. Shuru tayi tana sake saurarawa. Tabbas kunnanta ba gizo yake mata ba ,hakan yasa cikin sauri ta ajiye abincin ta ruga da gudu É—akin Amnah, gabanta na faduwa ta tura ta shiga. Wayam taga palon, da sauri ta tura bedroom É—inta inda sautin yafi fitowa. Anan taga Amnah duke Æ™asa ta É—ora kanta akan gado, sai lumshe ido take ga yara zube bisa bargo. Ihu Nene ta saki tare da fashewa da kuka aguje tayi É—akinta ta É—akko sabuwar reza tana share hawaye, tazo ta rungume yaran ta yanke cibinsu tare da shimfiÉ—asu bisa gado,Da kyal ta miÆ™ar da Amnah suka nufi toilet. Suna shiga ta zaunar da ita a kan sit ta fito da gudu tayi part din Ammi. Ko sallama batayi ba cike da ruÉ—ani take faÉ—in zaman mu yazama na banza ,munzama Æ™attin wofi ,,bamu rike Amanar kwandon sukari ba wallahi, Maryam fito kiga .. Aguje Ammi da Amal da Hamrat suka biyota hankali tashe suka haura sama,Tare da tura É—akin Amnah. Anan sukaga yara biyu sai tsotsar hannuwa suke... Gaban ammi ya fadi tace" Nene minike gani haka, ina diyar tawa?. Hararata Nene tayi tace" bansani ba, Bayan tagama duk kan Æ™oÆ™arin ta kana mukazo , Wallahi Amina jarumace, Ita kaÉ—ai ta haifo yaranta biyu sak, ga sunan ki kula dasu in'kinga dama bari inje wajenta toilet.. Cikin tsananin farin ciki da godiyar Allah Ammi ta karasa wajen, kyakyawawan yaran da idonsu yake abuÉ—e sai kokarin tura hannu suke cikin baki ta zubama ido ,Tana ganin tsananin kamarsu da iyayen nasu.. Gabaki É—aya ta haÉ—esu ta rungume ta saki kukan farin ciki, tana godiya ga Allah, Amal da Hamrat kau sai ihu suke suna farin ciki Sunyi Ya'ya. Ammi ta bada umarni wa Amal a haÉ—omata ruwan zafi toilet din Sadeeq. . Dan Danan ta kawomata ta wankesu tas aka naÉ—esu cikin towel É—in su mai tsananin taushi... Nene kam bayan ta shiga toilet ta iske Amnah zaune sai kuka take, kamar ranta zai fita. Itama kukan tasa tace'' wallahi Amina bansani ba ,kiyi hakuri kinji tawajena, banson haihuwa zakiyi ba, naga yanzuma watan naki yakama, baifi kwana ukku ba,Nason sai kince dan naga ubanki gero yake saidawa to bahaka bane banjiba kinji... Amnah tace'' Nene Yah Sadeeq, akwai abinda ya faru dashi ,muna tsaka da waya naga wani ta bayanshi ya daga sanda ya zubamai ,daga nan wayar shi ta faÉ—i, kinji silar haihuwa ma Nene, Wallahi wani abu ya faru bazan yafewa kaina ba, saboda harda son ya farantamun yasa yace muyi Vidio call, gashi na dauke hankalinshi har wani ya cutamun shi. Salati Nene tai ta saki tana tafa hannu,, sosai Hantar cikinta ta kaÉ—a, amma ta lallasheta tare da faÉ—in ta tayashi da addu'a insha Allah yana lafiya, Allah zai É—orashi akan su... Shuru tayi har Nene ta gyaramata jikinta tass kana suka fito . Inda taga su Ammi taita jeramata sannu cikin tsananin so da kulawa. Suna palo zaune saiga Mamy da Hajiya Turai,m sunyi sallama sun shigo, fuskar su cike da farin ciki. Anan suka gaggaisa Hajiya Turai taja Amnah wani É—aki, nan ta umarceta da ta tsaya ta dubata. Bayan ta dubata ta fahimci dole a mata É—inki, dan ta Karu Sosai. Haka ta fiddo kayan aikin ta dan dama Asibiti