Downloaded from GNOVELS.COM.NG This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG For feedback and support Facebook : https://facebook.com/gnovels Twitter : https://twitter.com/gnovels Telegram : https://t.me/gnovels KARUWAN CIKIN GIDA OUMYASMEEN DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA ME JIN KAI. ALLAH KA BANK IKON GAMA LITTAFIN NAN LAFIYA KAMAR YADDA NA FARA LAFIYA. GARGAƊI ________________________________ BAN YADDA WANI KO WATA SUYI AMFANI DA ƊAYA DAGA CIKIN SHASHI NA WANNAN LITTAFI BA BATARE DA IZINI NA BA 08141785374. Copy is not allowed 🚫 Bismillahir ramanir rahim Episode 1 ABUJA OSOKORO.. Wata sassanyar iska ke kaɗawa yayin da bishiyu ke rangaji iskar nan a hankali take ratsa jikin ta na kasan cewar kayan jikin ta marasa nauyi ne miƙa tayi ta , tashi tsaye bata da tsayi sai dai Ubangiji yayi mata kira me kyau me daukar hankalin duk wanda ya kalle ta ɗan ƙaramin tsaki ta ja , ta dauki wayar ta da take neman dauki ta ƙara a kunne tace '' eman yau bana jin zan iya attending lecture so idan kinga da faraga ki min kawai attendance.., saurarawa tayi domin jin me eman din za tace jan ƙaramin tsaki tayi tace '' ni wallahi na manta ma gwara ni da ku yanzu kina ina ne nake jin tashin kiɗa kar dai a club kika kwana...?, dariya eman tayi tace '' no ba'a club na kwana ba ina mai tama ni da su jee a satin nan nake so na koma gida saboda Islam tace momy ba lafiya so ina so naje naga ya jikin ta yake amma kafin nan ina so na yi solving wannan matsalar da nake ciki har yanzu ba mu cimma matsaya ba idan har ya takura zan saki video ba abin da ya dame ni abin kunya baya na bashi.., zama tayi ta ɗora kafa ɗaya kan ɗaya tace '' ke wannan ita ce matsalar ki ni ga babbar matsalar da take cikin gidana wannan shegiyar yarinyar me kama da zubin karuwai wai jibi zata ta zo karatu a kuma a nan gidan zata zauna.., wannan matsalar ita take damuwa wallahi gashi my man ya kasa fahimta ta , na fiso nayi rayuwa ni kaɗai ni da miji na , kuma kinga idan har tazo zata saka min ido ne a cikin rayuwa ta ni ina tunanin tun da ba sona suke ba C.I.D aka turo ta kuma wallahi wannan yarinyar duk bu ɗewar idanuwana ta fini. Dariya eman tayi tace '' jawaher me kike tsoro ko dai abin da kike wa wasu kike tsoran ayi miki shi..? amma in ba haka ba ban ga abin kin ta zo ta zaunar miki ba idan tayi miki ba sai kici kuttumar uban ta ba ki nuna mata ruwa ba sa'an kwando bane ba mamaki ke abin da kike yi kaɗan ne akan ta.., shiru tayi tana sauraran ta sannan jawaher tace '' haka za a yi wallahi sai ta gwammace zaman hostel akan zaman cikin gidana yanzu idan ta zo zuwan da kuke yi kuna sakewa babu fa wannan shikkenan magana ta ƙare nima yan wa'yanda nake kawowa muke raƙashewa babu wannan kaf dangin su a rasa wa za ta zauna ta yi karatu a hannunsa sai shi., ke fahimtar dani akwai aure a tsakanin su ne wannan abin da kike yi yayi yawa ko dai kishi ne Eman ta faɗa tana danne dariyar ta. wani ashar jawaher tayi tace '' bara na turo miki picture din najlah zaki zan dole na tashi hankalina kinsan namiji dan kumana ne ba'a shedar sa.., eman tace '' haka ne wallahi kawata karki manta ki turo min picture din ta.., shegiya na fasa ma turo miki saboda tsabar son tsegumi har so kike na turo miki to bazan turo ba duk sanda ta zo kya ganta.. Cewar jawaher. dariya eman tayi tana kashe wayar ta. tashi jawaher tayi ta bar guiding tana fita wanda yake kula da gurin ya kwashe kayan da ta yi amfani da su tura kofar da zata sada ta da main parlour tayi, turus tayi ganin bakon al'amari dakyar ta iya sai ta kan'ta tace '' sweet saukar yaushe...?, gaban ta yana lugudan uku uku har ga Allah bata son abin da ya tsira kwanan nan sai ya dinga dawowa batare da ya faɗa mata ba , zama tayi akan ɗaya daga cikin kujerun alfarma na parlour ta dauke kai daga kallon najlah da take danna waya . ba tare da ta kalli inda jawaher take ba tace '' ina wuni.., lafiya kawai tace ta mai da hankalin'ta kan mijin ta ɗaukan pillowcase tayi ta rungume ta kashe idanuwan'ta tana aika mai da wani irin kallo me rikitar da wanda aka yi domin shi murya ƙasa ƙasa tace '' sweet kace min sai jibi zata tawo chanza rana tayi kenan..?, hannunta Jawad ya kama tare da aika mata wani irin sako yana yin messages din hannun ta . tari najlah tayi domin ta ankarar da su basu kaɗai bane da sauri ya dawo cikin hayyacin sa. idanuwan'sa har sun canza launi yace '' jawaher kai ta dakin da zata zauna.., tashi tayi tana sakar wani shu'umin murmushi tace '' am kanwata ki zaki iya tashi sorry fa na rage miki jin daɗin ki.., tashi najlah ta gyara zaman hijabin da yake jikin ta ta dauki trolley bag din ta ta fara ja tsaya, tsayawa tayi batare da ta juyo ba , ita daman ta dade da sanin cewa zuwan ta gidan ya Jawad akwai babbar matsala tana da gudun hulakanci dan haka wallahi wata ran dole su kwashi yan kallo inhar jawaher ta ci gaba da yi mata haka , wannan wanne irin rashin hakuri ne da rashin kunya a gaban ta suna yun kurin aikata abin da ba dai-dai ba , tana cikin wannan tunani ne taji yace '' jeki zan saka a daukar miki ita , ki dena ɗaukar kaya masu nauyi.., to kawai tace ta bar jakar ta anan bude mata dakin tayi shiga tayi ta kwanta a tamkekem gadon da yake cikin bedroom din, bin ko ina take da kallo tashi tayi ta cire hijabin ta , wayar ta , ta dauka ta lalubo number hajiya bugu ɗaya ta dauka fashe mata da kukan shagwaɓa tayi tace '' Hajiya wallahi bazan iya zama a cikin gidan nan ba auntu jawaher bata da kirki ni nafi son na zauna a gurin ya Aliyu nafi so nayi B.U.K dan Allah ku mai dani can tun da nan ko admission basu fara bayar wa ba.., Hajiya tace ''Najlah yanzu ke da ace aure kai miki ya kenan tun da kika ji zancen tafiyar nan kika daga hankalin ki, kinsan dai halin family din abban ku duk abin da suka tsara ba wanda ya isa ya ja dashi dan haka kiyi hakuri har ki gama zama ki dinga zuwa hutu bawai dindindin zaki zauna ba.., ajiyar zuciya ta sauke tace '' inna su adal suke..?, abban ku ya tafi da su gidan anni Cewar hajiya Najlah tace '' idan sun dawo kice ina gaishe da su, Hajiya tace '' to za suji insha'Allahu . sallama su kayi ta kashe wayar ju yowar da za tayi suka hada ido da Jawad da sauri ta da baya daukan hijabinta tayi ta saka kasa cewa komai tayi kirjinta na tsanan'ta bugu har ga Allah bata son wannan kallon kulla da yaya Jawad yake mata shi ko kunya baya ji ta sha kama shi yana kallon ta sai dai ya waske. trolley din'ta ya shigo mata da ita sannan yace '' duk wani abu da kike bukata ki yi min text messages zuwa gobe insha'Allahu ina ga zan tafi Dubai.., a hankali tace '' Nagode sosai Allah ya ƙara arziki bana bukatar komai, komai abba ya siya mun.., ƙafarsa ya ɗora akan gado ya jingina da bango yace '' bakya jin zafi ne..?, da sauri ta juyo jin maganar sa waskewa yayi ganin rashin dacewar maganar da yayi yace '' baki kunna AC ba kin zauna haka.., ajiyar zuciya ta sauke da har sai da ya jiyo lokacin da ta sauke ta fita yayi ya dafa kan'sa me yake shirin aikatawa ne . cin karo sukai da jawaher tace '' abincin ka ya haɗu wanka zaka fara ko cin abincin..?, kai wa Najlah nata ni sai nayi wanka zanci ban sani ba ko tana jin yunwa.. da sauri ta kalle tace '' She's just girl, ot is this house not hers? If she's hungry, she should just speak up. I'll go and prepare your bath water.., kallon ta yayi da sauri ta hadiye sauran zancen nata kitchen ta shiga ranta duk a ɓace wayar ta ce tayi ringing da sauri ta ɗauka tace '' zan kira ki ya dawo bana cikin nutsuwa ta.., tana kai wa wannan ta kashe wayar ta , tana sakar gauran numfashi cikin takaici ta hada komai a cikin tray zura wayar ta , tayi a aljihu ta ɗauka kai tsaye dakin Najlah ta nufa ko da tace batai knocking ba ta shiga tarar da ita tayi bata cikin dakin sai dai motsinta da ta ji a toilet tsaki taja ta ajiye a kasa zata juya Najlah ta fito daga ita sai towel gaban jawaher ne ya faɗi ta raina kan'ta wani abu ne ya tokare mata maƙogaro tabbas sai yarinyar nan ta bar gidan nan idan fa zata iya tunawa da aure a tsakanin su to idan shi ya zo ya ganta a cikin wannan hali ya ke nan dakyar ta iya saita kan'ta tace '' am gashi nan..., thanks kawai ta ce ta zauna akan stool tana tsane gashin ta hand dry ta dauko ta fara busar da gashin ta na muzayen asali bugo mata kofa tayi murmushi Najlah tace '' mahaukaciya duk wannan abin da kike yi akan yaya ne insha'Allahu sai yayi mata har uku bayan ke.. gama shiryawa tayi ta buɗe trolley din'ta ta dauko duguwar riga ta wani material an mata ɗinkin T line daga sama rigar ta bude daga ƙasa ta tsuke kulle kofar ta tayi ganin ita kaɗai ce ba kowa kawai sai ta cire towel din jikin'ta bra ta saka da pant sannan ta saka rigar dan dai saman da faɗin sa amma duk da haka ya fito mata da kirar jikin ta tubke gashin kan'ta tayi ta saka chantili cap feshe jikin'ta tayi da turare ta zauna buɗe abincin tayi ta dan taɓe baki ita irin wa'yannan abincin na turawa be dame ta ba ɗan danawa tayi ina baza ta iya ci ba daman tun a ido taga ba zata iya ci ba gashi hanjin cikin ta har wani curewa suke guri ɗaya. tashi tayi ta buɗe fridge ban da lemo da ruwa ba wani abu da zai iya tare mata yunwa tashi tsaye tayi ta kama kugunta to yanzu ina ta dosa kenan gaskiya ba zata kashe kan'ta ba dan haka , ta dauki mayafin'ta ta yafa ta fito ɗauke kai tayi lokacin da ta gan su hannun su a tsarke da na juna suna saukowa daga kan stair case tamkar wasu tattabari taɓe baki tayi tace '' aikin banza wannan aunty jawaher din yar uwar karuwa ce sai wani nanike mai take shi kuma tattabari sarkin aure yana biye mata ..., tafaɗi haka a cikin zuciyar ta Cikin barikan ci tace '' sister akwai abin da kike bukata ne....?, ajiyar zuciya ta sauke tace '' uhmm daman bazan iya cin wannan abincin ba ne zan girka da kai na., dafe goshin ta jawaher tayi tace '' oh na fa manta baki saba ba cin irin wannan abincin ba sai local dishes.., murmushi tayi tace '' ai yana da kyau mutum karya watsar da al'adar sa, good girl haka ake so ga kitchen din can kije ki dafa abin da kike so. cewar jawaher. bata ce komai ba ta juya tabar gurin dining table suka nufa Jawad ya ja mata kujera ta zauna shima yaja ya zauna serving ɗin'sa ta fara yi tace '' am sweet ba ka ce komai ba maganar tafiya Turkiyya da zanyi bikin zeey yana fa matsowa ya kamata muyi abin da za muyi wallahi su mami ma ni suke jira one month kaɗai fa zan yi amma duk kabi ka ɗaga hankalin ka za mu dinga video call nasan abin da kake nufi komai za mu iya ta video call... kasa kai chokali bakin sa yayi yace '' video call me zai saka ban da ya ƙara tun zurawa ?, wani numfashi ta furzar me wuci tace '' sweet idan ka hana ni tafiyar nan bakai min adalci ba mutane nawa ne suka amfani da video call kuma suna in joy mode din Please i begging you Ka barni yanzu siyayyar zeey na kasa zuwa ka tuna lokacin auren mu mene ba tai min ba , dan yanzu zata sake aure sai kuma ni na kasa yi mata abin da tai min bana bukatar kudi kawai so nake na taya ta zaɓen kayan dakin ta da wasu abubuwan tun da daga can har Katar za mu.., limshe idanuwan'sa yayi ya dauki tissue ya goge bakin sa yace '' zan duba na gani.., riƙe hannunsa tayi tace '' kai ma fa tafiya za kayi ka temaka ka barni.., hannunta ya riƙe yace '' school fa ya zakiyi da karatun ki wa zai zauna a gidan..?, gumi ne ya karyo mata ta san shi sarai da dabi'ar son tayi karatu tace '' am yanzu muna first semester ne so karatun be kankama ba kafin na dawo komai ya kankama gida kuma ga Najlah nan me zai faru da ita da ace tayi aure da yanzu tana gidan mijin ta .., kura mata ido yayi ya hura mata iska da sauri ta limshe idanuwanta. murmushi yayi yace '' zan shiga study room zanyi aiki ki huta lafiya.., binsa tayi da kallo ranta duk ba dad'i kullum addu'a ta Allah ya saka ya barta ta tafi wannan tafiyar tashi tayi ta shiga dakin ta ta murza key dauko waya tayi a cikin aljihunta ta lalubo wata number ta yi dialling ringing ɗaya kai picking call din cikin sauri tace '' ka bani lokaci mana har yanzu yaƙi amincewa kasan ba zan iya tafiya wank guri ba , batare da izinin sa ba amma ka kasa fahimta, ta Jawad yana da kafiya da tsayawa akan ra'ayi ɗaya na lura duk irin kokarin da nake yi baka gani kullum da kai nake kwana nake tashi idan ka faɗi haka bakai min adalci ba , mutumin nan yanzu abubuwan da take yimin kamar ya fara zargina dole mu bi komai a sannu kar kwabar mu tayi ruwa.., shiru tayi tana saurarawa domin jin me zai ce kit taji ya kashe wayar ciro wayar tayi tana jan ƙaramin tsaki buɗe dakin tayi ta fito bata gansa a parlour ba zama tayi akan kujera tana girgiza kafa ranta duk a ɓace idan jawad ya hanata tafiyar nan tabbas ya gama da ita ga wannan kaddarar da tazo mata kan'ta gaba ki ɗaya , ya kulle tama rasa ma za tace da sauri wata shawara ta fado mata zuciya duk yadda akai ummin jawad bata san da zuwan Najlah ba. da sauri ta dauki wayar ta , ta samo laluban number ummi bugu ɗaya ummin jawad ta ɗauka jawaher tace '' Assalamu alaiki ummi barka da yamma ya su taufiq.., cikin isa da nuna ƙatsai ta ummi tace '' wassalamu alaiki barka dai suna lafiya da fatan kuna lafiya.., gyara zama tayi tace '' eh wallahi ummi lafiya qalau alhamdulilah.., Ummi tace '' masha Allah haka ake so ya kaɗaici kuma.., wani murmushin jin dad'i tayi domin an tabo mata inda yake mata kaikayi tace '' yama dawo ɗazu abin da ya sakani dad'i ma tare suka dawo da Najlah za tayi karatu anan.., da sauri ta tashi hadiman da suke mata tausa a kafa sai da suka tsorata saboda tashin da tayi na baza ta da kuma hanzarin ta tamkar ta ga wani abin ƙi cikin tantance zancen jawaher tace '' wacce NAJLAH..? yaushe JAWAD ya dawo ƙasar nan ban sani ba kuma be sanar dani ba..?, murmushin jin dad'i tayi tace '' Najlah Hajiya Farida ɗazu ya dawo be dade da dawowa ba ina ga sai ya nutsu zai kira ki ya sanar da ke..., cikin tsananin ɓacin rai tace '' yanzu haka tana cikin gidan ki lallai yaro be san wuta ba sai ya taka , da zaki ce kina ga sai ya nutsu wannan wanne irin kinibibi ne tafiya yayi fa YOLA daga dawowar sa ina JALINGO be sanar dani ba balle ya zo Nagode da sanar da ni da ki kayi sai an jima..., kit ta kashe wayar ta wani tsalle dad'i jawaher tayi tare da rawa wannan game din tasan ita ce za tayo winner wata kila zuwa gobe ta yardar da kwallon mangaro ta huta da guɗa ummin JAWAD lafiya ce. Wannan boom ɗin tasan gaba ki ɗaya ahalin alkali mudassir ɗan muzu da su zai tashi sai ummi ta ya mutsa hazo zama tayi tana cewa duk mutumin da zai hanani kwanciyar hankali a gidan miji na to tabbas ina da boom me tashin rayuwar mutum gayawa jini na wuce. wata dariya ce ta zo mata , ta mugunta lokacin da taga NAJLAH da plate ta fito daga kitchen uhmm babu a house ta faɗi da dan karfi domin NAJLAH ta ji ta. sarai ta ji furucin ta sai dai bama ta nuna tasan me take faɗi ba. wuce ta tayi ta koma dakin ta. WANNAN KENAN JALINGO TARABA STATE. Sai zaga ye tamkeken parlour take wanda ya cika da kayan alatu na jin daɗin rayuwa tun da sukai wannan maganar da jawaher take buga number JAWAD amma a bata shiga. Altab ne ya shigi daga shi sai riga armless sai wando three-quarter ga wata uwar sarka a wuyan sa kai kace jikan bambaline shi cikin sauri yace '' ummi lafiya naga kina ɗawafi..., Altab ba dole kaga ina ɗawafi ba Wallahi lamarin dagin mahaifin Jawad ya ishe ni dole muyi fito na fito da su haba wannan wacce irin jaraba ce su barmin ɗana ba ruwan su dashi. zama yayi yace '' ummi kenan Allah ya kyauta amma dai lokacin da kika tafi kikai fushin zuciya wa ya rike miki shi ni wallahi duk irin wa'yannan abubuwan dama zaki gane ki dena saka kanki a ciki.., ji tayi tamkar ya zuba mata wuta a fusa tace '' lallai altab sai yau na kara tabbatarwa shaye shayen da kake yi ya ta ɓa maka kwakwalwar ka fice ka bani guri wanda baya kishin kan'sa.., tashi yayi yana sosa sumar kansa da ta sha gyara yace '' kudin hannu na sun ƙare me zan samu ne..., Ubanka za ka samu altab, wallahi nagaji nagaji ka nemi sana'a ka fara yi kudina bana shalholiya bane bana tara matan banza bane idan ka yi zuciya ka tafi ka nema a, duk wani abu da kake yi a guest house ina sane dakai wallahi ka guji ranar da zan faɗawa jawad. altab yace '' to shikkenan kar Allah ya saka ki bayar wallahi ba zaki ƙi gani ba tun da haka kika ce zan ɗin gima miki babban aiki na bar ƙasar badai kin fara tsanata ba dan ina faɗa miki gaskiya da kuma munafukai da suke wure miki kunne any way dake da su za ku gani yasin daga nan zuwa karshen shekarar nan kowa zai ga abin da zai faru da shi.., EPISODE 2 Dan Allah altab karka fasa abin da kayi niya me ka mai dani banki ko me kullum kace na baka kuɗi to wallahi zan kirawo JAWAD ya zo ya raba ni dakai da me zan ji.. be ce mata ƙala ba ya wuce yana cewa za dai ki gani har su munafukan naki.. Dafa kan'ta tayi tace '' altab ni kake faɗawa haka.., fita yayi yana sakar fito zama tayi tamkar wacce ruwan sama ya jiƙa ta bata san yadda za tayi da altab ba yana neman ya gagare ta , da sauri ta tashi cikin sauri ta sau stair case shiga bedroom din ta , tayi da sauri ta bude wata loka wani key ta dauko ta ma yar ta rufe fitowa a hankali take saukowa saboda jin alamun kamar akwai baki a ƙasa aikuwa ilai Hajiya rukayya ce haɗe rai tayi ta zauna tare da ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya akan kilishi tace '' Hajiya rukayya nasan tun jiya sakona ya isa kunne ki amma me yasaka sai ya zu kika zo..?, Wani murmushi Hajiya rukayya tayi tace "It's only now that I got the time" Ummi hannunta ta ɗun kule waje ɗaya tace '' okay yayi kyau zaki iya tafiya na riga da na gama so yanzu bani da bukatar ki, daman kwaɗayi ya kawo ku kowa ya san kuɗa gurin kwaɗayi yake mutuwa.., What ni kike faɗawa haka...? ya cutar min da yarinyar ki dinga faɗa min haka lallai ma Hajiya bilki good yayi kyau tun da haka kika ce kuje ku ɗa Allah dakin ya kusan kashe min ya' ki dinga faɗa min haka.. da sauri ummi ta ɗago tace '' to kima godewa Allah da be nakasa ta ba in banda iskanci duk wani abu ai tayi shi a waje ta shigo da yan iska cikin gidan sa ta tunda tunanin ba zai iya yi mata komai ba saboda gata yar gwal suna mai shaye shaye wannan wacce irin rayuwa ce.., dariya Hajiya rukayya tayi tace '' da yar tawa da ɗan naki ai dan jumane da yar jummai sittin ce take dukan saba'in.., wani kallo tayi mata tace '' dan haka dole ya je ya samo yar mutunci ya aura..., wata uwar buɗa Hajiya rukayya ta saki tace '' wallahi karya kike baki isa ki canza ayar Allah ba Ubangiji ne yace Az-zāninī laa yankihu illā zāniyatan aw mushrikatan, waz-zāniyatu laa yankihuhā illā zānin aw mushrik; wa hurrima dhālika 'alal-mu’minīn wallahi, you're lying The relationship between Altab and Samha hasn't even started. No one has the right to enter this house,, Haka kika ce ga hanya nan zo maza ki barmin gida na tun kafin na ci miki mutunci... Cewar ummi tashi Hajiya rukayya tayi tace '' au cin mutuncin na nawa kuma ɗan haka ina me sheda miki tun da sheɗanin dan ki ya lalata min ya' to wallahi zama yanzu suka fara shi, duk ba shi ya cutar min da yar tawa ba mene be koya mata ba , itama rashin jin ta ga samari nan nawa suka fito suka ce za su aure ta daman dole zaman su ya zamo da zargi saboda an riga tun a waje an lalata zamantakewa ba ta yadda za ayi a cikin gida ta ginu wallahi ko yawo kike yi a kan dutsai tsirara altab be isa ya saki samha ba shi da ita mutu karaba talmin kaza da kike cewa son abin duniya mu kayi ke da ba kya so ki zubar dashi a ƙasa ban da rainin da kukai mana kuna ganin mu talakawa ne , amma har kya budi baki, ki faɗa min haka kamar yadda kike son ɗakin haka nake son ya'ta in ban da rainin hankali har mu zaki kalla kice son abin duniya ya rufe mana ido Hajiya bilki kin manta amintar da take tsakanin mu kin rufa idon ki, kin ci min mutunci bayan kice kika zo kina lallaɓani akan auren nan shima haka to wallahi ba ku isa ku mai damin yata ba bazzawara.., cije lips din tayi ji take tamkar ta shaƙe ta har Hajiya rukayya ta fita bata ce komai ba ji tayi kamar tayi cille da wayar ta da sauri ta dauki key da mukullin da ɗazu ta fito da shi ta fita daga cikin part din ta cikin sauri take komai har ta isa part din altab shiga gate ɗin farko tayi sannan ta bi ta wata kofa nan ne ta shiga ainin farfajiyar gidan ga motar altab a ajiye a parking space kai ta gyaɗa da alama yana cikin gidan, tura kofar parlour sa tayi jin kiɗa na tashi tamkar a shahararren club din america.. jirine ya kusan kwasar ta dafe kan'ta tayi da yake juya mata a gurin ta sulale a ƙasa numfashin ta na kaiwa yana kawowa da sauri ya ƙaraso gurin ta. ɗago mai hannu tayi tace '' basai ka taɓani ba zan iya tashi..., dafa bango tayi dakyar tana tafiya limshe danuwanta, tayi da suka cika da kwalla bata so ta zubarwa da altab hawaye domin hawayen ta masifa ne a rayuwar'sa biyota yayi tace '' wallahi tun kafin ranka ya ɓaci ka kawshe matan da kakawo cikin gidan nan ban da iskanci da wulakanci gidan auren ka zaka kawo mata kuna shaye shaye.., to shikkenan ummi zan kwashe su amma bazan je na tawo da matata.. da sauri ta juyo jin zancen da ya furta anya kuwa kan'sa ƙalau lallai, ɗazu ma da ta mara mai baya dan dai Hajiya rukayya ta nuna mata rashin mutunci ne amma ko dukan da yayi wa samha bata ji dad'i ba duk da itama da laifin ta idan mace za tayi aure komai barin sa take yi a waje ta shigo gidan mijin ta da kyakkyawar niya amma ita bata san wannan ba ta dinga tara matan banza kuma bata kunyar wani ya gani suna shaye shaye ajiyar zuciya ta sauke tace '' ga hanya nan tafi wallahi yan uwanta sun shirya tsaf kana zuwa zasu kama ka haka kurum ka kama yar mutane ka naɗa mata duka ita , duk abin da ake aikatawa me take maka..? wallahi ko da wasa kar na kara ji ka saka hannu ka daki yar mutane mace da kake gani daraja ne da ita.., shiru yayi har ta gama zancen ta , ta fita da sauri hany ta biyo bayan sa tace '' Man what is happening..?, shafa gefen fuskar'ta yayi yace '' no bakomai ke da su mufee ku tafi zan neme ku ko wacce ta turo account number din'ta.., da sauri ta riƙe mai hannu tamkar za ta shiga jikin sa tana mai wani irin kallo tace '' amma didn't you say we would spend the night here today? How many of us are even here?,, matsar da ita yayi daga jikin sa yace '' Please hany kuyi abin da nace kafin raina ya ɓaci idan kuka kika ce ba in da ki tafi wallahi sai na farfasa miki jiki da duka ba ku ga abin da take shirin faruwa ba oh da ba mahaifiyar ki bace shine ba abin da ya dame ki to duk iskancina ina son mahaifiyata bana so na rasa ta.., bata ce komai ba ta juya ta bar gurin samin su mufee tayi suna zaune sun yi ɗare ɗare akan gadon sa suna busa shisha tace '' maman My man ta bashi umarni ya fitar damu daga cikin gidan nan ku taso mu tafi yace ko wacce ta turo mai account number din'ta..., ransu be so ba suka tashi suka bar gidan bama suyi mai sallama ba.. *OSOKORO........* *STUDY ROOM....* tunda ya shiga yake aikin office da ya tarar mai kwana biyu da yake yayi busy ba ya ƙasar sai yanzu ya samu yake rage wa kan'sa ne ya dauki chaji gaba ki ɗaya wayoyinsa ya kashe su, yana bukatar hutu da kaɗaici domin yayi aikin sa ba kuskure.. ji yayi an yi knocking kofar sa yasan wace dafa goshin sa yayi yace '' abu ɗe yake.., jin haka da sauri ta murɗa handle din ta shigo zama tayi akan ɗaya daga cikin kujerun da suke study room din tace '' ummi ce ta bugo duk layin ka a kashe yake ce maka.., ajiyar zuciya ya sauke shi ya amshi wayar tare da karawa a kunne yace '' Assalamu alaiki ummi barka da yamma..., JAWAD riƙe gaisuwar ka bana so bana so wallahi ai baka mai dani mutum ba wayancan Mutanen da na raba ka dasu sune mutane har ka iya zuwa yola baka zo gurina ba ina matsayin mahaifiyar ka , ka kyauta dole suyi min abin da suka ga dama su nuna min ban isa da kai ba sai su, suka isa dakai ban ce maka ba , na rabaka da duk ahalin ɗan buzu musamman ma Hajiya farida bani da wata wacce na tsana sama da ita dan haka kai gaggawar mai da mata da yar ta , wallahi wallahi wallahi JAWAD idan ka sake kayi abin da na ke zargi to bani ba kai ban da iskanci tun wuri ka rabu da ita mana to wallahi alkali mudassir ya taro abin da yafi karfin sa domin duk abin da yake faruwa ina sane wato za su fage da guzuma su harbi karsana ko to sunci karya bakai ba jinin Hajiya farida da Alhaji Sharif.., kifa kansa yayi akan table rasa ina zai saka kan'sa yayi anya kuwa Mahaifiyarsa, tana tsoron Ubangijin'ta me wannan baiwar Allah tayi mata tun da ya taso be san dadin uwa ba , watan sa takwas ita da mahaifinsa suka rubu dan haka bata tafi dashi ba ta bar shi ba ruwanta ya mutu ko yayi rai sai bayan ya kammala digree dinsa na farko yana shirin tafiya egypt ƙaro karatu ta bayyana be rayu da ita ba , tun daga bayannara ta zuwa yanzu kullum cikin saka shi take a damuwa da farko da ta bayyana yaji dadi be taɓa zaton ba hajiya ce mahaifiyar sa ba suma haka su NAJLAH sai a lokacin suka san me yake faruwa ajiyar zuciya ya sauke yace '' ummi insha'Allahu zan kiyaye duk abin da kika shinfiɗa min wallahi bawai haka kurum naje yola ba a'a na can na sauka gobe nake so na zo mu gaisa.., kashe wayar tayi saboda ai ta riga da ta isar da sakon'ta miƙa wa jawaher yayi, amsa tayi tace '' amma sweet lafiya ko ba wani abu ne ya faru ba..?, bece mata komai ba ya nuna mata hanyar fita sum sum ta fice tana danne dariyar ta , ci gaba yayi da aikin sa bayan ya gama ya tashi ya fito ba kowa a parlour kai tsaye bedroom din sa ya nufa tana kwance tana waya tana ganin sa ta katsai wayar tace '' badai la gama ba ? Amma kuwa idan haka ne kayi saurin gamawa..., zama yayi bakin gado yace '' eh na gama kije kice NAJLAH ta haɗa min coffee.., tashi tayi tana cewa to an gama oga kiss tayi mai a kumatu tace Allah ya bar min kai ya makantar da idon yan mata akan ka..., dan murmushi yayi mata yace '' amin..., da sauri ta dawo ta zauna riƙe hannun sa tayi tace '' idan har hasashena ya faɗa min gaskiya kamar akwai abin da yake damun ka amma kaki sanar min idan ma tafiyar ce baka so nayi sai na fasa shikkenan magana ta ƙare amma wannan haɗa ran ban saba da shi ba kullum na fiso mu ɗore cikin so da kaunar juna da fahimtar juna shekara biyu da auren mu bamu taɓa samin matsala ba kar yanzu akan tafiyar nan mu samu beb idan haka ne ni wallahi na hakura ma da nayi tunani ko wani abu ummi ta faɗa maka da na kuma ƙara wani tunanin sa naga ita uwa ce me son farin cikin ɗan ta ba za ta taɓa faɗa maka abin da zai saka lokaci kali lan ba ka shiga cikin damuwa , ina kyautata zaton nice sanadin komai, saukowa tayi ƙasa ta damƙe hannuwansa idanuwan'ta ya taru da kwalla fal sakin hannuwansa tayi ta haɗe hannuwanta biyu alamar ban hakuri ta ci gaba da cewa. Dan Allah ka yafe min mijina bana so ka kwana kana fushi da ni bana so na zama sillar bakin cikin ka , ka dawo daga tafiya kamata yayi na faran ta maka be kama ta na bakan ta maka ba... Kwantar da kan'ta tayi yasha kan'ta yayi yayin da wani sanyi yake ratsa zuciyar'sa hakika annabi yayi gaskiya da yace idan namiji ya dace da mace ta gari to kamar ya samu rabin addini ne yana kaunar jawaher yana son ta fiye da son da yake wa kan'sa baya iya kallon ko wacce mace a matsayin mace , Hakika jawaher rabin jikin'sa ce.. cikin daddaɗan sauti yace '' wallahi baki yi min komai ba idan ma kwai na yafe miki sweet stress ne yayi min yawa ina bukatar hutu amma ni baki min komai ba jeki, ki faɗa mata , ta haɗa min kafin na fito daga wanka.. Hmmm ku biyoni dan jin wanne darasi wannan labarin ya kunsa # KURUWAN CIKIN GIDA EPISODE 3 Ɗago idanuwan'ta tayi cike tab da hawaye share mata yayi yace '' bana so na ganki cikin damuwa.., Murmushi tayi ta tashi, ta karasa share hawayen ta , fita kai tsaye bedroom din NAJLAH ta shiga turawa tayi ba tare da tayi sallama ba , tana kwance wayar ta na hannun ta taɓe baki tayi ta kalle tace '' sweet yace ki haɗa mai coffee.., ajiye wayar hannun ta , tayi bata ce mata komai ba ta miƙe ganin haka ita mata fita, tana shiga tarar dashi tayi ya shiga wanka zama tayi tana charting da wayar ta fitowa yayi yana tsane jikin sa batare da ya kalli inda take ba yace '' kin faɗa mata..?, ajiye wayar ta , tayi tace '' na faɗa mata amma bata ce min komai ba bama ta kalli inda nake ba balle nasan taji me na faɗa.., ajiye towel din hannun sa yayi ya fita a hankali yake saukowa cikin nutsuwa kamar ba sauri yake ba yana sauka kai tsaye bedroom din NAJLAH ya nufa murɗa handle din kofar yayi da sauri ta dago tare da ja da baya tun da take dashi a rayuwar'ta bata , taɓa ganin sa acikin makamancin wannan yanayi ba ko exercise zai yi da dogon wando yake tafiya balle wannan daga shi sai towel a ɗaure a kugu lallai auren da yaya yayi ya mai dashi wani iri, ƙasa tayi da kan'ta tace '' yanzu zan kawo maka.., okay ita da kikai mata shiru kenan raina ta kika yi..?, ya jefo mata wannan tambayar bata , taɓa tunanin jin wata magana makamancin haka abakin sa ba. turi ƙaramin bakin ta , tayi tace '' nace mata to.., karya kenan take miki..? da sauri ta ɗago kwallah har ta fara taruwa a idanuwanta ja da baya tayi tana sauke ajiyar zuciya ganin ya matso kusa da ita tamkar zai shige jikin ta da sauri ta, tashi tace '' bara naje na duba kar ya gaji da tafasa.., ratsawa tayi zata wuce riƙe hannunta yayi da sauri ta juyo anya kuwa yaya Jawad lafiyar sa qalau ko kallon ta ya ke kamar jawaher ta shiga uku da sauri ta saka ɗaya hannun nata , zata cire hannunta da ya riƙe wani irin shock yaji ajikin sa da sauri ya cika mata hannu kasa koda motsi yayi dakyar ya iya ɗaga kafar sa ina yaga abin ba zai yiwu ba hannun sa ya saka ya kashe switch din fitilar dakin a gigice ta ɗago da kan'ta sai dai kafin ta gama tantance wanne yanayi take ciki ya hanka ɗata kan gadon ta yunkurawa tayi zata fita aguje amma ina be bata damar haka ba , domin ya danne ta kuka ta sakar mai , sosai ta shiga kici niyar kwace kanta amma ina ya ƙi bata damar haka. ji tayi an buga mata pillowcase agigice ta , tashi tana zabga uban gumi ganin shine gaban tane ya faɗi tunowa da tayi da abin da ta gani a cikin mafarkin ta , da sauri ta ja baya gaban ta na faɗuwa cikin haɗe girar sama da ta ƙasa yace '' NAJLAH sannun ki na saka ki aiki shine , kika zo kika kwanta har kikai bacci daman ai tace baki bata amsa ba .., cikin sanyin murya tace '' nace mata to wallahi ban san lokacin da bacci ya dauke ni ba na ɗora akan gas Allah ya saka me kone ba bara na tafi na duba kafin yace wani abu ta fita cikin sauri, ko ina na jikin ta rawa yake daman ya lafiyar kura balle tai hauka, tana tafiya a hankali jikin ta na motsawa balle yanzu da ta fita da sauri zama yayi ya ɗora ƙafafuwan'sa ɗaya kan ɗaya ciro wayar sa yayi daga aljihun kayan baccin da ya saka farare tas dasu fara operating din ta yayi har ta kawo ta ajiye mai be ɗago ba. cikin daddaɗar murya me dadin sauraro tace '' yaya gashi nan na kawo maka a ina zan ajiye maka..?, akaina zaki ajiye.. da sauri ta ɗago ganin ita yake kallo sai tai sauri ta ajiye tare da matsawa daga gurin zama tayi agefe tana wasa da gefen mayafin'ta so take yi ya dauki kayan sa ya fita. wayar tace tayi ringing da sauri ya kalli gefen sa BLOOD LINE sunan da yaga tayi saving number din dashi ajiye coffee ɗin hannunsa yayi ya dauki wayar tata ya soma juyawa nan ɗanan ɓacin rai ya bayyana afuskar sa kallon ta yayi yace '' wanne wannan...?, bakin ta na rawa tace '' yaya muneef ne.., ɗaga kan'sa yayi ya kalli agogo ƙarfe goma saura minti uku kallon ta yayi yace '' lokacin nan ya kira ki daman kun saba waya kenan..? kenan ba karatu yake ba tun har yakai lokacin nan be kwanta ba be kuma ya zauna yana karatu ba ya kira ki..?, NAJLAH bata da wuyar kuka dan haka a yanzu hawaye ne suka soma sintiri a kan fuskar'ta bata son wani issues ya haɗa ta da yaya Jawad saboda ya dinga tambaya ya saka mutum a kwana ko dan aikin sane amatsayin sa na alkali ya dinga bin diddigi sai yaga ya aka haihu a ragaya shi ya saka kaf Yaran Ɗan buzu suke tsoran sa har da wasu manyan ma bakin ta na rawa tace '' a'a yau ne kawai ya kira ni da wannan lokaci..., au daman kun saba waya son ki yake da sauri ya ɗago tace '' ya muneef ne fa..?, miƙo mata wayar yayi yace '' buɗe min.., karba tayi ta buɗe ƙara cewa yayi yace '' cire password gaba ki ɗaya.., jikin'ta na rawa ta amsa ta cire mai daukan coffee din yayi ya fita, tamkar an tsoma kaza cikin ruwan zafi haka jikin'ta yayi banda uban gumi da yake yanko mata. ba abin da take tunani sama da video's da tayi wani zubin da towel, wani balle ita tana son saka English wears duk da idan ta saka, sai ta saka hijabi amma wajibi ne tayi video ko photo wani zubin har da rawa, daman wannan ranar aunty hafsa take ji mata , tace duk randa Jawad ya karbi wayar ki , sai ya hanaki riƙe waya cewa zai yi tiktok kike yi be san cewa iya kan wayar yake ba. Shikkenan tayi mata baki yau gashi ya kamata a inda ba annu balle ta tare mata tasan gunduwa gunduwa zai yi da ita ya Jawad ba dai zafi ba. Bayan fitar sa kai tsaye baranda ya nufa tura glass door yayi ya shiga wani guri da flower's abin sha'awa ga wasu fararen kujeru da table a tsakiyar su bangaren hannunsa na dana wani lilone zama yayi akan lilon tare da ajiye tray din hannun sa akan center table daukan magazine yayi ya soma dubuwa ya dan daɗe, yana dubuwa sannan ya ajiye ɗaukan wayar Najlah kai tsaye gallery ya shiga da sauri ya cire glasses ɗin sa gani yake ba dai-dai ya gani ba a hankali ya furta NAJLAH da sauri ya shiga hannun sa har rawa yake buɗe video yayi daga ita sai wata riga me karamin hannu ta lafe ajikin ta , da wando three-quarter skiing tight tana rawa ta , tana bin wata waka.. fita yayi ya dauki wayar sa ya danna wata number ya kara akunne ba a dade ba aka dauki wayar sallama yayi. Tace '' wa'alaikis'salam JAWAD ya mutuniyata kardai kuka tai maka sai ta dawo kasan Najlah ba dai rashin yadda ba.., cije lips din'sa yayi na ƙasa yace '' aunty hafsa kinsan NAJLAH tana tiktok naga kun fi good time da ita.., dariya tayi tace '' a'a bawai tiktok take ba kawai tana yin sa ne prevent kasan Najlah akwai son English wears amma bata tiktok.., hmmmm kareta kike yi nagani a wayar ta. murmushi tayi tace '' a'a wallahi ko dai abin ne ya motsa nidai ina ta zuba ido naga big result.., kashe wayar sa yayi bece mata komai ba ci gaba yayi da binciken wayar ta be ga wani abu ba , banda dai wannan video ajiye ta yayi ya ci gaba da shan coffee ɗin'sa sai karfe sha ɗaya ya tashi dauke kayan yayi ya kai kitchen. bayan ya ajiye ya fito kai tsaye dakin ta ya nufa murɗa handle yayi ya shiga tana zaune a yadda ya barta tana jin shigowar sa da sauri ta , tashi jikin ta na gumi taja baya miƙa mata yayi ƙin amsa tayi domin bata san ko yayi haka ne domin ya kafa mata tarko ɗaka mata tsawa yayi yace '' ba Magana nake miki ba.., da sauri tace '' dan Allah kayi hakuri.., haɗe rai yayi be ce mata komai ba ya ƙara miƙo mata jikin ta na rawa tace '' to ka ajiye akan bedside drawer zan dauka.., limshashshun idanuwan'sa ya buɗe masi kama da me jin bacci ya kalle ta mai da wayar aljihunsa yayi yace '' good lallai ma yarinyar nan kin raina ni ko..?, da sauri ta girgiza kan'ta tace '' a'a kai hakuri.., okay zo ki karɓa kafin na kifa miki mari... jikin ta na rawa ta karɓa sai dai hannun ta ya riƙe be bata wayar ba , kuka ta rushe dashi tace '' wayyo Allah hannuna ya Jawad zai karye.., murmushin mugunta yayi ya cika ta tare da miƙa mata wayar ta kin amsa tayi ta kifa kan'ta a gado tana kuka ita , ta dade da sanin cewa ya Jawad zuwa gidan sa da tayi hmmm akwai matsala Allah ne kaɗai yasan irin kalubalen da zata fuskanta, ta nunawa su Hajiya amma sun kasa fahimta. ajiye wayar yayi akan gado ya fita ta dade a haka sannan ta kashe fitilar dakin, ta ta kwanta.., yana fita kai tsaye bedroom ɗin ya nufa jawaher tana kwance tana charting tana ganin sa ta ajiye wayar tace '' sweet ka dade ko bata ɗora bane..?, zama yayi yace '' na zauna a abaranda ne nasha iska.., hannunsa ta riko ta kai bakin ta za tai mai kiss da sauri ta ɗago jin kamshin turaren NAJLAH a jikin sa bakin ta na rawa tace '' sweet kamshin me nake ji..?, da sauri ya kalle ta yace '' ban fahimta.., kwallace ta , taru a idanuwanta tace '' ya kake abu kamar baka gane me nake nufi ba , JAWAD kamshin turaren NAJLAH naji a hannun'ka me ya kai hannun ka har ta shafi turaren NAJLAH wallahi nayi trusting ɗin ka amma yanzu kana neman jefa ni cikin zargi kar mu fara rayuwar zargi a cikin gidan nan..., what jawaher kanki ɗaya kuwa kike faɗar haka..?, ɗam tayi ta buga kan'ta tabbas bata cikin nutsuwar ta , amma abin da taji bashi da nasaba da abin da , tasha, batayi tunanin zai shigi yanzu ba , tasha totalling syrup zama tayi a ƙasa kan'ta na juyawa tashi tayi tana tan gaɗi da sauri ya riko ta ya taɓa kan'ta yace '' sweet yanzu daga wannan magana sai ki shiga wannan hali..?, limshe idanuwan'ta tayi bacci ba fusgarta ganin haka sai ya lallaɓa ta tayi bacci dai-dai ta mata kwanciyar ta , yayi ya tashi ya dauro alwala zama yayi ya fara karatun Alkur'ani mai girma bayan ya idar misalin ƙarfe 1;20 yayi Sallah sannan ya kwanta ************ 1:30 CLUB Motocine jere tamkar ba dare bane gurin wasu ma yanzu suke zuwa wata motace tayi parking yayi dan ta toshe wa masu fita hanya saboda a ƙan hanya ta ajiye motar fitowa tayi tamkar bayar musulma ba wani irin mini skirt ne a jikin ta wanda ake wa kira dashi gwara babu kanta yaci kalbar attachment sai wura hanci take fuskar nan tamkar zata gasar sarauniyar kyau duk uban adon nan da taci kallo ɗaya zakai mata , kasan cewa ranta a ɓace yake saboda idon ta yayi ja taku take ɗanɗai shiga cikin gurin tayi tamkar zai tsaya saboda ƙiɗa ratsawa tayi ta shiga ko wa yana sabgar gaban sa ba wanda ya lura da ita, itama kai tsaye table ɗin da ake sai da giya ta nufa zama tayi ta dauki guɗa, ɗaya ta kai bakin ta da sauri mutumin yace '' a'a gaskiya yau billahilazi kika shamin baki biya ba kika taɗa hankalin karya to yasin sai na yi miki rashin mutunci.., ajiyewa tayi sai ta tashi saboda abin da take nema ta samu gyara zaman p-cap ɗinta tayi ta dauki kwalbar ta bar gurin binta ya dinga yi da sauri ta hau sama a guje ya biya har sama dakin da taga ya shiga da wasu yan mata nan ta shiga a kuje ta buga kofar dakin duk wannan abin da yake faruwa bama su san ana yi ba , saboda sheɗan ya buga musu gangarsa ɗaukan kwalbar tayi ta buga akan wata marashiyar budurwa ƙara ta saki da ta dinga amsa kowa a club ɗin.., da sauri matashin nan ya riƙo ta yana cewa nailah anya kuwa lafiyar ki kalau kin ga abin da kikai mata fa..? ɗurƙusawa tayi tace '' DAZ aza ton ka ni irin banzayen yan kwalta din nan ne da za'a ɗinga cik su daga ƙarshe a jefar da kwallon mangaro to kayi kuskure wallahi wallahi wallahi wannan abin da nayi maka kaɗan ne daban caccaka mata wuƙa ba a ni zaka yaudara ka baro ni da gidan iyayena ka kawo ni bariki kake tunanin barina kuma to kayi kuskure DAZ kayi Kuskure wallahi.., wanda ya biyo ta ya tsaya yana kallon ikon Allah gaskiya nailah yar bala'ice ga jini sai mulala yake ko a jikin ta da sauri yace '' wallahi bara na kirawo yan sanda wannan ta'asar da ki kayi ba'a san a inda zata tsaya ba.., dalla can rufe min baki ka bari masu abin faɗa su faɗi kudin ka kake ji ko ..? shiru yayi jikin sa na rawa kar shima ta lumamai kwalba domin ya lura bata da imani lokacin da aka raba shi tayi bacci Dala ta ciro a bayan wayar, ta ta cilla mai tace '' matsiyaci dauki nafi karfin naci maka abu wallahi..., Wannan matashin tallafo kan wacce aka fasa yayi ya ɗauke ta suka fita zama dirshen tayi zuciyar'ta na tsananin bugu ya tafi ya barta bata san yadda za tayi ba shima dayan tafiya yayi ya barta da sakakken baki. dakyar ta , tashi ta fara tafiya ranta duk a bace fita tayi daga gurin gaba ki ɗaya samu tayi mutane na ta jiranta saboda tayi parking da dai-dai ba.. Copy is not allowed 🚫 EPISODE 4 Tana zuwa ba wanda tayiwa magana ta shiga motar ta tayi baya , sannan ta fita da gudu Allah ya rufa asiri Bara buge wani ba tamkar zata tashi sama haka take gudu a daidai wani gida tayi parking din motar ta , fitowa tayi ta soma buga gate din gidan ma mallakiyar gidan ta buɗe kofar gate din cikin mamaki tace '' Nailah kice cikin daren nan..., kallon ta tayi tare da tabe bakin ta tace '' hmmm wallahi deeyana raina a ɓace yake.., okay shigowa daga club kike ne..? shugowa tayi ta jingina da bango tace '' daga can nake budurwar DAZ na fasawa kai , wallahi deeyana namiji ba dan goyo bane dan kunama ne ki kalli irin halarcin da nayiwa DAZ amma har ya iya saka min da wannan abin.., dariya tayi ta riko hannunta suka shiga ciki shisha ta ɗauka ta fara sha bata cewa nailah komai ba sai da ta sha kashi isarta tace '' barki nayi ki wuce nailah gaki mace har mace amma kin tsaya wani banza irin DAZ yana ɓata miki rai ki shiga harkar sahun manyan mata kin ganni nan ba ruwana da tension ɗa namiji mijina tamkar photo yake a gurina dan dai bana son idon mutane ya komo kaina da tuni na dade da yanka mai ticket ya kama gaban sa , to ta wani fannin aure suttura ne kuma mutuncin ɗiya mace ne amma banda haka da tuni labari yasha bamban Na'ilah mace tafi namiji iya soyayya mace zata ririta ki tamkar kwai ni wallahi na zata oder matan da na yi ce , ta zo shiyasa ka ma na buɗe kofa ashe ke ce.., taɓe baki Nailah tayi tace '' ai sai kuyi ni kam bana sha'awar wannan harka.., dariya deeyana tayi taci gaba da sabgar gaban ta. kara knocking din kofar akayi da sauri ta tashi tace '' har sun zo..., rikota nailah tayi tace '' hmm kinga kina budewa batare da kin tambayi waye ba wata ran za kiyi dana sani.., da sauri ta juyo tace '' DA NASANI kuma ta me ..? naga kema budewa ta da wuri yayi miki amfani.., ajiyar zuciya ta sauke tace '' nidai na faɗa miki amma idan baki ji ba ci gaba da yi..., hmm kawai tace ta fita leƙawa tayi ta wata yar kofa sannan ta buɗe da gudu wata matashiyar budurwa ta rungume ta cikin so da kauna kulle kofar tayi ta kamo hannunta suka shiga ciki, zama tayi akan ɗaya daga cikin kujerun parlour tace '' deeyaa wannan kawarki ce..?,. da sauri deeyana tace '' Nailah ce wacce nake baki labarin'ta ba na turo miki picture's din ta ba ko baki gane ta ba ..., wow a zahiri tafi kyau picture din da kika turo min ya boye ainihin zahirin kyawun ta duk wannan maganar da take yi ko sau ɗaya Nailah bata dago ta kalle ta ba , gaba ki ɗaya haushin kowa take ji wannan wanne irin salon yaudara ne daman an dade ana faɗa mata haka sai yau taga zahiri. dariya deeya tayi ta dafa ta , tace '' sweet me yayi zafi shi ba wuta ba sorry haka ahalin maza suke one day insha'Allah zaki samu wanda zai yi zame miki tamkar uba.., ture hannunta tayi ta cije lips din'ta kwanciya tayi ta ɗora kafa ɗaya kan ɗaya idanuwan'ta na kallon sama zuciyar'ta na faman bugu tamkar zata fasa kirjinta ta fito deeya saka hannu tayi akan kirjinta tace '' sorry sis kar ki sakawa kanki damuwa akan wannan dan wahalar.., ture hannunta tayi saboda , saka hannunta da tayi tana messages din nipple din'ta da yaka bata saka bra ba ta fito ƙara mai dawa tayi ta kifa kan'ta a kirjnta tace '' Nailah be kamata ki dauki garar bakin ciki ba ki ɗorawa kanki..pauzy zo ki tayani rarrashinta wani saurayin'ta ne ya yaudareta duk da ta fasa kan shegiyar budurwar tasa.., tashi pauzy tayi ta zauna kusa da ita tace '' kiyi hakuri ki dena damun kanki kinga sweet ma ta damu ganin halin da kike ciki Please ki manta da shi shi ya saka wallahi bana saka kaina a soyayyar ɗa namiji.., tashi zaune tayi tace '' Please ku rabu dani hutu nake buƙata kun wani zo tamkar zaku shege jikina kar wacce ta ƙara taɓani deeeya kinsan bana son wannan rayuwar ko..? ku rabu dani wallahi ko kaɗan banji sonsa ya ragu a cikin zuciyar'ta ba sai ma kara nunkuwa da yayi ni dashi duk kaddara ce ta kai mu ga shiga wannan halin da kuma laifin iyayen mu sune SANADI. pauzy hannu ya zura cikin rigar' nailah tana matsa mata maman'ta wani dogon numfashi nailah ta saki tare da riƙe hannun deeya itama deeya hannunta, ta rike nan fa labari ya chanza aka hau lamari baji ba kama hannun yaro wannan shi ne karon farko da nailah ta aikata haka. ASUBA TA GARI kiran sallar asubar farko a kunnen NAJLAH tashi tayi da sauri ta miƙe ta shiga toilet dauro alawala tayi ta fito ji tayi ana knocking din kofar ta , ba mamaki yaya ne dan haka ta buɗe da sauri ganin sa tayi tare da jawaher hannunsu sarkafe dana juna yana ɗauke kai tayi tace '' barka da asuba.., barka dai ashe kin tashi da muka zo ni da sweet mu tashe shi jawaher ta faɗi haka Cikin wani irin salo. dauke kai Najlah tayi sam matar batai mata ba ko kaɗan tace '' eh wallahi har na yi alwala jira nake a tayar nayi sallah.., okay sweet lokaci na kurewa muje na raka ka mu dawo ko...?, zare hannunsa yayi yace '' nan ma is okay yayi thanks.., murmushi tayi mai ya mada mata da martani da alama ma sun manta da wanzuwar NAJLAH a gurin fara tafiya yayi jawaher tace '' sweet.., juyowa yayi kiss tayi mai ta wura mai iska ganin wannan rashin kunya tafi ƙarfin ta da sauri ta bar gurin jikin'ta na rawa.. zama tayi akan gado kirjinta na tsanan'ta bugu haka zata zauna da wa'yannan karuwan ba ko kunya suna aikata abin da sukai niya anya kuwa ba zata kira aunty hafsa ba ta faɗa mata har ga Allah ba zata iya ba , suyi abu su barta da jin kunya. kiran sallah aka kirawo da sauri ta tashi ta tada kabbarar sallah bayan ta idar tana sujjadar ƙarshe sosai ta tsaya tana kai wa Allah kukanta bayan ta dago tayi zaman tayya tayi sallama azkar ta zauna tana yi har karfe bakwai tayi shiga toilet tayi ta , tayi wanka ta fito daure da towel a jikin ta zama tayi akan stool ta kifa kanta a drawer ta dade a haka sannan ta tashi wayar ta ta ciro a chaji ta kirawo number din aunty hafsa bugu ɗaya ta dauka NAJLAH tace '' Assalamu alaiki aunty Barka da asuba ya su aslam suke..?, wa'alaikis'salam barka dai suna lafiya qalau alhamdulilah yanzu ma breakfast zan haɗa musu yau akwai makaranta kin tashi lafiya..? Najlah ta share kwalla muryar ta na rawa tace '' alhamdulilah eh yau akwai makaranta aunty.., aunty Hafsah tace '' na'am NAJLAH me ya faru muryar ki na rawa..?, bana son zaman gidan nan aunty wallahi abin da suke ko ke sai sun bawa kunya kuma kinsan halin yaya badai mugunta ba jiya Allah ne ya rufa asiri be yi gunduwa gunduwa da nama naba. ta karshe maganar cikin kuka. dariya aunty tayi me isarta tace '' look najlah me ruwanki da rayuwar su, ki nutsu kiyi abin da ya kai ki duk wannan nunkufurcin da kike yi bakya son zama ne kwata kwata , kina da kulafici da ace yanzu gidan mijin'ki aka kai ki, kiyi yaya kenan..? shima cewa za kiyi bakya son zama, duk wani abu da za suyi kauda idon ki, wata ran sai labari komai yana da lokaci kema akwai zuwan naki lokacin very soon yana nan zuwa JAWAD kuma ko giyar wake yasha ba zai iya kai hannu jikin ki ba da sunan duka ki sa wannan a ranki, aunty jiya fa murɗe min hannu yayi yadda kika san zai karya ni ita kuma muguwar matar sa , duk ihun da nayi ko motsinta ban jiba akan yaga video a wayata. dariya aunty Hafsah tayi tace '' to ban da abin ki ya za ta shiga tsakanin ku, kefa da jawad me raba ku sai Allah ina muku fatan haka insha'Allahu mutu ka raba.., da sauri Najlah tace '' kai aunty hafsah wannan wacce irin magana ce.., kinga yanzu dai zan yi aiki in anjima zan kiraki mu ci gaba da magana. to ki kirani dan Allah. karki damu kanwata zan kiraki. ta fada haka tana kashe wayar ta tashi najlah tayi domin ta saka kaya, ji tayi an turo kofar da kin ta da sauri ta rarumi hijabi ji tayi tamkar ta nutsai a cikin ƙasa Saboda kunya tasan ya riga da ya gama ganin ta gashi towel din ko mazaunanta be rufe mata ba kasa tayi da idon ta tana wasa da hannunta cikin deep voice din sa yace '' breakfast is ready kiyi sauri ki shirya, kai ta gyaɗa mai fita yayi be ce komai ba da sauri ta buɗe wardrobe abaya ta dauko C-green an mata aikin beadwork a jikin ta yar Turkiya dauko riga da wando tayi ta saka sannan ta saka abayar tare da daura dankwalinta bata tsaya bata fuskar'ta ba wajen kwalliya kawai lipstick ta saka tushe hancinta tayi , ta feshe jikinta da turare saboda tana da asma slippers ta saka ta fito tun daga nesa ta jiyo kamshin turaren jawaher har makaki yake mata a maƙogaro ya mutsa fuska ga fuskar'ta taci uban make over to ai wannan kwalliya sai dai a kirata da make over tamkar jambaki zai yi magana a bakin ta ‘‘O‚‚ kowa akwai kiwon da ya amshe shi in banda haka ita ko iya shakar numfashi ba za ta iya da wannan uwar kwalliya ba , ga uban gashin doki, karasawa dauke kan'ta tayi da sauri jawaher ta tashi ta ja mata kujera dai-dai lokacin da takai hannu zata ja kujerar dining table ɗin ja baya tayi ta sarke hannun ta jawaher bayan ta ja mata tace '' kanwata bisimallah ya kwanan kaɗaici..?, Najlah tace '' Nagode alhamdulilah.., Hakan da tayi ba ƙaramin kimarta Jawad ya kara gani ba , yana so a nuna ana son jininsa ana ji da shi kallon jawaher yayi wani fari tai mai tace '' ya dai..?, kafe ta yayi da idanuwan'sa tari ne ya sarke Najlah da sauri ya taso zai bata ruwa jawaher tayi maza ta dauko lemon gabanta ta miƙa mata tare da kamar na hannun JAWAD ta kai bakin ta, tana bin sa da wani irin kallo. ikon Allah haka NAJLAH tace a zuciyar ta kasa shan ruwan tayi zama tayi tane cewa Alhamdulilah na dawo dai-dai. wani miskilin murmushi JAWAD yayi ya koma ya zauna serving dinta tayi tun da ta fara cin doya dakwai da tea bata ɗago ba hankalinta ya mayar gaba ki ɗaya kan abin da take ko farfesun da ta zuba, mata bata jin zata iya ci saboda cikin'ta ya cika baza ta iya ci ba. matsar dana gaban ta, tayi tace '' nakoshi.., da sauri ya ɗago yana kallon ta abin ya bashi mamaki yace '' har kin koshi ko rabi baki ce ba na gani.., kan'ta na ƙasa tace '' eh nakoshi.., Jawaher ta ɗora hannunta akan nasa tace '' sweet inaga ta koshin ne tun da ba za taiwa kan'ta mugunta ba , bata koshi ba tace mai ta koshi kasan doya akwai cika ciki..., Haka ne ya faɗa yana ci gaba da cin abincinsa gyara zama tayi tace '' sweet ya maganar tafiyar tamu ne..?, kije Allah ya kai ku lafiya wani ihu tayi tare da tsalle ta rungume shi tana yi mai kiss duk sai data ɓata mai fuska Najlah da ta fito miƙa mai waya anni za tayi magana dashi taga abin da ya kusan sumar da ita dan kunya ƙasa tayi da idanuwanta tamkar ƙasa ta tsake ta shiga, ita wallahi mamaki halin yaya take yanzu shi ya koma haka Allah me iko. Copy is not allowed 🚫 EPISODE 5 Da sauri ya saki bakin jawaher da yake mata wani irin kiss jikin'ta a sanyaye ta miƙa mai wayar tace '' anni ce take son magana da kai.., amsa yayi, ya kara akunne gaisawa su kayi sannan ta tambaye shi ya iyalin