Downloaded from GNOVELS.COM.NG This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG For feedback and support Facebook : https://facebook.com/gnovels Twitter : https://twitter.com/gnovels Telegram : https://t.me/gnovels [30/12/2018, 21:35] Maryam Obam Group Kd: *JAWAHEER* *STORY AND WRITEEN BY......* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA* *(maryam Obam)* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝* *{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}* *wattpad @maryam-obam* *WWW.Maryamobamnovels.com* https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/ *DEDICATED TO.....* *Nafisa mrs dan'malikin kawo* Page 1 *Da sunan Allah mai rahma Mai jin qai wanda ya kara bani ikon fara rubuta wani labari bayan na kammala *TAMBARIN TALAKA* *yanda na fara lafiya Allah kasa in gama lafiya🙏* *Wannan labarin ban yishi dancin zarafin wani koh wata ba So idan kaga abunda ke ciki yayi shige da rayuwanka badan kai nayi ba ko dan ke* *ban yarda wani ko wata su canza Min labari tako wani siga ba duk wanda yayi haka ba tare da izini naba ban yafe ba* Kasar Spain kasa ce da take da mutane fararan fata wato turawa sannan ita wannan kasar yare daya takeyi wato Spanish sai wasu tsirara suke English a airport mutane ne makil anata ihu tare da gudu Wanda yaja hankalin Wanda basu san dalilin ihun ba, suma suka fara dubawa koh lafiya wani matashi ne kallo daya zaka masa kasan cewa shima bature ne jami'an tsaro ne a zagaye dashi yayin da mutane suke ta faman miki mishi paper da biro wasu kuma nata faman daukanshi hoto tafiya yakeyi yayin da yake daga musu hannu shima wata yarinya karama yaga tana miko mishi takarda da biro tsayawa yayi ya amsa tare dayi mata signing sannan ya shafa kanta ya mika mata takardan har waje mutane suka bishi inda motoci ke jiran su, daya daka cikin motar aka bude mai Ya shiga yana daga ma mutane hannu jan motar akayi Suka bar wajan, wani dangareren Gida suka nufa bayan Sun faka aka bude motar fitowa yayi ya nufi kofar shiga cikin gidan bell ya danna wata baturiya daka gani Mai aiki ce dan Tana sanye da kayan masu aiki itace ta bude kofar ganin wanda yake bakin kofar yasata saurin rungumeshi tare da fadin sannu da zuwa duk cikin yaren Spanish suke magana da Fara'a ya amsa da nagode ina Dad? Tace yana ciki yan..... Kafin ta karasa sai ga wani mutum ya fito dan dattijo da sauri ya nufi saurayin yayi hugging dinshi yana fadin My son barka da zuwa dan sakinshi yayi tare da buga kafadan shi yana fadin ina alfahari dakai murmushi saurayin yayi tare da fadin ngd Dad zama yayi akan kujeran dake falon wanda yasha kayan more rayuwa tare da fadin mai aka ajiye min? Dad yace your favorite mai aikin gidan ce ta Kawo mai coffee amsa yayi tare da fadin thank gina yana dan hadawa da turanci cikin maganan shi, Sha ya farayi sannan ya tashi ya nufi dinning inda ya bude wata hummer ya zuba abinci ya fara ci bai wani ci da yawa ba ya tashi ya haura dakinshi dake gidan wai waye wannan saurayin ne..... Muhammad samir sunansa dan asalin kasar Spain ne domin a nan mahaifinshi yake dan kwallon kafa ne a laliga wanda yake bugama FC Barcelona yana daya daka cikin manyan yan kwallon da ake alfahari dashi a duniya baki daya Wanda akafi sani da m samir tun yana yaro Dad dinshi yace Mum dinshi ta rasu bai taba ganin koda hotan mum dinshi ba, abun yana damunshi sai yasa bai cika zama kasar shi ba dan yana fushi sosai idan ya tuna bai san waye mum dinshi ba, a hannun gina ya taso duk da ita ba musulma bace amma mahaifinshi na kula Dashi tun yana karami yake son buga kwallon kafa kasancewan son kwallonshi yayi yawa yasa bai wani yi karatu mai zurfi ba daka secondary Skul ya gama ya fara buga kwallon kafa duk da sai mai hanya yake samu shima Dad dinshi yana daya daka masu kudin kasar Spain sai yasa bai wani sha wuya ba wajan hayewa, da yana premier league inda yake buga ma Manchester United daka baya ya koma laliga yake buga ma Barcelona wanda aka bashi number 7 domin irin cin kwallon da yake yi number dinne ya dace Dashi sunan mahaifinshi Muhammad Ali, sai yake amfani da sunan Dad din nashi Kafin nashi, m samir matashin saurayi kwata2 shekaranshi 28 a duniya yana da kudin Dashi kanshi bai san nawa ke gareshi ba domin bayan kwallo yana business amma bashi yake kula dashi ba yana da budurwa mai suna sonia yar kasar England duk da ba musulma bace amma yana sonta kuma ita yake son aura tunda addininshi bai haramta mishi hakan ba wannan shine kadan daka labarin shi...... Koda ya shiga daki wanka yayi yasa boxer da singlet kwanciya yayi tare da daukan wayanshi yana dannawa message ne kala2 gasu nan duk bai bude ba ga wasu na kara shigowa Dan tsaki yayi domin bai san ta yanda zai fara karantawa ba inda yana tare da Sonia ne data karanta mai dialing din number dinta yayi ya kara a kunne bugu biyu ta daga tare da fadin swt hrt I miss you wen r u coming bck dariya yayi mai sauti tare da fadin Sonia yau fah nazo Spain and jiya muna tare tace kasan bana son kayi nisa Dani in baka dawo ba nan da 1 week zan zo Spain yace OK zan dawo b4 d tym kafin nan munyi match din da za'ayi inma ban dawo ba sai kizo dan nima nayi missing dinki sosai nan sukaci gaba da hira na soyayya duk cikin harshen turanci kafin suka kashe wayan. *NIGERIA* Garin abuja wata matashiya ce cikin riga da wando tasa karamin gyale ta yane kanta kallo daya zaka mata kasan yar wani babban mutum ce domin cikin falon da take zaune ya isa ya nuna maka suna da dukiya yarinyar fara ce tana da tsawo amma ba sosai ba sannan kuma ba wada bace tsawonta dai normal tana da manyan ido sosai ga gashin ido kaman tasa lashes gata fara kaman kalan larabawa kyanta ya wuce duk yanda mai karatu yake tunani wani saurayi ne ya shigo falon da sauri ta tashi tana fadin Ozil dan Allah karfe nawa barce suke da wasa nasha koh 2 ne gashi nasa duk channels din da ake kwallo amma ba'a fara ba, yace toh m samir ai ba zasu nuna ba a nan nima yanzu gidan ball zani inga irin cin da za'a ma Barcelona tace haba dai muna fa da m samir taya za'a cimu dariya yayi yace haba mu madrid ai muke da yan wasa ba kuba gidan madara tace dan Allah ni mubar wannan musun muje Gidan kallon tare in yaso in mun dawo asa mana irin dish din Gidan kallon, wata mata ce ta amshe da fadin amma kam jawaeer kina da aiki dan rashin mafadi da kamun kai sai kice zaki Gidan kallon ball bayan kin san duk Maza ne a ciki babu mata? Kai kuma kabir harda biye mata koh? Baki ta turo tare da fadin mum dasu M samir za'a buga fa kuma kin san in ban ganshi ba zan shiga cikin damuwa, Mum salati tayi tare da fadin jawaeer anya ba gamo kikayi ba ki dauki son duniya ki daura ma wanda bai san dake ba bai masan da zaman ki ba may be ma bai san kasarki Nigeria ba, tace mum taya zaki ce bai san Nigeria ba bayan anayin World Cup nidai Mum mun tafi kallo sai mun dawo ta kalli kabir tace Ozil muje dan Allah tym na tafiya fita sukai suka bar Mum na jimami tare da tausayin yarta ita kuma kalan jarabawan ta kenan son dan kwallo har take fadin shi zata Aura in bashi ba babu wanda zata Aura gashi ita ba yarinya ba balle ace yarinta ne tunda yanzu tana shekara 20 dai2 a duniya zama Mum tayi tana tuna baya lokcin da jawaheer taga m samir ta rude take fadin shi zata Aura har take gaya ma dad dinta kullum tayi sallah sai tace Allah yasa ya aureta wai wacece jawaheer?........ Ku biyoni dan ji yawan comment shi zai nuna min kuna son ci gaba..... *Maryam obam* [31/12/2018, 14:16] Maryam Obam Group Kd: *JAWAHEER* *STORY AND WRITEEN BY......* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA* *(maryam Obam)* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝* *{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}* *wattpad @maryam-obam* *WWW.Maryamobamnovels.com* https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/ Page 2 Alhaji Jibrin mai dala dan kasuwa ne na daya wanda a Nigeria ake alfahari dashi bama Nigeria ba harta kasashen waje baya siyasa duk wani Abu da akeci shi yake kawo wa babu wanda bai san sunanshi ba a Nigeria harta karamin yaro yasan Alhaji Jibrin mai dala yana daya daka cikin masu jerin masu kudin duniya za'a iya cewa yana cikin na hudu ko na uku matarshi daya hjy bilkisu yaransu uku umar shine babba yana aiki a nnpc yana da Mata sai khalil shi bashi da aure ya kammala karatun shi Oxford sai jawaheer da take karatu a nan abuja tana 2lv tana karantan English duk da dukiyar su sunyi karatun addini dan dukansu babu wanda bai sauke al'qur'ani ba da sauran littafai, mahaifinsu yana matukar ji da jawaheer baya iya musa mata ga duk abunda take bukata kodan ita daya ce Mace yarshi oho, jawaheer kyakyawa ce ajin farko gata fara Sol kaman balarabiya ga manyan ido ga lips dinta Pink gwanin Sha'awa tana da hanci dogo siriri komai dai Alhmdlh, kabir Abokin khalil ne yana zuwa Gidan suna kallon ball jawaheer bata son kwallo koh kadan gashi idan anayi su Khalil a falon Gidan suke zama su kalla wata rana jawaheer ta dawo daka lecture taga suna kallon ball zama tayi tana dan yatsina fuska a dai2 lokacin akaci kwallo khalil ya kwala ihu kallon TV din tayi taga wanda yaci kwallon gabanta ne taji yana dukan uku2 M samir taji ana ta fadi shi yaci kwallon wani irin dadi takeji da taji musulmi ne nan ta Fara tambayan Khalil waye wannan yace M samir kenan tace wani team yake yace Manchester United lokacin yana Man u bai koma barce ba, wayanta ta dauka tayi searching sunanshi a Google nan taga biography nashi da pictures dinshi ta Fara saving tun daka ranan ta fara kallon Ball kabir kuma ya zama abokinta kullum suna cikin waya yaushe za'ayi premier league sometimes ma har Gidan ball take zuwa taga koh an rubuta in Man u za suyi wasa tun bata fadin manufarta ba harta fara gaya wai ita shi zata aura Mum dinta inta fara maganan tsaki takeyi tace bata da hankali Dad dinta kam biye mata yakeyi in Mum dinta taji hakan sai tabar musu wajan dan ba zata iya jin wannan shirmen na jawaheer ba in banda abunta ina ita ina farin fata bature mai kyamar bakin fata yau koh kasar su kaje haka za suyi ta nuna maka kyama musamman ma idan suka ganka bakin fata ita gwara jawaheer dinma fara ce sol, duk wani receiver jawaheer tasa ansa a Gidan dan kawai saboda kallon ball dakinta ta manne shi da hotunan m samir duka Khalil dan Manchester United ne kabir kuma dan Madrid suna ce mai Ozil sai itama jawaheer yar Manchester United ce da M samir laliga suka siyeshi ya koma Barcelona itama tabar man u ta dawo Barcelona dan ita M samir take bi, jawaheer bata kula ko wani saurayi saboda a ce warta m samir zata Aura wannan shine labarin jawaheer bari mu dawo kan labari. Koda suka isa gidan kallon ball cike yake da mutane makil duk maza jawaheer tsayawa tayi tana tunanin yanda zata shiga kallon kabir tayi tace Ozil taya zan shiga?bude kofar motar yayi tare da fadin ina zuwa fita yayi jim kadan sai gashi yace mata ta fito, fita tayi ta bishi sukai ciki Ashe Gidan kallon ball din waje2 ne akwai na yaku bayi akwai na masu hali kuma yana da girma daki daya suka zauna ita da kabir babu kowa a ciki gashi har anyi nisa, Madrid suna cin daya Barcelona kuma 0 ana 1-0 jawaheer kallo takeyi amma kaman za tayi kuka dan takaici domin su ake ci shiko kabir sune suka ci, M samir ne ya buga wata kwallo ta shige Raga ihu ta saki tare da fadin a gooooooo wow my Luv ina sonka shiko kabir shuru yayi tare dajin haushin cin da Barcelona sukayi yanzu sun dawo 1-1 har akaje half time babu wanda ya kara ci suna nan zaune ita da kabir suna fira har aka dawo, ci gaba akayi da kallo Real Madrid ne suka kara ci jawaheer kam haushi kaman ya kashe ta ana cikin haka aka buge m samir ya fadi kasa tare da rike kafar shi jawaheer bata san lokacin data fara kuka ba buguwan sosai yayi dan haka dole aka cire shi aka sa wani jawaheer ganin haka yasa ta fara kuka Dan tasan m samir ba karamin buguwa yayi ba wanda yasa har ya kasa tashi fita tayi daka Gidan kallon da gudu tana kuka tare dajin radadi cikin zuciyarta mota ta shiga kabir yazo ya sameta yana fadin haba jawaheer maiya sameki kuma kinga kun kara ci ma, tace kabir baka ga anji ma my samir ciwo ba har an cire shi mai yasa bazan yi kuka ba? Kabir yace haba jawaheer aiba wani serious ciwo bane, tace what ba serious ciwo bane kana ganin har an cire shi kuka ta kuma Saki tare da fadin dan Allah shigo mu koma Gida kabir kafin zuciya na ta buga kabir cikin tausayin kanwar tashi kuma kawarshi tunda yanzu sunfi shiri ma akan Khalil shiga motar yayi ya kunna suka tafi babu abunda kake ji sai kukan jawaheer hmmmm. *Maryam obam* [01/01, 13:31] Maryam Obam Group Kd: *JAWAHEER* *STORY AND WRITEEN BY......* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA* *(maryam Obam)* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝* *{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}* *wattpad @maryam-obam* *WWW.Maryamobamnovels.com* https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/ Page 3 A haka suka Isa gida yana fakawa ta fita da gudu tayi hanyar falo a hanya suka hadu da khalil tareta yayi yana fadin jawaheer kukan miye haka kufa kuka ci wasan kun cire madrid cikin kuka tace bros baka ga anji ma M samir ciwo ba, kallonta yayi na second biyar sannan yace kiyi hakuri kibar wannan kukan zai tashi a next wasa zaki ganshi dago kai tayi tace dagaske? Kai ya daga mata alaman eh yace dawa zaku buga next tace *CELTA DE VIGO* yace ok karki damu ki daina wannan kukan kabir na gefe yana kallonsu dakyar tayi shuru ta shiga ciki ido ya bita dashi yana tausayin kanwar tashi da yake ganin abun nata ya wuce tunaninshi dan shi dauka yake duk abunda take fada wasa ne amma yanzu abun ya fara bashi tsoro, kabir ne ya dafa shi tare da fadin kaga sis gaba daya hankalinta ya tashi, khalil yace ozil abun jawaheer ya fara bani tsoro fah kalla yanda take kuka dan kawai anjima M samir ciwo, kabir yace hakane amma jawaheer tana sonshi ne kaga duk abunda ya faru dashi dole taji wani iri ,khalil yace haba kabir irin wannan son yayi yawa kalla fah yanda tazo hankali tashe tana kuka, kabir yace kasan masoyi baya san ganin masoyinshi cikin wani hali, khalil tsaki yayi tare da fadin wlh abun yana ban mamaki in banda jawaheer ita da take Nigeria yar Africa ina ita ina wani bature wanda ko mutuwa za tayi bazai iya cewa yana sonta ba balle yace zai aureta haba aishi nasan bazai iya bama ace celebrity ya auri yar africa yar nigeria kuma gashi bature impossible abun kunya ne a gareshi, kawai dai sis na son daura ma kanta abunda yafi karfinta ne kawai, kabir yace haba khalil miye abun kunya a cikin SO wlh so ya wuce duk yanda kake tunani shifa so babu ruwanshi da addini launin fata, ka duba ka gani musulmi yake auran christen sannan turawa nawa ne suke auran yan africa..... Khalil ne ya dakatar dashi tare da fadin inma bature ya auri yar africa toni ban taba gani ba mutanan da suke kyamar bakar fata duk da jawaheer fara ce ita yar africa ce kuma idan suka tashi jam'u zasuyi suce bakar fata yan africa so kaga duk daya ne sannan shifa M samir duk duniya an sanshi sai kawai ace gashi yana auran yar Nigeria haba impossible mu ma bar wannan maganan kawai ,kabir yace bari kaji khalil abunda nake so ka fahimta shifa so babu ruwanshi sai kaga namiji handsome amma idan kaga matarshi sai kaji wani iri dan muni, haka sai kaga mace mai kyau amma mijinta mummuna kaman a yanka shi a boye wukan dan muni, toh kaga shi so babu ruwanshi da launin fata kyau muni kawai idan zuciya taji ta kamu toh babu ruwan mutum da duk abunda wani zaice, khalil murmushi yayi kawai tare da fadin kasan waye M samir kuwa world celebrity ne wanda ganinshi kawai tashin hankali ne sannan idan ya fito mutane zagayeshi sukeyi tako ina duk da yawan security din da suke zagaye dashi ko kasan yawan billions din da yake samu duk month banda na business dinshi da ake mai? Kabir ka daina yaudaran kanka wlh M samir yafi karfin jawaheer duk da jawaheer babu namijin da zai ganta baiyi burin auranta ba ,amma farin fata bature bazai auri jawaheer ba dan turawa suna kyaman mu sosai, kabir yace hmm khalil M samir musulmi ne bana tunanin zai kyamaci musulmai koda kuwa yan africa ne.... Khalil yace kai ni maganan nan ta isheni muje ka raka ni,kabir yace yunwa nake ji wlh ka bari inje ciki inci food din mum sai mu fita khalil tsaki ya danyi tare da fadin kazo muje mana ba dadewa zanyi ba haka kabir ya bishi suka fita tare. Koda jawaheer ta shiga cikin falon gidan taga mum dinta da dad da gudu ta fada jikin dad din nata tana kuka cikin damuwa iyayen nata suke tambayanta ko lfya mai aka mata? Cikin kuka tace dad anjima M samir ciwo mum tsaki tayi tare da kawar dakai daka kallonsu da takeyi dan tasha ko wani abu aka mata da farko ashe shirmenta ne data saba dan haka mum take daukan duk wani abu nata indai akan M samir ne, dad ya kalli mum yace haba bilkisu mai yasa kike irin haka kina ganin yarinya ta shigo cikin wannan halin sai ki dinga sakar mata tsaki ,tace toh mai zance? Indai akan wannan shirmen ne na jawaheer bani da abun cewa sai dai tsakin yarinya kullum bata da aiki sai fadin M samir M samir haba dan Allah ,jawaheer jin haka yasa ta kara fashewa da kuka dad yace yakuri J ki kyale mum dinki sannan M samir zai tashi insha Allah cikin shagwaba tace dad dagaske? Kai ya daga ya kuma cewa insha Allah, hawayen fuskanta ta goge tare da fadin dad dan Allah yaushe zaka hadani dashi? Murmushi yayi tare da fadin Ambassador dinmu na kasar Spain bashi da lafiya yana asibiti munyi magana idan ya warke zai fadamin sai ya hadaku dariya ta saki tare da fadin kai dad ina sonka sosai dad idan ya ganni zaiji yana sona kuwa? Mum tsaki tayi ta tashi tabar wajan dan takaici shiko dad ci gaba yayi da sauraran yar tashi yace sosai kuwa ai nasan idan ya ganki saiya rude sosai dan babu wanda zaiga my daughter yace bata mai kyau ba ,jawaheer cikin jin dadi tace dad kaga idan muka hadu ina gama skul sai ayi bikin mu koh?dariya dad yayi yace duk yanda kika tsara hakan za'ayi tashi dad yayi tare da fadin bari in fita ina da meeting karfe 6 kice ma mum dinki na fita tace ok dad take care yace i will my dear fita yayi ita kuma ta nufi dakin mum din nata ,a zaune taga mum tayi tagumi jawaheer tace mum lfya kuwa? Mum ta sauke ajiyan zuciya tare da fadin yauwa zo nan ki zauna bayan jawaheer ta zauna kusa da mum take cewa dad yace in fada miki ya fita,kai mum ta daga alaman toh, sannan ta kalli yar tata tace jawaheer wai yaushe zaki gane kin girma ne? Yaushe zaki farka daka wannan mahaukacin mafarkin da kikeyi ne? Shifa wannan mutumin da kike hauka a kanshi bai sanki ba yau ki duba shekarunki ishirin a duniya amma baki da saurayi tsayayye duk masu sonki in sunzo sai ki koresu yaushe zaki fahimci cewa shi wanda kike hauka a kansa bazai iya auranki ba..... Kukan jawaheer din ne yasa mum yin shiru tana kallonta cikin kuka tace mum ba mafarki nakeyi ba Mum kema kin san M samir gaskiya ne yana cikin duniyar mu kinga mum shiba mafarki bane mum bana jin zan iya auran ko wani namiji inba M samir ba wlh mum shi nake so inama zan iya nunama duniya zuciya ta taga irin son da nake mishi mum ko kin san idan ban sami M samir ba zaku iya rasani mum wlh ina cikin hayyacina tsantsar sonshi ne yasa nake duk wannan abun mum ki fahimce ni..... Salati mum ta saki tare da fadin nashiga uku wlh jawaheer kin samu tabin kwakwalwa..... Tace mum lafiya na qalau babu abunda ya sami kwakwalwa na ,mum cikin tausayi tace inko babu abunda ya sami kwakwalwanki toh wlh kinyi gamo ne cikin biyun nan dole akwai daya ban taba ganin irin wannan masifan ba dan Allah jawaheer ki cire wannan abun indai kina so in tabbatar da kina cikin hankalinki, kuka jawaheer ta kuma saki tare da fadin mum nayi kokarin inyi hakan amma na kasa mum idan ban auri M samir ba mum bana tunanin iya ci gaba da rayuwa na mari mum ta sakar mata ji kake tas....... *comment dinku yana min kadan sannan plz sharhi nake bukata ba thx ba dan yana da matukar amfani* *maryam obam* [02/01, 14:23] Maryam Obam Group Kd: *JAWAHEER* *STORY AND WRITEEN BY......* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA* *(maryam Obam)* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝* *{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}* *wattpad @maryam-obam* *WWW.Maryamobamnovels.com* https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/ Page 4 Rike wajan tayi tana hawaye mum tace jawaheer ki farka daka wannan mafarkin da bazai taba zama gskya ba, keba yarinya bace ki daina yaudaran kanki kuka mum ta saki itama ta fara magana cikin sanyin murya tare da sigar rarrashi tace jawaheer ke daya ce y'ata mace ina sonki fiye da yanda kike tunani bana son duk wani abu da zai saki cikin damuwa koya taba lafiyanki nafi kowa son inga yau kin sami abunda kike so amma wannan abunda kike so bamai yihuwa bane dan Allah jawaheer ki cire wannan kwallon a ranki da shi dan kwallon da kike so ki nutsu ki fitar da miji cikin manemanki kiyi aure idan kikayi aure hankalinki zai kwanta zaki manta da wani M samir, kai jawaheer ta fara girgizawa tare da fadin kiyi hakuri mum inama zan iya hakan da nayi farin ciki Allah ya sakamin son M samir bana iya ganin zan iya rayuwa da wani namiji inba shiba mum ki fahimce ni ban taba kin duk wani abu da kika fadamin ba wannan yafi karfina ne son M samir a jini na yake wlh mum Allah shine daya koh toh idan ban sami M samir ba zan iya mutuwa tana fadin haka ta tashi tabar dakin mum din nata da gudu tana kuka itama mum din kuka ta saki tare da fadin wlh jawaheer tayi gamo dole insa ayi mata addu'a na shiga uku wannan wani irin bala'i ne ita kuma irin tata jarabawan kenan son bature wanda suke kyamar yan africa suke kiran yan africa animals mum daukan wayanta tayi ta kira maman kabir hjy hauwa, bayan ta dauka suka gaisa hjy hauwa tace bilkisu lfya kuwa naji muryanki kaman kina cikin damuwa? Tace hmmm hauwa kedai bari kawai wlh jawaheer tana son sani cikin damuwa maganan nan bata waya bace kina gida yanzu in shigo? Hjy hauwa tace ina nan ki bari bari ni inzo mum tace toh sai kin shigo ina dakina in kinzo hjy hauwa ta amsa da toh sannan suka kashe wayan. Basu dade dayin sallama ba hjy hauwa ta shigo gidan, da sallama ta shigo dakin mum, mum ta nuna mata waje tare da fadin bismillah ga waje nan, bayan hjy hauwa ta zauna mum tace hmmm hauwa ina cikin damuwa sosai, hauwa tace mai yake faruwa bilkisu kimin bayani nan mum ta fara bama hjy hauwa labari irin abubuwan da jawaheer takeyi itama hjy hauwa salati tayi tare da fadin ikon Allah wannan wani irin sabon al'amari ne haka? Mum tace wlh kema kya fada yarinya kaman wacce tayi gamo da aljanu, hjy hauwa tace gskya nima ina tunanin haka domin inba aljanu ba babu abunda zaisa ta dinga tunanin haka Allah sarki jawaheer ,mum tace toni yanzu miye mafita? Hjy hauwa tace mafita daya shine mu kaita wajan malami ya mata ruqiya kin san akwai *BAQIN ALJANI* *sunan novel dina* da basa bayyana sai suyi tasa mutum yaita abu kaman hauka ko su hana mutum aure duk yanda akayi jawaheer tana tare dasu inko ba haka ba ai ba zata kamu da son wanda bata taba gani ba bata da tabbacin ma zai aureta ,mum tace oh ni bilkisu na shiga uku ,wlh da walaki dan jawaheer da ba haka take ba tama tsani kwallon kafa amma lokaci daya yarinya ta birkice, yanzu yaushe zamu wajan malamin? Hjy hauwa tace bari in kirashi inji yaushe yake nan, doka mai kira tayi ringing uku ya dauka bayan sun gaisa tace mlm dan Allah yaushe kake nan akwai yarinyar kawata da take da matsalan jinnu inaso mu kawota koh Allah zai sa a dace, ban san mai yace mata ba naji tace toh Allah ya kaimu sannan sukai sallama, kallon mum tayi tace yace gobe da karfe hudu mu sameshi a islamiya sannan tare da jawaheer din zamu ,mum tace Allah ya kaimu, hjy hauwa tace ameen wannan abu sai an hada da addu'a, mum tace kedai bari wlh idan kika shiga dakinta gaba daya hotan dan kwallon kafa dinne duk ta manne shi dashi sai kace abun hauka harta cup din da take amfani dashi na kwallon kafa ne duk an manna hotan yaron a jiki rannan tiles din dakinta naji tana fadin zata sa a saka mata mai hotanshi wai a cire mata na dakinta dakyar na hanata sai carpet tasa ta rufe tiles din carpet dinma mai hotan yaron, hjy hauwa tace ikon Allah jawaheer ita tata jarabawan kenan Allah sarki yarinya mai nutsuwa amma lokaci daya ta canza kiyi hKuri insha Allah gobe idan mukaje wajan mlm komai zai zo da sauki insha Allah, tashi hjy hauwa tayi tare da fadin bari in koma gida dare yayi mum tace toh ngd sai goben fita hjy hauwa tayi Bata dade da fita ba khalil ya shigo dakin yana fadin mum ina jawaheer naje dakinta inata nocking naji shuru gashi tasa key a dakin kota fita ne? Mum tace hmmm tana ciki babu inda taje ya wuce tana can tana tunanin shirmen banzan ta data saba,khalil yace kai sis rigima dazu muka gamayi da ita wai anji mishi ciwo shine tazo tana kuka wlh mum abun sis ya fara bani tsoro fah ,nasha wasa takeyi amma naga ita dagaske takeyi ashe, anya mum ba zamu kai autarki asibitin kwakwalwa ba, hararanshi mum tayi tare da fadin ai duk kune kuka sata fara kallon wannan shirmen dariya yayi tare da fadin babu ruwana mum tunda bani nace ta kalla ba ita ta kawo kanta harta fara kallo gashi yanzu ta fini zagewa, mum ajiyan zuciya tayi tare da fadin Allah ya kyauta ya amsa da fadin ameen sannan ya tashi yana fadin mum inaso inje dubai cikin week din nan gskya, mum tace mai zaka jeyi? Dariya yayi ya fara tafiya yace indan huta mana na gaji da zama waje daya, mum tace matsalanka ce wannan tunda ga office an baka kaki zuwa kullum kafi son kaita zama gida yau baka can gobe baka can, dariya kawai yayi sannan ya fita. Jawaheer tunda ta shiga daki ta rufe take ta faman aikin kuka a kasa ta kwanta akan hotan M samir tana shafa wajan fuskanshi tana fadin nasan zaka soni kaman yanda nake sonka inaji a jiki na, zanzo gareka very soon inaso ka nuna ma mum lafiya na qalau kawai sonka ne yamin yawa kazo ka aureni ka nuna ma mum baka fi karfina ba ni nasan kaine zaka aureni kazo kaba mum mamaki kaji my luv kuka ta kara saki tare da furta ina sonka sosai nasan yanzu kana cikin wani hali na ciwo amma Allah zai baka lfya inajin zafin jin ciwonka har cikin raina........ Hmmm ku biyoni muga yanda zata kaya da jawaheer a wajan mlm shin zama ta yarda taje kuwa? Dagaske aljanu gareta kaman yanda mum tace duk ku biyoni ... *maryam obam* [03/01, 16:47] Maryam Obam Group Kd: *JAWAHEER* *STORY AND WRITEEN BY......* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA* *(maryam Obam)* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝* *{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}* *wattpad @maryam-obam* *WWW.Maryamobamnovels.com* https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/ *DEDICATED TO.....* *Nafisa mrs dan malikin kawo* Page 5 KASAR SPAIN M samir tunda aka fitar dashi daka filin kwallo aka nufi hospital dashi domin ba karamin faduwa yayi ba, koda aka nufi asabiti dashi hannunshi na rike da kafarshi yana cije baki, gocewan kashi yayi an kaishi asibiti kafin ace me har an gyara kafan nan labari ya bazu na ciwon da yaji inda masoyanshi keta jimami koda dad dinshi yazo hspt din cikin tashin hankali amma ganin yaron nashi a zaune yana waya yasa hankalinshi yadan kwanta saida ya gama wayan sannan ya kalli dad din nashi yana dan murmushi tare da fadin dad yakake dad din ya amsa da fadin my son ya kafan naka da fatan dai baka jin zafi sosai kai ya daga alaman eh duk cikin yaren spanish suke maganan, kallonshi dad din yayi sannan yace my son dawa kake waya haka? Ko wacece nasan soyayya kukeyi, dan murmushi yayi sannan yace sunanta sonia yar england ce ba kowa yasan muna soyayya ba sai yasa ba'a baza labarin ba, fuska mahaifinshi ya tamke sannan yace my son ka rabu da ita kasan bana son ka auri wacce ba musulma ba, M samir ya kalli mahaifin nashi sannan yace dad miye dalilinka bayan kasan addini na bai haramta min auran wacce ba musulma ba, baka tunanin jahadi zanyi idan na aureta tayu ta musulunta, kai dad din nashi ya girgiza alaman bazaka gane ba, sannan yace my son kasan kai fitaccene a duniya u r d world biggest celebrity zanso ace ka auri musulma domin duniya tasan kana kishin addininka ka duba ka gani yawanci celebrity musulmai basa auran musulma yawancinsu na rasa miye dalili sannan idan suka auri wacce ba musulma ba tarbiyan yaransu yakan banbanta kai yanzu da kake son auren yar england koh kasan yau idan kuka rabu yaran da kuka haifa sun zama nata? Sannan kasan daka ranan da suka koma gareta addininta za suyi kaga baka da ikon hana su, amma in musulma ce koda yar kasar england dince idan kuka rabu yaranka a wajanka zasu zauna duk da ka'idan kasarsu ce haka mace keda iko da yara amma su musulmai a wajansu ba haka bane tunda ba haka addininmu yace ba ,namiji shine shugaba ba mace ba, m samir murmushi yayi tare da girgiza kai yace dad duk da haka bana tunanin zan iya fasa auren sonia muna son junanmu and tunda tana sona duk wani abu da nace shi za tayi, dad murmushi yayi tare da fadin ba zaka fahimta ba har yanzu kai yaro ne, m samir dariya yayi tare da fadin dad next month zan cika 28 fah shima dad din dariya yayi tare da fadin koda 40 ka kai a matsayin yaro nake kallonka..... Shigowan dr ne yasa firan nasu ya tsaya dr yace ya kafan? Amsawa yayi da fadin ban san mai zance ba inajin zafi sosai ,dr yace kayi hakuri zai rage, kai ya daga alaman yaji, dr yace ga press nan da yawa suna son sanin halinda kake ciki ko zan iya fada musu halin da kake ciki? Yace miko min phone dinka bashi dr din yayi ya shiga wajan recording ya fara magana cikin harshen turanci tunda sako ne yake son bayarwa ga duniya baki daya musamman ma masoyanshi..... Ina lafiya ina kira ga masoya na da suyi hakuri nan bada dadewa ba zasu ganni, amma yanzu ina bukatan addu'a daka garegu ngd yana fadin haka yasa stop tare dayin saving ya mika ma dr din wayanshi tare da fadin kaba yan jarida din, dr din cikin jin dadi ya fita domin wannan maganan da yayi a wayanshi ba karamin kudi zai samu ba dan saida ma yan jarida zaiyi. NIGERIA ABUJA washe gari bayan jawaheer ta tashi bata fito daka daki ba ganin har 11 yayi bata fito ba yasa dad dinta ya nufi dakinta amma a rufe saida ya kira sunanta sannan ta tashi tazo ta bude mai kofar, rungumeshi tayi tana kuka tare da fadin dad dazu naji a news M samir ya sami gocewan kashi dad dan Allah ka kaini spain in ganshi ko zanji dan sauki, dad cikin tausayin y'ar tashi ya dagota daka jikinshi yana share mata hawayen fuskanta yace kiyi hakuri jawaheer ki daina wannan kukan nayi miki alkawarin hadaki dashi indai Ambassador kasar spain na nigeria ya warke, cikin kuka tace dad koba ta hanyar ambassador ba zaka iya hadamu plz dad do something ni daya nasan mai nake ji a cikin raina dad yace shikenan my dear zansa a mana visa na kasar spain zamu tafi cikin week din nan cikin jin dadi tace i luv u dad, dariya yayi tare da fadin muje kici abinci toh ,binshi tayi suka nufi dinning zama sukayi dad da kanshi ya zuba mata abinci ta fara ci mum ta fito tagansu ta tabe baki tare da fadin Allah ya baki lfya jawaheer dad yace bata jin dadi ne? Mum tace a'a ina nufin lafiyan wannan sabon haukan da yake son kamata, tamke fuska dad yayi tare da fadin kinga bilkisu ki dinga sanin abunda zaki dinga fada akan jawaheer bana son irin abubuwan da kike mata kina nunawa kaman baki damu da ita ba,mum tace Allah ya baku hakuri nayi shuru dad yace hakan shine alkhairi jawaheer na zaune tana jinsu lokaci daya kuma ta fada duniyar tunani gata a kasar spain sun hadu da M samir ya ganta ya rude harya furta mata kalman so ido ta lumshe cikin jin dadi a hankali ta furta i luv you too wanda bata san maganan ta fito ba jin mum dinta tayi tana fadin kaga abunda nake fadama koh wlh jawaheer tayi gamo da aljanu, ya kamata ka yarda da abunda nake fadama, dad baice komai ba illa kallon jawaheer din da yake tayi cikin tausayi duk cikin yaranshi yafi son jawaheer sai yasa komai ta kawo yake dauka harya biye mata amma a gskya wannan karan shima ya fara tunanin abubuwa da dama duk da dai baya son ya nuna mata ta gane, ganin irin kallon da dad dinta yake mata irin kallo na tuhuma yasa tabar wajan da sauri, mum hannu ta tafa tana fadin oh ni bilki naga takai na, yarinya sai tayi abu kaman mai aljanu anjima kuma tayi kaman mai tabin hankali, dad yace wlh bilkisu abunda kike ma jawaheer inda badan ke kika haifeta ba da sai ince kin tsaneta ne, akan me zaki dinga danganta ta da me aljanu ko tabin hankali duk wannan maganganun da kikeyi sam bai kamaceki ba ki daina ma y'ata irin wannan munanan alkaba'in bana so, shuru mum tayi bata kara cewa komai ba dad tashi yayi tare da fadin ni na tafi villa ina da meeting da shugaban kasa, mum tace Allah ya taimaka amma dan Allah kayi hakuri bana so ka fita kana fushi dani kaji my handsome, dariya dad yayi tare da fadin kin iya zolaya bilkisu ki ganni tsoho dani kice min wani handsome cikin dariya itama tace ai a haka kullum nake ganinka, fita yayi yana fadin bari in tafi 12 dai2 zamu fara tattaunawa, har yayi nisa mum tace anjima zamu fita nida jawaheer cikin jin dadi yace ko kefa ai yana dakyau ki dinga janta a jiki sosai sai kun dawo sannan akwai kudi a wardrobe din daki na in bakya bukatan taba naki ,yana fadin haka ya wuce. Karfe hudu dai2 mum ta nufi dakin jawaheer cikin shirinta ganin jawaheer tayi tana zaune tana kallon waya nufanta tayi tana fadin jawaheer kinyi sallah kuwa? Tace mum ina fashin sallah ai, mum tace ok toh maza ki tashi ki shirya zaki raka ni, tace mum kije kawai bana jin fita yau kaina na ciwo, mum tace haba jawaheer fitan nan danke zanyi fah, tace mum ina zamu? Mum tace kedai ki tashi ki shirya ban san dogon zance, bata fuska tayi tare da fadin wlh mum kaina ciwo yake dakin bari gobe mu fita ,mun tace kin san bana son shirme koh maza ki tashi kisa hijab muje, kallon mum tayi tace hijab kuma ina zamu haka? Kodai wani ne ya rasu? Mum tace babu wanda ya rasu kawai wajan da zamu ne bana bukatan ki bini saida hijab, badan taso ba ta shirya tare da saka hijab din, mota suka shiga mum tace jawaheer ta zauna a gaba, hjy hauwa zata zauna a baya ita da mum ,bayan sun shiga driver yaja gidan hjy hauwa suka biya suka dauketa sannan suka nufi islamiyyan, hjy hauwa tace driver yayi parking bayan ya tsaida motan suka fito amma banda jawaheer mum tace jawaheer ki fito mana bude motar tayi ta fito shiga islamiyyan sukayi inda aketa karatu wani office suka shiga suka zauna babu kowa a ciki jim kadan sai ga wani mutum yazo ba wani babba bane amma kana ganinshi kasan mlm ne dan irin shigan da yayi, gaisawa sukayi sannan hjy hauwa tace mlm ga kawata nan sannan ga yarinyar nan sai a sannan jawaheer ta dago ta kalli mlm din, mum tace mlm dan Allah a mata ruqiya domin aljanu ne nake tunanin suka shigeta, jawaheer da sauri ta kalli mum din nata ta fara hawaye tare da tashi tsaye...... *maryam obam* [04/01, 14:50] Maryam Obam Group Kd: *JAWAHEER* *STORY AND WRITEEN BY......* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA* *(maryam Obam)* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝* *{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}* *wattpad @maryam-obam* *WWW.Maryamobamnovels.com* https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/ *DEDICATED TO.....* *Nafisa mrs dan malikin kawo* Page 6 Ta kalli mum tace mum mai hakan ke nufi? Mum kallon aljanu kike min kuka ta saki mai karfi tare da fadin mum nifa lafiya na qalau bani da komai kaman yanda kike tunani kallon mlm din tayi tace mlm ka kalleni dakyau nayi kama damai aljanu ko tabin hankali? Matsowa tayi kusa da mlm ya danyi baya kadan tare da fadin auzubillah karki matso kusa dani haram, mum ta tashi ta rikota tare da fadin zoki zauna jawaheer kwace jikinta tayi daka na mum tace mum bazan iya zama ba, amma inaso mlm ya cire miki zargin da kike min yanzu, kallon mlm tayi da yayi shuru yana kallon ikon Allah, tace mlm mai zaka min ka nuna ma mum dina ni lafiya na qalau, mlm yayi gyaran murya tare da fadin da farko dai ki zauna zanyi miki yan tambayoyi kadan, zama tayi akan kujera tare da kallon mlm tace inaji, mlm yace ya sunanki? Tace jawaheer, kai ya daga alaman yaji yace kina mafarkin ruwa ko wani yana saduwa dake kai ta girgiza alaman a'a, yaci gaba da tambaya kina mafarkin gaki a daji ko kuma ana binki tace a'a, nan dai yaita mata tambayoyi tana bashi amsa harya gama ya dauko wani magani ya bata yace tasha, bata musa ba ta amsa tasha bayan ta shanye tace mlm shikenan? Yace eh an gama, tace mlm bari kaji wani abu kasan miye matsalata? Shuru yayi ba tare da yace mata komai ba tace mlm Allah ya jarabceni dason wani mutum wanda badan nan kasar bane dan kwallon kafa ne nasan zaka iya saninshi sunanshi M samir, mlm a kullum inna kwanta ina ganinshi yana kuka tare da fadamin yana da wata matsala amma idan abun ya fito kar in gujeshi duk wuya in zauna dashi sannan yamin zai aureni duk wuya yace in daure ni tashi ce, ban taba fadama kowa wannan ba kullum sonshi na karuwa a raina duk da a kullum ina kokarin in cireshi a raina amma na kasa, abun kaman kara karuwa yakeyi kullum tun bana iya fadama iyayena harna fara fada musu abunda ke cikin raina dady dina ya fahimceni amma ita mum dina ta kasa itace mahaifiyata ita ya kamata tafi kowa fahimta na tasan wani hali nake ciki ya nake ji, amma mum ta kasa fahimta na saita fara min kallon aljanu da tabin hankali wanda hakan yana batamin rai mum dina tana nesa dani wanda hakan yasa nafi sabawa da dad dina akan mum dina shuru tayi domin kukan da yazo mata lokaci daya, wajan yayi shuru na wajan second biyar sannan taci gaba da fadin kiyi hakuri mum ina fadin hakane dan kisan abunda yake damuna, ban taba soyayya ba sai akan M samir duk da bai san inayi ba, sometimes nakan so incire abun a rai na har inyi kokarin sauraran wasu amma na kasa, tashi tayi tace mlm nasan kai zaka iya fahimta na wlh bana tare da wani cuta illa ciwon so wanda nasan idan ban sami abunda nake soba zai iya zama ajalina, nasha kallo a fina finai irin abubuwan da so yake haifar wa dariya nakeyi ko ince karya ko hauka, domin ina tunanin hakan bazai taba faruwa da gaske ba, ashe ba haka bane, yau gashi abunda nake ma dariya nake ganin karya ne gashi ya faru a kaina har nima ana min kallon mara hankali, ni nasan wannan yana cikin jarabawan rayuwa na, mlm pls make my mum to understand dat i dnt have any jin tana fadin haka ta fita, duka da ido suka bita mum kasa magana tayi mlm yace hjy yarinyarki bata da aljanu kaman yanda kike zargi sannan bana tunanin tana da tabin hankali lafiyanta qalau, kawai tsabar son mutumin nan ne yasa mata take haka which kuma abunda na fahimta kaman bata da kawaye wanda take fada musu matsalanta ku take fadama wa amma dad dinta yana fahimta har yake biye mata amma ke kina nuna mata kaman ta sami tabuwa, kuma ita a nata ganin kune ya kamata kusan wani hali take ciki tunda kune iyayenta, hjy ya kamata ki dinga janta a jiki kina bata shawar wari wanda zata fahimta koda tana firan dan ball din da takeso ki daina nuna mata kyara hakan yakan sa yaro ya tsani kanshi yaga kaman iyayenshi sun tsaneshi yana da kyau ka maida danka abokinka ta yanda zaku dinga bama juna shawara jan yaro a jiki yana sa komai zaiyi saiya fadama iyayenshi sannan nunama yaro kyara yana sa ya dinga boye abubuwa da yawa wanda in ba'ayi wasa ba nan gaba za'ayi dana sani wanda ba'a fata, jikin mum yayi sanyi tace ngd mlm tabbas hakane jawaheer bata da kawa ko daya na tabbata inda tana da kawa da tare zasu dinga shawara rashin kawar ne yasa take fada mana ni kuma sai inki fahimta in dinka mata kallon hauka, mlm kasan ba komai iyaye suke dauka ba amma yanzu da naji maganan ka na fahimci komai yaronka ya fada maka koda shirme ne ka nuna masa kulawa akai, nan suka ma mlm godiya tare da bashi kudi yaki amsa yace dan Allah yayi baya bukatan kudi saida mum tace babu kyau maida hannun kyauta sannan ya amsa suka wuce, a mota suka sami jawaheer tana ta kuka, mum cikin tausayin yar tata suka karasa motar bayan sun shiga mum tace jawaheer kiyi hakuri kibar wannan kukan batai shuru ba har suka sauke hjy hauwa suka wuce bayan sun shiga gida da sauri jawaheer ta shiga gida tana kuka a falo taga dad dinta nufanshi tayi tana sauke ajiyan zuciya, cikin damuwa yake tambayanta mai aka mata? Bata bashi amsa ba sai kukan da take tayi mum ce ta shigo falon ganin dad yace bilkisu mai aka mata haka? Kodai wannan magan ganun naki kike ta fada mata? Hjy bilkisu cikin damuwa tace kayi hakuri da abunda zan fada maka yanzu inaso kamin adalci sannan ka fahimce ni, wlh nayi hakan ne dan ina zargi amma daka baya saina fahimci kuskurena, munje wajan wani mlm ne a islamiya domin ina zargin aljanu jawaheer take dasu, dad yace what? mum tace kayi hakuri ka gama saurara na shuru yayi amma fuskanshi a tamke nan mum ta bashi labarin abunda ya faru, dad baice komai ba sai kama hannun jawaheer da yayi yace tashi kije kiyi wanka kizo kici abinci sannan ki fara shiri jibi zamu tashi zuwa spain bata san lokacin data tashi ba dan murna lokaci daya kuma tace dad r u serious? murmushi yayi tare da fadin yes jawaheer bana daukan abunki da wasa komai naki inaso inyi miki yanda kike so hugging dad dinta tayi tare da furta u r d best dad in d world tana fadin haka ta nufi dakinta. Kallon mum dad yayi yace bilkisu na rasa mai yasa gaba daya kika canza bakya jin duk maganan dana fada miki, yanxu kinji dai abunda mlm din yace Allah yasa ki dauka kiyi amfani dashi, tace kayi hakuri insha Allah komai ya wuce sannan wannan abunda ya sami jawaheer na jarabawa zan kara dagewa wajan roqan Allah akan ya zaba mata mafi alkhairi a rayuwa, yace yauwa ko kefa, dan murmushi tayi tare da fadin kasan ita daya ce yarinya ta mace duk wannan abunda kaga inayi duk sonta yaja hakan tunda babu mai so yaga nashi ya shiga wani hali, dad yace hakane sai muyi ta addu'a sannan tare na mana visa harda ke zamu tafi jibi da khalil mum tace tafiyan family ne kenan gaba daya dariya dad yayi yace mun dade bamuyi irin tafiyan nan ba gaba dayan mu, tunda muka dawo daka saudiya bamu kara fita mu duka ba naso muje harda umar babban dansu kenan, amma yace shima zaiyi tafiya, mum tace Allah ya taimaka, ya amsa da ameen...... Toh jawaheer za'a spain koya zata kaya??? *maryam obam* [06/01, 01:05] Maryam Obam Group Kd: *JAWAHEER* *STORY AND WRITEEN BY......* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA* *(maryam Obam)* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝* *{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}* *wattpad @maryam-obam* *WWW.Maryamobamnovels.com* https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/ *DEDICATED TO.....* *Nafisa mrs dan malikin kawo* Page 7 Jawaheer shiri take sosai domin tafiya spain ko abinci bata iya samu taci dan murna sai dad yayi dagaske take ci, kaman yanda dad yace jibi zasu tafi hakan ta faru domin dai rana bata karya inji masu iya magana, yau jirginsu ya daga zuwa kasar spain..... Su jawaheer an sauka a kasar spain tunda suka sauka ta lumshe ido tana jin wani irin nishadi tare da farin ciki sai take ganin kaman gata ga M samir nan, wata katuwar mota ce taxo ta daukesu da kayansu wani gida suka nufa gidan sama, bayan sun karasa gidan suka shiga komai na gidan an rufe da farin kyalle saboda kura cirewa sukayi suka zauna a kujeran falon, hjy bilkisu ta kalli mijin nata tace wannan gidan fah nadai san baka da gida a kasar nan, murmushi yayi tare da fadin saboda jawaheer na siya, munyi waya da ambassador akan ina son gida a kasar nan shine ya hadani da wani kin san shi yana asibiti, toh wannan gidan ma mutumin yace nayi sa'a harta yan kasar sun kasa siyan gidan dan yayi kudi da yawa, mum tace ah lallai kam ai dole dan gidan ya hadu gskya duk da banga ko ina ba, jawaheer ta tashi tare da fadin bari inga gidan khalil shima binta yayi nan sukai ta zagaya gidan wanda yasha kayan more rayuwa ga gidan kato a kalla dakuna sun kai bakwai a gidan, mum tace ma dad naga su turawa basa irin gida haka babba, yin katon gida sai balarawa, dad yace suma yanzu turawan sun fara, jawaheer ce ta fito daka wani daki tana fadin dad ni wannan ne dakina na riga na zaba, dad yace ok dear duk inda ya miki nan zaki dauka, khalil yace dad ya kamata a bata daki a kasa ne, kafin dad yayi magana ta amshe da fadin sai kace namiji zan zauna a kasa dad shi zai zauna a kasa ya dinga gadi yaga masu shiga da fita, khalil yace ni din zan zama mai gadin nufota yayi da nufin ya kamota ta fara gudu shima yana binta dad da mum dai dariya sukayi mum tace kuna jin karfin jikinku ne sai yasa kuke ta wannan gudun, saida suka gaji dan kansu suka zauna suna maida numfashi, dad waya yayi aka kawo musu abinci tare da masu aiki biyu turawa duk ta hanyar mutumin da ambassador ya hadasu dashi, saida suka huta sannan alhaji jibrin mai dala ya shirya dan zuwa duba ambassador a asibiti, harda su mum da jawaheer jawaheer tayi shigan riga da wando sai tasa boyfriend jacket akai mai tsawo tare da yafa karamin gyale a kanta ta nada shi kaman hijab, duk da batai makeup ba tayi kyau sosai, cikin wata sabuwar jeep suka shiga nan driver yaja su suka nufi hspt din, kafin su shiga dakin da ambassador yake saida aka basu wani kaya suka daura akan nasu domin haka ka'idan asibitin yake, bayan sun shiga suka sami ambassador yana jin jiki duk da yana dauriya amma kana kallonshi kasan ciwo nacin shi, alhaji jibrin mai dala yace sannu ambassador ya jikin ya amsa da fadin da sauki alhmdlh, nan suma su jawaheer suka gaidashi ya amsa da fadin jikin alhamdlh, alh jibrin yace dama haka kake jin jiki? Ambassador yace ai jiki yayi sauki ma sosai akan da, cikin tausayi alh jibrin yake kara fadin Allah ya kara ma lfya, ambassador yace ameen, amma lfya kuwa PA dina yace kana ta kira cikin damuwa? Alh jibrin yace ah a ka barshi kawai inka warke mayi magana, ambassador yace haba haba ka fadi mana kai ka sani koh zan tashi, alh jibrin yace zaka tashi mana insha Allah, dama akan maganan dan kwallon kafa din nanne M samir wlh kaga yarinya ta ga tanan ya nuna jawaheer wacce tayi tsuru tana sauraransu, ita take son ganinshi, ta hanamu sukuni, ambassador yayi shuru yana ji har alhji jibrin ya gama sannan ya sauke ajiyan zuciya tare da fadin babban magana, alh jibrin yace kaman ya? Ambassador yace gsky ganin M samir yana da matukar wuya kaman a nigeria ne talaka yace yana son ganin shugaban kasa kaga hakan bamai yuhuwa bane a garesa, inaga kaman ma wannan zaifi sauki, domin M samir yana daya daka cikin matasa masu kudin duniya ganinshi zaiyi matukar wuya dama wani ne daka cikin yan kwallon dana hadasu, sai dai ta ganshi in za suyi wasa a cikin fili, jawaheer fita tayi da sauri tana kuka tare da fadin shikenan bazata sami ganin M samir ba shikenan burinta da mafarkinta zai zama karya kenan mota ta shiga ta zauna tana ta rusgan kuka driver din da aka hadasu yana ta kallonta ta mirror cikin tausayi, gashi babu daman ya tambayeta ko lfya, Haka su dad suka shigo motar suka sameta tana ta rusgan kuka, nan dad ya fara aikin rarrashi amma kaman kara zugata yake dan haka ya barta in sunje gida ya rarrasheta dakyau, koda suka isa gida fita tayi tana kukan dukansu suna tausaya mata musamman dad, zata wuce daki khalil ya rikota yana fadin haba lil sis mai yasa zaki sa kanki cikin damuwa haka? Cikin kuka tace bakaji abunda ambassador yace ba tunda ambassador bazai iya hadani dashi ba bana tunanin zan iya ganinshi tako wani hanya, shikenan komai nawa ya tsaya, bazan sami cikan burina ba bros ina son M samir a kullum da burin ganinshi nake kwana nake tashi indai ganinshi zaiyi wuya har haka kenan mafarki na ya zama karya..... Kasa tayi tana kuka cikin tausayi dad ya matso kusa da ita yace jawaheer kiyi hakuri insha Allah na miki alkawarin ganinshi tako wace hanya, kai ta girgiza tare da fadin dad baka ji abunda ambassador yace ba gwara in koma nigeria in nemi ganin shugaban qasa zaifi min sauki akan ince ina son ganin M samir, dad bana tunanin zanyi tsawon rai domin duka tunani na da jini na yana tafiya da M samir a kullum, zuciyata tana bugawa da tunaninshi dad in har ganinshi zai zama wahala a gareni miye amfanin rayuwa na? Ganin kowa yayi shuru yana kallonta yasa ta danyi murmushi wanda ake cewa yafi kuka ciwo tace dad nasan kuna min kallon rashin hankali ko wani abu makamancin haka, nasan koda kai bakamin mum tana min, amma abunda nake son ku fahimta shifa so ba karya bane wlh da ana cire abu a rai da tun tuni na cire shi na huta amma Allah ne yasa min sonshi wanda nasan shine kaddarata Allah yamin komai na rayuwa ban rasa komai ba komai nake so ina samu amma abu daya ya gagareni samu shine farin ciki na wato M samir, na yarda Allah baya bama bawa komai dole saiya jarabceka, wasu Allah kan basu dukiya da komai sai ya hanasu haiyuwa wasu kuma sai suzo a talaka abinci ma dakyar suke samu amma sai Allah ya azurtasu da haiyuwa lallai babu yanda Allah bayayi lumshe ido tayi wanda ya kada yayi ja, tace dad bana son zama a kasar nan inaso mubar nan da gaggawa nasan bazan iya cire M samir ba amma zan koma kasata inje inyi ta jinyar zuciyata har lokacin mutuwa na yayi...... Hmmm muje zuwa *maryam obam* [08/01, 17:32] Maryam Obam Group Kd: *JAWAHEER* *STORY AND WRITEEN BY......* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA* *(maryam Obam)* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝* *{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}* *wattpad @maryam-obam* *WWW.Maryamobamnovels.com* https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/ *DEDICATED TO.....* *Nafisa mrs dan malikin kawo* Page 8 Shuru tayi tana kuka.. Mum ta matso kusa da ita tare da rungumota tace kiyi hakuri jawaheer tun farko abunda nake so ki fahimta kenan amma yanzu alhmdlh tunda kin fahimta, ba komai bawa yake soba yake samu a rayuwa duk kudinka duk gatanka akwai abunda yafi karfinka, sannan Allah yakan jarabci bayinsa ta hanya da dama idan kayi hakuri sai ya zama hala silan shiga aljannanka, nasan abunda kikeji jawaheer amma inaso kiyi tawakkali kiyi kokarin cire M samir da tunaninshi a ranki duk da nasan ba abu mai sauki bane gareki, amma ki gwada kiba wani chance ya shigo rayuwanki zaki rage duk tunanin M samir,...... Murmushi tayi wanda ake cema yafi kuka ciwo tace mum bana tunanin zan iya hakan domin son M samir a jini na yake bana tunanin zan daina sonshi har sai ranan dana daina numfashi.... Mum tace jawaheer ki gwada bama wani dama zaki manta dashi ...... Tace shikenan mum zan gwada tana fadin haka tayi dakinta ta kwanta tana kuka. Dad ya kalli mum tare da fadin miye mafita? Mum tace mafita daya shine mu koma nigeria ka zaba mata wani ta aura zata cire duk son wannan mutumin da nasan bazai taba auranta ba, dad shuru yayi can ya nisa yace Allah kasa mu dace, duka suka amsa da ameen khalil shima dakinshi ya shige haka su mum. Jawaheer tunda ta shiga daki take kuka har bacci ya dauketa,cikin baccin ne tayi mafarki...... Gata da M samir cikin wani garden wanda an saka kujeru da shape din heart kallonta yake tayi yana mata murmushi lokaci daya kuma ya tamke yace mai yasa kinzo kusa dani kike son ki kara yin nesa dani? Ko kin daina so nane? Tana kokarin yi mishi magana ya tashi cikin fushi yayi gaba tashi tayi tana binshi da sauri tana kokarin ta bashi hakuri amma yayi mata nisa, farkawa tayi duk tayi zufa sai faman sauke ajiyan zuciya take lokaci daya kuma tasa kuka tare da fadin bazan tafi ba bazan bar kasar nan ba har sai na ganka kaman yanda kake bukata cikin kuka take fadin Allah ka nuna min M samir da gaggawa Allah ka tausayamin badan halina ba, Allah kasan ina son wannan bawan naka tsakani da Allah, Allah ka tausayamin koda bazai aureni ba Allah ka nunamin shi a zahiri kuka ta kara saki mai karfi. Kwanan su jawaheer biyar a spain bata fita ko ina, kullum tana gida tana kuka tare da roqan Allah ya nuna mata M samir in alkhairi ne a rayuwanta dad yace su shirya jibi zasu tafi dama sati daya za suyi, jawaheer tace dad babu inda zani, dad yace kaman ya? Tace dad sai naga M samir zan bar kasar nan, mum ji tayi kaman an daba mata wuka dan takaici cikin damuwa tace haba jawaheer kece fa kika ce mubar kasar nan sai yasa mukace sati daya kawai za muyi dan Allah kiyi hakuri kizo mu koma zamanki a nan baida wani fa'ida domin babu abunda zai kara miki inba takaici da bakin ciki ba, jawaheer ki taimaki rayuwanki tare da namu kibar wannan mutumin munfi kowa kaunarki ke bakya tunanin halinda muke shiga idan muka ganki cikin damuwa haba jawaheer ko so kike ki kashe mu da naki damuwan? Kuka jawaheer ta fara tare da fadin kiyi hakuri mum nima bada son raina nake haka ba, wlh mum zuciya tane take sani aikata duk wannan abun nasan kuna sona fiye da tunani na sai yasa kuke hakuri da duk wani abun dana kawo kuke dauka mum kodan farin cikin ku zanyi kokari in manta da komai amma dan Allah ku tafi ku barni a nan na wata daya nayi alkawarin in banga M samir ba wlh zan dawo sannan inaso inna dawo ku bani auren duk namijin da kuka zaba min, zan rungumi kaddarata nayi alkawari mum, wani guntun hawaye ne ya silalo a fuskan mum na tausayin yar tata inama tana da hanyar ganin M samir dayau saita sada yarta dashi kodan tayi farin ciki lokaci daya kuma ta rungumeta tana shafa mata baya tare da fadin kiyi hakuri jawaheer ni mahaifiyarki ce bana son ganin damuwanki duk kankantansa sai yasa wani lokacin nake miki abu wani iri amma badan bana kaunarki bane a'ah duk saboda kar kisa kanki cikin damuwa bana so ki zauna a kasar nan ke daya, jawaheer ke mace ce kuma kina da rauni bawai ban yarda dake bane a'a tarbiya ya zama abunda ya zama sai yasa naki yarda ki fita karatu waje nace ki zauna a abuja kiyi inkin gama ki dawo gida, dan Allah jawaheer kiji tausayina ki bimu jibi mu koma tare badan niba, cikin kuka tace mum baki taba tambayana abu na kasayi miki shiba a rayuwa ko inyi miki musu, amma wannan karan kiyi hakuri mun bazan biku ba M samir ya fadamin kar inyi nesa dashi in zauna..... Mum salati tayi cikin kuka tace a ina kika hadu dashi harya fada miki hakan? Tace cikin mafarki na mum yayi fushi dani saboda nace zan bar kasar nan, mum tace jawaheer anya lafiyanki qalau kuwa? Yanzu ke mafarkin ne kike yarda dashi? Murmushi jawaheer tayi tare da fadin mum nasan mafarki ba gaskiya bane amma akwai wanda yake zama gaskiya wannan mafarkin da nayi inaji a jikina gaskiya ne shima yana jin wani abu a tare dani, cikin takaici mum tace dan Allah tashi ki bani waje sannan wlh jibi dake zamu tafi kinji na rantse dakinta ta nufa tana kuka. Wata baturiya ce ta fito daka cikin jirgi kallo daya zaka mata ka gane tana da kyau sosai bata da tsawo sosai tasa riga da wando fuskanta tasa glass kanta tasa brown attachment jan dan karamin akwatinta take har wajan da taga wani ya rike abu mai sunanta SONIA alaman ita yazo dauka cikin harshen turanci tace mishi hi am sonia yace mata ok nan suka nufi inda aka faka mota ya bude mata ta shiga direct asibiti suka nufa, wani daki ya nuna mata ta shiga tana budewa taga M samir a ciki yana zaune shi daya yana duba wayanshi da sauri ta nufeshi tayi hugging dinshi tare da fadin nayi missing dinka ya jikinka, lolaci daya kuma tasa kuka dagota yayi yaja mata hanci tare da fadin bana son kukanki naji sauki dana ganki saina kara samun lfya so stop crying kin san bana san ganinki cikin damuwa dan murmushi tayi tare dasa bakinta cikin nashi tayi kissing dinshi na wajan minti daya sannan ta sakeshi tace i really miss u murmushi yayi tare da fadin i miss u too inga tunda kin zo zan koma gida saiki dinga kula dani kai ta girgiza tare da fadin babu inda zaka sai abunda dr yace cikin dariya yace i luv you so much baby u r my happiness, manneshi tayi a jikinshi dad dinshi ne ya shigo dakin kallo daya ya musu yaji tsanar yarinyar ....... No editing kuyi hakuri da typing error😀 *maryam obam* [09/01, 21:41] Maryam Obam Group Kd: *JAWAHEER* *STORY AND WRITEEN BY......* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA* *(maryam Obam)* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝* *{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}* *wattpad @maryam-obam* *WWW.Maryamobamnovels.com* https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/ *DEDICATED TO.....* *Nafisa mrs dan malikin kawo* Page 9 Sonia tana ganin dad din M samir ta ganeshi dan ta sanshi a hoto, mika mai hannu tayi shima bata yayi sannan tace hi am sonia from england am samir girl i know dat he told u about me but iz good to introduce by my self, dad din tsayawa yayi yana kallonta duk da bawai ya dauki hakan da wani abu bane dan turawa ne su sun saba ganin fiye da haka amma shi mahaifin m samir musulmi ne kuma yana kishin addininsa sai yasa baya sha'awan ya auri wacce ba musulma ba, abun takaici ma ita wannan gata ba musulma ba kuma yar kasar england dad din fita yayi tare da fadin ni na tafi sai zuwa anjima, dad bai dade da fita ba dr ya shigo ya duba shi m samir yace yana son tafiya gida dr yace ya bari gobe sai ya tafi gidan dan yau za'a cire mai abunda aka samai a kafa, kai ya daga alaman ok, bayan fitan dr sonia ta kalli m samir tace mai yake damun dad dinka ko bashi da lafiya ne? Yace maita gani? Dan murmushi tayi tare da fadin naga ina mishi magana ya daure fuska kaman baya so na? M samir dariya yayi yace ba haka bane dad yana da sauki a hankali zaki fahimci haka, kallonshi tayi tace badai a gidanku zamu zauna ba koh? Yace mata a nan zamu zauna kina da matsala da haka ne? Tace eh bazan iya zama gida daya da dad dinka ba, dan shuru yayi yana nazarin magananta tare da tunanin abunyi.... Katseshi tayi da fadin in kuma baka da wajan sani zan tafi hotel, murmushi yayi tare da fadin no ba zaki hotel ba kece fa matar da zan aura komai kike so dole inyi miki akwai gidana sai muje can ki dinga kula dani har in gama warkewa, kai ta daga mishi alaman gamsuwa sannan suka canza firan da maganan yanda zasu tsara auransu in sun tashi yi. Jawaheer gaba daya duniya ta mata zafi, maganan mum take ta tunawa da tace dole tare zasu koma, gashi dad dinta yana ji baice komai ba, dan tsaki tayi lokaci daya kuma ta tashi tayi toilet wanka tayi ta shirya cikin wata doguwar riga english wear tare da yafa karamin gyalen kayan, duk da batai makeup ba tayi kyau sosai idonta yayi zuru2 alaman tana cikin damuwa, falo ta fito taga mum a zaune ita da khalil, tace mum zan fita in dawo, mum cikin jin dadi tace ko kefa jawaheer ai gwara ki saki ranki dan murmushi tayi khalil yace muje tare nima inga gari ita da khalil suka fita a kafa har sukaje wani katon super market gaba daya rigunan da m samir yake sawa ta dinga jida da duk wani abu da akwai pic dinshi a jiki, tare da daukan ball har guda biyar khalil tausayi yaji tana bashi domin yana gani wannan abun na jawaheer ya wuce yanda yake tunani in tayi wani abu kaman ba ita ba, har ta gama khalil bai dauki komai ba yana kallonta cikin damuwa, kallonshi tayi tace yadai babu abunda zaka siya kai? Ajiyan zuciya yayi tare da fadin babu abunda zan siya muje mu biya kudin mu wuce, bayan sun biya kudin wasu daka cikin ma'aikatan suka tayasu fitar da kayan khalil ya tsayar da taxi akasa kayan suka wuce gida, koda suka isa gida mum da dad suna falo, jawaheer ajiye kayan hannunta tayi sannan ta nufi inda dad yake ta zauna tana fadin dad plz kazo muyi magana dan Allah dad ka tashi muje, dad dariya yayi tare da fadin ok muje, tashi yayi suka fita mum ta girgiza kai tare da fadin Allah ya baki lfya. Jawaheer kallon dad tayi tace dad dan Allah ka tausayamin karka bari mum tace zata tafi dani, kasan ban samu abunda nazo garin nan danshi ba,plz dad ka tausayamin ka bari inga m samir ,dad yace jawaheer kiyi hakuri ganinshi ba abu bane mai sauki amma kizo mu koma insha Allah nayi miki alkawarin sadaki dashi amma sai kinyi hakuri kin bani lokaci kadan, kai ta girgiza tana hawaye tace dad ka tausayamin badan niba dad idan na koma gida wlh tunani zai kasheni tunani zaisa in mutu zuciya ta zata buga dad wata daya kawai nake bukata wlh dad in ban ganshi ba nayi alkawarin zan dawo sannan bazan kara yi muku maganan shiba duk da nasan ba abu bane mai sauki amma zanyi shuru har sonshi ya kashe ni, dad jikinshi yayi sanyi yasa hannu yana share mata hawaye yace kiyi hakuri jawaheer kinji mum dinki ta rantse amma zan mata magana kinji? Kai ta daga alaman eh. Washe gari jawaheer ta shirya cikin riga da wando tasa wani karamin gyale ta rufe kanta sannan tasa boyfried jacket akan kayan yau babu laifi ta shafa powder tayi kyau sosai saita fito kaman balarabiya wata karamar jaka ta dauka ta rataya, falo ta fito babu kowa hakan ya mata dadi sosai dan bata son tambaya, taxi tahau ta fadamai inda zata hospital din da ambassador yake aka kaita sauka tayi ta biya kudin taxi din ta shiga asibitin a dai2 lokacin taga an bude wata kofa an turo wani akan keke ido ta ware tare da fadin M sa....... m samir.............. *maryam obam* [11/01, 19:42] Maryam Obam Group Kd: *JAWAHEER* *STORY AND WRITEEN BY......* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA* *(maryam Obam)* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝* *{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}* *wattpad @maryam-obam* *WWW.Maryamobamnovels.com* https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/ *DEDICATED TO.....