take Mamy ta mata waya shiyasa ta haÉ—o komi Tinda ta gida ce... Anan ta ÆŠinke Amnah tass ,kana ta kamo hannuta suka fito tana tafiya A'hankali, dan ita bama murna haihuwar take ba lafiyan mijinta take neman taji. Tana zama tace'' Amal kirawoman Abbas,kiji ya suke. Da sauri kam ta É—aga wayar ta, anan tayi Sa'a tashiga, dan itama ba kullum suke wayar ba. Bayan ya É—auka taji muryarshi ba cikin walwalaba, hakan yasa tace" Honey lafiya?.. Yace ki tashi daga cikin mutane muyi magana. Tashi tayi tana kallon Amnah da ta bita da ido cike da hawaye, Amal na shiga tace" inajinka lafiya dai ko? ina Yah Dee? Abbas Yace" Amnah mutayashi da Addu'a Dan ita yafi buÆ™ata,, É—aya daga cikin yan ta'adda ne ya bugamai sanda agefen wuya , Amma yayi nasara kasheshi ta hanyar halbi,yanzu haka muna babba Asibitin cikin garin munkawoshi, Dan baya mikar da wuyan Sosai.. Salati tasa tana sakin kuka tace" kar dai kacemun ya samu naÆ™asu?. Yace'' A'a Amal insha Allah bama fata, buguwace kawai, ai'munmayi nasara insha Allah bazamu jima ba zamu dawo . Hawayenta ta share tace'' to yanzu.. Da sauri yace yawwa likitocin sunfi to ina zuwa ya kashe wayar. Zama tayi É—akin cikin zullimin abinda zatacema yar uwar Tata.. A palo kau Nene ta shiga kiching ta haÉ—oma amnah Tea mai kauri tabata Amma tace A'a ta Æ™oshi. Nene tace'' wai miyasa kike haka? Kuka tasa tace Nene" bansan ya yake'ba, kuma Amal ta tashi daga kusa dani, Dan Allah kice tazo ta fadamun halin da ake ciki, Wallahi inaji ajikina Baby na cikin matsala.. Anan duk yan palon suka fahimci akwai damuwa, bayan Mamy ta tambayi ba'asi Amnah ta faÉ—amusu, Hankalin kowa ya tashi sukayi jugum- jugum.. Nene tayi Æ™arfin hali ta kwalama Amal kira. Bayan ta fito suka zubamata ido. Ƙasa tayi da kanta tana share hawaye. Jikin Amnah ya É—auki rawa tace "sun kasheman shi ko? dama ya faÉ—aman ta tafi luuu zata fadi , Ammi ta tare ta tana share hawaye tace muyi Addu'a kinji. TaÆ™arasa cikin dauriya dan ita kaÉ—ai tason yataji.... Amal tace Aunty" bai mutu ba ,sundai bugamai sanda agefen wuya, sunje Asibiti Abbas yaban tabbacin kwana kusa zasu dawo ,saboda aikin ma ya kare tinda duk sun kashe wayan da ake zargi, da kuma wa'yanda keda sanya hannu a ciki.. Nene tace to sake kiramana Abashen kiji mana. Amnah ta sake kira ya É—auka cikin farin ciki yace "Dear Alhamdulillah Abinda muke tinanin zai faru bai faruba , Buguwace kawai yayi, yanzu haka sun'samai abu a'wuyan sunbashi magani, kai tsayema gida zamu wuto insha Allah, zuwa dare ko yamma muna tare daku. Ihu ta saki cikin jin daÉ—i hakan yasa ta datse kiran tana faÉ—amusu, take palon ya rikice da murna saiga Annabin na fadin Nene kubani Tea da abinda na haifa... Dariya suka sanya su duka . Suka bata su ta shiga kallonsu, kyawawa ne ajin farko,masu tsananin kama da juna ,sunbiyo ta, sunbiyo Baban su sosai, take taji Æ™aunar su na ratsa bargo da jijiyar ta. Nene ta kawo Tea da felfesu sai kamshi yake ta zaunar da Amnah ta bata taci sosai ,kana tace su tashi su tafi sukwanta ta huta. Anan Amnah ta tashi Amal ta biyo ta da