nasa alhamdulilah yace , anni tace '' to JAWAD na sanka ba dai iya mugunta ba yadda kasan kurtun soja ne ya raine ka , dole sai kai hakuri da halin NAJLAH yarinya ce a sannu a hankali kana nuna mata nan zaki bi wannan hanyar tafi zata koma yadda kake so, dan Allah ban da nuna isa su ya'yan yanzu lallabi da nasiha ke aiki a jikin su kar kuma inji wani abu ya biyo baya nasan ka sarai tun kana yaro dan haka , ka kular min da jika karatu tazo dan haka bana son jin wata magana.., sosai ƙarshen maganar ta , ta bashi dariya shafa kai yayi yace '' insha'Allahu zan kiyaye amma ita ma ku ja mata kunne jiya video's naga ni a wayar ta , a haka za tayi karatun ga kallon fina finan yan Japan da Philippines.., Dan Allah dai a kula kaji dan Allah barka to yace sukai sallama miƙa mata wayar yayi lokacin jawaher ta bar gurin amsa tayi jikin ta na rawa ita kuma haka Allah ya haɗa ta da kaddarar zama da wa'yannan mutane da ba su san mece kunya ba juyawa tayi tana tafiya a hankali tamkar wacce kwai ya fashewa a ciki. tana shiga daki ta rufo dakin ta , ta kwanta dan ya mutsa fuska tayi tsoron ta ɗaya lokacin period dinta yazo ba karamar wahala take sha ba shiyasa kama abinci ta ci shi kaɗan, duk hankalin'ta ba a kwance yake ba. sosai take juyo saboda cikin'ta ji tayi anyi knocking da kyar ta iya tashi gumi duk ta wanke mata fuska ta buɗe kofa yaya ne fa shirin tafiya wajen aiki zama tayi a ƙasa tana matsar kwallah tace '' yaya JAWAD mutuwa zanyi cikina ciwo yake min.., da sauri ya ɗurkusa kasa ya tallafo habar'ta yace '' Najlah me yake damun ki..?, cikin ta tayi mai nuna dashi ba ƙaramin tashin hankali take ciki ba kuka ta rushe dashi ta kifa kan'ta akan cinyarsa tana kuka jawaher ce ta shigo ta gama haɗa trolley din'ta tace '' to me yake faruwa sallama na shigo nayi mata..?, kallon ta yayi yace '' har kin shirya..?, kai ta ɗaga mai fuskar'ta cike da alhini ta durkusa tace '' me yake damun ta..?, ta ƙara mai maita masa tambayar da dazu tayi mai ajiyar zuciya ya sauke yace '' cikin'ta ke ciwo.., innalillahi sannu normal ciwon cike ne ko na period ta faɗa tana kallon Najlah. ƙasa magana Najlah tayi sai juya kai take yi hannunta na kan mararta jawad ya kalli jawaher yace '' sweet kawai ki tafi Allah ya kiyaye hanya ba zan samu damar kai ki ba zan kirawo doctor kar na ɓata miki lokaci tun da shi jirgi baya jira.., haka ne wallahi to Allah ya bata lafiya ta faɗa tana tashi daga tsugunan da tayi ranta fas tamkar zata , taka rawa fita tayi tare da ja musu kofa ɗago kan Najlah yayi yace ''sannu kinji ko bara na kirawo doctor ya duba ki.., ƙara rushewa tayi da kuka ta girgiza mai kan'ta tare da riko hannun sa tace '' karka kirawo shi allura zai min a hankali zai sake ni bana so a ka kirawo doctor.., haɗe rai yayi yace '' bana son zancen banza sai ma kin zaɓi abin da za ayi miki bacin kuma baki da lafiya.., kuka ta ƙara rushewa dashi cire mata mayafin'ta yayi sannan ya balle mata riga ya cire ganin irin gumin da take yi itama ba tayi kokarin hana shiba saboda bata cikin nutsuwar ta. kwantar da ita yayi a akan gado ya cire rigar sa ta lauya da wular da ya saka ya matsar da briefcase din'sa da wasu folder's da ya fito da su daukan wayar sa yayi ya dannawa doctor Kira bugu ɗaya ya ɗauka yace '' doctor Dan Allah kazo gidana akwai mara lafiya..., doctor yace '' wallahi bana gari amma bara na turo maka sister zuwairat insha'Allahu zata so cikin gaggawa itama tasan aikin ta.., okay ba damuwa sai ka turo ta ɗin ya faɗa yana kashe wayar sa , zama yayi kusa da ita kuka ta ƙara rushewa da shi ta riko hannunsa tace '' kiramin Hajiya ta zan mutu yaya.., da sauri ya kalle ta , shi be san ya zai yi da yarinyar nan ba rakinta yayi yawa dauke kai yayi yace '' ina wayar ki, ki kirata da ita mana.., kuka ta rushe dashi ta kwantar da kanta a cinyar sa tace '' yaya cikina ciwo.., ya buɗa baki kenan zai magana wayar sa tayi ringing da sauri ya ɗauka saboda yana kyautata zaton doctor ce ɗagawa yayi ai kuwa ilai itace sallama tayi mai tare da gaishe shi cikin girmamawa amsawa yayi tace '' ina bakin gate masu gadib gidan sun hana ni shigowa..., Okay karki damu suna kan aikin su ne , zan musu magana yanzu. to tace mai ya kashe wayar gyara mata kwanciya yayi ya fita kuka ta ƙara rushewa dashi har suka dawo bata sani ba doctor zuwairat ta durkusa ƙasa tace '' innalillahi wainna ilaihir raji'un sannu me yake damun ta..?, ta ɗago da kan'ta tana kallon Jawad cire medical glasses dinsa yayi yace '' ciwon ciki.., oh Allah ya bata lafiya idan tana yi allura ake mata ko magani ake bata da sauri Najlah ta firgita tare da ja da baya hawaye wani na bin wani gaban ta na faɗuwa tace '' dan Allah karki yi min allura karki bani magani yanzu ma ya fara saki duk wata haka nake yin sa.., dariya abin ya so ya bawa doctor sai ta danne ta zauna akan gado tace '' yanzu idan ban miki wa'yannan abubuwan da kika faɗi ba , me zan miki..? kefe mace, ce wannan ciwon da kike gani ko kwatan ciwon haihuwa be kai ba.., da sauri Najlah ta ɗago lokaci ɗaya suka haɗa ido da Jawad hawaye ta share ta kalle sa tace '' cikin nawa ya dena yi min ciwo ba sai tayi min komai ba.., haɗe rai yayi yace '' ni sa'an kine ko ita da kike faɗa mana haka..?, murmushi doctor tayi tace '' na lura yar daru ce kawai bara na rubuta mata magani idan taci abinci ta sha zai saka ta bacci insha'Allahu kafin ta tashi cikinta ya cika kuma period din zai zo batare da ta ƙara wahalar da ita ba.., okay ba damuwa rubutu tayi mai a takarda ta miƙa mai kuɗin'ta ya dauko ya bata tai mai sallama tare da godiya ta fita be biya takan Najlah ba , ya fita ya bawa me musu aike ya siyo mai zama yayi a parlour yana jin sautin kukan ta ransa duk a ɓace yake ciwon kai kuka yake saka shi , ga wannan kukan da take har tsakiyar kan'sa yake jin kukan nata. tsaki yaja jin anyi knocking ya tashi ya buɗe kofa ya karbi ledar maganin yace '' riƙe canjin..., godiya yayi mai ya rufe kofar kai tsaye kitchen ya nufa rasa me zai mata yayi gwara ya tambaye ta me take so komawa yayi dakin ya ajiye ledar maganin a kan bedside drawer ya zauna yace '' me za kici.., ɗago da kan'ta tayi ta kalle sa tace '' dambu..., da sauri ya kalle sa shi tun da yake a rayuwar sa ya taɓa kwatan ta dambu ko da yayi zaman hostel bayayinsa tunda wani aikin sai mata cikin mamaki yace '' dambu kuma...?, kai ta gyaɗa mai ba tare da tayi magana ba ajiyar zuciya ya sauke yace '' sai dai na yi miki oder take a way ni ban iya dambu, ba bana jin jawaher ma ta iya gashi ɗazu ta bawa me yin girki hutu sai ta dawo tun da gaki a cikin gidan zaki saboda tafiya za tayi.., dauke kai tayi wato gata baiwa ko ta girkawa mijinta ban da ita mara hankali ce bama ta damu abincin wannan shi ake cewa mijinta ba Allah ɗaya gari bamban. jin tayi shiru yace '' magana fa nake miki..?, ya tsuna fuska tayi cikin ta na murɗawa tace '' a'a barshi kawo min yogurt.., tashi yayi ya fita bajimawa ya kawo mata tsiyaya mata , yayi a cikin kofi amsa tayi ta tashi ta fara sha tas ta shanye sannan ya ballo mata magani da ruwa ya miƙo mata kwalla ce ta taru a idanuwanta ta kura mai ido zuciyar'ta tamkar zata faso kirjinta ta fito saboda tsabar fargaba hade rai yayi, dan haka ba shiri ta amsa ta saka a bakin ta amai ne ya taso mata , da sauri ta shiga toilet ta fara kwara amai gaba ki ɗaya abincin da taci sai da ta amayar dashi. hankalin sa ne ya tashi da sauri ya shiga toilet din duk ta ɓata jikin'ta da amai gashi jikin ta ya saki dole sai ya temaka mata ta gyara jikin'ta, KARUWAN CIKIN GIDA Copy is not allowed 🚫 EPISODE 6 a hankali ta furta zan iya gyara jikina ka tafi aiki.. da sauri ya kalleta still har yanzu tana jikin'sa yace '' za ki iya kar na tafi ki shiga wani hali..?, kai kurum ta gyaɗa mai zuciyar ta na wani irin mugu tamkar zata fasa kirjinta, ta fito, haka kurum ku sancin su yana jefa ta a wani irin yanayi dan baka bata so musamman kallon da yake mata be gamshe ta ba , bata aminta da shi ba. tashi yayi ya fita da kyar ta iya cire kayan ta, sai dai tsantsin aman da tayi, ya kwashe ta, ta faɗi ƙasa ihu ta saka da sauri ya shigo rintsa idon'ta tayi, shikkenan ya gama da ita ya gama ganin komai kai ta girgiza tace '' yaya la fita faɗuwa nayi zan iya komai dan Allah ka fita.., ganin yanayin da take ciki idan ya fita be mata adalci ba dan ba iyayen su be kamata ace ya wufuntar da ita ba. kuka ta rushe dashi ta fara ture shi be saurara mata ba tas ya gyara mata jiki ya naɗeta a towel ya fito da ita tamkar wata jaririya, kwantar da ita yayi a gado sannan ya koma toilet din ya gyara shi tas wanka yayi ya fito, daukan kayansa yayi,ganin tayi bacci sai ya fita ya jawo mata kofar ta ,kai tsaye bedroom din'sa ya shiga ajiye kayan hannunsa yayi ya ɗauki wayar sa message din jawaher ya fara cin karo dashi kamar haka sweet yanzu muka tashi kai mana addu'a i love You limshe idanuwan'sa yayi ba ƙaramin sanyi yaji ba a zuciyar yi mata reply yayi ya ajiye wayar yana jinsa acikin wani irin yanayi duk abin da yayi ɗazu karfin hali ne amma yaki da zuciya shi ya riƙe shi be aikata abin da zuciyar sa take kawata mai ba. Wannan kenan Nailah tashi tayi dakyar kanta na mata wani irin ciwo dafe shi tayi tace '' deeya bani maganin ciwon kai , wallahi kaina ciwo yake.., tashi deeya tayi ya buɗe drawer din'ta ta miƙo mata magani tare da bude fridge ta dauko mata ruwa watsa su tayi a bakin ta ta kora da ruwa sannan ta saki ajiyar zuciya ranta duk a ɓace pauzy ta kalla tace '' haɗa min ruwan wanka gida zan tafi..., Gida kuma..? cewar deeya gyaɗa mata kai tayi tace '' gida nake son zuwa kudin hayar da DAZ ya kama mana ya ƙare ko daman ace be ƙare ba ina son tafiya gida nagano wanne hali su baba suke ciki.., Mahaifinki fa Cewar deeya jingina tayi da , allon gado tace '' hnmm ba abin da zai min iya yakaci yace zai dauko yan sanda su fita dani kuma yayi tabanza ba inda zani wallahi gwara duk abin da zanyi na zauna a gidan iyayena su kan'su sun sallama ni ina da right din da zanyi abin da na ga dama.., to Allah ya kyauta pauzy ya faɗa tana tashi daga kan gadon deeya jin ana buga kofa suka yi da sauri deeya ta tashi tace '' anya kuwa ba Yusuf ne ya dawo ba.., da sauri nailah tace '' Yusuf kuma daman ya sanar miki zai dawo.., gumi ne ya wanke mata fuska ta gyada kai tace '' yadai ce min a cikin satin nan zai dawo tun da naji bugu da safiyar nan to ba mamaki shi ne wallahi.., jikin'ta na rawa tace '' maza dan Allah ku tashi ku saka kayan ku.., ai bata ƙarasa ba taji wayar ta tana yin ringing da sauri ta dauka tuni sunan da tayi saving number sa ya fara yawa a screen din wayar ta kallon pauzy tayi tace '' wallahi Allah shi ne.., dariya pauzy tayi tana saka bra tace '' to mana ki ɗaga ba abin da zai zarga tunda ba gardawa ya gani ba.., Kina kuwa da hankali kinsan me kike fadi wanne ba abin da zai zarga kinsan maganar da mutane suke faɗa mai a waje kuwa matar sa tana tara mata bana arziki ba matar sa kaza da yake shi ya aminta dani sai dai ma yazo ya bani labari.. tashi Na'ilah tayi tace '' ni na hakura da wankan nayi a cikin gidan mu, bara na kwashe kayan can da mukayi amfani dasu akwai kwalaban da muka sha da shisha ke sai kije ki ji dashi.., okay Dan Allah maza ki dauke zan daga wayar sa , to tace mata , ta fita ita kuma ta dauki wayar tana cewa my love ina toilet ne kai hakuri ka kirawo bana kusa.., daga can tana iya jiyo zallar farin cikin da yake ciki yace '' okay ba damuwa fito kofar gida..., cikin nuna mamaki tace '' na fito kuma me ya faru..?, honey ki fito mana ki ganewa idanuwanki. daukan mayafin'ta tayi tace '' to bara na dauko mayafina na fito hice ko ba mazan da suke taruwa yan zaman banza ni wallahi bana son haka , su dinga kallon haramun.., cikin jindadin riƙe mai amanat sa da tayi yace '' to ai lahira akwai darmar lahira haka kurum ku dinga zama akan hanya baka bawa hanya hakkin'ta suna kallon shige da ficen matan mutane., kai dai bari abin nan nayi min ciwo my love 💕 😘. Cewar deeeya Yusif yace '' to bakomai wata ran sai labari insha'Allahu mun kusan matsawa mu bar musu gurin yanzu da yake safiya ce ma ba kowa.., yauwa har naji dad'i wallahi. ta faɗa tana fitowa daga parlour bude kofar gate din tayi shigowa yayi hannunsa riƙe da jaka da kayan yan sanda rungume shi tayi tana sakar mai kiss tace '' honey nayi missing dinka sosai wallahi.., kiss shima yayi mata yace '' nima haka ya babyn..?, shafa cikin ta , tayi tace '' baby mun yana cikin koshin lafiya.., riƙe hannunta yayi ya kulle kofar suka shigo tamkar ba ai komai ba , parlour tsaf ga su pauzy sun ci hijabi tamkar wasu mutanen arziki har ƙasa suka durkusa suna gaishe shi amsawa yayi yana cewa Barka da Safiya ya mutanen gidan.. Nailah tace '' barka dai yallaɓai wallahi kowa lafiya sannu da zuwa.., sannu yace haka ma pauzy yace mata ta bashi amsa cikin ƙasa dakai shiga su kayi bedroom ɗin su deeya ta zauna akan gado cikin kissa tace '' baby nayi maka laifi dan Allah ka yafe mini.., zama yayi kusa da ita yace '' baby laifi kuma wanne..?, kwantar da kan'ta tayi akan kafaɗar sa tana jan zip din Jean's ɗin sa tace '' wa'yannan ya'yan makotan mu ne na gaji da zaman kaɗaici gashi ba komai nake iya yiba saboda baby ɗazu ma amai na gama yi bana iya cin abinci idan har ni, na dafa shi, shine na yiwa maman su magana ta bani su wallahi ba ruwan su dan Allah ka yafe min ban nemi izini kaba nayi gaban kaina.. cikin fusgar numfashi saboda salon da take mai ya saki wani nishi yace '' oooh ba damuwa, duk abin da ki kayi dai-dai ne.., ba addu'a ba komai haka suka fara biyawa junan su buƙata dan dai ta kauda mai da zargine ta biye mai amma ita ko kaɗan bayan gaban ta. bayan komai ya wakana ya kwanta yana cewa baby yau mun tabka abin kunya tun da ma dawo kin bar bakin ki su kaɗai a parlour wata kila duk ihun da nayi sun ji shi gyara kwanciyar ta , tayi a kan kirjinsa tace '' a haba ba abin da za suni idan ba sun ji ai ba wani abu bane ba suma kansu za su zo yadda ka dade baka gidan nan , na baka kulawa yadda ya kamata sai dai kuma idan mutum me so ta ka. Sane wanda baya son auren mu ya dora shine zai bani gurguwar shawara, yau watan ka nawa baka gidan nan , ka dawo na kasa baka farin ciki kullum ina alfahari da kai kana riƙe min kanka baka bawa matan waje saɓanin wasu mazan a yanzu da suna da matan su amma suke bin wasu kaga kuwa dole na yi wa Allah godiya nake kuma ƙara son nayi maka duk abin da kake so nayi maka shi akan lokaci.., limshe idanuwan'sa yayi yana cewa nima haka nakewa Ubangiji godiya da ga bani ke a matsayin mata ta , ina rokon Ubangiji har gidan Allah muna tare.. amin ya Allah tace parlour kuwa duk abin da ke wakana suna ji pauzy tace '' kaji tsoran Allah kaji tsoran shedaiyar mace.., murmushi nailah tayi tace '' gaskiya kam kamar ba jiya muka gama Magana da ita ba amma ga yadda take tura kansa a cikin leda.., tafawa su kayi suka ci gaba da hirar su. Wannan kenan. TURKIYYA *Calista Luxury Resort* ba ƙaramin kyau gunrin yayi mata ba , dan haka take bin ko ina da kallo tace '' habibtee gaskiya wannan gurin yaci kudin nasa komai unique ba ko a ina zaka samu haka ba , sai muyi shekera a gurin nan ba ruwan wani da wani.., shafa bayan'ta yayi yace '' idan kinji ana cewa duniyar hutu da jin dad'i to wannan kenan.., zama ta yi ta ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya tace '' na lura da haka wallahi.., wayar tace tayi ringing da sauri tace '' miko min waye ya kira ni.., wannan dan wahalar mijin naki..? da sauri ta kalle sa ta haɗe ranta tace '' alhaji be kamata ace kana jefan mijina da irin wa'yannan kalmomin ba ni, narasa me yaha haɗa ka dashi kuke wannan takun sakar.., dauke kai yayi be ce mata komai ba , ɗaga wayar tayi cikin fargaba da yake dazu ta yi mai text message sun sauka ajiyar zuciya ta sauke ta ƙara wayar a kunne tace '' hello sweet heart ashe kaga text message dina ya me jiki..?, ta faɗa tana tashi daga gurin da alhaji yake zaune. hakan da tayi ba ƙaramin fusata alhaji yayi ba , da yana da hali da tuni ya dade da kau da Jawad a doran ƙasa yasha tura mai yara su kashe shi amma yana tsalle tarkwan da ha ɗana mai amma ba komai wata ran hakar sa zata cimma ruwaaa... bata jima ba ta dawo ta zauna akan cinyar sa tana shafa sajensa tace '' ya haj ya na ga ranka kamar a ɓace yake me ya faru lokaci ɗaya wannan kyakkyawar fuskar ta nuna ɓacin rai.., saka hannunsa yayi yana shafa breast din'ta yace '' yanzu baby na biya mana kudi mu tafi wata ƙasar amma mun zo kamar baki da time dina ayyuka nawa na ajiye domin na faranta miki, ki zaga duniya na nuna miki yancin ki da wancan mutumin ya tauye miki shi ya barki a zaune a guri ɗaya bakya fita yawan buɗe ido,sai tafiya hajji malama ki fita ƙasashen turawa kiga yadda rayuwa ke wakana.., kan'ta ne ya fasu bata da amsar bashi tana son mijin ta ban da kwaɗayin abin duniya da kuma son kyali duk wanda take ciki be wa dace ta , ba sai wanda ta hangi a waje ba , abin da zai kai ta ga wannan rayuwar haɗe bakin su tayi tana mai wani irin zazzafan kiss 💋 wanda ya kusan tafiya da numfashinsa na hucin gadi. ganin wasan ya kai iya wasa ta dauke ta suka faɗa gado cikin fitar hayyaci su, sukan su, suke biyawa junan su buƙata ba karamin gigita masa lissafi take ba musamman yanzu da takai jijiyar sa bakinta tana sucking dinta zagewa yayi yana wani irin nisha hade da ihu shiyasaka kaf yan matan sa yake son jawaher ta iya sarrafa namiji a kan gado.. Ya Ubangiji ka shiryar damu ka bamu ikon bin tafarkin ka , hakika wanda Allah ya shiryar shine shiryayye. wannan kenan sai karfe goma Najlah ta tashi tana mustsuka idanuwanta da sukai mata nauyi tuno da abin da ta faru tayi ba ƙaramar kunya ce ta rufe ta ba , shikkenan fa ya gama ganin komai towel din ta ne ya zame da sauri ta daure shi a kirjinta, tare da tashi cikin nata ya cika ta ga wata iriyar yunwa da take ji tamkar an mata yasa a cikin'ta ko da daga jin yadda take ji a jikin'ta tasan yanzu jinin ya zo.. KARUWAN CIKIN GIDA. Copy is not allowed 🚫 EPISODE ⁷ Dakyar ta iya tashi, ta shiga toilet gyara kan'ta tayi sannan ta fito bude wardrobe tayi ta dauko riga da skirt straight me tsaga a gaba rigar kuma half bubu ce sosai mix and match din tayi mata kyau kasancewar ta , kaya suna amsar jikin'ta gyara kan'ta tayi ta daura dankwali. turare ta ƙara shafawa a jikin'ta da yake gari ne na zafi bata ce zata shafa mai ba a yanayin da take ciki zata iya amai cire zanin gadon tayi, ta canza sannan ta fito kai tsaye kitchen ta nufa gidan shiru tamkar ba mutune masu rai a cikin sa buɗe fridge tayi domin bata jin zata iya girki. gaba ki ɗaya fridge din ba , wani abu da zai iya riƙe mata ciki tsaki taja kamar ance ƙara buɗe gidan sama wasu lemuka ta gani, bata taɓa ganin irin su ba kamar liquor amma ba shi bane saka hannu tayi, ta dauko sai dai batai gigin sha ba ta duba direction din sa zaro ido tayi, ta dafa bango kiri kiri ga sunan giya a ciki to a cikin gidan nan wa yake shan giya jikin'ta har wara yake ta mai da lemon ta rufe tana zaro ido to ko acikin ma'aikatan gidan ne..? tun da taga akwai Christian a cikin su zare ido ta dinga yi yawa wacce tayiwa sarki ƙarya. da sauri ta gunna fanfo ɗin sink ta wanke hannunta buɗe fridge tayi, ta dauko tarwaɗa ta zama ƙanƙara sakata tayi a ruwa domin ta narke blending kayan miya tayi sama sama saboda tafi so ta gansu a ciki batare da sun niƙe ba bayan ta juye ta ƙara niƙa albasa itama sama sama tafi ma kayan miyan fitowa ginger ta daka guda ɗaya ɗanya ta ajiye a gefe bayan kankarar ta gama narkewa ta wanke tarwaɗa da lemon tsami saboda karni da kuma yauƙinta zai ragu. allaiyahu ta dauko ta yanka shi sannan ta ajiye shi ɗora tukunya tayi akan wuta, ta kunna gas farar shinkafa ta dauko gani tayi ba sai an ma gyara ba yar gwamnati ce. wankewa tayi ta zuba a cikin ruwanta , ta rufe fara soya kifin nan tayi da manja sannan ta cire ta ajiye a gife ta zuba tattasanta amma bata zuba albasa ba , saboda tafi so ta dinga jinta sama sama ita bata dahu luqub ba ita ba ɗanya ba. bayan ta gama soya miyar ta , ta zuba mata komai ta fasa tarwaɗar nan a ciki amma ta zare mata ƙaya sannan ta zuba allaiyahunta nan da nan gidan ya dauki kamshi gama tuwon ta , tayi. ta zuba a plate ta zuba miya ragowar ta saka a cikin flask kafin tuwon ya wuce sai ta gyara ko ina tamkar batai komai ba sannan ta fito kamar ance ɗaga kanki sama suka haɗa ido da yaya JAWAD da laptop a gaban sa gaban tane ya fadi kenan tun ɗazu yana gurin nan amma bata gansa ba tabbas da ta , fito taji kamshin sa , ƙasa tayi da kan'ta saboda kunyar da ta kamata alama yayi mata , tazo ajiye abincin hannunta tayi ta ƙarasa gurin sa tsugunawa tayi tace '' yaya gani.., sai da ya gama shan kamshin sa , sannan yace '' ya jikin naki..?, kan'ta na ƙasa tace '' da sauki.., Allah ya ƙara sauki idan kin gama cin abincin ki sha magani kar kuma nazo na ganki baki sha magani ba ranki zai ɓaci ya faɗa still hankalin'sa nakan laptop din'sa Najlah tace '' insha'Allahu zan sha.., period din tazo...? habawa ji tayi tamkar ƙasa ta tsage ta shige ciki , wata iriyar kunya ce , ta kamata shiru tayi ta ƙasa magana juyowa yayi ya kalle ta yace '' tashi kije.., tashi tayi tana jin yadda idanuwan'sa suke yawo a jikin'ta ƙasa tafiya tayi ta fadi Allah ya saka ta dafa wata flower da akai decoration da su a flower duk wata kusurwa akwai ta da sauri ya tashi ya riƙe ta yace '' subbanallahi ya za a yi daman ki saka wannan skirt din baki san yanayin jikin ki dana , da dayan zu ba ɗaya bane gabaki ɗaya yanzu jikin ki a buɗe yake sai kin gama period din nan zaki dawo dai-da kiyi taking care.., kura mai ido tayi hannunsa ya saka zai tsokane mata ido da sauri ta kautar da kan'ta, wata iriyar kunya ta kamata a hankali yace '' me kike kallo..?, kai ta girgiza mai alamar ba komai okay kawai yace , ya koma inda yake ya zauna ganin haka ita ma sai ta bar gurin cikin sauri ta dauki abincin ta , ta shiga daki zama tayi ta fara ci cikin nishadi abincin ba ƙaramin dad'i yayi mata ba bayan ta gama ci ta fito domin ta wanke plate din da ta ɓata ji tayi yace '' kin sha maganin naki..?, da sauri ta juyo ta girgiza mai kai to me kike jira ya faɗa haka yana kallon ta ƙasa tayi da kan'ta, ta turo dan ƙaramin bakin ta , tayi bata ce komai ba , takaici ne ya kama shi lallai ma yarinyar nan ta raina shi yana magana ta nuna mai kamar da bango yake magana ta kowa yayi a har ida take kwasa tayi a guje har tana ƙoƙarin hardewa zama yayi a kan sofa yace '' zubo min abinci.., leƙo da kan'ta tayi a cikin, kitchen idanuwanta fal da kwalla tace '' dan Allah ba zaka dake ni ba..?, da sauri ya juyo yace '' me kikai min da zan dake ki..?, hawayenta ta goge tace '' yaya jawad gida nake son zuwa.., ido ya kura mata yau kwananta ɗaya tana maganar tafiya gida yace '' da gidan Aliyu ne ba zaki ce , zaki tafi gida ba ko..?, da yake nan an daure ki a gidan dodo shi ne kika damu kanki sai kin tafi gida.., kasa magana tayi jin maganar da yace a cikin zuciyar ta , tace ba dole na so tafiya gida ba , kai gaba ki ɗaya baka san mene tausayin dan adam ba muguntar ka tayi yawa.. ganin tayi shiru yawa me tunani yace '' kije ki zubo min naci yunwa nake ji.., kana cin tuwo. da sauri ya kalle ta yace '' zaki zubo min ko sai na taso..?, da sauri ta shiga flask din ta dauko mai ta ajiye a gaban sa sannan ta dauko plate da chokali ta ajiye mai ruwa ta dauko mai da lemo ta kawo mai zata bar gurin yace '' zauna anan idan kin shiga dakin me za kiyi..?, zama tayi badan ranta ya so ba , kunna TV yayi ya kai tashar labarai BBC zaman da tayi ba ƙaramin takurata yayi ba , ko wanne motsi idan tayi tana jin idanuwan'sa a jikin ta , wayar sa ce tayi ringing ajiye chokalin hannun sa yayi ya dauka tare da ɗagawa yace '' Hisham dan Allah dan duba office dina Ka turo min takardun nan insha'Allahu gobe zan shiga shari'ar naga yadda zata kaya Allah ya bamu nasara da sa'a.., Hisham yace '' Allah ya temake ka ban fito ba yanzun nan nake shirin barin gurin nan nabar madam tana zaman kaɗaici.., girgiza kai Jawad yayi yace '' dan iska kai dai ba zata taɓa chanzawa ba maza dan Allah ka dauko min su ka turo min.., dariya Hisham yayi yace '' aini ba irinka ba ne ga nama ina gani, naiwa kaina ƙita amma insha'Allahu zaka faɗa cikin tarko..., da sauri ya kashe wayar yana jan ƙaramin tsaki idan ba maganin wannan dan iskan yayi ba , ba zai sarara mai ba. yaya bacci nake ji. Najlah ta faɗa tana kallon TV ganin ga a inda hankalinta yake sai yayi mata banza be kulata ba , wanne bacci karfe uku da kusan rabi. juyowa tayi har hawaye ya fara zubowa a kuncinta cikin shashsheƙa tace '' bacci nake ji.., okay lokacin sallah yayi zaki kwanta duk baccin da kikai ɗazu be ishe ki ba..?, cewar Jawad share hawayen ta tayi tace '' kwanciya nake son yi.., murmushi yayi yace '' good tashi ki kwanta.., tashi tayi har ta fara tafiya yace '' zo.., juyowa tayi ta dawo ta durƙusa tace '' gani.., dan jim yayi sannan yace '' jeki daki na ki dauko wata leda ki kawo min..., ƙasa tayi da kan'ta tace '' ina ne dakin naka.., da yake ita bata taɓa hawa sama ba. idan kika hau zaki ga wata baranda na facing dinki ki shiga ciki zaki ga daki.. tashi tayi tace '' to.., fara tafiya tayi har ta hau sama kallon ko ina take gwanin sha'awa gaskiya yaya ba ƙaramin kuɗi ne dashi ba gini yawa a ƙasar waje haka ta raya a zuciyar ta shiga gurin da ya kwatanta mata shi zaro ido tayi ganin ta a wani guri wannan shi ake kira da aljannar duniya shiga Cikin tayi ashe parlour ne sai wata kofa murɗawa tayi ashe toilet ne mai da kofar tayi ta rufe ta nufi daya kofar tana turawa ta leƙa zaro ido tayi ta shiga tana kalle kalle can ta hango ledar limshe ido tayi sosai kamshin room freshener da aka saka a cikin Humidifier ya birgeta daukan jakar tayi ta fito kawo mai tayi dai-dai lokacin da ya fito daga kitchen tsayawa tayi har ya ƙaraso cikin ladabi ta miƙa mai amsa yayi yana cewa sai yanzu kika ga damar kawo mini..? kai ta girgiza tace '' dakyar na gano dakin.., wani shu'umin murmushi yayi yace '' uhmm zama ki san shi ne.., kallon sa tayi cikin rashin fahimta sai dai be bata damar tambaya ba, sai ma haɗa rai da yayi ya zauna yana buɗe jakar yace '' ungo.., kallon takardun da ya miko mata tayi amsa tayi tana dubawa, takardar makaranta ce haka ta ayyana a ranta ganin rubutun da yaje jikin takardar yace '' gashi nan sun baki admission wata me kamawa zaki fara zuwa.., godiya tai mai har zata tashi yace '' nace miki na gama da ke ne..?, kaita ta girgiza yace '' okay ban da saka mayafi ko kayan ado hijabi ne har ƙasa da niqab da safa banda kula maza duk da nasan kina da hijabi na saka a dinka miƙi wasu insha'Allahu zuwa jibi zan kawo miki.., da sauri ta ɗago jin wannan fi'ili na yaya Jawad sai kace wata matar liman wannan kunshe kai yayi yawa a hankali tace '' yaya safa, fa da niqab wallahi shaƙe ni za su yi ga zafi.., haɗe rai yayi yace '' ni sa'an kine na kafa miki doka ki dinga fadamin ga zance ga magana to wallahi karki bi kiga yadda zamu kwashe dake a cikin gidan nan , wannan tsari na ne dole ki bi.., ajiyar zuciya ta sauke tace '' insha'Allahu zan bi.., yauwa ungo karɓa tayi chocolate ce daga gani me tsaɗa ce daman ita gwanar shan zaki, ba karamin farin ciki tayi ba da wannan chocolate din. tashi tayi tana murna ta shiga daki wanka tayi ta chanza pad, sannan ta saka kaya marasa nauyi kwanciya tayi ta dauko chocolate din da ya bata, ta fara ci a ko gama sha ba tai ba bacci ya fara ɗaukan ta. ajiyewa tayi dakyar ta matsar da wayar ta gefe ta kwanta lokacin an gama idar da sallar la'asar bacci ne me nauyi yayi a wan gaba da ita. dawowar sa kenan daga masallaci ya shigo yaga tana bacci zama yayi a gefen gadon ta , ya kura mata ido a hankali ya saka hannu ya matsar da gashin kanta da ta rufe mata fuska, shi sai yau, yaga kamar da ake cewa suna yi da ita . ko lokacin da yana makaranta abokanan karatunsa sun kawo masa ziyara suna ganin ta suka fara cewa Jawad ga copy dinka wallahi kuna mutukar kama da ita limshe idanuwan'sa yayi masu kama da me jin bacci tabbas JINI ƊAYA BA WASA BA. haka ya ayyana a ransa. gangaro da hannunsa yayi kan kirjinta ba ƙaramin shock yaji ba musamman da fatar hannun sa ta hadu da ta kirjinta. KARUWAN CIKIN GIDA EPISODE ⁸ https://www.youtube.com/@nasreenminallah Juyi za tayi da sauri ya dauke hannun sa tare da tashi tsaye ajiyar zuciya ya sauke lokacin da yaga bata buɗe ido ba ta koma baccin ta ja mata kofa yayi ya fita daga dakin kai tsaye part din sa ya nufa ba zama yayi tare da zuba uban ta gumi abubuwa da yawa ne suka hana shi sakat. daukan laptop din'sa yayi ya soma aikin sa domin tunanin da yake ya ragu....... amma ina kasa komai yayi dafa kansa yayi da ya soma sara mai matsar da laptop din tayi ɗaukan wayar sa yayi ya kai tsaye number jawaher ya kira har ta gama ringing din'ta bata dauka ba ajiyewa yayi sai gashi ta kira Muryar ta ƙasa ƙasa yawa tame maye wannan yanayi nata baƙaramin ƙara saka Jawad tayi ba cikin wani hali tace '' sweet heart baccin gajiya nake wallahi kaga jiki na duk yayi sanyi yakake NAJLAH tayi maka abinci ko restaurant kaje ka siya..?, hnmm beb ni yanzu ba abinci nake buƙata ba.. kirjin tane yayi wani irin bugu tashi zaune tayi tasan sarai halin mijin nata kar yace ta dawo gobe, kudi ba matsalar sa bane cikin kwantar da hankali tace '' beb me kake bukata.., Keeeee yaja karshen maganar. zaro ido tayi tace '' ka saka aranka ka riga ka samu ma..bara na kiran ka video call.., jawaher video call bazai amfanar dani komai ba sai ma ya ƙara tun zura ni.. my justice to kasha lemon tsami insha'Allahu duk abin da kake ji zai yi ƙasa. ajiyar zuciya kawai ya sauke yace '' to yanzu yaushe zaki dawo wallahi jawaher bazan iya jurewa ba.., gaban tane ya ƙara faɗuwa tace ''haba sweet me kuma ya kawo wannan maganar..?, ajiyar zuciya ya sauke yace '' sai anjima.., ya faɗa tare da kashe wayar bin wayar ta , tayi da kallo Alhaji kallon ta yayi yace '' me ya faru ya kira ki da wannan tsohon daren kamar besan ban bancin naija da turkiya ba..?, da sauri ta kalle sa tana mamakin halin alhaji karfa ya manta jawad mijin tane kuma ya na da ikon kiranta a ko wanne lokaci... bata ce mai ƙala ba ta , tashi tsaye fridge ta buɗe ta dauko ruwa me sanyi gorar sa har hazo hazo take yi ya kusan ƙanƙara balle murfin tayi ta kafa baki bata cire ba , sai da taga ba komai a ciki sannan ta cire jan dogon tsaki tayi tana miƙa jingina tayi da bango tayi shiru ganin yanayin da ta shiga alhaji ya matso kusa da ita kama lips din ta yayi kau da kai tayi tace '' Alhaji in har ba zaka cire tsanar da kake wa Jawad ba, ba shakka alakar mu tana shirin yankewa ina son mijina ya za a yi ka dinga nuna min baka son mijina nima din kenan ba sona kake ba akwai abin da kake so kana samu zaka yardar da ƙwallon mangaro ka huta da ƙuɗa.. JAWAHEER ni kike faɗawa wannan maganar..?, wani murmushin takaici tayi ta dauke kan'ta daga kallon sa da tayi tace '' wanne dare ne jemage be gani ba ....?.da har kake tunanin zan raga maka..?, tashi yayi ya zo har inda take yace '' DAREN MUTUWAR SA...., da sauri ta kalle sa tace '' me kake nufi da haka...?, kardai kwantan ɓauna kake min..?, ɗage kafaɗa yayi alamar owo miki.. rakiya tayi mai da ido har ya fita daga dakin tsaki tayi ta dauka kwalbar giya da ɗazu yayi musu oder ta , ta fara sha ba kakkautawa.. ************ TARABA STATE.. UMMEE ni gaskiya matata tane buƙata ke kirawo yaya yaje ya basu HAKURI tun da dai kin korar min beb ɗina.. da sauri Hajiya bilkisu ta kalle sa tana mamakin halin ALTAB kwata kwata bashi da kunya ƙasa magana tayi sai girgiza kafa tayi idanuwan'ta ya kaɗa yayi jaaa. cije lips din'ta tayi anya kuwa lamarin nan na ALTAB ba da sa hannun wannan BAKIN mugun me jikim hankaka fatar jikin sa fari , amma naman sa baki dole ta saka a gayyato mata malamai suyi mata abinci ke idan kuwa haka ne ƊAN BUZUU ya taɓo abin da yafi karfin sa.. UMMEE wai ba zaki rabu da mutanen nan ba su basa gaban ki amma ke kullum suna cikin zuciyar ki me ya saka zaki saka sharri ga alkairi kuma auren ki da ya mutu daman can Ubangiji ya nufa rabo nane ya fito dake daga gidan nan ni da bani da wani karatun addini amma nasan haka amma ke , karatun ki be miki amfani ba wallahi... *WALLAHI TAUSAYIN YAYA NAKE DA YAZO DAGA CIKIN TSATSON KI* hannnu ta ɗaga mai tace '' ya ishe haka haka jawad nace ya ishe haka tun kafin na faɗa maka wata bad magana ka fitar min daga cikin dakin nan shasha komai dan kai nake da ubanka ba wani bane.., dariya yayi yace '' wallahi bana bukatar Dukiyar haram ubana kuma da kullum kike rainawa alhamdulilah yana da nashi arzkin kina gidan wani amma kina kallon arzikin tsohon mijin ki......NIFA TRUE CE BAZAN FASA FAƊA BA wallahi..., pillowcase ta dauka zata jefa mai da sauri ya kauce yana fita da gudu daga cikin dakin nata.. dafa kan'ta tayi da yake tsananin sara mata daukan waya tayi tana kallon Luxury watch da yake manne a bango ƙarfe goma sha biyu na dare dogon tsaki taja ta rasa wannan wanne irin meeting Alhaji alee suke kamata yayi ace iyan zu kana cikin gidan ka , ba mamaki Saboda halin sa Ubangiji ya jarrabe su da yaro me halin ALTAB...SIYASA KO MUGUN WASA... haka ta raya a ranta da sassarfa ta hau stair case cin karo tayi da AFNAN..da sauri ta kalle tace '' AFNAN ina zaki cikin daren nan na ganki da shirin fita wannan liqab din fa...?, gaban AFNAN ne ya faɗi ta sauki ajiyar zuciya tace '' so nayi na tsorata ki fa nasan yanzu ina ƙasa kina jiran daddy.., tamkar an zuba mata ruwan sanyi haka yaji a cikin zuciyar ta , tace '' bana son shashancin banza zo ki wuce ai sai ki saka na fara wani tunani akan ki.., murmushi tayi tace '' haba UMMEE kamar baki san wacece ni ba , ina yaddar da kika bani..?, AFNAN zo ki wuce bana son jin wata magana.. jin taku suka yi a bayan su gaba ki ɗaya suka juya Alhaji alee ne yana rike da briefcase fuskar'sa ba wata fara'a kallo ɗaya zakai mai kasan yana cikin ɓacin rai cikin tsananin kaushin murya wacce ke bayyana ɓacin rai yace '' KI FAƊAWA ɗan ki bakin rijiya ba gurin wasan yaro bane idon kuwa yaki ba zai ƙi gani ba.., Alhaji kome ALTAB yayi be kamata mu juya mai baya ba.. hannu ta ɗaga mata yace '' ya ina zance kina juya min wani guri na dabam danƙi JAWAD nake nufi ya fita daga sabgar mu idan kuwa yaki zamu shafe shi a doran kasa wallahi.., Alhaji alee ni kake fadawa zaka kashe ɗana...?, UMMEE ta faɗa cikin tsananin zafin zuciya.. bece komai ya wuce ya barta da sakakken baki kallon kallo aka shiga tsakanin afnan da UMMEE. kasa cewa komai tayi daukan waya tayi ta soma laluben layin JAWAD kash tararwa tayi switch up tsaki taja tace '' tsiyar Jawad kenan ai ta kiran sa aban za ni ban ga amfanin wayar jawad ba.., UMMEE be kamata kuyi magana a cikin waya ba kawai gobe mu tafi Abuja sai ayi komai kya ma kori waccan shegiyar idan be mai da ta gidan su ba.. Good idea haka za ayi kin Kawo shawara me kyau..... tafiya tayi dakin ta sai sake sake take yi har bacci ɓarawo ya dauke ta batare da ta cire kayan jikin ta ba À bangaren Alhaji kuwa yana shiga ya cire babbar rigar sa sai wuci yake zama yayi akan gado yana girgiza kafa a yanzu babbar matsalar sa JAWAD idan be kawo karshen sa ba to lashakka shi jawad zai kawo nasa ƙarshen duk me son tono sirrin ka , wanda ka bunne tsahon shekara da shekaru baka so kuwa ya san shi ai maƙiyin kane.. babbar matsalar sa abin da boka yace yayi yana tunani akai anya kuwa zai iya , wayar sa ce tayi ringing da sauri ya daga yace '' wallahi Alhaji na kasa yanke ko wacce irin shawara wankin wula yana so ya kai mu RANA tun yaron nan yana yaro naso mu gama dashi tun da tun farko alamu sun nuna yar manuniya ta nuna shi ne zai zama tarnaki a gare mu amma kaki fahimtar haka.., haka zaka daure kayi ita da man duniya ba'a samun ta , ta cikin sauki, ka manta me muka yi a teluwar mu ta farko wannan ba wani abu bane ita siyasa idan kana so a dama dakai to zubar da jini kaci mushe aljanna ta me rabo ce... shiru yayi yana sauraren sa sai kuma yace '' to zan gwada na gani.., wanda ya kirawo yace '' yauwa ko kai fa haka ake so.., sallama yayi mai ya kashe wayar sa... OSOKORO ABUJA.. tashi tayi tana zare idanuwa ji tayi an ƙara knocking kofar ta gaban tane ya ƙara faɗuwa bakin ta na rawa tace '' wane..?, JAWAD yace '' ki haɗa min coffee ki kawo min.., da sauri ta kalli agogon da yake banne a jikin bangon dakin ta , 1:00 tashi tayi tamkar an zare mata laka tace '' to.., saka hijabinta tayi har ƙasa ta buɗe kofar yana sanye da fararen kaya pyjamas tana sanye da medical glasses duk da shigar bacci ce kayan ba karamin amsar sa sukai ba.. dauke kai tayi daga kallon da tai mai na yan mintoci tace '' za'a saka maka sugar a ciki.., zuba mata ido yayi tamkar wanda zai cinye ta , yace '' in zaki iya dauka ta ...da sauri ya canza akalar zancen da cewa a'a ba sai kim saka ba.., kai kurum ta gyada mai batare da ta fahimci katoɓarar zancen da ya so yayi ba.. hawa saman sa yayi ya zauna yana jiran ta shiru shiru bata shigo ba tashi yayi domin yaje yaga ko lafiya cin karo yayi da ita, ta jinginar da kan ta a bangon part din nasa ga tray din tea a gaban ta , ta fara bacci kura wa announce baby face dinta ido pink lips din ta har wani sheƙi yake dan ƙarami abin sha'awa da sauri ya kau da fuskar sa tare da tsugunawa a hankali yace '' NAJLAH NAJLAH NAJLAH.., da sauri ta tashi tana mustsuka idon ta , tace '' kayi hakuri na buga ne naji kamar kana toilet shine na zauna idan ka fito na ƙara bugawa sai nayi bacci.., kai ya girgiza yace '' me makon ki shigo kamar ba mallakin ki ba.., da sauri ta kalle sa tana nanata kallamar mallakin ki, ita awa ko yana nufin tun da shi ɗan uwanta ne komai nasa nata ne nata nasa ne ehmn haka yake nufi ba wani abu ba ta raya wannan a zuciyar ta tashi tayi tace '' gashi nan bacci nake ji.., ke wai bakya gaji da bacci...? ɗazu ba kinyi ba maza zo ki taya ni hira sai ki tafi ki kwanta.., marairaice fuska tayi za tayi magana ya ɗora hannun sa akan lips din sa yace '' shiiiii bana bukatar jin komai daga gare ki...., ba yadda ta iya haka tabi bayan sa suka shiga ciki zama tayi a kasan carpet akan gado ya zauna yace '' tashi daga kasan nan zo ki zauna anan.., ya faɗi haka yana nuna mata gado.. jikin tane ya fara rawa ganin yadda yayi maganar alamun baya son raini tashi tayi ta zauna nesa dashi shan coffee ya fara hankalin sa kwance... buɗe wani kwali yayi ya dauko chocolate ya miƙa mata guda uku amsa tayi tana mai godiya ta riƙe su juyowa yayi yace '' ki sha mana ajiyar me zaki yi musu...?, NAJLAH tace '' nayi brush..., sai kuma aka ce idan anyi ba'a kara yin wani kome..?, ya tambaya yana kafe ta da idanuwan'sa masu kama dana mejin bacci na yadda ta iya haka ta buɗe ta fara sha bacci na fusgarta me uban nauyi har kuma yaci karfin ta, kwanciya tayi ya juyo domin yayi mata magana sai yaga tayi bacci.. ajiye coffee din sa yayi da yake ya gama sha gyara mata kwanciyar ta yayi tare da cire mata hijabin da ta saka kayan bacci ne a jikin ta doguwar riga ce me net iya kan mazaunan ta da kirjinta nan ne kawai ba net amma kan cikin ta duk net ne ba abin da baya gani hannun sa ya saka ya zagaye Cibiyar ta dashi Allah sarki NAJLAH bata san me yake faruwa ba.. baccin ta take cikin kwanciyar hankali... KARUWAN CIKIN GIDA EPISODE ⁹ https://www.youtube.com/@nasreenminallah Cire hannun sa yayi ya janyo blanket ya lulluɓa mata tare da yi mata addu'a tashi yayi ya shiga toilet wanka ya ƙara yi sannan ya dauro alwala ya fito shinfiɗa daduma yayi , ya tada kabbarar sallah bayan ya idar ya dade yana kaiwa Allah kukan sa daukan Alkur'ani me girma yayi yana karantawa sai da yaga ƙarfe biyu da rabi tayi sannan ya rufe tare da ajiyewa a inda ya dauko shi dauke prayer mat din yayi ya ninke ya ajiye ta a cikin wardrobe.. zama yayi a bakin gado yana kara janyo blanket domin ya rufa mata rufen da yayi mata ɗazu ta cire kamar wata ƙaramar yarinya yan dogon tsaki yayi , ya rasa ma yake damun sa shi dai kawai gashi gashi nan ne. ƙasa riƙe kan'sa yana ji indan be rage damuwar sa ba bazai iya bacci ba duk abin da yayi domin ya guji shiga wannan yanayi amma abin yaci tura... Allah ya gani ba shi da yadda zai yi kuma ba ta haramta a gare sa ba. zame rigar ta yayi tuni breast din'ta ya bayyana hakan ba karamin gigita shi yayi ba ashe zaton da yake musu sun fi haka , tamkar wani yaron goye haka ya dinga shan su, a duniyar NAJLAH gani take mafarki take yi tsoro ne ya kamata gashi ta kasa buɗe idanuwan'ta saboda baccin da ya saka barin jikin ta radadi da zugin da suke mata ya wuce sanin ta a hankali ta fara kuka tana matsar da kan'sa. tausayin tane ya kama shi ya ɗauke kan sa daga kirjin ta kura wa nipple din'ta idon sa yayi, yayi jajir breast ɗin ta ya kumbura tausayin tane ya ƙara shigar sa mai da mata dasu yayi tare da gyara mata kwanciya.. ya fita ya bar dakin ya kuma parlour toilet din da yake parlour sa ya shiga yayi wanka sannan ya fito ya shiga dakin sa ya chanza kaya ya dawo parlour ya kwanta a kujera tamkar ba abin da ya faru... kiran sallar asubar farko a kunnuwanta a hankali ta buɗe idon ta da yake mata nauyi amma ina ta saka buɗe sai bacci da ya ƙara fusgar ta.. bata da wani zabi da ya wuce tayi baccin jikin ta ba kwari tun da ba sallah za tayi ba . A bangaren Jawad kuwa tashi yayi wanka sanna yayi sake kaya ya tafi masallaci be dawo ba sai da gari yayi haske sannan ya dawo shigowa dakin yayi hasken da ya shigo ta cikin window fararan curtain din da suke dakin suna ɗagawa abin ka da sanyin safiya rangajin da bishiyu ke yi suna bada iska me tsayi ita ke ratsa cikin dakin har take daga curtain din hasken ne ya doki idon ta a hankali ta buɗe shi a yanzu baccin ya sake ta fas ta buɗe idon tare da ɗora su a kyakkyawar fuskar Jawad da yake shugowa cikin dakin yayi shirin sa , da alama ba kamar aiki zai fita da sauri ta tashi zaune ƙasa tayi da kan'ta duk kunya ta kamata, gadai hajabin ta a jikin ta amma ai ta tabka abin kunya a kan gadon yayi ta kwanta tasan sai dai ya tafi parlour ya kwanta bakin na rawa tace '' ina kwana yaya.., batare da ya kalli inda take ba yace '' lafiya qalau.., ya faɗa yana buɗe wata kofa bin bayan sa tayi da kallo da sauri ta ,tashi tsaye cikin hanzari ta , fita daga cikin dakin baki ɗaya kallo ɗaya tayi wa wata luxury bed sofa da take parlour taga blanket kenan anan ya kwana.. to ai wannan bata da maraba da gado ta faɗa a hankali tare da dan gudu tabar dakin baki ɗaya saukowa tayi gaban tane ya faɗi ganin Hajiyar Jawad da kanwar sa AFNAN sai hura hanci suke suna kalle kalle lokaci ɗaya suka ɗago idanuwan su, suka kalli NAJLAH da take saukowa cikin hanzari duk kan motsin da za tayi sai albarkatun kirjin ta sun motsa haka kugunta da mazaunan ta yawa da gayya take haka cikin tashin hankali UMMEE ta buɗe baki tace '' kuttumar ubancan ke yar gadon munafurci daman kina cikin gidan nan , salon karuwancin da aka koya miki ki ɓata min tarbiyyar ɗana to wallahi daga yau kin bar kwana a cikin gidan nan dan uwar ki.., wannan kalamai da UMMEE tayi ba ƙaramin daga mata hankali sukai ba , bata tsaya tantance me yake shirin faruwa ba taji afnan ta fusgo ta ta cire mata hijabin da yake jikin ta. ta kurewa tayi bakin ta har fashewa yayi dai-dai lokacin jawad ya sauko cikin tsananin ɓacin rai ya miƙawa NAJLAH hijabin ta , tare da kifawa AFNAN mari yace '' daman ashe baki da mutunci sa'ar kice da zaki kiyi mata haka..?, ba shakka sun ruga da sun shanye ka tun da akan wata yar karuwa kake cin zarafin yar uwar ka to wallahi idan kai sun shanye ka ni karya suke karyar HAJIYA FARIDA wallahi.. kuka Najlah ta fashe dashi wannan wacce irin rayuwa ce haka UMMEE kama hannun AFNAN tayi tace "'farida ta shanye shi zo mubar masa gida ina mahaifiyar ka ban isa na saka ba balle hanaka Allah ya isa tsakani na dake farida kuma inhar ni na durkusa na haife ka , jinina ke yawo a jikin ka ka mai da wannan yar karuwar gidan su salon iya karuwanci ya saka ta kasa barin yarinyar tayi karatu a gaban ta sai ta kai ta wani guri domin taji dad'in watsai wa wallahi duk sai nayi maganin su ita kuma shasha ta kama hanya ta tafi can wata uwa duniya tabar wannan yarinyar agidan ta sai tayi mata sakiyar da ba ruwa.., buɗe baki yayi zai magana UMMEE tace '' inhar bakai abin da nace maka ba to kar ka ƙara yi min magana..gidan ka kuma nabar maka shi ban da nayi Wa wa'yannan ƙedarayen rashin mutunci ai hanani sukai na shigo kai kuma ka saka ni a black list Layin a kashe sai na da kirawo wannan yarinyar tace ta tafi uwar ta haɗa kayan daki akwai haɗa kayan dakin da ya wuce ki zauna a gidan mijin ki al wallahi jawaher ban za ce kwata kwata bata da hankali bata dauko halin uwar ta ba..., tafi haka suna barin parlour rasa inda zai saka kan sa yayi wannan wanne irin kalami UMMEE ke fadi ko kunyar idon NAJLAH bata ji ba tana jifan Hajiya da karuwa matar da iya mace kamila me addini ta kai.. tashi najlah tayi wani irin radadin kirjinta ke mata ga wannan damuwar ummin JAWAD ita da zai kai ta gida da tafi kowa jin dad'i wallahi.. dakin da aka sauke ta ta shiga tana shiga ta faɗa toilet cire rigar jikin ta , tayi kurawa kirjinta ido tayi, yayi jajir kan nipple din'ta ya yi tsayi kai hannu tayi ina kasa taɓawa tayi to ko ba mafarki take ba me jiya ya faru da ita aljanu wata zuciyar'ta, ta faɗa mata haka gaban tane ya fadi jin wannan kalamar aljannu ai bata san lokacin da ta rushe da kuka ba tare da ɗora hannu aka ta zun duma uban ihu Jawad da yake parlour tamkar an dasa shi ya rasa takameme tunanin da zai yi ya jiyo kukan ta.. da sauri ya shigo dakin sai dai be tarar da ita ba, motsinta ya ji a toilet da sauri ya shiga ganin sa da tayi ta saurin saka hijabinta tare da kara fashewa da kuka rungume shi tayi tana kuka tana cewa dan Allah yaya ka mai dani gida wallahi bazan iya zama a nan gidan ba.., kamo ta yayi suka fito zaunar da ita yayi akan gado yace '' kiyi hakuri da abin da UMMEE tayi ko da wasa kuma kar inji wannan maganar a gurin wani.., kai ta gyaɗa mai ta ci gaba da shashshekar kukan ta. baki da baki ne kika tsaya yi min kuka me yake damun ki ko faduwar da kika yi kin ji ciwo..?, ya tambaye ta cikin kulawa.. girgiza kai tayi tace '' gidan nan akwai aljanu.., hade rai yayi yace '' bana son iskancin banza wanne aljani kuma..azan zaune kalau.., kan'ta ta kifa akan gado tana kuka daman tasan ba lallai ya fahimce ta ba cikin muryar kuka tace '' wallahi akwai aljanu jiya nayi wani irin mafarki yau na tashi kirjina nayi min ciwo sosai kuma duk sun kumbura.., tuni ya dauki hasken abin da yake faruwa kenan ta gane da yake chocolate din da tasha ta bacci ce dan haka take zargin akwai aljanu a gidan bawai realty a bin ya faru ba... tausayin tane ya kama shi dagota yayi yace '' ki dinga addu'a idan zaki kwanta muga me yafa ru a kirjin naki ko na kirawo me kamun kirji ne..?, Jawad ya fadi haka yana kallon ta cikin tsantsar kulawa.. goge hawayenta tayi tace '' wallahi ina yi.., to ki da ɗa mu ga kirjin naki..?, tashi tayi ta rufe fuskar'ta da tafukan hannunta tace '' a'a ba sai ka gani ba..., tashi yayi yace '' okay Allah ya kiyaye gaba ki gasa jikin ki da ruwan zafi komai zai war ware insha'Allahu.., kai kurum ta gyaɗa mai fita yayi ita kuma ta shiga toilet yadda yace tayi haka tayi bayan ta gama tayi wanka ta fito shafa mai tayi sannan ta saka kaya English wears ne riga t-shirt fara tas sai adon flowers pink colour da yarfin blue sai wando falazo pink colour an mai adon flowers white and blue kamar yadda adon rigar ta yake tubke kanta tayi da yake akwai kabbasa a jikim su bata fesa turare ba sai humra da ta saka ta shafe jikin'ta da ita stocking tayi ta saka hijabi har ƙasa ta fito yana zaune a parlour zama tayi a dan nesa dashi tace '' me zan dafa...?, ba tare da ya kalle ta ba yace '' duk abin da kika yi niya ki dafa mana.., yaya kar nayi kaki ci.... fa ta faɗa tana wasa da yan yatsunta.. wani kallon kasan ido jawad yayi mata yace '' ya za'a yi naki ci bani nace kiyi ba..?, muje na taya ki.., tashi tayi tsaye tayi tace '' a'a ka barshi zanyi.., me kike ɓoyewa ne naga kika turo hijabi gaba..? Jawad ya fadi haka yana kafe ta da idanuwan sa.. gaban NAJLAH ne ya fadi ta shiga uku kar dai ya gane bata saka bra ba ina ita ina sakawa kirji na ciwo.. bakin ta na rawa alamar rashin gaskiya tace '' aah bakomai.., okay to fito da hannun ki na gani..., ya faɗa yana kara jifanta da wani irin kallo me cike da ma'anoni kala kala.. ba tare da wani tunani ba ta fito da hannun ta ji tayi ya fusgo ta tare da cire hajabin ta , ya ajiye a ƙasa yace '' daga yau karna ƙara gankn ki da wannan bargon bana son salon munafurci tamkar wata munafuka ki dinga sim sim da hijabi kina turo shi gaba inda ba , baki mukai ba to dole ki zauna a cikin gidan nan ba hijabi.., rintsai ido tayi jin wannan maganar sa kuka ta saka ta fusge jikinta daga nasa ta shiga daki wayar ta , ta dauko ta lalubo number aunty Hafsah bugu ɗaya ta dauka fashe mata da kuka tayi tace '' aunty wai yaya ne yake ce min be yadda na dinga saka hijabi ba a cikin gidan na dan Allah ina ruwan sa da hijabi na , sho komai sai ya takurawa mutum kuma wallahi gidan nan akwai aljanu masu bin mutum cikin dare wallahi ba karya nake ba shima cewa yayi na dinga addu'a..., Dariya zancen ya bawa aunty Hafsah tace '' look NAJLAH gidan sane fa, yana da iko ya saka miki doka kibi, kuma karki manta matsayin da yake da shi a gurin ki dan haka kiyi kawai abin da yace ku zauna lafiya ke waya faɗa miki akwai aljanu a cikin gidan kinga NAJLAH ki kiyayi kanki da irin wannan chamfi ɗin dan bakya son zama a guri sai kice akwai aljanu..., Kuka ta saka tace '' wallahi akwai jiya nayi mugun mafarki yau na tashi kirjina a kumbure kuma ciwo yake min sosai ko rigar ciki bana iya sakawa..., Da sauri aunty Hafsah ta tashi zaune tace '' sannu Allah ya kiyaye gaba amma dai ki dage da addu'a irin haka har aurar mace suke, su dinga mu'amalar aure da ita sannan ki dage da shan fruit sai kuma ki dinga hada kankana ki markade ta ki markada dabinan ajuwa sai kwakawa da marada karki saka sugar ki saka zuma...ki dinga sha Insha'Allahu komai zai zama tarihi zaki sha mamaki.., Aunty Hafsah ba addu'a sai cin wannan abubuwan shi mene amfanin cin su ko aljanin baya son sune...?, dariyar da take cinta ta danne tace '' ina kuwa aljani yake son fruit baya son da ko kaɗan yauwa ko dage da addu'ar neman tsari daga abokan gaba sai kuma ki ƙara rike azkar ba wanda ya isa ya cutar da ke yauwa na manta zan aiko da miski ki dinga amfani da shi kisan basa son shi a gaban ki zaki dinga sakawa dan kadan ko a cikin pant din ki sannan zan aiko miki da sanferar lallai da ganyen magarya idan kika gama period ki tafasa su ki dinta shiga ciki..., ba tare da dogon tunani ba tace '' Insha'Allahu zan kiyaye... amma kar ki faɗawa yaya kawai dai ki bashi ya kawo min ina yarona yake.., aunty Hafsah tace '' to uwar kunya bazan faɗa mai ba ...yana bacci har yanzu be tashi ba.. uhmmm to ke yanzu sai ki iya faɗa mai komai gaskiya yana hutawa da yawa irin wannan bacci haka ta ƙarshe maganar cikin shagwaɓa.. aunty Hafsah tace '' to mene a cikin ido ban da ruwa, wani karatun ma sai ya zo sai na karanta mai ya karanta miki zaki fi ɗaukan nasa.. a'a wallahi bana so na yafe kai aunty hafsah cewar Najlah dariya aunty Hafsah tayi bata ce komai ba NAJLAH tace '' to sai anjima ki gaisar min da kowa ina anni problem.., aunty Hafsah tace '' gidan ku NAJLAH maman tawa kike fadawa haka..?, dariya tayi tana kashe wayar ajiyewa tayi ta tashi toilet ta shiga ta wanke fuskar'ta sannan ta fito bata tarar dashi a parlour ba , hakan ba karamin dad'i yayi mata ba , shiga kitchen tayi ta soma, kirga musu farfesun jelar sa, saci da bread tun da yace tayi abin da taga dama to wallahi wannan za tayi.. rage wutar gas tayi ji tayi a jikin ta kamar ana kallon ta da sauri ta juyo gaban tane ya fadi bakin ta ya soma rawa ta irin kunyar sa taji wai me yasa ya jawad ya zama haka ne daga shi sai short boxer duk wata halitta ta jikin sa ya fito masa da ita komai a fili yake gashi ba riga a jikin sa gashi ne kwance a kirjinta dantsai hannun sa duk a murɗe yawa wani dan dambe........ Ja da baya tayi a hankali tace '' ke lafiyar ki ki kula zaki bari.., kai kurum ta gyaɗa mai tana ja da baya ransa ne ya ɓaci yace '' ba magana nake miki ba.., ya fada yana kafe kirinta da kallo domin fa sharin nipple dinta rada rada ya fito komai ana ganin sa.. kai ta girgiza mai tace '' bakomai wallahi kayi hakuri.., dafa kan'sa yayi yace '' wai ke bakya gajiya da laifi haka bakya gaji da bada hakuri oya zo kashe girkin nan.., jikin ta na rawa ta kashe tamkar rakumi da akala haka ta bishiii ganin za su hau sama, ta chake a stair case tace ''' yaya ina zamu...?,, Gidan yankan kai ya bata amsa yana kallon ta.. ƙasa tayi da kan'ta tabbas jawaher ta tafi ta barta da , tashin hankali wai anya kuwa ba chanzawa yaya dabi'u tayi ba...yaya da ko da gajeran wando baya iya fita balle har ya yarda su gansa bin sa tayi a baya suka hau saman kai tsaye dakin sa ya shiga itama bin bayan sa tayi yace '' maza ki gyara min daki, kin kwanta saboda tsabar ƙazanta kin tafi kin barsa a haka..., ajiyar zuciya ta sauke ta soma gyara shi yana zaune duk inda tayi ya bita da kallo ranta ne ya yi masifar ɓaci ta lura dai yaya ya zama dan iska to in ba Dan iska ba ina ruwan sa da bin jikin ta da kallo ko kallon JAWAHEER yake mata ne to ai basa kama ko a fuska balle a jiki... gamawa tayi ta wanke mai dukka toilet din sa ta saka turaren wuta, sannan ta zauna tace '' bayan wannan akwai wani a bu da zan maka...?, zaro ido tayi ganin abin da ya miƙo mata amsa tayi kasa ce mai tayi me za tayi mai da wannan shaving cream din ganin yadda lokaci ɗaya ta firgita sai abin ya so ya ba shi dariya NAJLAH bata da wayewar jawaher... lokaci ɗaya ya ayyana haka.. a ransa a fili kuwa sai yace '' za kiyi min aski ne .., yaya wallahi Allah ban iya ba NAJLAH ta faɗa tana saka hannun ta a baki alamar da gaske take bafa ta iya ba.. wani miskilin murmushi yayi yace '' wa yake miki naki shaving din.., da sauri tace '' eeeeehhhh..., Jawad yace '' uhmmm ai nasan kin ji abin dan nace.., wani yawo ta haɗiye kwana daya kan nabiyu a gidan yaya Jawad amma komai yana shirin rikice mata ja da baya tayi tace '' dan girman Allah kayi hakuri wallahi Allah ba zan iya ba.., jawaher ke min tun da bata nan ke sai kiyi min... bani number ta nayi mata waya ta dawo sai tayi ma ka bara na sauka ƙasa na dauko waya ta ta faɗa tare da tashi tsaye kafin ta isa kofar da zata fita daga parlour sai ta neme ta , ta rasa painting dakin ya saje da ko ina ba alamar kofa ko tsagar da zata nuna mata kofa farin kwan da yake a dakin sai ya maye gurbin dark green wanda yake ta walwale yana kawowa yana daukewa ya kawo blue Black sai ya kaso dark green.. da sauri ta ɗaga kan'ta sama sai kuma ta kalle sa tace '' yaya ka buɗe min kofa ba dauko waya ta babu kofa fa..., Yan aljanna ku taya ni nemo wa Najlah kofa.. Wannan littafin na kudi ne duk meson 1k amina alhasan Muhammad 8141785374 opay KU TURO DA SHEDA TA WANNAN NUMBER 08141785374. Yan niger 1000fcfah AMINA MUHAMMAD ALHASAN KANO My nita sai kuyi screen shot Ku turo ta wannan number 08141785374 Ina sanar muku akwai complete document na dukka littafin nan 1:.JIKAR MAMMAN COMPLETE DOCUMENT 1K 2:.HAUWA KULU WOMEN LEADER COMPLETE DOCUMENT 500 3:.DESTINY LOVE 400 4:.BINTA YAR JAGALIYA COMPLETE DOCUMENT 300 5:.YAR HANNU A LAGOS 1K 6:.GIDAN MAGAJIYA Complete document 1k 7:.UWAR GAFALALLU COMPLETE DOCUMENT 1K 8:.BAƘIN SHAFI 1K COMPLETE DOCUMENT 9:.YAN ZAMAN MAKKAH 1K COMPLETE DOCUMENT 10:.MU ZUBA MU GANI COMPLETE DOCUMENT 200 11:. KIN CUCE NI 300 Dan Allah idan kinsan ba siya za kiyi ba karki yimin magana duk maganar da za kiyi idan ba receipt evidence na gani ba bazan amsa ba dan Allah mu kiyaye Number iya WhatsApp take yi 08141785374 ban da kira KARUWAN CIKIN GIDA EPISODE ¹⁰ https://www.youtube.com/@nasreenminallah Wani kallo ya jefe ta dashi sai kuma ya danna remote farin haske ya maye gurbin blue da green yace '' ga chocolate din ki can dauki kayar ki , ki fita.., da sauri ta juya tace '' tana ina..?, bed side lamp ya faɗa a takaice. hango ta tayi can sai kuma tace '' to.., zuwa tayi ta dauka sauran guda biyu ta zo gaban sa ta tsuguna tace '' na dauko buɗe min kofa.., a bude take da sauri ta kalle sa jin abin da yace zai kuma ba tayi musu ba , ta tashi ta isa gurin kofar ihu ta saka tare da barin gurin ba shiri tace '' wallahi yaya shocking kofar take zo ka taɓa kaji wayyo Allah na shiga uku wallahi yunwa nake ji.., wani kallo yaje feta dashi yace '' inzo na taɓa naji tunda ke kinji ba shikkenan ba idan kin ga ba zaki iya fita ba ga , guri nan zauna ai ba turke na kafa miki ba..., hawaye ta share tace '' yunwa nake ji.., dauko laptop dinsa yayi yana dannawa yace '' ga fridge nan akwai snacks da milk sai ki dauka.., ba yadda ta iya ta bar gurin hawaye nabin kuncinta budewa tayi ta dauko cake guda uku sai fresh milk zama tayi ta fara ci tamkar wacce akai wa dole sai taci haka ta ke ci a hankali har ta gama ajiye kwalin fresh milk tayi tace '' yaya yaushe za ka mai dani Yola kaga ummi tace ka , mai dani gida sai na koma gidan yaya aliyu ko gidan su yaya muneef nayi karatun.., tun da ta fara zancen ta ya kafe ta da idanuwan'sa har ta gama haka kurum Maganar ta , ta taza memai tamkar ta watsa mai ruwan zafi bece mata komai ba ya mai da hankalinsa ga laptop din'sa kiran JAWAHEER ne ya shigo mai accepting yayi da yake video call ne dariya tayi tace '' Hy sweet heart good morning..., murmushi yayi ya jingina da bayan kujerar da yake zaune yace '' hy good morning how are you feeling today..., martanin murmushin sa ta mayar mai tace '' I'm feeling great today yaya kewata kayi da yawa ko kaɗan wallahi yau dakyar nayi bacci saboda baka kusa dani.., takarseh maganar ta cikin shagwaɓa NAJLAH da ta kusan sandarewa saboda mamaki kasa kunne tayi domin jin me zai ci duk da yana magana a hankali sai ka saka kunne sosai sannan zaka ji matar da ta saka kafa ta , bar cikin gidan ta da sunan raka kawa siyaya ita ke cewa batai bacci ba Saboda gata yarinyar goye meshan nono ba ta iya rayuwa idan bashi ba.. Jawad kuwa bata ji me yace mata ba sai jin dariyar tayi tana cewa abincin ka yayi kewar ka kalli yau ba wanda ya shashi.. wallahi ganin ka da nayi dan baka ji ba yadda breast dina ya soka min.. da sauri Najlah ta ɗago kan'ta dai-dai lokacin da shima ya ɗago ido suka haɗa takaici ne ya tokare zuciyar NAJLAH shikkenan yaya shima ya zama ɗan iska wata uwar harara ta gallamai tare da murguda baki tare da jan tsaki tace yan iska juyawa yayi taga yayi magana kome yace owo ya rufe laptop din sa , ganin yana nufuta da sauri ta , tashi tsaye kirjinta na dukan uku uku tace '' ba daku nake ba subbutar baki nayi.., are you sure..? kai ta gyaɗa mai ta kasa magana.. murmushi yayi yace '' okay ni sa'an wasan kine yan iska ko..? kema yau zan koya miki kinga sai mu zama yan iska uku wato kina gani na ko da yaushe shine har kikai min wannan rainin da zaki harare ni ko faɗa mana magana ni da matata.., kuka ta saka tace '' dan Allah kai hakuri bana so wallahi ba kyau jadda ma yace duk me yi Ubangiji yana fushi dashi haka ma aka faɗa mana a islamiyyar mu..., wani kallo ya jefe ta dashi, yace '' au Allah..?, mai maita abin da kika ji jawaher ta ce.., da sauri ta zaro ido tace '' wallahi ba zan iya ba., au kina so kenan muyi ya fadi haka yana tsare ta da idanuwan'sa zama tayi tana kuka tace '' a'a dan Allah kar kayi... cewa tayi kirjinta na ciwo saboda rashin ka.., da sauri ya kalle ta yace '' haka kika ji..? hawaye ta share ta daga mai kai rigar'sa ya fara ƙoƙarin cirewa da sauri ta zunduma ihu tace '' wallahi haka naji tace.., OKAY tashi ki fita.. tashi tayi da sauri tana kuka nufi kofar bude wa tayi ta fita tana ci gaba da kuka ta rasa wannan wacce irin rayuwa ce ta shigo ta , tana neman rasa mutuncin ga aljanin dare da jiya, ya azabtar da ita a parlour ta zauna tana share hawayen ta. tashi tayi ta shiga daki kulle dakin'ta tayi ta kwanta bata ƙara sauraran girki ba , bata farka ba sai karfe biyu shima bugun da yake mata shi ya farkar da ita da sauri ta tashi tana mustsuka idanuwan'ta saka hijabinta tayi ta wanke fuskar'ta ta buɗe kofa ta ɗan leƙo kan'ta ganin sa da manyan kaya tamkar wani shehun malami sai abin ya bata dariya yawa ni haɗe girar sama data ƙasa ita kuma aunty JAWAHEER irin kaddarar ta kenan ko da yake ai taga baya mata masifa ba zato taji yace '' idan kin gama kallona sai ki fito.., sosa ƙeya tayi ta turo baki gaba tace '' to ina kai ne ka hana ni fitowa ka tare kofar.., okay ni na hana ni fitowa ko..? ganin yana ƙoƙarin shigowa da sauri tace '' a'a bara na fito to matsa.., yace za ki iya buge ni ki wuce.., ƙasa tayi Da kanta zuciyar'ta na tsananin bugu. turo dan ƙaramin bakin ta tayi tace '' kayi hakuri ka matsa min ni ba zan iya buge ka ba.., matsa mata yayi tana fitowa daga corridor din dakin ta tayi turus ganin naki mace da mijin ta sai yar su. kallon sa tayi tace '' yaya baki kayi ne..?, JAWAD yace '' a'a ban sani ba..., hmmm kawai tace ta ƙarasa sallama tayi da sauri suka juyo tare da amsa mata sallamar'ta durkusawa tayi ta gaisheni su, suka amsa cikin sakin fuska matar tace '' a'a tashi kanwata wallahi san tana kama da kai wannan ita ce copy dinka a komai bata barka ba wallahi Masha Allah kamar kai kaki ka zubar.., a zuciyar NAJLAH tace '' to dan muna kama ai ba halin mu ɗaya ba.., Hisham yace '' wallahi kuwa koni farkon gani na da ita da nayi dana je YOLA wallahi naga kamar su., tashi tayi ta shiga kitchen ta barsu suna hirar su. ɗaukan tray tayi ta zuba snack sai lemo ya ajiye musu komawa tayi ta ƙarasa farfesun da take ta yi diban nata tayi takai musu godiya sukai mata matar tace '' sannu mun saka k hidima.., Murmushi kawai NAJLAH tayi JAWAD kuwa tamkar baya gurin yana ta danna wayar sa yarinyar nan na kan cinyar sa Hisham ne yace '' wai ina Madam take ne..?, JAWAD yace '' tayi tafiya ne.., dariya yayi yace '' Allah ya dawo da ita lafiya idan kunyi waya ka faɗa mata mun zo yi mata ta ya jiki kenan kafar tata har ta samu sauki..?, Eh wallahi NAJLAH barin wajen tayi tana taɓe baki shiga toilet tayi ta yi wanka ta chanza pad. fitowa tayi daure da toilet tana tsane kan'ta ya shigo da sauri ta saka hijabinta yace '' ke wai baki iya tarbar baki bane kin tafi kin barsu..?, Ƙasa tayi da idon ta , tace '' gani nayi ba gurina suka zo ba, kayi hakuri bara nayi saka kaya sai naje.., kafe ta yayi da idanuwan'sa yana jefan ta da wani irin kallo ja da baya tayi ganin irin kallon da yake mata ta turo bakin ta ranta duk ba dad'i ta ita bata san wannan kallon wallahi.. matsuwa kusa da ita yayi yace '' ni kike wa kananun magana ko..?, da sauri ta girgiza kan'ta tace '' wallahi ba abin da nace yaya kai hakuri.., ta fadi haka a tsora ce domin tsoran yaya JAWAD ya ƙara shigar ta, ga halin muguntar sa ga wannan kuma sabon halin nasa ko lokacin da take gida idan yaje irin wannan kallon yake jifan ta dashi, ta rasa dalilin sa na yin haka ko su basma baya musu haka ita din ce dai katsai mata tunani yayi da cewa kefa nake jira kin tsaya tunanin da ba zai amfanar dake komai ba Ya Allah yaya JAWAD yawa me gani har hanji haka ta raya a zuciyar ta afili kuma sai tace '' to ka fita zan saka kayana..., wani kallo yayi mata yace '' ba zan fita ba zo ki fitar dani idan har kin matsu na fita.., da sauri ta kalle sa tace '' yaya kaya fa zan saka .., wani kallo ya jefe ta dashi da sauri ta hadiye sauran zancen ta tana ci gaba da ja baya so taka ta yi wuf ta shiga toilet idan ya gaji ya fita sai kace wata yar iska zata saka kaya a gaban sa idan shi yana ganin ba wani abu bane to ai ita tana da kunya... **** ɗaukan kayan ta tayi , ta shiga toilet da gudu tana dariya shima abin dariya ya bashi ganin yadda ta faki numfashin'sa ta dauki kayan ta, ta shiga toilet saka kayanta tayi ta fito tana rara gefe. haɗe rai yayi yace '' zo ki wuce tun da kin riga kin aikata a bin da kikai niya.., bata ce komai ba, ta fita. bin ta yayi a baya har suka isa da sauri mubeena ta miko mata hannu amsar ta tayi tana cewa aunty ya sunan ta.. ai nayi fushi bakya so muyi zuminci ko tambaya ta sunana baki yi ba ,balle akai ga exchange number. zama tayi tace '' kaina bisa wuya na kiyi hakuri yanzu dai fara faɗa min sunan yar tawa.., Matar Hisham tace '' mubeena.., Murmushi NAJLAH tayi tace '' Masha Allah, Allah ya yara mana ita..to aunty ya sunan ki..?, safeera.. Masha Allah ni kuma NAJLAH. ta faɗa tana jan kumatun ta tashi tayi ta shiga daki dauko wayar ta tayi ta buɗe wardrobe din ta shopping da abba yayi mata da zata tawo ta buɗe ta dauko turarurruka guda uku sai turaren kabbasa da aunty rafi'at ta bata da yake tana aure a Maiduguri to shi ne ta fara sana'ar saida turare ta zuba a wata jaka me kyau ta fito miƙa mata waya tayi tace '' ungo saka min number ki.., amsar wayar tayi ta saka mata tayi Flashing itama ta , yi saving number ta. ta miƙo mata amsa tayi safeera tace '' da wannan number kike chatting.., Najlah ta ɗan saci kallon Jawad sai kuma akai Sa'a shima, ya ɗago kai fa sauri ta dauke kan'ta tace '' eh da ita nake yi.., okay idan naje gida nayi miki magana ma dinga gaisawa tanan yanzu zumincin yanzu sai ta media amma dai zaki zo ki wunar min ko..?, Najlah tace '' idan yaya ya barni zan je mana..., Hisham yace '' hmmm wannan uban yan kullan tab.., JAWAD yace '' maman mubeena har na kai shi.., taɓe baki tayi tace '' ai duk halin ku ɗaya yar unguwar nan sai a sawa mutum ta kum kumin fita.., Hisham yace '' ki faɗi gaskiya yafi ni ko zuwan mu gidan nan nawa zuwan jawaher nawa..?, dariya tayi tace '' ai SAN ya fika ka iya kulle wallahi.., kallon agogo yayi yace '' to hirar ta isa haka lokacin sallah yayi tashi mu je muyi sallah.., cewar JAWAD. tashi Hisham yayi suka fita dariya Hisham ya fara haɗe rai jawad yayi yace '' kai lafiyar ka qalau kuwa..?, wallahi ina dariyar yadda akai kake tsoran wannan dan ƙara min abin nifa wallahi dani ne da tunani anyi an gama sai dai ta fashe kowa yaji warin ta ko kuma babbar hanya kake tsoro ne ban sani ba.., uban babban hanya nake tsoro kawai dai akwai abin da nake jira ne is very young. dariya Hisham yayi yace '' hmmm young fa, ai irin haka yafi dad'i kai zakai saitin ka yadda kake so saitin ya tafi., JAWAD yace '' hmmm kai dai wallahi Allah ya shirye ka muna ƙoƙarin sallah kana wannan zance.., dariya Hisham yayi bece komai ba, alwala suka yi sannan suka tafi masallaci. Cikin gida kuwa safeera ce ta tashi a tayi Sallah sannan ta dawo jan NAJLAH take yi da hira , dan sakin jiki tayi da ita saboda tana son yara ɗazu ma ganin JAWAD ya dauke ta , hakan ya saka bata kula ta ba gudun kar kuma wani abu ya biyo baya yazo yana mata ba dad'i. jin sallamar su, suka yi amsawa safeera tayi Hisham yace '' to uwar surutu taso mu tafi Najlah ta , takura miki da zance ko..?, girgiza kai tayi tace '' a'a naji daɗin zuwan ku ina zaune ni kaɗai ba , abokin hira.., Kallon ta JAWAD yayi ya cije lips din'sa yace '' daga dawowa sai kace tafiya ai na zata sai dare..?, a'a wallahi yanzu zamu tafi idan ka matsi da ganin mu, to ka biyo mu ka ramawa kura aniyar ta daman ka ajiye yarinya ba wani me debe mata kewa wallahi JAWAD hmmmm. haɗe rai yayi salon Ya saka Najlah ta raina shi ya dauki mubeena da take wasa a cinyar Najlah dariya yarinyar ta shiga yi mai yana mata wasa. tashi safeera tayi tace '' to auntyn mu sai na ganki a gidana sauran kuma SAN ka hana ta zuwa.., murmushi yayi yace '' sai JAWAHEER ta dawo ma zo mu wunar muku..tun karfe 6 na safe za mu zo sauran kuma kuce yayi wuri.., Kamar gaske Allah ya kai mu Lokacin Cewar safeera Amin ya Allah cewar Hisham da JAWAD NAJLAH dauko jakar nan tayi ta miƙa mata amsa tayi tana mata godiya shima HISHAM yayi mata godiya tare da cewa JAWAD ka taya mu godiya JAWAD yace '' to kudi ya dauko ya bawa mubeena suka ƙi amsa amma yace shi ba su ya bawa ba yarsa ya bawa. Ba yadda suka iya ya daure su da jijiyoyin jikin su suka amshi kudi tare da yin godiya. har wajen motar su suka raka su sannan suka juyo suna shiga Jawad ya rufe kofar parlour da sauri Najlah ta kalle sa wani kallo yayi mata yace ''hmmm wana kama wato ko a gida ma haka zaki ce na barki ke kadai ko ba abokin hira kin ce min kina son yin hira ne..?, wallahi Najlah ki kiyaye randa zan riƙe ki a hannuna zaki yi bayani ne abu ɗaya ne ya cece ki gift din da kika basu da yau hmmm kin fahimci wane ni.. ajiyar zuciya ta sauke ganin ta kubuta.. juyawa tayi ta kwashe kayan da, ta kawo wa su safeera takai kitchen ta dawo juyowa tayi taga still yana gurin nan a tsaye tamkar wani wanda ya haɗiyi sanda taɓe baki tayi ta juya ta shiga daki ta rufo. tabar sa a tsaye yana tubka da war wara maganar da suka yi da Hisham ita ke tunowa yana nazari akan ta. yana kuma hango wutar da take gaban sa a hankali ya furta ummi dafa kan'sa yayi yana rokon Ubangiji ya ganar da ita gaskiya kafin lokaci ya kure mata , besan wannan wacce irin tsana bace haka. ajiyar zuciya ya sauke ya hau saman sa. **************************** YOLA. UNGUWAR DOUGIREI ƊAN BUZU ESTATE. Kyakkyawar tsohuwa ce zaune akan carpet gaban ta kayan ciye ciye ne kala kala duk da tsohuwa ce hakan be hana a gane ita din buzuwa bace ta usul gefen ta wasu yan mata ne zaune suna duba atamfofi ko wacce na fadar ra'ayin ta. da alama jikokin tane dan ba'a ce ya'yan taba gefe bangon da yake kallon dining room katon photo JAWAD tare da wani farin tsohu ya rungume shi JAWAD da kayan lauya a jikin sa hannun sa rike da wata farar takarda kallo ɗaya zakai mai ka fahimci su dukan su, suna cikin zallar farin ciki anyi wa frame din ado da ruwan gold hakan ya kara kawata farin painting hannun dama kuma na cikin dining room din katon picture JAWAD ne da wannan tsohuwar sai tsohon nan ya ja mai kunne da ga gani shidin dan gaban goshi ne. kallo ɗaya zakai wa hamshakin parlour kasan cewa ita din tsohuwar gata ce. da tagaji da wanna uban musun da suke yi tace '' ku dai Allah yayi muku ruwan ido wallahi ni ina tsohuwa ma bana wannan abu da ni nake yi cewa za kuyi rikicin tsofa ne kunga waccan zata yi muku kyau ne adon blue blue din nan ba fari ba baki duk za tayi wa mutum kyau tun da wannan anko din ba iya gidan nan za a yi ba Aliyu ma yace ku yi maza ku zaɓa wanna sample ne sai ayi ta da yawa rabawa yan uwa da abokanan arziki..., wata ce a cikin su ta daga wacce anni ke nuna musu tace '' ANNI amma ba zai saka a rubuta sunan ba ko..?, ANNI tace '' basma ina zan sani.., Gaskiya ANNI kice kar ya saka mana suna wallahi mu mun fi son ta a haka kuma ALLAH kin fadi gaskiya wannan ba wanda ba zata yi wa kyau ba Cewar unaisa hmmm Allah ya kyauta wannan kuma shi ya sani. Dan Allah Anni Ki kira shi kice kar a saka suna. wallahi ba da waya ta ba wato nice marainiyar wayon ku ko da JAWAD ne kuce ya fiye daure fuska shima Aliyu daure fuska yake yi ashe abin naku rainin hankali ne wallahi muhibba ku fita daga cikin idona na rufe. tashi basma tayi tace '' ai dadin ta ma muna da wayar da sai ki kumburan zuciya da wannan maganar taki.., Uhmmm wallahi bara Sharif yazo yayi min tsakani da ku ko da yake Allah ya kawo yaron kirki JAWAD wallahi shine maganin ku shima sharif din ai kun raina shi bakwa kallon sa da gashi.. dariya dukkan su, suka saka suna sai Anni hade rai tayi ta soma lalubo number JAWAD da sauri muhibba ta karbi wayar tana cewa dan Allah anni kiyi hakuri, karki kunto mana kura da tsakar rana Allah sarki sister tana can tana fama. basma tace '' wallahi kuwa tana can.., ANNI tace '' hmm waya faɗa muku zai mata wani abu wallahi NAJLAH yar gata ce a gurin Jawad kuma za ku gani..tun tana yarinya yake dawainiya da ita yake nuna mata kulawa..., ANNI har yakai ya MUNEEF da ma baya son ɓacin rainta..? Cewar ramlat Dariya ANNI t@yi tace '' yaro man kaza ko wanne allazi da nashi amanu kunga shiga ta daki ba za a yi wannan musun da ni ba... bani waya ta..., Mika mata tayi suka bita da kallo suna mamakin abin da ANNI tace sai kuma suna ci gaba da sabgar su cikin nutsuwa. ********************** TARABA STATE JALINGO POV UMMIN JAWAD wallahi Ummi idan baki tashi tsaye akan yaya ba za su saka ma gaba ki ɗaya yace bake kika haife shi ba ga har muka tafi be fito da waccan shegiyar ba. balle ya biyo mu ya bami hakuri kar kaɗa ƙafa ta shiga yi ranta duk a ɓace ta buɗa baki za tayi magana taji sallamar SAMHA da sauri ya juyo ita da ALTAB ne yana riƙe da kayan ta a cikin. Lugaggage ga jakar ta ya riƙe ta a hannun sa yawa wani yaron ta, ga wata kwandaleliyar sarka a wuyan sa da wani three-quarter wando jikin sa duk sarka daga shi har ita ba , wanda ya cire takalmin sa haka suka shigo cikin parlour. sakar baki tayi tana mamakin rashin kunyar ALTAB Allah me iko. zama SAMHA tayi tace "' sannun ku..," ta faɗa tana dauke kai haɗi da sakin kwai tana latsa wayar ta shi kuwa zakara sarkin neman suna hana rike da jakar ta ya saba ta a hammata yace '' ahhh ummi baki ji tana gaishe da ke ba.., tabbas idan ba tayi da gaske ba bakin cikin JAWAD ALTAB yana neman kashe ta kwanan ta be ƙare ba su biyu ne mazan ta kamata yayi ace taji dad'in su, sun faranta mata sun mai da ita yar gata abin kwatance amma gashi nan suna neman halaka ta kwanan ta be ƙare ba me ake da auran yar tasha duk da shima ɗan nata dan tasha ne amma da ace ya samu matar arziki ai da sai ta shi za tayi cikin kunar rai ummi tace '' ALTAB ka fita daga kai har sharar matar ka bana kaunar ganin ku.., wani kallo SAMHA tayi mata sai kuma taja kwafa ta tashi tsaye tace '' wallahi ni kabewar ƙabari ce baƙin cikin me taushe ni da kalin majina ce dole idan aka hau ni a zame.., amma wallahi yaya sam halin ka be yi ba kana gani take faɗawa mahaifiyar mu bakaken maganganu..? Ke saurara min tun da nazo gurin nan ban saka dake ba , balle ki dauki kaso kuma sannan kina ina Lokacin da momcy ta zo gidan nan taci mata mutunci amma duk da haka ina kallon ta a matsayin UWA wannan faɗan su, su ta shafa ba mu ba ko ba haka ba HONEY 🍯..? ta ƙarshe maganar tana yi wa ALTAB wani irin kallo irin na gogaggun yan bariki.. Altab da ta kusan kunce mai kai yace '' kyale ta so take nayi kasa kasa da ita zo mu fita idan ta wuce ma dawo ke AFNAN ki dinga tofa mata FALA'I DA NASI three three a ruwa tana sha sai Ayatul-kusiyyu maganin sheɗanu domin daga gani ummi ta samu shafar aljannuuuu..., jiri ne ya fara ɗiban ta ta dafa bango da kujera zuciyar ta na tsananin bugu ita yau dan da ta haifa yake faɗawa tana da aljanu aga ban matar sa tabbas ba tayi lalacewar da haka zata faru a kan'ta ba wallahi sai ta nunawa SAMHA din mahaifiyar ALTAB ce kuma ba'a sauya wa tuwo suna. har suka fita bata dauke idanuwan'ta ba akan kofa. cije lips din'ta tayi ta fara tafiya dafe da kirjin ta. AFNAN bin bayan ta , tayi har ta shiga daki maganin ta ta ɓallo mata da ruwa ta bata , tasha bacci ne ya dauke ta ta gyara mata kwanciya ta rufo mata daki ta fito.. Shiga dakin ta , tayi ta kulle ta dauki laptop din'ta ta buɗe tana danne danne tana kallon agogo lokaci bayan lokaci knocking kofar ta aka yi da sauri ta , tashi tare da buɗe wa rungume wacce ta shigo tayi tare da sakar mata kiss a wuyan ta tace '' wallahi baby nayi missing ɗin ki.., murmushi tayi tace '' anya kuwa bafa kya nemana ke wallahi tsoran ki yayi yawa, yawa wacce zata dauki ciki.., dariya AFNAN tayi tace '' hmmm kawai dai iya taku ne amma wallahi nayi missing din ki musamman ma wa'yannan tausasan boobs ɗin ki shekaran jiya fa zan fito around 2 clock wallahi muka haɗu da ummi dakyar na fitar da kai na wallahi.., zama tayi tana cire abayar ta tsirara tayi haihuwar uwar ta ashe ko inner bata saka ba breast ɗinta a tsaye yake kyam tamkar an wura balo susucewa AFNAN tayi tane cewa wow baby kamar ƙara miki kyau aka yi wallahi. Murmushi tayi tace '' kema kin yi kyau amma ai gashi nan ni na ina zuwa gurin ki.., zama tayi tana ƙare mata kallo yawa tsohuwar mayya tace '' uhmmm wallahi ba zaki gane ba.., ta ina zan gane tun da har yau kin kasa waye wa duk wani hanyar da bara da na nuna miki bakya fahimta kamar ba yar University ba kina da hanyar da za kiyi abu iya son ranki a gaban iyayen ki bare da kowa ya zarge ki ba , ai yanzu wayewa tazo duk wata yar bariki da ta amsa sunan ta wala matar aure ko budurwa ki zaune a gidan iyayen ki ba me ce miki me yawon ta zubar jibe ki kin ƙi yadda ki fito duniya ta ganki daga anyi magana kice ya Jawad Ni wallahi kin saka min son ganin ya Jawad din nan idan yayi min nayi wuf dashi duk da bana sha'awar ɗa namiji wallahi amma wani zubin zuciya na son dan ɗana yadda maza suke.., My real fan's ya kuke ganin wannan tafiyar...? Jar ubancan kaka kara ƙaƙa akwai fa kulleka to dai kar ku manta da yi min reacting comments.. nice taku har kullum YAR' MUTAN Yakassai wacce kuka fi sani da OUMYASMEEN. Ku biyo ni domin warware muku wannan kullin.. Littafina na kudi ne. Wannan littafin na kudi ne duk meson 1k amina alhasan Muhammad 8141785374 opay KU TURO DA SHEDA TA WANNAN NUMBER 08141785374. Yan niger 1000fcfah AMINA MUHAMMAD ALHASAN KANO My nita sai kuyi screen shot Ku turo ta wannan number 08141785374 Ina sanar muku akwai complete document na dukka littafin nan 1:.JIKAR MAMMAN COMPLETE DOCUMENT 1K 2:.HAUWA KULU WOMEN LEADER COMPLETE DOCUMENT 500 3:.DESTINY LOVE 400 4:.BINTA YAR JAGALIYA COMPLETE DOCUMENT 300 5:.YAR HANNU A LAGOS 1K 6:.GIDAN MAGAJIYA Complete document 1k 7:.UWAR GAFALALLU COMPLETE DOCUMENT 1K 8:.BAƘIN SHAFI 1K COMPLETE DOCUMENT 9:.YAN ZAMAN MAKKAH 1K COMPLETE DOCUMENT 10:.MU ZUBA MU GANI COMPLETE DOCUMENT 200 11:. KIN CUCE NI 300 Dan Allah idan kinsan ba siya za kiyi ba karki yimin magana duk maganar da za kiyi idan ba receipt evidence na gani ba bazan amsa ba dan Allah mu kiyaye Number iya WhatsApp take yi 08141785374 ban da kira KARUWAN CIKIN GIDA EPISODE ¹¹ https://www.youtube.com/@nasreenminallah https://chat.whatsapp.com/HRMOP1wuYgMI1zNjPiRYkS Wani kallo AFNAN tayi mata tace '' Baby ya JAWAD fa..? sai kuma tayi wani murmushi wanda ya tsaya iya lips din'ta tace '' ai yar bariki sai ɗan bariiki kin taɓa ganin inda aka zuba shara a cikin tsaftaccan ruwa..? launin kalar sama a bin sha'awa ne saboda me kyau ya sha bambam da mara kyau..I'm warning you, I swear, even as a joke, don't ever let me hear those words from your mouth again.., da sauri Baby ta tashi ta nuna kirjinta tace '' tab AFNAN ni kike faɗawa haka kalle ni da kyau ban yi lalacewar da za ki faɗa min haka ba wallahi ,just because you saw a buffalo in the wild, doesn’t mean it looks like a domestic cow to you Aure ne kuma kamar na aure JAWAD na gama ne in yaso ki mutu da bakin ciki.., mai da kayan ta , tayi ta dauki jakar ta fice tabar AFNAN da sakakken baki. cikin tsanin bakin ciki haka take taka stair case har ta sauko da sauri ta juyo sakamakon frame din da ta gani cikin mamaki ta isa kusa da katon picture din cikin tsantsar mamaki dakyar take iya motsa labban ta tace '' ALHAJI ALEE BABALLE KWARA. cire hannunta tayi daga kan picture din to mene alakar'sa sa JAWAD tabbas akwai lauje cikin nadi amma koma mene tabbas za tayi ramuwar gayya ne dan WALLAHI sai ya ɗan ɗana abin da yafi wanda mahaifinta ya ɗan ɗana azzalumi macuci no wonder shi ya saka ga ya'yan sa nan duk ba na kirki ta tabba ma JAWAD ba shi ya fe Shi na saboda su irin mutanen nan tun a duniya Ubangiji yake hukunta su...aje can su kara ɗan ɗanar abin da yafi na nan.., juyawa tayi ta fara tafiya jin ana ƙoƙarin saukowa tana fita batai wata wata ba ta buɗe motar ta , ta shiga tayi mata key a guje ta fita daga cikin gidan Allah ya rufa asiri batai gaba da kan me gadi ba. aguje ta fita tana sharara gudu babban burin ta , ta isa gida. tana zuwa tayi parking ta fito da sauri ta shiga tamkar wacce aka faɗo da ita haka ya shigo cikin gidan tace '' Amma ina abbati..?, da sauri ta ɗago tace '' nusaiba lafiya kika shigo cikin gidan nan tamkar an wullo ki..?, kama kugu tayi tace '' Amma yanzu ba lokacin magana bane, nan gaba zaki san dalili ina abbati yake...?, banza tayi mata ta mai da hankalin'ta wajen TV da sauri ta fita tana kalle kalle can ta hange shi, da sauri ta ƙarasa tace '' abbati yau Allah ya wanke mana takaici.., dirowa yayi daga kan motar sa yace '' me ya faru takaicin me..?, Hmmm yau na gano gidan kwara lokacin ɗaukar fansa yayi na dade ina zuwa gidan amma ban taɓa sanin cewa gidan sa bane. Kai dan Allah tabbas lokaci yayi da zai fahimci ainihin mu suwa ye. amma wani hanzari na gudu ba dole mu zauna mu tattauna da sauran yan uwan namu, duk me goyan bayan wannan tafiyar tamu ta daukan fansa gwara mu san da wa muke zauna ne . ABBATI yace ''kai lallai ma har sai mun tsaya wata shela duk dan takazar uban da be bi mu ba billahilazi mun raba jaha dashi ai wannan mutumin idona idon sa , sai na shake shege ya mutu kowa ya huta domin barin irin su kwara a doran duniya, BARA ZANA NE GA RAYUWAR AL'UMMA.., yes wallahi haka ne sai ka shigo cikin gidan ta faɗa tana juyawa bata ta jira me zai ce ba. shima komawa yayi ya zauna yana ci gaba da danna wayar sa. ********************** ABUJA POV EMAN hmmm TJ kenan, jawaher tayi nisa bata ji ba kira ba lallai ta fahimci me muke so da fahimtar da ita ba ni wallahi ban san ma ta , tafi ba sai da na dawo daga gida da yake mommy ba lafiya jikin ta yayi tsamari shine nasani ma.tayi tafiya ɗora kafa ɗaya kan ɗaya yayi ya sha shisha tare da fesar da hayaki yace '' gaskiya jawaher yar akuya ce , amma very soon zan yi maganin ta ni zata ci amana har ta , tafi wata ƙasar da wani namijin wallahi idan ta cikan ciki sai na fasa kwan kowa ya shaki warin sa ai tun farko ba haka mukai da ita ba yau shekara nawa amma ta kasa abin da ya dace daman can yaudara ta , take ba aure na za tayi ba wai zata tara kudin da ba za muyi talauci na idan kuwa haka ne wallahi Allah yayi wadaran wa'yannan kudade da har yanzu basu taru ba yasin na gaji nagaji EMAN nasan dai karshen mu ace prison to wallahi ni ko a jiki na kar tayi abin da ya dace ta gani duk inda take ta dawo idan kuwa taki zan ɓallo mata ruwa.., kwantar da kai EMAN tayi tace '' a'a TJ mutunci ma wani abu ne kasan komai sai ana binsa a sannu a hankali sannan sai a sami nasara wani satin zata dawo kayi hakuri wallahi dana ga kiran ka gaba har faɗuwa yayi gaskiya bata kyauta ba komai zai faru kar ta manta baya a yanzu kudade sun budewa Jawaher ido kuma tana cikin tsaks me wuya ga aikin da mahaifiyar sa , ta saka ta tayi.., da sauri ya kalle ta tare da cire glasses ɗin sa yace '' what me kike shirin faɗa min ne dan Allah ci gaba ...?, Mahaifiyar wa wanne aiki ta saka ta..?, a'a bakomai kaga TJ sai an jima daman na riga na faɗa maka akwai inda zani kar su zo suna jirana. okay ba damuwa sai kin dawo yau ba jin dad'i kenan, har na saka a tanadar mana abubuwan nishadi. wine ta ɗauka ta sha tace '' a'a wannan ma ya isa thank you... bye.., bye ya faɗa yana kissing din kumatun ta. da sauri tabar gurin har tana neman gurdewa bude motar ta tayi ta shiga ta saki ajiyar zuciya a hankali tace '' Allah ya so ni ban yi ɓari zance ba , wayar ta ce tayi ringing ganin sunan DEEYA da sauri ta ɗauka tace '' DEEYA gani nan zuwa wani dan uzuri na tsaya yi ina Na'ilah take..? ta shigo kuwa..?, sauraran me zata ce mata tayi sannan tace '' okay na fahimta sai na tawo.., ta faɗi haka tana kashe wayar ta. Key tayiwa motar ta , a hankali ta fara tafiya har ta fita daga cikin gurin shakatawar ta hau kan babban titi sakin music 🎵🎶 a hankali take bin wakar kamar haka Estoy tan enamorado de ti Que la vida se me va Pero no me importa Estoy tan enamorado Que me la paso soñando Despierto pensando en ti Cada segundo que pasa Siento que te quiero más Eres tú mi alegría Mi paz y mi felicidad Y si algún día me faltaras Yo no sabría qué hacer Porque sin ti mi vida Ya no podría entender isa cikin gidan deeya tayi kashe motar ta tayi ta fito knocking tayi mata , ganin kamar bama tasan tana yin knocking ba sai ta buɗe jakar ta , ya fito da wayar ta kira ɗaya tayi mata ta ɗaga tace '' DEEYA ina kofar gidan ki fa.., okay kiyi hakuri gani nan zuwa. kashe wayar tayi bata ce komai ba , batare da jimawa ba ta buɗe kofar shigowa tayi DEEYA na cewa wallahi na dauka ba zaki zo ba a ina haka kika tsaya..?, hmmm na je gurin wani friend ɗin na ne. Dariya deeyana tayi tace '' wallahi Eman ke ayuce da sassafe ki fita ke ko gajiya ba kya yi.., Murmushi EMAN tayi tace wallahi ko ɗaya ba abin da kike tunani bane Hajiya ban da abin ki kin taɓa ganin inda mutum ya gaji da neman kuɗi. Allah ya kyauta cewar deeeya Eman ta zauna tana cewa amin. Drink da snack ta kawo mata , eman tace '' yau gidan naki ba mutane.., Hmmm oga yana nan ina zaki ga jama'a daukan lemo tayi tasha tana dariya tace '' ah no wonder shi ya saka har kika samu damar yi min faɗa ina Na'ilah take..?, daukan remote din AC tayi tana cewa ta koma gidan tsoho.. saboda sun yi fada DAZ gidan da ya kama musu kudi ya kare. da sauri EMAN ta ajiye kofin hannun ta tace '' Innanallahi wainna ilaihir raji'un haba dai me yace mata amma dai be mata tujara ba ko...?,ita duk shekarun da tayi tana bariki ta rasa tara kudin da zata siya gida tana tsakiyar abuja ta koma local area kash gaskiya wayon ta ya zama na banza.., murmushi tayi tace '' kisan ita ba wai tana yin wannan harkar bane saboda kudi ta tsaya ne iya DAZ karshe yaci amanar ta.., Gyara zama Eman tayi tace ''' Kuttumar ubancan lallai Na'ilah bata da hankali kan bala'i duk yadda take da kyau haka kash kinsan tun ranar da muka hadu a gidan ki naji yarinyar tayi min komai yaji big lady ce amma ta tsaya kan'ta ya shiga cikin tukunya haka,, tashi DEEYA tayi tace '' wallahi kuwa amma ai yanzu ta dauki izina ..., Eman kallon ta tayi ta shafa plat tommy din ta tace '' wai ba abin da zan ɗan rage gajiya ta ne ko yana ciki ne ...?, a'a baya nan ya tafi kauyen su amma bazai jima ba gaskiya nasan nan da karfe goma ya dawo. a muna da lokacin raƙashewa kice. ta faɗa tana tashi, shiga cikin bedroom suka yi zama tayi a kan gadon ta , hira suka fara sai kuma zancen nasu ya sauya salo. Allah ka tsare mana imanin mu ka raba da sharrin shaidan Allah ya shirya mana zuri'ar mu.... *********** OSOKORO. buɗe datar ta tayi messages din safeera ne ya fara shi gowa sai na yaya MUNEEF da sauri ta shiga nasa wani sanyi ne ya shiga zuciyar ta ganin yana online typing ta fara yi mai kamar haka ta tura emojis din fushi 😡 tace wallahi yaya nayi fushi tun ranar da ka kira ni baka ƙara kira ba ni ban daukar bi wannan uzurina naka ba.. Kiran sane ya shigo wayar ta video call dauka tayi tana turo bakin ta dariya yayi yace '' haba my mine ashe zaki iya fushi dani wallahi ko jiya sai da na kirawo ki amma wayar user busy kamata yayi nayi fushi dake amma ban ba shine na yi miki magana ta WhatsApp.., ajiyar zuciya ta sauke tace '' to shikkenan ya kake ya kasar taku.., Alhamdulilah amma ina da correction ɗaya.. ajiye wayar tayi ta gyara mayafin'ta da ya sauko tace ''to mene shi.., yauwa my Princess ƙasar su ba ƙasar mu ba. bisimallah ga coffee ina sha ko kice zaki sha.. NAJLAH tace '' a'a Nagode bana sha ya MUNEEF kayi magana kuwa da su basma ai bata ƙarasa ba ta zaro ido da sauri ta katsai kiran Allah yana gani bata san ya shigo ba kuma a yanayin da ta ganshi ba karamin tsorata ta yayi ba jikin ta ne ya soma rawa ganin yadda idon Jawad ya ƙaɗa yayi ja abin ka da farin mutum fuskar nan tasa tayi ja alamun ɓacin rai muraran akan fuskar'sa tashi zaune tayi bakin ta na rawa tace '' wallahi Allah ya MUNEEF ne.., da hannu yayi mata nuni ta bashi wayar kuka ta saka tace '' wallahi shine idan na miko maka ba zaka dake ni ba...?, ransa ne ya ƙara ɓaci ya daka mata tsawa yace '' ni sa'an wasan kine na zaki miƙo min ita ba..?, dauka tayi ta miƙo mai zuciyar sa ce tayi wani irin bugawa sakamakon ganin ta daga ita sai wata doguwar riga me sirrin hannu a haka take video call ɗaga hannu yayi zai mare ta da sauri ta dafa kuncin ta , tayi ƙasa tare da zun duma ihu ta rufe idanuwan'ta ta tabbatar wannan mari idan yayi mata sai ta kusan suma domin ba zata manta karon ta dashi ba lokacin sun dawo daga makaranta shi kuma ya shigo yola gaishe da su jadda da yake baya sati uku be shigo Yola ba. ashe tun a a kofar Makarantar su wani yana bin su , har direba ya sauke su sai a nan yayi mata magana tayi banza dashi daya takura mata sai ta karbi complement card din sa ashe duk abin da yake faru Jawad yana tsaye yana kallon su. zata tafi ya riko hijabin ta be yarda ba sai ta bashi number ta shine ya fita ya kusan marin sa ya faffaɗawa mutumin magana bayan mutumin ya tafi.......... ya jawo ni tamkar zai kashe ta dakyar jadda ya kwace ta , ya rufe shi da faɗa sai da nayi kwana uku ina jinya dan haka a yanzu ma tayi zaton idan ya mare ta suma za tayi sai kuma taji ya fasa a hankali ta buɗe idanuwan'ta, tana kuka nuna ta yayi da ɗan yatsa yace '' wallahi NAJLAH ki kiyaye ni daga yau sai yau na iya MUNEEF ba na ƙara ganin ki , kina video call da wani ranki sai ya ɓaci wallahi ban da tsabar rashin kamun kai a haka kike video call ba kunya kina nuna mai kin girma ko..? zama yayi ya ci gaba da cewa idan aure kike so sai ki faɗa min na faɗawa jadda daman shi ya saka kike matsa sai kin tafi karatun ne bakya so, aure kike so..ko to shikkenan za muyi miki shi.., da sauri ta saka kuka tace '' dan girman Allah kayi hakuri wallahi na dena abin da nake yi bazan ƙara ba kayi hakuri ni ba aure nake so ba.., daga baya kenan aure ba fashi baba me gadi daman yana da hali me kyau ko shi ko masa'udu me wanki da guga duk za su iya da halin ki. da sauri ta ɗora hannu aka tana kuka tana bashi hakuri tamkar dutsai haka jawad ya zame mata sai da ya gama isar sa yace '' daman wannan ciwon cikin da kike yi ai duk alamu ne , na aure kike so dan haka ba fashi.., share hawaye tayi ta gaji da kuka a yanzu hawaye baya zubowa sai kawai ihu da take yi tace '' kayi hakuri bazan kara yin video call ba wallahi na dena karka aura min baba ko masa'udu idan ba kace dole ne a cikin gidan sai ka hadani da wani.., kina son MUNEEF..?, da sauri ta kalle sa ta gyada kan'ta ran Jawad ne ya ƙara ɓaci fiye da farko sai da ma yayi dana sanin fadar haka tashi yayi yace '' good yayi kyau daga ke harshi zan maganin ku yana karatu ke kuma baki fara ma karatun ba , yana neman hana ki karatun shima ya kasa nasa dole na haɗa meeting kowa yasan me yake faruwa badai aure kike so ba.., dan girman Allah kai hakuri kar ka faɗa musu wallahi bazan ƙara ba ni gani nayi da baba me gadi ko masa'udu gwara ya MUNEEF amma .. yimin shiru kafin na fasa miki baki... sarai tasan zai iya dan haka yaja bakin ta , ta tsuke fita yayi kifa kai tayi a kan gadon ta , tana kuka da sauri ta ɗago jin wayar ta na ringing ashe be tafi da ita ba sunan aunty Hafsah ta gani da sauri ta dauka ta ƙara rushewa da kuka... dakyar ta lallashe ta tace '' me ya faru yi min bayani..?, kwashe duk a bin da ya faru tayi ta faɗa mata dariya aunty tayi hakan da tayi ba ƙamarin kular da Najlah yayi ba cikin ɓacin rai tace '' aunty na faɗa miki damuwata shi ne kike min dariya.. wallahi sai na kashe wayar sai kiyi dariyar ki son ran ki da ai na bugu miki nace miki yaya ya karya ni kya dauki maganar serious dan wallahi yaya da ace a soja yazo gunduwa gunduwa zai dinga yi da mutane Allah ne ya rufa asiri yaya lauya ne ba dan sanda ba ko soja da lamarin wallahi sai ya fi haka... muni zama a cikin gidan nan kaddara ne wallahi dan ma dai ita ma matar tasa shegiya ce da wallahi tausayin ta zan dinga ji to itama bata da hali ko kaɗan.., aunty Hafsah danne dariyar ta , tayi tace '' to Allah ya rufa asiri dai hakan be faru ba to ai yanzu kema abin tausayi ce tun da ke ma a cikin gidan kike cewa za kiyi ina tausaya mana da zama ya haɗa mu da yaya amma fa NAJLAH kin aikata kuskure ya za a yi ki yi video call da namiji..ko dan kare mutuncin kan ki da kuma igi.... da sauri taci burki saboda katoɓarar da take shirin yi. da sauri Najlah tace '' yaya MUNEEF ne fa ba wani namiji ba kuma wallahi na saka mayafi ba abin da ake gani shima lokacin da ta zo mayafin ya cire ne..., ajiyar zuciya ta sauke tace '' to tun da baya so kuma kinga kina karkashin ikon sa be kamata yi abin da baya so ba duk wani abu da baya so sai ki kiyaye sai ku zauna lafiya har Allah ya albarkaci rayuwar ku.., uhmm aunty Hafsah kenan ku wallahi bakwa ganin laifin yaya komai ni ce me laifi.... NAJLAH shifa namiji ne kuma yana gaba dake Najlah komai yayi dan kyautatuwar rayuwar ki ne.. wallahi da zaki tona zuciyar sa yafi kowa son ki da kaunar ki ko kuda idan har zai taɓa jikin ki ya zame miki matsala ba zai so ba NAJLAH har yau kin kasa tsayawa ki fahimci wane JAWAD. turo baki tayi tace '' ya su Hajiya..?, suna lafiya qalau na turo miki atamfar anko din TAUFIQ.. wani uban tsalle ta daka tace '' dan Allah kai amma naji dad'i, amma wallahi idan na muka zo bazan dawo ba shikkenan haba na gaji da halin yaya JAWAD... dariya aunty Hafsah tayi tace '' hmmm aike yanzu ba wanda ya isa ya raba ku dashi.., kai aunty wannan fatan kike min kamar baki son wahalar da nake sha ba. NAJLAH wacce wahala halin ki ke ja miki fa. to zan gyara ta faɗa tana turo baki. da sauri tace '' yauwa yar albarka .., sallama su kayi ta kashe wayar har akai sallar isha'i tana zaune a gurin dan ko girki bata ɗora ba tun da ita matar sa kafar yawo ce da ita bata lura da abin da ya dace ta shige ta tafi ta baiwa masu aiki hutu ga baiwa ta zo. tashi tayi, ta cire kayan ta , tashi ga wanka bayan ta fito ta shafe jikin ta da turare ta saka sleeping dress riga da wando gaban rigar abude take dan haka ta balle boturan gaban rigar tata. kashe fitila tayi ta ta kulle kofar ta , ta kwanta lulluba tayi da blanket ta fara charting da yaya muneef tunawa tayi bata yiwa aunty safeera reply na da sauri ta shiga ta amsa sallamar ta tare da yi mata ya suka je gida ta ci gaba da charting bama ta online ci gaba tayi da charting din ta , ba ƙaramin farin ciki ya MUNEEF yake sakata ba duk wata damuwa tata sai taji babu kaso hamsin. da yake uban barkwanci ne.. har sha biyu suna tare kamar daga sama taga messages din ya Jawad da sauri ta kashe datar ta ta dafe kirjin ta yana zaro ido a hankali ta buɗa message din kamar haka *da ubanwa kike chatting a wannan lokaci....? ki kashe datar ki , ki zo ina jiran ki sauran kuma ki tsaya ɓata lokaci* a hankali tace '' na shiga uku yau shikkenan laifi kan laifi kunna bedside lamp tayi ta dauki hijabin ta ta saka zura slipper dinta tayi ta buɗe kofa ta fito tamkar wacce kwai ya fashe wa a ciki haka ta dinga tafiya jikin ta na rawa hawa sama tayi. saka hannu tayi za tayi knocking kofar sa , sai kuma taga a buɗe take turawa tayi a hankali ta shiga tana leke baya cikin barandar wajen ƙara shiga tayi baya cikin parlour sa to yana ina ..?haka tayi wa kan'ta wannan tambayar ganin ba me bata amsa ta nemi guri ta zauna tana cewa yaya problems ni gaskiya ba zan shiga bedroom din sa ba.. ganin shiru shiru bashi ba labarin sa ta ɗaga murya tace '' yaya yaya gani na zo da tun da zu.., shi kuwa tun shigowar ta part din nasa yana ganin ta har zaman ta a kan kujera ta cikin ƙatuwar plasma da take cikin dakin nasa sai kace TV ce amma ba abin da yake kallo da ita ya haɗa ta ne da CCTV CAMERA kashewa yayi ya tashi zaune daga kwanciyar da yayi daukan wayar sa yayi ya zoro kan'sa yace '' uban sa yake miki ki zauna anan me na faɗa miki shine kika zauna kina kwala min kira nazo na same ki ko..? kinfi karfin ki zo gurina..?, da sauri ta tashi tace '' dan Allah kayi hakuri , NAJLAH idan ban yi hakuri dake ba yanka ki zanyi. turo kamarin bakin ta tayi , tabi bayan sa tsugunawa tayi a kusa da inda ya zauna tace '' dan Allah kayi hakuri.. gani ina charting ne da su basma akan maganar bikin yaya TAUFIQ.., banza yayi mata yana danna wayar sa sai da ya gama abin da yake ya ajiye gyara zaman tayi tace '' yaya bacci nake ji ɗaya saura.., kallon a gogo yayi yace '' ai kin iya zama kiyi charting ko..?, da sauri ta girgiza kai tace '' dan Allah kayi hakuri.., NAJLAH NAJLAH NAJLAH hakuri hakuri ke kuma bakya gyara halin ki ko..? insha'Allahu zan gyara tashi yayi ya miƙo mata leda yace '' ungo na manta ban kawo miki ba naga ba kiyi abinci ba na yi mana take away.., yaya naƙoshi.......... da sauri ya kalle ta , yace '' me kika ci..?, nasha yogurt ta bashi amsa tana wasa da hijabin ta. haɗe rai yayi yace '' ina wasa dake maza karba ko ranki ya ɓaci anan kuma za kici..., share kwalla tayi ta buɗe take away shawarma ce sai kidney souce da chip's buɗe fridge din sa yayi ya dauko mata 5alive me sanyi kadan taci shima ɗan dai yayi mata dole ne. kofi ya dauka ya tsiyaya mata lemo ya miƙa mata amsa tayi tasha kaɗan tayi gyatsa tace '' wallahi na koshi cikina tamkar ya fashe.., Okay fita da su ki kai kitchen ki dawo zaki taya ni aiki.. tashi tayi tace '' to.. daukan kayan tayi ta fita zuwa kitchen tayi ta ajiye su ta buɗe dakin ta , kai tsaye toilet ta nufa ta wanke bakin ta sannan ta fito.. hawa saman tayi ta shiga bakin ta dauke da sallama ɗagowa yayi ya amsa sallamar ta , baƙaramin bacci take ji ba ko idanuwanta sun nuna haka zama tayi nesa da shi, wata uwar hamma ta saki tace '' yaya bacci nake ji.., okay tashi ki tafi ki kwanta da sauri ta miƙe tana murna tace '' sai da safe.., JAWAD yace '' Allah ya tashe mu lafiya fita tayi tana cewa amin tana saukowa da gudun ta, ta karasa dakin ta toilet ta shiga tayi alwalar kwanciya bacci bayan ta fito ta kwanciya tayi tare da shafe jikin ta da addu'a mantawa tayi bata rufe kofar ta ba tashi tayi ta saka key ta ajiye a kusa da kanta ta kashe komai ta kwanta. lokaci kan kani bacci yayi awan gaba da ita. bangaren JAWAD kuwa misalin karfe 2:00 dai-dai ya gama duk wani abu da ya zame mai dole slippers din'sa ya saka ya bude drawer key's ne da yawa ɗaya ya dauka a cikin su tare da duba suna cire shi yayi ya saka a aljihunsa ya janyo kofar sa. a hankali yake saukowa dan karamin tsaki yaja ganin tabar kwan ko ina a kunne kashewa yayi na ko ina ya rufe kofa a hankali ya saka key ya buɗe dakin ta..., mai da kofa yayi ya rufe dum light ya kunna blue a hankali ya saka hannu ya yaye mata blanket din'ta tayi nisa da bacci baby face din ta , tayi fayau inner cap din ta , ta cire gashin kan'ta duk ya barbaje a kan pillowcase. botir din rigar ta ya fara budewa ajiyar zuciya ya sauke ya kwantar da kan'sa a saitin zuciyar ta da alama baƙaramin dadin bacin nata take ji ba domin a hankali bugun zuciyar ta ke fita tamkar an tsara shi.... ɗauke kan'sa yayi ya cire slippers din'sa ya hau kan gadon ya kwanta jan blanket yayi ya rufe su tare da juyo da ita tana facing din sa..... *OUMYASMEEN...* FREE PAGES YA KUSAN KAREWA KU HANZARTA BIYA DOMIN CI GABA DA KARANTAWA CIKIN KWANCIYAR HANKALI.. IYA YAWAN REACTING DIN KU DA COMMENTS DIN KU IYA YAWAN READ MORE........ Wannan littafin na kudi ne duk meson 1k amina alhasan Muhammad 8141785374 opay KU TURO DA SHEDA TA WANNAN NUMBER 08141785374. Yan niger 1000fcfah AMINA MUHAMMAD ALHASAN KANO My nita sai kuyi screen shot Ku turo ta wannan number 08141785374 Ina sanar muku akwai complete document na dukka littafin nan 1:.JIKAR MAMMAN COMPLETE DOCUMENT 1K 2:.HAUWA KULU WOMEN LEADER COMPLETE DOCUMENT 500 3:.DESTINY LOVE 400 4:.BINTA YAR JAGALIYA COMPLETE DOCUMENT 300 5:.YAR HANNU A LAGOS 1K 6:.GIDAN MAGAJIYA Complete document 1k 7:.UWAR GAFALALLU COMPLETE DOCUMENT 1K 8:.BAƘIN SHAFI 1K COMPLETE DOCUMENT 9:.YAN ZAMAN MAKKAH 1K COMPLETE DOCUMENT 10:.MU ZUBA MU GANI COMPLETE DOCUMENT 200 11:. KIN CUCE NI 300 Dan Allah idan kinsan ba siya za kiyi ba karki yimin magana duk maganar da za kiyi idan ba receipt evidence na gani ba bazan amsa ba dan Allah mu kiyaye Number iya WhatsApp take yi 08141785374 ban da kira KARUWAN CIKIN GIDA Ina yiwa daukacin Al'ummar musulmi Barka da sabuwar shekara Allah ya sada mu da alkairan da ke cikin ta ya raba mu da sharrin da yake cikin ta duk abin da zai zama fitana a gare mu Allah ya kare mu ya tsare mu Allah ya albarkaci neman mu alfarmar annabi Muhammadu Sallallahu alaihi Wasallama. https://www.youtube.com/@nasreenminallah https://whatsapp.com/channel/0029VaLdFeg4SpkQ9xyW5c0k EPISODE ¹² Limshe idanuwan'sa yayi yana jin wani sanyi na ratsa gangar jikin'sa addu'a yayi ya kashe dum light ya lulluɓe su wayar sa ce tayi ringing ganin sunan jawaher da sauri ya ɗauka yana tashi zaune ƙarawa yayi a kunne cikin tashin hankali yace '' jawaher lafiya kike kuka me ya faru..?, ci gaba da kuka tayi tace '' wani mugun mafarki nayi wai kai min kishiya wallahi Jawad da kai min kishiya gwara na kashe ka na kashe kaina bazan iya jure ganin ka , kana mu'amala da wata mace bayan ni , babban abin tashin hankali yadda na baka yarda ace kaci amanata Jawad bansan irin son da nake maka ba.., a hankali ya juya ya kalli NAJLAH da take bacci cikin kwanciyar hankali zuciyar sa ce tayi wani irin rawa tashi yayi ya buɗe kofa ya zauna a kan luxury sofa yace '' Jawaher kinsan dai mafarki ba gaskiya bane..? akan kinyi wannan mafarki sai kuma duk kibi ki ɗaga hankalin'ki karfa ki manta ni mijin mace hudu ne idan naga zan iya har nayi kwarkwara..., wani irin zabura tayi tace '' sweet wallahi da kuwa ka sake ka aikata haka ka , wacce ka auro ka faɗa mata ta fara kirgen ranar mutuwar ta wallahi Jawad bazan iya jurar ganin ka da wata ba me na rage ka dashi duk wani farin cikin ka ina ƙoƙarin na baka shi, JAWAD ka dinka tuna baya..., murmushi yayi yace '' Hassim zan tuna ko me.., wani sauti cikin ta yayi ta shiga cikin ruɗani lokaci ɗaya tamkar tana gaban sa cikin dari dari tace '' sweet na kiraka Ka kwantar min da hankali bawai ka ɗaga min hankali ba.., dan murmushi yayi da ya tsaya iya kan lips din sa yace '' okay yanzu dai ki koma baccin ki, to kai min alkawarin duk wuya duk rintsai ba zaka guje ni ba ko da ace wani ne ya kawo maka aibuna zaka toshe hanyar nan ka nuna mai yardar da kayi dani ba zan taɓa ha'intar ka ba a ko da yaushe ka zamo me yafiya mijina...... Shiru yayi yana nazarin kalaman ta sannan yace '' jawaher akwai wani abu da kike ɓoye min ne ...?kike wannan zance sanin kan kine ina son ki ina kaunar ki me zai saka na juya miki baya idan kema ba juya min baya kikai ba.., ajiyar zuciya ta sauke me karfi sannan tace '' HONEY ba abin da nake ɓoye maka kawai dai na faɗa ne kasan dan adam tara yake be cika goma ba duk abin da kaga baka so a shirya nake ka fadan shi ni kuma zan gyara ina kaunar ka mijina.., Murmushi yayi da har sai da wushiryar'sa ta fito yace '' nima ina sonki Allah ya bar mu tare.., amin ya Allah dare yayi ka huta lafiya.. kema haka ya faɗa yana kashe wayar tashi yayi ya koma dakin ya kwanta kwantar da Najlah yayi a jikin sa ya rungume ta yana shakar daddaɗan turaren ta wanda har yau ya kasa tantance wanne irin kamshi yake yi gashi da kama jiki shekaran jiya ma kayan sa gaba ki ɗaya kamshin turaren ta yake. haɗe bakin su yake ƙoƙarin yi sai dai ta kasa bashi damar haka duk da tana cikin mayen bacci akwai abin da take iya fahimta kuka ta saka mai kamarin sauti tana matsar da kan'ta. kura mata ido yayi ya saka hannu ya matsar da gashin ta da ya rufe mata fuska , lokaci ɗaya tausayin ta ya durar mai gyara mata kwanciya yayi, tashi zaune yayi ya dafa kan'sa da yake tsakanin sara mai , yana rikon Ubangijin da ya bashi juri da hakuri abin da yake ganin ko giyar wake ya sha ba zai taɓa aikawa ba ko kallo be ishe shi ba sai gashi lokaci ɗaya zuciyar sa na neman bijirewa daga kan tsarin da ya dasa ta , duk da waccan din zabin rabin jikin sa ce be ƙi ba ya amshe ta yana fatan ta zame mai alkairi cikin rayuwar sa , wannan fa wata zuciyar ta yi mai wannan tambayar bashi da amsar bayar wa dan haka yaja bakin sa ya kulle. wayar sa ya duba karfe uku saura cije lips din sa yayi tabbas idan ya ci gaba da zama haka batare da ya nemawa kan'sa mafita ba akwai matsala tamkar me amfani da wani magnet inhar zasu kasan ce inuwa ɗaya tabbas mafarkin rayuwar sai ya canza salo duk kan wani gini da yayi sai yaji yana rugujewa tamkar ba da kyakkyawan tubali ya gina shi ba. yana so ya koyi sarrafa rayuwar sa ba tare da an sarrafa mai ita ba ta hanyar bashi doka da oda tun daga bayyanar ta yake tunanin komai zai sauya ashe ba haka bane rayuwar dadin da yayi a baya zata juya ta zame mai ruwan zafi duk da a wani ɓangare tana nan a matsayin ta be canza mata ba guri ba a duk lokaci da ya ɗaga ido ya dube ta sai yaji wani irin matsanancin farin ciki....... ada yana tunanin ba wanda ya fishi sa'a amma a yanzu komai ya rushe abubuwan da yake kallo sune hasken rayuwar sa ashe ba haka ba ne wa'yanda yake tunanin sune dubu a rayuwarsa kafin bayyanar ɗaya daga cikin dubu ashe su ne hasken nasa me ya saka rayuwa ta zaɓi tayi mai a haka shin wai shi bashi da Sa'a ne ko me rintsai ido yayi ya cije lips din'sa tunani na shirin haukata mai rayuwa inhar be bar sa ba dawowa yayi ya kwanta tare da canza salon kwanyar tasu. a zafafe yake yin komai da yake baya cikin hayyacin sa. a wannan lokaci kuka ta saka da karfin ta saboda yafi na jiya ciwo ganin numfashin ta yana fusga ga kuma lalurarta sai ya dakata tashi yayi ya dauki key din sa da wayar sa ya bar dakin. Lokacin karfe hudu tafiya nasa part din yayi, ya shiga toilet ya sakarwa kan'sa shower kifa kansa yayi a bango yana jin yadda ruwan sanyi ke ratsa kan'sa wani irin ciwo da radadi zuciyar sa ke masa , wanda bashi da masaniyar me hakan ke nufi wasu abubuwa yake hangowa dafa Glass shower cubicle yayi zuciyar sa na tsananin bugu dakyar ya karasa wankan da yake lokaci ɗaya zazzaɓi da ciwon kai suka rufar mai. buɗe wata haddiyar Glass door yayi fararen towels ne jere sai kamshi Shaghaf oud by Swiss Arabian suke ɗaukan ɗaya yayi ya daura sannan ta dauki na tsane kan'sa ya fito zama yayi a dressing mirror dauko *RITUAL HOMME 24H HYDRATNG* ya shafa tashi yayi ya buɗe wardrobe dinsa ya dauko jallabiya feshe jikin sa yayi da turaren Musik Maqam addu'a yayi ya kwanta bacci karfe biyar da rabi dai-dai ya tashi da sauri ya shiga toilet ya dauro alwala ya fito a cikin sassarfa yake taka stair case domin an kusan kiran sallah. dakin Najlah yaje yayi knocking tamkar da dutsai yake ko motsi ba tayi ba jan ƙaramin tsaki yayi ya kalli agogon hannun sa besan ko ta fara sallah ba amma bara yaje ya dawo yau ba zai zauna zaman har sai rana ta fito sannan ya dawo, da yake dazu ko da wasa be kallo kasan ta ba balle yasan halin da take ciki....... duk bidiran yayi, yi asama yayi shi. tafiya ya fara yana tasbihi a cikin ransa sai dai ka kula sosai sannan zaka ga yana motsa bakin sa. ana idar da salla ya dan jima kadan sannan ya taso duk zaman da yayi tana ransa yana shigo ya buɗe dakin ko sallama be tsaya yi ba samun ta yayi ta haɗa kai da gwuiwa tana kuka jin motsin sa da sauri ta taso ta rungume shi tare da sakin wani kukan har da shashsheka idanuwanta yayi jajir haka fuskar'ta ma abin ka da farar fata. cikin tashin hankali ya ɗago fuskar ta yace '' Najlah me yake faruwa baki da lafiya ne..?, ba bakin magana kai ta girgiza mai domin bata san ta yadda za tai mai baya ni ba. kamota yayi ya riƙe hannun ta suka fito daga cikin dakin bataimai gardama ba ta bi shi har dakin sa zaunar da ita yayi a kan gado sannan yace '' ki faɗa min me yake damun ki, kinsan ba abin da na tsana sama da ina yi wa mutum magana yayi shiru.., ƙara fashewa tayi da kuka tayi ƙasa da kan'ta zamewa tayi ta zauna akan carpet. taci gaba da kukan ta zuba mata ido yayi yaga iya gudun ruwan ta, tashi yayi ya fara shiryawa domin tafiya aiki yau akwai cases da dama a gurin sa dan haka insha'Allahu takwas a court za tayi mai... ganin yana ƙoƙarin cire kaya da sauri ta kurawa kafar wandon ta ido tana ci gaba da kukan ta. tashi tayi ta fara tafiya tana murza idanuwan ta tana ci gaba da kukan ta dakatawa yayi da saka wandon sa yace '' NAJLAH.., juyowa tayi hawaye na ci gaba da bin fuskar ta , tamkar an buɗe fanfo miko mata hannu yayi a hankali ta kalli gaban rigar ta ashe a bude yake kuka ne ya ƙara kwace mata ganin kusan botira uku a buɗe kuma na saman wuyan ta wajejan kirjinta miƙa mai hannu tayi ta karaso gunsa riƙe hannun ta yayi ya zaunar da ita kwantar da murya yayi yace '' yanzu NAJLAH kuka kika zaɓa akan ki faɗa min me yake damun ki, idan ni ba ki dauke ni a matsayin dan uwa ba ina wayar ki kirawo Aliyu ko taufiq ko aunty rafi'at ko aunty Hafsah ko MUNEEF ko saran family wa'yanda kika dauka yan uwa, wa'yanda zaki iya sharing farin ciki ko bakin ciki ko kuma ga tawa wannan kirawo wanda kikai niya.., ya ƙarshe maganar sa yana ajiye mata wayar sa a kan cinyar ta kuka ta fa tashe da shi tana girgiza kai kifa kan'ta tayi a kan gado cikin dashewar murya saboda kukan da ta yi tace '' kayi hakuri yaya ba haka nake nufi ba bansan yadda zan maka baya ni ne wallahi bazan iya ƙara kwana a cikin gidan nan ba kirjina ciwo yake min haka lips din'na duk sun kumbura suna yi min zafi baki na wani irin kamshin mouth spray yake kullum cikin dare kamar ina baby feeding...two day's kenan.., tamkar be san me yake faruwa ba ya dan shiga tunani na wani lokaci sannan yace '' baby feeding fa kika ce..?, cikin dare ake baki yara kike basu abinci suna da girma ko basu dashi yan shekara nawa ne..?, kanta ta dago tana kuka tace '' bafa yara bane kamar babba ne yana taɓa min breast din'na.., kai ya jinjina yana tunani sai kuma can yace '' daman kina da breast, kallon sa tayi sai kuma kunya ta kama ta ƙasa tayi da idon ta dan murmushi yayi yace '' okay kina addu'a idan zaki kwanta..?, wallahi har alwala nake yi amma baya fasa zuwa kuma anan gidan na fara haka dan Allah ka mai dani gurin Hajiya ta wallahi bazan iya ba ciwo yake min sosai... okay mu gani ina ne yake miki ciwo JAWAD ya faɗa yana tsare ta da idanuwan'sa. da sauri Najlah ta ɗago ta turi bakin ta tace '' a'a ba sai ka gani ba.., kai ya jin jina yace '' yau ina tunanin zan tafi Yola akwai case din da nake bincike acan ina tunanin zani gida baki da abin da za a tawo miki dashi..?,ina tunanin zan iya kwana uku zuwa biyu.., Ihu ta saka tare da buga ƙafafuwan a ƙasa kamar wata ƙaramar yarinya tace '' dan Allah ka tafi dani kar ka barni wallahi bazan iya kwana ni kaɗai ba a gidan nan yayi min girma dan girman Allah ka tafi dani yaya.., kura mata ido yayi tabbas NAJLAH yarinya ce a ko yaushe wautar ta da yarintar ta ƙara fitowa suke ga uwa uba kuruciya da take diban ta ban da haka mene na wani yin buri har da buga kafa a ƙasa , bayan yanzu ta gama kuka yanzu kuma ya dena ta manta da wannan maganar dauke idon sa yayi yace '' idan kuma da gidan kine ya za kiyi kike cewa yayi miki girma bakya ganin bake kaɗai bace akwai cleaner's akwai security ba abin da zai cutar da ke idan ba ikon Allah ba.., yaya to ai kaga ban girma ba idan na girma nayi gida sai na kwana ni kaɗai amma dan Allah ka tafi dani.. haɗe rai yayi domin ya lura ta mai da maganar sa wasa yace '' ba inda zani dake au shi ya saka kike taɓa kenan ke har yanzu baki girma ba amma ai kin iya soyayya har kike zabar wanda zaki aura.., Kuka ta fara tace '' wallahi ba saurayina bane shi ɗan Allah kayi hakuri ka tafi dani...bazan iya zama ba ni kaɗai ba .., Oh kenan idan kika tashi aure me mata zaki aura..? shiru tayi bata ce komai ba tashi yayi yace '' ki fita zan shirya na riga da na gama magana.., fita tayi a guje tana kuka tana shiga dakin ta kayan ta , ta soma haɗawa a trolley din'ta hijabi ta saka idan taje gida tayi wanka ko wanke fuskarta ba tai ba duk jirwayen hawaye jin alamun saukowar sa da sauri ta fito tana jan jakarta tana nishi... turus yayi haɗe ran'sa yayi ya daka mata tsawa ihu ta saka mai ta durkusa ƙasa tana hawaye haɗe rai yayi yace '' ga kudi nan akan dining idan kina da bukatar wani abu sai kiyi amfani da su idan sun yanke miki kiyi min magana zuwa jibi zan dawo..., banza tayi mai tana kuka ganin bata da niyar magana ya dauko bandir din kudin ya ajiye mata a kusa sa da ita ture kuɗin tayi tana ci gaba da kuka ce mai a kayi tana bukatar kudi zai bata, tafi son zuwa gida... ajiye briefcase din'sa yayi ya lura idan be tauna tsakuwa ba domin aya taji tsoro Ba zata denai mai wannan iskancin ba yawa wata yarinyar goye daukan cable din caza yayi yayo kan'ta da sauri ta tashi amma bata bar gurin ba duk tabi ta wahalar da kan'ta tausayin ta ne ya kama sa. zama yayi yace '' zo., hawaye ta goge tace '' dan Allah kai hakuri ka tafi dani.., kizo na miki... Ko ranki ya ɓaci. zuwa tayi tana raragefe duban agogon'sa yayi yace '' ki gyara gidan nan zuwa karfe uku zan dawo sai mu tafi zan mana booking na jirgi ayanzu office zani.., kallon sa tayi tace '' dan girman Allah da gaske kake...?, na taɓa faɗa miki karya ne kina ɓatan lokaci NAJLAH. da sauri ta tashi tana jin dad'i tashi shima yayi ya dauki briefcase din'sa cikin jin dad'i tace ''a dawo lafiya Allah ya tsare hanya ta bada abin da ake nema.., murmushi yayi ya girgiza kai ya fita yana fita ta dafa indomi taci Sannan ya yi wanke wanke abincin da taci jiya ta ajiye ya lalace. zuwa tayi a cikin dustbin harta saman sa sai da ta gyara ta dawo ƙasa dakin Jawaher ne dai bata taɓa ba, ba ruwanta wanka tayi ganin jinin ya ɗauke tayi wankan tsarki ta fito shiryawa tayi cikin wani material milk colour da adon flowers gold rigar bubu ce da wando falazo. Lokacin karfe ɗaya sallah tayi ta zauna tana kallon agogo a hankali ta furta lokacin ma , baya sauri. kwanciya bacci tayi da yake bata jin yunwa ɗaukan wayar ta tayi tana charting basma CE tayi mata magana Mutanen abuja ganin ko sai ancike form da wowar ku, kuwa sai baba ta gani. dariya NAJLAH tayi da taga wannan messages din shiga tayi ta tura mata sticker dariya 😂🤣 bata ce komai ba kashe datar ta , tayi ta kwanta bacci ne ya dauke ta. ƙarfe 3:02 ta tashi da sauri ta kalli a gogo jikinta ne yayi sanyi tana tunanin anya kuwa zai zo zuba ta gumi tayi jin karar buɗe get da sauri ta fito harabar gidan tun daga nesa ta hango shi washe baki tayi tana murmushi ma'aikatan gidan zuwa sukai suna mai sannu da zuwa ƙarasawa tayi tana biye dashi a baya ne nuna ya ganta ba suna zuwa wajen kofar da za ta sada su da parlour gidan ya janyo ta ya shigo da ita cikin faɗa yace '' NAJLAH bansan wanne irin kunne ne da ke ba wallahi bakya ji yanzu haka kika fito ba kunya duk yawan mazan da suke gidan nan kika ratsa su kika tsaya a bayana NAJLAH gadi na aka baki bani da labari ne wallahi sai na fasa tafiyar dake inga ta tsiya.., kwalla ce ta taru a idon ta , tace '' dan darajar annabi kai hakuri na dena wallahi.., Banza yayi mata ya zauna yace '' kawo min ruwa.., da sauri ta shiga kitchen ta dauko mai durkusawa tayi tace '' gashi yaya..., amsa yayi yana cewa dauko kayan ki kala uku ki tawo.. tashi tayi tane cewa ina da wasu a can. Okay idan za mu dawo kya kwaso su akan me zaki ajiye musu shirgi , da sauri ta kalle sa idanuwanta sun taru da kwalla tace '' shikkenan na bar gidan kenan...? idan aka bada hutu bazan dinga zuwa hutu ba shi ya saka na bar kayan acan.., kallon ta yayi, yayi wani murmushi na gefen baki yace '' ehmn kin bar gidan ke da zuwa gidan sai dai ziyara kin zo nan kenan mu biyu a cikin gidan nan yayi mana yawa gwara mu ƙaro wani mu zama mu uku tun da Allah be bamu yara ba.., da sauri ta kalle sa sai hawaye shar shar ya soma bin fuskar'ta ta kasa ma magana.. sakar baki yayi yana kallon ta yace '' Najlah zama da nine bakya so kome..?, juyawa tayi tabar gurin toilet ta shiga ta wanko fuskar ta ta saka hijabi ta fito cikin shirin ta shi kuma lokacin ya sauko daga sama cikin farar shadda gezner an masa dinkin babbar riga ya saka bakin glasses aikin jikin ta ma baki ne dan haka adon wular sa ma akwai baki a jiki takalmin sa Hermes shima baki da sauri tace '' na manta ba dauko wayata ba..ina zuwa.., da sauri ta shiga cikin dakin ta dauko jaka ta saka wayar ta , ta zuge zip din ta rataya ta. fitowa tayi ta tace yaya ganin bata gansa ba a guje ta kwasa yana tsaye a kusa da da dining room yana kashe fitilun dakin da sauri ya kalle ta , yace '' NAJLAH.., juyowa tayi tana dariya tace '' na zata ka tafi ka barni.., girgiza kan'sa yayi yace '' Allah ya shirye ki..., tsayawa tayi ya karaso kallon luggage din'sa tayi tace '' yaya kwanaki da yawa za muyi kenan..?, a'a akwai takardu a ciki na fada miki bincike zai kai ni za kuma muyi meeting. kai ta gyaɗa kai tayi tana turo baki. Fitowa suka yi ya kulle kofar parlour shigewa gaba yayi tana binsa a baya direban da zai kai su airport tun dazu yake jiran sa yana ƙarasowa da sauri ya bude masa kofar baya shiga ya fara yi sannan sai NAJLAH kullo kofar yayi cikin sauri ya shiga yayi wa motar key tuni me gadi ya wangale musu gate hawa kan titi suka yi suka fara sharara gudu har suka isa airport NAJLAH sai murmushi take bakin ta yaƙi rufuwa fitowa suka yi yayi sallama da driver suka shiga reception tararbar sa suka yi cikin mutuntawa da yake sun san sa fuskar sa ba boyayyiyar fuska bace sosai NAJLAH tayi mamaki yadda suke mutunta shi. Checking din kayan su aka yi sannan suka fara ƙoƙarin fita daga gurin domin hawa jirgi lokaci yayi tamkar daga sama yaji SAN juyowa yayi EMAN ce. tana sanye da wasu arnan riga da wando kurawa NAJLAH idanuwa tayi ta saka wani katon glasses ganin sa ta cire shi kan'ta ba dan kwali sai taunar chingum take ga wani namiji a kusa da ita da alama tare suke kallon ta yayi yace '' eman ya karatu.. murmushi tayi tace '' alhamdulilah ina wuni ya aiki .., alhamdulilah ya hidimar biki Jawad yace yana mamakin EMAN shifa shi ya saka tun farko ya tsani alakar su da Jawaher amma na tuna na mai ba haka ba , ba wanda zai kalli EMAN yayi mata kallon Musulma murmushi tayi tace '' alhamdulilah su Jawaher suna can sun amshe mu ni kuma ina nan ina nana abubuwan ne ya hadar mana da yawa wallahi yanzu ma daga lagos nake akwai oder kayan da muka yo to acan ta sauka... okay Allah ya temaka Amin tace tana murmushi in kiya tayi wa TJ da ido kauda kai yayi yana miƙawa JAWAD hannu gaisawa suke ya tambaye shi ya aiki TJ yace '' Alhamdulillah., masha Allah EMAN tace '' amma wannan sister ka ce kuna kama wallahi.., dauke kai Najlah tayi tana jin tsanar eman a ranta yawa ba musulma ba JAWAD yace '' eh .., sallama yayi musu ya riƙe hannun NAJLAH suka hau jirgi eman kuwa tace '' kut amma Jawaher bata da hankali wallahi TJ kalli yarinyar nan ka gani iya mace ta cika ta tafi gantali ka barta a cikin gidan ta tasan mijin ta ba dutsai bane Allah ya saka na kura bace da fatar akuya suka ajiye mata a cikin gidan ta daga ganin wannan yarinyar yar iska ce kana ga ko kallon inda muke ba tayi ba.., taɓe baki yayi yace '' me ruwan ki da ita Insha'Allahu sai ya karo mata aure dan kuttumar uban ta badai ni za taci amana ba , yau auren su yayi shekara biyu koma sama da biyu amma da yake ita shegiya ce bata san mahimmanci riƙe alkawari ba ai gashi nan ta rashe gindi ta zauna ita da tace min ba zama taje yi ba ki faɗa min auren nan na Jawaher da me ya amfanar dani..?, Wallahi kana da matsala TJ baka da hakuri ko kaɗan yanzu wanne irin abu ne bana yi maka kaman ta da ita muci gaba da rayuwar mu... kedin da kike hannu biyu wallahi ki guji ranar da Ubangiji zai kama ki ke fa nifa wallahi kyankyamin ki nake yi yasin wani kallo tayi mai ba shiri ta tofar da chingum din da yake bakin ta tace '' amma dai kai anyi dan akuya wallahi ni ban ce maka ina kyankyamin ka ba sai ni zaka faɗa min haka good yayi kyau ai na gama buɗe baka kaci ba dare ba rana yanzu kuma ni zaka fadawa haka idan kana kyankyamina uban wa yace maka kazo kayi..., buɗe rigar'sa yayi ya zaro yar karamar wuka yace '' billahilazi ki iya bakin ki ko yanzu lahira tayi baƙuwa dan uwar ki har ni zan dinga magana kina saka baki kin dinga kaza kaza ne ke ga shegiya kina daure mata gindi tana tafiya yawon bariki ku ci gaba da abin da kuke inhar kere yana yawo zabo ma na yawo kar ku canza halin ku shegu yan kutumar uba ni zaki dinga danne wa baki san wani irin abu ne ya cakar min zuciya ba da kika ce sai kin mai magana saboda kin mai dani wanda be san ciwon kan'sa ba da har zan hana ki, kiyi mai magana kice sai kin yi..., tafiya ta fara tabar shi yana ta faɗa, da alama yau ya shata tafi ƙarfin kan'sa. ******** YOLA suna sauka mota ta zo daga gida ta ɗauke su NAJLAH bakin ta , tamkar me tallan makilin sai washe shi take. suna sauka da sauri ta tashi zata buɗe murfin mota rike hannun ta yayi yace '' uwar rawar kai.., a hankali ta zare hannun'ta daga nasa fitowa tayi tana murmushi dai-dai shugowar motar nihilah parking tayi ta fito wani irin harbawa zuciyar ta , tayi ganin Jawad abin so da kaunar ta wallahi jawaher ko za tayi hauka sai ta aure shi ajiyar zuciya ta sauke ta ƙaraso kusa da shi tace '' ya Jawad sannu da zuwa..., ba tare da ya kalle ta ba yace '' yauwa ya aiki.., Alhamdulilah tace tana ƙoƙarin danne hawayen ta ganin hankalin'sa gaba ki ɗaya yana kan Najlah yana miko mata wayar ta da jakar ta amsa Najlah tayi tana cewa aunty nihilah ina wuni.. bata ce komai ba ta juya ta fara tafiya cikin isa tana karkaɗa key din motar ta......... Free pages ya kusan karewa domin shiga paid group ku hanzarta biya ki karanta cikin kwanciyar hankali.... Wannan littafin na kudi ne duk meson 1k amina alhasan Muhammad 8141785374 opay KU TURO DA SHEDA TA WANNAN NUMBER 08141785374. Yan niger 1000fcfah AMINA MUHAMMAD ALHASAN KANO My nita sai kuyi screen shot Ku turo ta wannan number 08141785374 Ina sanar muku akwai complete document na dukka littafin nan 1:.JIKAR MAMMAN COMPLETE DOCUMENT 1K 2:.HAUWA KULU WOMEN LEADER COMPLETE DOCUMENT 500 3:.DESTINY LOVE 400 4:.BINTA YAR JAGALIYA COMPLETE DOCUMENT 300 5:.YAR HANNU A LAGOS 1K 6:.GIDAN MAGAJIYA Complete document 1k 7:.UWAR GAFALALLU COMPLETE DOCUMENT 1K 8:.BAƘIN SHAFI 1K COMPLETE DOCUMENT 9:.YAN ZAMAN MAKKAH 1K COMPLETE DOCUMENT 10:.MU ZUBA MU GANI COMPLETE DOCUMENT 200 11:. KIN CUCE NI 300 Dan Allah idan kinsan ba siya za kiyi ba karki yimin magana duk maganar da za kiyi idan ba receipt evidence na gani ba bazan amsa ba dan Allah mu kiyaye Number iya WhatsApp take yi 08141785374 ban da kira KARUWAN CIKIN GIDA OUMYASMEEN ga channel dina kuyi min subscribe Dan Allah wai ina masoyana suke. https://www.youtube.com/@nasreenminallah https://vm.tiktok.com/ZSBRtRQmN/ EPISODE ¹³ JAWAD kallon NAJLAH yayi ganin ta haɗe rai ya danyi murmushi rufe motar yayi da sauri ya riko hannunta ganin ta fara ƙoƙarin tafiya yace '' ina zaki..?, turo ƙaramin bakinta tayi tace '' gurin hajiya ta.., sai mun fara zuwa gurin jadda. tamkar zata yi kuka tace '' to.., domin ranta ne so ba babban burin'ta ta ganta a kusa da hajiyar ta. tamkar ance kalli sama hango yaya saif tayi a baranda ya sarke hannu wansa a kirjin'sa riga ce armless a jikin sa maroon colour da wando three-quarter milk colour murmushi yayi mata tare da ɗago mata hannu. kallon JAWAD tayi tace '' ya jawad kalli ya saif daman yana ƙasar nan...?, kallon inda take nuna mai yayi sai kuma ya dauke kan'sa tare da jan hannun ta bata da zaɓi da ya wuce ta bishi. tamkar wasu mata da miji sabon aure ba ƙaramin kyau sukai ba yadda ya rike hannun ta batare da ya cika ta ba suke tafiya cikin nutsuwa da izza. turus Hajiya Sameeerah tayi tana kallon su ta kasa danne mamakin ta da sauri ta juya ta shiga part dinta, tana shiga cikin parlour kan sofa ta dura tamkar an jifota cikin ɗaga murya tace '' NIHILAH NIHILAH NIHILAH, da sauri NIHILAH ta fito daga ita sai towel tace '' aunty ina cikin toilet fa kike kirana lafiya naga ranki a ɓace..?, dauko min ruwa NIHILAH maza dauko min ruwa.. da sauro ta ƙarasa saukowa ta buɗe fridge ta dauko mata ruwa me sanyi har ya fara kankara. shayewa tayi tas ta ajiye robar tace '' wai kuwa kin san JAWAD ya shigo garin nan ashe yarinyar nan a gurin sa take...?, zama NIHILAH tayi tace '' wallahi aunty na gansu har gaisawa mu kayi ashe daman tana gidan sa abin nan ya ban mamaki wallahi to me jadda yake nufi ne kinsan fa shegen tsohon nan wallahi shirun sa ba alkairi bane ba... kaf dangin nan wa yake bari ya tafi wani gurin yayi karatu..., cikin mamaki HAJIYA SAMEEERAH tace '' karatu kuma.., sauka tayi daga kan hannun kujera tace '' aunty karatu mana nasan da karatu za su fake su gina wani rami ke wallahi wannan makarkashiya ce akwai manufar yin haka..., hannunta ta daga ta tafa tace '' tabbas haka ne, hmmm amma idan sun san wata ai basu san wata ba kinsan wannan rawar kafar da farida take yi take kafafa ita ta raine shi ba mamaki yanzu haka so take ta bashi wannan yarinyar ta gaban ta , tunda ba wanta a gaban ta.., kuttumar durin uwar nan lallai da anyi gagarumin bala'i cikin ƊAN BUZU lokacin da zai auri Jawaher kowa yasan ina son sa amma da yake waccan m kafar katafilar tazo aka ce abata damar ta yanzu kuwa wallahi dole nice zan aure shi kuma daga ni ba ƙari aunty.... ta gumi Hajiya Sameeerah tayi ta lula duniyar tunani mafita kawai take nema amma ko wacce hanya tabi a rufe ruf ba kofa ko ɗaya. ******** bangaren JAWAD kuwa suna shiga babbar parlour jadda bakin su ɗauke da sallama ambassador Mukhtar HASHIM BUZU ya ɗago da kan'sa da yake ƙasa ya kalli kofa lokacin Jawad ya sako kafar sa four eyes suka yi tabbas buri yayi kama da mutum dole ya ga Saif a cikin gidan nan ba mamaki tare suke da shi Lokaci ɗaya zuciyar sa ta harsaso mai wannan maganar saurin kawar da ita yayi jadda da yake kishingiɗe da sauri ya tashi zaune fara'ar fuskar'sa da annurinta sun ƙara daduwa cikin tsantsar farin ciki yace '' zo nan jikata welcome when did the beautiful queen arrive ...? karasowa tayi kusa dashi ta zauna tace '' jadda barka da lokaci.., jan kumatun ta yayi yace '' barka dai ja'ira duk kin bi kin cinya wa Jawad abinci gashi nan kamar ana wura miki iska.., murmushi tayi tace '' kai jadda ni nafi son zaman nan.., murmushi yayi ya kalli Jawad da ya tsaya a tsaye tamkar an dasa shi yace '' kai kuma aikin soja ka koma bani da labari..? ka wani tsaya kamar ka ha ɗiyi sanda aṭṭas, as-ikka, illa gesegh.., ya ƙarshe maganar cikin yaren Tamashek (wato yaren buzaye..) Najlah cewa tayi daddy barka da wannan lokaci. Murmushi yayi yace '' barka dai ya karatun..?, wasa ta fara da yan yatsunta tace '' bamu fara ba.., tashi yayi yana cewa to Allah ya saka ku fara a Sa'a.. amin tace kallon jadda yayi yace '' jadda ka huta lafiya.., kai kurum jadda ya gyaɗa mai kai ya tsare JAWAD da har yanzu ya kasa zama sai a lokacin JAWAD yace '' JADDA asi, ha-nna yan umidag iyyan. Ul iyyi ad awid, ad yokh, ghas ayit. Meyaɣ!" dariya JADDA yayi yace '' ni na isa na yi maka yan ubanci Najlah tare ta gan mu zo ka zauna a kusa dani ina zan kai wannan fushin haka.., dariya yayi ya ƙara so sun kusan gware da ambassador Mukhtar dan Allah ya rufa asiri JAWAD ya ba shi hanya. zama yayi Najlah tashi tayi tace '' jadda ka huta lafiya ni zan tafi gurin hajiya ta.. bazan amsa ki ba wato kin zama bahaushiya ko....? kin manta da asalin ki tun ɗazu ina yi miki Magana kina bani amsa da harshen Hausa. murmushi tayi tace Insha'Allahu zan gyara.., uhmmm kin koma ga cuku nan ko kin manta dashi ne..? kai ta girgiza ta dauke shi a cikin akushi me kama da bowl chokali ɗaya tayi ta limshe idon'ta tace '' masha Allah yayi dai-dai yasha zuma jadda...anni ce tayi ko...?, murmushi yayi yace '' ke idan ba ita ba wa kike ganin zai iya wannan duk kun ruga da kun bar al'adar mu daga shawarma sai pizza kuka iya ci shi yasaka ga kunan kuke saurin tsofa idan kunji ana abinci ka maganin ka to abincin gargajiya ake nufi ba dangin fulawa ba kayan basir.., dariya tayi tace '' jadda kenan Allah ya bar mu dakai.., limshe idon sa yayi ya cire farin glasses ɗin sa yace '' hmmm najlah shekarun da nayi a baya bazan taɓa yin su a yanzu ba kullum girma da ɗa cinmun yake ina ƙara kusanta ga Ubangiji sai dai fatan dacewa da rahamar Ubangiji kullum dai addu'ar da nake yi Allah ya nuna min karshen warware war komai duk kan wani bara gurbi ya zama tarihi bakin shuni ya ɓace da ta dawo yanzu.., Uhmmm jadda na tafi bazan iya da wannan zancen naka ba , wannan tsoho kaji hausa ga yadda kake shigar da hausa cikin hausa kamata yayi shashin hausa na jami'ar Bayero ya baka award. dariya yayi yace '' ja'ira ina ne ban zaga ba tun da nayi suna a kano ai kuma zance ya ƙare duniya ta san da zamana magana ake fa ta babban dan kasuwar haƙo ma'adanan ƙasa.., fita tayi tana cewa ni dai na tafiya jadda idan na biye maka sai mu kwana kana ban labari bayan baka zauna a kano ba sai ka kwaso jiki ka dawo Yola.. Kaniyar ki Najlah da ban dawo yola ba ai sharif na zai ga farida ba yace yana so ga inda muka fi kusancin yare dasu ina ni ina zama cikin hausa zalla duk da fa kanawa mutane ne ba garin da zaka je ka zauna ba a damu da rayuwar ka ba ko da kuwa kai ka , kawo kudi duniya sama da kano ta dabo.... hannu ta ɗaga mai tace '' na tafi kayi da yaya.., murmushi yayi mata ya mai da hankalinsa kan jawad yace '' Jawad abin da kayi ka kyauta kenan...?, kallon mamaki yake wa jadda nashi yana tunanin me yayi cikin danne mamakin sa yace '' jadda me ya faru...?, ungo nan ya yi mai dakuwa. gyara zama yayi yace '' jadda na tawo da takardun nan fa.., yayi maganar da nufin kaucewa maganar da jadda yake son yayi mai. a'a barsu a gurin ka ni nan ba abin da za su yi min. cewar jadda. JAWAD yace '' to shikkenan zan cigaba da ajiye su, uhmm yayi haka ya iyalin naka da fatan dai kowa lafiya qalau...? ajiyar zuciya ya sauke yace '' kowa lafiya qalau..., badai wata matsala ya ajiya ta.. ɗago kan'sa yayi yace '' jadda kana ji da wannan ajiyar taka.., dan murmushi yayi yace '' tabbas ina ji da ita idan lokaci yayi na sanin amfanin ta zaka sani duk da kai ma nasan zaka fahimci hikimar yin haka.., jadda matsala fa.. dafa kafaɗar sa yayi yace '' a'a muna neman tsari da ita Jawad ka zama namijin mazaje mana kamar yadda kirar jikin ka ta nuna to zuciyar ka ta nuna haka ka dena saurin karaya da sauri baka da rauni akan abubuwa amma akan wannan maganar kana da saurin nuna raunin ka wacce aka ta ya kamata ace ka tsaya ka zama gwarzo..., ganin suna wannan zancen cikin zancen na kwaso yan matan kafafuwana nace ba dani ba gaɗa a lahira to ba abin da nake fahimta. nace ke oumyasmeen gwara kiyi gaba ko kya samo wani labarin.. *********** NAJLAH kuwa tana shiga part din su ta ajiye bowl dinta akan center table saboda motsin Hajiya da tayi a kitchen saɗaɗawa tayi ta shiga ta rufe mata idon ta Hajiya murmushi tayi tace '' Najlah cika min idona bana son sangarta sai kace wata ƙaramar yarinya.., cika ta tayi cikin shagwaɓa ta turo bakin ta , tace '' ban tsoratar dake ba ...?, ban sani ba ke kin isa ki tsoratar dani kai Hajiya ban da cika baki.. Uhmm sai kiyi ta faɗa tana kashe gas tare da mai da murfin tukunya. Hajiya ta me kike dafa mana...? Ko baki san da zuwan mu ba yaya be faɗa muku ba ...? cewar Najlah.. Hajiya tace '' to yar jarida ban sani ba zo ki bar nan gurin, fita tayi tana dariya zama tayi akan kujera ba jimawa Hajiya ta fito kallon bowl din hannun ta tayi tana ajiye flask akan dining tace '' a'a ina kika samu cuku...?, jadda ta bata amsa tana ci gaba da sha.. ƙara sowa tayi ta zauna tana ƙare mata kallo gaban ta na faɗuwa ganin kallon da take mata tace '' Hajiya da gaske ne kema kinga kibar da jadda yake cewa nayi...? ni dai nasan ba wata kiba nayi ba , saboda ban da zama cikin fargaba ba abin da nake bana son zama a gidan yaya wallahi.., haɗe rai tayi tace '' ai sai ki cire hijabin da jakar tunda ba wani zai daukar miki ba.., murmushi tayi ta cire Hajiya tace '' jiki kitchen ki ƙarasa dauko min kayan abinci ki kai dining .. tashi tayi tana ajiye bowl din hannun ta da kallo Hajiya tabi kugunta da shi ajiyar zuciya ta saki me nauyi wani irin sanyi ne ya ratsa ta ganin abin da take zargi ba shi bane ba.. bayan ya gama kai wa ta dawo ta zauna tana cewa Hajiya miyar nan da kifi sadin kika yita ko..? kallon ta tayi tace '' eh me ya faru.., wallahi zuciya'ta tashi take yi, kifin badai karni ba.. gaban Hajiya ne ya fadi tace '' ke duk irin kayan kamshin da na saka anya kuwa lafiyar ki qalau Najlah...?, dariya tayi tace '' kai hajiya wallahi lafiya qalau nake, ni dai bazan ci ba Allah ya saka jadda ya ban cuku.., ta gumi tayi tana sauke ajiyar zuciya kullum zuciyar ta cikin zulimi take bata da iko da tuni ta dakatar da komai duk da abin da suka yi shi ne dai-dai suna da ikon yin komai.. Hajiya Hajiya firgigit ta ɗago ta kalli NAJLAH tace '' na'am.., Hajiya tunanin me kike ne ina ta kiran ki baki amsa ba Wayan cewa tayi tace '' ba dole nayi miki shiru ba kece idan kika fara kiran mutum tamkar makauniya.., dariya tayi tace '' ina abbana yake..., yana cikina, na boye shi aikin san yanzu lokacin dawowar sa ne.. Hajiya ta faɗa tana jefawa Najlah harara. tashi Najlah tayi tace '' wallahi nayi missing dakina hajiya ina key yake na buɗe.., ke zo.., zuwa tayi ta zauna a ƙasa tana kallon hajiya, dauke kai Hajiya tayi tace '' me ya faru kika dawo..?, Hajiya bani kaɗai bace ni da yaya ne dan Allah hajiya ki saka baki kar na koma gidan yaya wallahi bana son zama.. hade rai tayi tace "' shi ya saka kika bar kayan ki ko..? to da su zaki koma ko dan kwali ban yarda kin bar min ba a cikin gidan nan ba.." kuka ta saka ta kwantar da kan'ta a kafar Hajiya shafa bayan ta , tayi tace '' Najlah me ya saka bakya son zaman can naga dai yaron nan ba dukan ki yake ba balle zagi amma duk kin ɗaga hankalin ki sai kin dawo nan.., cikin shashsheƙa tace '' wallahi bana son zama yaya ya fiye faɗa matar sa yar hulakanci ce .., murmushi tayi tace '' kina yin rashin ji ko..? najlah me son ka ne fa zai faɗa maka gaskiya ita kuma matar sa , yau da gobe zata hakura har ku saba da ita.., share hawaye tayi tace '' Hajiya aunty Hafsah bata faɗa miki ba..?, ɗago haɓarta tayi tace '' a'a me ya faru.., hawaye ne ya ƙara zubo mata daga cikin idanuwan'ta tace '' kirjina ke min ciwo.., subbanallah me ya faru kin faɗawa Jawad .. na faɗa mai amma yace na ɗinga addu'a.. ajiyar zuciya ta sauke saboda sam bata kawo komai a ranta ba ta zata ciwon kirji ne wanda ta sani tace '' ya faɗa miki gaskiya domin addu'a ita ce gaba da komai.., kwantar da kan'ta tayi tana jan ajiyar zuciya... TAUFIQ ne ya shigo da sauri ta tashi tare da rungumshe shi cikin farin ciki ashe ba shi kadai bane tare yake da JAWAD dakyar ya iya ɗaga kafar sa ya shigo da ita cikin parlour durkusawa yayi yace '' Hajiya ina wuni na same ku lafiya.., Cikin farin ciki da sakin fuska tace '' lafiya qalau alhamdulilah ya iyalin naka..?, tashi Jawad yayi ya zauna a kasan carpet yace '' lafiya qalau alhamdulilah..., Masha Allah ko ba tare da ita kuka zo ba..? Wannan yarinyar ta zo ta tisa ni gaba da kuka.. murmushi yayi yace '' a'a ba tare muke ba nazo wani aiki ne shine na tace ba zata iya zama ita kaɗai ba sai ta biyo ni.., harararta Hajiya tayi tace '' ke dai najlah naga ranar da zaki girma to cika shi kin wani makale mai.., murmushi tayi ta fara tafiya TAUFIQ zama yayi a ƙasa kusa dashi ta zauna Hajiya tace '' Allah ya temaka jawad sai hakuri halin najlah kana ta yi da baki ko..?, a wannan karon kallon najlah yayi sai kuma ya kalli Hajiya yace '' wata ran zata dena ne Insha'Allahu.., hmmm Allah ya saka...... Amin ya Allah cewar Jawad Hajiya kallon najlah tayi tace '' kawo mai abinci..., tashi tayi ta shiga dining room ta zuba mai dai-dai wanda tasan zai iya ci ta kawo mai shiga kitchen tayi , ta dauko mai lemo da ruwa ta kawo mai tashi hajiya tayi TAUFIQ ma tashi yayi yana cewa yaya sai an jima ai kana nan ko..? Insha'Allahu ina nan sai gobe zan fita. to shikkenan ka huta lafiya ya faɗa yana fita najlah gama ajiye mai tayi zata , tafi ya riko hannun ta da sauri ta kalle sa idanuwanta har sun fara tara kwallah. kama kunnen ta yayi yace '' bakya ji ko..? yanzu mene ba wani rungume taufiq..? cikin rawar murya tace '' na dena kai hakuri.., najlah idan ban yi hakuri ba yaya zanyi da halinki. turo baki tayi buge mata baki yayi da sauri ta rufe bakin ta , tana cewa Wallahi yaya da zafi.. okay zo muci abinci.. dago wa tayi ta kalle sa tace '' a'a na sha cuku na koshi.., Jawad yace '' to zauna ki taya ni hira har na gama ci..., yaya hira fa kace ni ban iya ba kuma daman kai ma kana hira naga kullum sai kace baka son surutu.. limshe idon'sa yayi be ƙarasa rufewa ba ya bude tamkar me jin bacci zuba, mata su yayi wani irin yar taji a jikin ta dauke idon ta tayi ta mai da kanta ƙasa. murmushi yayi yace '' to a yanzu ina so maza bani labari.., uhmm uhmmm wallahi ban iya ba ni, ko Nobel bana karantawa. da gaske.. hannunta ta saka a baki tace '' Allah.., uhmm kamar gaske, ai anan kuke sanin komai.. yaya Allah bana yi su basmah ke yi. to shikkenan na yarda ya faɗa yana yin bisimallah. **********ABUJA.. da sauri ta dauki wayar ta da take ringing ganin bakuwar number taja ƙaramin tsaki har ta kusan katsaiwa sai kuma tayi tunanin kar dai samu ne ,da sauri ta dauka tare da karawa a kunne shiru tayi tana sauran'ta salati eman ta saki tace '' na shiga uku me ya kai ki faɗa har ta kai ku da zuwa police tasion..?, zeey tace '' ba faɗa mu kai ba wani Alhaji ne ya turo min da kudi zamu hadu to na saka shi a tiktok wannan posting din da nayi yau kinga na ma rufe fuskar sa da sticker amma Jawaher ta gane shi tayi min magana ta WhatsApp.., cikin sauri eman tace '' ya kikai shiru ina jin ki..?, daga can ɓangaren zeey tace '' ka tsaya ban gama ba idan ma kudin katin ka kake ji ni zan tura maka 50k ka saka kati.., cikin ƙaguwa eman tace '' ci gaba ina jinki kin tsaya dogon bayani.., zeey tace '' to sai take cemin idan ban yarda da shi ba karna yarda dashi yana da HIV ni kuma kinga ya za ayi na yarda dashi, shine nace mai a'a ba bazan iya ba sai yace ban isa ba na turo mai da kudin sa ni kuma wallahi kudin nan babu su babu dalilin su.., innanallahi wainna ilaihir raji'un gaskiya kam amma har nawa ne kudin da kika kasa biya har kika zabi a kai ki prison.. hmm ba wasu fa kudi bane one million ne kuma nacin ye bazan biya ba.. abin da nake so ki kirawo ya hajja yayi magana su sake ni kinsan baya daukar bakuwar number shi ya saka ma ban kira shi ba.. Eman tace '' okay ba matsala amma ita Jawaher ya akai ta san shi kuma hat tayi mai farin sani yana da HIV idan ba suna mu'amala ba.., Zeey tace '' kinga bani da wannan lokacin tunanin ina nan zarni duk ya ishe ni idan na fito mayi magana.., to shikkenan sai an jima okay ta faɗa ta kashe wayar ta kallon maleeka tayi da take fitowa daga toilet daure da towel tace '' maleeka kin ji abin da ya faru an gama zeey wai kuma abin da yake daure min kai JAWAHER ce tace mata mutumin yana da cutar HIV ita ya akai ta sani idan har ba tana mu'amala da shi ba.. cire towel din tayi ko kunya bata ji haihuwar uwar ta ta buɗe wardrobe tace '' ya kike bani wani labari a juye me ya faru Jawaher ce take da HIV ko me..?, haka nake tunani domin kwanaki na ganta a inda ya ban mamaki naje promise hospital na ganta, tana gani na ta firgita.., kan uban can lallai yau akwai gagarumar matsala to karfa mijinta yana zaune ta shafa mai bakar ƙaddara..? hmmm ai wata kila m faruwa ta faru yanzu dai kinga nama rasa ta ina zan fara wallahi. cewar EMAN. maleeka ta saka doguwar riga ta zauna tace '' tab akwai chakwakiya fa..?, wata dariya ta sheke da ita har da riƙe ciki kash hmmm hhhhh Da kallo Eman take binta ganin yadda take dariya tace '' ke kuma lafiyar ki qalau..?, wannan fa abin tashin hankali ne duk mutanen ta namu ne.., naki dai ni an faɗa miki ina marke sai me gida biyu maganin gobara ta faɗa tana dukan bayan ta.. ganin ta mai da abin nata wasa tashi tayi ta bude wardrobe ta dauko rigar'ta kimono ta saka dankwalin ta daura akan ta , ta saka jaka tace '' kinga banga ta zama ba bara a fito da waccan shegiyar sai kuma na ga me hali zai yi ai wannan abin tashin hankali ne ina neman tsari da kanjamau..... tashi maleeka tayi tace '' eman yamma fa tayi yanzu ina zaki basai ki kyale ta ba taci uban'ta .., gaskiya maleeka baki da hankali wallahi maganar cin uba ai taci kwana a prison ance miki kwanan gidan uba ne..? zanje naji yadda za a yi amma bara dai na kirawo ya hajja.... toke wanda ake magana kin san sane..?, maleeka ke kinsan mu motar haya ce fa , wannan ya dauka ya sauke ina zan san sa amma mafiya yawanci ai duk mutanen mu ɗaya kuma kinsan halin jawaher badai kwashe kwashe ba wallahi yadda kika san bata son jikin ta kowa ya zo ta buɗa mai..... Wannan littafin na kudi ne duk meson 1k amina alhasan Muhammad 8141785374 opay KU TURO DA SHEDA TA WANNAN NUMBER 08141785374. Yan niger 1000fcfah AMINA MUHAMMAD ALHASAN KANO My nita sai kuyi screen shot Ku turo ta wannan number 08141785374 Kar ku kirani ko kiyi min maganar banza banda rainin hankali sai ku dinga damin mutum da Flashing ko ayi min magan ta WhatsApp maganar banza wani abin ma be shafe ni ba. masu zagina kuma kuci gaba akwai Allah. Ina sanar muku akwai complete document na dukka littafin nan 1:.JIKAR MAMMAN COMPLETE DOCUMENT 1K 2:.HAUWA KULU WOMEN LEADER COMPLETE DOCUMENT 500 3:.DESTINY LOVE 400 4:.BINTA YAR JAGALIYA COMPLETE DOCUMENT 300 5:.YAR HANNU A LAGOS 1K 6:.GIDAN MAGAJIYA Complete document 1k 7:.UWAR GAFALALLU COMPLETE DOCUMENT 1K 8:.BAƘIN SHAFI 1K COMPLETE DOCUMENT 9:.YAN ZAMAN MAKKAH 1K COMPLETE DOCUMENT 10:.MU ZUBA MU GANI COMPLETE DOCUMENT 200 11:. KIN CUCE NI 300 Dan Allah idan kinsan ba siya za kiyi ba karki yimin magana duk maganar da za kiyi idan ba receipt evidence na gani ba bazan amsa ba dan Allah mu kiyaye Number iya WhatsApp take yi 08141785374 ban da kira KARUWAN CIKIN GIDA Ga channel dina kuyi min subscribe Dan Allah wai ina masoya na suke. https://www.youtube.com/@nasreenminallah https://vm.tiktok.com/ZSBRtRQmN/ Domin samun update kuyi following dina https://whatsapp.com/channel/0029VaLdFeg4SpkQ9xyW5c0k Book ¹ EPISODE ¹⁴ Dariya maleeka tayi tace '' Allah ya kyauta.., a fusace eman tace '' ya kyauta abin da yafi haka yar rainin hankali.., ƙasa karawa zancen tayi ganin kiran jawaher da sauri ta ɗauka ta kara a kunne tace '' yar halak yanzun nan zancen ki nake kinga waccan mara hankalin har barazanar kisa yake min.., dariya Jawaher tayi tace '' kizo ki dauke ni ina airport.., zaro idanuwanta tayi tace '' har kin yi me ke da kika ce sati uku za kiyi hmmm ɗazu naga mijinki da yar uwarsa a airport gaskiya jawaher baki da hankali kina da kamar wannan a cikin gidan ki, kika saka kafa kika fita kika basu fili na ganta masha Allah komai yaji dan ma a cikin hijabi na ganta fa.., kinga eman karki batan rai sai anjima idan zaki zo kizo aikin banza Allah ya saka tafi kowa kyau a duniya ita , tayi kan'ta saboda tsabar kyau. dariya tayi tace "shikkenan sai nazo daman fita zan yi.., kashe wayar ta tayi bata tsaya sauraran ta ba , wani irin tururi zuciyar'ta ke mata Jawad ya bar garin da Najlah kuma be faɗa mata ba cije lips din ta , tayi ranta duk a ɓace duk irin kudin da tabarnatar saboda ta faranta mai zuwa fa tayi akai mata virginal rejuvenation shi ya saka ma bata sanar dashi yau za ta dawo ba gyara zaman tayi tana kallon mutanen da suke shige da fice a reception din. zuciyar ta na mata ƙuna duban agogon hannun'ta tayi taja ƙaramin tsaki yawa wacce zata bar garin tun dazu tazo taƙi zuwa...... bata ida zancen ta ba taji tace '' your welcome.., da sauri ta ɗago tace '' haba eman tun dazu nake jiran ki amma baki zo ba.., hmmm na tsaya kiran ya hajj ne zeey tana tsare wallahi yanzu dai zai je ya fito da ita..amma jawaher ke ina kika ji wannan zance..? haɗe rai jawaher tayi ta ɗagawa eman hannu tace '' ban sani ba kinzo ki dauke ni ko kinzo ki tutsiye ni da tambaya..?, hmmm Allah ya kyauta banza jawaher tayi ta shige gaba bata da wani zaɓi da ya wuce tabi ta har suka fito ba wanda yace wa da kowa komai bude mota tayi ta zauna eman ta zauna a mazaunin driver. a hankali ta fara tuki ta saki waka tana bi Jawaher da tayi kicin kicin ta haɗe rai ko da suka hau kan titi ba tayi gudu ba a hankali take tuki ran Jawaher ne ya ɓaci tace '' eman lafiya kike wannan tafiyar...?, juyowa yayi eman tayi tana sakin staring tace '' Wallahi Jawaher baki da hakuri baki ga tafiyar nan nake ba , nasha syrup ne jiki na duk ya mutu haka ma wallahi nayi kokari.., ke kinyi shaye shaye na kirawo ki, kuma ki zo saboda kina so mu mutu tare wai me ya saka eman baki da kai ne wato kaddarar da Allah ya ɗora miki nema sai ya dora min to wallahi sauko ni na tuƙa mu jiki na duk ciwo yake wallahi so nake na huta, ga takaicin da na kwaso a tafiyar nan bafa tare muka dawo ba , sorry zanyi abin da kike so amma me ya faru kika tawo kika bar shi..?, cewar eman. bar tunamin kayan takaici jiya na tafi beach club ina dawowa Sai na tarar da Alhaji da wata baturiya wai har ya ke cewa zai iya rabuwa da kowa akan ta bafa ta fini komai ba , shine naji haushi yau na tawo ni zai raina hankali yabar ganin saboda da kudin sa nake tare da shi ba abin da na nema narasa wallahi Jawad ko a cikin maza shidin gwarzo ne... shiru eman tayi ta yiwa me gadi horn buɗe mata yayi ta danna hancin motar ta cikin gidan take cewa amma to jawaher lamarin ki, yana bani mamaki wallahi. dai-dai ta parking tayi ta fito tare da luggage din ta ta rataya jakar ta security din gidan ne suka zo yi mata sannu da zuwa. amsa musu tayi sama sama tana ji kanta na ƙara girma a hankali take tafiya tamkar wata ɓauna kofar da zata sada ta da part din ta , ta shiga a kulle ta gani bude jakar ta tayi ta ciro ki tana rayawa a zuciyar ta , ta tabbata basa cikin gidan nan to ina suka tafi, kallon eman tayi tace '' yace miki ga inda za ji..?, cikin rashin fahimta tace '' wake nan..?, haɗe rai tayi tace '' wa nake miki magana ban da Jawad..., okay be faɗa ba wallahi yarinyar ma yar girman kai ce wallahi ko gaishe ni ba tayi ba.. buɗe Kofar tayi tana cewa ai yar iska ce ba ta tsotso ba a nonan uwar ta nifa idan na tuna ummi na nan sai naji sanyi a rai na wallahi ummi da kike ganin ta idan har tana raye ba zata taɓa bari jinin farida ya shaƙi iskar yanci ba inhar tana da ikon yin haka kinga kuwa Jawad ko giyar wake ya sha ba zai taɓa gigin cewa zai aure ta ba , shi ya saka ma wallahi ko a jiki na.., ta fadi haka tana tura kofar dakin ta yadda ta barsa haka ta tarar dashi kimono din jikin ta ta cire wasu arnan kaya ne suka bayyana dasu gwara babu rolling din kan'ta tayi a cire tana sauke ajiyar zuciya eman tace '' Jawaher hakan ba hujja bace idan zaki farka ki farka tun kafin dare yayi miki.., cikin tsananin zafin rai tace '' wallahi eman zan ci kuttumar uban ki wai me kike nufu dani ne masifa kike jawo min okay na fahimta wato kina baƙin ciki ina da aure mijina na sona so kike ya sake ni na dawo mu ci gaba da haɗa kafada ina yawo hotel hotel ko..?, dariya tayi tace '' yanzu mene marabar ki da yawo a hotel din me kika fasa ko da kikai auren ina ji ticket kika yanka ma da lasisin KARUWAN CI.., harararta tayi tace '' muka dai yanka aini dake wallahi shiga aljanna sai dai muga ana yi abu nawa muka yi dan haka batun ki zo kina yi min wa'azin banza ki fara yiwa kanki.., Jawaher wallahi dole na fada miki gaskiya ko za ki tsire ni baki san darajar aure ba da ace nice na samu damar ki wallahi zama zanyi inban da ƙaddarar rayuwa me kika nema kika rasa mazan da kike bi ba fin mijin ki suke ba , mazan da kike bi wallahi Jawad ya fisu komai zaman aure ne kika ki yadda kiyi in banda kina so ki halakar da rayuwar bawan Allah nan me zai saka ki dinga bin wasu a waje yanzu ya yaya akai kika san cewa saurayin zeey yana da HIV..?, kinga bani da lokacin ki ta faɗa tana shiga toilet ran eman ne ya ƙara ɓaci hankalin'ta a tashe tuno alkairin da jawad yayi mata arayuwa tayi ba zata bar shi ya kusanci Jawaher ba inhar bata tabbatar da wannan zance ba inda kuwa tana da ita wallahi sai ta fasa kwannan kowa ya san me yake faruwa. ficewa tayi a fusace har taje parlour sai kuwa ta saka hannu a bakin ta ta ciji ya tsanta da sauri ta dawo buɗe dakin Jawaher tayi murmushin mugunta ta saki tana kallon kofar toilet din ta da sauri ta karasa gurin ta murza mata key. cire mayafin'ta tayi ta buɗe bed side drawer bata komai ba haka ta dinga bi tana neme neme amma ba abin da ta gani cikin gajiya ta buɗe lokar ƙasa wasu takarsu ne suka zobo har zata mayar da su idanuwanta suka sauka akan wata takarda da sauri ta ɗauka ciro wayar ta , tayi snapping din ta ta ajiye haɗa su tayi guri ɗaya ta mai da wannan lokaci Jawaher bata san me yake faruwa ba ajiyar zuciya ta sauke tana komawa kofar toilet din tare da buɗe kofar tamkar wanu abu be faru ba ɗaukan jakar ta tayi ta fita daga cikin gidan baki ɗaya. fitowa Jawaher tayi tana tsane kanta da towel kallon ko ina tayi tana ba alamar eman kenan ta tafi ta bawa kan'ta amsa dogon tsaki taja tana zama akan dressing mirror mai ta shafa ta busar da gashin ta , tashi tayi ya buɗe wardrobe ta ciro wata ƙaramar riga ta shan iska ta saka hawa gado tayi tana janyo wayar ta kai tsaye layin Jawad ta kirawo har ta gama ringing be dauka ba. text messages tayi wa ma'aikatan gidan da ta basu hutu saboda bata nan tace ta dawo ta mai da wayar ta ajiye jakar ta , ta buɗe ta ciro magani ballowa tayi ta watsa a baki buɗe fridge tayi ta dauki ruwa ta kora tana kwanta a hankali bacci yayi awan gaba da ita. ******** yaya ni zan tafi na yi wanka ai ba abin da zan maka ko..?, batare da ya kalle ta ba yace '' uhmm kwashe kayan nan.., da sauri ta tashi tana kwashe wa , da kallo yabi bayan ta dashi har ya kulewa ganin sa. tashi yayi ya fita tana kai wa kitchen ta ajiye ta fito direct dakin ta , ta shiga yana nan yadda yake kwanciya tayi tana sauke ajiyar zuciya tayi mamaki ma da ta gansa a buɗe gashi dai tashin kamshi yake rungume pillowcase tayi tana limshe idanuwan'ta. ta jima a haka kafin ta tashi ta shiga toilet kayan ta , ga cire kuwara kirjinta ido tayi gadai shatin hannu a jiki ga kuma nipple's din ta da ya fara tsayi da fadi zama tayi akan Bathtub tana zuba uban ta gumi to ko Hajiya zata nunawa ta gani ne ita ba haka suke ba , ta shiga uku. kuma gashi bata iya tuna komai badan zafi da radadi da take ji. dakyar ta yakice wannan tunanin tayi wanka ta gasa jikin ta , ta dauro towel juyawa tayi ta jawo kofa gaban tane ya fadi lokacin da ta gama kullo kofa ganin Jawad tayi yana danna wayar sa lokaci ɗaya idanuwan su ya sarke dana juna. turo bakin ta tayi tana kokarin komawa toilet yace '' admission din ki ya fito...idan mun koma zan kaiki makarantar ki fito dashi ki nemi yan ajin ku sai kisan yaushe za a fara lecture.., be ida ƙarasawa ba ya ga ta shiga toilet ta rufo abin dariya ya so ya bashi sam hankalin sa baya kan'ta yana duba wasu takardu ne da HISHAM ya turo mai tashi yayi yana wani murmushi me cike da ma'anoni kala kala.... ya fita tana jin fitar sa ta fito tana saka mukulli a dakin ta , tace wallahi yaya ya dena abin da yake haka kurum ya shigo min ba ko sallama kuma ya ganni a haka ko a jikin sa. bayan ta gama kullewa kaya ta saka ta zura hijabinta ta buɗe kofa ta fito ganin ana ƙoƙarin kiran magariba komawa daki tayi daman fa alwalar ta sallah ta tada bayan ta idar ta zauna tana lazumi kamar yadda ta saba jin muryar aunty hafsa da sauri ta juyo tana sakin murmushi da sauri ta tashi ta rungume ta , tana tsalle tace '' Oyoyo aunty na kafin na shigo miki har kin zo..?, ba dole na zo ba auta guda ta faɗa tana zama akan gado cire hajabin ta tayi tace '' dafa yanzu zan shigo miki naga an kirawo sallah sai na zauna ina yi.., naga shiru shiru baki zo ba shi ne nace bara ni na zo.. Najlah tace '' wallahi kuma kina raina.., da kallo aunty Hafsah ta bita hannu ta saka a fuskar'ta tana cewa kai aunty hafsah sai kace na canza muku kama sai kallona kuke ta yi. ta faɗa tana turo bakin ta ajiyar zuciya ta sauke tace '' Jawad ya iya kiwo kin ƙara girma.., ajiyar zuciya ta sauke tace '' aunty Hafsah wallahi bana jin daɗin zama a cikin gidan nan nafi son zama a cikin gidan nan idan ba nan ba to gidan ya Aliyu shi bashi da takurar yaya kuma gidan sa ba aljanu wallahi aunty kirjin ciwo yake min kuma har fa shatin fingers na gani a jiki.., ta ƙarshe maganar tana share hawayen ta. kamo hannunta tayi ta zaunar