yaran,suna shiga ta iske É—akinta tass sai masifaffan kamshin turaran wutar UMSAD INCENSE yake, duk kan wani Æ™arni haihuwa ya dakushe shi, ga lafiyayyan zanan gado mai taushi. Amal tace''" Aunty kibasu Mama sufara sha saiki kwantar dasu, sai kema kisamu bacci ko?. Cikin gamsuwa ta É—aga kai tare da zaro Mamanta daya cika kamar ya fashe tamai Addu'a kana ta tausama namiji a baki. Kamar jira yake ya fara sha cikin natsuwa, saida ya Æ™oshi kana taba Baby' guda, halam -halam takama tana zuÆ™a da masifar Æ™arfi har Æ™ara saida Amnah ta sanya. Amal taita dariya tana fadin "Wannan kece, wannan kuma Yaya nane ta nuna boy É—in. Duka wasa ta kaimata ta tashi ta ficce tana dariya.. Amnah na gama basu ta kwantar dasu tana sakin Murmushi, ,tare da binsu da kallo har baccin ta gajiya yayi gaba da ita.. Kamar wasa cikin baccin ta farajin ana shafa fuskarta , tare da kissing din lips É—in ta cikin tsananin buÆ™ata. Da sauri ta buÉ—e idonta ta saukesu fess akan farin cikin rayuwar ta dake ta zuba murmushi mai Æ™ayatar wa . Cikin tsananin mamaki take binshi da kallo, wani irin farinciki da baida misali, Tare da murje idonta dan tabbatar da gaskiyar abinda take gani gabanta . Kai ya jinjina mata yana kamo hannuta yace. "Sweetheart nine dai mijinki, na iso gareki a lokacin da natabbata kinfitar da Ran sake ganina da Æ™afafuwan sai dai ko gawana. Dariya farin ciki ta saki tare da miÆ™ewa ta rungumeshi sosai tana tsalle farin-ciki tama manta da haihuwa tayi sai sumbatar ko ina na jikin shi take. A'hankali yace" Sweety Baby nah karki taushemun shi fa.. Da sauri ta kalli gadon taga wayam ba yaran. Tace "kai ina yarana? Cikin mamaki yace" wane yara kenan? ya faÉ—a yana kallon cikinta da har lokacin yake a kumburr kamar bata Haihuba.. Tace kai Baby kana nufin bakaga yaran da na haifa ba?.. Fuskarshi cike da mamaki yake kallonta. Irin kallon ko mafalki take bayan ga ciki jikin ta. Zatai magana Nene ta turo kofa ta shigo hannuta rike da yaran da har an'canzamusu wanka sunyi kyau sosai, sai kamshi suke ta nufo wajen shi tana rawa tana jijjiga yaran tace" ga yaran kwandon Sukari, dama ni na É—aukesu danaji shigowar ka,, na kumayi worning akan duk wanda ya faÉ—ama ta haihuto saina cimai mutunci, gasunan nasake shiryasu, da yake Namamajo ne kai har ka iso wajen mataka ko? To maza a fita waje. Murna tasa ya kasa koda kwakwaran motsi, sai kallon yaran yake yana kallon Nene ya kalli Amnah. Kan su ankara ya juya ga Annabi ya sunkuceta yayi sama da ita sai juyi yake da ita cikin tsananin farin ciki yake faÉ—in" kin biyani, kingama mun komi ,ina fatan Allah ya miki tukuici da Aljannah,Dan ni bantara abinda ya can-canta da kyauta agareki ba, kalaman Æ™auna kam babu wanda baifaÉ—amata bata daga karshe ya kwantar da ita akan gado tare da hawa kanta ya tausa bakin shi cikin nata. "Jiri yasa sauran kaÉ—an Nene ta saki yaran, aguje ta ajiyesu ta ficce tanajan Allah ya isa ta sauka Æ™asa tana dafe kirjinta , tace'' Allah yajikan Bashari Ba rabon kaga iskancin yaran zamani wannan ai kamin kwana arba'in in'bansa Ido ba sai dai inji wani nishi za'afiddo yan hudu... Amnah kau taga Æ™auna kamin ya koma ga yaran ya haÉ—asu duka ya Rungume ya fashe da kuka ,tare da kwantar dasu yayi sujjada nuna godiyarshi ga Allah, tare da dawowa ya É—aukesu ya fara sumbatar su... Amnah tace'' Baby ya jikin ka. Yace "Babu ciwo, yau ko kasheni akai indai zansamu Aron nunfashin da zanga wayan nan kyakwawan yaran da Allah yabani to zan godemasa kamin in koma gareshi, Alhamdulillah! Alhamdulillah !!ke Alkhairi ce gareni matata, haihuwar yaran nan nasarace gareni, gashi aikin da aka shiryama wata shidda wata hudu ya yishi ,an'gama cike da nasarori. Wuyan shi ta shafa inda keda bandege tace " Allah ya sakamaka Baby kaji ,kayo wanka kasha magani sai ka kwanta ko. Murmushi yayi yace "bana gajiya da ganin ki da kyakyawan yaran da Allah yabani ,ni banmason da mene zangodemasaba Wallahi. Tace "kaciyar da marayu, ka kyautatama wayanda basu da shi, kayi yafiya da juriya ga wanda ya É“atama, shine kawai abinda zakayi... Ki ya jinjinamata cikin gamsuwa ya kwantar da yaran ya tashi ya shiga part dinsa, yayo wanka Amal ta kawomai abinci yaci kaÉ—an yana rike dayaran, yaba Annabin abinci saida yaga ta koshi kana ya É—orasu akan cinyarshi ya fara musu photo, sunyi masifar kyau suduka annuri ne A fuskar su. Washe gari gidan ya cika da mutane dan gabaki daya yan gidan su Amnah sun iso ,harda matan Baban ta dangin Baban ta kowa da kyauta da Allah ya horemai da yazo da ita. Hakama matan Abokan aikinsa sunata zuwa, kuma suna samun tarba ta mutunci. Gefe guda kuma soyayya suketa kashewa sai Nene tayi dagaske yake komawa É—akin shi yana fushi. Da yamma aka yanka Raguna manya guda goma akaita rarrabawa sadaka,Daga baya aka zubamai wani mai yawa a ledoji ya nufi gun almajirai dake bara bakin titi ya fara rabamusu,Har ya juya zai shiga mota yaga wani mutum zaune bisa keken guragu da wata matashi budurwa na turoshi. Tsayawa yayi cikin tausayawa yace "Ayyah yakuwa Æ™are bakusamu ba. Da sauri Yarinya tace" Uncle Dee. Kallonta yaui da sauri tare da zaro ido yace kune dama har yayi zuciya zai shiga mota ya tino kalaman amnah(kazama mai yafiya ga wanda ya cutama). Kuka Alhaji Musbahu yasanya yace sadewq ina nemanka sosai dan neman gafarar ka natabbata alhakinka bazai taÉ“a bari in rintsaba da halin da nike ciki kware ace namutu. Tin ranar da ka watsar damu takaici yasa na sume ,matata ita kuma ta falka,tana ganin halin da nike ciki ta dauke motar tayi gaba abinta, ta barni da Bily dako tafiya batayi,kwanan mu ukku a haka inba É—oyi da Æ™afana keba bakajin komi awajen da mukex dan ni ba kafa bily ma haka. Daga karshe wani makiyayi ya taimakamuna ya kaimu asibiti aka taimakamun aka yanke kafa, ita kuma akamata magani amma har yanzu bata iya tafiya ita kadai saida abu, shiyasa kawai muke yanke shawara zuwa nan nemanka ka yafe mana ko munga haske, Rashin ganin ka yasa muka fara bara ,tana turani har musamu na abinci . Kai ya gilgiza yace in Umma. Kuka Alhaji Musbahu yasa yace nima bansani ba banganta inda muke ba. Sadeeq ya zaro kuÉ—i masu tsananin