da ita tace '' kiyi hakuri kinji ko wanne bawa akwai irin tashi jarabawar idan kika saka hakuri da juriya sai komai ya zo miki da sauki wannan damuwar ba abin da za tayi miki sai ma ta ƙara jefa ki a cikin mtsala ƙarshe ki hadu da wani ciwon bayan wanda kike dashi.., wasa take yi da yan yatsunta tace '' insha'Allahu zan dena.., yauwa kanwata kina abin da kuwa nace miki kiyi ..?, da sauri ta dago idon ta da suka fara canza launi zuwa ja tace '' mene na manta wallahi.., cikin mamaki tace '' kin manta fa kika ce min zancen shan fruit.., zan dinga sha wata kila ma shi ya saka be dena zuwar min ba .. cikin jin dadi aunty tace '' ko ke fa yanzu na ƙara karɓar miki wasu a gurin kawata fanna yar barno.., ta faɗa tana buɗe wata jaka bama ta lura akwai jakar ba sai yanzu, zuba mata ido tayi tana kallon ta har ta gama fito da su tace '' wannan tsugunawa za kiyi akan sa.., amsa tayi tana budewa wani kamshi me ya daki hancin ta me dad'i tace '' aunty ai wannan turare ne ...?, ehmn shi akan sa zaki dinga tsugunawa na miyagu ne cewar aunty Hafsah. najlah tace '' ikon Allah daman haka turaren miyagu yake me kamshi a dakina zan dinga turarawa wallahi har kayana.., karɓa aunty Hafsah tayi tana hada rai tace '' najlah ba na wannan bane ga abin da nace kiyi dashi ki wara kafarki sosai hayakin ya shiga ko ina na gaban ki.., karba tayi tace '' to.., dauko wani abu tayi me kamar zuma tace '' ungo shi kuma wannan sha zaki dinga yi.., da sauri ta buɗe ta saka hannu ta lakara sha tayi tace "da dadi kamar dabino..ko?," uhmm shine. ta faɗa tana dauko wani magani a cikin wata kwalba tace "shi kuma wannan rabin chokali zaki dinga diba kina saka zuma da madara ta ruwa kina sha, safe da yamma..,yana da karfi karki diba da yawa" to najlah tace mata tunda dai ba masu daci bane ba , to ai bata da damuwa dasu a rana ɗaya ma sai ta shanye su tas, tamkar aunty Hafsah tasan me take rayawa tace '' wallahi ina me ja miki kunne duk randa kika kuskura kika shanye su tas sai kin faɗawa mutanen garin ku, ballanta yadda kike ke kaɗai ba wani matayi a kusa dake , hmmmm sai an kai ki gadon asibiti wallahi..., saboda da me aunty cewar Najlah.. Aunty Hafsah tace '' baki ji me nace miki ba yana da karfi shi a ka'ida ma amfiso asha lokacin da za'a kwanta amma ke dan ya ratsa ki tace ki sha sau biyu.., amma aunty Hafsah maganin mene shi..? ajiye wanda ta dauko tayi tace '' zaki tsaya tambaya ko zaki barni na gama yi miki bayani wannan abin da kika ce yana damun ki naga number ta a wani group na mace me daraja naga kuma ana ta yaba aikin maganin ta shine nayi mata magana tun daga barno ta turo min dasu wallahi najlah wa'yannan da kike gani na kashe kudi sosai duk dan na siya miki mutunci saboda ko kana da kyau ka ƙara da wanka.., Najlah da ta kasa fahimtar zancen aunty Hafsah tace '' mutunci kuma aunty ba cewa kikai maganin miyagu bane to aini da mutunci na da wa kika taɓa ganin munyi faɗa balle har mutunci na ya zube a idon mutane..., tab aiki game kare ka sai yanzu ta kara tabbatar da zancen Hajiya akwai matsala babba ajiyar zuciya ta sauke ta dauko wani tana cewa ungo wannan sarke zaki dinga yi dashi aina san ke bakya fada shi wannan da kike gani ²in¹ ne ba abin da baya magani.. to ta faɗa tana kwanciya akan gado. mai da su jaka tayi tana cewa kin gane ko..?, uhmm nagane Nagode Hajiya ce ta shigo kallon jakar tayi tace '' Hafsah zo.., tashi tayi tana bin bayan'ta NAJLAH kau da kai tayi da alama maganar sirri za suyi tace kwayi ku gama ba inda zan koma nasan dai ba zai wuci tace tayi min faɗa ba akan nadena cewa bana son zama a gidan yaya. ta fada tana canza guri. Hajiya kuwa basu tsaya a ko ina ba sai a dakin ta , ta kalle hafsa tace '' me ya saka kikai haka kinsan fa bana son wannan abu Hafsah.., zama tayi cikin kwantar da murya tace '' kiyi hakuri bamu isa mu da katar da wannan kaddarar ba illa mubi ta da addu'a wallahi tun da kika ga kare na shinshina takalmi dauka zai yi ni banga aibun abin nan ba maganar mutane kike tsoro akwai hujja da dama to me ne abin damuwa Hajiya addu'a ce kawai taki yadda ba mutum ɗaya bace kina ganin abar abin nan haka ai akwai matsala dole a gyara ko ina...., ajiyar zuciya ta sauke tace '' Hafsah ba zaki fahimci abin da nake son ki gane ba wallahi inhar ta sani sai abin nan ya rushe wa gari ya waya daman mutane za a raba su da fadar abin da sukai niya ne..?, hmmmm da wannan dan wannan amma da yinsa fa rashin sa ba zai canza mata suna ba , bama ma fatan haka Allah ya kawo mafita ya ganar fa ita gaskiya.. cewar aunty Hafsah. Hajiya tace '' amin ya Allah addu'a ce magani sai mu ci gaba da fadawa Allah kukan mu Allah ya sani bawai shi nake ƙi ba halin ta nake gudu kar daga gyara azo kuma a ballo wani sabon ciwon kinga anyi ba ai ba kenan... Wannan littafin na kudi ne duk meson 1k amina alhasan Muhammad 8141785374 opay KU TURO DA SHEDA TA WANNAN NUMBER 08141785374. Yan niger 1000fcfah AMINA MUHAMMAD ALHASAN KANO My nita sai kuyi screen shot Ku turo ta wannan number 08141785374 na kusan buɗe paid group me kike jira ne Hajiya ta..? Ina sanar muku akwai complete document na dukka littafin nan 1:.JIKAR MAMMAN COMPLETE DOCUMENT 1K 2:.HAUWA KULU WOMEN LEADER COMPLETE DOCUMENT 500 3:.DESTINY LOVE 400 4:.BINTA YAR JAGALIYA COMPLETE DOCUMENT 300 5:.YAR HANNU A LAGOS 1K 6:.GIDAN MAGAJIYA Complete document 1k 7:.UWAR GAFALALLU COMPLETE DOCUMENT 1K 8:.BAƘIN SHAFI 1K COMPLETE DOCUMENT 9:.YAN ZAMAN MAKKAH 1K COMPLETE DOCUMENT 10:.MU ZUBA MU GANI COMPLETE DOCUMENT 200 11:. KIN CUCE NI 300 Dan Allah idan kinsan ba siya za kiyi ba karki yimin magana duk maganar da za kiyi idan ba receipt evidence na gani ba bazan amsa ba dan Allah mu kiyaye Number iya WhatsApp take yi 08141785374 ban da kira KARUWAN CIKIN GIDA Ga channel dina kuyi min subscribe Dan Allah wai ina masoya na suke. https://www.youtube.com/@nasreenminallah https://vm.tiktok.com/ZSBRtRQmN/ Domin samun update kuyi following dina https://whatsapp.com/channel/0029VaLdFeg4SpkQ9xyW5c0k Book ¹ EPISODE ¹⁵ Shiru aunty Hafsah tayi tana tunani can tace '' amin ya Allah.., Hajiya tashi tayi ta fita jin sallamar Abba haka ma aunty Hafsah da kallo ya bisu yana cewa kaga uwa da yar'ta me kuke tattaunawa wa haka.. aunty Hafsah ɗurƙusawa tayi tace '' Abba sannu da dawowa.., yauwa Allah yayi muku albarka ke da yan uwanki. amin tace tana tashi zaune ta zauna a kan carpet Hajiya kuwa tace '' kasan damuwa ta bata wuce wannan maganar ba.., dan murmushi yayi yace '' insha'Allahu ba zamu taɓa nadama ba ki dena damuwa.., Allah ya yarda ta fada tana shiga kitchen buɗe fridge tayi ta dauko ruwa me sanyi sannan ta bude kitchen cabinet ta dauko glass cup ta fito buɗe mai tayi ta zuba mai tare da ajiye ragowar a kan Center table. dai-dai lokacin najlah ta fito washe baki tayi tamkar me tallan ma-clean tace '' abba sannu da dawowa.., ajiye kofin hannun sa yayi yana wara mata hannu yace '' daughter saukar yaushe..?, da gudu ta tawo ta rungumshe shi cikin farin ciki tace '' dazu muku zo.., ta faɗa tana zama a kusa da shi, tashi aunty Hafsah tayi tace '' hajiya sai da safen ku.., Hajiya tace '' ba zaki ci abinci ba zaki tafi haka sa wuri.., murmushi tayi tace '' ban tawo ba sai da naci abinci.., najlah da sauri tace '' muje naga twins..nasan irfan yafi Arif girma ko..?, ehmn sun girma dukkan su ba wanda yafi wani girma. tashi tayi tace '' abba na tafi.., okay sai kin dawo. bin bayan aunty Hafsah tayi tun da suka fara tafiya ba wanda yace wa da yayiwa wani magana har suka shiga shashin ta najlah ita ce sahun gaba ta shiga bata rai tayi ganin ya jawad da yaya mutallab suna hira irfan a hannun sa yana mai wasa durkusawa tayi tace '' ya mutallab ina wuni.., ɗagowa yayi yana cewa autar Hajiya ba zaki gyara halin ki ba , kin shigo tamkar an jefo ba sallama.. turo ƙaramin bakin ta tayi tana cewa zan gyara Insha'Allahu kayi hakuri.. ya mutallab yace '' hakuri hakuri yar lukuta.., aunty Hafsah dariya tayi tace '' abin har da cin mutunci.., mutallab yace "' mommy twins karya akai mata ne ga ta nan kamar bukka..," ba ƙaramin shaƙa najlah tayi ba idanuwanta har ya fara kawo kwallah tashi tayi ta hau kan kujera tace '' bani irfan.., kallon ta yayi yace '' wannan arif ne irfan yana hannun Jawad.., ikon Allah wallahi na zata shi ne to yaron ne gaba ki ɗaya kamar su ɗaya aunty hafsa kema kina gane su..?, zama tayi tana cewa me zai hana na gane su.. jawad da tun da najlah ta shigo bece komai ba tamkar ma baya gurin sai operating wayar sa yake yi irfan ya zubawa screen din wayar sa ido yawa me fahimtar wani abu kallon sa aunty hafsa tayi tace '' jawad ba magana laifin me nayi..?, ɗago sexy eyes din sa ya kalle ta yace '' bakomai na same mu lafiya..?, uhmm yau sarautar ce ta motsa bara na saya kaina...anya kuwa Jawad a haka zan baka gaskiya da sake murmushi yayi yace '' to ai ba tilas nayi muku ba hanya a buɗe take.., dariya tayi tace '' kamar gaske da kuwa ranar ka kasa bacci.., hmmm kawai yace yana ci gaba da operating wayar sa... mutallab yace '' sai kace ba namiji ba kike faɗa mai wannan maganar..., jawad yace '' yawa fada mata dai.., aunty Hafsah tace "' akwai ranar kamu ne zan dawo muku da wannan maganar wallahi....," a'a riƙe abar ki basi kin dawo mana da ita ba ko Jawad....? Jawad yace '' uhmm ani na ma rasa bakin magana sai kace wata kayan gabas.., dariya tayi tace '' wallahi zan kama kune..., najlah ta karbi arif da yake hannun mutallab ta shiga daki ganin ita ba gane zancen nasu take ba suna magana a juye aunty Hafsah itama bin ta tayi tana shiga ta zauna Najlah kallon ta tayi tace '' wallahi aunty Hafsah kina da abin haushi ba sai ki kyale shi ba ya gama isar sa idan yayi niya yayi miki magana kinga sai wani wura hanci yake da wani hancin sa yawa butorami.., dariya sosai aunty Hafsah tayi tace '' wallahi kamar ki ɗaya yadda kika san kaki yayi kema kenan haka hancin ki yake..?, shafa hannun'ta tayi tace '' habawa ai hancina me kyau ne kina ganin sa yawa biro dai-dai misali ya samu irin hancina da wallahi ya caɓa., me ya saka bakya ganin kyawun jawad..? aunty hafsa ta cillo mata wannan tambayar. da sauri najlah ta ɗago ta kalle ta , tace '' bakin halin sa kinga komin kyawun mutum inhar yana da bakin hali mummuna ne kinga wallahi yaya MUNEEF ya fishi kyau kaf gidan nan fa shi a ka tarawa muni.., zaro ido auntu Hafsah tayi tace '' uhmm akwai ranar da zan tuno miki wannan maganar idan kika ce idan ba Jawad ba sai rijiya.., kai aunty ina neman tsari wannan idan ba matar sa ba wazai iya dashi ki dena ma yi min wannan zancen. na dena ta faɗa tana karbar arif da yake neman abinci zaro mamanta tayi ta soma bashi najlah zuba musu ido tayi tana tunani to wai aunty Hafsah bata jin zafi ne ko me ko ita dan dai ba yaro bane ko kuma na aljanu ne yafi zafi..kauda kan'ta tayi tana cewa aunty Dan Allah ki bawa su abba hakuri kar su mai dani gidan yaya wallahi bana son zama. zuba mata ido tayi tace '' najlah ki kwantar da hankalin ki, Jawad ba zai taɓa cutar dake ba.., uhmm najlah tace tana kwanciya kiranta jawad yayi shiru tayi mai har sai da ya kira ta sau uku tashi tayi tamkar wacce kwai ya fashewa a ciki ta fita dan nesa dashi ta zauna tace '' yaya gani.., ki zama cikin shiru gobe idan na dawo da wuri zan mana booking ki cikin dare ne mu isa gida, na gama duk wani abu da zanyi sauran meeting shi ya zaunar dani da ace bashi da gobe da wuri za mu tafi.. ya mutallab ta kalla tuni idon ta ya kawo kwallah tace '' bafa inda naje ko gurin su basma banje ba balle gidan aunty rafi'at ta dawo hutu..dan Allah ya mutallab ka bashi hakuri shi ya tafi zuwa wani satin Allah zan dawo da kai na ai nasan hanya ko kuma sai na yiwa isa driver magana ya kai ni.., ya mutallab dariya ce ta kubbuce mai Allah me iko wannan dreamer ta jawad da najlah besan lokacin da zata ƙare ba yawa masu ganin hanjin junan su najlah bata kaunar ganin ta kusa da jawad ko kaɗan yace '' a'a auta kunfi kusa tare ba ganku.., najlah tana jin wannan magana ta saka kuka da sauri aunty hafsa ta fito tace '' Najlah lafiya kike kuka..?, shiru tayi mata tamkar magana take yi da dutsai kallon Jawad tayi tace '' Jawad me ya faru dukan ta kayi...?, tashi yayi yana zura wayar sa a aljihu yace '' kar Allah ya saka na dawo baki shirya ba kiga yadda zanyi dake a cikin gidan nan.., tuni aunty Hafsah ta dauki haske dariya tayi ta , ta zauna tace '' kiyi hakuri kinji goben ki shirya duk inda zaki sai ki je kafin ya dawo ku tafi. , banza tayi mata taci gaba da kukan ta sai da tayi me isar ta , sannan ta tashi ba sallama ta bar shashin nata ji tayi an bangaje ta da sauri ta juyo nihilah ce daukan hannu tayi da zummar zata zabgawa najlah mari ya saif ya riƙe hannun ta yace '' ban da bangaje ta da kika yi har zaki dauki hannu ki mare ta me tayi miki ai ita ya kamata ta mare ki ba ke ki mare ta ba.., saif ka cika min hannu na ina ruwan ka dani baka ga take min kafata yi ba tana tafiya tamkar wata ballagaza.., dan murmushi yayi yace '' ko makaho ya shafa ya san najlah ba ballagaza bace tun da bata nufin kowa da sharri ko tana bin mazan banza.., Wannan maganar da saif yayi mata baƙaramin ciwo tayi mata a raina cikin mamaki tace '' saif ni kake jifa da irin wannan kalaman..?, ko baki jiba na ƙara mai maita miki..? ya faɗa yana sakin hannun ta. NAJLAH bata ce komai ba tabar gurin duk abin da yake faruwa akan idon jawada ne da yake tsaye a baranda hannun sa rike da magazine yana dubawa. ganin najlah tabar gurin ya zauna akan kujera yana ɗora kafa ɗaya kan ɗaya wayar sace tayi ringing da sauri ya dauka ganin me kiran ƙarawa yayi a kunne yana cewa ummi barka da yamma.. ina ka tafi kai da najlah. ko amsa gaisuwar sa ba tayi ba taje fo mai wannan tambayar da ta saka hanjin cikin sa kaɗawa. cikin dakiya yace '' najlah kuma ummi waya faɗa miki wannan zancen.., jawad kar ka mai dani ban san me nake ba tambayar ka nayi ina kuka tafi bance ka mai dawa farida yar ta ba, wallahi jawad idan na ji wata magana yasin zan iya tsine maka. kan'sa ne yayi wani irin sarawa bakin sa na rawa yace '' ummi tsinuwa kuma..?, da kyau tunda kaji abin da na fada maka ta faɗa tana kashe wayar ta. bin wayar yayi da kallo ya dafa kan'sa besan ya zai ba yana cikin tsaka me wuya sai dai fatan da yake Ubangiji ya fidda fashi ummi uwa ce a gare shi haka hajiya ko wacce da irin nata matsayin. besan me ya saka ummi ta tsani Hajiya ba duk da alkairin da tayi mai kamata yayi ta so ta ta kaunaci jinin ta. *******ABUJA. OSOKORO.. Jawaher bata tashi ba sai bayan sallar isha lokacin abin da ta sha ya sake ta daukan wayar ta , tayi da sauri ta dafa kan'ta da yake juya mata kiran ummi ne sai kiran jawad su kaɗai ta gani sai wata bakuwar number... ajiye wayar tayi tana cewa wannan jarababbiyar matar idan ban gama yi mata aikin ta ba , baza kyale ni na shaki iska ba ke mece makomar ki wata zuciyar ta jefo mata wannan tambayar lokaci guda. gumi ne ya fara tsassafo mata ta dafa kanta a fili tace '' anyi kitso da kwarkwata tab wallahi akwai saki aini banyi wannan tunanin ba shikkenan na tashi a *ZERO* dole a sake saban lale. tashi tayi tana dafa bango ta fita kai tsaye kitchen ta nufa tana zuwa ta buɗe fridge kamar wasa abin da take nema bata gansa ba gaban tane ya fada a fili ta furta na shiga uku kar dai ya gani da sauri ta shiga fito da komai na cikin fridge din sai da ta gama tas amma bata ga komai ba zare ido ta fara tana riƙe da kugu ko shugaban ma'aikatan gidan zata kirawo to amma ai ta bawa ma'aikatan part din ta hutu su saran da ba a kasan ta suke ba basu da hurumin shigowa part din ta tana cikin wannan tunani ne sunan Najlah ya fado mata a rai. ranta ne yayi mugun ɓaci tasan nawa ta saka ta siya da zata dauke mata ita wata kila ma ta faɗa mai ko da yake ba lallai tasan mece ba ko dai sha tayi..? bata da me bata wannan amsar haka ta , tafi tabar kayan da ta fito dasu zama tayi akan kujera tana tunani to yanzu me ya rage mata bata da wata dabara bata sha'awar zuwa club saboda fuskar'ta ba boyayyiya bace. gashi sunyi faɗa da eman balle ta kawo mata ji take idan bata sha ba , bata taɓa samun nutsuwa ba sosai ta lula duniyar tunani. komawa daki tayi ta dauko wayar ta kiran Jawad tabi yana dauka ta fashe mai da kukan shagwaɓa tace '' wallahi nayi fushi yau fa na dawo ashe baka nan wallahi nayi maka tana din abubuwa da dama ina zuwa naga shiru shiru baka dawo ba jiki na duk yayi sanyi nayi missing din ka sosai.., shiru yayi yana sauraren ta yace '' kiyi hakuri aiki ne ya taso yanzu haka ina Yola.., da sauri ta tashi zaune tace '' Yola ina najlah..?,tare kuka tafi itama tun da na dawo banji koda motsin ta ba..?, eh tare muku da ita gobe zamu dawo ta kusan fara zuwa lecture. uhmm my mine wai can Yola babu makaranta ne naga kamar bata son zaman gidan nan my love be kamata a matsa mata ba ko dan a samu ta fito da sakamako me kyau.. ta faɗa tana addu'ar Allah ya saka ya amince da shawarar ta Allah ya gani bata kaunar ganin najlah gwara a kawo mata kowa da akawo mata wannan yarinyar. Jawad yace '' Jawaher tambayar ki nayi kin fini sanin abin da ya dace da ita ne.., daman sarai tasan za'a rina wai an saci zanin mahaukaciya domin Jawad yana da wuyar sha'ani ba ayi mai gwanin ta. cikin kwantar da kan'ta tace '' Allah ya baka hakuri mijina ba haka nake nufi ba dama shawara na baka idan ka dauka fine idan kai rejecting fine bawai nace dole bane my love girman kujerar ka .., ta faɗa tana dariya. okay yayi cewar Jawad Jawaher tace '' yanzu yaushe zaka dawo..?, Insha'Allahu gobe. tamkar yana ganin ta , ta saki murmushi tace '' to Allah ya dawo da kai lafiya.. amin ya Allah yace sallama yayi mata ya kashe wayar sa bin wayar tayi da ido ranta duk a ɓace wato sai ya kara dawo da najlah insha'Allahu ba zata dawo ba haka kurum tazo tana saka mata ido a cikin sha'anin ta. bakuwar number nan ta kirawo bugu ɗaya aka dauka tare da yi mata sallama amsawa tayi tana cewa am ban gane me kira ba idan ba damuwa zan iya sanin da wa nake magana... wanda kuka haɗu a tiktok har nayi miki magana ta DM kika bani number ki, wancan satin kin dawo ne..? dafa kan'ta tayi tace '' ooh wallahi na manta eh wallahi na dawo yakake.., alhamdulilah wallahi na matsu ne kin dawo ki faɗa min address din ki duk inda kike zan zo ko ni ne zan baki address dina..? dan shiru tayi tace '' zuwa jibi sai muyi maganar yanzu ina wani abu ne.., dan Allah ki temaka wallahi tun da kika turo min video din ki na kasa samun sukuni ko kallo nake sai na ji na jiƙe ki temaka min.. shiru tayi tana saurarar sa ita bawai ki tayi ba gyaran da ta batar da kudin ta , tayi wa jawad ba shikkenan ya yashi aban za wani can ya mora tana cikin wannan tunanin ne taji yace '' kin yi shiru sweet heart baki ce komai ba.., gaskiya yau bani da lokaci kamar yadda na fada maka a farko yanzu ma haka abin yake ina da wani uzuri amma tabbas jibi zamu haɗu idan Allah ya kai mu. to ya na iya amma ban so haka ba naso na danɗani zumar ki... murmushi tayi tace '' dayau da goben ai duk abu ɗaya ne.., hakane sweet heart naso ace na jini akan ki kai wayyo Allah ranar sai na kusan suma saboda dad'i.. gyara zama Jawaher tayi tace '' indai nice abin da yafi suma ma zaka yi.., yihuuuu ya saki wani ihu yace '' wallahi ni sheda ne kallo ɗaya nayi wa hantsar ki nasan ke kankana ce uwar ruwa....., jawaher tace '' dan ma baka ji abarka tana juyi a ciki ba.., Allah ko ya ce mata haka.. Jawaher tace '' uhmm.., yanzu beb turo min account number ki ladan jiyar dani dad'i da ke Kai yanzu zan baki tukuici... zaro ido Jawaher tayi tace '' harda tukuici bayan ba ayi komai ba.., waya faɗa miki ba ayi komai ba , domin kinga mutuniyar sai zubda ruwa take saboda jin muryar ki da nayi.., karyar da wuya tayi kamar yana ganin ta tace "'to godiya nake ...," abubu haka tsakanin mu amma dollar account zaki bani.. wani dad'i jawaher taji wato ba ƙaramin kamu tayi ba , wannan yar hirar da suka yi shi ne har zai bata dollar kai ji tayi kan'ta ya kara girma gaskiya ita me sa'a ce , shi ya saka ko sau ɗaya ba zata taɓa yadda ta dena gyara kan'ta ba duk wanda ya dandana ta sau daya baya barin ta wanda be dandana ta ba so yake ya ji dadin yadda take.. sweet ya naga kin yi shiru ko dai na ɓata miki rai ne.. jawaher tace '' a'a baka batan rai ba hallaɓai.., dariya yayi yace '' haka nake so baby na karki damu da tsofa na wallahi ras take har yanzu tana aiki yadda kika san ta dan shekaru 25.., dan murmushi Jawaher tayi tace '' ba damuwa sai an jima ko.., to nabar ki lafiya abar kaunata. ya faɗa yana kashe wayar ciro ta tayi daga kunne ta , tana shiga cikin gallery din wayar ta password ta saka a inda tayi hide wasu picture shiga cikin wani folder tayi ta danna kan wani hoto kura mai ido tayi tsoho ne sosai dan akalla yayi shekaru 60 zuwa 70 years abin ka da kudi jikin sa be wani lalace ba ta gumi tayi tana kallon bakin sa da wani gurin ba haƙora Allah me iko shi kuma wannan me yake nema a duniya idan ba Allah yayi masa rahama ba shekarun sa sun ja.. kamata yayi ace ya rungumi carbi da karatun Alkur'ani...me girma to sai dai shi tsohon dan bakiri ne wasan da kuruciyar sa me ya aikata fita tayi tana jan ƙaramin tsaki ajiye wayar tayi tana tashi zaune da sauri ta dauki wayar tayi mai text messages din account number din ta , ta zauna ta shiga cikin WhatsApp din ta Kai tsaye ta shiga cikin group din su na diamond classis ladies ganin irin messages din da yake shugowa da alama yau akwai sabon update abin mamaki ga group din mayan matan da ba kataba tunanin suna wannan harka ba zaka gansu a ciki.... Sai mace takai ta kawo ake saka ta aci buɗe video da taga ana ta magana akan sa tayi tabe baki tayi ganin yadda suka haukace musamman ma masu yin lesbian a cikin gidan wata sabuwar bakuwa suka yi wai ita baby crystal iya kyau tana da nata kyawun tsaki ta ƙata ja tana cewa ko mene abin rudewa a jikin ta mmwwssss gani tayi anyi tagging dinta duba sakon tayi wannan baby din nan ce tace aunty admin me zan samu kallon dp din ki nayi naji kin tafi dani.. da sauri tace '' Allah ya tsari gatari da saran ciyawa me zan yi da yar uwata mace emojis ta saka na 🙄😲 duk randa kika shirya tana bata amsa ta fita daga cikin group din har zata kashe datar ta , taga dollar din da wannan mutumin ya sako mata zaro ido tayi dollar dubu biyu ce ji tayi kamar ta tashi ta , taka rawa dan dadi gaskiya ita me sa'a ce.. afili tace gaskiya malami na ya iya aiki ko da yaushe sai samin nasara nake duk abin da naso samu samu nake na mallaki jawad a lokacin da kowa yake min kallon bamu dace ba wata dariya ta saki har da shewa ba tare da tayi sallah ba ta kwanta ita kanta ta manta yaushara bonta da tayi sallah. bacci ne ya kwashe ta. Allah ka tsare mana imanin mu amin summa amin.. washe gari da safe taci kwalliya tamkar zata gasar sarauniyar kyau sai zabga kamshi take zama tayi a parlour ta ɗora kafa ɗaya kan ɗaya gaba ki ɗaya ma'aikatan gidan ta kirawo kafin kace mai kowa ya hallara mazan su da matan su, sai da ta gama shan kamshin Sannan ya ajiye wayar ta da take dananwa tace '' nata raku ne akan cewa duk wanda ya san ba zai iya aiki ba zai iya ajiye aikin sa..,kofa a bude take.. kowa kallon kowa yake anya kuwa matar nan kanta ɗaya yawa wacce ta sha kwaya suna bakin aikin su ta saka aka kira su amma take musu wannan zancen.. dafa kan'ta tayi daya ci uban nail tace '' yauwa wannan daman shine Abin da ya saka na tara ku kowa zai iya zama tafiya ke rose ki gyara min kitchen ki dora min break fast..., rose ta rusuna tace '' Madam na gama komai kin manta nakai miki kinci ko wani za a ƙara dafa miki..?, okay I forget sorry.. jikin su na rawa suka bar mata parlour suna mamakin Hajiyar tasu yau yawa wacce ta sha kwaya tafi ƙarfin kan'ta.. JAWAHEER kuwa bayan tafiyar su tashi tayi tana tan gadi shiga bedroom tayi zubewa tayi dakyar take iya gane inda take yau kwayar da tasha tana da yawa shi ya saka har take wasu abin da ya huce hankali.. kwanciya tayi tana numfashi tare da mike wa tana buga ƙafar'ta wani irin ihu taka saki sai kuma ta saki dariya tamkar mahaukaciya..sabuwar kamu.. dakyar ta tashi ji tayi dakin na juya mata dafa kan'ta tayi tana cewa dan girman Allah karka fado min ka tsaya zan fita a hankali ta faɗa tana nuna pop din dakin... gani tayi *swarovski* a hankali ta fita tana dafe kan'ta a kofar dakin ta zube tana mai da numfashi kallon saman dakin tayi tana ganin kamar zai fado mata dakyar ta kara tashi da rarrafe ta hau sama ta shiga dakin ta tana mai da numfashi buɗe fridge tayi ta dauko wata allura a hannun'ta ta tsira Allah ne ya rufa asiri bata karya allurar ba a jikin ta tamkar ba jikin ta tsira ba haka ta caka ta tare da danna ta cikin naman hannun ta tana mai da numfashi... da kallo tabi jinin da yake zuba a hannun ta.. lemon tsami ta dauki ta sha ta dade tana mai da numfashi Sannan ya fara dawowa hayyacin ta allurar ta cire tana yago tissue paper ta saka akan hannun ta gaskiya kwayar nan yau taku san toma mata asiri ya kai doctor ta bata me karfin haka ne bayan tasan bata shan irin wannan gwara wacce zata lula da ita gaji mare a hankali yanzu da jawad yana nan tace mai shikkenan kashin ta ya bushe daukan waya tayi ta kara a kunne ana dauka ta soma faɗa tace '' wannan wanne irin hulakanci ne yanzu da na rasa raina kinsan gram nawa kika bani...? dakyar na dawo dai-dai.. cikin tashin hankali Jawad yace '' innalillahi wainna ilaihir raji'un.., da sauri ta zaro wayar akunne tana mustsuka idon ta da sai taga kamar number doctor ya kirawo ashe ta jawad ce ta shiga uku shikkenan kashin ta ya bushe da sauri ta kashe wayar ga baki ɗaya gaban ta ya shiga dukan uku uku to me zata ce mai innalillahi wainna ilaihir raji'un tashi tayi dakyar tana haɗa hanya ta shiga toilet cire kayanta tayi ta sakarwa kan'ta shower amma ina bata samu sauki ba sai ma wani zafi dakan ta ya ƙara dauka batare da ta saka towel ba ta fito jin sallamar zeey tayi dakyar ta iya amsawa ta zauna akan gado zeey shigowa tayi tana cewa Jawaher lafiya na ganki a haka..?, ta faɗa tana zama tare da kamo hannun ta... sister sannu da sauri ta ɗago kai wanne baby din nan ce to yaushe suka haɗu da zeey ko daman can zeey ta santa ne bata da me bata amsar nan daka kai tayi gaban ta na ci gaba da faduwa idan auren ta ya mutu ta shiga uku tambayar zeey tayi tana kwantar da kanta akan cinyar tare da shafa mata gadon baya kamar wata ƙaramar yarinya dakyar Jawaher ta iya cewa zeey na shiga uku ina cikin halin maye na kirawo Jawad kuma nayi barin zance wallahi waccen shegiyar ce ta bani kwayar da tafi karfin kaina ban lura ba nasha da yawa wallahi dakyar na dawo dai-dai shine na buga mata nace bata kyauta min ba ashe jawad ba kirawo wallahi sakina zai yi... baby zama tayi tana riko hannunta tare da shafa mata shi a hankali tamkar ke shafa mata mai tace '' sorry sis insha'Allahu ba abin da zai faru ki dena damuwa...., hannunta ta kwace tana zame wa a ƙasa tare da rushewa da kuka tace '' shikkenan na shiga uku wallahi idan gata nane duniyar nan ba wanda ya isa ya dawo dani Jawad yana da taurin kai.., tashi baby tayi ta isa gaban picture din sa shafa fuskar'sa tayi tace ''masha Allah kyakkyawa dashi.., chak jawaher ta tsaya da kuka nan danan idon ta yayi jajir kurawa baby ido tayi tana wuci mijin nata zata shafawa fuska lallai yau zata koya mata hankali a hankali ta jawo karbar turare duk irin tsadar turaren nan haka ta fasa shi dukkan su juyowa sukai suna kallon ta ganin ta zama tamkar wata mahaukaciya sai wuci take yi...... turka shi..... yanzu fa aka fara me kike jira biya 1k ki karanta labarin ki cikin kwanciyar hankali.... kiyi nishaɗi iya Nishadi kiji dad'i ki kore duk wata damuwa a ranki Hajiya ta duk a cikin 1k uhmm labarin nan bana yara bane na mayan hajjiyoyi ne wa'yanda suka amsa sunan su.. free pages ya kusan karewa hanzarta biya domin ki shiga paid group. 8141785374 amina Alhasan Muhammad opay. Yan Niger 1000fcfah My nita. ku turo da shedar biya tanan 08141785374 dan girman Allah ban da kira ki Flashing idan kuma baki shirya ba kar ki min magana dan Allah turo receipt ki gani a cikin group.. KARUWAN CIKIN GIDA Ga channel dina kuyi min subscribe Dan Allah wai ina masoya na suke. https://www.youtube.com/@nasreenminallah https://vm.tiktok.com/ZSBRtRQmN/ Domin samun update kuyi following dina Book ¹ EPISODE ¹⁶ Kafin baby ta ankara sai jin saukar kwalba tayi akan ta , Allah ya rufa asiri ta kauce kaɗan ce ta sameta da sauri xeeey ta riko hannun Jawaher tace '' innanallahi wainna ilaihir raji'un jawa lafiya kuwa kike ko har yanzu a bin da kika sha be sake ki ba..?, fincike hannun'ta tayi tace '' kalle ni da kyau ras nake ko baki ga abin da tayi min ba fuskar mijina ta shafa.., da sauri baby ta kalle ta , tana mamaki anya kuwa kan matar nan qalau yake dan ta shafa picture sai ya zamo matsala a fusa ce tace '' wallahi idan abuja gatan ki ce yau sai kinyi kwanan gidan yari ban da ke tsabar dabbba ce daga shafa picture sai ki fara wuci kina wani zabure zabure wato ke ga giredin mahaukaciya ko..? yau zan nuna miki haukana ya fi naki ke haukan karya kike yi wallahi duk shaye shayen ki na taka ki naci uwar ki tunda har kinsha kwaya ta makar dake kinga kuwa ke yar shaye shayen karya ce..., da sauri zeey ta riko baby tace '' Please baby calm down Dan Allah kiyi hakuri bata cikin nutsuwar ta , shi ya saka ta aikata miki haka.., Oh bata cikin nutsuwar ta ko ..? yanzu zan dawo da ita cikin hankalin ta when she saw her in the prison that damned woman buɗe baki xeey tayi za tayi magana da sauri ta shiga tsakani sakamakon marin da Jawaher ta zabgawa baby a fusa ce baby ta fita zeey kallon jawaher tayi tana cewa wannan wanne irin kishi ne Jawaher daga taɓa fuskar mijin ki sai ya zamo matsala ke kenan idan yaga a bin da kike kashe ki zai yi..?, zama tayi tana dafa kan'ta duk gashin kan'ta ya har gitsai tace '' Please zeey hutu nake so bana son hayaniya taci Sa'a ba huka a kusa dani da sai na datsai mata hannu kinsan kowa yadda nake kishin miji na...? to idan baki sani ba bara na faɗa miki akan *MIJINA..* ba abin da bazan iya yi ba kuma ban yarda wata mace ta matso kusa dashi ba.., tur kashi sai an jima.. ba tare da ta kalli inda take ba tace '' Please zuwa anjima kiyi mana order din wine zan tura miki kudin bana son fita saboda yan sa ido..., ba inda zani ta faɗa tana fita tsaki taja tana tashi doguwar riga ta dauko ta saka tare da katon hijabi da liqab bakin glasses ta saka a saman liqab din ta. ta dauki jakar ta , ta fito parlour wayar ta ce tayi ringing dogon tsaki taja tare da mai da ta cikin jaka. fita tayi ta bayan gidan ko tsaya rufe kofar ta ba tayi ba , ta bayan gidan ta fita ba wanda yasan da ta fita sosai take sauri har ta fito bakin titi tsarar me mashin tayi ta hau kallon ta yayi ya yana cewa hajiya baki fadi inda zan kai ki.. dan jim tayi sannan tace '' kai ta tafiya idan munzo gurin zan nuna maka.., cire P-cap din sa yayi yana kare mata kallo tun daga sama har ƙasa yace '' kai gaskiya akwai matsala kin dai san lamarin ƙasar nan ba gaskiya sauka duk hau dina ina tsoran zuwa gurin jami'an tsaro kar daga zuwa neman arziki da abin da zan rufawa kaina asiri na shiga uku taba kaɗai nake sha awani kaulin ance ma taba ba shaye shaye bace dan haka ras nake da hankali na hajiya fito fito tun kafin na jirgita napep din nan na juya ki a ƙasa da ki jawo min tsiya gwara ni na yi miki haka kurum zaki yi min runton zubuni...., Jawaher tsayawa tayi tana kallon ikon Allah anya kuwa wannan lafiyar sa qalau ganin yana bata mata lokaci tace '' kaga ɗan gaba kadan idan kasha kwana zan sauka zan biya ka kudin ka.., miƙa mata hannu yayi yace '' in gani a ƙasa kune irin wa'yanda idan an dauke ku sai ku ce zaku je ku amso kudi a neme ku a rasa.., nayi maka kama da matsaya ciya ta faɗa tana zube jakar ta kudi ta zaro zaro ido yayi ya koma a cikin napep yace '' Allah me iko hajiya dala fa na gani..?, cillo mai dala dari tayi tace '' da hallacan jani mu tafi.., fa sauri ya dauka yana juya ta sai da ya tabbatar ba jabi bace yace '' an gama idan garin abuja kike so ki zaga zan zagaya dake Hajiya.., banza tayi mai tafiya suka fara yana juyowa yana kallon ta yace '' mun isa ...?, kai take girgiza mai sai da suka zo wani guri me bakin gate tace '' anzo.., sauka tayi kallon ta yayi yace '' hajiya bani da. chanji fa.., fita tayi tai mai banza tura gate din nan tayi ta shiga katuwar haraba ce da motoci kala kala da sauri ta dawo Allah ya saka hana tsaye tace '' yanxu xan fito ka tsaya anan..zaka mai dani.., to Hajiya an gama ya fada yana shin shina dollar da ta bashi.., juyawa tayi ta ta fara tafiya shiga ciki tayi wajen kamar gurin shakatawa ne a jikin bangon wajen anyi zanen shisha da picture's din kayan maye stair case ta taka ta shiga gurin tamkar a ƙasar waje kake kowa harkar gabas sa yake ba wanda ya kulata mata ne birjik da samari suna ta sha'anin su ba ruwan wani da wani gaban teburin da ake siyar da abin da giya ta tsaya mutumin ya ci kito ga tattoo a jikin sa ATM ta mika mai pos ya miko mata tare da zura katin ta , password ɗin ta , ta saka ta miƙo mai kuɗin da zai cira ya cira ya miko mata buɗe fridge yayi ya miƙo mata da haka ya saba da ita yasan wacce take so a cikin leda ya saka mata karba tayi tana cewa thanks.. kai kurum ya gyaɗa yana bin ta da kallo har yau be taɓa ganin fuskar'ta ta ba amma ya akai mace kamar ta musulma tana shan giya ko uban gidan ta take siyawa duk yadda akai mace ce me riko da Addinin Musulunci.. wani ne a cikin matasan nan ya taso yace '' malama yau sai kin cire mana wannan abin naki kullum sai dai ki zo ki tafi wannan ai munafurci ne.., gaban Jawaher ne ya fadi a hakali ta ɗago fuskar'ta tana kare mai kallo ba ƙaramin razana tayi ba liqab ɗin fuskantar ta ya fusge saka hannu tayi ta kare fuskarta da sauri yace '' queen..!, ɗagowa tayi tana kallon sa a hankali ta furta hassimi.. miƙa mata liqab dinta yayi yana naushin iska cije lips ɗin sa yayi yana mata kallo tun da ga sama har ƙasa yace '' idan kere na yawa zabo na yawa wata ran zasu hadu a gidan tara.., da sauri ta mai da liqab din ta , tace '' dan girman Allah hassimi kai min rai.., tabe baki yayi yana kare mata kallo yace '' queen kin manta karatun mu na baya...? a gaban ki mutum nawa nakai lahira duk dan saboda sun ci amanata, shi ne ke kika aikata ko..? wato kin kile kin manta da yawa da farantin shinkafa duk tashancin ki da yawan tallanki wallahi ba idon da zaki buɗe min daga ke har shegiyar matar nan..ba ance dan ta kike aure ba.., fitsari ne ya kusan kubbuce mata haɗa hannuwanta tayi tace '' dan Allah kai hakuri.., kallon giyar da ta fado daga hannun ta duk ta fashe har ma'aikatan gurin sun zo gyara matsawa tayi shi kuwa juyawa yayi yace '' kin ci Sa'a ɗaya muna gurin da akwai security da yanzu sunan ki gawa..so kina da sauran lokaci Jawaher yar gidan magajiyar karuwai.., da sauri ta fita tana harda kafafuwa gudu ta ke yi har ta fita tana ganin me napep ta shiga tace ''' dan girman Allah jani Ka bar nan gurin.., shiga yayi yana mamaki yace '' hajiya lafiya kin shiga cikin kwanciyar hankali kin fito jikin ki na rawa..?, Buga kujerar mashin din tayi tace '' dan girman Allah ka tafi mubar nan.., tada mashin din sa yayi yana cewa hajiya ba wani abin kuwa kikai ba duk kin bi kin firgice.... banza tayi mai jikin ta yana rawa sai zare ido take ana zuwa inda zata sauka tace '' nan yayi sauke ni.., da sauri yayi parking a guje ta fita tamkar zata tashi sama , ta kofar da tabi tanan ta shiga cire liqab din nan tayi tana sakin ajiyar zuciya duk da haka wai waye take tayi ragon azanci ma.... da bata ce ya duba mata ko ana bin ta ba shiga part din ta tayi ta kulle ko ina tana zare ido gani take kamar zai biyo ta... zama tayi ana mai da numfashi ɗaukan wayar ta , tayi ita yanzu ba kiran inna ba mayyar kudi ce yanzu zata ce a kawo kudi zata buge bakin su amma bata da zabi dole tabi ta gurin inna saboda duk shu'umancin'ta inna ta fita number ta , ta shiga lalubowa ta danna mata kira har ta tsinke ba'a dauka ba jan tsaki tayi tana share gumi tare da ƙara danna mata kira a wannan karon an dauka inda aka ce keee jawa lafiya kike damuna da kira to wayar ta , tana hannu na shegiya kaska rabi me jini.. tsaki ta ja tace '' jujal kai da ita duk ɗaya daman hassimi yana kasar nan...?, kut billahilazi tun da ya ferde cikin yar gidan malam ya ari kafar kare dan durin uwa amma yanzu ya dawo jiya ma sai da yazo gurin inna ke da tuni sai dai kiji bakin labari dan kuttumar uba so yayi ya antaya inna maleshiya me tukwane da nayi ƙoƙarin nayi mai hayya hayya naga ya fi ni cin mushe na matsa idan ma antaya ta lahira yayi ai son abin duniyar ta ne ya ja mata da kuma son zuciyar'ki kiri kiri kin ki yarda muzo gidan ki sai aike wato kina aure famli (family )din masu hannu da mai ko shi ne kike gudun asalin ki.., ya fada cikin Muryar rikakkun yan daba.. dogon tsaki taja tace '' wallahi jujal ba'a taba ka da shirme tambaya ɗaya nayi maka , ka tsaya yi min wani sokon bayani me inna tace masa..?..., kan bala'i inna suma tayi da taji huka a makoshi har gudawa tayi kai innar mu nason duniya da yawa.. wallahi jujal da ba dan ina tsoran halin ku ba gida zan siya muku to ina tsoran halin inna.. Wallahi kul karki soma ni dai zan kwaso kayana na dawo idan bakya son ci gaba da auren ki auren ki yayi karkon dabino to gayyato inna *KINSAN FA INNA UWAR BANZA CE...* ba yaren da take ganewa sama da yaren kudi kwanaki ta zama uwar adashi aka bata kudi wallahi jawa ina baki labari kudin nan tas ta cinye su saboda tsabar rainin hankali sai tace wai gara ta cinye su kuwa , suka kai ta chaji moshan kwanan ta biyar ana biyar din ne malam yaga Allah da annabi ya je suka ga girman sa , suka sallamo sa da sharadin duk wata zata kawo kudin to yasin ko kobo taki ta kai haba ai inna bala'i ce son kudin ta A to mauch (is to much ) inna is big kirimila ( crime ) is over over.. saboda takaici kashe wayar ta , tayi tana jan dogon tsaki da ace jujal zai gane ya dena wannan turancin na hauka... daya fi mai mutunci da suttura.... wallahi. ta gumi tayi duk halin inna da ya fadi tasan sarai wannan karamin aikin ta ne rasa inda zata saka kan'ta tayi hassimi a garin abuja yana yawa tab wannan shi ake kira da tashin hankali ba'a saka maka rana... KARUWAN CIKIN GIDA Ga channel dina kuyi min subscribe Dan Allah wai ina masoya na suke. https://www.youtube.com/@nasreenminallah https://vm.tiktok.com/ZSBRtRQmN/ Domin samun update kuyi following dina Book ¹ EPISODE ¹⁷ tashi tayi tana zagaye parlour yawa me ɗawafi.. ta rasa gano hanyar fita daga cikin matsalar nan inna ce mafitar..ta to itama tsoransa take ji amma tasan tsoran na ganin ido ne be kai har zuci ba inhar inna tasan tana da kudi tofa tas sai ta cinye su, sannan zata yi mata maganin matsalar ta..ummi a'a ummi kan'ta ta sani akwai babban kullin da yar yau ta kasa gano bakin zaren sa domin uwa ba zata iya yin abin da ummi tayi ba dukka inna ita , ta haife ta amma akwai banbanci hali tsakanin su ko yaya inna na nuna tausayi da jin kai na mahaifiya ummi fa da wata ƙatuwar gada take gina mai ta afka shi tare da shafa babin rayuwar sa , saboda wannan amfanin fa ta shigo da ita cikin rayuwar sa anya kuwa *UMMEE* ita ta haifi Jawad.. gaskiya akwai ayar tambaya tasan tana gama yi mata aiki to ita zata ginawa ramin da yafi na dan ta ta jefa ta ciki to tayi wa danta haka ma domin ta mallaki dukiyar sa balle ita Jawaher ya kamata ki san abin yi haka ta fada a fili shiga daki tayi ta fara bincike sai da ta sauke komai na cikin loka din ta tana nishi tana komai ta matsar da loka sai ka kura ido sosai sannan zaka gane a tsakan kanin tayar din dakin zaga gane akwai yar kofa da za a iya ɗaga shi daga shi tayi rami ne zuru ru a hankali ta leƙa cikin ramin tana haska fitilar wayar ta. wani murmushi ta saki ganin har yanzu a jiyar ta , tana nan tashi tayi tana mai da numfashi gyara komai tayi ta koma ta zauna... YOLA...... Uhmm ni dai Anni kice bazan koma ba nasan wallahi idan kikai magana zai yarda... wani murmushi tayi da ita kaɗai tasan manufar sa ta ci gaba da dama furarta qala bata ce mata ba basma dariya ta fara har da rike ciki tace '' wallahi tausayi kike bani sai bin kan'su kike yi to ga shawara kice ba inda zaki wallahi.., banza tayi mata mihibba tace '' tab yaya Jawad da bakar zuciya ya dinga tamole da ita a harabar gidan nan... kwanciya tayi tana cewa yauwa sis faɗa mata dai gaskiya wannan gurguwar shawara ta bani haka kurum ya janyo ya ballamin kafafuwa. Ramlah tace '' shikkenan ya rage mata fara shi.., ANNI da take jin hirar tasu tace '' au daman bata siyar ba..?, dukkan su , suka ce me ta siyar..?, farashin nata.. cewar ANNI. NAJLAH kallon ta , tayi tare da turo baki ta , tashi tace '' wallahi anni kin nuna min matsayi na wannan abin da kika bani bazan ci ba , ta karshe maganar tata tana dawo mata da kwanon gasassun yan shila da ta ajiye mata.. dariya tayi tace '' uhmm wannan kuma ke zai amfana bani ba da kin san amfanin sa a jikin mace da baki dawo min da shi ba.., murguɗa baki tayi tace '' eh din bana ci kuma wallahi ko da naci kashin da kika ce karna tauna sai na tauna.., karshen maganar tane ya makale ganin Jawad da sukai ido hudu da shi yana sanye da ash colour na manlace an mai dinki janfa da wando aikin jikin rigar monogram ne a gogon sa rolex ya kalla ya ɗago kan'sa idanuwan'sa , sanye cikin farin glasses yace '' ki shirya nan da zuwa uku zamu tafi.., da sauri ta kalli lokaci karfe ɗaya da rabi.. idanuwan'ta ne ya ciko da kwallah ANNI tace '' gata nan na mata wannan taci ba zata ci ba akan nayi mata faɗa nace kai ne daidai da zamanin ta.., wani kallo yayi mata da sai da hantar cikin ta , ta kada bama iya ita kadai ba har sauran bakin su ba rawa suka ce yaya barka da shigowa.. ba wacce ya kalla a cikin su tamkar ba zai amsa ba cikin soft voice din sa yace '' barka dai..., tamkar sun ga mala'ika haka suka nutsu kallon najlah yayi ya zuba mata sexy eyes din sa, kasa ko da haɗa ido dashi tayi hakan da yayi ba karamin nutsuwata najlah tayi ba Allah yana gani tana tsoran yaya Jawad turo baki tayi tace '' to.., daukan bowl din tayi domin ta gane inda abin nasa ya dosa ta fara ci da sauri ta , fito dashi kwallah har ta , taru a idon ta , tace '' wallahi ɗaci yake yi..., ANNI tace '' oni indo Allah me iko kai wai kuncin da kake saka kanka baya damun ka ne ka kasa sakin fuska yaron nan kamar sun ga wani mala'ika kai Jawad bakai ba wallahi..kai kenan kullum cikin kunci..wani zubin da gaskiyar najlah gaka tsoho ga haɗe rai abin yayi maka yawa.., ɗan murmushi yayi ya shafa saisayen da yayi hakan sai ya kara bayyana tarun ilimin sa da nutsuwar sa wa'yanda shekaru suka haifar mai da ita juyawa yayi yace '' ki same ni a part dina ki tawo har da abincin naki.., kai *SA BAKA DARIYA SAI HAMMA* kar kaci ba na maza bane.. bece mata qala ba ya fice domin wannan maganar ba ƙaramin ciwon kai take saka shi ba , zuwan najlah yayi ma , yayi mamaki da har yana iya biye mata suyi magana shi magana bata dame shi ba zai iya wuni bece da kowa qala ba musamman ma idan babban case yazo yana bukatar nutsuwa zai koma gefe ne yayi abin da ya dace. shiga part din da yayi direct bedroom ya nufa ajiye briefcase din sa yayi ya soma cire kayan sa daga shi sai boxer Najlah ta turo kan'ta cikin dakin tare da kwala mai kira domin har taji dad'i baya ciki idan yace me ya saka bata zo ba sai ta ce mai a tazo baya cikii. jan baya tayi tare da saurin sakin bowl din ta saboda abin da ta gani da sauri ya riko shi Allah ya rufa asiri be fadi kasa ba ajiye wa yayi zata fita a guje ya danna wani remote kofar ta rufe still bata juyo ba tun da take bata taɓa ganin gaban babban mutum irin haka ba sai yau ya shiga uku. jikin ta wani irin rawa yake daman haka yake girma.. Jawad kuwa takaici ne ya ishe shi ya daka mata tsawa yace '' ke bana son shashancin banza daman a bin da kike son gani kenan kuma kin gani amma baki ga banza ba me ya hana baki sallama ba da zaki shigo balle neman izini daman aure kike so ko..?, ƙara gigicewa tayi ta kifa kanta a jikin kofa tana kuka tace '' dan girman Allah kai hakuri ni ban ga komai ba ,ni wallahi bana son aure kar ka faɗa musu.., zama yayi yana zubawa ass dinta ido limshe ido yayi yana jin wani magnet na jan sa duk kukan da take yi qala be ce mata ba sai da tayi ya ishe ta , tayi shiru a lokacin yace '' keeee... zo.., jikin ta , ne yayi sanyi ta juyo tana sunne kai wai a haka ma a cikin boxer tagani taji wannan tsoran ina ga tagan ta zahiri ya fadi haka a cikin zuciyar sa. tamkar kazar da kwai ya fashewa a ciki haka ta iso gaban sa tace '' yaya gani.., kinganni ko..? yayi mata wannan tambayar yana kafe ta da idanuwa. girgiza kai tayi tace '' ba abin da na gani..., Oh amma kika razana.. zuburo baki taji kirjin ta na tsananta bugu har yana gano yadda kirjinta yake zama yana ƙasa abin ka da tubarkallah badai dukiyar fulani ba.. dan murmushi yayi yace '' cire hijabin nan na jikin ki.., da sauri ta kalle sa tace '' yaya hijabi ne fa.., ta fadi haka tana zaro idon ta.. yes na gani ko ce miki akai tuwo ne a cikin ido na.. kai ta girgiza tamkar wata ƙadan garuwa... yace '' oya cire ko ranki ya ɓaci.., jikin ta asanyaye ta cire riga da skirt ne a jikin ta wuyan up shoulder ne dan haka yana iya hango fararen breast din ta da suka yo sama. kauda kai yayi yace '' zo nan ..., tashi tayi jikin ta na wani irin yi mata sanyi tamkar an tsoma kaza a ruwa ta karasa gaban sa fisgota yayi ta fado ƙasa ya mai data kasan sa kuka ta saki tace '' dan girman Allah kai hakuri Allah ba abin da na gani.., goma mata hancinsa yayi a kan lips din sa yace '' nima sai na rama.., kau da kai tayi ta fara kuka tace '' dan Allah karka kalli komai.., dariya abin ya ba shi yace '' saunawa kuma sai fa ba kalla banza kwaila....me kika ajiye a kirjin naki ko kuma boomboom ya faɗa yana shafa boomboom ɗin ta. Saboda takaici bata san lokacin da ta rushe da kuka ba ganin numfashin ta ya fara up and down sakamakon hannun sa da ya saka a cikin rigar ta yana squeezing Nipple din'ta. da sauri ya ɗaga ta tare da buɗe fridge ruwa ya dauko batai mai gardama ba ta amsa tana sha tasha da yawa sosai sannan ta kauda kan'ta tana sauke ajiyar zuciya.. tamkar bashi ya gama yi mata haka ba ya haɗe rai fuskar nan ba walwala yace '' dauki, kici.., sauka kasa tayi tana gyara zaman rigar'ta , dauka tayi ta soma ci dakyar tana kokarin amai haka taci shi sweet ya bata da sauri ta amsa tana jefawa a bakin ta saboda bakin ta ɗaci yake mata. tashi tayi ta nufi hanyar toilet bece komai ba ya bi bayan ta da ido shiga toilet tayi tana wanke bakin ta still ba abin da ya canza ganin abubuwa tayi kala kala a hankali ta soma dauka tana karanta direction din su hannun ta , takai kan wata kyakkyawar kwalba dauka tayi karantawa tayi kamar haka a fili *CLODZYME MOUTH &THROAT SPRAY* da sauri ta buɗe ta saka a hancin sa zuciyar'ta ce lokaci ɗaya ta buga ƙara sakawa tayi kamshin da bakin ta yake lokacin da tayi mafarkin wannan mutumin yana taɓa mata jiki.. ba shiri ta jefar dashi tare da zunduma ihu da sauri ya shigo kuka ta saki tace '' wallahi aljanin nan da yaka taɓa ni indan dare yayi shi ya ajiye wannan mouthspray din kamshin da baki na yake yi lokacin da lips dina ya kumbura shi wannan yake yi.., kallon kasa yayi har ya fashe rasa ma me zai ce mata yayi dan haka ya kamo hannun ta suka fito danka mata bowl yayi yace '' jeki ki shirya idan lokaci yayi sai mu tafi.., ɗaukan hijabin ta , tayi ta zura ta fita. cin karo tayi da uncle Mukhtar shi da ya saif da kallo ya bita, gaishe shi tayi cikin kulawa ya amsa mata gaisuwar ta , tare da cewa daughter me ya faru naga fuskar ki duk hawaye..? kwabe fuska ta ƙara yi tace " bugewa nayi shi ne abincin ya zubu yaya yayi min faɗa...,'" tsintar kan'ta tayi da yin wannan karyar saboda baza ta iya faɗa mai me ya faru ba.. gaskiya yaya be kyauta ba sannu kin ji ya faɗa yana shiga cikin mota saif ya zagaya mazaunin driver ya zauna da yake dukkan wata dukiyar sa saif ne akai.. dan haka duk inda za su tare suke zuwa key yayi wa motar yana cewa ashe meeting yaya ya zo yi garin nan n nayi mamaki be dade da zuwa ba kuma again ya ƙara dawowa.. Dad wallahi ina tausayin yaya ba ruwan sa abubuwa sun mai yawa ta ko ina harin rayuwar sa ake yi kwanaki fa ankak mai hari akan wata Shari'a da yayi ta ɗan gidan Alhaji Ibrahim me kudi dan sa farid da yayi rep din wata yarinya me tallah so su kayi su kashe shi kasan HARIS Jami'in tsaro ne shi yake bani labari ashe dadewar nan da yayi a austria ba hutu yake ba , neman lafiyar sa yake kasan poison aka saka mai a gurin taron ƙarawa juna sani na kungiyar lauyoyi ta duniya kubace me hatsari shaƙar ta yayi yanzu haka yana kan magani ne naji yace kamar ta taɓa mai hunhu.. idon sane yayi red colour yace '' saif ya isa na tambaye ka ni me ya shafe ni da wannan labarin nan naka..?, juyowa saif yayi yace "amma Dad, he's your son you shouldn’t say something like that about someone who concerns you directly. That statement isn’t right..., ambassador Mukhtar yace " "Saif, I swear, if you don’t quit saying that to me, you’ll seriously piss me off.., kai hakuri Insha'Allahu bazan kara ba.. ya fada yana fara tafiya a hankali.. Wannan kenan Jahar Adamawa. *BINYERI GUNDUMAR MAYO-BELWA* duka ta saka mai baya tana cewa wai kai baka jine tun dazu naka ce maka ga a inda zaka sauke ni amma shine kai kunnan uwar shegu ko..?, mai mashin din faka mashin din sa yayi sauka tayi tare da sauke buhunta kwance habar zaninta, tayi ya ciro wata matacciyar naira dari da hamsin tace '' ungo karbi sauri nake ina jin ba haya.., wani kallo yayi mata tsaki taja ta zura mai aljihu cikin masifa tace ''' ya zaka tsaya kana kallo na kamar ka samu matar ka to Allah ya isa ka kalli haramun.., wullama taya yayi yana cewa bana son rainin hankali nayi miki kama da wanda za ki bawa wannan kudin..? na dauko ki tun daga kasuwa shine don rashin mutunci zaki dauki wannan ki bani bana so kije Allah ya isa daman na lura ki tsohuwar banza ce..., cire mayafin'ta tayi tace "' kan bala'i lallai ka taɓo tsuliyar dodo har ni zakai wa Allah ya isa to dan Allah idan ka gamu da wani a hanya kace wacece inna magajiyar karuwai..," Kedai baki ji dadin halin ki ba Wallahi. aehiriri ta saki wata uwar buda tare da durkuwa ta dauki kudin ta tace "' wa ai kayan Allah ya isa yafi dad'i wallahi ni gaba ta kai ni yaro bara na faɗa maka idan ina. Cin kayan Allah ya isa wani dad'i nake ji domin da be isa ba , ba zai yi uwar ka ba dan durun uwa ware ko yanzu na saka a yi gunduwa dakai sa'arka ɗaya yanzu ba da bane da yasin na zuke maka jini to yanzu na karbi Musulunci amma da nanu maka ni jinin ƙabilar *CHAMBA ce* " jan mashin din sa yayi yana mata Allah ya isa ganin tana kokari dauko huka a kugunta.. shiga cikin gidab tayi dore da jakar babko dinta saukewa tayi tana cewa ina yan iskan gidan nan suke..to wallahi ga kaya nan na kawo na shaɗana amma kudi hannu sai da na zabi giredi sannan na saro.. wacce take zaune akan kujera tana duba fuskar'ta, ta ajiye mudubin hannun ta , tace '' mu gani.., da sauri ta rarumi jakarta tace "' lah lah ban faɗa miki ba amma jeki ki gayyato yan uwan ki..," ke wallahi baki da yarda ki bari na gani mana sai kace zanci ba kowa a cikin gidan duk sun tafi nema nima yanzu zan tafi.. Oh to gani dubu ɗaya ɗagawa a gwada dubu biyu sakawa ana neman zaɓi dubu uku... kai jama'a wai dan Allah inna ina zaki kai kudi ne haba ni ban taɓa ganin wannan lukutar masifar ba wallahi.. taikun ubanki ta faɗa rarumar jakar ta a guje jujal ya shigo yana shiga bayi. da sauri ta suri jakar ta , tana shiga uwar daki tare da rufo kofa daga labule tayi wani dogon tsaki tayi ta fito tana cewa malam lafiya baka san nan gidan matan aure bane...? Hajiya kiyi hakuri na sani danki jujal anyi kittifakin duk wata dabba da take area nan shi ke sace ta jiya ya sace wani katon zakara..shine aka kawo karar sa.. kuttumar ubancan kai jaburu fito fito ashe yanzu ka fara ha'inta, ta ban sani ba.. dan kato dagora yace '' wallahi hajiya sai addu'a lamarin ya'yen nan kiyi hakuri karki yi mai baki dane ka haifa amma baka haifi halin ka ba.., jaburu da yake leƙowa yana sanda yace '' na fito ba zaki danka ni gurin sa ba ko..?, kai wannan kai ta shafa akwai wani dan durin uwar da ya isa ya zo cikin gidana ya daukar min yaro na fito wannan case din da nake dakai daban ne.., ta fada tana kwance damarar da tayi mamaki ne ya kama dan kato da gora Allah me iko ya kasa fahimtar ina zancen ta ya dosa. fitowa yayi yana cewa gani nan.. kai dan kwal ubanka ashe jiya ka kama katon zakara shine ko yanka daya ka bani inma siyarwa kayi ai ka bani ladan ganin ido.. zaro ido dan kato da gora yayi yana cewa Hajiya zakaran sata ne fa.. yatsuna fuska tayi tace '' ni na sata..?, ta fada tana zaro ido.. fita yayi yana cewa a wannan tafiyar sai na dauko bataliya da uwar da danta duk halin su ɗaya.. dariya inna tayi ana cewa Wallahi jaburu kaban mamaki wannan abin kamar lagwani zaka gudarwa me makon ka tafasa mai jiki da duka ko yasan ruwa ba sa'an kwando bane ba.. uhmmm wallahi inna wannan da kike gani yasin yakai ni gurin su na shiga uku sai sun fasa min fatar jiki da duka.. Mtssww yar uwar ka jawa ita , ta gado halina wallahi kai kaga nan namiji amma ba kamar ba namiji ba tur da halika tun kafin na daga maka nono ka fito min da kudin da kasiyar da zakaran nan.. kai inna gaskiya na siya kaya dasu yanzu ba ko sisi ya faɗa yana fito mata da aljuhun sa.. jaburu bazan fa yarda ba sai ka fito min da kudi kai din duk wata hanyar cuta ka santa dan haka fito min dashi ko yanzu wallahi ranka ya ɓaci...... KARUWAN CIKIN GIDA Ga channel dina kuyi min subscribe Dan Allah wai ina masoya na suke. https://www.youtube.com/@nasreenminallah https://vm.tiktok.com/ZSBRtRQmN/ Domin samun update kuyi following dina Book ¹ EPISODE ¹⁸ Haba inna zan miki karya ne nace miki babu su lamma ne suka ce muci abinci da kuɗin..... tashi tayi ta tsaye tana cewa shikkenan ka cuce ni jaburu me makwan ka kawo ko sululu (taliya ) ne na dafa mana muci kasan mahaifin ku baya cas baya as sai fakewa da yake a kofar gida da suna malimta ba tafiya nema shi kuma ba zai iya bugun kasa ba wai a cewar sa haramin ne shi ya zauna inda Allah ya ajiye shi, Raliya da ta sheka uwar kwalla ta fito tace '' to na tafi karki bawa , wani dakina zan dawo.., to masha Allahu bani kudin kwanan yau da kika yi.. ta faɗa tana me ko mata hannu Raliya tace '' haba INNA wallahi kinsan ba wanda yazo jiya bani da kudi ki bari idan na dawo nayi miki balance.., tab lallai baki da hankali a'a uwar balance za kiyi min ba balance ba maza jaburu fito mata da kayan ta. waje zuwa anjima nasan wani zai zo ya kama.. shigowa malam yayi da buta a hannun sa da alama alwala ya zo yayi domin an kusan kiran sallar la'asar idan ya daura alwala zai zauna ya yi karatu kafin lokacin sallah yayi jin abin da take faɗi yace '' wai fauziyya ban hanaki tara min mutanen banza a cikin gidana ba...?, wani kallo tayi mai tare da cewa ke raliya zo ki fice karki dawo min idan ba kudi kika zo da shi ba yauwa haɗa har da kayan ki.. ganin bata kula shi ba ya debi ruwa abuta ya shiga bayi yana nema mata shiriya a zuciyar'sa. Raliya tace '' inna dan girman Allah kiyi min afuwa wallahi jiya na wanda na kwana dashi ke kanki sheda ce.., wani uban salati ta saki tana tafa hannaye tace '' uhmm fito fili kice ina zargina ina yi muku laɓe.., wani numfashi ta saki ta buɗe jakar ta. ta ciro dubu ɗaya tace '' gashi nan wallahi da ita , na tashi sai ki riƙe zan ciko miki dari biyar.., amsa tayi tana juyawa alamar ta raina tace '' ke wai ban tara ku ba na faɗa muku na kara kuɗin dakunan gidan nan to shinkafa ma ta ƙara tashi da sauran kayan masarufi dole nima na ƙara farashin kwana a cikin gidan nan duk ƙaruwar da taga zata iya to , ta lalemin kuɗi ta bani kalas.... to shikkenan Insha'Allahu zan ciko nawa ne..? kwana ya koma dubu biyu.. okay ashe ma ba tsaɗa ta fada tana fita zama tayi tana cewa jaburu naji ɗazu kana cewa yar uwar ka , ta bugo ko..? ciro wata matacciyar waya yayi yana cire batirin cikin ta , tare da sakawa a baki ya mai da yace '' eh ta bugo na ma bata shawara ba sai kin kirawo ta ba.., fisgar wayar tayi tace '' da yake kai ka haifa min ita ai dole kace ka bata shawara matsa min daga gurin nan ko yanzu na bajeka a gurin nan.., matsa mata yayi yana fita waje.. number jawa ta lalubo ta dannawa kira sai dai a kashe taji wayar tsaki taja tana ajiye wayar a kan taga fito da kayan da ta siyo tayi tana ɗagawa tana ajiye wa. ★★★★★ kuka sosai tane Hajiya zuba mata ido tayi ta kasa cewa komai kwantar da kan'ta tayi a kan cinyar Hajiya tace '' wallahi bana son komawa Hajiya ke baki ga abin da suke ba ko kunya ta basa yi musamman ma jawaher shi kuma yaya ya dinga biye mata. dan murmushi tayi ta matsar da kalbar da ta rudewa Najlah fuska tace '' ban da abin ki najlah matar sa ce fa me ruwan ki da wannan, wannan ba dalili bane ba me ya saka bakya son zama a gurin yayan ki..?, shiru tayi ta turo baki Hajiya tace '' maza tashi ki shirya biyu da arba'in.., ƙasa koda motsi tayi hajiya sai da tayi mata jan ido sannan ta , tashi gaba ki ɗaya kayan ta , ta haɗa mata driver ya zo ya ɗauka jawad sai da yabi ko ina na cikin gidan yayi musu sallama sannan ya shigo saminta yayi ta zuba ta gumi fuskar nan duk hawaye ta kasa riƙe su, mene dalilin da najlah ke gudun sane..? ya tambayi kansa bashi da me bashi amsar nan dan haka dole ya kawar da ita sallama yayi ɗago kan'ta tayi a razane tamkar taga wani dodo batare da ta amsa ba hajiya da take cikin daki ta fito tana cewa najlah maza tashi ku tafi kin dai san jirgi baya jira Allah ya kiyaye hanya.. tashi tayi fuskar'ta duk ta kumbura kallon ta yayi yace '' a haka zamu tafi ki saka mutane su dinga kallon mu maza jeki ki wanke fuskar ki , Hajiya tace '' kyale ta Jawad neman hanyar labewa take karta jawo maka asara ita ba abin da ya dame ta .., to yace addu'a tayi musu yace amin har gurin mota ta rako su shiga najlah tayi tana sauke ajiyar zuciya shima shiga yayi direba ya ja su . suna zuwa airport checking akai musu lokaci yanayi suka hau najlah da take farko shi kuma yaka ciki tun da suka shigo wani matashi yake kallon ta lura da haka Jawad yayi ya kalle ta yace '' tashi dawo nan.., batai musu ba , ta dawo jawad ya zauna yana aika mai da kallon banza dauke kai yayi, zaman jirgin ne ya addabi jawad domin lokaci bayan lokaci yana kallon matashin nan still idon sa nakan najlah. ji yayi kamar ya shaƙe shi ya huta ya saba biyan first class amma a wannan dawowar da za suyi kawai sai ya biya normal set ashe rabon ran'sa ya ɓaci ne.. suna sauka ya kamo hannun najlah suka fito suna ƙoƙarin barin reception din ya gamu da wani abokin sa tsayawa da suka yi suna magana matashin nan ya tawo gub najlah da take zaune tana danna wayar'ta sallama yayi mata ɗagowa tayi tana amsawa domin ta zata irin me tambayar nan ne.. wayar sa ya miƙo mata yace '' dan Allah ki samin number ki.. wallahi tun da kuka shigo nake kallon ki dan ma yayan ki kamar baya so nayi miki magana.., juya kan'ta da za tayi suka hada ido da jawad da sauri ta , tashu tsaye tare da barin gurin tunowa tayi da lokacin da jawad ya kusan ballanta akan wani yayi mata magana yaushe zata ƙara yadda ayi na biyu.. jawad sallama suka yi da abokin nasa lokacin najlah ta zo kama hannun ta yayi suka soma tafiya ganin be mata magana ba hankalin ta ya kwanta. har suka shiga mota bece mata komai ba. sai ma mai da hankalin sa yayi kan waya da alama abu me mahimmanci yake yi horn suka yi masu gadi suka wanga le gate din gidan. turo hancin motar su direve yayi Najlah tabi motar yan sanda da tagani a cikin gidan da kallo tana mamakin me ya kawo yan sanda ko ya canza ma'aikatan gidan daga sojoji ya kawo yan sanda ne. bata da me bata amsa haka ta buɗe murfin mota, ta fito shima fitowa yayi be bari an bude mai ba ma'aikatan gidan da sukai jigum jigum suka karaso gurin ubangidan nasu, suna gaisheni sa Alhaji Barka da zuwa ka dawo lafiya.. Barka dai ma same ku lafiya..? ya faɗa yana yiwa najlah alamun ta shiga cikin gidan.. wucewa ciki tayi me gadi yace '' Alhaji wa'yannan yan sanda zuwa sukai su tafi da Hajiya shi ne muka hana su shiga ciki su kuma suka ki barin gidan sai ya fito.., da sauri jawad ya kalle su yace '' okay ba damuwa bara naje naji me ke tafe dasu karku damu kowa ya koma bakin aikin sa kai isa shigar da kayan dake cikin boot ciki..a parlour zaka ajiye idan na zo na shigar mata dasu daki.. an gama oga suka ce suna barin gurin. ƙarasowa gurin su yayi ya miƙa musu hannu suka gaisa ɗaya daga cikin sune ya ciro I'D card yace '' suna na jibrin abba gumel daga hukumar yan sanda an aiko mu ne daukan Hajiya domin tayi faɗa da wata har ta fasa mata kai.., duban I'D card din sa yayi tabbas haka ne amma me ya haɗa ta da Jawaher yace '' okay ba damuwa ku koma za mu zo Insha'Allahu yanzu na dawo zuwa anjima zan zo., basu yi mai gardama ba kasancewar babban mutum ne idan yace a kore su daga aiki ta zauna korarsu za ayi suka ce to godiya yayi musu ya shiga cikin gidan jawaher ya tarar a zaune ta ci ka gaban ta da kayan motsa baki tana ci ta ɗora kafa ɗaya kan ɗaya sallamar da yayi ne ta janyo hankalin ta , ta juyo da sauri tare da rungume shi tana farij ciki kiss tayi mai a kuma tu tare da haɗe bakin su. dai-dai lokacin najlah ta , fito shan ruwa domin ta duba babu a cikin fridge din dakin ta. ƙasa ɗaga kafar ta , tayi saboda kunyar da taji ta kamata wai su wa'yannan basu da hankali ne kome ku tsabar rashin kunya ne juyawa tayi ta , koma Jawaher da ta lura da ita , saki wani malalacin murmushi kadan ta gani sai sakewa ta gagare ta a cikin gidan nan shima Jawad sarai ya ganta. sakin juna suka yi suna aikawa da juna wani irin kallo tamkar zasu cinye junan su ji suke kamar sun yi shekara dari basu haɗu ba Jawad da ya gara jin wani irin son Jawaher yana shigar mai zuciya ji yake ba macen da takai ta komai wani irin kallo yake binta dashi kamo hannunta yayi yana cewa sweet heart kin kara kyau.. komai naki na musamman ne.... wata dariya tayi tana jifan sa da kallo ƙasa tace '' uhmm dauke ni mu shiga daki kaga irin tanadin da nayi maka.., wani irin dad'i ne ya ziharce shi yace '' a you sure..?, kai ta gyaɗa mai cikin wani irin salo tace '' amma a dakin kusan da najlah zan nuna maka mu shiga ciki.. be mata gardama ba domin ji yake ko me tace mai yi zai yi domin ya faranta mata shaf ya manta da maganar yan sanda balle yayi mata ita.. ajiye briefcase din sa yayi ya ɗauke ta , tamkar wata yar baby ya buɗe dakin wow komai ta gyara shi ga wani irin kamshi da yake fiddawa.. sauke ta yayi akan gado da sauri ta , tashi ta janyo hannunsa tana wasa da yan yatsunsa tace '' no ba sai ka wahala ba yau ni zan yi komai ka dawo daga tafiya kuma in wahalar da kai a'a gaskiya.., da kallo ya bita har ta gama cire kayan ta , ta cire mai kashe fitila tayi ta mai da ita dum light sosai jawad taka binta da kallo ji yayi ba wanda ya fisa sa'ar mace a duniya.. wani irin zazzafan romantic take masa shima yana mai da mata da martani haɗe bakin su tayi a cikin zuciyar sa ya shiga karanto addu'ar da manzo Allah ya umarta ta saduwa da iyali. ya fara ƙoƙarin daukar hanya gam ya ji ta kara susucewa yayi gaskiya sweet ke ta musamman ce kullum kamar sabuwa kike ƙara zama.. ɗan ya mutsa fuska tayi alamun wai zafi take ji rarrashin ta ya fara tana sakar mai kukan shagwaɓa lokacin da ya shiga ihu suka saki a tare duk wani abu da yake faruwa tamkar a cikin dakin najlha kasa kwanciya tayi domin ba abin da bata ji rasa inna zata saka kan'ta tayi taji dad'i wai su wa'yannan basu san kunya ba ne ba ina dakin su yake tashi tayi, tana zagaye dakin tare da toshe kunnuwan'ta. har komai ya lafa ji da tayi Jawad yace ya bawa jawaher gift din one million ta zaro ido ikon Allah sai kallo. ta gumi tayi indai su yaya zasu ci gaba da irin wannan abu, bata san yaya zata yi ba kuma duk tasan makirci jawaher ne shi kuma yake biye mata. tashi tayi ta shiga toilet wanka tayi ta fito daure da towel riga da wando ta saka sanna ta ɗora abaya a sama green colour da adon milk colour an mata beadwork mayafin ya daura kalbar da hajiya tayi mata , ta zubo hadon bayan ta bata tsaya yin kwalliya ba banda lipstick da ta saka slippers ta zura ta fito tunda matar gidan bata. bata abinci ba ita bara ta nemawa kan'ta abinci jarababbun banza ina zasu tuna da ita , sai kace sun shekara basu haɗu ba ko wanka ta tabba bata kaishi yayi ba balle ta bashi abinci ko itama asan da ita suka hau abu duk wannan maganar a zuciyar ta , take yin ta shiga kitchen tayi ba komai bama alamun an ɗora girki a cikin gidan balle tasa ka ran ɗauka shiga store tayi ta debo fulawa ta ajiye to tana da kuka ko kanwa domin wallahi sha'awar dan wake take cikin sa'a ta buɗe cabinet taci karo da robar kuka da kanwa daukowa tayi ta ajiye. wanke hannun ta , tayi ta ɗora ruwa ta kunna gas dawowa tayi ta kwaɓa fulawa dai-dai yadda take son ta nan danan ruwa ya tafasa ta soma jefa dan wake bayan ta gama ta wanke hannunta kwai ya dauka ta wanke shi ta saka a cikin ruwa. buɗe fridge tayi ta dauko salad da tomato da onion ta wanke su sannan ta soma yanka su ta ƙara wanke su ta ajiye sannan ya sauke dan wanken ta ta tsame shi sauke kwai tayi ta dauko bowl ta zuba. da yake taga suna da manja ta zuba ta saka yaji da magi sannan ya kawo wannan salad din nan da ta yanka da su albasa tumatur ta saka sai kwai daukan lemo tayi ta fito dai-dai lokacin jawad da Jawaher suke saukowa sarkafe da hannun juna da alama hirar da suke yi ne dad'i ce jawad sai murmushi yake dauke kai tayi, tayi kamar bata gansu ba da sauri jawaher tace '' am sorry ganin honey ya mantar dani ban saka an yi miki girki ba shi dai ga nashi can.., ta faɗa tana shafa gemun jawad... dan murmushi najlah tayi tace '' lah ba damuwa ko sunyi balallai na iya ci ba saboda girkin na da nasu is different...., wani abu ne ya tsayawa jawaher a makoshi wato ita da take cin na cooker's bata san darajar kan'ta ba kome..kallon Jawad tayi domin ganin wanne action zai dauka akan ta shi kuwa jawad nunawa yayi be ma san me suke faɗa ba ya wuce a zuciyarsa kuwa cewa yayi ashe bawasa na ajiye a cikin gidana. najlah ma shiga daki tayi habaka da tayi ba karamin bakantawa jawaher rai yayi ba sun tafi sun barta sai ta ma rasa tsayuwar me take yi a gurin nan juyawa tayi ta hau sama ta fasa ma saukowa har taje ƙarshe taga idan ta fushi kenan ta nuna mata taji haushi da sauri ta sauko tana cewa honey honey wallahi yau ba ƙaramin farin ka sakani ba , bawai dan ka bani gift ba a'a ganin ka da nayi ba karamin jin dad'i nayi ba da farin ciki da na dawo naga baka nan gani nayi gidan nan yayi min baƙi na kasa sukuni ina jin kamar na rasa rabin jiki na raina duk yabi ya ɓaci shi ne fa wata kawar zeey ta shafa face ɗin ka na rotsawa shegiya fuska wallahi duk macen da tayi kuskuren aurar ka koda na wuni ɗaya ne sai ta bakunci lahira Jawad ba Jawaher ne , domin ni kaɗai aka halicce ka...duk wanda zai soka a duniyar nan bayan nice balle wasu mutane da suke nuna maka son karya a face a zuciya ba haka bane son manufa ne da kwaɗayin abin hannun ka..da karfi take fadar haka. najlah kuwa tabe baki tayi tace '' kaga mahaukaciya kamar abu me kyau kike faɗa kema da kinyi zaman gidan yari...ke kinfi dawanau cin kai wallahi mahaukaciya ai gashi yan sanda sun miki dirar mikiya a cikin gidan ki dan ma yaya ne wallahi da wani namjin ne da tuni ya fasa miki baki ya kora ki gidan ku.. Jawad da ya zuba mata ido har ta karasa so zama tayi akan cinyar sa yace '' sweet me ya sakaki kai haka yanzu fa dole naje gurin su na basu hakuri.., turo baki tayi tace '' face dinka fa ta shafa.., to sweet ni ta taɓa..? kwantar da kan'ta tayi tace '' ina son Ka * MIJINA* duk ranar da aka wayi gari kai min kishiya mutuwa zanyi bazan iya jurar ganin ka , kana shiga dakin wata ba..., dan murmushi yayi yace '' kidin ga addu'a idan hakan yana cikin kaddara ta Allah ya yaye miki wannan kishin naki.., dan turo baki tayi tace '' beb mu dena maganar nan wallahi har naji zuciya ta na wani irin bugu.., to shikkenan Allah ya kyau.. amin tace tana tashi daga kan cinyar sa abincin sa ta soma zuba mai soma ci yayi kwata kwata abincin be mai dadi ba kallon ta yayi yace '' anya kuwa ba zamu canza cooker's ba wannan abincin be mun ba.., Najlah da ta fito daga daki ta saki murmushi ta ƙaraso tace '' yaya ga wannan nan na dafa amma kaɗan na iya ci daman cin girkin arna sai wanda yayi niya amma ni sam ba suyi min ba..daga masu yawo da mini skirt sai masu yawo da three quarter kuma a cikin gidan hausawa musulmai tamkar babu kishin addinin Muslunci ba.., wani abu JAWAHEER ta haɗiya tace '' najlah ya ishe ki haka ya ishe ki Jawad kana kallon ta , tana gasa min magana wannan fa maganar da take yi dani fa take ni bana yiwa na ƙasa dani rashin kunya idan kuwa nakasa dani yayi min komai gatan shi sai na hukunta shi domin wannan ba , tarbiyya bace.., da sauri jawad ya kalle ta haka ma najlah ran'sa ne ya ɓaci daga wannan maganar kallon JAWAHEER yayi yace '' shut-off....stop don't tell me anything jawaher tarbiyar da aka bawa najlah ita aka bani me najlah ta fadi da har zaki wannan maganar..? eyeee.., ganin yadda ya zame mata tamkar zaki tsoro ya shigi zuciyar'ta bata , taɓa zaton jawad zai iya yi mata wannan shouting din ba ja da baya tayi ta ruga sama da gudu kuka na shirin subbuce mata tunda sukai aure yau ne kaɗai suka sami matsala har Jawad yake ɗaga mata murya wato najlah annoba ceee.. juyowa gurin najlah yayi da sauri ta ajiye bowl din hannun'ta ta tafi daki da gudu binta yayi zata , rufo kofa ya tare ya shiga durkusawa tayi tana kuka tace '' dan Allah kai hakuri wallahi banyi dan ranta ya ɓaci ba.., dake nake magana kika sako baki daman kasa kunne kike kiji wacce hira muke yi..? maganar da nayi ba da karfi nayi ta ba amma har kin ji najlah kinsan halina.., ture dankwalin kan'ta tayi tana kuka tace '' wallahi kawai nazo wucewa naji banyi haka da wata manufa ba kayi hakuri bazan sake ba..zanje ma na bata hakuri amma dan Allah karka dake ni.., KARUWAN CIKIN GIDA Ga channel dina kuyi min subscribe Dan Allah wai ina masoya na suke. https://www.youtube.com/@nasreenminallah https://vm.tiktok.com/ZSBRtRQmN/ Domin samun update kuyi following dina Book ¹ EPISODE ¹⁹ ta faɗa tana tashi tsaye takaici ne ya kama shi wai karya dake ta kamar daman can din yana dukan ta. cikin ɓacin rai yace '' nidai na faɗa miki wallahi karki sake na gara ganin kin ƙara abin da kikai yanzu.., da sauri ta gyaɗa mai kai cikin daure fuska yace '' ɗazu wanda ya tambaye ki number kin basa ko..?, da sauri ta girgiza mai kai hawaye nabin kuncin ta tace '' wallahi Allah ban bashi ba.., wanni kallon kin raina min hankali yayi mata da sauri taja baya tana kuka tace '' Allah da gaske nake.., juyawa yayi zai fita zama tayi akan gado tana cewa haka kurum kace ba wanda zai kula bayan kana nema kayi min aure.. ashe be tafi ba sai ji tayi yace '' what.., da sauri ta juyo jikin ta har rawa yake. tace '' Allah ba abin da nace.., idon sane ya kaɗa yayi ja lokaci ɗaya ɗaga hannun sa yayi zai mare ta sai kuma ɗunkule hannunsa ya juya, ya fita bece komai ba. najlah ta , tsorata da taga yanayin sa zama tayi tana dukan bakin ta , tace '' nima wanne tsautsayi ne ya kai ni da faɗar haka bayan nasan ban bayar ba kuma ga yaya da mugun ji uhmm koma mene aishi ya jawo ta faɗa tana kwanciya a kan gado. jan wayar ta , tayi ta soma charting jin anyi kiran sallah magarib, ta tashi. tayi ta shiga toilet ta ɗauro alwala ta fito. shinfiɗa daduma tayi, ta zura hijabi ta tada sallah. bayan ta idar ta zauna tana lazumi sosai gidan ya zama tamkar ba kowa ko motsin mutum ɗaya bata ji ba duk da daman ba wata hayaniya take ji ba amma Jawaher tana kunna kida tai tabin waka to yau ba wannan. dariya tayi da ta , tuna irin faɗan da suka yi ta ci gaba da jan carbinta bayan an tada sallar isha ta tashi tayi sallah tana idarwa ta fito domin hanjin cikin ta ta fara motsi yunwa take ji. ta koma tare da zuro kan'ta tana kallon hagu da dama domin tana tsoran haduwa da yaya. ganin jawaher tayi taci uban wasu kananan kaya rigar kwata kwata bata da hannnu iya cibiya ga wando nata ko cinya be rufe mata ba ga wani uban hil da ta saka kai kace irin arnan nan ne na kudu wanda basu san ma mene Musulunci ba. kanta yaci attachment brown colour ga uban gashin ido kare mata kallo tayi tas ana mamakin anya kuwa matar nan ba mahaukaciya bace kai biri yayi kama da mutum duk yadda aka yi ta taɓa hauka koma yanzu tana cikin sa kallon hannun ta , tayi duk farata kallar kayan da ta saka bayan kuma ɗazu babu shi a hannun'ta kauda kai tayi ta fito tana addu'ar Allah karya haɗa ta da yaya. keee gaban tane ya faɗi jin sunan da Jawaher ta kira ta , dashi amma sai ta dake ta nuna ma bama tasan tana yi ba. taci gaba da tafiya cikin ɗaga murya tace '' ke dake fa nake.., banza tayi mata da sauri jawaher ta , tashi tace '' najlah.., sai a lokacin ta juyi bata kalle ta ba sai ma kau da kan'ta da tayi tace '' yes.., da sauri jawaher ta , tofar da chingum din da take ci a ƙasa eh lallai matar nan kan uba tab tace '' tun ɗazu ina kiran ki kin min banza yanzu kuma kince min yes ni sa'ar wasar kice ke yarinyar nan ko sharing miji muke abin da za kiyi min kenan.., wani kallo najlah tayi mata tace '' kin gama na tafi dan wallahi yunwa nake ji...?, JAWAD JAWAD JAWAD wallahi sauko sauko bazan iya ba dole ki tattara kayan ki , kibar min cikin gida sai kace wacce muke sharing din miji kike min wannan uwar gadarar to gidana kika zo dole kibi dokata kuma karki sake ki shigar min kitchen tunda ke baki da kunya.. wani kallo najlah tayi mata , tace '' wannan ne kuma baki isa ba tun da ke ba ke kika siyo abincin ba..., hannu ta ɗaga zata mare ta da sauri ta rike dai-dai shigowar Jawad ashe baya cikin gidan a tare suka juyo tare da sakin hannun juna.. da wani kallo ya bisu na tuhuma ganin haka najlah tace '' yaya sannu da , dawowa hannun aunty ne ga buge na fito ne naji ihun ta.., da sauri jawaher ta kalle ta , ta shiga uku yarinyar karama ta iya munafurci da kissa kasa magana tayi sai ma sakar baki da tayi tana kallon ta.. shi kuma yace '' okay sannu hice ko baki ji ciwo ba..?? tamkar wata kadangaruwa ta ɗaga mai kai. good yace ya zagaye su ya huce. ajiyar zuciya najlah ta sauke tana barin gurin jawaher da ta rasa gaba ki ɗaya abin da ya dace tayiwa yarinyar nan. shiga kitchen ta dauko madara da zuma ta fito , har yanzu tana inda ta barta da alama mamaki ya kusan kashe ta. a zuciyar NAJLAH kuwa cewa tayi kaɗan kika gani yar iska me kama da zubin karuwan Lagos.. huce ta , tayi tana dariyar mugunta kasa ƙasa da wani kallo jawaher ta bita da shi sai kuma ta hau sama da dan gudun ta kai tsaye study room din Jawad ta shiga yana zaune ya baza takardu a gaban sa ga computer agaban sa da hannu yayi mata nuna ta fita da alama zoom meeting suke yi domin taji Muryar mutane. tamkar ta kurma ihu haka ya jawo mai kofa ta rufe. to ita yanzu ina ta kama ne..? bata da wata madogara fa hmmm dole tasan abin yi kafin yarinyar nan ta zame mata ciwon idanu.. kar fa wata ran tace tana son Jawad wata zuciyar ta jefo mata wannan maganar a fili tace '' da kuwa wallahi nayi gunduwa gunduwa da ita.., wayar tace , tayi ringing ganin sunan inna da sauri ta dauka daman bukatar inna take saukowa tayi tana cewa wallahi inna ina cikin matsala ina bukatar temakon ki inna komai ya fara lalacewa, ban san ta ina zan fara ba inna yau Jawad ni ke ɗaga min murya , daman can be kama shi ba yadda muke so amma yanzu yafi da lalacewa inna wayyo Allah na shiga uku inna ga hassimi ya dawo kar fa Jawad ya neme shi suyi magana kwanakin baya , ya yi min maganar sa inna. ta karashe maganar ta , tana buɗe dakin ta key tayi mai ta rufe ta zauna Inna kuwa dariya ta dinga yi tace '' da kika ce bakya ji..wato jawaher ke kaza ce ci ki goge baki da yaya kika aure she ..? wanne irin fadi tashi ne banyi da ku ba amma duk kunna namin ku ba yan goyo bane wai yanzu takai ta kawo hajiya bilki ni zan ɗaga waya na kirata taki ta daga wato buƙatar ku , ta biya kun mata da inna kun mai da inna juji.., wallahi inna ba haka bane ba , so nake na siya miki gida ki dawo nan ko na gina miki wani acan kinga kya zuba yan haya kudin ne be hadu ba.. oooh yaushe rabon ki da zuwa *BINYERI* ...? tun fa ranar da aka dauke ki aka kai ki ɗakin Jawad yau shekara nawa sai dai muyi waya kuma nasan kina nan kina halin naki sai ma abin da yayi gama na sani saboda son abin duniyar ki ba zai barki kiyi zaman aure ba.. dan haka turo da dubu dari biyar zan je gurin malam za ayi mai abin da ma zai manta iyayen gidan nashi.. inna yayi yawa wallahi bani da wannan kudin a haɗa a har UMMEE.. cikin faɗa inna tace '' to sai an jima duk randa kika samo kudin kya kira ni..ita kuma wannan ba abin da ta isa tayi na riga da , na dade da gamawa da ita, ke kinga ko kallon banza tana yi miki ballantana baraza..?, da sauri jawaher tace " a'a dan Allah kiyi hakuri zan turo miki..,'" wata dariya ta saki tace '' oh sai anjima dan katina yana karewa.., kit, ta kashe waya kafin ma Jawaher tayi magana dan cije lips din'ta, tayi ita kan'ta tasan dole INNA taci kudi kafin tayi mata aiki amma ba yadda za tayi dole ta ɓatar da koma nawa ne ganin asirin ta ya rufu.. ★★★★★★ duk wani magani da , aunty ta bata sha tayi na turaren nan ne kawai ba tayi ba ta yi brush tayi wanka kayan bacci ta saka ta kashe komai ta kwanta tana janyi wayar ta.. wani murmushi ta saki lokacin da taci karo da sakon ya MUNEEF da sauri ta shiga alamun kuka ya saka yana cewa beauty kin barni cikin kewa ko ..? ko iya bacci bana yi.. rungume wayar ta , tayi tare da ɗagowa ashe ma yana online video call ya kira ta. Sai da kirjinta ya buga sannan ya dauka tuno da fadan yaya tayi MUNEEF yace '' najlah bana ganin ki kunna fitila.., dan murmushi ta saki tace '' uhmm a'a.., Saboda me nima bara na kashe ki dena gani na mene amfanin ke kin ganni ni bazan ganki ba gwara kenan na kira ki normal call, na dade da sanin ko shekara nayi ban kira ki ba....ba zaki taɓa nemana ba.., turo baki tayi tace '' Allah ba haka bane yaya muneef kasan halin yaya shine ke hana ni wai ɓata lokaci ne kwanaki har cewa yayi zai fadawa su jadda aure nake so...ba karatu ba..., dariya MUNEEF yayi yace "' da kuwa nafi kowa murna kinga sai nazo na dauke ki mu tafi tare mayi karatun tare Allah ya mallaka min ke najlah Allah idan na dawo zan wa ya haidar magana yayi wa yaya ko jadda Insha'Allahu tare dake zan koma.., dan shiru tayi tana tunani can tace '' ya muneef su nihila zasu yadda...?, me ya saka kikai min wannan tambayar ina ruwa da abin da ke cikin zuciyar'su wannan su ta shafa Allah ya ganar da su gaskiya.., Wallahi ina jin tsoro kar tace a'a bata sona ban san dalili ba.. karki damu bame raba mu idan ba ikon Allah ba wanda ba yadda za muyi da shi ina ma neman tsari da shi. to Allah ya shige mana gaba mana. cewar najlah. wani dad'i ne ya shige sa..., yace '' amin ya Allah bye naji kina hamma Allah ya tashe mu lafiya kin dai ki barina, na ganki.., bye Amin ya Allah tace tana kashe datar ta da wayar baki ɗaya ajiye ta , tayi. tayi addu'a ta kwanta. wannan kenan. honey kayi hakuri idan ma akan fadan ɗazu kake fushi dani.. ta faɗa tana kamo hannun sa. zare hannunsa yayi yace '' JAWAHEER ban taɓa zaton zaki iya kallon idona ki faɗi haka ba hajiya fa kinsan irin matsayin da Hajiya take dashi a gurina kamata yayi inhar kina yi min son gaskiya ki so duk wani wanda ya shafe ni.. Najlah kuma nayi mata fada tace kiyi hakuri zama ta baki hakuri amma ita ba , tayi haka domin ta ɓata miki rai ba... wallahi inhar kina son zaman lafiya a cikin gidan nan to ki kauda ido akan najlah komai tayi yarinta ce ke babba ce be kamata ace kina biye mata ba..., wani abu ne ya tokare mata.. zuciya dannewa tayi tace '' to shikkenan Insha'Allahu zan gyara ba komai , wallahi komai ya wuce.., ta karshe maganar ta , tana kissing din sa biye mata yayi wayar ta ce tayi ringing da sauri ta cika shi ganin wanda ya kira ta shiga uku besan tana da aure bane ya kira ta a wannan lokaci kallon Jawad tayi da gaba ki ɗaya hankalin sa na kanta... KARUWAN CIKIN GIDA Ga channel dina kuyi min subscribe Dan Allah wai ina masoya na suke. https://www.youtube.com/@nasreenminallah https://vm.tiktok.com/ZSBRtRQmN/ Domin samun update kuyi following dina Book ¹ EPISODE ²⁰ Sauri tayi ta kashe wayar gaba ki ɗaya tace '' wayyo Allah waya ta , ta mutu ba chaji ni wallahi shaf na manta ban saka ta a chargi ba gashi gobe ina da lecture tun 8:30 clock zan fita wata kila sai yamma zan dawo. shiru yayi tamkar me nazarin wani abu jikin jawaher ne yayi sanyi ta kalle sa tace '' sweet lafiya kayi shiru....? , wata nannauyiyar ajiyar zuciya ya sauke yace '' a'a bakomai.., ajiye wayar ta , tayi akan bed side drawer tace '' Please mijina ka faɗa min gaskiya me yake faruwa, naga kamar kana cikin damuwa dan Allah ka faɗa min me yake damun ka..? kar nima ka jefa ni cikin damuwa.., kama hannunta yayi, yay mata kiss a kan hannun ta kumatun ta , ya ja yace '' bakomai.., are you sure..? yes ya faɗa yana kashe fitilah.... ihun da suka ji da sauri jawad ya tashi yace '' kamar kukan najlah.., jawaher kokarin rike shi take ya fisge hannun sa ya fita da gudu yake sauka domin jin ihun yayi yawa knocking ya fara yi ganin kofar a kulle. jin ana bugu tace '' yaya bazan iya buɗe wa.., ta karshe tana kuka da sauri ya juya key ya dauko lokacin, jawaher ta biyo shi budewa yayi jikin sa na rawa da gudu najlah ta rungume shi jawaher ta kunna fitilo haske ya gauraye ɗakin. wani abu ne ya tokare mata zuciya ganin najlah a jikin jawad ga kirjin ta sai gogar na jawad yake duk da ya fita tsayi sai ta koma karama a jikin sa dauke kai tayi tana zama a bakin gadon ta , tace '' me yake faruwa kike kuka..?, ajiyar zuciya ta sauke tace '' mafarki nayi wani abu ya zo cinye ni.., ɗago kan'ta jawad yayi yana shafa gadon bayan ta yace '' ki dinga addu'a kinji be kamata kiyi ihu ba idan abin cutarwa ne cutar da ke zai yi.., hawaye ta share ta kara kwantar da kan'ta a jikin sa tace '' to.., jawaher tamkar ta shake ta haka take ji, tashi tayi tace '' cika ta mu tafi Allah ya kiyaye gaba.., ƙara rungume shi tayi tace '' wallahi ba zan iya kwana ni kaɗai ba.., da sauri ta kalle ta , tace '' ke me kike nufi da wa kenan za ki kwana.., ta faɗa wutar kishi na ruruwa a cikin zuciyar ta da idanuwanta tuni suka soma birkicewa... zaunar da ita yayi yana rarrashin ta yace '' kiyi alwala kiyi addu'a kinji ba abin da zai same ki idan ba ikon Allah ba..., kukan shagwaɓa ta saka mai , habawa jawaher ba shiri tabar dakin domin ba zata iya kallon wannan bakin cikin ba. lallaɓa najlah ya shiga yi har tayi bacci gyara mata kwanciya yayi ji yayi an riko rigar sa , hannun'ta yabi da kallo ta riƙe shi gam da alama har yanzu tsoro take ji, ga announce baby face din ta , tayi ja da alama taci kuka dan murmushi ya tsinci kansa da yi, a hankali ya cire mata hannu a jikin kayan sa kallo yabi kan kirjin ta da sauri ya kau da kai gudun samin matsala, domin ji yake tamkar ya aika ta abin da zuciyar'sa ke ƙi tsa masa. duk da haka sai da yakai mata kiss kan kirjin'ta da yake bata ƙarasa balle botiran rigar ba ya ƙara gyara mata kwanciya tare da kashe mata fitila addu'a yayi mata ya duba ko ina normal normal sannan ya rufo kofar. sai a lokacin ya tuna da Jawaher dan murmushi yayi besan wanne irin kishi ne da ita. hawa sama yayi ya buɗe dakin sa , samun ta yayi ta zuba ta gumi jin sautin buɗe kofar sa , da sauri ta juyo ta kalle sa tace '' har ka dawo..?, kura mata ido yayi yace '' uhmm.., tashi tayi tace '' ai na zata kwana za kayi acan ni wallahi ban ma yarda akwai abin da ta gani naga take taken yarinyar nan kai kuma ka dinga biye mata.., zama yayi yana miƙo mata hannun sa kin bashi hannunta, tayi sai ma fita da tayi ta bugo mai kofa. girgiza kai yayi ya tashi ya shiga toilet wanka yayi ya fito domin shiga dakin najlah da yayi ba ƙaramin riƙe kan'sa yayi ba da tuni lamari ya ɓaci.. to be kwanta ba sai kusan ɗaya.. lokacin jawaher tayi bacci yaje dakin ta , ya kwanta kusa da ita. ta fara ture shi sai kuma ta hakura ganin irin salon da ya fara bi da ita wanda ya gigita tunanin ta tabbas JAWAD jarimi ne.... ko a cikin maza. kiran sallar asuba shi ya tada shi da sauri ya shiga wanka a gurguje ya fito boxer kawai ya saka da jallabiya maroon colour sai kamshin turare yake iya bath spray yake ko tsayawa saka turare be yi ba. tashin jawaher ya fara yi amma ta ture hannun sa ƙara tashin ta yayi yace '' sweet tashi wallahi bana son kin tashi da hurin nan da kike yi kin san mahimmanci sallar asuba kuwa., tashi tayi tana turo baki tace '' Please wallahi jiki na har ciwo yake ko wanka ban yi ba.., cikin takaici ya kalle ta yace '' daman cikin dare dana tashi naje nayi wanka ba kiyi ba...?, uhmm wallahi bacci ya dauke ni.. ransa ne ya ƙara ɓaci yace '' kinsan kuwa illar barin sperm a jikin mutum..?, ILLAR BARIN MANIYYI YA BUSHE A JIKIN MACE. Ƙamshi mara daɗi da wari a farji: Busasshen maniyyi yana iya cakudewa da gumi ko jinin al’ada ko ruwa na farji, ya haifar da wari mara daɗi. Wannan wari yana iya zama abin kunya da damuwa, musamman ga mace mai tsafta. Cututtukan farji: Busasshen maniyyi yana iya zama gurbin da bacteria ko fungi ke hayayyafa, wanda ke iya haddasa: Bacterial vaginosis Candidiasis (infection na yisti) Kaikayi da zubar ruwan fari mai wari farin ruwa mai santsi ko cakude da rawaya: Yawan barin maniyyi a ciki ba tare da an wanke ba na iya kawo fitar farin ruwa mai launi, wari, da nau’i iri-iri. rikicewar sinadaran farji (pH imbalance): Maniyyi yana da alkaline, farji kuma acidic. Idan aka bar maniyyi ya bushe, yana rushe daidaiton sinadaran farji wanda ke haddasa itching, kumburi da rashin jin daɗi. Yiwuwa mace ta kamu da cututtuka masu watsuwa ta hanyar jima’i (STIs): Idan ba’a tsaftace farji ba bayan jima’i da bushewar maniyyi, zai fi sauƙin yaduwar kwayoyin cuta idan an kamu dasu Najasa ta manne jiki: Busasshen maniyyi a jikin mace har ta zauna da shi yana hana karɓar ibada (sallah, karatun Alkur’ani, shiga masallaci) Allah (SWT) yana son masu tsafta: “Lalle Allah yana son masu tuba kuma yana son masu tsarkake kansu.” (Suratul Baqarah: 222) Haramtaccen kasancewa cikin janaba Mace cikin janaba ba ta da izinin yin wasu ibadoji sai ta wanke kanta. A duk lokacin da aka yi jima’i, ko an samu inzali ko ba a samu ba mace ta wanke jikinta ko da aƙalla ta share maniyyi kafin daga baya ta yi wankan janaba. A guji barin maniyyi ya bushe a ciki ko a waje, domin kare lafiya da ibada. ya mutsa fuska tayi tace '' naji Insha'Allahu zan gyara ka tafi lokaci na kurewa.., girgiza kai yayi ya fita ba tare da cewa komai ba knocking kofar najlah ya fara tashi tayi ta buɗe hannunta rike da carbi cikn sanyin murya kamar ko da yaushe tace '' yaya barka da asuba.., barka dai har kin tashi..?, bata ce komai ba ta gyaɗa mai kai.. good Allah yayi miki albarka. amin tace tana juyawa ba ƙaramin dad'i yaji ba da ya ganta har , ta , tashi. kai tsaye masallaci ya huce... najlah komawa tayi ta zauna ana tada sallah ta tashi, ta tada kabbarar sallah bayan ta idar ta dade tana addu'a yau ba ƙaramin dad'i taji ba ganin, abin da yake faruwa da ita be fari da ita ba sai mugun mafarki... tashi tayi ta shiga tayi wanka ta fito daure da towel wasu riga da wando ta ɗauko gray colour yan gidan puma ta saka rigar takai iya cinyar ta sai wando shi kuma be ƙarasa rufe mata kaurin ta ba hijabi ta saka ta fito.. kai tsaye kitchen ta nufa ma'aikatan gidan har sun fara ƙoƙarin ɗora breakfast cikin girmamawa suka fara gaishe da ita. amsawa tayi cikin sakin fuska tare da tambayar su, ya aiki cikin jin dadin bata da girman kai suka ce fine.. daukan madara tayi ta fito cin karo tayi da Jawaher da wasu shegun kayan bacci. dauke kai tayi zata wuce ta , tace '' najlah.., ganin a yadda ta kirawo sunan ta sai ta jiyu tun daga sama har ƙasa take kallon ta sai kuma ta dauke kai tace '' me kike yi da madara haka jiya kin sha yau ma kin sha ..? ko ance miki kyau ta yake dauko ta ne..?, rasa wacce amsa zata bata tayi dan haka ta shige zata wuce ta janyo hijabin ta , tayi shaƙe mata wuya yayi ba shiri ta cire shi tana tari ƙasa tayi domin ciwon ta na asma na shirin tashi. jawad shigowa yayi bakin sa dauke da sallama chak ya tsaya da sauri ya ƙaraso yana kallon JAWAHEER a rikice yace '' ko baki san tana da asma ba kin tsaya kina kallon ta .., cikin kuka da sarkewar numfashi najlah tace '' yaya shake min wuya tayi dan na ɗauke madara wayyo Allah mutuwa zanyi.., ransa ne yayi mugun ɓaci tunda ga alama nan hijabin najlah na hannun ta ɗagowa yayi ya dauke ta da mari hagu da dama yace '' jawaher kinsan kuwa me kikai..? najlah ta na da asma madarar da ta dauka ke kike siya..na lura.., be karasa ba yaga najlah na shirin suma da sauri ya dauke ta , ya fita da ita dawowa yayi ya dauke key din mota ya fito buɗe motar yayi ya saka ta sannan ya shiga mazaunin direba...ya zauna.. jawaher kuwa kusan daskarewa tayi a tsaye har yanzu ta kasa amince da Jawad ne ya mare ta har sau biyu tana riƙe da kuncin ta , jira take ta farka daga mafarkin da take so take , taji ta farka amma abu yaci tura zama tayi tana cije lips din ta sai yanzu ta ƙara tabbatarwa da ba mafarki take ba a zahiri haka ya faru...ba kuka ta fashe da shi kasa ko da motsi tayi gashi tana da appointment da wannan alhajin tunowa da tayi da wannan maganar da sauri ta , tashi tahau sama tana ci gaba da kukan ta wayar ta , ta dauka number eman ta buga har ta katsai bata dauka ba , bata gaji ba haka ta dinga kira sai a na hudu ta dauka ƙara fashewa tayi da kuka tace '' eman na shiga uku jawad yau da hannun sa ya mare ni.., eman ko dai kin hako wannan abin ne wallahi haka jiya yayi min hulakanci kuma duk akan wannan shegiyar yarinyar.., dariyar ta , ta danne a cikin zuciyar ta , tace waya ce miki barno gabas ce faɗa da aljanna ba riba ai kin dena miƙe kafafuwan ki inhar ina numfashi amma afili sai tace '' haba jawaher shikkenan dan mun yi faɗa sai na tafi makabarta ina hake hake ni wallahi na ma manta da abin da muka yi in banda yanzu da kika tuna min.., eman dole nayi wannan tunanin yau ma fa wa'azi ya zauna yana yi min jiya kuma shiru yayi yana tunani anya kuwa jawad be fara fahimtar wanu abu, ba ko kuma an fahimtar dashi na tambaye shi yace min ba komai ni wallahi ban aminta da zaman najlah a cikin gidan nan ba , yarinyar nan abin da take yama bani mamaki jiya fa rungume shi tayi a jikin sa , tayi bacci eman dan girman Allah idan kinsan zafin zuciya ya saka, ki kin je kin rusa min aiki na ki faɗa min wallahi Malam ya tabbatar wa da inna inhar ba tonowa akai ba to aikin nan bashi ba warware wa.., aikin san shi yake da yau da gobe karki manta matsayin Jawad zai zauna a haka ne mutumin da yake rike babbar kujera ta alkalan alkalai shi kike tunanin zaki shin fiɗe kafa kina iskanci son ranki na tare da ya gano ki ba... hmmm eman ba zaki gane ba Jawad ya sauya min ko dama can ban samo kan jawad ba kamar yadda nake so marina fa yayi akan najlah.. ta faɗa tana share hawayen ta. eman tace '' Allah ya kyauta sai ki faɗawa INNA..ko UMMEE.., cikin takaici tace '' UMMEE fa kika ce..? to JAWAHEER idan ba su ba wa ne zai miki maganin matsalar ki dole ummee ta sani saboda sai kina yar gaban goshin sa, sannan zata samu abin da take so.., jawaher tace '' anya kuwa wannan shawarar da kika bani me bullewa ce..?, kinga jawaher tunda tan tama kike sai an jima idan kika yanke shawara kya ban labari.. da sauri jawaher tace '' eman kin canza min da ba haka kike min ba me ya faru ko dai fadan da mukai da ke ne baki huce ba..?, kinga ni wallahi na manta sai an jima ina tare da baby ne.. oh to shikkenan idan kika gama kya kira ni. ta faɗa tana kashe wayar ta , ko zeey zata nema to amma zeey tayi mata me..? ita da har yau take so ta koma gidan mijin ta ba farko amma abu ya gagara.. zuba ta gumi tayi, ta rasa hanyar bullewa.. ********************** jawad yana kaita asibiti suka amshe ta , saboda lalurarta data, tashi tana bukatar temako sosai. zama yayi yana zuba ta gumi ganin likitan ya fito da sauri ya tashi cire facemask din ta, tare da cire safa tace '' yallaɓai karka damu mun samo kan'ta sai dai dan Allah a guji abin da zai ƙara saka ciwon ta, ya tashi. Insha'Allahu ya faɗa yana buɗe dakin da suka kai ta , tana kwance an saka mata Oxygen kirjin'ta sun saka mata wani abu tamkar wayoyi irin na cable din chaza. tausayin ta, ne ya kama shi jan kujera yayi ya zauna a kusa da ita yana riƙe da hannun ta. dauke mata kalbar da ta zubo mata fuska lokaci ɗaya tayi fayau lamun tana jin jiki tamkar wanda, ta dade bata da lafiya.. wayar sace tayi ringing da sauri ya ciro ta number abba ya gani jikin sane yayi sanyi besan da wanne baki zai sanar mai yace jawaher ta shaƙe najlah na. dauka yayi jikin sa a sanyaye gaisawa suka yi cikin farin ciki da mutunta juna abba yace '' ya iyalan naka da fatan kowa yana lafiya..?, cintar kan'sa yayi da jin nauyi da kunya saboda karyar da zai yi yace '' alhamdulilah kowa yana lafiya.., abba yace '' to Allah ya taya ka riko.., amin ya Allah. sallama suka yi, sanna ya kashe wayar yana ci gaba da kurawa najlah ido a hankali ta soma buɗe idon ta sauke shi tayi akan fuskar Jawad kasa kallon sa , tayi dan haka ta dauke kan'ta, ta rasa dalili bata iya kallon sa idanuwansa wani irin kaifi suke mata. hannun ta ya ƙara riƙe wa gam yace '' ya jikin naki..?, ba tare da ta juyo ba tace '' alhamdulilah na samu sauki.., masha Allah me kike bukata yanzu..?, ɗaya hannunta, ta saka tana kokarin cire Oxygen din da aka saka mata. da sauri yace '' ya zaki cire ta.., kuka ta sama mara sauti tace '' bana son ta, na fiso na shaki iska..., haɗa rai yayi yace '' najlah baki bari ko sai ranki ya ɓaci..su ba su san da iskar ba suka saka miki Oxygen ko kin fisu sanin abin da ya dace da ke ne.., saki tayi tana kuka har da buga kafa. gaskiya yaro yaro ne ya faɗa a cikin zuciyar sa a haka zai yi abu da ita , to idan Ubangiji ya basu rabo tayi yaya dashi kenan dashi yana da yakinin ba abin da zata iya to ita kan'ta ba a gama rainon ta ba , balle tayi rainon wani tashi yayi zai fita sautin kukan ta , ta ƙara tace '' dan Allah karka tafi ka barni.., juyowa yayi ya yi mata wani kallo da sauri ta sauta kan'ta tana kauda kan'ta ta rasa dalili duk lokacin da yaya yayi wa mutum wani kallo to wallahi take mutum zai nutsu. juyawa yayi ya fita office din likitan ya , yi knocking.., bashi izinin shugowa tayi, shiga yayi ya zauna yana cewa Ya tashi ne wai bata son oxygen.., to yallaɓai dama kirana kayi ba sai ka sha wahalar zuwa da kanka, tunda ta dawo normal sai a cire mata muje na gani.., tashi yayi yana cewa bakomai wallahi to muje din.. fita yayi ta bishi a baya bude dakin yayi har yanzu tana ƙwance ƙaraswa gadon, ta tayi tana tambayar ta ya jikin nata me yake damun ki yanzu..?, najlah tace '' ba abin da nake ji yanzu dan Allah ki cire min wannan Oxygen din nan ya takura min.., okay ba damuwa ta faɗa tana cire mata duk abin da suka saka mata tare da ƙara gwada ta , magani ta rubuta mata ta miƙa mai tace '' tunda ta samu sauki zan sallame ku.., okay ba damuwa cewar Jawad.. sallama ta basu kasa fita da najlah yayi a wannan yanayin da take ciki wani kishi ne ya dannar mai zuciya ashe daman a haka ya dauko ya sam be lura ba. yaya ba yanzu, zamu tafi bane..?. Wannan maganar da tayi ita , ta dawo dashi cikin nutsuwar sa yace '' najlah yanzu, zamu tafi amma bara na fita na dawo.., turo baki tayi tace '' zaka dade to mu fita tare mana bana son zaman asibitin nan.., abinda ba yanzu za muyi ba idan na gama jarabawa na gama littafin dake waje na sa WANNAN LITTAFIN NA KUDI NE 1k Duk meso zai biya ta wannan hanyar 8141785374 Amina alhasan Muhammad opay Ya turo da shedar biya ta nan 08141785374 Yan niger 1000fcfah ta my nita Ku turo da shedar ta nan 08141785374 Dan girman Allah idan baki shirya ba karki min magana inga receipt evidence shine zan kula ki bana son flashing yi min magana ta WhatsApp. Dan Allah a kiyaye. KARUWAN CIKIN GIDA Ga channel dina kuyi min subscribe Dan Allah wai ina masoya na suke. https://www.youtube.com/@nasreenminallah https://vm.tiktok.com/ZSBRtRQmN/ Domin samun update kuyi following dina Book ¹ EPISODE ²¹ Wani kallo yayi mata da sauri ta kawar da kai fita yayi ya jawo mata kofa ta gumi tayi tana tunanin wanne irin zama za su yi bata san rashin imanin JAWAHEER ya kai haka ba sai yau da ta shake ta , da ace su hajiya sun mara mata baya da duk haka ba zata faru ba , yaya mugu matar sa mugu kifa kan'ta tayi tana kuka bata san ya shigo ba sai ji tayi ya dafa ta da sauri ta juyo zuba mata ido yayi yana kallon ta cikin tuhuma yace '' najlah kukan me kike akwai wani abu da yake miki ciwo ne..?, kai ta girgiza tace '' gida.., okay ungo wannan saka mu tafi.. noke kafaɗa tayi tace '' uhmm gidan mu fa Yola..., haɗe rai yayi ya miƙa mata amsa tayi tana kuka ta saka riƙe hannunta yayi suka fito. buɗe mata mota yayi ta shiga ya zagaya ya shiga mazaunin driver. key yayiwa motar ya fara tafiya yace '' me zaki ci..?, banza tayi mai tana kauda kan'ta girgiza kai yayi ba tare da yace komai ba ya ci gaba da tafiya har suka isa gida sai yanzu yake tunowa akwai maganar zuwa gurin yan sanda shaf ya manta zasu ɗauke shi ƙaramin mutum amma insha'Allahu kafin ya tafi office sai ya fara biyawa can. parking yayi bece mata komai ba ya rufe motar yayi gaba najlah da sai yanzu ta ankara da sauri ta soma jijjiga murfin motar tana bugawa kuka ta fara yi mai bawa shukoki ruwa da gudu ya isa gaban sa yana Alhaji kamar da mutum a cikin motar nan.. remote ya danna yana cewa okay da sauri najlah ta fito iya tashin hankali ta shiga daman tasan shirun nan da yayi mata ba abu bane me alkairi ba. da gudu tabi bayan sa har suka shiga cikin parlour bata dena kuka ba shiru alamar ba kowa a cikin parlour. shiga dakin ta , ta tayi da gudu be tsaya bij kanta ba ya hau sama kai tsaye toilet ya shiga yayi wanka sannan ya fito. a gurguje ya shirya cikin dark blue suit daukan briefcase dinsa yayi ya fito daman yasan ba lallai ya sami Jawaher a cikin gidan ba duk da ya san bata aikata daidai ba amma sai ya tsinci kan'sa cikin nadama. saukowa yayi gidan ya ƙara shiru saboda yan aiki suna bangaren su, suna gama aikin su sai subar part din nata su koma na su. Kiran najlah ya shiga yi shiru yaji dakin najlah ya leƙa tana kwance bacci ya ɗauke ta shiga yayi ya dan buga pillow da take kai sarai tasan shine ɗan haka tayi kamar bacci take ta saka hannnun ta , ta buge mai hannu tare da ture hannun nasa ta juya ta koma barinta na hagu. tana facing ban go. a hankali ya kara cewa najlah.. banza tayi mai ganin bata kula shi ba ya fita yana ja mata kofa yana fita ta doka uban tsalle ta tashi tana cewa wallahi tun da har ka rufe ni a mota zaka sani. komawa tayi ta zauna tana buga game a wayar ta gajiya tayi da zaman dakin ta fito rufe kofar parlour ta jawo tana zagayawa bayan gidan sosai take mamakin girma irin na gidan. jin jina kai ta dinga yi tana ayya irin kudin da ya Jawad yake dashi ci gaba tayi da tafiya wani guri ta gani zagaye da gabion da alama guiding ne shiga ciki tayi flowers ne kala kala masu kyau ga bishiyo zaro ido tayi ganin ɗawisu, su hudu suna yawo a cikin gurin da sauri tabi bayan su, tafiya suka fara suna ƙoƙarin guje mata dariya ta dinga yi da ta gaji da zagaye ta zauna akan wata farar kujera inda a gurin kujeru ne da table a tsakiyar su ajiyar zuciya ta sauke tana ci gaba da limshe idon ta sosai take jin kukan tsintsaye kala kala. buɗe idon ta , tayi tana kallon sararin samaniya tashi tayi domin ta soma gajiya da zaman da take yi a gurin shiga parlour tayi ta huce kitchen indomi ta dafa taci ta sha ruwa sannan ta koma bedroom dinta kwanciya tayi tana sauke ajiyar zuciya. ★★★ gaskiya yallaɓai bazan yarda ba ko baka ga yadda ta fasan kai ba , bayan tun jiya nake jiran ku na kashe kudina naje anyi min treatment. cewar baby ta fada tana girgiza jikin ta da kugu.. sai kace gaɗa ta zo yi. cije lips din'sa JAWAD yayi besan ya akai jawaher tasan wannan yar iskar yarinyar ba me zubin karuwai sai da aka kirawo ta domin a kashe case ɗin ba tare da ya kallo inda take ba yace '' tun da kince baki yadda ba ki fadi nawa kika kashe na biya ki.., maida idon ta sama tayi tana kallon pop din da yake office din tace '' Ni ba kudi nake so ba saboda basa gabana ba kudin da ya isa ya ruɗani adalci kawai nake so ayi min abi min hakkina. juyowa yayi ya kalle ta yace '' ke wai baki da kunya ne baki san wannan waye a gaban ki ba shine fa cheif justice na ƙasa baki ɗaya wallahi dan yana da kirki ne da ba zan taɓa zuwa ba balle ki gansa kiyi mai rashin kunya, yallaɓai tafi dan uban'ta tayi abin da taga dama ai dai gurin mu zata kai kara to kune sama damu..ko a gidan giya ma akwai babba.., dakatawa tayi da chingum tace '' what lallai ma a fasa min kai sannan kake wannan maganar wato kasar nan ba adalci ba za'a iya hukunta na sama ba shikkenan akwai babbar kotu ta wajen Ubangiji.., Jawad danne ɓacin ransa yayi yace '' look officer be kamata ace kayi mata haka ba