yawa yace "gashi kunyi wani abu yafara Æ™oÆ™arin shiga mota. Kuka yasa yace" baka yafemun ba? Yace Allah ya gafartamana tare da faÉ—awa mota yayi gaba yana share hawaye tino yanda akama mahaifin shi da Æ™anwar shi... Ranar suna yaran suka ci sunan Sadeeq ana cemasa Saleem ,Ita kuma macen Amina, ana cemata Saleemah, aiko sunsha tsogwami wurin Nene tace. *Basuyima kowa karaba sai kansu, dan har kaya ta ta hada tace iskancinsu ya isheta, taya zasu dinga wulakantata suna iskanci gabanta. Dariya akai tayi ana bata hakuri kana ta zauna aka cigaba da shagali, anci ansha kowa ya samu turmin atamfa mai kyau ,hakama mai jego tashiga ta fita kowa yazo sunan ya tabbatar dana yaran gatane ,dan gabaki shiga suke ta kece raini da mai jego da Ango jego da baby's,gashi gaba É—aya members É—in ÆŠAN DAKO Group babu wanda bai samu falleliyar atamfa ba ,kaji kam ba acewa komi,cen na hango su UMSAD INCENS ana ma mai jego kyaututuka da turarukan kamshi masu sanyi, inda naga su Mom Asas, Ummu yasmin, ruky, khaulat an'zage anata kwasar shoki da naman kaji, oum Adnan da oum ilham kau da Æ™aton cikinsu sai rawa suke , Aysha yar fillo na rike su saboda lalaurin da suke ciki. Gaba É—aya dai, da wanda ban ambata ba suna ciki, Jannat baiwar Allah Uwar marayu ,sai É—a'amin take tana jawomusu Ayoyi, kai kowa sai da yaci ya koshi, da yamma taro ya watse aka bar mai jego da ÆŠumbin kayan arzikin data samu. Da daddare Sadeeq ya dawo gida murna kamar me, inda ya tabbatar mata da an'bashi muÆ™amin mejor, sukaita ihun farin ciki da alkawarin hada gagarumar walima. Washe gari bayan an'gama soyen nama Nene tace" zata wuce da Amnah, inda Sadeeq yasa mata kuka Akan tayi zaman ta ai'shima jikanta ne, tayi zamanta dan Allah gidan sunfi jin daÉ—in ganin ta nan takama ma Amnah kula da yaran... Aiko Nene tace itama tanaso ta zauna anan tasamasu ido gudun ciki da goyi. Cikin farin ciki suka amince. Haka sukayi zamansu inda Nene ke kula da Amnah sosai ,tana gyara abinta da aiken da Mamy keyowa,yaransu kau masha Allah kullum girma suke suna daÉ—a wayo. Ranar da suka cika kwana arba'in washe gari harabar gidan aka shirya kwarya-kwarya walima ,ta matsayin da sadeeq ya taka anan fa gida ya cika sosai abunka ga ana ganin maiko- maiko. Gayya sukayi ta ban mamaki, inda akaci akasha ,sunsha kwalliya ta kece raini kowa da sonsu da begen su ya bar gidan bayan an'bashi kyaututuka masu yawa a babba jikka. Bayan taro ya watse suka dawo ciki, inda Sadeeq keta É—auki ya zama ango Amnah na mishi dariya. Ana gama sallah isha ya mikomata yaran tare da fiddo mamanta ua basu suka sha sosai kana ya sumbace su yace" to yaufa Daddy zaije filin danbe, dan haka ku bamu wuri yaran Daddy. Dariya tayi tace ina zasu?. Yace" wajen Nainah Fita yayi dasu yana ta musu wasa har É—akin Nene. Nene na ganin shi tace" oyoyo ga" Sallau da Salmai. Yace Gaskiya Nainah kidaina É“ata sunan su. Tace bazan bariba bani su nan tashi katafi kabani wuri. Dariya yayi yace haba ta wajena hajjin bana dake insha Allah? Ihu Nene tasa tana murna tare da faÉ—in" maza- maza