kuskure ne ya riga tayi kiyi hakuri, bawai ina nufin cewa baki da hanli bake aa wanna dan isani ne ko wai cin hanci na baki a'a ba ɗaya Allah ya baki hakuri.., kallon Jawad tayi taga gaba ki ɗaya ko , kallo bata ishe sa ba wani kululun takaici ne ya shage mata maƙogoro tace '' okay shikkenan ba matsala na hakura.., Jawad zura hannu yayi a aljihu ya miko mata rafar kuɗi yan dubu dubu.. da kallo tabi kudin ta girgiza kai tace '' bazan karfa ba wallahi ai jawaher kawata ce kawai dai a lokacin sabani ne ya shiga tsakanin mu da sharrin shaidan ni yar taraba state ce.... to aku sarkin magana tambayar ki yayi cewar officer. wani kallo tayi mai tare da daukan jakarta a inda ta ajiye ta akan table tace '' am Alhaji dan Allah muje ka sauke ni a hanya wallahi bansan gari ba ko sati uku banyi da zuwa garin nan ba karatu nazo.., Jawad ko kula inda take be ba yayiwa officer sallama ya fito tafiya yake tamkar me tausayin kasa yana ƙarasowa escort din sa ya buɗe masa kofar mota shiga yayi da sauri ya zagaya baya ya zauna direve ya tada motar suka fara tafiya. basu tsaya a ko inaba sai a wajen aikin sa parking suka yi ya fito tunda ga kan kananan ma'aikata har manyan ma na kasa dashi suka shiga gaishe shi duk inda ya gifta girmama shi ake yi. buɗe masa kofar office din sa aka yi shiga yayi da sauri sakateriyar da take kula da office din ta , tashi tana gaishe shi mutane ne kusan guda goma suna zaune dalama shi suke jira ɗaga mata hannu kawai yayi suma suka shiga gaishe shi amsawa yayi yana ƙoƙarin shiga cikin office ɗin sa. ja mai kujera, zama yayi yana kallon tarin folder din da ke gaban office dinsa bisimallah yayi ya dauki na farko tare da neman temakon Ubangiji *ALHAJI ALEE BABALLE KWARA* runtsai idanuwansa yayi mijin UMMEE cije lips din'sa yayi tuni idanusa suka kada sukai ja , yajawa mutumin nan kunne amma yaki yarda yabi abin da yace so yake ya yaye mai fatar akuyar da ya saka akan ta kura. UMMEE kawai yake kallo amma da tuni ya gama da mutumin nan forder din'sa ta dade tana yawo akan table din sa ajiyewa yayi a gefe yana daukan wata , gama dubawa yayi ya bada umarni wa'yanda suke waje daya ya shigo cases, kala kala..ya tarar wani kansa har sarawa yake gama ganin su yayi ya ci gaba da aiki a cikin laptop din'sa jin sallamar Hisham yayi amsawa yayi ba tare da ya kalle sa ba jan kujera yayi ya zauna yana cewa kwara fa ya aiko takarda ta gargadi ka manta da sabgar mutumin nan kawai besan mutuncin kan'sa ba.., ɗago idon sa yayi yana cire bakin glasses ɗin da ya saka yace '' akan mee..?, look JAWAD abune da kasani na sani wannan mutumin suke da gwamnati yanzu ba abin da bazai iya ba gurin ya kawar da kai dan haka , ka kyale sa wallahi duniya ta ishe shi darasi.., Please HISHAM mubar maganar nan.. to shikkenan angon...? ya fada yana dariya haɗe rai Jawad yayi yace '' ango kuma kai ka daura min auren da kake cemin ango.., kanwata mana. HISHAM ya fada yana danne dariyar sa. Jawad ya ɗago yana kallon sa tare da girgiza kai yace '' Allah ya shirye ka tayi kankanta, ta ko ina na girme tanafi karfin ta.., abin ba anan yake ba., oga a hankali zaka buɗe hanya gwara a yi maza a yita ko Allah zai saka mu samu baby. da sauri Jawad ya kalle sa lallai kan HISHAM ya kunce wace za ta iya daukar ciki har ta haife shi ya raine shi. ganin irin kallon da jawad yake mai yace '' look man ita fa mace sunan ta mace wallahi abin da kake rainawa yake baka dariya wata ran kuka zai baka dan haka tun wuri ka dawo cikin hayyacin ka yaran nan da kake gani sun fi dadin sha'ani wallahi saboda abin da kake so su zama shi zaka nuna musu kwakwalwar su fresh take, kaine na farko dan haka abin da kake so shi za a yi.., Uhmm wallahi bazan iya ba kai haba is different kasan kuwa wace big lady... dariya Hisham yayi yace '' a'a sai ka faɗa jawad ko ta ina na fika gaskiya wasu fa mayan matan wallahi kalle su nan abin da suke yi kare ba zai shin shina ba duk kyalkyal banza ne bakomai ne a cikin gasara ba ban da ruwa malam auri yarinya tayi shirme a gaban ka , kayi dariya maganin tension kenan me ya saka wa'yanda suka manyan ta wasu a cikin su, idan suka tashi aure suke auro yara domin su mori kuruciyar su kai na lura girman kan ka yake hanaka morar arziki.., dariya yayi yace '' kai bana son wannan zancen kai daman ba tun yau nasan cewa kai jarabar ka , tafi karfin ka.., ai shi ya saka saboda jarabata nayi mata *BIYU* ban zauna da daya ba.. wani littafi Jawad ya dauka ya hullomai yana cewa wallahi HISHAM ka kiyaye ni. HISHAM yace '' gaskiya ta na faɗa maka sannan kuma nake bin dare ina raya sunan bayan na saka maganin bacci.. saboda tsoran uwan tale su giwa babba..., haɗe rai Jawad yayi yace '' wallahi HISHAM ka kiyaye ni..., Jawad gaskiya ce bazan gaji da faɗa maka gaskiya ba duk idanuwan'ka sun makance baka ganin ko wacce mace sai Giwa babba. hmmm zan faɗa mata kaga ta dena ganin ka da mutunci. to ai ita tasan ba karya na faɗa ba , ba giwa bace ba.. shafa kan'sa yayi yana sauke ajiyar zuciya abubuwa sun mai yawa ganin haka Hisham yace '' JAWAD ka dena saka , damuwa a ranka komai yana da iyaka insha'Allahu wata ran sai labari ɗazu UMMEE ta kira ni tana faɗa..., furzar da wata iska yayi me huci yace '' me tace maka...nayi..?, kuyi hakuri da wannan wallahi na fito daga makaranta ruwa yayi min duka gashi ba damar na koma cikin makaranta na yi nisa. KARUWAN CIKIN GIDA Ga channel dina kuyi min subscribe Dan Allah wai ina masoya na suke. https://www.youtube.com/@nasreenminallah https://vm.tiktok.com/ZSBRtRQmN/ Domin samun update kuyi following dina Book ¹ EPISODE ²² Wallahi JAWAD ko zance ɗaya ban fahimta ba faɗa take yi sosai wai ni nake zuga ka idan na cika dan halak nabar ka.. kai ya jinjina yace '' Allah ya kyauta kaga yanzu fa daga police tasion nake.., subbanallahi me ya faru..?, cewar Hisham. Jawad yace '' madam ce ta bugawa wata kwalba a kai dakyar yarinyar ta yarda kaga wallahi duk raina a ɓace yake.., tab Allah ya kyauta dole ranka ya ɓaci bata kyauta ba me ya haɗa su..? dauke kai JAWAD yayi da daga kallon sa yace '' akan ta taɓa picture dina da yake dakin sama.., Picture dinka wannan wanne irin kishi ne..? to naga bedroom sirrin mutum ne me yakai yarinyar har bedroom har taga picture dinka, ta taɓa..? Jawad yace '' wallahi abin da na kasa fahimta kenan naso nayi mata wannan maganar sai kuma naga ba ita ya dace ta amsa min ba ban da Jawaher, jawaher kuma ina tunanin tayo fushi tabar gida.., wani kallon HISHAM yayi wa Jawad gaskiya jawad abin tausayi ne amma afili sai yace '' ina ta , tafi me ya faru da har tayi fushi..?, bashi labarin abin da ya gani da kuma abin da najlah ta faɗa mai. Hisham yace '' tab Allah ya kyauta ka kyale ta kawai duk inda taje tama dawo.., haka nake tunani ya fada yana ƙoƙarin ɗaukar wayar sa sosai yayi mamaki ganin sunan Abba, Allah ya saka lafiya ba ɗazu sukai waya ba ya fada yana ƙara wayar sa a kunne.... sallama yayi jikin sa , asanyaye domin besan me zai ji ba. abba amsawa yayi yana cewa dazu mantawa nayi ban faɗa maka ba daddy Ka bashi da lafiya yana ma asibiti ka kira shi kai mai ya jiki idan da hali kaje har landon din kai mai ya jiki.. buɗe baki yayi zai magana kamar abba ya sani yace '' JAWAD bana son jayayya kayi abin da na saka ka sai an jima., ya faɗa yana kashe wayar sa ciro wayar yayi a kunnen sa yayi shiru HISHAM tashi yayi yana cewa oga bara na tafi naje na ci gaba da aiki na. kai kurum Jawad ya gyaɗa mai ya dade yana kallon number daddy baya tunanin zai amsa amma dan cika ummarnin abba zai kira shi domin abba mutum ne yayi mai komai a rayuwa mutumin daya toshe kunnuwan'sa ya biya mai sadaki ya bashi ɗiyar'sa ɗanna masa kira yayi, ta kusan katsaiwa aka dauka JAWAD sallama yayi. Mubashshar yace '' daddy yana bacci amma idan ya tashi zan mai magana.., ya fadi haka ba tare da ya amsa sallamar sa ba sarai ya gane me maganar yana jin mom Ihsan tana cewa kai junior wane ya kira shi kake ce mai yana bacci..?, kit ya kashe wayar be karasa jin me za suce ba ajiye wayar yayi yana binta da kallo jikin sa ne ya ƙara sanyi. ci gaba da aikin sa yayi gaba ki ɗaya zuciyar sa ba walwala jin ringing din wayar sa , an kirashi da wata number wanda ta fara da +44 da alama kiran daga Landon ne , ɗauka yayi ya kara a kunne Muryar saif ne yake cewa sorry yaya ga daddy nan ya shiga toilet ne.. dan murmushi yayi yace '' saif bakomai ya jikin nasa...?, Alhamdulilah wallahi da sauki jinin sane ya hau kuma a jiya lafiya muka zo kasar nan. Jawad yace '' Allah ya kara sauki.., amin yace yana miƙawa daddy wayar dan shiru yayi sannan yace '' ina wuni...?, Daddy yace '' lafiya ..., ya amsa mai a takaice. Jawad yace '' ya jikin naka yanzu abba ke sanar dani..?, Oooh ya kyauta da sauki. sosai Jawad ya danji zafin yadda yake amsa mai duk Abba ne ya ja mai sai yace '' Allah ya ƙara sauki.., amin cewar daddy. amsar wayar Ihsan tayi tace '' sai an jima an hana shi magana me tsayi.., bece komai ba ya kashe wayar aiki ya dinga yi domin karma ya bawa kwakwalwar sa , wani hutu da za tayi tunani.. POV... JAWAHEER. Wallahi baby naji dadin haɗuwa dake ya faɗa yana shafa fuskar ta. Jawaher murmushi tayi tace '' anya kuwa ka kai ni jin dad'i.., murmushi yayi yace '' gaskiya na fiki irin wannan haɗuwa haka dakyar abun nawa fa yake shiga yadda kika san ni na buɗe ki .., Allah ya hajj. riƙe hannunta yayi yana wasa da zoben hannun'ta yace '' wallahi gaskiya kin cancanci duk wata kyauta ungo wannan key din motar.., zaro ido tayi tana kallon key din Benz tuni wata zuciyar ta ambato mata sunan *JAWAD...* yayi yaya da shi me za tace mai amsa tayi tana murmushin dole tace '' Nagode Allah ya jikan mahaifa wallahi ba abin da zan ce maka alhaji daga haduwar mu har da wannan hidima..?, saka hannunsa yayi a baki yace '' kinfi karfin haka wallahi kedai kici gaba da gyara ko nawa ne tambaye ni ki gyara ciki da waje domin naji dadi .., wasa ta fara yi da key din motar tace '' Nagode sosai.., haɗe bakin su yayi sun dade a haka sannan ta dubi lokaci karfe bakwai da sauri ta kalle sa tana tashi daga cikin sa tace '' zan tafi gida dare yayi.., Oh ba damuwa ba za kiyi wanka bane sai muyi tare mu kara shan soyayya.. daukan kayanta tayi ta fara sakawa tace '' a'a idan naje gida na yi.., Please baby dan Allah idan kinje ki kira ni wallahi ban so tafiyar nan taki ba dan dai kince bakya kwana.. kai gwara jawaher ki faɗawa mutumin nan gaskiya ya zage da yawa da wannan shawarar da zuciyar ta , ta bata tace '' sweet sai dai gobe muyi waya ina da aure.., kut wanne wawan namiji ne ya barki kina fita ai irin ku ko kofar gida ba'a fari ku tafi ina da wannan agida wallahi hini da kwana aikin more rayuwa zan dinga yi.. sosai kalmar wawan namiji ta daki zuciyar'ta, tana son Jawad tana kaunar sa dan haka tace '' be kamata kace mai wawa ba ya bani dukkan wata yarda ne.., Alhaji yace '' gashi nan kinci amanar sa kuwa.., dan murmushi tayi ta dauki jakar ta , tace '' Nagode sosai wannan key din motar ka bawa direba ya kai min wani gida idan na gama dukkan wani shirina saina fara hawan ta zan baka address din inda za'a kai ta...., Saboda me ya fada yana mata kallon ban koshi ba .... kauda kan'ta tayi tace '' Saboda JAWAD mana.., Bakinta ya subbuce.. ta fadi haka da sauri ya tashi yana kallon ta cikin mamaki yace '' JAWAD cheif justice...?,kodai wani..?, Kai ta gyaɗa mai Alhaji yace '' tab dara taci gida..., ban gane ba kasan sa ne ...?, cewar jawaher Beb na san sa mana ni yaron sane nine shugaban Company sa na J.Buzu na sarrafa ɗanyan mai..amma mai ya saka kike wannan harkar yana da dukiyar da har jikokin jikokin sa ba za suyi talauci ba Jawad be dogara da albashin sa ba ,yana business din ɗanyan mai...? kaga sai an jima zan maka text messages din address din gidan.ta fada tana tafiya.. kai kurum ya gyaɗa mata ya shiga tunanin kala kala .. yadda ta shigo da facemask cikin hotel din haka ta fita da shigar ta, ta kirki hijabi da safa da facemask shiga motar ta tayi ta fara tafiya tana tunane tunane, anya kuwa ba turo wannan mutumin akai ba domin a tarwatsa ta..? to wa zai haka ...? kawayen ta basu da wata a laka da Jawad eman ce kaɗai itama tana jin ko number sa bata da ita... da wa'yannan tunane tunane tayi parking ta fito Lokacin ana ƙoƙarin kiran sallar isha dai-dai lokacin kuma motar Jawad ta danno cikin gidan da sauri ta juyo kirjinta na dukan uku uku bata san me zata ce mai ba ko kawai ta fake da faɗan su. da sukai dazu, ba halin Jawad bane lokacin sallah yayi ya ci gaba da tafiya zai tsaya ne a hanya yayi to me ya dawo dashi cikin gaggawa haka. tana wannan tunani aka buɗe mai mota fitowa yayi cikin sauri ya nufu wani fanfo ya daura alwala ya ƙara fita duk tana tsaye tamkar be ganta ba . juyawa tayi ta soma tafiya har ta shiga parlour ta , bakomai a ciki ko motsin najlah bata ji ba to ko dai be dawo da ita ba , aikuwa da tafi kowa murna wallahi. hawa sama tayi ta soma cire kayan ta shiga toilet tayi gaba ki ɗaya jikin ta ciwo yake mata sai da ta gasa ko ina sannan tayi wanka fitowa tayi daure da towel shi kuma Jawad a lokacin ya shigo. zama yayi akan gado yana ajiye jakar sa kallon ta yayi gaba ki ɗaya jikin ta yayi sanyi tsugunawa tayi tace '' Dan Allah kai hakuri insha'Allah hakan ba zata sake faruwa ba ga abincin ka nan nasan su rose sun dafa maka.., kauda kan'sa yayi yace '' bakomai ya wuce amma jawaher ina kika tafi.., wani dam dam kirjin'ta yayi har sai da Jawad yaso ya fahimta amma sai ta matsai tace '' bayan naje makaranta na biya gidan DEEYA kawata..akwai littafin da zan karba to wallahi ban ma same shi ba ta rasa inda ta ajiye gashi gobe za muyi test...., Jawad yace '' jawaher ki dena wasa da karatun ki ba'a siyar da littafin ne kika tsaya baki siya ba, ko faɗa min fa baki ba..?, tashi tayi tana zama kusa dashi tace '' kai hakuri wallahi ganin tana dashi shi ya saka ban siya ba amma insha'Allahu haka. ba zata sake faruwa ba.., Allah ya saka. Sweetheart '' abincin ka fa baza ka ci bane..?, kamo hannunta yayi yace '' da hannunki nake so ki girka min jawaher bana iya ci gashi kuma ban iya cin abincin restaurant ba.., dan dam tayi tace '' ina najlah take tayi maka wallahi nagaji...?, nasan da najlah ai na saka ki.., tashi tayi tace '' to me zaka ci...?, abu dai mara nauyi.. to na dafa maka indomi..? ta tambaye shi. JAWAHEER indomi fa kika ce...?, buɗe wardrobe ta dauko rigar'ta tayi tace '' to ka faɗa min mana kaga ban san abin da zuciyar ka ke ra'ayi ba..?, kinga kawai barshi nasha yogurt. bata ce komai ba daman haka take so bayan ta gama saka , kaya ta kwanta karfa Jawad ya neme ta, kan uba tab yadda na gaji duk wannan zancen zuci ne.. ajiye wayar sa yayi dauka tayi ta soma bincike ganin ya saka wa wata folder key da sauri ta dago tace '' buɗe min nan me kake boye min Jawad idan ma aure kake nema ka faɗa min ko kuma picture din yan mata ne ashe baka so ayi zaman lafiya a cikin gidan nan tunda har kake sakawa wayar ka key...?, wani kallo yayi mata ba kin ma raina min hankali yace '' JAWAHEER ajiye min waya ta, kinga ina ɗaukar wayar ki ne ko kuma ce miki akai kowama irin kine da ko da yaushe canza key ko wacce folder ki na taɓa tambayar ki sai ni saboda kin raina ni..., tashi tayi ta soma sharar kwallah tace '' shikkenan Jawad dan kaga ina son kane shi ya saka kake min abin da kaga dama yanzu da aka kawo ni *UMMEE* amanar junan mu ta bamu dole na binciki halin da kake ciki nasan damuwar ka , koda ace bata ce min haka ba idan har ina son ka dole zan binciki yaya kake.. wallahi Jawad dan kaga na damu dakai ne kake min haka..amma ba komai shikkenan na dena ungo wayar ka ku daman maza kun gaji harkar munafurce munafurce wasu ma aure suke yi a boye.., janyo ta jikin'sa yayi ya soma lallashin ta , tana ci gaba da kuka har kuma baccin gajiya ya soma daukan ta. ★★★. Najlah kuwa tana kallon wucewar jawaher tabe baki tayi tana tunani tun da ta dawo ba suyi waya da Hajiya ba da sauri ta dauki waya ta danna mata kira sai dai har ta katsai bata dauka ba komawa tayi ta kwanta tana game a wayar ta. jin alamar mutum ya shigo mata da sauri, ta , tashi zaune tace '' yaya kai hakuri banji sallamar ka ba ..., zama yayi yace '' ina zaki ji kina game.., ƙasa tayi da kan'ta ta fara wasa da hannun'ta. Jawad yace '' ya jikin naki hice ko kin sha maganin ki..?, kai ta gyaɗa mai kallon ta yayi yace '' baki da baki ne..?, Nasha. Good yayi kyau mu gani.. gaban tane ya fadi ta dauki ledar maganin buɗawa ya shiga yi ko ɗaya bata sha ba kallon ta yayi yace '' wannan mene .., Yaya nasha kasan akwai aljanu a cikin gidan nan ina ga su, suka maida maganin haka amma tabbas na sha.. ta faɗa tana ja da baya gudub karya dake ta.. dan murmushi yayi wanda shi kaɗai yasan ma'anar sa , yace '' NAJLAH ni dake wa aka fara haifa shekara nawa na baki..?, uhmm yaya ban san shekarun ka ba amma dai kai aka fara haifa kaga har su ya *TAUFIQ* ka girma ni kuma nice ƙarama dukka gidan sai twins su kuma ya'yana ne...., da kallo kawai ya bita kuruciya na diban najlah ga abin da ya tambaye ta , ga kuma amsar da take bashi.. da sauri tace '' yauwa idan an haɗa shekarun mu gaba ki ɗaya tun da kai ne babba zakai shekara kamar saba'in haka ko fi kaga ko ni shekara ta goma sha bakwai na girma ban ma cika sha bakwan ba sai watan gobe.., da sauri ya kalle ta tab najlah ta kulle mai kai me makon shirman ta yayi masa rashin dadi sai ya tsinci kansa a cikin farin ciki yaji dukkan wata damuwar sa ta yaye. rufe bakinta tayi tana dariya tace '' wallahi yaya ka tsofa.., shagala yayi da kallon ta , sai da yaga ta kifa kan'ta Sannan ya saki ajiyar zuciya yace '' najlah kin raina ni wane tsoho..?, dariya ta ɗanne tace '' ba dakai nake ba kai hakuri.., najlah dukan ki zanyi ne..?, girgiza kai tayi tana matsar da kitson ta da ya zobo gaban goshin ta wula ta ɗauka ta zura tana mai da gashin ta baya.. Jawad yace '' ba abin da kike bukata..?, a'a idan ma na faɗa ba yimin za kayi ba.. da sauri ya kalle ta yace '' waya faɗa miki bazan yi miki ba.., to zaka mai dani gida..? haɗe rai yayi yace '' bance miki ba kin zo kenan ba inda zaki kara zuwa idan dai ba ziyara ba..?, ka faɗa min.. ta faɗa tamkar tayi kuka. good ashe kina da saurin riƙe magana. shiru tayi bata ce mai komai ba. tashi yayi yana zura hannunsa a aljihunsa ciro wata akwati yayi me kyau ta miƙo mata amsa tayi tana budewa kyakkyawar sarka da zobe na gold zaro idon ta , tayi tace '' yaya ajiye maka zanyi...?, a'a naki ne .. Nagode sosai wallahi Allah ya saka da alkairi bara na faɗawa Hajiya da aunty.. juyawa yayi a zuciyar sa yace '' hakkin kine najlah..., ƙara kiran Hajiya tayi amma ba'a dauka ba bisa dukkan alamu dai bata kusa da wayar kiran wayar aunty Hafsah tayi tace '' ko suna ina ma owo gaba ki ɗaya basu yi picking call din ba..., ajiye wayar tayi ta kwanta tana kallon sa tashi tayi ta ajiye shi a cikin wardrobe din ta wannan gift din na yaya baƙaramin farin ciki ya saka ta ba.. kwanciya tayi ta shiga YouTube ta soma kallon wani film me taken *LEGAL WIVE....* na kasar filifindis.. ★★★★TARABA STATE. UMMEE har yanzu baki dauki wani mataki akan ya *ALTAB* ba wallahi abin da yayi yawa.. UMMEE tace "hmmm AFNAN altab yafi karfina hajiya rukayya taci nasara akai na kina ga wannan yar iskar yarinyar bata da aiki sai kawo kawayen ta , yan bariki cikin gidan nan shi ya kawo ita, ta kawo suyi shaye shaye suyi mankas tur da auren yar bariki wallahi....." wallahi UMMEE tun farko kece da laifi kika haɗa yaya da SAMHA.. *AFNAN* ALTAB ne fa ya bata musu yarinya nifa uwa ce ya zan zuba ido na ga ya aikata haka ban saka ya aure ta ba so nake rayuwar ta alkinta ina tunanin idan yayi wannan auren shikkenan ya dena abin da yake tun da danme yake abin da yake badan mace ba , to ga macen nan a kusa da shi... UMMEE kyale dan iska kamar baki san yadda suke ba sai dai shiryar Allah wacce tafi ta mutum.. To almunafiku hutar ku dabam.. da sauri suka juyo UMMEE tace "altab suwa ye munafukai...?," uhmm inji me ciwon ajali a dan ya tsa ba zama na zo yi ba UMMEE ya fada yana gyara tsahuwar sa.. altab nifa mahaifiyar kace..? UMMEE kinji na buɗe baki nace bake kika haife ni ba , ni wallahi bana son runton zunubi.. ALTAB idan zuwa kayi ka batan rai ga hanya nan ka fita.. zama yayi yace '' tsohuwa Allah ya huci zuciyar ki daman zuwa nayi ki faɗawa yaya, ya yi wa yan custom magana su sakar min kayana jiya suka kama su a Lagos kuma wallahi ba karamar asara zan yi ba coken ce fa kuma bama tawa bace kawai kwangilar shigo da su garin nan aka bani saboda ni nasan tsageru shi mutumin babba ne amma baya so sunan sa ya fito saboda mutuncin sa zai zube.. daga mai hannu tayi tace '' ALTAB ya isa ya isa lalacewar ka har takai a baka wannan kwangila wato kai baka san darajar kanka ba shine kakar ba..?, UMMEE mazajen kuɗi fa zan samu...baki ji me nace miki ba babban mutum ne me fada a ji idan aka kama shi da wannan sabga sunan sa zai ɓaci nifa wana ajiye...? dan ma ina tsoron zubewar mutuncin yaya da billahilazi cikkaken dan safara zan zama... KARUWAN CIKIN GIDA Ga channel dina kuyi min subscribe Dan Allah wai ina masoya na suke. https://www.youtube.com/@nasreenminallah https://vm.tiktok.com/ZSBRtRQmN/ Domin samun update kuyi following dina Book ¹ EPISODE ²³ Yaba *ALTAB* UMMEE kake faɗawa haka..?, kinga sako na bayar tsaka ko kinji na saka sunan ki wallahi ki kiyaye ni hmmm ci gaba da saka baki wata ran sai nayi miki ɓarin makauniya a fuska. kinga *AFNAN* ba ruwan ki shige ki bar parlour nan idan har ba zaki iya yin shiru da bakin ki ba. shiru tayi takaicin halin *ALTAB* to dadin ta ma hukuma maganin ko wanne dan iska ce kuma yana tsoron hukuma da , abin da zai yi kare ba zai shin shina ba. fita yayi bayan ya gama bayanin sa shiru dakin ya dauka UMMEE ta zuba uban ta gumi tana tunani. ★★★. lafiya tun ɗazu sai juye juye kike..?, Jawaher da take cikin matsanancin tashin hankali saboda sai yanzu yake kwance ta tuno bata ga period din ta ba , ta shiga uku , TJ ne mutumin da suka yi mu'amalla bayan ta gama period din ta lokacin bata sha wani magani ba gaba ki dayan su a buge take to tabbas ciki ne da ita.. ƙara taba ta yayi yace '' jawaher tunanin me kike yi..?, da sauri ta juyo tace '' aa bakomai kawai ina tunanin rayuwa.., kamar akwai abin da kike ɓoye min..? hannunsa ta kamo tace '' baka yarda dani ba ko..?, jawaher me ya kawo wannan maganar na ganki a damuwa kina tunani me zurfi nayi miki magana kin kalle ni sai kuma kika ƙara nisa cikin tunanin ki.. idan har kina damuwa nima damuwa nake shiga ki fadan gaskiyar abin da ke damun ki.. murmushi tayi ta kwantar da kan'ta a kirjin'sa tace '' wallahi bakomai kawai ina tunanin rayuwa da yan uwana da inna bayan wannan ba komai.., to jibi ki tafi mana tunda gobe kince kuna da test idan zaki dawo sai kiyi min magana ni ma zanje na gaishe da su.. da sauri tace '' a'a kasan wannan semester ta kusan karewa mun kusan jarabawa idan muka gama sai na tafi kaima ta yiwu kana da lokaci...kullum muna waya da su ina jin muryar su, suna jin tawa., okay haka yayi ba damuwa ya fada yana jan blanket. ajiyar zuciya ta sauke tana yiwa Ubangiji godiya da temake ta ya yarda da abin da tace kwanciya ta gyara ta rufe idon ta Allah Allah take safiya tayi.. ras gaban ta ya faɗi jin hannun Jawad ya fara yawo a jikin ta da sauri ta, ture hannun sa tace '' please sweet wallahi na gaji ba zan iya komai ba.., hannunsu ya haɗe guri ɗaya yace '' kiyi hakuri nasan da gajiya ko kaɗan ne kibar nayi.., juyowa tayi idan ba tayiwa Jawad da gaske ba to wallahi ba zai hakura ba gwara suyi baram baram idan ya so gobe sa shirya wancan shegen ya gama yi har wani zafi zafi gaban ta ke mata Jawad yayi sai suma koma ta farke. tace '' Jawad wallahi gajiya bazan iya ba bara na bar maka dakin nan.., tashi yayi yace '' basai kin barmin dakin ba dakin kine kwanta ni bara na tafi nawa.., wani sanyi taji tace '' daya fi maka ta faɗa tana jan bargo.. tasan sarai rasa ya ɓaci ɗan ne wa kawai yayi fita yayi da sauri ta rufo kofar ta , ta murza mata key kunna kwai tayi ta buɗe wata loka da karamin key kayan shaye shaye daukan kwalba biyu tayi tas ta shaye su. ta nemi guri ta kwanta lokaci ɗaya bacci ya kwashe ta. ɓangaren jawad kuwa kusa da dakin najlah yaje ya kwanta duk da yasha lemon tsami amma abin yaci tura juyi kawai yake rintsai idanuwan'sa yayi ba tun yau jawaher ta saba yi masa haka kome ne dalilinta bashi da masaniya, cikin ikon Allah bacci ya kwashe shi. koda aka kira sallah asuba dakyar ya iya tashi lokaci ɗaya zazzaɓi ya rufe shi ko hannun sa dakyar yake iya ɗagawa za maya yayi yana cije lips din sa. buɗe kofa yayi yace '' najlah najlah.., najlah buɗe kofa tayi tana waige sai kuma ta gansa a ɗaya dakin kara sawa tayi tace "' yaya barka da asuba..," hannu ya miƙo mata a hankali ta miƙo mai hannun ta , tamkar me shawara ta bayar ko karta bayar cikin wani irin yanayi ga cikin sa da ke ciwo yace '' haɗa min ruwan dumi ki kawo min nan nayi alwala..,. da sauri ta kalle sa tace '' yaya hannun ka zafi baka da lafiya ne..?, kai ya ɗaga mata cikin tausayawa tace '' sannu.., shiga ciki tayi tace '' yaya kai min nauyi bazan iya zaunar dakai ba ka zauna ga guri..sai na tafi na debo maka ruwan da zan iya shigar dakai toilet da nayi sai kayi wanka ko zazzaɓin zai sauka.., murmushi yace '' karki damu idan na dafa ki zan iya tafiya basai ki kawo min nan ba sai ki haɗa min a ciki.. right..?, to tace dafa ta yayi suka soma tafiya tace '' wallahi yaya kamar zan faɗi nauyi ne dakai.., bece mata komai ba har suka karasa toilet zama yayi ta haɗa mai komai ta juyo tace "shikkenan abin da kake bukata ina so naje nayi sallah..?," cikin yanayin rashin lafiya yace '' idan kin idar ki dawo.., to tace mai ta fita lokacin har an tafi raka'ah ta biyu da sauri ta tada sallah bayan ta idar ko zaman yin addu'a ba tayi ba ta fito dakin sa ta koma samin da tayi a zaune da a'lama sallar ma a zaune yayi ta , tausayi ya bata tace '' yaya ko likita za a kirawo..?, ɗagowa yayi ya kalle ta yace '' a'a insha'Allahu zan sami lafiya basai kin kirawo likita ba ko ya zo ba abin da zai iya yi min.., da sauri tace '' yaya consultant doctor fa...?, wallahi najlah ba abin da zai iya yi min to shikkenan yanzu wane zai iya yi maka sai a kiro shi. JAWAD yace '' kinga mubar maganar nan dauko min kayana a wardrobe.., anan dakin..? ta tambaya. Eh anan dakin yace mata yana kallon ta. tashi tayi ta buɗe wardrobe harta ɓangaren boxers dabam ne sosai tsarin wardrobe din ya burgeta kallon sa tayi tace '' yaya ma su nauyi zan dauko maka ko mara sa nauyi..?, marasa nauyi domin yanzu zafi nake ji.. najlah tace '' na kunna maka A.c..?, riƙe hannun'ta yayi yace '' a'a jeki dai ki dauko min kayana.., to tace ta koma dauko mai wasu riga da wando tayi mara nauyi rigar ma bata da hannu ta miƙo mai, kallon ta yayi yace '' ina boxer...?, da sauri ta kalle sa tab wallahi ba zata iya daukowa ba ja da baya tayi tace '' baga wannan ba ka saka mana.., kallon milk trouser din da ta dauko mai yayi yace '' to idan ma saka wannan ban saka boxer ba mene amfanin sa..baki ga kafar saba me girma ce kuma bashi da tsayi idan nayi wawan zama fa..?, rufe fuskar'ta tayi da tafukan hannayen ta , tace '' kai yaya da girman ka to ni ban gansa ba ko na kirowa aunty JAWAHEER ya dauko maka.., kinga kawai kice baza ki dauko ma nasan da ita nace ki, dauko min yau gaba ki daya ma duk wani aikin ta ke za kiyi har zuwa gobe sai jibi zata amsa aikin ta. turo baki tayi tace ''ni bance maka haka ba shi ne zaka faɗi haka.., NAJLAH na gama magana fa... kauda kai tayi ta dauko mai ta ajiye mai tace '' me zaka ci...?, JAWAD yace ''fried yam da egg sauce.., Juice fa ta fada tana kokarin fita daga dakin.. JAWAD yace '' zo ki zauna a nan karki yi yanzu sai an jima.., zama tayi dan nesa dashi ƙoƙarin cire riga ya fara da sauri ta juya mai baya ya kalle kofa. murmushi yayi tashi yayi ya saka kayan sa sannan ya juyo da ita yace '' na gama.., a hankali ta saka hannun ta , ta ture hannayen sa da yake kan ƙafar'ta tace '' har yanzu baka fadamin ba..., kiyi duk abin da ki kai niya.. tashi tayi tana cewa to dakin ta , ta koma tayi wanka sannan ta zauna tana azkar karfe bakwai dai-dai ta tashi ta shiga kitchen cikin sauri take komai domin bata sani ba ko zai iya karfin halin tafiya aiki. strawberry and banana smoothie tayi mai ta saka a fridge karfe bakwai da minti arba'in ta gama komai daukowa tray tayi ta jera mai sannan ta fito cin karo tayi da Jawaher tana taku daddai koda ta ganta bata karasa saukowa daga stair case ba sai ta tsaya tana jifan ta da wani irin mugun kallo. dauke kai tayi ta wuce dakin Jawad da sauri ta biyo ta har tuntube take yi wato shi ya saka Jawad yace ya gaji da cin abincin yan aiki duk dalilin zuwan wannan bakar dagar aikuwa yau zata yi maganin su najlah ajiye tray tayi yace '' nagode Allah yayi miki albarka.., amin tace tamkar an wurgo jawaher haka ta shigo tana haki tace '' Jawad ban gane me kake nufi da haka ba , mun fara sharing din kane kai da najlah wato shi ya saka kace baka son abincin yan su rose ko...?, da sauri najlah ta kalle ta ta juyo ta kalle Jawad wanda ya nuna bema son me take fadi ba cikin ɗaga murya tace '' to ke kuma yar kanzagi shishshigi ba farin jini ba zaki burge ni ba sai yau kin aure Jawad..haka dai zaki kare.., da sauri ta ƙara kallon Jawad yana jiran taji me zai ce amma shiru najlah tace '' matsamin na wuce.., Idan naki fa..? ta faɗa cikin fada domin wani irin kishin Jawad ne yake taso mata. najlah ja da baya tayi tace '' ni bazan kulla ki ba ko na yarda muyi fada domin bansan wanne irin kashi ne dake ba haka kurum na kwaso tsiya Sannan ni ba karya bace da ko da yaushe za a jini ina wan wan man your business., wani irin daskarewa tayi ko da wasa bata , taɓa tunanin jin wannan amsar a bakin najlah ba lallai yarinyar nan ta raina ta kallon jawad tayi tace '' kana jin me tace ko..?, Sai a lokacin jawad ya ɗago ya kalle ta yace '' me tace..?, haba wa jawaher ji tayi kamar ta shake shi kuka ta fashe dashi ta fita daukan waya tayi ta lalubo number UMMEE har ta katsai bata dauka ba kara kira tayi sai a lokacin UMMEE ta dauka tana cewa ke lafiya kike min kiran mafarauta da safiyar nan bafa nason rashin hankali da barikanci me ya faru... yadda kuka san jawaher ta dannawa UMMEE ashar amma sai ta danne cikin muryar kuka tace '' wallahi UMMEE tun da yarinyar nan tazo gidan nan muke samun sabani da jawad baya gani na da gashi yadda kika san matar sa komai ita , take mai yau kuma har ce min tayi karya jiya marina yayi akan ta wallahi ummee nagaji aure ba hauka bane tafiya gidan mu zanyi idan yaso ita , ta maye mai gurbina.. Kuttumar ubancan to ga hanya nan tafi akwai wanda ya rike ki, kin manta ranar da na kira ki , kika ji daukan waya da yake a lokacin kina cikin kwanciyar hankali ga UMMEE yar iya daukan dukkan wani tension bara ki faɗa min ko to ke da ita sai naci takazar uban ku ke , wallahi ki kiyaye ni kinfi kowa sanin wace ni kallon ke kawai nake naga iya ina film din bake zai kare a wacce chapter ne ita kuwa shegiya ta samu guri ko bara ta sheka ayar ta lafiya qalau jinin farida zai zo waje batare da ya hargitsa gurin ba farida bakar annoba ce fa na tsane ta , wallahi na tsani duk wani tsatson ta shima so yake ransa ya ɓaci shi ya saka har yanzu be mai da mata da annobar ta gida ba wallahi ku bini a sannu ko ayi yakin duniya na uku a *DAN BUZU* ita kan'ta innar kallon ta kawai nake dan haka wannen ke ta shafa jawad ko yanka naman jikin yake ba abin da zai dame ni duk wanda ya iya allon sa ya wanke ya sha idan kuwa kika nemi raba ni da , ɗana wallahi sai kin bar gidan nan.., UMMEE ɗa ko dan rana ta fada a zuciyar'ta amma afili sai tace '' ummee wallahi ba haka ba ne akwai abin da nake shiryawa ne takarda biyu ce ta rage min ban gama haɗa miki komai ba sai mu tafi plan na gama kiyi hakuri.. yanzu ma zan turo miki wasu kudade.., UMMEE wani sanyi taji tace '' oh to maza turo min su ita kuma zanci uban'ta wallahi...farida kamar mayya ta kasa rabuwa da duk wanda ya shafe ni..tasani sarai bana kaunar ta , bana kaunar duk wani me kaunar ta amma da yake mayya ce taki rabuwa da ɗana.., jawaher tace '' bashi take so ba kudin hannunsa take so..., zanyi maganin ta kuwa sai an jima, ta faɗa tana kashe wayar wani sanyi ne ya ratsa jawaher ta fita tana yar waka. cikin daki kuwa najlah fita za tayi jawad yace '' ina zaki..?, yaya zuwa zanyi nayi breakfast..., zauna muci tare wannan yayi min yawa kina so nayi nauyi da yawa ko..? kizo kina nayi nauyi na tsofa. kallon sa tayi ta gefen ido tana cewa to ka riga da kayi dan kaci wannan ba abin da zai ƙara maka kuma kai kace nayi maka shi. hmmm haka ne amma kinsan kayan kiba ne ko me makon ki ban shawara kar nace to nadai ƙara tsofa kece a ciki ni ba ruwana.. ni kuma ko aunty jawaher. ta faɗa tana nuna kan'ta.. dafa kan'sa yayi yace "' ashe mugunta kika shirya..," zama tayi a ƙasa tace '' uhmm uhmm kai fa kace nayi maka yanzu kuma kazo kana challenging dina to dena ci na hado maka salad kace sai ka rame sannan kayi exercise shikkenan..., hannun'ta ya riƙe yace '' a'a barshi nagode daga magana sai kuka.., ƙoƙarin kwace hannun'ta tayi amma sai ya hanata haka ya riƙe hannun'ta gam bin hannun'ta tayi da kallo tace '' yaya zaka karya min hannu tun dazu kake riƙe min hannu..., ina jin daɗin rikewar ne idan na riƙe sai naji zazzaɓin da nake ji ya ragu ko bakya so na samu lafiya ne. kallon sa tayi tace '' to ka sassauta min rikon nan kuma ka dena shafa min fatar hannu bana jin dad'i wani iri nake ji kamar shocking.., da sauri ya kalle ta yace " da gaske..?, Allah yaya to nima cika ni na ci abincin. cika ta yayi tare suka soma ci ba wanda ya kara cewa kowa komai dakin ya dauki shiru zare hannun ta , tayi tace '' na ƙoshi.., kin koshi kuma guda nawa kika ci..?, ya faɗa yana haɗe ran sa tamkar bashi ne ɗazu yake wannan maganar ba. walllahi na koshi bara naje na wanko hannu na shikkenan ai ba abin da zan maka ko zan koma daki na. okay wanko ki dawo , kin manta dazu me nace miki.. turo baki tayi ta , tashi ta wanko hannun ta, ta dawo sosai take jin bacci kwantar da kan'ta tayi a kan kujera jawad yace '' bacci kike ji..?, kai ta daga mai yace '' okay kwashe kayan nan ki zo ki kwanta a kan gado.., to tace mai ta , tashi domin jikin ta duk yayi la'asar bata san dalili ba dauke kayan tayi ta kai kitchen ta dawo kwanciya tayi akan gadon tana limshe idon'ta wani irin bacci ke fusgarta. lokaci guda bacci ya dauke ta jawad tashi yayi ya wanko hannun sa ya dawo fita yayi daga dakin gaba ki ɗaya ya hau sama takardu ya dauko da laptop yana cije lips din'sa ji yake kamar ciwon na ƙaruwa saukowa yayi ya tarar da su rose yace '' ba abin da za ku girka yau.., gaishe da suka soma yi amsawa yayi yana barin gurin. to suka ce suka bar gurin tare da rofe kofar parlour. ajiyewa yayi ya soma aikin sa yayi lokaci zuwa lokaci yana juyowa ya kalle najlah da take baccin ta cikin kwanciyar hankali. tunowa yayi bata sha maganin ta ba tashi yayi ya tafi daki ya dauko mata tare da dauko mata ruwa wata kwaya ya jefa a cikin ruwan lokaci ɗaya ta narke batare da ta canza kalar ruwan ba. ajiye wa yayi ya soma tashi ta , tashi tayi tana turo baki tace '' idan na tashi zan sha yanzu kaina zai fara ciwo wallahi.., haɗe rai yayi yace "zaki sha ko sai ranki ya ɓaci...," ɓallo mata yayi ya bata amsa tayi ta sha tare da ƙara kwanciya yace '' najlah ki tashi ki zauna ya ɗan faɗa miki sai ki kwanta.., yaya bacci wallahi nake ji. to shikkenan ya fada yana janyo laptop din'sa. wannan kenan. *DEEYA NAILAH EMAN* mafita nake nema ko kalli P test din nan result din da ya bayar ciki ne fa dani.. Hmmmm wallahi kin ban mamaki ke daman akan wannan kika tara mu ni wallahi na zata wata maganar ce kina hana da aure ba baki da shi ba mene abin damuwa.. cewar deeeya. wani kallo tayi mata tace '' bafa na Jawad ba ne.., idan ba nashi bane sai me aure ai ya bashi Na'ilah ta faɗa tana danna wayar ta. EMAN tace '' calm down jawaher wannan fa cikin Ubangiji ne ya baki kuma yayi haka ne domin karki tashi a tutar babu randa Jawad ya mutu tofa idan ba tumulin taka ba , ba ba abin da zaki samu, kuma kinsan yana gab da mutuwa ko da ace be shaki poison din da aka saka mai ba gubar da kike bashi kullum tana fa aiki a jikin sa , sannan kinsan dai komai nisan jifa kasa zai dawo idan asirin ki ya tono ko dan wannan yaron wallahi zai kalle yaron nan ya kasa komai bangaren UMMEE bata da komai domin a lokacin zaki nuna mata ruwa ba sa'an kwando bane ki buda komai ki juya komai ya koma kan'ta ke ce barazana tayi miki, wallahi JAWAHEER wayon ki na banza ne yasin kwata kwata baki da wayo ko kaɗan sannan mu kuma yan bada shawara sai asan yadda za a yi damu bayan komai ya lafa sai ki dawo kan TJ kici uban sa dole yayi wa dan da wahala kinga da wannan cikin baƙaramin alkairi zaki samu ba wallahi.., DEEYA tace '' wallahi EMAN bansan kina fa ƙwaƙwalwa haka ba sai yau idan kuwa dukkan wannan plan din ya tafi dai-dai ni ma kashe nawa auren zan yi tas wallahi na aika shi barzahu naci dukiya ga ta gurina ga ta gurin jawaher wallahi zaman kasar nan nafi karfin sa.., Na'ilah tace '' to wani hanzari ba gudu ba wannan abin duk yayi daidai amma bana goyan bayan kisa haba zunubin ina zaku kai shi muma fa sai mun samu namu kason wallahi...., jawaher tace '' gaskiya ina tausayin Jawad wallahi yana kaunar yara idan na kawo mai dan shege cikin gidan sa ban kyau ta.., dallacan rufewa Mutane baki ashe daman baki da hankali to wallahi idan kikai mana bakin cikin shiga daular nan, yasin sai na fasa kwai kalli motar da nake hawa jiya na samu wani dan rainin hankalin saboda yana kallo na talaka zai neme ni ta baya zai bani miliyan hamsin..miliyan hamsin din taci abu takazar uban ta haka nace masa na duddura masa ashar yanzu haka wani bokan ne zai ce yayi haka zai samu kujerar dan majalisar tarayya da yake nema.., cewar EMAN. Na'ilah tace '' lallai eman to ai yanzu abin da ake kenan biya mun bukata na baki abin duniya kin zama two SIM kenan to su karima jos abin da suke kenan wallahi...kike ganin su suke baki sha'awa nima dan dai bana son na haɗa DAZ da kowa ne amma da wallahi kudi zan samu.., kash amma gaskiya Na'ilah baki da hankali ko kaɗan sarai nasan abin da suke aikatawa kenan wata ran fa sai an dinga sakawa mutum pampas saboda mutum zama yake uncontrol Cewar jawaher. DEEYA tace '' kunga wannan duk matsalar ku ce ga wannan babban issues da muke tattaunawa ki bar cikin nan muga abin da Allah zai yi.., wallahi bazan bari ba sai dai duk abin da za kuyo baku da hankali idan fa na mutu nazo haihuwa nace wa Ubangiji me...? idan yaron ya taso ya girma yasan gaskiya da wanne ido zan kalle sa haba gaskiya kun ban mamaki wallahi wato ku biyan buƙatar ku, kawai kuke dubawa.. tashi DEEYA tayi tace '' kan bala'i lallai JAWAHEER aikuwa idan kin ki ji ba zaki ƙi gani ba wato daman kin zo ki lasa mana zuma a baki ne ko duk kudin Jawad mi tashi a banza a wofi tumunin takaba kaɗai za a baki insha'Allahu wannan cikin namiji ne ni daman kullum addu'a nake Ubangiji ya azurta ki da samun ciki irin wannan gida ne ake sakar jiki a haihu domin gobe.. NAILAH tace '' DEEYA waya san gawar fari ban da Ubangiji...?, kinga bana son tsohon wa'azin ki, ki zauna kiyi wa kanki idan kika dawo dai-dai sannan sai kizo ki yi min gwara ni ina zaman gidan miji ke zaman gidan mahaifinki ma ,ya gagare ki zama dan haka baki isa ba ko faɗa min dabarun zaman duniya magana ake ta kudade ma kuɗai mazaje.. sosai ran Na'ilah ya ɓaci wato daman zaman gidan mahaifi daraja ne dashi koda kuwa ke karuwa ce kina cikin sutturar ki ta kalli eman mana ta fadawa haka , ita da iyayen ta karatu suka turo ta basu san me take aikatawa ba idan zata koma gida ko mota bata zuwa da ita waya kuwa tun wayar da mahaifinta ya siya mata alokacin da za'a kawo ta makaranta, bata siyar da ita ba cire kayi kan ta , take ta ɗora ta komar musu da ita su gani..tace... '' amma deeya kin ban mamaki har idon ki ya rufe ki faɗa min haka...?, EMAN tace '' Please be kamata dan mun samu banbancin ra'ayi ba kuzo kuna fadawa junan ku magana kamar ba classis ladies ba kalle mu, mu hudu abin sha'awa ko wa zancen mu yake bamu taɓa samun sabani ba muna zaune tsakani da junan mu tsakani da Allah...., zama suka yi dukkan nu daman jawaher ita a zaune take ta zuba ta gumi, tana cikin tsaka me wuya bata san ya za tayi ba gashi suna barazanar tona mata asiri tayi sake da suka san sirrin ta amma bakomai idab sun san wata basu san wata ba dukkan nin su tana da video su tace '' *DEEYA NAILAH EMAN* lallai idan kuka ce zaku tona min asiri to fa zamu tonawa juna asiri kun saka rigar karya, kun fake da business kun mai da da dalin tiktok wajen sheka ayar ku, wajen kawalci mayan mutane su ganku suyi muku DM ko kuma su bawa wani yayi muku magana ya haɗa ku da su dan haka yadda ake ganin ku da mutunci wallahi sai na tona muku asiri....za ayi yar tone tone a tiktok ko wacce update dinta zai baza duniya kowa ya gani ni za kuyi wa barazana..., da sauri ko wacce ta kalli yar uwar ta deeya ta cire dankwali taja ɗamara tace ''miko wayar ki ko muci kuttumar uban ki.., wallahi deeya saɓa mata kamannin za muyi ke kin manta mu su waye duk tashancin ki mun fiki.. cewar Na'ilah. Eman tace '' wallahi da asirin mu ya tonu gwara mu aika ki rahira karshen mu gidan yari baza dai ace dukkan mu za a kashe mu ba balle ma muna da manya a hannun mu maza dauko wayar nan da hannun ki ma zaki goge shi.., wanne ta goge tayi restor din wayar gaba ki ɗaya fakat ba kare bin damu.. cewar DEEYA. Na'ilah tace '' ya kika tsaya kina kallon mu ko sai kin ga mun dauko muciya da taɓarya mu sauke miki gaɓoɓin jikin ki yar akuya..., KARUWAN CIKIN GIDA Ga channel dina kuyi min subscribe Dan Allah wai ina masoya na suke. https://www.youtube.com/@nasreenminallah https://vm.tiktok.com/ZSBRtRQmN/ Domin samun update kuyi following dina Book ¹ EPISODE ²⁴ Na'ilah uwa tace akuya.. JAWAHEER ta faɗa tana nuna kan'ta. DEEYA tace '' to ai tayi miki da sauki daba tace yar tinkiya ba maza fito da video nan.., jawaher tashi tsaye tayi kallon abin take yawa almara tace '' ni zaku daka wallahi kunsan ko giwa ta rame tafi karfin rami.., kunga ku dakata kar wacce ta , taba da hannu mu nemi icce domin tace wa xeey wani yana da kanjamau idan ba tare suke shan magani ba, ya akai ta sani...?, cewar EMAN. da sauri jawaher ta kalle ta , tace '' eman ni kike faɗawa haka..?, kinga jawaher ke kika takalo wannan faɗan da kinsan ba zaki iya ba kika fara dan haka maza ki fito da wayar ki ko yanzu wallahi mu aika ki lahira dukkan mu kinsan tsofaffun crimenal ne ba wacce bata da record a police tasion.. cewar DEEYA. kan jawaher ne ya soma wa juyawa idan wani ya faɗa mata haka zata faru zata ƙaryata dafe kan'ta tayi da sauri deeya ta shiga kitchen kafin ta tantance ta buga mata muciya a gadon baya ta dura wani uban ashar tace '' tun kafin nayi miki irin wannan guda dari shidda har sai naga kin dena motsi ki fito da wayar ki.., da sauri jawaher ta ɗurƙusawa domin ba karamin jin dukan nan tayi ba. jawaher shawara nake baki karki kiyi taurin kai ki fito da wata sahunki a likkafa ki bayar ayi mata restor. Cewar EMAN. kinga eman ke kika tsaya lallaɓata wallahi mu da ita shege ka fasa duk wanda ya safa kuttumar uban sa ba dan halak bane gwara muyi rugu rugu da naman ta idan ya so muce hatsari ne mu kwashe ta mu kaita asibiti.. cewar DEEYA. Na'ilah tace '' tsaya tsaya DEEYA mubi komai a sannu karfa garun wannan dukan cikin da muka kwallafawa rai ya zube ayi biyu babu., EMAN tace '' au ke magana ma kike ayi biyu ba bu ai daman niyar zubar da dan banza take gwara mu ,mu muzubar mata dashi magana ake fa ta tonan asiri yar rigar mutuncin da muke da ita a gurin masu mutunci ta yaye kowa ya koma mana kallon sheɗanu dan haka yau ko mu ko ke dan takazar ubanki..,, kunga samo min abu mu rufe mata baki karta tara mana jama'a..? daure ta sukai tamau suka dinga jibgar ta , tamkar Allah ya aiko su. kamar ace kalli can suka hango inda ta wurga wayar eman daukan ta , tayi tai mata kwatsatsa sannan ta dauraye ta , tas a cikin ruwa yadda ko wajen uban waye aka kai ta baza ta moru ba ɗagowa tayi tana haki tace '' ku dakata kamar jini ya balle mata.., kallon ƙasa suka yi da sauri deeya tace '' maza dauko mota kwara mu kaita asibiti cikin ya zube a can idan ya so ma kira shi.., da wannan shawarar suka kunce ta , tas Na'ilah ta gyara parlour tamkar ba'a yi komai ba jawaher ko iya ɗaga hannu bata yi suka zurata a bayan mota eman da deeya da Na'ilah suka shiga gaban mota suka gwamutsa. basu tsaya a ko ina ba sai a asibiti suka fito fuskar su, cike da alhini deeya da eman har da kuka Na'ilah ke rarrashin su tana basu baki. aguje likitoci sukai kan'ta da yake asibitin nan take da folder cikin sauri suka shiga emergency room da ita deeya zama suka yi tamkar basu zaman makoki suka zuba ta gumi eman tace '' ke ya za ayi da motar ta..?, ta faɗa ƙasa ƙasa. deeya kifta mata ido tayi tana nuna kan'ta subarta da komai kar su yi magana fahimtar hakan da suka yi suka ja bakin su, suka tsuke. Na'ilah tace '' ya kamata fa a sanar da mijin ta.., what baki da hankali haka kurum za a ɗaga mai hankali sai gobe zai sani wallahi. cewar eman. DEEYA tace "' gaskiya Na'ilah shaye shayen da kike ya fara taɓa miki ƙwaƙwalwa yanzu sai mu sanar dashi yazo kulle ya farke gwara mu ƙara kafa mata worning da kyau ko da wasa tace tak to wallahi can zata , tafi...,, Na'ilah jan bakin ta tayi ta tsuke jikin ta yayi sanyi. idan sunga wani zai huce sai su kara dada sautin kukan su tamkar basu, suka aikata haka ba.. wata doctor ce ta , fito sanye da labcort hannun ta da wasu takardu tace '' Please kuyi hakuri ku dena kuka abin ya zowa mrs Jawad da sauki duk da cikin jikin ta ta zube sakamakon bugawar da yayi insha'Allahu yanzu zamu ɗorata ta samu karaya uku a cinya ɗaya a hannu wuyan tama ya karya gaskiya wallahi Allah ne yayu da rayuwar ta domin ba'a fiye samun mutum yayi irin wannan hatsarin ba ya tashi..., share hawaye eman tayi deeeya kuwa wani bakin ciki ne ya durar mata da taji cikin da suka kwallafawa rai ya zube, zubewa tayi a ƙasa tana kuka har da buga kan'ta tana ganin duk wani mafarkin rayuwar ta ya rushe kai Allah ya tsinewa JAWAHEER duk taurin kan'ta ne ya jamusu. mamaki ne ya kama su eman to wannan kukan fa ko duk a cikin shiri yake to suma bara su bita karta, tashi ta tsine musu tas fara rokota suka yi suna kuka doctor wasu nurse ta kirawo guda uku suka dinga rarrashin su dawowa doctor tayi ta shiga dakin fito da Jawaher akai duk ta fita hayyacin ta suka shiga da ita dakin theater. ★★★★ BINYERI. kai wallahi yau ko ubanka be isa ya hanani zuwa gidan ya'ta ba. inna ta fadi haka tana haɗa kayan tsubbun da takarbu a gun malamin ta. da niyar idan takaiwa jawa ta cake mata kudin ta a lokacin. ɗaga wani abu tayi tana cewa wannan shi ne na yar iskar yarinyar da malam yace min tana cikin gidan yar uwar ka idan ba akawar da ita ba to zata zame mata babbar matsala kawai sai nace a haɗa ta cutar hauka mutukar wannan abin ta shake shi shikkenan an gama kai sai nayi wata tara sannan zan dawo. ta karashe fadar haka tana mai da kwalbar cikin jakar ta. jujal yace '' insha'Allahu ba zaki gano gidan ba bata ce karki zo ba , zata zo salon kije ki kashe mata aure..,ni gani nan a zaune ko mashin shini babu.., da sauri inna ta juyo domin jin abin da yace tace '' juburu ni zan kashewa jawa aure..?, to ke iya bala'in ki wa ya bari..? yanzu ga yar ɗagwas nan sai da kika ga ta fito hankalin'ki ya kwanta.., jan kujera yar tsuguno tayi ta zauna tace '' jaburu na lura duk karatun da nake maka tabayan kunne yake shiga yake fita humaira da kake gani mijin ta talaka ne malamin makaranta me na ƙasa yaci balle ya bawa na sama...? shi ya saka na doka sammako na siya biro da nemi alfarma aka bani takarda naje na miƙa mai ya sakar min ya'ta jawa kuma idan Allah ya azurtata da haihuwa a cikin gidan nan hmmmm jaburu wallahi makka sai dai kayi kyautar ka dan haka saki zuciyar ka , ba kashe mata aure zan yi ba wannan ma kayan gyaran aure ne naje gurin malam me gobe da nisa me aiki kamar yankan huƙa nakai mai naira na gugar naira yayi min wannan hadin na manta da uwa da dangi.. idan bake ba sai rijiya akan ki saina kashe uban kowa ke nake gani.., kut billahilazi wannan wakar soyayya ya biya miki jaburu ya faɗa yana rufe bakin sa saboda ganin yadda inna ta dage tana karanto kalaman soyayya kamar irin yar yau din nan. INNA tace '' kai da hallacan abin da yake nufi da ya fadan haka ba wanda ya isa ya faɗa mai yaji.., hmmm wallahi karya yake fada miki. a'uzubillahi minar sheɗanir rajim, bakin ka ya sari ɗanyan kashi dan uwar ka fice min a gidan nan wallahi bansan kai ba mutumin kirki bane ba sai yau. cewar inna. tashi yayi yana wallahi karya ne wallahi. haka kurum ya ci miki kudi a banza dama ni kika bani nayi miki kuluboto tunda shi suke muku da surkulle abu ta dauka zata bugo mai da sauri ya fita a gije yana dariya. karasa hada kayanta, tayi tas tana ƙoƙarin fito dasu tsakar gida humaira ya shigo da malam malam yace '' ina zaki..?, mayafinta ta rufa tace '' gidan jawa..., da sauri ya kalli kayan da yake gaban ta yana mamaki yace '' baki faɗan ba , kuma gidan surukinki za kije da wannan uwar jakar da wanne ido zaki kalle sa to ban amince ba.., malam wallahi tafiya ba fashi dai nayi. Allah ya shirye ki bazan baki ko sisi ba kudin mota Allah ya kiyaye hanya. dariya inna tayi tace '' wannan maganar amin in da gaske kake amma malam tun lafin na haifi jawa ka dena bani kudin unguwa cefa ne ma sai da wallahi tallahi dan haka kaga baka isa ka faɗa min naji ba.., Malam yace '' gani nayi yawon ki bana kare bane shi ya saka nace bada kudina ba wallahi cefane kuma ina yi muku iya daidai karfina sai dai rashin godiyar Allah irin naki, wallahi a kullum dana sanin auren ki nake.., ahayye ras cas kas to mana ka sake ni sai a raba gadon ya'yana a bani idan kana da guri ka yanki naka idan kuma baka dashi ka ƙara gaba wallahi jibe ni cas dani kana sakina, wallahi saurayi zan aura me jini a jika na mori kuruciya mu yini mu kwana muna sunna. kasa cewa komai yayi ya shiga daki domin halin inna yana saka shi a cikin tunani gaban yar ta , take fadar haka shi ya saka ga ya'yan su ne gaba ki ɗaya babu na Allah be sani ba ko yanzu aure ya gyara jawa, daman ance wanda be ji bari ba , ba yaki gani ba iyayensa basa so haka ya aure ta da zummar zai musuluntar da ita zai yi shahada irin su ake son aura gashi nan abu yana bin ya'yan sa a haka ma tun da ran iyayen sa ta nemi afuwa. kuma sun yafe mai shi ya saka a kullum jan hankalin sa ga matasa su dinga yiwa iyayensu biyayya ba abin da iyaye zasu kawowa ɗan su wanda zai cutar dasu sunfi kowa sanin me ya dace da ya'yan su. Ya Allah ka bamu ikon yiwa iyayen mu biyayya wa yanda suka rigamu gidan gaskiya Ubangiji ya saka aljanna ce makomar su. mu da namu suke raye Allah ya azurta su da lafiya yayi musu nisan kwana me albarka ya bamu ikon yi musu biyayya idan tamu tazo Allah ya saka mu cika da imani. amin summa amin 🤲🏻🤲🏻 yana zaune yana wannan tunanin yaji tayiwa humaira sallama ta fita. *★*★*★ ABUJA OSOKORO. ASIBITI. 3:00 aka fito da Jawaher daga dakin theater agwanin ban tausayi duk an like mata jiki da bandeji wuyanta ma wani abu suka saka mata ya tsaya chak kikam. shiga da ita daki aka yi..su deeya suka shiga dakin suna ci gaba da kuka Samuel yace '' idan baku dena kuka ba zaku fita a yanzu bata san karar komai.., tsit suka yi suka nemi guri suka zauna. fita yayi yana cewa ya kamata mijin ta ya zo domin muna bukatar sa da gaggawa... kallon kallo a ka shiga ba wanda ya , iya ce mai komai har ya fita. Na'ilah tace '' deeya taso mu tafi gurin aikin sa domin ina tunanin ba me number sa a cikin mu.., a'a ina wayar ta cire layin ta a kirawo shi..cewar deeya. Eman tace '' ina da number sa bara na kirawo shi.., Allah ya saka ya dauka kinsan halin mayan mutanen nan basa ɗaga bakuwar number idan har basu da saving number din mutum. dan jim tayi sannan tace '' ina da saving number sa yana da tawa.., to kira shi maganin karya hallarah cewar deeeya. eman ciro wayar ta. tayi ta soma kiran sa amma switch up wayar jikin ta sanye ye ta kalli su Na'ilah tace '' waya fa switch up take yanzu ya za a yi.., ke kyale shegiya barsa yayi aikun sa cikin kwanciyar hankali idan wannan arnan ta ƙara zuwa muce yayi tafiya be dade da hawa jirgi ba yadai san ba'a ɗaga waya idan ana cikin jirgi. Cewar deeeya. good haka ya kamata muyi. cewar EMAN. da wannan shawara suka ƙara sakar jiki suka bararraje abincin da aka kawo da kayan motsa baki da aka saka a cikin fridge sai da suka cinye kusan rabi suka nemi guri suka kwanta ko wacce ta hau charting ko sallah basu kula suyi ba. ★★★★. kaga nan gidan dana ne wallahi yata ke aure a cikin gidan nan ka buɗe min ba shiga yau nake jin wata sabuwar jaraba ka tsaya kana kallo na kana saita ni da bindiga wannan wacce irin unguwa ce kafin na shigo na sai da aka gama chaje min kaya tsaf sai kace sun ga wata yar fashin daji.... sojan da yake tsaye da bindiga yace "Did you inform them before coming? If you didn't inform them, you will never be able to give it to him, bawan Allah wallahi ko primary ban shiga ba , balle na gane wannan yaren turawan ba.. cewar inna. Joseph kara maimaita mata abin da yace yayi domin shi baya jin hausa daga Enugu aka kawo shinan aiki ko wata biyu beba... INNA share hawaye tayi domin taba san da wanne yare za tayi amfani ba ya jita zama tayi a kofar gidan wani irin tsawa ya daka mata hadi da ihu sai data fita a guje tabar jakar kayan ta ball yayi da ita yana nuna ta da dan yatsa yace '' nace miki nan gurin ba a shiga batare da izinin masu gidan ba irin kune masu bin gidajen jama'a kuna bara zaki bar nan ko sai na fasa miki kai..da alburishin bindiga., INNA zare ido ta fara kamar tsohuwar mayya. shawaye ta share, tana lalubo number jawa shiru ba amsa sai wani yare da take ce mata. cikin gida kuwa. Jawad dakyar ya iya karasa aikin da yake da yake tun da najlah ta kwanta bacci be kara kallon inda take ba sallama dakyar ya tashe ta , tayi ta ƙara komawa ta kwanta. sai ya ci gaba da aikin sa yanzu kuwa ganin abin yaci tura dole ya nemawa kansa mafita. tausayinta yake shi ya saka ya kasa yi mata komai har i yau. cire mata hijabin ta yayi, ya ajiye gefe daga doguwar rigar'ta sama yayi ya a hankali ya zame mata pat din ta. habawa kusan gigice wa yayi tun kafin ya kai da yin wani abin. wani irin kamshi me ya bugi hancin sa har sai da ya limshe idon sa. wara ƙafar'ta yayi a hankali ya zura karamin dan yatsan sa na ƙarshe gaban ta da dan karfin sa chak ya tsaya sakamako kasa shiga da yayi duk irin baccin da yake kan'ta be hana ta jin wani mala'ikan zafi ba a haka ko rabi be shiga ba. wani kuka ta saki mara sauti da yawa da alama har yanzu bacci na kan'ta. tausayinta yaji ya zare daman yasan haka zata faru besan tayaya zai shiga gurin nan karamin dan yatsa taji zafi ina ga Hajiya babba. rungume ta yayi yana sakin ajiyar zuciya share mata hawayen ta ,yayi ya mai da mata da pant ɗin ta , virginal ce dole ta samu jin wannan zafin ko ina aka taɓa a jikin ta dole taji zafi. adai haka ya rage damuwar sa sannan bacci ya kwashe shi ana ƙoƙarin kiran sallah ya tashi wanka yayi ya fito ya soma tashin ta , tashi tayi tana mustsuka idanuwan'ta shar shar hawaye ya soma bib kuncinta sai haɗiyar zuciya take. zama yayi yana cewa najlah lafiya ne ya faru.. kuka ta saka baza ta iya ce mai ga , abin da ya faru da ita ba still har yanzu gaban ta zafi yake mata ga kirjin'ta saukowa tayi ta shiga toilet bata ce mai komai ba ganin haka fira yayi yana addu'ar Allah ya bashi ikon jurewa amma tabbas a bukace yake besan iya yaushe zai dauka suna wannan dreamer ba. cire kayan ta , tayi tai wanka tsarki domin duk da abin da ake mata bawai dad'i take ji ba pant ɗin ta jike wa yake daura towel tayi ta fito bata tarar da shi ba daman tayi tsammanin haka shiga bedroom dinta tayi ta canza kaya dauko turaren da aunty hafsa ta bata , tayi ta juna banner ta zuba shi, ta tsuguna tana leken gurin da yayi ja. taba fatan batai losing virginal din'ta ba. gamawa tayi ta share hawayen ta , ta tada sallah. bayan ta idar takai wa Allah kukan ta Allah yayi mata katangar karfe da wannan aljanni da duk bayan kuna biyu yake zuwar mata tamkar me lissafa kwanaki yau abu yayi gaba har gaban ta ya ke taɓa wa.... Jawad kuwa bayan an idar da sallah ya tsaya yayi azkar sannan ya dawo tun daga nesa INNA ke ɗaga masa hannu karasowa yayi ta fashe da kuka ko amsa gaisuwar sa ba tayi ba tace '' yau naga banu a garin nan wani har wurgi yayi min da kaya..., hakuri ya soma bata sanan ra share hawaye ta suka gaisa. knocking yayi Joseph ya buɗe kofar harara ta zabga mai zai amshi kayan ta , ta buge hannun sa tace '' wanne irin hulakanci ne bakai min ba sai da kaganni da uban gidan ka sannan zaka nuna Ni me daraja ce.., Jawad bece komai ba , amsar jakarta yayi har suka shigo parlour zama tayi tana cewa kawo jakar nan Allah yayi maka albarka. amin yace yana kwalawa najlah kira fitowa tayi abaya ce a jikin ta dark blue tayi mata kyau mayafin abayar ta daura shi duk da fuskar ta ba walwala amma ba ƙaramin kyau tayi ba. ganin tsohuwa da sauri ta ɗurkusa tace '' sannu da zuwa.., sakar baki da hanci Inna tayi dole malam yace zaman wannan balarabiyar akwai matsala mace har mace duwawuka sai juyawa wa suke kamar da gayya take juya su kai gaskiya jawa ta cika mahaukaciya da har bata, bata labarin yarinyar nan ba... sai boka ne ya bata labarin ta. jikin najlah ne yayi sanyi ganin irin kallon da take binta dashi ta tashi tsaye INNA ta saki wata dariya ta rashin gaskiya tace '' ikon Allah ɗana amma dai wannan kanwar kace kamar ta ɓaci.., zama yayi yana cewa eh wallahi kin zo Lafiya...? Lafiya qalau alhamdulilah na same ku lafiya. Alhmdllh lafiya qalau gashi jawaher bata nan ta , tafi makaranta. INNA tace '' to Allah ya dawo da ita lafiya.., Jawad yace amin ya Allah . Najlah kayan motsa baki ta haɗu mata , ta kawo mata gaban center table da sauri inna ta cire hijabi tana cewa yar nan sannu ya sunan ki...?, najlah tace '' najlah ., Masha Allah sannu da aiki naja'atou ni wallahi nafi gane sunan gargajiya wannan lankwashe lankwashen ban iya shi ba. dan murmushi najlah tayi tace '' a'a ba naja bane najlah ne ko wanne dabam ne.., riƙe hannun'ta tayi fatar iya da take kaushi kaushi ji tayi ta muzanta, domin har wani lubu lubu ga uban taushi taji fatar najlah nayi tace '' yar nan yi min afuwa zan faɗa miki naja wallahi ko za'a saka min huka a makoshi bazan iya faɗar wannan suna ba me uban wahala...., najlah tace '' to..,. ta faɗa tana barin gurin shiga daki tayi ta zauna ta zuba ta gumi abubuwa da yawa nayi nata yawa akai wayar tace tayi ringing da sauri ta dauka Hajiya ce kuka ta she dashi dakyar tayi shiru Hajiya tace '' auta bana son wannan damuwar dake kike fa me yayi zafi kamar ba a gidan dan uwanki, kike ba..me Jawad yake miki wallahi nasan Jawad ba zai taɓa yi miki abin da zai cutar dake ba....., share hawaye tayi tace '' hajiya ba shi bane...., hajiya tace '' to waye ....?, hawaye ta share tace '' wata ran sai ba kwanta bacci naji ana taɓa jiki na wallahi bakarya nake ba.., to ni bana son irin wannan zancen addu'a zaki dinga yi kinji ko da wasa kar wanda kika kara faɗawa a haka a zuciya ake barin komai, ni da mahaifinki da yan uwanki muna yi miki addu'a ba abin da zai iya cutar da ke.. to yau fa har da sauri Hajiya tace '' innalillahi najlah yanzu me nagama faɗa miki...?, tayi saurin katsai ta. to ba da duk abin da yake damuna ba ina faɗa miki kuma kina ban shawara bana boye miki komai shi ne yanzu zaki ce bakya son ji kema kenan tsoran aljanun kike kar su kama ki. najlah ta fada tana turo baki cikin shagwaɓa. Hajiya tace '' a'a ni ba tsoran su nake ba kawai dai ki koyi rike sirrin ki najlah wata ran aure za kiyi sai duk abin da ya faru a gidan ki na dade da ba na dadi ba sai ki faɗa min..., to ai yanzu ban yi ba. to Allah dai ya kyauta ya Jawad yake...? hmmm yau bashi da lafiya wuni yayi a kwance nace zan kirawo mai likita yace nabari ba abin da zai iya yi mai aunty kuma tun safe ta fita.. HAJIYA tace '' najlah bana son rashin hankali ki kula dashi sosai ki tambaye shi me yake so domin nasan halin ki ba lallai ki kula da shi ba.. wallahi Hajiya duk nayi mai na bashi wayar ki tambaye shi. da sauri tace '' Allah me iko a'a Allah ya shirye ki gabanta yawa yar fari ni wallahi najlah idan ace a yar fari kika zo ban san me za kiyi ba.., Hajiya yaya tsoho yana da gabon ta ne shima ai ɗan fari ne.. ta faɗa tana danne dariyar ta.. cikin rashin fahimta Hajiya tace '' wane kuma yaya tsoho najlah..?, yaya fa ta faɗa tana dariya.. Hajiya tace '' hmmm Allah ya kyauta duk randa ya jiki ba zaku kare ta dadi ba ki ci gaba ban hana ki ba wallahi. kai Hajiya to shikkenan sai an jima. sallama suka yi da sauri tace '' yaya ya bani sarkar gold kiyi mai godiya ki fadawa abbana.., Hajiya tace '' to zan mai Godiya ina taya ki murna. to ngd sosai ta faɗa tana kashe wayar. parlour kuwa. INNA kwashe cinyoyi tayi tana cin kazar da najlah ta kawo mata sai ta kora da lemo me sanyi ba irin abin da bata wassafa ba a zuciyar ta domin taga guri ba dole fata ta koma katifa ba mutum yana cin wannan abubuwan dadin. Jawad fitowa yayi ko a jikin INNA hatta dan kwali ta cire wata kananan kalbace wacce akai mata da zaren riƙe gashi domin kanta kamar hammatar ɗan iska yake ko kunya bata ji ba daukan dan kwalinta tayi ta daura tana Barka da saukowa Alhaji. kunya ce ta kama Jawad yace '' inna sannu da hutawa.., wayar sace tayi ringing be jira me zata ce ba ya kauce daga gurin domin yaga kiran daga asibiti ne Allah ya saka lafiya gaisawa suka yi sannan aka sanar mai abin da ya sami Jawaher. wani irin rawa zuciyar sa tayi amma Bama su sanar mai zubewar cikin ta ba. godiya yayi masa yace gashi nan zuwa sannan ya kashe wayar. dawowa yayi yace '' INNA gama cin abinci ki shirya nakai ki inda jawaher take.., bata kawo komai aranta ba tace '' to.., ci ta gama yi tas sannan ta goge hannun ta jakar kayanta ta dauko Jawad yace ta kawo ya shiga da ita daki. batai musu ba ta bayar da jaka bayan ya kai daki ya sauko fita suka yi najlah tace a dawo lafiya.. kallon yayi yace '' yauwa najlah sako hijabin ki mu tafi.., da sauri tace '' ga mayafina nan bara nayi rolling.., wani irin kallo yayi mata tuni ta koma ta dauko hijabinta tana kunkuni INNA tace '' naja gata yayi miki naga duk ranki ya ɓaci gwara ana kare mutunci wallahi mazan yanzu yadda kika san masu gindin ayu haka suke barin ma irin ku masu komai masha Allah, kunya ce ta kama najlah tayi shiru Jawad kuma nunawa yayi be ma san me yake faruwa ba ma.. buɗe mota yayi da sauri Inna ta shiga gaba najlah dan murmushi tayi domin abin ya bata dariya ta shiga baya. ko direba me tsaya jira ba yayi wa motar key a hankali ya soma tafiya horn yayi me gadi ya buɗe mai gate. sosai najlah take mamaki to me ya sami Jawaher gaban tane ya fadi lokacin da taga sun shiga asibiti parking yayi INNA ta sauko tana wage wage budewa najlah murfin mota yayi sosai najlah tayi mamaki yaya ne ya buɗe mata murfin mota Allah me iko haka ta raya a zuciyar'ta fitowa tayi ta sakar mai murmushi shima martani ya mayar mata hana rike hannunta jerawa suka yi suna tafiya abin sha'awa Inna na bin bayan su tana kalle kalle wani Bature ne ya wuce da sauri tace '' lah bature ikon Allah har masu jajayen fata zuwa asibitin nan suke.., bata da me bata amsa duk abin da taci karo dashi sai tayi Magana har suka isa word din da Jawaher take. dakin da likitan ya faɗa masa ya shiga INNA ihu ta saka tace na shiga uku jawa kece a haka da sauri su deeya suka tashi suna gaishe da ita amsawa tayi tana shafa kafar jawaher da aka sakale.. deeya tace '' INNA sai hakuri muma munyi kuka kamar ba gobe tare za mu tsallaka titi sai tace bara ta fara yi gaba shi ne me mota ya buge ta wallahi ko tsayawa beba ya gudu ashe ma tana da ciki cikin tas ya zube.. zaro ido INNA tayi ta shiga uku mafarkin da kullum take yi gashi wani tsinanne ya zubar da shi... INNA tace '' wallahi ba zan yarda ba tunda har ya zubar min da jika na yasin bazan yarda ba kai idan Alhaji zaka yarda ni ba zan yarda ba shekara nawa Allah be baku haihuwar nan ba sai yanzu sai wannan shegen ya zubar da cikin nan.., kuka take sosai su deeeya ma kama kuka suka yi sai kace mutuwa aka yi. najlah mamaki ne ya ishe ta daga anyi bari sai kuka Allah da ya bata zai ƙara bata..wani Jawad juyawa yayi bece komai ba ya tafi gurin likita. Na'ilah tace '' kanwata zo nan ki zauna kya zatsa ya a tsaye..., shigowa tayi tana gaishe su hadi da tambayar ya me jiki amsa mata suka yi suna sharar hawaye.. zama tayi a lokacin jawaher ta buɗe idon ta a hankali haɗa ido tayi da INNA Inna da take kallon ta tace '' sannu jawa Allah ya tsinewa wanda ya buge ki har ya yanyo mana wannan asarar..., KARUWAN CIKIN GIDA Ga channel dina kuyi min subscribe Dan Allah wai ina masoya na suke. https://www.youtube.com/@nasreenminallah https://vm.tiktok.com/ZSBRtRQmN/ Domin samun update kuyi following dina Book ¹ EPISODE ²5 Da ido kawai *JAWAHEER* ke binta ba bakin magana domin ko iya buɗa bakin ta ba za tayi ba. zama *INNA* tayi tana share hawayen ta ba ƙaramin bakin ciki taji da wannan abu ba. *NAJLAH* zaman gurin gundurarta yayi sai kallo suke binta dashi tamkar ba mutum irin su ba suke gani, *JAWAD* ne ya shigo tare da likita kara dubata yayi sannan yace '' Sakamakon kan'ta da ya bugu bata son hayaniya hakan zai ƙara nata ciwon kan da take fama da shi ɗan Allah kar dukkan ku, kuce zaku kwana mutun ɗaya ma ya isa shima ɗan ya zama dole ne , amma muna ma da ne kula da patient a asibitin nan.. Karab INNA tace '' ni zan zauna da ita ,su sai ko wacce ta koma gida lada ya isa godiya nake da kuka tsaya kuka kula da ita.., taɓe baki deeya tayi tana tashi tace '' ku taso mu daman yanzu muke shirin tafiya Allah ya kara sauki.., wani kallo *INNA* tayi mata tana cewa amin idan gaske kike yo tilashin wuya makoko kun ga abin alkairi shi ne ko wacce ta nade ƙafafuwan ta , tamkar wasu majiyata kuka ɗane kan gado kun gama ci kun koshi Ni wallahi da na shigo na zata suma marasa lafiya ne kukan da suke yi da bayanin da suke yi shi ya wayar min dakai yan bantan uba anzo cin banza banza bata samu ba..maza Umma ta gaida ashsha gayyar na ayyah.... *JAWAD* wata iriyar kunya ce ta kama shi me *INNA* take faɗi haka mutanen da suka tsaya akan yar'ta kamata yayi suyi daraja a idon ta.. zura hannu yayi a aljihu ya kirgi kudi yace '' Nagode sosai Allah ya bar zuminci ungo kwasha mai.., Wuf *INNA* ta karfi kudin tana cewa a'a wannan yayi yawa ba'a abu dan Allah sai ka biya su gaskiya ɗana hakan be kamata ba ko wacce zan bata dubu ɗaya ya isa ta hau mota har ta , samu canji sauran kudin zan ajiye ba fata ake ba ba'a san inda wannan ciwo na jawa zai tsaya ba duk kabi ka ƙarar da kudin ka yake nan wa'yannan masu zubin jar hudu fuska kamar an gasa ɗayan nama sama sama ko kobo ba za su baka ba. dan haka ke ungo. banza sukai mata dan dai da *JAWAD* ne amma wallahi da taji bakar magana matar nan ashe haka take da rashin mutunci gaskiya *Jawaher* gado tayi cewar *DEEYA* a zuciyar ta. gaba ki ɗayan su basu amsa ba suka fita sai ruwan Allah ya isa da sukai mata Jawad cije lips din'sa yayi ya ja kujera ya zauna kusa da najlah. da sauri *INNA* tace sannu dannan da alkunya zo ga wajen matar ka kaga na gaje maka guri. da zauri najlah ta kalle ta sai kuma ta kalli yaya sosai abin yake bata mamaki wannan wacce irin uwa ce Jawad yace '' a'a barshi nafi jin daɗin zama a nan.., to , to am dan nan dan Allah ina so a kawo min jakar kayana kaga ni zan dinga kula da ita har Allah ya bata sauki. Jawad yace "to insha'Allahu zan kawo miki ita...,, yauwa dan nan kiran sallar magariba aka yi. tashi Jawad yayi ya tafi masallaci najlah ta dauro alwala ta shinfida prayer mat ta tada sallah INNA na aikin cin abinci tamkar zai gudu ya barta bayan ta idar Jawad yazo yace '' to inna ni zan koma zuwa gobe zan dawo na kawo miki kayan ki.., to shikkenan ba matsala tashi najlah tayi da sauri tace '' ina kuma zaki ba tare za mu zauna ba ya za a yi ki zauna gida daga ke sai namiji.., da sauri najlah ta kalli INNA tace '' dan uwana ne fa.., dan dan uwanki ne uwa ɗaya uba ɗaya kuke..?, najlah tace '' ni ban iya zaman asibiti ba , bazan kuma fara ba.., tana sane tayi mata haka domin taga matar bata da mutunci ko kaɗan murmushi Jawad yayi bece komai ba ya riƙe mata hannu suka fita yaya wannan matar halinta bashi da kyau ni wallahi bazan ƙara dawowa cikin asibitin nan ba. kallon ta JAWAD yayi yace '' saboda me..?, baka ga abin da take fadi ba , bata iya magana ba kaga abin da tayi wa wa'yannan be dace ba.. buɗe mota yayi bece mata komai ba shiga gidan gaba tayi ya shiga mazaunin driver ya tashi motar tafiya yayi me dan nisa sannan ya iso bakin gate din asibitin horn yayi me gadi ya buɗe mai kofa. hawa kantiti yayi kunna karatun Alkur'ani yayi a hankali yake tashi a cikin motar. sai ka lura sosai zaka ga yana bib karatun da alama yana jin daɗin bin karatun domin wani annuri fuskar'sa ke yi kallon sa najlah tayi. sai kuma ta dauke kan'ta ta mai da kan'ta ta kwantar a kan cinyar ta , har suka isa gida bata kara ce mai komai ba , saukowa tayi ta fito riga shi barin gurin tayi domin ya tsaya hira da ma'aikatan gidan.. cire hijabinta tayi ta kwanta a kan gado tana sauke ajiyar zuciya wayar ta , ta dauko zaro ido tayi ganin har 20 miss call na ya muneef da sauri ta kirawo shi amma har ta katsai ba dauka ba tana katsaiwa ya kirawo ta , dauka tayi tana cewa kai hakuri bana kusa da wayar naje dubiya asibiti. muneef yace '' bakomai wane bashi da lafiya..?, gyara kwanciya tayi, tace '' matar yaya.., okay Allah ya bata lafiya daddy ma bashi da lafiya naje ma duba shi jiya wallahi yana jin jiki.., Allah sarki Allah ya bashi lafiya da yake kuna kusa ko...?, a'a bama kusa tsakani na dashi kamar ace miki kano da Kaduna.. ikon Allah ai naza ta kuna kusa da juna..ashe ba haka bane kana lafiya..? MUNEEF yace '' hmmm lafiya qalau alhamdulilah wallahi najlah ji nake kamar kinyi min nisa nazan taɓa samun ki ba kullum cikin fargaba nake dan kafin na tafi akwai wata magana da naji ƙarshen ta lokacin naje gurin jadda to har yanzu ban samu amsar ba..shi ya saka kin ganni duk na rame wallahi idan na tuna karshen abin da kunnuwana suka ji ina shiga tashin hankali..., haba yaya muneef ba abin da zai faru insha'Allahu. me kaji jadda na fadi..? dan jim yayi tamkar me tunanin ya faɗa ko karya fada sai kuma yace '' manta kawai da maganar.. kina lafiya ya karatun kin fara kuwa..?, a'a dan girman Allah ka faɗa min. tonda kin gamu ki sani cewa naji kamar jadda yana cewa ko yayi miki miji yana faɗawa Abba to badai naji suna ba amma wace a gaban abba idan bake ba.. dariya sosai najlah tayi tace '' gaskiya kai sai addu'a kasani ko maganar auren ya TAUFIQ suke yi bada yusrah aka haɗa su ba..?, wani sanyi ne ya ziyarce shi yace '' wallahi na manta da wannan zancen haka ne kuma kinji kuwa yadda naji i love You so much.., ɗagowa tayi tana cewa amma da ka tsaya kana wani tunani sai anjima kar yaya yazo yaga ina waya. okay sai an jima ya faɗa yana mata sallama itama tayi mai ta , tashi zaune Jawad ne ya shigo fuskarnan ɗaure tamau yace '' bani wayar ki.., jikin ta ba wani kwari ta miƙa mai wayar ta amsa yayi, yana dubawa ɗazu ya shigo bama tasan ya shigo ba , shine sai da ta gama wayar sannan ya dawo history call ya je ya duba sweetheart ya MUNEEF. wannan suna da ya gani ba ƙaramin dakar mai zuciya yayi ba , kasa tsayuwa yayi da ƙafafuwan sa yaja stoll ya zauna yana mai da boyayyiyar ajiyar zuciya zura wayar yayi a aljihu abubuwa da yawa sub wa kwakwalwar sa yawa ha zubewar cikin jawaher..ga abin da ya tarar najlah tayi, rintsai idanuwan'sa yayi yana neman dauki gurin Ubangiji. ko tukin da yaya karfin hali kawai yake mafarkin da yake na samun yara ya samu kuma ya rushe amma bakomai Ubangiji da ya ba shi, shi zai ƙara bashi wani. ita kuma yau najlah zai cire duk wani tausayin ta , ya hukunta ta dai-dai da abin da tayi daman Ubangiji ya sani ƙarfin hali take yake kawar dakai to yanzu takai shi bango... tashi yayi ya fita ba tare da yace mata komai ba tausayi ya bata tasan ba a cikin hayyacin sa yake ba maganar zubewar cikin jawaher dole ta bugi zuciyar sa , Allah ya bashi wani.. yana fita daga dakin najlah study room ya shiga zama yayi yana dauko laptop din sa ta ci gaba da aikin da yake ɗazu.. kiran sallar isha da aka yi shi ya taso dashi ya bar study room ya dauko alwala ya fito. ko kallon inda dakin najlah yake beba ya fita Masallaci. Najlah da tana la'akare dashi tsoranta ɗaya karya sauke fushin sa a kan ta , ganin ya fita, ta rufe kofar ta tana sauke ajiyar zuciya tada sallah tayi gaban ta na tsananin bugu bata san dalili ba haka kurum jikin ta yayi sanyi ta shiga cikin wani irin hali itama bata san dalili ba. bayan ta idar da sallah. ta dauki karatun Alkur'ani tana karantawa ta dade tana zaune sannan ta daga hannu ta riko Ubangiji Allah ya saka ta fara zuwa makarantar nan a sa'a domin gobe idan bata manta ba yace zata fara zuwa makaranta. cire kayan ta, tayi ta chanza sleeping dress, wata riga mara nauyi karamin hannu ne da ita iya gwuiwa fitowa tayi tana waige ko zata haɗu dashi shiru parlour ba kowa shiga kitchen tayi ta buɗe fridge ba komai a cikin fridge din sosai mamaki ya kamata to ina aka kai kayan cikin fridge din ko su rose sun kashe zasu wanke fridge din be bata da me bata amsa lemo ɗaya ta gani buɗe wa tayi ta shanye shi tas tana ajiye robar daukan madara tayi da kofi tare da chokali ta fito shiga dakin ta , tayi ta haɗa maganin da aunty ta bata , tasha, dukkan su ba wanda bata sha ba.. tashi tayi ta wanko bakin ta , ta dawo hawa gado tayi tana kashe bed side lamp daman ita , ta rage a cikin dakin daba ta kashe ba, dum light ta saka blue. addu'a tayi tana jan blanket ta kwanta. ba jimawa bacci ya ɗauke ta, JAWAD ana idar da sallah ya dawo murmushi yayi ganin kofar ta a rufe ya hau sama ya ci gaba da aikin sa be tashi ba sai misalin ƙarfe 12:00 dai-dai. fitowa yayi ya rufo kofar study room sannan ya shiga dakin sa toilet ya shiga yayi wanka bayan ya fito ya saka fararen pyjamas sai kamshi suke me sanyi da dadin shaka cire medical glasses ya cire yana zama tare da zare slippers din sa. dauko wayar sa yayi ya duba sakonni na IG din sa har zai sauka yaga wani text messages ya shigo masa wayar sa dubawa yayi, kasan masaniyar cikin da yake jikin matar ka..?, to nawa ne dan haka karma Ka dorawa kanka damuwa kai kayi tunani da ƙwaƙwalwar ka sweet idan da tana son haihu dakai da tuni ta haihu me ya saka take ture ka ba tare da ka, ƙarasa buƙatar ka ba ajikin ta..? number prevent ce jan tsaki yayi ya goge messages din domin ya yarda da Jawaher baza ta , taɓa abin da zata cutar da shi ba... ajiye wayar sa yayi yana kallo agogo sha biyu da rabi tashi yayi yana shinfida prayer mat kabbara ya tayar yayi sallah raka'a biyu a ƙarshen sujjadar shi ya dade yana faɗawa Ubangiji damuwar sa. yana rikon Ubangijin ya ƙare auren su daga sharrin sheɗan ya basu ya'ya nagari Ubangiji ya azurta shi da samin ya'ya. ɗagowa yayi idon sa ya kada yayi ja , yayi sallama zama yayi yana ci gaba da kai wa Ubangiji kukan sa, daukan Alkur'ani yayi kamar yadda ya saba kullum dukkan dare ya soma karantawa har ma ya kusan yayi sauka ko da yayi ƙara juyawa yake ya jima yana karatu sannan ya rufe Alkur'anin ya ajiye shi a ma'ajiyar sa , ya ninke prayer mat. ya ajiye ta daukan key yayi, ya kashe hasken dakin ya fito yana saka slippers din sa rufe dakin yayi duba ko ina yayi ya kashe dukkan wasu fitilu na sama. saukowa ƙasa yayi ya rufe kitchen da kofar shigowa parlour. ★★★★ idan Jawaher ta tashi ya kuke ganin za a yi kusan fa ba lallai ta barmu fa musamman wannan shegiyar tsohuwar idan ta sani. Na'ilah ta fada tana zama a kujera. hmmm abin da nake tunani kenan kalli dare yayi amma kamar ba dare ba tunani ya haɗa sakat.. Cewar eman. da sauri deeyana ta kalle su tace '' ba shakka amma ku kana nan ƙwaƙwalwa gare ku bisimallah ta faɗi me ya faru wallahi tun daga sama har kasa saina tona mata asiri wallahi ku saka wa ranku ruwan sanyi, ko giyar wake jawaher ta sha wallahi ba zata fadi yadda abin yake ba.., eman tace '' nima haka nake tunani amma ga wata shawara mana.., haɗa baki suka yi suka ce muna jinki, ajiye wayar ta tayi akan center table tace '' kinsan inna badai bin malamai ba daga ita har jawaher to kafin su fara bi akan mu, mu, muje a doke mata baki, ko maganar mu suka ji, jikin su ya soma rawa ba abin da ta isa tayi mana a dai yanzu munfi karfin ta , amma zata iya bin bokaye da malamai ta sabauta rayuwar mu jawaher da kike ganin ta bata da imani ko kaɗan duk da wallahi idan na rantsai bazan yi kaffara ba hassimi da TJ sune ƙarshen ta sune ajalin ta musamman ma hassimi da neman ta yake ruwa a jallo kwanaki dana hadu dashi sai da nayi fitsari a wando iya firgita nayi faɗamin yayi duk lokacin da ya hadu da Jawaher kuma wa'adin daya diba mata ya cika ranar ba za tayi kwanan duniya ba , shi ba'a cin amanar sa , kinsan fa da shi zata aura bayan ta rabu da TJ sai UMMEE ta zo mata da tayin auren Jawad hassimi ya kashe mata kudi kamar ba gobe kuma ɗan daba ne kisa a gurin sa ba wani abu bane kinga TJ wallahi karyar iskanci yake hassimi ya taka shi a komai.., DEEYA tace '' malaman sunci kuttumar uban su ashe zama da jawaher ya saka kin fara bin malamai kudin ki, zai cinye abanza a wofi..ni dan da kike gani na wallahi nafi karfin ko wanne shege da shegiya kuma duk inda hassimi yake zan nemo shi domin ga dama ta samu da zai rama abin da tayi mai..., dariya eman tayi tace '' wani abu da baki sani ba baby saboda jawaher tazo abuja akwai abin da take nema yar taraba state ce.., da sauri Na'ilah tace '' to uwar kwashe kwashen mata , karke ma kina cikin target din ta.., takalli deeya tana faɗar haka. dariya deeya tayi tace '' wallahi Na'ilah kin ban dariya me kike tunani idan nace miki nasan abin ya kawo baby garin nan zeey ce kawai bata san wace ita ba tane mi muyi kawance nace mata a'a ni bana wannan abu da wanda ban sani ba gudun bacewar rana shi ne take ce min gashi gashi ga abin da ya faru.., gaskiya deeya ko shaidan haka ya ganki ya kyalle ki eman ta faɗa tana tafa mata. kan deeyana ne ya ƙara fasuwa ta jita a sama tace '' hmmm sai randa na kwace kujerar chairlady shugabar classis ladies zaku san ni din bata wasa ɓace wallahi daman aure na da nayi yasin hijabi ya zame min wallahi baku da tunani, shi ya saka kwata kwata bakwa zancen aure Hajiya yi aure zauna a dakin mijin ki ba me zargin ki, fita inda kike so kusan daukan ku da ake yi kwana sun san baku da abin yi ne wacce matar aure ake dauka kwana..?, tafawa suka yi suna shewa Na'ilah tace '' amma Jawaher har fita ƙasar waje take yi.., wani kallo deeya tayi wa nailah tace '' baki da tunani jawaher ai mahaukaciya ce dole wata ran mijin ta ya fahimta kece kullum akwai wanda kike da appointment dashi ni kuma sai na hanga na hango na faki numfashin san nan nake sha'ani na randa mijinta ya fahimci an koreta a makaran wallahi ranar kashin ta ya bushe.., da sauri nailah tace '' ke dan girman Allah an kore ta..?, hmmm wallahi an koreta da ba rawar kan'ta ba tana da manya bata san idan aka kore kana University, ba manya ba ko uban manya ne dakai gaba da gaban ta inhar shugaban makarantar ba dan iska bane to wallahi ba wanda ya isa ya dawo dakai ita fa bata gyara C.O carry over din ta , tafi ashirin ni kuwa din iskanci na da tara yan tasha da nake yi wallahi ina zama ina karatu eman kece sheda bana satar amsa jawaher kuwa ta kware wajen satar amsa.., cewar deeya. Na'ilah tace '' wa'yannan wacce Jawad ya shigo da ita , ita ce wacce take zaune a cikin gidan nata..?, ehmn itace cewar eman.. DEEYA tace '' insha'Allahu sai ta aure shi..sai muga ta karyar miji na miji na yawa ita ce a duniya me aure..., hamma eman tayi tace '' wallahi bacci nake ji.., waya riƙe miki kafa..cewar Na'ilah banza tayi mata , ta shiga daki ta kwanta Na'ilah tace '' dakin mijin ki ta tafi ta kwanta fa kina kallo..?, deeya tace '' ai ta raina ni, nida mijin nawa.., suma tashi sukai, suka shiga daki suka kwanta. ★★★★ Landon. UNITED KINGDOM Westminster. Buckingham palace. 1:45 Mom Ihsan hawaye ta share idanun yayi jajir saif yace '' insha'Allah zan tashi .., saif idan anyi magana daddy ihsan yace ba abin da ke damun sa kunne ga ni kuma wallahi duk lokacin da ya tafi yola ya dawo sai ya kwanta a asibiti.. da sauri yace '' a'a mom karki ɗorawa kowa laifi an dai samu haka ya faru ne amma ba wanda yake tayar masa da ciwon sa ko yaya da kike gani yana Abuja sanin kanki ne abubuwan daka gaban sa yawa ne dashi... shiru tayi ta dauki tissue ta share hawaye ta na matsar kwallah babban tashin hankalin ta da aka dauke shi daga dakin da yake aka mai ICU ɗazu da taleƙa dakin wasu irin na'ura tagani a jikin sa tamkar an samu bangon da za'a ja hutar lantarki. zama tayi, tana share hawaye mubashshar yace '' kai wallahi na rasa wanne irin tunani ne dakai saif abune a buɗe tun da ya kirawo shi jikin sa ya rikirkice amma kake wani kwana kwana shi ne sanadi wallahi.., mom Ihsan tace '' kyale ni dashi kawai kallon sa , kawai nake gani banzan zance da yake yi yawa wanda ya sha kwaya.., mubashshar yace '' ke kuwa dan uwa rabin jiki ai dole ya kare shi yadda kika san tare sukai naƙudar sa da rukayya.., cije lips din'ta tayi tace '' barni dashi barni dashi zan maganin sa..., shiru yayi musu domin yasan ba zai taɓa ganar dasu gaskiya ba , amma yana rokon Ubangiji ya ganar da su gaskiya. ★★★ ABUJA OSOKORO. 12:50 GMT. key ya saka ya buɗe dakin najlah, a hankali ya mai da kofar ya rufe. pyjamas din'sa ya cire daga shi sai boxer ya hau kan gadon juyota yayi tana facing din sa light kiss yayi mata a kumatun ta yana jin zuciyar sa na ƙara in giza shi akan abin da yayi niya limshe idon sa yayi ko yaya yana kusa da najlah sai yaji ya samu wata iriyar nutsuwa a tare da ita wacce a gurin jawaher ko rabin ta baya samu shi ya saka aka ce mata suna suka tara ashe wannan maganar gaskiya akwai mace akwai muna mata.. zuciyar sace tayi wani irin rawa zai so ace wanna abin da yake faruwa tana kallon sa yana kallon ta , suna aikawa da juna kalaman soyayya dukka shidin bakon shiga ne a wannan fagen amma tabbas tun da zuciyar'sa ta samu abin da take so bema san lokacin da zai zubo mata da nasa kalman ba... jamata hanci yayi yana kwantar dakan sa a kan kirjinsa. fara sama yayi da rigar ta sa'a yace bata saka bra ba limshe idon sa ya ƙara cikin zafi zafi yake sararafata tamkar ba'a hayyacin sa yake ba , ji yaka anya kuwa ya taɓa jin abin da ya yaji a duniya...? kuka ta fara tana kokarin ture shi dukka bata da wani karfi still idon ta a rufe yake cikin yanayin bacci da ya ƙara haifar mai da wani irin energy a jikin sa tace '' dan Allah kai hakuri dan Allah karka cutar min da rayuwata karka tarwatsa min rayuwata kai waye ne me ya saka kake san cutar da baiwar Allah yarinya.., habawa jawad besan lokacin da ya haɗe bakin su guri ɗaya ba ya hanata maganar da take yi lakwas tayi daman bata da wani karfi maganin baccin da tasha a lemo me karfi ne.... addu'a ya karanto ya soma daukar hanya gam ba wata kafa cije lips din'sa yayi ji yake idan be yi ba ba zai mutu ji yake duniyar da yake cikin ta bama ya fatan dawowa zai so ya dawwama a cikin ta har abada tabbas najlah duniya ce..., tabbas ta cancanci fassara sunan tana kyakkyawa ce ta ko wanne fanni.. still bakin sa hana haɗe danata ko kuka be bata damar tayi ba sai dai buge buge take ƙara kwatanta shiga yayi amma abu ya ci tira sai da yayi haka yafi sau biyar sannan Allah ya bashi nasara da sa'a ya danna da karfi wani irin ihu ta saki saboda a lokacin ya cire bakin sa , ya maida kan kirjin'ta daga nan bata sake sanin inda kan'ta yake ba. Jawad be samu kan'sa ba sai misalin karfe hudu da rabi, ji yake tamkar an cire mai dukka wata damuwa tashi.. rungume ta yayi yana saka mata albarka kunna fitila yayi, abin da ya gani yayi mamaki sosai tashi yayi da sauri white bedsheet din gadon nata yayi faca faca da jini.., a lokacin JAWAHER be ga wannan abu ba dukkan ba wani abu bane saboda ko wacce mace akwai yanayin ƙaddarar ta , idan tazo ba jini bawai haka , yana nufin cewa ba , budurwa bace amma tabbas ni'imar najlah dabam ce.. daga ta yayi ya gyara ko ina ya cire bedsheet ya canza ɗayan ya dauka ya ninke shi tamkar ba ayi komai a dakin ba wanka ya shiga yayi ya fito ya mai da kayan sa itama mai da mata da kaya yayi bayan ya share mata jinin jikin ta haɗe da sperm din da ya hade da jini ya mai da mata kaya sosai ya tausaya mata saboda yadda ya ga gaban ta yayi Allah ya saka bata samu stitch ba domin yadda wajen yayi dakyar ne bata samu matsala ba , shi kan'sa yasan yafi karfin ta.. tashi yayi ya fita hawa sama yayi ya chanza kaya ya zauna yana jiran a kirawo sallar asuba yana duba agogo yaga lokaci yayi, ya fita. ana idarwa ko tsayawa azkar beba ya dawo domin hankalin sa gaba ki daya yana kan'ta.. shiga dakin ta yayi still har yanzu tana bacci ga lokacin sallah yayi gashi jiya bata samu wani ishashshen bacci ba kyale ta yayi ya koma sama tunowa yayi da bedsheet da sauri ya dauko shi a washing machine ya saka shi tas ya wanke ya busar dashi sannan ya shanya shi ya ƙarasa bushewa. zama yayi yana duba lokaci karfe bakwai dai-dai ya sauko still tana kwance yadda ya barta gaban sane ya fadi ya soma tashin ta sai dai ko motsi bata yi. habawa Jawad rasa inda zai saka kan'sa yayi, baya so kaita asibiti saboda kunya mutum kamar sa ace abu kaza ya faru ko safeera zai nema tunda gynaecology ce da wannan shawarar ya tashi ya dauko wayar sa kiran number HISHAM yayi ɗagawa yayi yana cewa Jawad me kake yi haka , kasan ni fa ba gauro bane ina da iyali kake kirana a wannan lokaci...? takaici ne ya ishe shi yace '' kaga bani da Lokacin ka sai ka nemo wanda bashi da mata ɗaya ɗaya dan Allah safeera tazo da kayan aiki najlah ba lafiya.., innalillahi wainna ilaihir raji'un me ya faru da ita.. sanin da yayi HISHAM ba aminin da zai yiwa rufa rufa bane kuma yana cikin tashin hankali be sa ni ba ko ba zata tashi ba ko motsi bata yi yace '' wallahi ko motsi bata yi nayi ne.., kai me kayi kaifa dan iska ne faɗa min me ya faru...?,kace kayi nasan me kayi...kana magana a juye ce maka akai hausa ba karanta..?, tamkar me rada Jawad yace '' am daman jiya ne.., JAWAD kabar yar mutane a wani hali kana kwana kwana jiya me aka yi...? Jawad tamkar wani zautacce yac "Yesterday I almost said she would wake up, but until now she hasn't woken up, sai dakai dan kunar bakin wake yarinyar Mutane tana kwance har kana da lokacin hada kalmomin turanci ka faɗa min.. lura da yayi HISHAM yana sane yake mai haka domin dariyar da yake danne wa ta subbuce mai kashe wayar sa yayi yana ayyana Allah ya saka komai ya lafa wallahi sai ya rama abin da yayi mai tasss. fitowa parlour yayi yana zagaya shigowar su rose ya gani tun daga parlour na ɗaya ransa ne ya ɓaci ya sauko daga kan step din da yake ya ƙaraso gurin su gaishe da shi suka yi kan'su a kasa dan jim yayi sannan yace '' yauma basai kun girka komai ba ku tafi.., rose cikin fargaba tace '' sir Allah dai ya saka ba wata matsalar aka samu ba.., Jawad yace '' a bakomai kuje har yanzu kuna kan akin ku kawai JAWAHEER bata nan ..., to suka ce suna godiya. fita suka yi suna fita safeera ta shigo gaisawa suka yi tace "tana ina...,'" jagora yayi mata har dakin ta , samin sa tayi tamkar ba abin da ya faru sai fuskar ta da ta kumbura haka ma idanuwanta.. taɓa zuciyar ta , tayi tace '' karka damu kawai ta shiga shock ne zan duba ta insha'Allahu yanzu..., to yace tamkar wani yaro Karami abin dariya ya so bawa safeera zata so ace Hisham yana nan da yau sai cikin sa ya kusan murɗe da saboda dariya Jawad din da ko kallo mata basu ishe shi ba Jawad me ji da kan'sa yau yarinya karama ce ta mai dashi haka.. ɗaga rigar'ta, tayi zaro ido tayi da sauri ya leƙo yana cewa doctor ba dai wata matsala ta samu ba .. tunda yasan yara ƙanana suna kamuwa da cutar, yoyan fitsari dan haka ta faru ba zai taɓa yafewa kan'sa ba da ya kasa control din kan'sa gaskiya najlah ba ƙaramin Sa'a taci ba ta cabke zuciyar namiji kamar jawad, duk da shima da alama bema son yana matukar sonta ba.. da sauri tace '' a'a zan yi mata stitch ne..., jawad yace '' to idan akai zata , tashi kuma ba zafi kar zafin ya zame mata biyu ba'a bari a warke daga wannan ciwon sannan sai ayi stitch din..?, safeera ta danne dariyar ta domin ta lura iya gaskiyar sa Jawad yake fadi tausaya mata radadi da azabar da zata sha yake tace '' a'a idan kuma ya jima sai yafi haka zafi taji dad'in jikin ta sai yafi mata zafi.., to ya fada yana fita alurar kashe zafi tayi mata , tas ta dinke ta , sannan tayi mata allura ta saka mata ruwa fitowa tayi tana cewa na gama yi mata dan Allah a kula ban da aiki me nauyi karta motsa jikin ta abu me ruwa zata dinga ci mara nauyi saboda bayan gida zai iya haifar mata da matsala..idan taci me tauri wajen zai iya farke'wa , zuwa sati biyu zan dawo na duba shi na rubuta mata magani nayi maka text messages domin ba takarda a hannu kaje ka siyo suna rage radadi banda magana me karfi ko tari sannan ta dinga shiga ruwa me dumi zai temaka mata..., jikin Jawad a sanyaye yace '' to ngd safeera nawa ne kudin aikin naki...? haɗe rai tayi tace '' kanwa ta fa na gyara haba yallabai ko kobo ba zan amsa ba..., godiya ya kara yi mata sannan ya raka ra har wajen motar ta shiha tayi shima ya dawo key ya dauko ya shiga motar da well care ya isa ya mika wayar da maganin da ta rubuto suka bashi Sannan ya basu kuɗin su ya fito. shiga mota yayi, gudu sosai yana tunanin karya ta , tashi parking yayi, ya fito cikin sauri ya shiga parlour shiga dakin ta yayi ya zauna a kusa da ita... ya zuba mata ido yayi yana kallon ta fuskar ta , tayi fayau ture kalbar kan'ta yayi yana riƙe hannun ta , ruwan hannun ta ne ya kare cire mata yayi yan ci gaba da kallon ta , ya dade sosai a zaune wanda shina be san iya adadin lokacin da ya ɗauka a haka.. najlah a hankali ya soma daga idon ta , dayi yi mata nauyi tas abin da ya faru da ita jiya ya dawo mata ihu ta zunduma da sauri ya rufe mata baki hana cewa na shiga uku najlah baki san baki da lafiya ba akwai ciwo a jikin ki.. fisge fisge ta fara dakyar ya samu ta dena yana cewa nine fa baki gane ni ba..? wani marayen kuka ta rushe dashi tana kwantar da kan'ta a kan cinyar sa sosai kasan ta ke mata zugi wanda ta rasa dalili jawad tausayi ta bashi yace '' kiyi shiru kinji yan zu me ke miki ciwo....?, ɗago idanuwan'ta tayi ta kalle sa so take tayi magana amma ji take bakin ta yayi nauyi ƙara kwantar da kai tayi a jikin sa zuciyar'ta sai wani irin harbawa take. shiru tayi tamkar ruwa ya cinye ta saboda duk wani kuka da take da motsin da take tamkar ƙarawa jikin ta ciwo take ko ina na jikin ta ciwo ga kasan ta zafi. shafa bayan ta yake a hankali yace '' tashi na raka ki, kiyi wanka sai kiyi sallah.., bazan iya tashi ba kafafuwana cirewa za suyi zafi suke min dan Allah me likita tace maka nace nayi losing virginal din'na ko..?, shafa fuskar'ta yayi yace '' virginal kuma...? faɗa min me ya faru..?, ɗagowa tayi ta kalle sa kirjinta na duk kan uku uku tace '' ehmn mutumin nan ne ya zo na mashi hakuri, amma sai yaƙi.., najlah mafarki fa ba, ba gaskiya bane. mai da kan'ta tayi tace '' to kafata bata dena aiki ba ...? zan ƙara tafiya kuwa..?, Jawad ya ɗaga ta yana cewa insha'Allahu muje na haɗa miki ruwa, har toilet ya ɗauke ta , ya Kaita ajiye ta yayi akan kujera hada mata ruwan zafi yayi. kallon ta yayi yace '' gashi nan ki yi wanka sai ki gasa jikin ki, ki dade a cikin sa Saboda zai temakawa ciwon ki.., kai ta ɗaga mai fita yayi ya ja mata kofa, dakyar ta iya cire rigar'ta, shatin fingers ta gani akan breast dinta hawaye ta goge Allah yayi mata katangar karfe da wannan aljanni. dakyar ta iya wankan tsarki sannan tayi wanka towel ta daura batare data shiga cikin ruwan da ya ce ta shiga ba wannan ma karfin hali take zama tayi tana matsai kafafuwan'ta da ko iska bata so, ta shiga.. ganin shiru shiru bata fito ba ya leƙo yana cewa lafiya har yanzu baki fito ba , hawaye ta share tace '' bazan iya fitowa ba kafafuwana ciwo yadda kasan basa jiki na haka nake ji..., sannu kinji Allah ya baki lafiya. ya faɗa yana daukar ta kamar wata jaririya be ajiye ta a ko ina ba sai a kan gado buɗe wardrobe yayi ya dauko mata doguwar riga da pant sai bra ya miƙo mata kallon sa tayi tace '' ka fita zan saka kaya na.., da sauri ya kalle sai kuma ya juya ya , fita dariya na cin sa wai fita zan saka kaya, to wanne dare ne jemage be gani ba..?, Najlah kuwa a hankali ta dauki rigar ta saka tana ya mutsa fuska ko pant bata iya ɗaga kafar ta , ta saka ba yadda ya ajiye mata haka tabar su bra kuwa ta saka ai sai ta kusan zaucewa saboda ciwo komai fa ciwo yake mata. a hankali ta dafa kan gado ta dauko hijabi ta saka tana tayar da sallah a zaune zaman ma da take na karfin hali ne , dakyar ta idar da sallah domin allurar da akai mata , ta fara sakin ta. cire hijabinta tayi tana sakin kuka kasa ƙasa shigowa yayi hannun sa rike da tray da kofi sai tururi yake.. ajiye mata yayi yace '' najlah nace ki fadan me ke damun ki, kinki kuma kin zauna kina kuka...ga tea nan ki sha ba komai a cikin ki.., kuka ta ƙara rushewa dashi tana girgiza kan'ta tace '' mutuwa zanyi yaya zafi yake min bana iya daga ƙafa'ta.., habawa jawad rasa inda zai tsoma ran'sa yayi zama yayi yana janyo jikin sa sosai yake rarrashin ta amma fafur taki yin shiru babbar damuwar sa ba komau a cikin ta sai sperm din sa ya kamata ace taci ko wani abu ne.. cikin faɗa yace '' wallahi idan baki shaba ranki sai yayi mugun ɓaci.., ganin yadda ya koma mata asalin jawad tashi tayi tana dafa kasa da hannun ta , ta kasa zama da bombom din ta ta dauki kofin tea ta soma sha tana kuka... zuba mata ido yayi yana kallon ta. har ta maga sha daukar kofin yayi yana kallon ta , yace '' wannan fa naga ko rabi baki sha fa..?, na koshi ta faɗa tana ƙoƙarin hawa gado.. temaka mata yayi yana cewa kin dai gasa jikin ki ko tace shi ne jikin ki zai saki.., daga mai kai tayi magani ya ɓallo mata. dauko ruwa yayi ya miƙo mata yana cewa kisha zaki kara jin daɗin jikin ki.. amsa tayi ta sha tana runtsai idon ta, kauda kai tayi tana mai da kai ta kwanta. ranar haka ya yuni yana hidimar najlah tayi kuka ta gaji ta hakura sai kuma, takara ci gaba da kuka gaba ki ɗaya, ya rasa yadda zai yi da ita sai ririta, ta yake kamar kwai shaf ya manta da zancen jawaher da take asibiti. bayan ya dawo daga masallaci anyi sallar isha ya zauna yana kallon ta , yace '' najlah ni ko daukar ki zan yi na kaiki gidan Hisham safeera ce ta duba ki ta , ƙara dubawa domin wannan kukan da kika yuni kina yi kar ya lalata ciwon ki.. ni wallahi ba inda zani haka kurum ta ga gaba na.. shiru yayi ya zuba mata ido tun da yake be taɓa ganin wannan rigimar ba ga uwar shagwaɓa da take mai gaba ki ɗaya ta susuta shi..ta hana shi sakat idan tana wani abin sai ya shagala da kallon ta. dauke kai tayi tana turo bakin ta , tace '' uhmm yaya.., Jawad yace '' na'am najlah.., hawaye ta share tace '' yanzu tafiya zakai ka kwanta ko..?, eh akwai abin da zan miki ne..? yaya toilet zan shiga ina jin fitsari amma ban san ta ina zai fito ba ciwo na.. karki damu be shafi nan...ba da sauri ta kalle sa tace '' ta nuna maka ka gani ne..?, eh nagani.. da sauri ta ɗora hannu akai tana zaro ido tace '' dan Allah fa.., uhmmm na gani shikkenan ta kashe ni haka kurum ta nuna maka wallahi taci amanar aikin likita.. NAJLAH wallahi idan baki dena kukan nan ba ranki zai ɓaci wai me kika dauke ni ne tun ɗazu nake lallaɓa ki , kina kuka yanzu daga faɗar magana sai kuka, shi wannan kukan magani ne? abinci kinki ci na tambaye ki me kike so kinyi shiru.., ina kike so na saka rayuwa ta..?, ne kalli wunin yau yadda nayi shi ko baccin ɗazu dana kwanta kika zunduma ihu sai dana tashi amma ina zuwa naganki a yadda na barki.., shiru tayi tana kwanciya , tamkar ba da ita yake ba , ganin zai tafi yana shirin kashe mata fitila tace '' dan Allah ka dawo nan dakin ka shinfiɗa blanket a kasan gadon nan , ka kwanta.., to zanyi haka..yanzu zan tafi nayi wanka ne na shirya sai na dawo.. Najlah tace '' nima zan yi wanka..sai nayi fitsari, to ya faɗa yana daukar ta toilet ya kai ta ya nannaɗe mata riga ya saka ta akan masan zama riƙe shi tayi gam tana kuka tace '' yaki zubowa wallahi ciwo wayyo Allah na Hajiya ta wayyo aunty Hafsah wayyo Abba wayyo aunty rafi'at..., yau jawad yayi dana sani yafi sau nawa , gaba ki ɗaya ya damu kan'sa ganin halin da take ciki daman, ga ciwon najlah raki, ya lafiyar kura ɓalle tayi zawo hakuri ya rage mai shi yanzu wannan yadda ake faɗar ciki idan ta samu besan ya zai ba.., kwata kwata be dauki abin haka ba , jawaher tayi amma be kai na , najlah ba. dakyar ta cije tayi fitsari. fita yayi tai tsari sannan ya dawo ya haɗa mata ruwa ya fita, cikin sauri yake hawa sama dakin sa ya shiga da sauri ya dauki wayar sa ganin ana kira number inna ce , ɗagawa yayi yana karawa a kunne yace '' Assalamu alaiki.., haba Jawad ina ya ban ka sallah zaka , kasa alwala tun jiya da ka saka, kafa ka tafi yarinyar nan , na cikin mawuyacin hali ko a jikin ka shi ne baka dawo ba tun safe nake zuba ido ganin kai baka san zuru ba shi ne na kirawo wa ka barni tun kayan da na zo dasu jiya.. dafa kan'sa yayi yana cewa '' inna kiyi hakuri wallahi Allah aiki ne yayi min yawa , bawai ina sane naki zuwa ba insha'Allahu gobe zan kawo miki ya jikin nata.., uhmm da sauki anma ce a siya wannan maganin aeropin paracetamol.. kudin su dubu biyar.. dan jim yayi yana mamakin son kudi irin nama matar nan komai a asibitin bayarwa suke sai dai kawai su cira a kudin ka shine take mai wannan lissafin amma saboda ita din uwa ce sai yace '' insha'Allahu idan nazo zan baki.., yauwa sai anjima ko bari su gaisa ba suyi ba dariya yayi kai idan da ranka zaka sha kallo banda kudin data kwace shi ne yanzu take neman dubu goma.. shiga toilet yayi ya cire kayan sa , ta sakarwa kan'sa shower tana rufe idon sa , wani irin sanyi yake ji na ratsa shi da nutsuwa, albarka kuwa shi kansa besan iya adadin da ya sakawa najlah ba... ★★★. buɗe maltina tayi tana cewa mutuwar wani tashin wani rabon naci nawa kason Ubangiji ya kawo ni nan , Allah ya hana jaburu zuwa domin ɗazu yace besan me take kullawa ba zai zo ayi komai dashi tasan son zuciyar sa , jaburu a yanayin satar sa ko mutum ya samu damar sacewa sacewa zai yi , idan yazo nan shikkenan tata ta kare wuf wuf zai yi ya dinga kwashe komai da sauri ta dauki waya tana kallon jawaher tace '' wallahi jawaher idan jaburu yazo tofa komai ya tsaya min gwara na saka yar ɗagwas ta hana shi zuwa.. da kallo jawaher ta bita domin tun ɗazu take mamakin INNA har karyar da tayi tana jin ta kash bata san wane ya faɗawa INNA wannan maganar ba. ta kwaso jiki ta tawo gashi nan ko ɗazu sai da sukai fada da wata nurse ba'a isa a faɗa mata gaskiya ba sai tahau tijara yawa a gidan dambe aka raine ta. juyar da kai tayi dakyar tana fatan Allah ya kawo jujal yayi gaba da ita ko nawa ne zata bashi ya tattara ta su koma BINYERI. uhmmm kyayi kya gama sai wani kallo kike bina dashi wallahi jawa da ace ba'a gida na haife ki ba ta tabbas ce wa zanyi chanza min ke aka yi duk wani take taken ki ina lura tun jiya sai wani hade rai kike kina fici fici da ido, kamar kwallon a gwaluma ke daman ido ba ido ba.. karawa wayar tayi a kunne tace '' yauwa yar ɗagwas wani temakon za kiyi min kina jina naji kinyi shiru alooo aloo aloo (Hello ) ciro ta tayi a kunne dubawa tayi ashe ta , ta goce mita ta dinga yi tana ci gaba da shan maltinar ta, wata gyatsa tayi ta miƙe kafafuwan ta , tana cewa malam yaso yi min tsakiyar da babu ruwa ya cuce ni , ina can a zaune ko ficika baki san ki turo mib ba gaskiya jawa ban san inda kika gado wannan bakin halin ba.. ta fadi haka gana ƙoƙarin zira batirin wayar ta , ta ★★★ fitowa yayi daure da towel a kugun sa da wani kuma a hannu yana tsane gashin kansa zama yayi akan dressing mirror chair yana dauko mai ya soma shafawa zuciyar sa na gurin najlah ko yanzu ta gama zai je dai ya gani.. shaf shaf ya gama ya zura wando three-quarter daukan blanket yayi ya dauki wayar sa ya fita samin ta yayi a ƙasa daga ita sai toilet tana jan ajiyar zuciya.. ajiye kayan hannun sa yayi yana durkusawa yace '' har kin gama baki jira nazo na dauke ki ba..?, habawa najlah firgita tayi ganin sa ba kaya da sauri tayi baya towel din'ta ne ya kunce ba karamin gigita tayi ba da ganin sa da tayi ba kaya, jikin ta ya hau sama zikiri JAWAD da sauri ya riƙe ta yace.... Alhamdulilah ayau na kawo karshen book 1 Wannan litattafin na kudi ne 1k 8141785374 Amina alhasan Muhammad opay Turo da shedar biya ta wannan number 09061890481 Idan baki shirya ba , karki min magana dan Allah Downloaded from GNOVELS.COM.NG This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG For feedback and support Facebook : https://facebook.com/gnovels Twitter : https://twitter.com/gnovels Telegram : https://t.me/gnovels