tashi kaje ka huta, aini yau bani ba bacci sai raino. Fita yayi yana murna ya fada É—aki. Anan yaga Amnah ta Tsuke cikin wasu mahaukana riga da wando pink,yan kananu sai kamshi take zubawa, ta doso inda yake tare da rungume shi. Wani iri yaji shi ga numfashin shi na tsanan ta bugawa yanaji kamar ya haÉ—iyeta dan kamshi ta ya masifar hautsaina tinanin sa,Gaba É—aya baya ganin kowa sai ita.. Cike da buÆ™atuwa ya sunkuce ta sai kan gado. Cikin lokacin wasan nasu ya canza. Ganin halin da suke ciki yasa najamusu Æ™ofa nayi gaba. Bayan wata É—aya aka fara hidimar bikin Amal, lokacin ya kama su Saleem nada wata ukku, sunyi kubul- kubul masha Allah kamar yaran turawa. Amnah aka fara hidima dan sune manyan Yayye,Ga Sadeeq ya buÉ—emata bakin aljihu,Dan gabaki daya kayan dakin da akaima Amal sadeeq yayi su, yayin da Amnah kuma ta zubamata kayan kiching masu masifar kyau na zamani, takuma É—auki nawie abinci da akaci baki É—aya Atakaice ansha shagali daga karshe aka mika Amarya ÆŠakinta cikin sanya albarka iyaye ,Gidan Amal yayi kyau matuÆ™a,Dan Abbas Mahaifin shi mai Æ™udine Sosai... Bayan sati Daya da biki Abba ya shirya yaje gidan Amnah, anan ya fara musu Godiya irin karamcin da sukai mai, ko nera biyar basu bashi damar sawa a kudin saba. Sadeeq yace haba Abbah! ,am'fani ka haifi yara kenan masu albarka, ,yanda ka dauki É—awainiya da yarintar mu, ka kula damu tinda Allah ya kawo girman mu ya kuma bamu abinda zamu muku ai saiku zauna kuci moriyar haihuwa ,Kumana fatan muma Allah yasa namu su bimu. Abba yace hakane ya samusu albarka ya tafi. Rakiya sukai mai suka dawo suka ba Nene yaran Amnah ta kalleshi ta daga mai gira ,shima ita ya ÆŠagamata yana kashe ido É—aya, tare da bata hannu suka kashe ya duÆ™a yace hau babu. Da sauri ta haye tana dariya suka haura sama cikin farin ciki..... TAMMAT BI HAMDU LILLAH. ÆŠIYAR SHEKH. Kyakyawar yarin yace wadda tsananin kyanta yasa iyayenta É“oyen surar da Allah yamata ,ta hanyar tarbiyyantar da ita da rufe fuskarta da takunkumi, gudun kawo farmaki cikin rayuwarta, ta hanyar tarbiyya da Babanta SHEKH ya ginata da ita kuma yana fatan yasamu SHEKH fasihi mai tsoron Allah ya bashi kamilar É—iyar shi. Kaddara yasata barin gari zuwa wajen dangin mahaifinta Yola. Ahanyarta suka haÉ—u da yan garkuwa da mutane suka turata daji. Tom!! tom!! tom!!! Akwai wani hamshakin saurayi mai tashe da kuruciya da nera, É—an ÆŠalibin Shekh ne.kuma ya fadama shekh matsala yaronsa bashi da tarbiyya kamar É—an uwanshi som. Kaddara yasa yayi tafiya aka kwamushesy rana daga da Zarah ÆŠIYAR SHEKH. A inda aka umarcesu da su kusanci junansu inba hakaba ransu zaizama fansa gare su. Tom kardai incikaku da sututu sai mun haÉ—e... â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸ I Love You all my fan's 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 Downloaded from GNOVELS.COM.NG This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG For feedback and support Facebook : https://facebook.com/gnovels Twitter : https://twitter.com/gnovels Telegram : https://t.me/gnovels