* *Nafisa mrs dan malikin kawo* Page 10 *ina godiya ga masoya novel din jawaheer sannan masu kira na ko yimin message idan suka jini shuru ina godiya sosai da sosai a kullum maryam obam tana alfahari daku masoya na kudai kawai kuci gaba da suburbodo comment da shrhi* Dago kai yayi suka hada ido shida ita ganin irin kallon da take mai wanda ya saba ganin irinshi amma sai dai nata ya banbanta da sauran domin duk wanda ya ganshi sauri yake ya bashi paper dan ya mishi signing amma ita wannan tsayawa tayi ta bude ido tana kallonshi abun ya dan bashi mamaki dan haka ya sakar mata murmushi ko zata dawo cikin hayyacinta inma tana tunanin bashi ta gani ba amma ko gezau batayi ba daka kallon nashi da takeyi kai ya girgiza dai2 lokacin da aka turashi suka wuce gabanta jawaheer yanda kuka san gunki haka ta tsaya ido bude bigeta din da akayi ne yasa ta dawo hayyacinta ta fara dube2 amma bata ganshi ba jin ihun da ake tayi yasa ta fita da gudu wanda yayi dai2 da lokacin da aka taimaka mishi ya shiga mota wani irin kuka ta saki da taga anja motar daya shiga sun bar wajan, da yake turai ne babu ruwan kowa da kowa haka tayi kukanta dan kanta ta gaji ta tashi ta fita daka asibitin ta fasa zuwa wajan ambassador da tayi niya. Gida ta koma da kuka a nan taga dad shida khalil ganin ta shigo tana kuka dad ya tashi ya rikota yana tambayan lfya jawaheer daka ina haka mai aka miki maiya faru dake duk lokaci daya ya jero mata tambayoyin data kasa amsa mishi sai kuka,mum ta fito da sauri tana fadin maiya faru kuma? Cikin kuka tace dad wlh yau naga M samir da idona, mum tsaki tayi tare da fadin abun naki har yakai haka koh? Cikin kuka tace mum daka Allah babu kowa koh?..... Toh wlh naga m samir da idona, dad yace a ina? Tace dad naje asibiti domin inga ambassador saboda in kara roqanshi ko akwai wata hanya ban kai da zuwa dakin ambassador ba saigashi an turo m samir akan keke daka wani daki an fitar dashi, khalil yace baki mishi magana ba? Tace wlh na kasa gaba daya lokacin dana ganshi komai nawa ya tsaya har murmushi yayi min, wani hawaye mai zafi ya kara fito mata tace koda yau nabar kasar nan zanyi farin ciki domin naga abunda nake burin gani nake mafarkin gani kuma sai dai kash burina bai cika ba tunda ban mai magana ba, kamo hannun mum dinta tayi tana kuka lokaci daya kuma ta tsugunna a kasa kaman mai neman gafara tace mum baki yarda dani ba koh? Mum tayi murmushin karfin hali tace na yarda dake jawaheer murmushi jawaheer tayi sannan tace mum ki tausayawa rayuwar yarki nasan kunfi kowa sona mum wlh da kinji abunda nakeji da kin amince da duk wani abu dana roqa daka gareki wlh mum duk wannan abun da nakeyi saboda so nakeyi wanda bani nasa ma kaina ba Allah ne yasa min mum yau koda M samir bai aureni ba inaso inyi magana dashi koda sau daya ne a rayuwa na mum dan Allah ki barni inyi wata daya a kasar nan kafin in dawo na miki alkawarin indai nayi wata daya ba tare dana ganshi ba wlh zan dawo sannan na baku zabi ku aura min duk wanda yayi muku, mum dan Allah ki tausayamin, mum ajiyan zuciya tayi tare da dago jawaheer daka tsugunon da tayi, tace shikenan na yarda zanyi kaffara na rantsuwan da nayi zan barki kiyi wata daya amma kema ki sani ki riqe alkawarin da kika dauka in bakiga M samir ba duk wanda muka baki zaki yarda ki aureshi? Kai ta daga tare da fadin nayi alkawari mum ko waye zan aura mum tace shikenan sannan inaso ko mai za kiyi kiji tsoran Allah ki riqe mutuncinki a matsayinki na diya mace wacce rayuwanta kalillan ne, tace insha Allah mum bazan baku kunya ba, ranan jawaheer ta saki jiki na farko yau taga M samir gashi kuma mum ta yarda zata barta haka sukai ta fira dan gobe su mum za su wuce nigeria. M samir yana kallon lokacin da jawaheer tayi kasa tana kuka abun ya bashi mamaki na farko irin kallon da take mishi da kuma sanda ta fito da sauri taga sun wuce tayi kasa tana kuka abun ya daure mai kai har yaji yana son sanin dalilin kukan nata duk yanda akayi yasan ba yar kasar su bace dan bata mishi kama da yar kasar suba dan tafi mishi kama da balarabiya gaba daya da tunanin jawaheer suka karasa gidanshi da zai zauna shida sonia, bayan sun shiga ciki sonia tace bari taje ta mishi wanka yace nope zaiyi da kanshi dan yasan dad dinshi zai iya zuwa at anytime in kuma yaga hakan ranshi zai baci shi kuma baya son batama mahaifinshi rai, babu yanda sonia batayi ba amma yaki yarda tashi yayi yana jan kafa ya shiga toilet yana iya tafiya amma yana dan dingishi an sashi a keken tura marasa kafane saboda shi celebrity ne inya fito da kafanshi duk yawan security dinshi mutane za suyi ta ihu gashi kuma asibiti ne sai yasa aka sashi a kai kuma duk da hakan mutane sun ganshi din koda ya shiga toilet tunanin jawaheer ne ya dawo mishi mai yasa take kuka koma dai miye daka gani tana cikin damuwa sannan daka ganin alamunta tana son magana dashi, a hankali ya furta i have to find her. *maryam obam* [15/01, 02:30] Maryam Obam Group Kd: *JAWAHEER* *STORY AND WRITEEN BY......* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA* *(maryam Obam)* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝* *{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}* *wattpad @maryam-obam* *WWW.Maryamobamnovels.com* https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/ *DEDICATED TO.....* *Nafisa mrs dan malikin kawo* Page 11 *PLZ MASOYA NOVEL DIN JAWAHEER KUYI HAKURI KWANA2 ABUBUWA SUNYI MIN YAWA MASU TURO MIN MESSAGE DA MASU KIRA SUJI KO LFYA INA GODIYA SOSAI.... AMMA KU KARA HKURI BA LALLAI BANE KU DUNGA SAMUN POSTING KULLUM SABODA WASU ABUBUWA DA NAKEYI AMA ZAN DINGA KOKARI DN INYI MUKU INA YINKU SOSAI* Yau su mum zasu koma nigeria dukansu sun shirya an saka musu kaya a mota dan zuwa airport, mum tana tama jawaheer nasiha tare da kara tuna mata ta rike mutuncinta na diya mace, har suka fita suka nufi airport, aka fara kira nan su mum suka fara shiga cikin jirgi jawaheer tana ta daga musu hannu, har jirginsu ya tashi sannan ta koma gida, koda ta nufi gida wanka ta fada tayi tasa wata top mara hannu tare da wani wando 3quater tasa boyfried jacket mai dogon hannu tasa botir din boyfried din tare da saka wata hula a kanta duk da batai makeup ba tayi kyau sosai dan ita jawaheer bata cika son yin kwalliya ba, tafi son zama haka, ta gaban wani daki taje ta zauna da yake gidan gidan sama ne ta wajan dakin yana nuna maka ko ina da ina da gidajen dake kusa da nasu da kuma motoci masu tafiya da mutane masu wucewa zama tayi tana ta kallon masu kaiwa da komowa, lokaci daya kuma ta fara tunanin m samir amma idan ka ganta zaka dauka mutane take kallo amma hankalinta baya wajan gaba daya wani siririn hawaye ne ya zubar mata a ido tunawa da tayi taga m samir ido da ido amma ta kasa yi mishi magana lokaci daya kuma ta saki murmushi domin ta tuna da irin murmushin da yayi mata ido ta lumshe tare da fadin nasan kaima zaka soni kaman yanda nake sonka haka taita tunani a wajan har yamma tayi ta shiga cikin gida. Bayan m samir ya fito daka toilet karema dakin kallo yayi lokaci daya kuma yayi tsaki domin bashi da kayan sawa a nan, jikinshi daure da towel ya fita falo yaga sonia tana kallon news sunanta ya kira tare da fadin bani da kayan sawa a nan, murmushi tayi tare da tashi ta nufeshi tayi hugging dinshi tana fadin karka damu ai babu inda zaka nafi son ka zauna a haka inyi ta kallonka.... Dai2 lokacin dad dinshi ya shigo da yake sun bar kofar falon a bude jin sallaman dad dinshi yasa ya dan jata baya amma saita kara manneshi tana fadin come on, dad dinshi ranshi bace ya juya ya fita daka gidan, ganin haka yasa ya ture sonia yana fadin mai kikeyi haka? Bakiji dad dina bane? Tace naji toh mai kakeso inyi mishi? Magananta ta dan bashi haushi amma saiya dake yace daya shigo saiki sakeni sannan ki dawo ki zauna kalla fah yanda nake daka ni sai towel so kike yayi tunanin ko wani abu mukayi? Tace sai me dan yayi tunanin hakan ni ba damuwa ta bane, cikin bacin rai yace look sonia inaso ki sani idan ke ba damuwanki bane toni damuwa nane, domin addini na bai ce inyi haka ba nd..... Ta dakatar dashi tare da fadin ya isa haka ni nace ka shiga cikin addininka mai takura ma mutum addinin da baya ba mutum yancin kansa so ya kamata ka gane gskya ka dawo christen dan shine hanya mai bullewa, shuru yayi yana kallonta cikin mamaki harta gama, sannan yace u r wrong sonia addinina shine addini mai bama mutum yanci addini mai haske dat islam addinina ya haramta zina sai yasa Allah yaba namiji daman auren mata har hudu domin gujema baraka...... What u mean ur religion allow u to marry more dan 1 women? Kai ya daga mata alaman eh, cikin zafin rai tace what kind of religion iz dis how can man marry 4 wife dan murmushi tayi mai zafi sannan tace kana nufin idan mukayi aure zaka kara auran wata?? Kai ya daga mata tare da fadin bani da burin auren mace fiye da daya amma ban san abunda Allah zaiyi ba, cikin rashin fahimta tace bata ganeba, yace idan Allah yasa zan kara zan kara in kuma bai sa.... Ta dakatar dashi cikin kuka tare da fadin ita ba zata iya aurenshi ba dan me zaice zai kara wata mace bayan ita, sannan yasan ita a nata addinin mace daya ake aure kallonshi tayi cikin fushi tace bazan zauna dakai ba yau zan tafi sannan bazan dawo kasar nan ba ko inzo gareka ba har sai ka canza addini domin bazan iya auren muslim ba tunda haka addininku yake tana fadin haka ta fita yana ta kiranta amma bata tsaya ba gashi babu kaya a jikinshi, koda ta fita daukan jakarta tayi a motar daya kawo su ta wuce, zama yayi ya daura hannu a kai alaman damuwa lokaci daya kuma yayi tsaki tare da ware hannu alaman ban damu ba daki ya koma ya dauko waya ya kira waya dan a kawo mai kaya yana gama fadin abunda yake bukata ya kashe waya Jawaheer kullum bata fita sai dai tazo wajan dakin nan taita kallon mutane masu wucewa yauma tana zaune har yamma taji gaba daya zaman ya isheta dan haka ta fito waje ta tsaya ta gaban gidan tana kallon gidan dake kallon nasu domin gidan ya birgeta yana yin yanda aka tsara gidan a hankali ta furta duk yanda akayi suma nan kasar nan area din yana daya daka cikin wajan da masu kudin kasar suke dan gaba daya tsarin gidajen dake wajan gwanin sha'awa, ganin giftawan mutum tayi daka gidan dan murmushi tayi tare da fadin bari inyi karan bani in leka gidan ko zan saba dasu, dan zama mutum daya babu dadi, dan shuru tayi tana nazari nan fah kasar waje ne ba nigeria ba toh in taje mai zata ce musu? Wata zuciyar tace kije may be ma sun san m samir dinki dariya tayi lokaci daya kuma ta nufi gidan, koda ta karasa kofar gidan mutumin da taga ya gifta ta gani yana tsaye da ledoji a hannunsa alaman yana jira a bude mai kofa cikin harshen turanci take cemai sannu ni..... Bata kai ga karasa magana ba aka bude kofar tsayawa tayi cak tare da zare ido tana nuna wanda ta gani da hannu alaman kai ne ko gizau ne, lokaci daya kuma tayi murmushi tare da fadin no no ido nane ba m samir bane mai yasa idona kamin Karya mutumin da ganinshi ance min bamai yuhuwa bane sai gashi da towel a gaba na, duk cikin harshen turanci take maganan shiko mamaki abun ya bashi ganin yanda take mamaki kaman bashi ta gani ba, lokaci daya kuma yayi dariya tunawa da yayi itace shima yake nema matsawa yayi kusa da ita tare da riketa ya hura mata iska a fuskanta yace nine M samir nine a gabanki fadowa tayi jikinshi ganin kaman bata motsi yasa ya fara jijjigata...... *maryam obam* [16/01, 17:56] Maryam Obam Group Kd: *JAWAHEER* *STORY AND WRITEEN BY......* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA* *(maryam Obam)* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝* *{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}* *wattpad @maryam-obam* *WWW.Maryamobamnovels.com* https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/ *DEDICATED TO.....* *Nafisa mrs dan malikin kawo* Page 12 Daukanta yayi cak ya shiga da ita cikin gidan bai ajiyeta ko ina ba sai cikin dakinshi akan gadon dakin ya kwantar da ita, mutumin daya kawo mai kaya ya ajiye ya wuce, toilet ya shiga ya dibo ruwa a hannunsa ya yayyafa mata wani irin ajiyan zuciya ta sauke mai karfi, tare da bude idonta dishi2 ta fara gani fuskan M samir ta gani wanda yasa ta bude idan nata da sauri tana fadin bashi bane bashi bane mafarki nakeyi taya zan ganshi lokaci daya ba tare da nasha wahalan da ake fadamin ba, ganin kaman tana kwankwanto yasa yakai bakinshi cikin nata ya fara kissing dinta, gaba daya komai nata ya tsaya cak, saida yayi kissing dinta na wajan 1minute sannan ya saketa dan ya tabbatar yanzu zata cire komai da take tunani tasan shi dinne dagaske, amma ga mamakinshi sai yaga ta tsaya cak, kai ya dan buga wanda hakan ya nuna mishi shine first time da aka taba kissing dinta dan murmushi yayi tare da jan hancinta da hakorinshi ihu ta saki, tana kallonshi yace yes nine a gabanki, nunashi ta farayi tana murmushi lokaci daya kuma ta fara kuka, kallonta ya tsayayi yana mamaki, rungumeshi tayi tana ci gaba da kuka ta fara fadin ban taba tunanin zan ganka ba a rayuwa na, duk da nazo nan kasar dan in ganka amma ance min ganinka ba abu mai sauki bane kullum nayi sallah sai na roqi Allah domin ya nuna min kai koda sau daya ne a rayuwa na, na ganka a asibiti lokacin ban san dalilin da yasa na kasa yi maka magana ba, saj gashi yau Allah ya nuna min kai gaka a gabana jikina a cikin naka duk da bada son raina nayi hakan ba, tsabar farin ciki ne.... Cire jikinta tayi daka nashi taci gaba da fadin bana kallon ball amma ranan dana fara kallo na ganka lokacin kaci ball naji anata kiran M samir tunda na ganka naji Allah yasa min sonka, idan ina magana iyayena suna min kallon kaman bani da hankali amma ni daya nasan abunda nakeji bani da wani buri daya wuce in zama matarka, amma ance min hakan bamai yihuwa bane saboda celebrity bazai taba auren yar nigeria ba, koda burina bai cika ba zanyi farin ciki na ganka kuma kaine namiji daya daka dara kissing dina na farko a rayuwa na, dan shuru tayi tana kallonshi shima kallonta yakeyi lokaci daya ya fara magana cikin turanci shima yace lokacin dana ganki a hspt irin kallon da kike min nasan kina da magana a bakinki domin na saba ganin mutane kala2 amma ke irin naki kallon na daban kike min nd kuma lokacin da zamu tafi naga sanda kika fadi kina kuka..... Dan shuru yayi sannan yayi ajiyan zuciya yace ya sunanki? Tace jawaheer kai ya daga tare da kara nanata sunan yace nice name, amma baki kama da yar nigeria ba kinfi kama da yar dubai, murmushi tayi cikin jin dadi, yaci gaba da fadin ngd da kauna da kuma so da kika nunamin amma am sorry to say ina da wacce nakeso na gode da kauna, idonta ne ya kada yayi ja kirjinta ya farayi mata zafi lokaci daya taji wani abu yana son taso mata, ganin halin data shiga yasa ya tashi ya dauko mata ruwa ya bata amma bata ma san yanayi ba ganin haka ya bude ruwan yasa mata a baki babu shiri ta bude bakin ta fara sha, lokaci daya kuma ta kawar da goran ta fara kuka mai karfi tare da ruko hannunshi ta fara fadin bana tunanin akwai wacce zata soka kaman yanda nake sonka wlh son gskya nake maka bana wasa ba ka kalli idona babu komai sai sonka, tashi yayi yabar wajan jim kadan sai gashi yasa kaya, tashi tayi tazo inda yake tana kuka ta rungumeshi tana fadin i luv u, dan janta yayi ya mata peck a goshi sannan yace ta daina kuka, sakinta yayi tare da fara tafiya yace zai fita zuwa wajan dad dinshi, yana fadin haka ya fita kasa tayi tana ta kuka sosai kaman ranta zai fita, tayi wajan awa daya tana zaune a wajan tana kuka sannan ta tashi dakyar ta nufi gidanta har wani jiri2 take ji, koda ta shiga gida a falo ta kwanta tana kuka gwanin ban tausayi tare da surutai kala2 dama mum ta fadamin babu abunda zaiyi dani mai yasa na kasa yarda da mum mai yasa yaki yarda dani kuka ta kuma saki tana fadin mai yasa mai yasa, tana kuka. Shiko yana fita driver yaja shi zuwa gidan dad dinshi, koda suka karasa tafiya yake dakyar yana jan kafa, a falo yaga dad dinshi, gaidashi yayi dad din ya amsa fuska daure, murmushi M samir yayi tare da nufa wajan dad din nashi ya kamo hannunshi yana fadin kayi hakuri dad danka baya abunda kake zargi ka yarda dani, dad din yace bana zarginka dayin komai wanda ya sabama sharia, amma kasan idan mace dana miji suka kebe na ukunsu shaidan ne, ina jin tsoran ka fada halaka, samir bana sonka da wannan yarinyar kwata2 nafi son ka auri musulma yafi yanda yaranka zasu taso cikin cikakkiyar tarbiya, m samir yace okey dad naji amma saika fadamin who is my mum nd i want to see her picture, idan ka fadamin zanyi duk abunda kace min, cikin fushi dad din yace karka karamin irin wannan tambayar M samir cikin damuwa yace why dad mum dina kace ta rasu mai yasa kake boyemin labari na? Why dad? Dad din yace i dnt want you to knw anything about your mum, shima cikin bacin rai din m samir yace why dad miye a ciki dan na sani? Dad din yace wani abu ne because she's still alive...... Shuru dad din yayi domin baiyi zaton maganan zata fito ba, M samir yace what?...... *maryam obam* [19/01, 18:15] Maryam Obam Group Kd: *JAWAHEER* *STORY AND WRITEEN BY......* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA* *(maryam Obam)* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝* *{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}* *wattpad @maryam-obam* *WWW.Maryamobamnovels.com* https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/ *DEDICATED TO.....* *Nafisa mrs dan malikin kawo* Page 13 Dad din shuru yayi ba tare da yace mishi komai ba, m samir yace dad u mean u r telling me lies ol dis yrs, why dad mai yasa ka boyemin mahaifiyata why dad maina maka dana fuskanci wannan hukuncin? Dad tel me ina mum dina i want to see her plz kuka ya saki yana fadin mai yasa ka rabani da mum dina ol dis yrs mai yasa?...... Kuka ne yaci karfinshi ya kasa karasa maganan da yayi niya, dad din cikin tashin hankali yace samir ina jin kunya tare da takaicin fada maka koya akayi na sameka, shekaru talatin da suka wuce.......... LABARI Nayi aiki a nigeria a garin abuja amma da yake aikin contract ne na titi and kuma lokacin company dina akaba aikin, so dole yasa nazo nigeria ganin yanda akai aikin yayi kyau yasa aka kara bama company dina wani aikin wanda yasa dole na dawo nigeria amma wannan karan a wani gari na sauka yola garin akwai wani yare ana ce musu fulani ina son al'adun garin and kuma akwai abunda suke saidawa nono ina son abun sosai akwai wata yarinya mai suna khausar ,kullum tana kawomin nono ina siya batajin turanci ni kuma bana jin yaransu haka zami ta magana kaman kurame har na dan fara koya mata turanci da yake tana da hazaqa saita fara ganewa wanda bata ganeba tayi shuru in naga tayi shuru sai in gane bata gane bane, aikin da zanyi a yola yana da yawa, mun saba sosai sai daka baya na gane ashe sonta nakeyi domin kuwa akwai lokacin da tayi kwana biyu bata zoba na shiga damuwa sosai gashi ban san gidansu ba, a cikin yaran da suke mana aiki na tambayi wani ko yasanta yace eh ya santa ya san gidansu, a lokacin da naje gidansu na sami babanta bayajin turanci sai mutumin da naje dashi yake fassara mishi abunda nake fada, nan na tambaya ya jikin khausar yace lfya da sauki,inda na bukaci in ganta tana jin jiki sosai taji dadin ganina inda nace ma mahaifinta mu kaita hspt yace a'a basa zuwa asibiti su a gida suke magani babu yanda banyi ba amma tsohon nan yaki yarda haka na hakura na dawo cike da tausayinta ga sonta daya kamani lokaci daya, ganin bazan iya jurewa ba yasa na dauko dr yazo ya dubata dakyar babanta ya yarda, nan aka dubata aka gano maleria ne ke damunta, an bata magani cikin kwana biyu ta warke kaman ba ita ba, babanta yaji dadi sosai inda a nan nake fadama babanta ina son aurenta, tam ya tamke fuska tare da fadin bazai taba yihuwa ba yarshi ba zata auri bature ba, kai koh bahaushe ma bazai bama yarshi ba balle shi dama ba dan kasar nan bane, haka na dawo gida jiki a sanyaye tare da tarin tambayoyi, shin miye laifina danni badan kasar nan bane? Nima fa musulmi ne kaman su, rannan ina zaune sai gata tazo cikin dare tana kuka wai dama ina sonta ban taba fada mata ba? Gashi yanzu babanta yana kokarin aurar da ita ga wani dan uwanta hankalina ya tashi sosai na shiga damuwa amma irin kukan da takeyi shi yasa na fara rarrashinta har takaini da taba jikinta inda shaidan yayi nasara akan mu muka aikata aikin dana sani, ranan nayi nadama sosai haka itama babu abunda muke mu duka sai kuka, haka ta tafi gida tunda ta tafi ban kara ganinta ba na shiga damuwa sosai har takaini da kara zuwa gidansu dan inga mahaifinta koh zai hakura ya bani ita amma yaki babu irin magiyan da ban mishi ba amma yaki saurarana daka karshe ma korana yayi, ana cikin haka kwatsam sai gata tazo ta sameni tana kuka wai tana da ciki innarta ta gano tana roqona in bar garin domin idan ta fada shine ya mata cikin komai zai iya faruwa wanda zai aureta zai iya kasheni domin bashi da imani, da farko naki yarda amma irin kukan da tkeyi da roqan da takemin yasa nabar kasar gaba daya, ina nan spain ina fama da tunaninta da kuma watan da zata haiyu, har lokacin yayi na koma nigeria ban bari kowa ya ganni ba na nufi gidansu cikin dare suna bacci na dauko ka na gudo dakai kasar nan tare da taimakon wata abokiyar aikina wacce itama yar nigeria ce ta zauna a matsayin mamanka, tun kana karami kaman ka sak na mahaifiyarka sai dai ka dauko farina duk da itama fara ce amma na fita, tunda na daukoka ban kara komawa nigeria ba har yau amma nasan mamanka tana raye sannan har gobe ina son khausar wannan dalilin ne yasa naki yarda inyi aure. Kuka M samir yake sosai tare da fadin yanzu dama bata aure aka sameni ba, ni shege ne? Kuka yaci karfinshi dad duk da wannan abun da kuka aikata saida ka raba mum dina dani? Why? Why? Dad kasan irin ciwon da zata ji kuwa? Kasan wani hali zata tsinta kanta? Shin kasan ya zataji inta tashi bata ganni ba? Duk bakai wannan tunanin ba ka rabata dani, kuka yake sosai lokaci daya kuma ya fita yabar gidan dad din yana kiranshi amma kota kanshi baibi ba ya wuce abunsa cikin tashin hankali koh mota bai shiga ba a kafa yake ta tafiya yayinda mutane suka fara ihu tare da zagaye shi, security dinshi dake binshi dakyar suka fito dashi daka cikin mutane suka sashi a mota, kallon driver din yayi yace ya kaishi gidansa tunda ya fadi haka bai kara cewa komai ba sai kukan da yakeyi har suka karasa gida da sauri ya shiga ya fara dube2 lokaci daya ya furta whr iz she? fita yayi da sauri ya fara tambayan security dinshi ina yarinyar da tazo dazu ina take?...... *maryam obam* [21/01, 13:45] Maryam Obam Group Kd: *JAWAHEER* *STORY AND WRITEEN BY......* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA* *(maryam Obam)* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝* *{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}* *wattpad @maryam-obam* *WWW.Maryamobamnovels.com* https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/ *DEDICATED TO.....* *Nafisa mrs dan malikin kawo* Page 14 Cemai sukayi basu san inda take ba, daura hannu yayi akai cikin wani irin tashin hankali dakyar ya iya shiga cikin gida koda ya shiga shima a falo ya zauna yana kuka sosai wanda na rasa gane na bakin ciki ne kona farin ciki, amma zan iya danganta kukan nashi dana bakin ciki, lumshe ido yayi tare da tunanin yanzu shi shege ne bata hanyar aure aka sameshi ba, innalillahi wa inna'ilaihira jiun, yanzu duk wani kimarsa da darajansa zata ragu a idon al'umma idonshi ne ya kada yayi ja yanzu mahaifiyarshi tana nigeria a garin yola, shida bai taba zuwa nigeria ba taya zai nemeta yasan dad dinshi da wuya ya kaishi, jawaheer ita daya ce zata taimakeshi saboda itama yar nigeria ce, ido ya lumshe tunawa da yayi lokacin daya barta tana kuka akan ya sota, lokaci daya ya kawar da tunanin dan bashi bane yanzu a gabansa burinshi yanzu yaga jawaheer ta taimakeshi domin yaga mum dinshi. Jawaheer tana kwance akan kujeran falo tana ta rusgan kuka, lokaci daya zazzabi ya kamata mai zafi, wanda yasa duk wani gaba dake jikinta ya mutu, ga kanta dake faman sara mata wanda kukan da tasha ya haddasa mata ciwan kai din da zazzabi, dakyar ta tashi tayi alwala tayi sallah a zaune dan bata ji zata iyayi a tsaye, kuka take tana roqan Allah akan ya zaba mata mafi alkhairi a rayuwanta, harta gama ta kwanta wajan da tayi sallah din, gaba daya taji zaman garin ya isheta burinta ta ganta a nigeria domin kuwa tasan M samir bazai taba sonta ba har abada, dakyar taja jikinta ta dauko wayanta dake ta faman ruri tun dazu, sunan mum ta gani dan haka ta dauka da sauri tare da fadin mum..... Sai kuma ta saki kuka hankali tashe mum take tambayanta maiya faru jawaheer lafiya kuwa? Cikin kuka tace mum magananki gskya ne, tabbas gskyan hausawa ne da suke fadin duk abunda babba ya hango yaro bazai taba hangosa ba, mum cikin damuwa tace jawaheer dan Allah ki fadamin maike faruwa, wani abu aka miki? Tace mum inaso a fara maganan biki na kaman yanda kike so da duk mijin da kuka ga ya muku, mum tace jawaheer dagaske kike? M samir fa? Kina nufin kin hakura dashi? Duk lokaci daya mum ta jero mata tambayoyi wanda yasa jawaheer din wani sabon kuka, cikin kuka taba mum labarin duk abunda ya faru tare da fadin mum jibi zan dawo gida, ki fadama dad yama PA din ambassador magana, mum tace shikenan jawaheer zan fada mishi kiyi hakuri ki cire komai a ranki insha Allah komai zai wuce, tace mum bana tunanin zan cire komai domin son M samir a jini na yake na amince da zanyi aure ne saboda alkawarin da nayi mum inaso ki sani wlh duk wanda na aura gangar jikina ne kawai a tare dashi amma zuciyata tana tare da m samir mum ki tayani da addu'a kawai Allah ya bani hakuri da dangana amma ina cikin wani hali mum tana fadin haka ta kashe wayan tare da sakin kuka mai karfi, a yanzu jawaheer bata bukatan komai face ta ganta a kasarta nigeria domin ta cire tsammanin m samir zai sota, sai dai koba komai zatai alfahari da ganinshi da tayi tare da kissing dinta da yayi duk da tasan ba abu bane mai kyau tunda ba mijinta bane, sai dai a yanda take jinshi koda jikinta ya nuna yana bukata bata tunanin zata hanashi dan tana mai mahaukacin so, wanda bata ganin kowa sai shi, sai dai kash shi ta gefenshi ba haka bane irin yanda ya nuna baya sonta yasa take ganin kaman zata iya rayuwa da wani wanda ita da kanta tasan karya ne, m samir kadai shine burinta shine namiji daya da zata samu tayi farin ciki a rayuwa koda kuwa zai dinga dukanta ne kullum, lokaci daya ta tashi da sauri duk da bata jin karfi a jikinta tafiya take tana tangal tangal kaman zata fadi kofar gidanta ta nufa ta bude ido ta kurama gidan m samir din wanda hakan ya nuna mata alaman ya dawo yana gida, tunda taga security dinshi, kirjinta taji yana buga mata da karfi, lokaci daya ta fara tafiya domin zuwa gidan har ta kusa shiga ta tsaya, lokaci daya kuma ta juya zuwa gidanta da sauri dan bata jin zata iya zuwa gareshi yanzu, amma koda ta shiga gida kasa sukuni tayi wanda yasa dole ta kara nufa gidan duk da kirjinta na buga mata dan bata san mai zata tarar ba yanzu, amma haka ta daure ta shiga cikin falon gidan a kwance ta ganshi akan kujeran falon kallo daya zakai mishi ka gane yana cikin wani hali dake bukatar taimako, da sauri ta nufeshi tare da fadin m samir, nufanshi tayi tare da fadin baka da lfya ne? Idonshi ya bude daya kada yayi ja ya sauka a kan fuskanta, murmushi ya sakar mata tare da kokarin tashi amma ya kasa, dan haka ta fara kokarin dagashi amma ta kasa, murmushi ya kuma saki tare da fadin na miki nauyi koh? Dan shuru tayi sannan tace baka da lafiya jikinka da zafi u need to see a doctor, ido ya kura mata yace jawaheer kema jikinki zafi kina bukatan ganin dr tashi yayi dakyar tare da janyota jikinshi yace maike damunki? Kirjinta ya fara bugawa da karfi wanda hakan yasa ta kasa magana domin gaba daya tunda ya janyota jikinshi wani irin shock ya kamata tare da shiga cikin wani irin yanayi bakinta sai rawa yake alaman tana son cewa wani abu amma ta kasa, ido ya kura mata yana kallonta lokaci daya ya furta she iz pretty. *maryam obam* *JAWAHEER* *STORY AND WRITEEN BY......* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA* *(maryam Obam)* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝* *{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}* *wattpad @maryam-obam* *WWW.Maryamobamnovels.com* https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/ *DEDICATED TO.....* *Nafisa mrs dan malikin kawo* Page 16 Lokaci daya kuma ya furta nasara akan me? Bata bashi amsa ba dan kuka takeyi sosai ganin bata da niyan bashi amsa yasa ya tashi ya dawo kusa da ita zama yayi kusa da ita tare dasa hannunshi yana share mata hawayen dake zuba a fuskanta, yace jawaheer kibar wannan kukan koma miye insha Allah zaki samu ki dage da addu'a kinji kai ta daga alaman toh, sannan ta tashi tare da fadin sai anjima, bai tankata ba har takai bakin kofa ya kira sunanta tare da fadin inane gidanki? Tace can, dariya yayi tare da fadin can ina? Tace kazo muje saika gani, tashi yayi yana jan kafa dan har yanzu bawai ya warke bane tana gaba yana biye da ita a baya komai nata yana burgeshi kyanta nutsuwanta, maganan ta, tafiyanta kai komai nata ya mishi sai dai baya jin sonta a ranshi amma ya dauketa a matsayin kanwarshi domin so daya ne ya kuma bama sonia wacce bai san inda take ba a halin yanzu dan tunda ta tafi basuyi waya ba duk da yama dad dinshi alkawarin rabuwa da sonia amma baya jin zai rabu da ita dan itace rayuwanshi,.... Maganan jawaheer ne ya katseshi da take fadin shigo mana, sai a sannan ya gane sun zo gidan, shiga yayi da sallama, tace ya zauna a falo, bayan ya zauna ne ta nufi kitchen dan ta hada mishi coffee bata dauki wani lokaci ba ta kawo mai amsa yayi ya fara sha, sannan ya dago kai suka hada ido murmushi ya sakar mata yayin da ita kuma tayi saurin kawar da fuska dan taji kunyar kamata da yayi tana kallonshi, jinshi tayi yana fadin ina son idonki yana min kyau, bata iya cewa komai ba sai murmushi kawai da tayi, shima bai kara magana ba harya gama shan coffee din wayanta ne yayi kara dan haka ta tashi ta dauko taga ozil ne , dauka tayi da fadin kabir nayi fushi wlh sai yau? Yace kiyi hakuri m samir nasan nayi laifi tace uhm ni bazan hakura ba gaskiya, ban san mai yace mata ba naga ta saki dariya tare da fadin zan baku mamaki ku dukanku, nan dai sukai ta fira cikin harshen hausa har sukai sallama, Bayan ta kashe wayan ne ta kalli m samir daya zuba mata ido yana kallonta, saurin kawar da kanta gefe tayi, murmushi yayi tare da fadin wannan wani yare naji kinayi? Tace hausa, kasa fadin hausa yayi dan haka abun ya bata dariya, yace ya akeyi yana son ya iya, tace babu wuya mu a nigeria shine yaran da kowa yakeyi akasarin mutanan kasata koda wata kabila ne zaka sameshi yana jin hausa koda babu yawa domin hausawa sunfi yawa a kasar, yace a nigeria yare daban daban akeyi? Tace eh akwai yare kala kala, akwai fulani, hausa, igbo, yaruba, tibi, igala, idoma, ibra, kurama, gwari, da sauransu, yace kai yare da yawa haka a kasa daya kuma duka yan kasar ne? Tace eh duk yan kasar ne, yace wow inaso inga wa innan yaren, ke miye naki yaren? Tace fulani ce ni, dan shuru yayi sannan yace dayan yaran da naji kinayi ba naki bane kenan? Tace eh, yanda take mishi bayanin abun na sashi cikin nishadi yayin da take ta kara bashi labari akan kasarta shi kuma yana jin dadi, ganin irin kallon da yake mata yasa tayi shuru tare dayin kasa da kanta tana wasa da hannunta, murnushi yayi tare da kiran sunanta yace jawaheer dago kai tayi suka hada ido tayi saurin yin gefe da idonta, domin indai suka hada ido wani irin yanayi take shiga mai wuyan fassaruwa, yace kece mace ta farko da nake son yin fira da ita, idan ina magana dake inajin dadi sosai, i will like you to be my sister, murmushi tayi tare da fadin thanks alot yau ina cikin farin ciki daka daukeni a matsayin kanwarka, insha Allah zakai farin cikin zamana kanwarka tare da alfahari dani, mika mata hannu yayi alaman su gaisa, tashi tayi ta nufeshi tare da bashi hannu yace i luv you sister, shuru tayi domin ta lula wata duniyar inama ace yau wannan kalman daya fada mata a matsayin masoyiyyarshi da bata san wani irin farin ciki zatayi ba, hawaye ne ya fara zuba a idonta, jin hannunshi tayi yana goge mata da sauri ta dago ta kalleshi, shima dai ita din yake kallo, tace yau ina cikin farin ciki ban taba tunanin zan ganka ba a rayuwa na, wannan kukan da nakeyi na farin ciki ne, yau gani ga ka, kafin in ganka an fadamin ganinka tashin hankali ne amma da yake Allah mai tausayin bayinsa ne sai ya hadani dakai ba tare da nasha wahalan da ake fada ba, sai yasa ake cewa kar bawa ya cire rai da ikon Allah, na tabbata addu'ata ce Allah ya amsa sai yasa ya hadamu cikin sauki, yace hakane sister babu abunda Allah bazai iya ba, komai ya faru da bawa ya dauka a matsayin kaddara ne a rayuwanshi...... Shuru yayi lokaci daya kuma yace tabbas dad dina bashi da laifi dan an sameni bata hanyar aureba, lallai haka Allah ya tsara babu wanda ya isa ya canza hakan, laifi daya dad dina yayi daya raba mum dina dani, jawaheer tace shima yana cikin kaddaranka, kallonta yayi ta daga mishi kai alaman eh tace haka Allah ya tsara maka sannan gashi ta sanadin haka mun kara samun kusanci haduwa na dakai shima yana cikin kaddaranka........ *maryam obam* *JAWAHEER* *STORY AND WRITEEN BY......* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA* *(maryam Obam)* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝* *{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}* *wattpad @maryam-obam* *WWW.Maryamobamnovels.com* https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/ *DEDICATED TO.....* *Nafisa mrs dan malikin kawo* Page 17 *ina yinku masoya novel din jawaheer kaman yanda kuke son novel din jawaheer nasha kira da message kuyi hakuri na jina shuru insha Allah zan dinga muku posting kullum koda ba yawa😆* Yace kaddarana?? Kai ta daga mishi alaman eh, tare da fadin gashi ta sanadi na zaka kasata nigeria, murmushi yayi tare da fadin hakane harna kosa inje koh Allah zaisa inga mum dina, inko hakan ta faru ban san wani irin farin ciki zanyi ba, jawaheer tace insha Allah zaka gan..... Bata karasa ba tayi shuru tana kallonsa shima din ita yake kallo cikin sanyin murya tace kana da pic dinta?? Shuru yayi can yace a'a bani dashi, tace sunan anguwansu a yola din fah? Shima yace bai sani ba, jawaheer tace toh taya zamu nemota?? Wannan ba abu bane mai yuhuwa dole muna bukatar sunan anguwansu ko kuma hotan ta, wani irin zufa ne ya keto ma m samir wanda gaba daya shi baiyi tunanin haka ba dan yana ganin yana zuwa nigeria zaiga mum dinshi toh taya ma zai ganta shida bai santa ba, bai taba ganin hotanta ba, hannunsa ya buga a dayan hannunshi tare da tashi ya kalli jawaheer yace zanje wajan dad dina ya fadamin sunan anguwan su, coz i only know her name, fita yayi da sauri, duk da dingishi yakeyi, koda ya fita security dinshi na nan tsaye suna jiranshi, yace ku dauko mota muje gidan dad, daya ne ya tafi sai gasu da mota har biyu ya bude ta farkon ya shiga, kai tsaye gidan dad dinshi ya kara nufa, a falo yaga dad din nashi a zaune idanshi yayi ja, yana ganin dan nashi ya tashi da sauri ya rungumeshi yana kuka, jikin m samir yayi sanyi tare da tausayin dad din nashi, cikin kuka dad din ya fara magana samir yanzu zaka gujeni koh? Zaka koma wajan mum dinka gaba daya, bazan bar hakan ya faru ba, dad din mum dinka yaki bani ita bai lura da irin son da nake mata ba, dan kawai ni farin fata ne bai lura da cewa duk musulmai daya bane, samir har yanzu ina son mum dinka sai yasa nake masifar sonka ban san damuwa a tare dakai in wani abu ya sameka inaji kaman mum dinka ya sama, plz dnt leave me, m samir ya danja jikinshi daka na dad din nashi ya fara magana kaman haka dad bazan taba gudanka ba kaine mahaifina nasan irin son da kake min amma dad plz ka barni inje inga mum dina koda once ne in my lyf, tasan danta bai mutu ba sannan tasan danta baya mugun hannu, na tabbata har yanzu bata cikin nutsuwa tunda danta ya barta, dad din kai ya girgiza yace ina tsoran kaje kaki dawowa son, m samir yace dad indai ka fadamin inda take one week zanyi kawai in ganta in dawo kasan inada wasa nan da sati biyu, dad din shuru yayi can ya nisa yace sunan anguwansu guyuk idan kaje kace a nuna maka gidan liman, murmushi m samir yayi najin dadi yace ashe kakana liman ne a anguwansu, dad din yace eh, sannan yace toh taya zaka kaida baka san kasar ba? Yace dad akwai wata yar nigeria tare zamu, dad yace wacece a ina ka santa? Murmushi yayi tare da fadin haba dad nifa duk wanda nace maka na sani ba abun mamaki bane, dad yace hakane amma ya akai tazo wajanka harta ganka kuka hadu kuka saba, dariya m samir yayi yace hadin Allah ne, dad din murmushi yayi tare da fadin ina son ganinta, m samir yace gobe zan kawo ta bari in sanar da minister zan tafi nigeria jibi suyi arranging dad din yace ok m samir tashi yayi tare dayi ma dad din sallama. Tunda m samir ya fita jawaheer taji wani iri amma taji dadin sabawansu lokaci daya ido ta lumshe tana jin nishadi, burinta har yanzu bai wuce ace yau ya yarda zai aureta ba ita koda zai aureta baya sonta zata so haka, amma tunda yace a matsayin kanwa ya dauketa hakan ma abun alfahari ne a wajanta wasu ma signing dinshi suke nema su samu amma abun yaci tura ita kam gata gashi har kissing dinta ya taba yi wani murmushi ta saki cikin jin dadi haka har bacci ya dauketa. Washe gari da safe tunda jawaheer tayi sallah asuba tayi wanka, ta koma bacci bata farka ba sai wajan karfe goma tana tashi ta kara komawa tayi wanka, tasa wata doguwar riga tare da daura karamin gyalen rigan, kitchen ta nufa ta hada tea dan gidan babu masu aiki tunda su mum suka tafi suma suka wuce, tana cikin shan tea din taji nocking tashi tayi ta nufi kofar tare da tunanin ko waye, tana bude kofar taga mutum a tsaye cikin riga da wando yayi mugun kyau ya hade hannunshi biyu yana kallonta tare da sakar mata murmushi ganin irin kallon da take mai yasa yazo kusa da ita tare da mata peck a goshi yace morning sis, firgit tayi ta fara kame kamen mai zata ce, ganin haka yasa ya kamo hannunta tare da shiga cikin gidan yace nazo ki rakani wajan dad dina yana son ganinki, ido ta zaro tare da nuna kanta alaman ni zai gani, kai ya daga mata tare da fadin yes ke zai gani, matsowa tayi kusa dashi tare da fadin Allah yasa ba laifi nayi ba? Yanda tayi maganan cikin sanyin murya ya bashi dariya hancinta yaja tare da fadin bakiyi komai ba kawai yana son ganinki ne, ajiyan zuciya tayi tare da fadin yaushe zamu? Yace yanzu, tace ok ina zuwa dakinta ta shiga ta canza kaya tasa jallabiya tare da yafa gyalen jallabiyan tayi kyau sosai sak balarabiya, ga kamshi dake tashi a jikinta falon ta nufa lokacin data fito ido ya kura mata yana murmushi ganin irin kallon da yake mata yasa ta danji kunya, kaman ya lura da hakan yace sis kinyi kyau tashi yayi ya janyota tare da daukansu hoto yana fadin bani da pics dinki dama, ya daukesu da yawa sannan yace ta bashi wayanta, mika mishi tayi yayi dialing no dinshi cikin nata, sannan ya kalleta yace bani no dinki na kasarku, murmushi tayi tare da fada mishi ya rubuta, sannan yace suje, motarshi suka shiga wacce cikin motan kaman daki seat din motar ma kanshi abun kallo ne, ga tv har biyu a manne a motan dayan camera ne amma sai yayi kaman tv duk wani abu da akeyi a waje yana kallo ta ciki, jawaheer ta kara tsorata dashi domin tasan lallai m samir ba karamin mutum bane lallai haduwansu hadin Allah ne, Allah ya amshi addu'anta dole ace ganinshi tashin hankali ne amma sai gashi Allah yasa ta ganshi cikin sauki, wani hawaye ne ya gangaro mata, jin hannunshi tayi akan fuskanta yana goge mata, lokaci daya ta dago kai suka hada ido, sunyi wajan minti daya suna kallon juna, kowa da abunda yake sawa a ranshi, shine yayi karfin halin kawar da idonshi tare da janyota jikinshi yana shafa mata bayanta yana fadin jawaheer mai yake damunki? Cikin wata irin murya tace ina farin ciki da Allah ya hadani dakai cikin sauki, lallai haduwa na dakai akwai wani boyayy...... Shuru tayi domin taji abun ya mata nauyi, yace inaji akwai me? Tace babu komai murmushi kawai yayi tsayawan motar ne yasa ta gane sun zo inda zasu, fita sukayi m samir ya kamo hannunta zasu shiga tare tayi sauri ta janye hannunta kallonta yayi ba tare da yace mata komai ba, ganin irin kallon da yayi mata alaman tambaya yasa ta fara fadin kar dad yaga ka riqeni zaice banda kunya, murmushi yayi sai yaji ta burgeshi sosai, haka suka shiga cikin gidan koda suka shiga ya nuna mata waje ta zauna gina ta fito suka gaisa ta kawo mata coffee jim kadan sai ga dad da m samir, dad ido ya kura mata ganin suna isowa yasa ta tashi ta tsaya a tsaye har dad ya karaso dad yace ta zauna mana zama tayi a dan takure tare da gaida dad din ya amsa cikin sakin fuska tare dayi mata tambayoyi akan iyayenta tana bashi amsa dad ya yaba da tarbiyanta sosai kuma yaji ta burgeshi dan haka ya saki jiki da ita yana ta janta da fira sosai, suna cikin haka wayanta yayi kara dubawa tayi taga mum ce dauka tayi bayan ta gaida mum cikin harshen hausa tace mum zan kiraki tare da kashe wayan, tana gamawa m samir yace ta tashi su tafi, wata leda ta ciro cikin jakarta ta ajiye a gaban dad tare da fadin dad kayi hakuri babu yawa, dad rasa bakin magana yayi lallai yarinyar nan tana da kirki tarbiya ladabi sannan al'adunta abun burgewa ne, dad yana ta mata godiya, har mota dad ya rakasu tare da fadin ta kulan mishi da yaro sannan in komai yayi dai2 shima zai zo nigeria haka suka tafi cikin jin dadi, suna mota m samir ya kira sunanta jawaheer ta dago suka hada ido tayi saurin kawar da ido, kara kiran sunanta yayi alama ta waigo ta kalleshi, kin waigowa tayi, ganin haka yasa ya janyota jikinshi suna hada ido ta rufe idanta wanda hakan ya bashi daman kallanta dakyau tare da aiyana abubuwa da dama a ranshi...... *maryam obam* *JAWAHEER* *STORY AND WRITEEN BY......* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA* *(maryam Obam)* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝* *{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}* *wattpad @maryam-obam* *WWW.Maryamobamnovels.com* https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/ *DEDICATED TO.....* *Nafisa mrs dan malikin kawo* Page 18 Gaba daya ya gama karema jikinta kallo yayin da duk wani sassa na jikinshi ya mutu wani irin yanayi ya shiga mai wuyan musaltuwa jawaheer tana da kyau na bugawa a jarida tana tarbiya wacce za'a so ace mutum ya sameta a matsayin mata sai dai kash baya jin sonta, idanshi ne ya sauka akan lebanta wanda kallo kawai zakai mata ka gane yana da laushi ido shima ya lumshe tunawa da ranan da yayi kissing dinta, bai taba shiga cikin wani irin hali mara misaltuwa ba kaman ranan duk da ba'a hayyacinta ya mata ba, inda tana cikin hayyacinta kuma da yardanta hakan ya faru da ya zaiji?.... Karan wayan jawaheer dinne yasa ta bude ido wanda shima yayi dai2 da bude nashi caraf suka kara hada ido wanda wannan karan sun kasa daukewa daka kallon junansu har wayan ya tsinke, shidai yasan baya son jawaheer sonia yake so amma yana jin wani abu a tare da jawaheer wanda bayaji akan sonia..... Karan kiran nata ne ya kuma katsesu wannan karan dauka tayi taga mum dinta, tace mum ...... Mum tace inata jira ki kirani kinki kira ya maganan dawowan naki gobe? Kallon m samir tayi taga yana danna waya, tace mum gobe zan dawo amma bana tunanin abuja zan sauka,mum tace kaman ya ina zaki? Tace yola zani mum tace what?... Kina da hankali kuwa uban me zakiyi a yola jawaheer wlh zanyi mugun saba miki, ki tabbata gobe kin sauka a abuja inba hakaba zaki hadu da fushina wlh, tace mum pl...... Kit mum ta kashe wayan jawaheer kallon wayan ta tsayayi tana mamaki toh miye abun zafi dan tace zata yola, bama an barta tayi wata daya bane a nan ai bata ma kai wata dayan ba, jin hannun m samir tayi a kanta yana fadin what r u thinking sis? Murmushi ta saki tare da fadin babu komai, a hankali ya furta nagode da kyautarki da kika ba dad dina i really appreciate it, bata fuska tayi tace nima fa dad dina ne, yaji dadin magananta, domin yana son dad dinshi duk wanda yake son dad dinshi toh shima yana son shi, a haka har suka karasa gida gidanshi ya shiga itama ta shiga nata. Yanzu karfe 8 na dare a kasar spain amma zukata biyu sun kasa sukuni domin kuwa ko wanne yana burin ganin dan uwansa, jawaheer tana mugun san ganin m samir cikin daren nan, haka shima ta gefenshi babu wacce yake burin gani sai ita amma shi a nashi ganin ya danganta hakan ne da daukinshi na zuwa nigeria kuma itace zata kaishi, tashi yayi yasa riga ya fita, tana kwance tana tunanin m samir taji ana mata nocking tashi tayi taga ita sai rigan bacci dai2 gwiwanta ta nufi kofa, tana budewa taga flower a wajan amma babu kowa, dubawa farayi ko zata ga mutum, amma bataga kowa ba dan haka ta dauki flower din tayi shuru lokaci daya kuma ta shiga ciki dashi, dan karamin kwalin data gani ta dauka ta fara karantawa kaman haka..... *Hey am hare missing you u r d best sister in d world* ido ta lumshe domin yanzu tasan waya ajiye mata wani irin farin ciki taji yana shiganta, wayanta taji yana kara da sauri ta nufi bedroom dinta ganin number din da yake kiranta yasa ta dauka da sauri amma saita tsinci kanta da kasa magana, muryanshi taji yana fadin kinyi kyau cikin night gown kiyi bacci da wuri kin san gobe zamu tafi, tace ok yanzu zanyi bada dadewa ba, murmushi yayi tare da fadin ok sis good night tare da kashe wayan, wani irin murmushin murna tayi tare da rungume wayar a jikinta sai kace m samir dinne a gabanta ta rungume haka, ranan bacci tayi cikin nishadi haka shima ta gefenshi. Washe gari tun karfe 7 jawaheer ta dan ta makara da sauri ta shiga toilet tayi alwala sannan tayi sallah tare da neman gafaran Allah, bayan ta gama ta shiga toilet tayi wanka tasa wata doguwar riga, tare da hada sauran kayanta, tana gamawa kiran m samir ya shigo wayanta dauka tayi da sauri tana gaidashi amsawa yayi cikin murmushi tare da fadin zan turo a dauki kayanki 9 zamu wuce tace ok, basu dade da gama wayan ba taji nocking dan haka ta nufi kofan ta bude security dinshi ne suka shigo suka kwashe kayanta yayinda suka rufe komai na gidan da farin kyalle gudun kar kayan suyi kura tunda za'a bar gidan, bayan sun gama ta bisu suka tafi gidan m samir tare a falo ta ganshi shida dad dinshi cikin girmamawa ta gaida dad din nashi ya amsa cikin sakin fuska tare dayi musu addu'an samun nasara akan abunda zasu nema, fira suka farayi har 9 din yayi suka fito inda dad din m samir yake ta fadama jawaheer ta kula da m samir domin ya yarda da ita, tace insha Allah, da haka har suka nufi Airport, nan mutane suka fara ihu ganin m samir yayin daya rike jawaheer a makale dashi yan jarida nata dauka domin suna ganin budurwanshi ce duk yanda sukaso yace wani abu amma bai ceba koda suka zo shiga jirgi daukanta yayi ya daurawa sannan shima ya hau suka haura tana gaba yana binta a baya, daka shi sai security dinshi guda goma suka shiga jirgin aka rufe domin private jet ne, kusa da jawaheer ya zauna basu dade da zama ba masu aikin jirgin suka zo tambaya mai suke so, kallon jawaheer yayi yace ta fadi abunda take so, coffee tace kawai shima yace a kawo mai coffee din, kallon juna sukayi sukai murmushi wanda a dai2 lokacin jirgin ya daga domin zuwa nigeria....... Hmmmm ku biyoni dan jin yanda zata kaya ga m samir a nigeria *maryam obam* *JAWAHEER* *STORY AND WRITEEN BY......* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA* *(maryam Obam)* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝* *{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}* *wattpad @maryam-obam* *WWW.Maryamobamnovels.com* https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/ *DEDICATED TO.....* *Nafisa mrs dan malikin kawo* Page 19 Sai wajan karfe biyu jirginsu ya sauka a airport dake yola, fita sukayi, suka fara tafiya yayin da security dinshi ke zagaye dashi, nan mutane suka ganeshi musamman matasa nan aka fara ihu tare da daukanshi hoto, yana ta daga musu hannu,haka har suka samu suka fita, motoci ne makil a waje sodoji ne da yan sanda suka zo daukansu da motoci na alfarma, tare suka shiga mota daya shida jawaheer, sannan security dinshi suka shiga sauran, hotel aka kaishi kai tsaye dan sun so su fara kaishi government house yace a'a su kaishi inda zai sauka yana son hutu, hotel din gaba daya aka mishi booking babu kowa a ciki sai su kadai an zagaye hotel din da jami'an tsaro, domin kuwa kasar spain ta bada ajiyan m samir ga gwamnatin nigeria, shugaban kasa da kansa yasa governor din yola yayi mishi komai da komai, jawaheer kam abun mamaki yake ta bata koda yake ba abun mamaki bane dan he is a biggest celebrity in d world wannan ba komai bane, sai da yakai jawaheer har dakin da zata sauka sannan shima ya shiga nashi mai kallon nata dakin, yana shiga ya fada toilet dan yin wanka, koda ya fito daka wanka, yasa boxer tare da daura jallabiya yayi sallah, koda ya idar cire jallabiyan yayi, kwantawa yayi dan ya huta, bai dade ba bacci ya daukeshi. Ita ko jawaheer tunda ta shiga dakin take jinta wani iri na farko dai ba yunwa takeji ba dan taci abinci a jirgi, sannan ita ba rashin lafiya ba, gadai ta nan ne dai, wannan ne zuwanta yola na farko duk da ya kasance garin iyayenta ne shi, amma bata taba zuwa ba, sau da yawa takan rasa mai yasa iyayenta basa son koda firan garin yola ayi musu, musamman ma mum tafi tsanan mahaifar tata, lallai akwai wani abu amma kodai miye kiyayyar tayi yawa haka, dan murmushi tayi tare da fadin may be ma ba wani babban abu ya faru ba suka dauki karan tsana suka sama garin tare da watsar da danginsu gaba daya dama ance fulani nada riko, tashi tayi itama tayi toilet tayi wanka, sannan ta fito tasa kananan kaya riga da wando, tare dasa hijab dinta dan yin sallah azahar, bayan ta idar ta dauko wayanta tasa sim dinta na nigeria, kaman jira ake kiran mum dinta ya shigo wayan kin dauka tayi dan tasan indai ta dauka tasan tana yola sunanta sorry, amma da tayi tunanin rashin fadama mum din nata zai iya daga musu hankali suyi ta tunanin tana ina, dan haka kiran na tsinkewa ta tura ma mum message kamar haka..... *mum na dawo nigeria amma kiyi hakuri ina garin yola nida m samir muka zo, mum ki tayani da addu'a burina ya cika a kanshi duk da nasan kina min, tana gama rubutawa ta tura mata* koda saqon ya shiga wayan mum ihu ta saki tare da tafa hannu tana fadin lallai jawaheer yau ta wuce gonarta ta nunamin ban isa da ita ba, dad dake zaune kusa da ita yace haba bilkisu miye haka mai kuma ya faru? Kasa magana tayi sai miqa mai wayanta tayi amsa yayi shima ya karanta, salati yayi tayi tare da fadin mai yasa jawaheer zatai haka? Mum tace dole in tafi yola ina tsoran kar tarihi ya mai maita kansa, dad kallonta ya tsayayi tare da fadin koma dai miye kiyi mata addu'a sannan maganan zuwanki yola bai taso ba zanje da kaina in dauko ta, mum tace a'a tare zamu tafi, ganin yanda ta dage yasa dad fadin zasu tafi taren amma gobe da safe, mum badan taso ba dan taso su tafi yau din nan kar abunda take boyewa ya fito fili. Washe gari tun karfe biyar su mum suka nufi airport dan mum ta matsa sosai,koda suka je airport din saida suka jira dan jirgin karfe 7 zai tashi, kallo daya zaka ma mum kasan tana cikin tashin hankali yau itace zata yola wanda a kalla shekara ishirin da wani abu da suka wuce rabonta da mahaifarta Wani irin hawaye mai zafi ne ya zubo mata a ido, shiga jirgi aka farayi suma suka tashi suka shiga, nan aka rufe jirgi ya daga zuwa garin yola. Jawaheer tunda tayi sallah asuba, tayi wanka tasa wata doguwar riga gaba daya tun jiya bata cikin yanayi mai dadi, ta rasa dalili ga gabanta dake ta faman fadi, jin nocking tayi dan haka ta tashi jiki a sanyaye ta bude kofar murmushi ya sakar mata yayin data lumshe ido dan kamshin turarenshi ya bugan mata hanci wanda yake kara sa taji ya narkar mata da zuciya, wani irin kyau taga ya karayi yi mata sosai, duk da bawai wani canji yayi ba hasali ma riga da wando ne jikinsa kaman kullum kananan kaya, duka babu wanda yayi ma dan uwansa magana sai itace tayi karfin halin fadin morning, bai amsa ba sai hannunta daya kama sukai dakinshi tare, bayan sun shiga ya zaunar da ita, ido ya kura mata tare da fadin jawaheer maike damunki? Daga kai tayi ta kalleshi taga shima din ita yake kallo dan haka tayi saurin yin kasa dakai tare da fadin babu komai kawai.... Sai kuma tayi shuru, jin muryanshi tayi yana fadin kawai me? Tace gabana keta fadi ban taba jin irin yanayin da nakeji yau ba, murmushi yayi tare da fadin ki yawaita fadin innalillahi wa inna'ilaihira jiun, kai ta daga alaman toh sannan ya kalleta tare da fadin zamu anguwan da dad dina ya fadamin tunda bakya jin dadi ki zauna muje mu dawo, kai ta girgiza tare da tashi tace a'a tare zamu duk inda zaka a cikin kasar nan ina tare dakai,murmushi yayi tare da jan hancinta sannan yace kinyi breakfast? Kai ta girgiza alaman a'a wayan dake dakin ya kira ya fadi abunda yake bukata, bai wani dade ba aka kawo abunda yace, tea da chips nd egg aka kawo, tare sukaci sannan suka fita, motocin da aka kawo su jiya nan suka shiga inda jawaheer ta fada musu inda zasu tace guyuk in anje kuma ace gidan liman, kai tsaye driver din suka nufi hanya, hannun jawaheer na rike dana m samir yana kallon garin yanayin garin ya mishi kyau in yaga abu bai gane ba saiya tambayi jawaheer ta fada mishi, da haka har suka iso anguwan, babu laifi anguwan nada kyau, da tambaya har suka isa kofar gidan, koda suka isa jawaheer ce ta fito tace bari ta fara shiga, yace a'a tare zasu, haka suka shiga cikin gidan,babu laifi gidan yana da kyau duk da ba wani girma gareshi ba, sallama jawaheer tayi, wata yar dattijuwa ta amsa tace waye? Ku shigo, bayan sun shiga jawaheer taga tsohuwar fuskanta dauke da glass dam taji gabanta ya buga da karfi domin sak fuskan mum dinta sai dai kuma wannan tsohuwa ce ita ta girmi mum dinta sosai lokaci daya ta shiga rudani....... *maryam obam* *JAWAHEER* *STORY AND WRITEEN BY......* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA* *(maryam Obam)* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝* *{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}* *wattpad @maryam-obam* *WWW.Maryamobamnovels.com* https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/ *DEDICATED TO.....* *Nafisa mrs dan malikin kawo* Page 20 Muryan matan ne ya katse jawaheer daka duniyar tunanin data fada, tace sannunku ku karaso mana, wani karamin falo ta kaisu wanda daka gani an ware shine dan ajiye baki, falon sai kamshin turaren wuta yakeyi, jawaheer dai bin matar take tayi da ido, domin abubuwa ne fal a cikin ranta, fita tsohuwar tayi jim kadan sai gata da ruwa ta kawo musu, pure water mai sanyi, sannan ta zauna tare da fadin bismillah, m samir kallon jawaheer yayi wacce idonta nakan wannan tsohuwar,kafin yayi magana yaji matar na fadin sai dai ban shaida ku ba, cikin harshen hausa take magana, m samir bai san mai take fada ba dan haka ya kalli jawaheer tare da fadin tayi mata bayani, jawaheer tace da fatan mun sameki lfya hjy, amsawa tayi da fadin lfya qlau, sannan jawaheer tace dama mun zo neman khausar ne, da sauri matar ta tashi tare da kallon jawaheer lokaci daya kuma ta fashe da kuka tana fadin maiya kawo ku, waya turoku, mai kuka zoyi nan? Mai yasa zaku tunamin da ciwon da yake zuciya ta wanda ya kasa warkewa, kodai ku yan uwan muhd ne wanda ya bata min rayuwan yarinya, baxan taba yafe mai ba shine mutum na farko daya tarwatsa min a halina, ku tashi ku fita, m samir da bai san abunda ke faruwa ba sai kallon jawaheer yake amma yaga kaman matar fada take dan yanda take magana kadai ya isa ya nuna mishi hakan, jawaheer tace kiyi hakuri hjy wlh bada wata manufa muka zo miki ba, hasalima....... Dakata yar nan bana son jin duk wani abu da kuka zo dashi ku tafi kawai ku barni, jawaheer tace dan Allah ki saurare ni wannan da kike gani dan khausar ne kuma jikanki, gaba daya tsayawa tayi tana kallon jawaheer alaman ban san yaudara, kai jawaheer ta daga mata tare da fadin yaron muhd ne wannan a gabanki sai dai baya jin hausa, sai yaren kasar su spanish ko turanci, da sauri ta rungume m samir tana kuka tare da fadin ina kaje wajan shekaru ishirin da suka wuce a ina ka rayu, m samir farin ciki ne fal cikinsa tunda yaga ta rungumeshi alaman sunyi nasara kenan, kuma ya tabbata zaiga mum dinshi yanzu, sakin m samir tayi sannan ta kalli jawaheer tace yar nan fadamin a ina ya taso, nan jawaheer ta fara bata labarin abunda ya faru wanda dad din m samir din ya fada mishi da yanda abubuwa suka faru a baya tare da satoshi da yayi har ya girma a wajanshi, kuka ta kuma saki tare da fadin lallai muhd shine silan tarwatsa min dangina, amma babu komai munyi imani da kaddara wanda a wancan lokacin muka kasa fahimta, shigowan su mum gidan yasa jawaheer da tsohuwar suka fita shima m samir ya rufa musu baya, jawaheer tace mum dad mai kuka zoyi nan? Mum kam kuka takeyi yayin da matar itama take kuka tana fadin bilkisu dama kina raye, gaba daya jawaheer ta shiga rudani sosai dan haka ta matsa wajan dad dinta tana fadin dad maike faruwa ne? Dama sun san juna ne? Dad bai iya magana ba balle ya iya bata amsa, matar ta kamo hannun m samir ta hada dana hjy bilkisu tace ga danki nan bilkisu, jawaheer wani irin duhu ta gani ya rufe mata ido hannu ta daga tana fadin dama yaya nane kai jini nane kai mum dinmu daya ash..... Tif tayi kasa sumamma da sauri sukayi kanta suna fadin jawaheer musamman ma m samir da yafi kowa rudewa lokaci daya domin duk maganan da sukeyi babu abunda ya fahimta dan da hausa sukeyi sai dai ya gane mum itace mum dinshi, ruwa tsohuwar ta dibo ta fara yayyafa ma jawaheer amma ko motsi batayi ba, dan haka hankalinsu ya kuma tashi sosai dad ne yayi karfin halin fadin mu kaita hspt, jin an fadi hspt yasa m samir ya fahimta dan haka ya dauketa cak sukai mota ya shigar da ita yace ma security dinshi suje hspt mafi kusa, tafiya kadan sukayi suka isa wani asibiti inda akai emergency da ita domin ceto rayuwanta, mum babu abunda take sai kuka tare da fadin jawaheer insha Allan babu abunda zai sameki kuka take sosai gaba daya ta kasa zama, shiko m samir gaba daya ya rasa maike mishi dadi, ganin irin kukan da mum take yasa ya nufeta yana bata hakuri lokaci daya ta janyo m samir ta rungumeshi tana kuka mai cin rai, yau ya kamata ace ranan farin ciki ne a rayuwanta amma kash abubuwa sun jagule, ga danta Allah ya hadasu, ga jawaheer a asibiti rai a hannun Allah, sunyi wajan awa daya kafin dr ya fito da sauri m samir ya nufeshi yana tambayan ya jikin nata, yace suje office dinshi, binshi sukayi har office dr din sai kallon m samir yake yana mamaki kaman ya sanshi m samir ne ya katseshi da fadin dr ya jikin nata? Dr yace munyi iya kokarin mu sauran sai a barma Allah, dan harta farka tana fadin ashe yayana ne shikenan burina bazai cika ba, nono daya muka sha...... Tana cikin fadin haka ta kara suma ko numfashi baya fita amma yanzu mun sa mata oxygen numfashin ya fara fita, gaskiya tana cikin mugun damuwa wanda ba'a so mutum yakai irinshi domin sai anyi sa'an gaske mutum yake tashi idan yayi irin wannan abun, dayan biyu ne ko ka tashi da ciwon barin jiki ko kuma zuciyarka ta buga ka mutu, yanzu dai sai mu jira ta farka mu gani, hankalinsu gaba daya ya tashi m samir wani irin son jawaheer yaji yana shiganshi wanda bai taba jin irinshi ba sai a yanzu amma yana ganin hakan a matsayin dan tana kanwarsa ne jininsa wanda saida dr yayi bayani ya fahimta dan da turanci yayi, ashe duk son da take mai ashe yayanta ne shi lallai Allah mai iko ne, mai kuma yanda yaso, mum zuciyarta cike take da damuwa dad ma kam ba'a magana dan yafi kowa shiga cikin damuwa domin yar lelenshi wacce yafi so kaf yaranshi itace yau a kwance a gadon asibiti tana cikin yanayin rayuwa ko mutuwa gashi dr yace babu tabbaci, lokaci daya ya kalli mum yace anya ba zamu fitar da ita waje ba? Idan wani abu ya sami jawaheer bazan iya juran gani ba,mum tace nima haka nake tunani muyi magana da dr din. Koda aka fadama dr shawara ya basu akan suyi hakuri har zuwa gobe su gani sannan koda wajan suka kaita babu abunda zai canza, tare da fadin gwara ma suyi hakuri su barta a nan, dad yace bari dai suga zuwa goben tare da tambayan dr zasu iya ganinta? Yace eh su shiga amma karsu dameta da hayaniya, shiga sukayi dakin gaba dayansu, tana kwance akan gadon dakin ansa mata oxygen baka jin karan komai saina oxygen din da karan ac duk da ac a kunne yake jikinta babu abunda yake sai zufa, lokaci daya fuskanta yayi fayau tayi rama kaman wacce tayi ciwon kwana biyu bakinta yayi fari, mum ta kalli dad cikin kuka tana fadin kalli yanda ta koma yanzu2 anya jawaheer ba mutuwa za tayi ba, na shiga uku ni bilkisu....... Kuka yaci karfinta sosai dad ya jata suka fita m samir shima kukan yake tare da share mata zufan dake goshinta jikinta yayi wani irin dumi gashi kuma kaman babu jini yanda yaji jikin nata yayi wani irin tashin hankali ya kuma shiga tare da fadin wani irin ciwo ne haka lokaci daya?kallan fuskanta yayi yaga tayi haske tayi fayau gabanshi yaji ya fadi tare da fadin no zaki rayuwa my sister kuka ya saki sosai...... *maryam obam* *JAWAHEER* *STORY AND WRITEEN BY......* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA* *(maryam Obam)* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝* *{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}* *wattpad @maryam-obam* *WWW.Maryamobamnovels.com* https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/ *DEDICATED TO.....* *Nafisa mrs dan malikin kawo* Page 21-22 Jawaheer kam ko motsi batayi, m samir iya tashin hankali ya shiga gaba daya ya fita cikin hayyacinsa, mum ce ta shigo dakin domin a lokacin anata kiran sallah la'asar, kama hannunshi tayi wanda ya rike na jawaheer dashi, dagowa yayi da sauri wanda yake zargin jawaheer dince amma sai yaga sabanin hakan, mum ce cikin kuka take mai magana cikin harshen turanci tace kaje kayi sallah,baiyi magana ba sai tashi da yayi ya fita dan yin sallah, haka su mum sukai ta zama amma shuru bata farka ba, abun ya damesu sosai gashi har wajan karfe biyar yanzu gaba daya hankalinsu a tashe yake, mahaifiyar mum ce tace nikam bilkisu itama wannan din yarinyar kice? Mum zatai magana taga kaman jawaheer tana motsi da sauri ta nufeta tana kiran sunanta tare da fadin jawaheer ganin idon jawaheer din a bude yasa ta furta alhmdlh da sauri ta fita lokacin su dad na waje da m samir dad na ganinta yace bilkisu lfya kuwa? Tace ta farka zan kira dr ne, dad yace bari in kira shi, m samir da mum suka koma dakin, m samir suna shiga ya nufeta ganinshi yasa ta sakar mishi murmushi amma ta kasa magana, shima ya kasa furta mata komai sai murmushi da yake ta sakar mata shima, dr ne ya shigo dakin wanda yasa m samir niyan barin wajan amma ta rike mai hannun alaman ya tsaya, dr ganin haka yayi murmushi tare da fadin lovers, matsawa dr din yayi ya fara dubata tambayanta ya farayi amma bata bashi amsa da baki sai dai ta daga mishi kai kota girgiza mai kai, hankalinsu ya tashi sosai ganin taki magana dad yace dr mai yasa bata magana? Dr yace nima abunda nake son sani kenan amma karku damu zatayi, dr yace amma alhmdlh jikin da sauki nayi mamaki ta tashi ba tare da wani matsala ba, gskya ku kara godema Allah, dad yace toh dr ni yanzu magana kawai nakeso tayi, dr yace madam kice wani abu plz, ido ta lumshe alaman karma ya dameta, mum ta matso kusa da ita, tana fadin jawaheer plz kiyi magana, bude ido tayi ta kalli mum lokaci daya hawaye ya zubo mata sannan bakinta ya fara rawa tace mum, kowa ya kura mata ido ta kara matse hannun m samir sannan taci gaba da fadin mum m samir danki ne na cikin ki? Mum dan Allah ina son sani ance sunan mum dinshi khausar ba sunanku daya ba mum dan Allah ki fadamin maike faruwa wlh mum ban san mai yasa na tashi ba amma haka Allah ya tsara dan Allah mum ki fadamin miye tsakaninku ko zuciyata zata samu salama daka radadin da takeyi a halin yanzu, mum kuka ta farayi tare da fadin jawaheer zan fada miki komai kaman yanda kike son ji duk da banso fada miki ba, amma inason in kinsan gskya karki juyamin baya karki gujemu duk rintsi duk wuya....... TUNA BAYA..... Garin yola garine na fulani mu uku iyayena suka haifa a duniya ni daya ce mace a wajansu, yayyina maza ya abubakar sai ya abdullahi saini bilkisu wacce naci sunan kakata ake cemin khausar, mahaifina mlm kabiru shine limamin anguwanmu mutane suna girmamashi mahaifiyata kuma nafisa, muna kiranta da adda, ita daya ce wajan mahaifinmu duk wani gata da dan gata yake samu suna nuna mana duk da alokacin ba'a karatun boko bawai ba'ayi bane a'a anayi sai dai ba'a bashi muhimmanci, mahaifina koda haiyuwa akayi kasancewan shine liman shine yake radama yaro suna, sannan komai mai gari zaiyi saida saninshi, tunda na taso nake tallan nono domin wannan dabi'an fulani ne musamman wanda suke kauye, akwai dan mai gari wanda yake sona bayaji sosai gashi kashe mutum a wajanshi ba komai bane, sannan iyayena tun ina karama suka bashi ni dan haka irin tasu al'adan yake ana haifanki za'ayi kamunki, a bama wani ke ma'ana anyi miki miji tun kina karama, gashi kuma koda bakwa son juna baku isa ku karya alkawari ba, tunda na taso na tsani auwal, gashi yana bala'in sona, ko yazo wajena bana wani bashi fuska, akwai wani ma'aikata da nake kai nono inda na hadu da muhd mahaifin samir lokaci daya muka saba harya fara koyamin turanci daka baya ya fara sona, ya sami mahaifina akan yana sona, inda ya nuna mishi bazai hada zuri'a da farin fata ba wato bature bai fito ya fada mishi anyi min miji ba, babu yanda baiyi ba amma mahaifina yaki, irin son da muke ma junanmu wata rana naje wajanshi dan saboda shi gaba daya aka hanani tallan nono, na sata jiki naje, inda mukaci kukanmu har yakai daya fara ban hakuri yana sharemin hawaye sanadin da shaidan ya rinjayemu kuka ta saki sosai sannan taci gaba mun aikata sabon Allah, tunda na tafi ban kara fitowa ba har saida aka gano inada ciki hankalin iyayena ya tashi sosai nan sukai ta buguna tare da yayyina inda sukace in ban fadi wanda yamin ba sai sun kasheni, jin naki magana sukace wlh zuwa dare in ban fadaba sai an jefeni gashi kowa a gidan lokacin ya shareni babu maijin tausayi na, haka na sata jiki na samu muhd nake fada mishi abunda ya faru, mai makon inga yayi fada sai daga hannu yayi yana godiya tare da fadin rabo rabo lallai koba ta hanyar aure ba inda rabo sai an samu, kuka na fara mishi akan yabar garin dan wlh zasu iya kasheshi da farko yaki yarda sai dakyar ya amince dan saida na mishi alkawarin baza'a zubar da cikin ba sannan yabar kasar gaba daya, haka na koma gida iyayena suka kara rufeni da duka kaman zasu kasheni waina dauko musu abun kunya, in ban fadi wa yayi min ba sai sun kasheni, da naji wuya tare da tunanin muhd yabar kasar ma yasa na fada musu wanda yamin sun shiga tashin hankali sosai, gashi anje inda yake aiki ance yabar kasar, haka iyayena sukace a zubar da cikin naki yarda babu irin abunda ba'ayi ba amma cikin yaki zubewa, har yan gari suka san labarin abun kunyan dana aikata ko waje bana fita dan gori da zaki abun bama ni daya ba harta iyayena ana musu gori wanda hakan yasa aka cire mahaifina daka liman akaba wani, abun yama mahaifina ciwo wanda hakan yasa kaf yan gidanmu suka kara tsanata har gwara adda tana tausayamin in babana baya gida, ana haka har na haiyu cikin rashin gata, har nayi arba'in cikin dakin datti nake kwana da yarona, kwananshi arba'in da daya a duniya na nemeshi na rasa, nan aka dauka mahaifina ya kashe yaron ya boye, aka tsanemu a garin da kyara zagi wanda mahaifina yayi zuciya tare da fadin inbar gidan sannan inna kara zuwa mai gida Allah ya isa bai yafe min ba, babu irin hakurin da adda bata bashi ba amma yace inta kara magana a bakin aurenta, haka tana gani na tafi yayyina sune masu kara zugawa waina dauko musu abun kunya basa iya shiga cikin mutane, haka nabar gidan cikin dare banda kudi banda kowa, duk wannan abunda akamin ban damuba kaman rashin yarona wanda nake gani kaman mahaifin nawa ne ya daukeshi dagaske din, gaba daya na kara tsanan zaman kauyen ma tare da fadin gwara da aka koreni ma, haka naita tafiya cikin dare harna bar anguwanmu ina cikin tafiya ne cikin sauri saboda tashin hankali ko gajiya banyi ba, wata mota ta rugo a guje saura kadan ta bugeni, Allah ya taimaka, mutumin ya fito yana fadin haba baiwar Allah miye hka bakya duba hanya gashi cikin dare ina zaki, nace duniya zan shiga, yace subhanallah, haba baiwar Allah mai yayi zafi haka, kuka na saki tre da bashi labarin abunda ya faru ya tausayamin sosai inda yace in shiga motarshi muje ban musa ba na shiga sai naga ya nufi anguwarmu, direct gidan mai gari mukaje inda yayi2 in fito naki, haka ya shiga jim kadan saiga mai gari da mutane sun fito inda akasa na fito dole, mai gari yace wannan yar iskan zaka aura bawan Allah ko dai kaine ka mata ciki? Yace wlh ko daya, nan aka tura aka kira mahaifina bayan yazo ya ganni yace baya kaunar ganina, mai gari yace ya nutsu nan aka mishi bayani inda yace shiba mahaifina bane ya sallamani zan iya yin duk abunda naga dama tare da fadin har abada baya bukatar ganina,haka mai gari ya daura mana aure da mutumin da ba'asan ko waye ba...... *maryam obam* *JAWAHEER* *STORY AND WRITEEN BY......* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA* *(maryam Obam)* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝* *{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}* *wattpad @maryam-obam* *WWW.Maryamobamnovels.com* https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/ *DEDICATED TO.....* *Nafisa mrs dan malikin kawo* Page 23-24 Babu abunda nake sai kuka, bayan an gama daurin auren mai gari ya kalleni yace daka yau kar in kara shigowa wannan garin domin kar in lalata musu yara, haka muka tafi muka bar garin cikin dare, babu komai a raina sai tsanar garin da yan garin tare da mahaifina, haka muka shiga cikin garin yalo inda anan gidan mijina yake duk da bamai karfi bane sosai amma yana da rufin asiri yana da mota golf guda biyu daya ana mishi haya daya kuma shi yakeyi da kansa, yayi karatun boko rashin aikin yine yasa ya fara jan mota, iyayenshi sunyi mamakin auren da yayi amma da yake suna da tawakkali duk da abun ya bata musu rai ace yayi aure bada saninsu ba, haka suka hakura dan mamanshi ta dade da rasuwa wajan matar babanshi ya taso, suna nunamin gata sosai haka shima duk da yasan labari na, ina mamakin mai yasa ya yarda ya aureni, wata rana muna fira yake fadamin wai ya taba ganina ina tallan nono tun daka lokacin yaji yana sona, amma sanin al'adun mu na fulani yasa ya boye komai dan yasan kauyenmu kana jariri ake maka miji, sai kuma gashi yanzu kin zama matata, ina kokarin kyautata ma mijina, domin kaf duniya banda kamanshi dan ina ganin yafi kowa kaunata, shekara daya da aurenmu na haifi dana namiji santalele inda aka sa mishi sunan baban mijina wato umar, lokacin daya cika arba'in matar data riqe mijina ta rasu, munyi kuka sosai, tun bayan rasuwanta baba shima ya fara ciwo sosai, tsakaninsu wata uku shima ya rasu, kai munji mutuwar baba sosai, inda gaba daya zaman garin yalo ya ishemu dan dama ni bana son garin ina dai zama ne kawai, haka muka tattara muka koma kaduna muka sami gida muna haya, shekara biyu tsakani na kuma haifan da namiji muka sa mishi khalil, a lokacin mijina ya sami aiki a banki, lokaci kadan rayuwanmu ta fara canzawa, daka wajan aiki aka dawo dashi abuja inda aka bamu gida karami za'a dinga cirewa cikin kudin aikinshi, haka muketa rayuwa cikin kwanciyan hankali tunda na haifi khalil ban kuma samin ciki ba, abun yana damuna dan ina son samun yarinya mace, su umar har sun fara zuwa makaranta, wata rana munje anguwa nida mijina, motarmu tayi faci, nan ya fara kwance taya yana gyarawa ni kuma ina tsaye kusa dashi saiga wata mata tana ta gudu da alaman wasu ne suka biyota, tana zuwa wajanmu ta mika ma mijina kwali tana fadin dan Allah gashi akwai komai da komai a ciki ka ceci rayuwar yata daka fadawa halaka, tana fadin haka tabar wajan ta wuce da wajan minti biyar lokacin har mun shiga mota muna jimami tare da fargaban maita bamu, saiga wasu mutane da makamai sunzo sun wuce da gudu suna fadin miyi sauri karta bace mana, jin haka yasa muka gane kasheta suke son yi, haka muka karasa gida muka shiga da kwalin budewan da zamuyi muka ganki kina bacci abunki tare da magudan kudade dollars na amurka, mun tsora sosai wata takarda muka gani anyi rubutu kaman haka..... *salam ga duk wanda ya tsinci wannan yarinyar inaso ya riqemin ita amana wlh yar sunna ce bata hanyar zina aka sameta ba banda lokacin yin bayani sosai kar lokaci ya kure min, sunanta jawaheer duk wanda ya dauketa yayi amfani da wannan kudin na bashi halak malak, idan na rayu zan dawo neman yata wata rana in kuma sun kashe ni, shikenan* kallon juna muka fara nida mijina yace bazai dauki kudin ba zai kaiki wajan police dan yana tsoro ni nayi ta nuna mishi yayi hakuri mu taimakeki mu riqeki amanace mahaifiyarki ta bamu, da farko kaman taso ta ajiye kine sai Allah ya hadamu ta bamu, dakyar ya yarda lokacin da mukaje canzo kudin naira million dari ne kudin dai2 wlh munyi mugun firgita da yawan kudin, tun daka lokacin ya fara business da kudin yabar aikin banki rayuwa ya canza mana sosai, wlh jawaheer ina masifar sonki na dauki son duniya na daura miki haka mijina da nake ganin yafi kowa sonki domin yace tunda ya sameki Allah ya bude mishi kofofin arziki baya son ganin fushinki ko kadan munsha yin fada akanki nida shi, idan kikai abu na miki fada to in raina yayi dubu saiya baci sai yasa kika fi sabawa dashi dan yana yawan tafiya dake wlh ina takaicin fada miki bamu bane muka haifeki..... Kuka jawaheer take sosai lokaci daya ta fara fadin yanzu ba'asan inda iyayena suke ba, na shiga uku shikenan bani da wani gata a duniya mai yasa mum dina bata tafi dani ba, anya ma ta auren aka sameni kuwa kaman yanda ta rubut.... Mum ce ta toshe mata baki duk wanda ke wajan saida ya tausaya mata m samir shima hawaye yake amma bai bari sun gani ba dan da turanci mum ta fada mata komai, wani irin tausayin jawaheer yaji yana shiganshi sosai, shi gashi yaga mahaifiyarshi tare da taimakonta lallai shima ya zama hakki a kansa ya neman mata iyayenta, lokaci daya ya kalli mum yace mum babu wani shaida da za'a gane inda iyayenta suke? Mum tayi shuru can tace akwai international password da hotan mamanta a jiki, da sauri yace yana ina?? Mum tace yana gida abuja, yace mum plz mu koma yau can abuja din, mum tace dare yayi sai dai gobe, jawaheer kam bata komai sai kuka, adda itama fa fara rarrashinta tare da fadin yakamata tayi tawakkali insha Allah zaki ga iyayenki, dakyar jawaheer tayi shuru amma babu komai a ranta sai tarin bakin ciki da takaici yanzu basu dad banr iyayenta inta tuna hakan sai taji kaman tai ihu dan baki ciki, muryanta su mum sukaji tana fadin international password din wani kasa ne? Mum tace saudiya sannan ina tunanin itama yar can ne dan balarabiya ce ita, jawaheer bata kuma cewa komai ba, inda mum take tambayan adda ina mahaifinta adda tace hmmm labari mai tsawo amma bari in baki....... *maryam obam* *JAWAHEER* *STORY AND WRITEEN BY......* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA* *(maryam Obam)* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝* *{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}* *wattpad @maryam-obam* *WWW.Maryamobamnovels.com* https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/ *DEDICATED TO.....* *Nafisa mrs dan malikin kawo* Page 25-26 Mum tace maiya faru adda?? Adda tace bayan kin tafi na bujire ma mahaifinki akan bazan yarda ba dole a dawo dake gida yace sai dai in biki in kuma na biki a bakin aurena, muna zaune aka kirashi mai gari, bai dawo ba sai can cikin dare yazo yana fadin an miki aure kuka nasa ina fadin haba mlm kai yanzu baka san kaddara ba? Wlh abunda ka aikata ko wanda baije islamiya ba bazai aikata ba, kaine limamin wannan garin mlm mai yasa bazaka dauki kaddara ba? Mai yasa zaka yanke wannan danyan hukuncin wlh mlm ka manta da nauyin dake kanka na amanar da Allah ya baka na yaranka, yanzu da kuka mata aure kasan wata aura?? Miye sana'an mijin?? Dan gidan mutunci ne?? Duk baka saniba, kai dai burinka tabar inda kake saboda kunyar data dauko mata wanda bai wuce ya fada kan kowa ba, mlm ina iliminka?? Da har zaka bari wai magan ganun mutane suyi tasiri akanka harka manta da kaddara bayan Allah yace muyi imani da kaddara khairan wa shairan, Kai ka sani ko wannan jarabawan da Allah ya maka inka jure shine silan shiganka aljanna, amma saika kasa jurewa....... Kuka mlm ya saki yana fadin kaico na kaico na lallai yau na yarda da manzon Allah yace gwara ka auri mace mai addini, yau gashi matata ta tunasar dani abunda na manta saboda kunyar duniya , yau idan Allah ya dauki rayuwa na mai zance mishi, lallai ban kyauta ma bilkisu ba, ban mata adalci ba, yanzu ina zan ganta?? Adda cikin kuka tace nasan ganinta zaiyi mana wuya amma ni burina ka gane ka kuma fahimta amma alhmdlh tunda ka gane, nasan ko mu dade ko mu juma wata rana zata dawo garemu insha Allah kawai mu tayata da addu'a duk inda take Allah ya kareta, abun ya mata yawa ga batan yaronta ga koranta da akayi kai wannan wani irin ibtila'i ne, mlm yace wlh koni inayi mata duk abunda nayi bada son raina ba, lallai nayi dana sani wanda bashi da amfani a yanzu Allah yasa mijin data aura ya riqemin ita da amana, adda tace ameen ,mlm yace zanyi ta bincike har in gano inda take, adda tace Allah yasa a dace, tun daka wannan ranan mlm yake ta tunaninki kullum burinshi ya ganki yaga wani hali kike ciki, abubakar yayi aure yana da yara biyu, maryam da abdullahi sunan yayanki aka samai suna kiranshi da hamman, shi kuma abdullahi ya sami aikin mota yana zuwa gari2 yayi hatsari ya rasu munji mutuwarshi sosai, abubakar yake mana komai na rayuwa duk da shima bawai yana da wani karfi bane, mahaifinku ya saida shanayenshi ya gyara gidan nan tare da fara sana'a a kasuwa yana saida su hatsi wanda shida abubakar suke zaune suke saidawa tunda babban shago ne, duk da mahaifinki ba wani lfya gareshi ba kullum burinshi ya ganki ko ya sami labarinki amma shuru har yanzu, kinji abunda ya faru bayan tafiyanki, amma bilkisu ban taba tunanin zaki rabu damu ba tsawon wannan lokaci, tace adda kiyi hakuri wlh ina son inzo duk da nasan har yanzu baba yana fushi dani, amma inna tuna shida kanshi ya koreni sai inji bana son zuwa amma kullum kuna raina kuma kuna cikin addu'a na koda yaushe, Allah sarki ya abdullahi lokaci yayi Allah yaji qanka ashe bazamu sake haduwa ba, adda ta kalli dady tace Allah ya biyaka yanda ka riqe min yarinya tsakani da Allah kaima Allah ya baka abunda kake nema duniya da lahira, dady ya amsa da ameen. Jawaheer kam kallonsu take Amma ita daya tasan abunda take saqawa a ranta, shiko m samir idonshi na kanta gaba daya tausayinta yake ji, ya rasa dalili mai yasa yake jinta a ranshi yanzu, amma ta wani gefen yana ganin kaman tausaya mata yake dan shima ya taba shiga irin halinta na rashin mahaifiya lokacin da yasan mum dinshi na raye ba karamin ciwo yaji abu, itace ta zauna kusa dashi tare da kwantar mai da hankali wanda gashi yau sun hadu da mum dinshi duk ta sanadin jawaheer din, gashi kuma sanadin haduwanshi da mum dinshi yasa jawaheer tasan basu bane iyayenta, ido ya lumshe tare da fadin no matter what i will stay by ur side, jawaheer matsawa yayi kusa da ita, kallonshi tayi ta sakar mishi murmushi wanda bata san ya fito ba, shima murmushin ya sakar mata tare da fadin ya jikin naki? Tace naji sauki sai dai bana jin dadin zama a nan, inaso in koma abuja, yace kiyi hakuri gobe zamu tafi, kai ta daga mai alaman toh, adda tace bari inje gida dare yayi kar mlm ya dawo yaga bana nan,nama san yana gidan yanzu inna koma a kawo abinci, dady yace ki bari adda zamu siyo yanzu, nima inaso inga mlm ya kalli mum yace bari muje, jawaheer tace dad, cikin sauri duka suka kalleta, tace kuje da mum itama nasan tana bukatar ganin kakana, kowa dake dakin saida yaji tausayinta, mum tace a'a babu inda zani dawa zaki zauna, tace mum naji sauki kuma m samir zai zauna dani kije kiga kakana, mum wani hawaye ne ya zubo mata tare da zuwa wajan jawaheer ta rungumota tana fadin dan Allah duk wuya karki barni jawaheer ban taba banbantaki da yaran dana haifa ba, jawaheer ina sonki haiyuwanki ne kawai banyi ba amma wlh baki da banbanci da yarana, jawaheer itama cikin kuka tace insha Allah mum bazan taba gudunki ba, bani da wata uwa saike.... Kuka yaci karfinta dakyar ta seta kanta tace mum kije dare nayi, mum kallon m samir tayi tace ka kula da ita nima anjima zan dawo tare zamu kwana da ita, yace ok, sannan suka fita. Bayan sun fita m samir ya zauna kusa da ita, ido ya kura mata tare da fadin jawaheer kibar kukan nan haka, ya isa, murmushi tayi tare da fadin yana da amfani domin shine kawai nakeyi inji dadi, ido ya kura mata ganin irin kallon da yake mata yasa ta juyar dakai gefe, kirjinta yana buga mata da karfi duk sanda suka hada ido jin muryanshi tayi yana fadin bakya jin dadi in kina tare dani?? Da sauri ta waigo suka kara hada ido wani tambayan ya kuma jefo mata yace jawaheer mai kikeji in kina tare dani?....... *maryam obam* *JAWAHEER* *STORY AND WRITEEN BY......* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA* *(maryam Obam)* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝* *{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}* *wattpad @maryam-obam* *WWW.Maryamobamnovels.com* https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/ *DEDICATED TO.....* *Nafisa mrs dan malikin kawo* Page 27-28 Idonshi nakan nata yana jiran yaji mai zata ce, yayin da ita kuma tambayan yazo mata a bazata, dan haka yasa ta kasa koda motsa baki balle ta bashi amsa, ganin irin yanayin data shiga yasa ya hura mata iska a fuska wanda yasa ta lumshe ido da sauri, ido ya kara kura mata yana dan murmushi tare da fadin jawaheer kina da kyau sosai, da sauri ta bude ido dan ta gani ko shi dinne dagaske yake fada mata haka, ido ya kashe guda daya kaman yasan abunda yake ranta, yace kina mamaki koh? Gaskiya nake fada miki, kina da kyau mai daukan hankali jawaheer tun sanda na ganki naji kina min kama da larabara ina mai kyautata zaton kina da jini da larabawa, duk namijin daya sameki zaiji dadi sosai, sannan duk wanda ya aureki zanja mishi kunne ya riqemin ke da kyau, wani iri taji domin magananshi ta karshe ya nuna mata bawai yana sonta bane, jin tayi shuru yasa yaja hancinta tare da fadin jawaheer kin sani cikin farin ciki sosai ta sanadinki yau gani ga mum dina, kema Allah ya nuna miki iyayenki, kai ta girgiza tare da fadin bana bukatar ganinsu har abada zanyi rayuwa na ni daya ba tare dasu ba, ido ya kura mata ganin irin kallon da yake mata yasa ta juyar da kanta gefe, yace har cikin zuciyarki kike fadan wannan maganan?? Shuru tayi ba tare da tace komai ba, yace ki bani amsa, kuka ta saki tare da fadin mai zance da yafi wannan? A da ina farin ciki sosai tare da iyayena, amma lokaci daya komai ya canza min tunda nasan basu bane iyayena, ina mamakin mai yasa mum dina ta bada ni, ta tafi ta barni...... kuka yaci karfinta sosai janyota yayi jikinta ya rungumeta yana bata hakuri akan tayi shuru, dakyar ya samu tayi shuru, yace jawaheer inaso koda yaushe ki kasance maiyi ma kowa uzuri, karki yanke hukunci akan abunda baki san miye asalin faruwanshi ba, haka kawai mahaifiyarki ba zata bada keba, lallai akwai wani abu a labarinki, wanda hakan ya zama dole mu nemi mum dinki, jan jikinta tayi a nashi tace nemanta bashi da amfani bani da wani buri daya wuce in sami namijin da nake so, shima yana so na, wanda za muyi rayuwa cikin jin dadi sai sai kash, hakan bamai yihuwa bane, ina tunanin barin kasar nan gaba daya inyi nesa da kowa na wani lokaci, ido ya kura mata yana kallonta harta gama, yace har dani za kiyi nesa dani? Shuru tamai ba tare data bashi amsa ba, yace ina jinki jawaheer? Tace ni kawai so nake in huta, yace ba amsan da nake son jiba kenan, satan kallonshi tayi amma sai akayi rashin sa'a shima din ita yake kallo caraf suka hada ido, ya daga mata akai alaman ina jinki, tace nifa bance zanyi nesa dakai ba, murmushi yayi yace gashi kince za kiyi nesa da kowa, tace ni banda kai nake nufi, wannan karan dariya yayi tare da fadin jawaheer bazan taba barinki ba har sai na sadaki da mum dinki wannan shine alkawarin dana daukan miki, wani hawaye ne ya zubo mata tace mai yasa zaka min haka? Yace saboda u r my sister my best friend, ke kawata ce daka yanzu, wani irin murmushi ta saki lokaci daya tare dayin hugging dinshi tana fadin thanks alot. Bayan su mum sunje gida dad yaba driver kudi yace yasai abinci yakai masu jawaheer, sannan suka shiga cikin gidan, koda suka shiga falon baki suka zauna, basu dade da zama ba saiga mlm ya shigo falon yana fadin kai yau na gaj..... Bai kai da karasa maganan ba idanshi ya sauka akan bilkisu duk da tayi dan jiki kadan da kuma haske, hakan baisa mlm yaki ganeta ba, da hannu ya fara nunata yana fadin bilkisu, kece? Sai kuma ya daga hannu sama yana ma Allah godiya tare da hawaye wanda kana gani kasan na farin ciki ne, yace khausar matso kusa dani, da sauri mum ta karasa wajanshi itama tana kukan rungumeta yayi yana fadin dan Allah ki yafeni khausar nasan nayi miki ba dai dai ba, ki gafarce..... Tace haba baba ka daina neman gafara na kaifa mahaifina ne, komai kayi a kaina kayi dai dai, mlm yace Allah ya miki albarka khausar sai a sannan ya lura da dady, yace jibrin sannu, nan dady ya gaida mlm cikin girmamawa, mlm ya fara mishi godia akan irin riqon da yayi ma yarshi dan daka gani bama sai an tambaya ba kasan tana cikin kwanciyan hankali, adda ce ta shigo dauke da tray ruwa ne akai da zobo da kofuna, ta ajiye a falon, mlm yace yau ina cikin farin ciki sosai adda tayi dariya tace ina abubakar? Mlm yace yanzu zai shigo yaje anso mi..... Kafin ya karasa sukaji sallamanshi amsawa sukayi su duka ya shigo shima dai ba karamin farin ciki yayi ba na ganin kanwar tashi, nan adda tahau bama mlm labarin abubuwan da suka faru mlm yasha mamaki, yayi shuru can yace ita yarinyar tana asibiti ne da yaron naki? Mum tace eh amma yanzu zan koma dan inaso in kwana da ita gobe wai take son ma mu koma abuja, mlm yace kai da wuri haka muje asibtin tare nima inga yaron da kuma ita mai jikin, haka suka fita harda abubakar adda kawai suka bari a gida. Koda suka isa asibitin, suka karasa dakin inda suka iske jawaheer na sallah shi kuma m samir na danna wayanshi ba komai yakeyi ba sai game, dan bashi da sim card din nigeria bai samu ya siya bama, ganin sun shigo yasa ya tashi da sauri yana fadin sannu da zuwa mum, cikin harshen turanci amsawa tayi cikin sakin fuska, sannan tace mai jiki anji sauki kenan, yace eh alhmdlh, sai a sannan ya gaida su mlm da abubakar, mlm murmushi yayi tare da mika mai hannu danshi baya jin turanci, amma abubakar naji, mlm yace ni wannan yaran naku ban iyashi ba, duka suka saka dariya, mum tace ma m samir ga kakanshi shine babanta, ga kuma yayanta ta nuna abubakar, nan m samir ya kara gaidashi tare da fadin uncle ina farin cikin haduwa daku, abubakar yace nima haka uncle dinka yana cikin masoyanka danni dan barcelona ne, kuma kai nake so, dariya m samir yayi tare da fadin thanks my uncle, dai dai lokacin jawaheer ta idar da sallah, itama gaida mlm tayi cikin harshen hausa, amsawa yayi tare da fadin ya jikin naki? Tace da sauki alhmdlh, sannan ta gaida abubakar shima ya amsa cikin sakin fuska, nan mlm ya zauna kusa da jawaheer suna ta fira yana ta janta da surutu tana ta dariya m samir kuma ya matsa kusa da uncle dinshi yana fadin wai mai yasa take dariya mai ake fada mata haka? Dariya abubakar yayi yace wasa yake mata yana fadin shine zai aureta amma itace zata biya sadaki dan taimaka mata zaiyi, shima m samir din dariya ya farayi yi, tare da fadin uncle nima ina son koyan wannan yaran naku, abubakar yace ai babu wuya sai in fara koya maka, gashi naji ance gobe zaku tafi, kallon jawaheer yayi yace sis mu dan zauna a nan na kwana biyu mana, murmushi tayi tace ok duk yanda kace bani da zabi, yaji dadin abunda tace yana son biyayyan jawaheer tana son abunda yake so, mum ce tace au nama manta taci abincin kuwa?? M samir yace eh taci amma bada wani yawa ba, mum tace jawaheer kin taba ganin ana ciwo babu cin abinci?? Tace mum nafa ci kadan na rage, murmushi mum tayi dai dai lokacin dad ya shigo dauke da ledoji a hannunshi, mum ta tashi ta amsa tare da ajiyewa kayam fruit ne dasu kaji gassasu, mum taba jawaheer kaza daya ta mika ma mlm da abubakar mlm yace a'a shi tare da matarshi zaici dariya duka sukayi m samir shima yaci kazan yana ta fadin kazan akwai dadi suna tamai dariya yanda yake ta santi, dad yace jawaheer kinji sauki koh? Tace eh dad sai dai bana jin dadin komai amma ganin mum da kakana yasa naji dadi sosai, kowa ya fahimta abunda take nufi wato shiryawan mum dinta da mahaifinta yasa taji dadi sosai, kowa dake dakin saida yaji tausayinta tare dayi mata fatan itama Allah ya hadata da iyayenta, dad yayi murmushi tare da fadin Allah ya kara miki lafiya bari muje mu kwanta dare yayi, duka kowa ya fita amma banda m samir da mum, m samir yana son yi mata magana amma bazai iyaba dan mum na wajan haka ya fita tare da fadin good night, ji tayi kaman ta bishi, koda ya fita ya tarar dasu a waje, abubakar yace ma m samir a gidanshi zai kwana, security dinshi sukace ma abubakar dan Allah yayi hakuri an basu tsaronshi ne idan wani abu ya faru dashi zasu shiga matsala, duk yanda abubakar yaso m samir ya kwana a gidanshi haka ya hakura akan gobe zasu hadu, koda m samir ya koma hotel din daya sauka wanka yayi ya kwanta amma bacci yaki zuwa, sai juyi yake tayi gaba daya tunanin jawaheer yake tayi wanda ya hanashi sakat, ya rasa dalilin da yasa yake tunaninta har yake kokarin hanashi bacci abunda bai tabayi ba kenan ko sonia da yake so baya jinta kaman yanda yake jin jawaheer a yanzu, dan tsaki yayi tare da fadin tausayinta nake ji sai yasa nake tunaninta..... *maryam obam* *JAWAHEER* *STORY AND WRITEEN BY......* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA* *(maryam Obam)* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝* *{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}* *wattpad @maryam-obam* *WWW.Maryamobamnovels.com* https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/ *DEDICATED TO.....* *Nafisa mrs dan malikin kawo* Page 29-30 Haka yaita tunani kala2 yayinda yake ta tursasa ma zuciyarshi akan tausayinta yake kawai, wasa2 har wajan karfe biyu amma babu alaman bacci a idonsa sai tunanin jawaheer gaba daya ma kanshi ya kulle yama rasa mai yake ji a kanta, ganin babu baccin a idonsa ga tunanin yaki barinsa yasa ya tashi ya shiga toilet yayi alwala, sallah yazo yayi tare da roqan Allah akan ya zaba mishi abu mafi alkhairi a rayuwanshi, ya dauki lokaci mai tsawo yana roqan Allah akan ya zaba mishi abu mafi alkhairi, kafin ya tashi ya koma gado yana kwanciya bacci ya daukeshi. Ta gefen jawaheer ma haka abun yake bata so m samir ya tafi ba, ita inda so samu nema dashi ya kwana da ita amma sai dai hakan bamai yihuwa bane, babu abunda take sai tunaninshi tare dason qara ganinshi, duk da sau da yawa zuciyarta tana kara nuna mata tayi baya dashi dan ba sonta yake ba, amma ta kasa, a yanda takeji inda tana da halin cireshi a ranta data dade da cireshi, itama haka taita tunani har bacci barawo yayi awon gaba da ita. Jawaheer tunda ta farka tayi sallah asuba, bata koma bacci ba, har adda tazo da kayan abinci ita da mlm, jawaheer ta gaidasu cikin girmamawa inda suka tambayeta ya jiki ta basu amsa da fadin da sauki, dad dinta ne ya shigo cikin dakin yana fadin mai jiki anji sauki kenan? Murmushi tayi tare da fadin alhmdlh dad, dai dai lokacin dr ya shigo dakin tare da wata nurse, jawaheer na ganin dr ta tashi tare da fadin dr yau zani gida koh? Dariya dr din yayi daya kafeta da ido yace a'a ai kya bari ki dan kara jin sauki koda nanda sati biyu ne, ido ta zare tare da fadin ni kam yau gida zan tafi dan na warke sosai, dr yace shikenan zaki iya tafiya amma ki dinga kiyaye wa ki rage yawan tunani, tace insha Allah, murmushi yayi tare da kallon dad yace alhaji Allah ya kara mata lfya, jiki yayi sauki komai yayi normal, dad yace hakane mun godema Allah komai yayi kyau, dr ya kuma waigawa wajan jawaheer yace zanzo gida inji mai kike tunani haka har ya miki yawa kika fadi lokaci daya, mlm yace likita ni take tunani amm zanyi hakuri in aureta haka, duka suka sa dariya, jawaheer sai tunanin maiya hana m samir zuwa take tayi, haka suka fara shirya kaya har suka fitar da komai aka bama jawaheer magani Suka shiga mota, direct gidan adda suka nufa, koda suka isa jawaheer dakin adda ta shiga ta kwanta dan bata son wata fira a halin yanzu tafi jin dadi ta ganta tayi shuru, tunawa tayi da wayanta dan haka ta fito ta dauki hand bag dinta dake falo, mum tace mata yauwa jawaheer maza kizo kiyi wanka saiki kwanta gaba daya, tace to mum, dan shuru tayi can tace mum kayana basa nan suna hotel din da muka sauka, mum tace bude akwatina ki dauki zani anjima ko gobe kyaje ki kwaso kayan bata kara magana ba ta nufi dakin da kayan mum suke ta dauki zani ta nufi bayi dan tayi wanka, bayan ta fito daka wanka daka ita sai saurin kirji sai kayan data cire a hannu, kasancewan bayin gidan a waje yake, tana saurin ta shige ciki sukaci karo wanda shima a dai2 lokacin ya shigo gidan kuma bayin daka shi sai kofar gidan, tsayawa tayi taga dawa ta buge ganinshi tayi yana mata murmushi itama bata san lokacin data sake murmushin ba, sai taji kaman tayi hugging dinshi, a hankali ya furta mata ya jikin ki? Tace da sauki, yace naje hspt akace min kin dawo gida, ban tashi da wuri ba yau jiya banyi bacci da wuri ba ina ta tunani, tace tunani kuma? Yace eh, shuru tayi tana dan nazari shi kuma idanshi na kanta, katseta yayi da fadin ina mum? Tace tana ciki shiga yayi itama binshi tayi a baya tana shiga tayi daki, mai ta shafa cikin kayan mum ta dauko jallabiya tasa duk da ya mata yawa amma haka tasa, tana zaune tana jiyo firan mum da dan nata, uncle abubakar ya shigo, nan firan ta canza zuwa na ball, mum tace bada ita ba, jawaheer kwanciya tayi amma ba bacci takeyi ba, kawai tana tunani ne, tunda tasan basu mum bane iyayenta take jin wani iri saita tsinta kanta da rashin sakewa kusa dasu, harta dad bata sakewa in yana wajan sabanin da, wani zubin in abun nata ya tashi haka zatai ta shagwabe ma dad dinta wanda a yanzu bata jin zata iyama fira dashi kaman da, wani guntun hawaye ne ya zubo mata, babu komai a ranta sai bakin ciki tare da takaicin mai yasa basu kasance iyayenta na gaskiya ba, mum ce ta shigo dakin hannuta dauke da tray, ganin tana kuka yasa mum tayi saurin karasawa wajanta tana fadin jawaheer mai ya sameki?? Tayi saurin goge hawayen tare da fadin babu komai mum, ido mum ta kura mata tare da fadin jawaheer nasan abunda kike tunani bazai wuce kice bamu bane iyayenki, tun ranan da kika san haka kika rage yin magana damu, kika daina sakewa a gaban mu, jawaheer wlh dai dai da rana daya ban taba cireki a raina ba, har gobe ina miki kallon yar dana haifa a ciki na, mai yasa kema ba zaki daukemu a matsayin iyaye ba jawaheer?? Kuka jawaheer ta kara fashewa dashi tare da rungume mum tana fadin ba haka bane mum har gobe kune iyayena kawai ina takaicin daya kasance baku kuka haifeni ba, amma ban taba canzaku daka matsayin da kuke ba, mum tace toh kiyi shuru ga abinci kici sai kizo muje falo ayi fira dake, bata musa ba ta dauki cup din tea da white rice ns stew ta fara ci, mum tana zaune harta gama ci, duk da ba wani da yawa taci ba, amma tasha tea din da yawa, mum ta dauko mata magani tasha, sannan suka fita falo, tunda ta fito idanshi na kanta harta zauna, akan kujeran dake kallon nashi, gaida uncle abubakar tayi ya amsa tare da tambayanta ya jikin nata? Tace da sauki alhmdlh, murmushi yayi tare da fadin badai ciwon bane yasa kika rame kayan naga ya miki yawa, itama murmushin tayi wanda ya kara fito mata da kyanta, tace a'a kayan mum ne nawa yana hotel din da muka sauka, adda ce ta shigo da kayan jawaheer tana fadin ga wasu da kika canza a asibti na wanke miki su, tace lah adda wanki kuma, keda kanki? Adda tace gasu maza kije kisa sai kuje ki dauko sauran, bata musa ba ta tashi ta nufi daki dan canza kaya, jim kadan sai gata ta fito cikin hijab, ido m samir ya bita dashi dan ba karamin kyau hijab din ya mata ba, mum tayi murmushi tace jawaheer hijab na miki kyau amma bakya son sawa, murmushi tayi, tana kokarin zama taji muryan m samir na fadin muje mu dawo, dan haka bata karasa zaman ba suka fita, security din na ganinsu suka bude musu baya suka shige, kai tsaye hotel din suka nufa har suka karasa babu mai ma dan uwanshi magana, har suka shiga ciki ta nufi dakin data sauka ta fara hada kayanta tana cikin hadawa ya shigo dakin ya hade hannunshi biyu a kirjinshi ido ta dago suka hada murmushi ya sakan mata tare da nufanta ya zauna kusa da ita, ita dai bata cemai komai ba tana ta hada kayanta, hannunta ya kamo tare da janyota jikinshi kirjinta ya fara bugawa da karfi fuskanta ya dago suna kallon juna ido ta rufe da sauri amma tana jin saukan numfashin shi, jin muryanshi tayi yana fadin kina fushi dani ne? Ido ta bude da sauri ganin har yanzu ita yake kallo yasa ta kara rufe idonta murmushi yayi tare da fadin sunanta jawaheer bata amsa ba haka bata bude ido ba, yace mai yasa kike fushi dani, ido ta bude tare dayin kasa da kanta, ganin haka ya kara janyota jikinshi yace fadamin, tace niba fushi nake dakai ba, yace to mai yasa bakya son yin magana dani yau? Tace ba haka bane , yace toh miye? Dariya ta saki tare da fadin babu komai kawai bana son yin magana ne yau, yace har dani bakya son yin magana? Kai ta daga alaman eh, murmushi yayi tare da sakinta ya tashi tsaye yace ok kiyi hakuri da takura miki da nayi akan saina miki magana, in kin gama ki sameni a mota, da sauri tace to wazai fito min da kayan? Yace keda kanki mana tunda baki son a dameki, murmushi tayi tare da tashi tayi hugging dinshi ta baya tace sorry ba haka nake nufi ba, kana daya daka cikin mutane masu muhimmanci a rayuwa na, koda zan zauna daka ni sai kai bazaka taba gundura na ba, waigowa yayi tare da fadin really? Kai ta daga mai alaman eh, hancinta yaja tare da fadin zo in tayaki hada kayan, zama yayi suna ta hada kayan har suka gama, ya kira masu aikin hotel din suka fara fitar sa kayan zuwa mota, suma fita sukayi ya kalleta yace yau kinyi kyau, tace nagode, bayan sun shiga mota yace ma jawaheer ina ake saida sim? Dariya tayi tace nima ban taba zuwa state din nan ba, amma muje mtn office, tace ma driver suje mtn office yace ok, hannunta ya kamo tare da fadin kema zaki canza naki sim din, da sauri ta dago tana kallonshi tare da fadin saboda me?? Shuru ya mata ba tare daya bata amsa ba, har suka karasa mtn office, fita sukayi suka shiga wani office aka kaisu daka shi sai jawaheer, jim kadan sai ga wani ya shigo yana bama m samir hannu tare da fadin ban taba tunanin zan ganka ba a rayuwa yau gani gaka, m samir yayi murmushi mutumin yace plz zamu iya daukan hoto? M samir yace ok nan mutumin ya fara daukansu, sannan ya tambayi m samir mai yake so yace sim card guda biyu sannan yana son number shigen iri daya, mutumin ya dauko sim biyu ya bashi, special number karshen ne kawai ya ban banta, daya 7 daya 8, nan aka mishi register dayan ma da sunanshi akayi, har aka gama suka fito, nan mutane suka fara ihu tare da daukanshi hoto, dakyar security dinshi suka fitar dashi sukai mota, suna cikin tafiya ya kalli jawaheer yace bani wayanki? Kallonshi tayi ba tare da tace mishi komai ba kota miqa mai, hannu ya miqa mata ganin haka yasa ta bashi wayan, hannu yasa a kunnenta ya ciro dan kunnenta ya ciro abun sim din, ya cire nata yasa mata sabon daya, shima yasa daya a nashi, sai daya gama ya miqa mata wayanta tare da karya sim dinta, da ido ta bishi tana son yi mishi magana amma taga ya daure fuska ganin haka yasa tayi shuru tare da mamakin mai yasa ya mata haka, bai karayi mata magana ba har suka karasa gida, security dinshi suka fara shigar mata da kayan, itama ko kallonshi batai ba tayi cikin gida dan karya mata sim da yayi ba tare da wani dalili ba abun ya bata haushi, yana kallonta ya bita da murmushi dan yasan taji haushi, amma shi daya yasan dalilin da yasa yayi hakan, koda ta shiga a tsakar gida taga adda ita da mlm, bayan ta musu sannu da gida, tace ina mum? Adda tace ta fita ita da babanki basu dade da fita ba, m samir shima ya shigi gidan, tana ganinshi tayi ciki, adda tace toh ni yanzu bajin yaranka nake ba, ta kwada ma jawaheer kira tazo da sauri, adda tace taya zaki shige ciki bayan kin san mu bama jin turanci, fada mishi ya tayaki shigar da kayan, kallonshi tayi wanda shima itama din yake kallo yana mamakin fushin da takeyi dan an karya mata sim, tace ance wai ka tayani shigar da kaya, murmushi yayi tare da daukan akwati itama ta dauki wasu suka shigar dasu haka har suka gama kwashewa mlm ya fita daka gidan dan komawa kasuwa, itama adda ta nufi dakinta, ya rage daka m samir sai jawaheer a falo wanda sukai shuru su dukansu, tashi yayi ya matso kusa da ita, yace mai yasa kike fushi? Mai akayi miki? Tana son ta tambayeshi mai yasa ya karya mata sim amma saita kasa dan ya mata wani irin kwarjini, ganin tayi shuru yace saboda na karya miki sim kike fushi koh? Toh idan na kwace wayan fah????........ *maryam obam* *JAWAHEER* *STORY AND WRITEEN BY......* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA* *(maryam Obam)* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝* *{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}* *wattpad @maryam-obam* *WWW.Maryamobamnovels.com* https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/ *DEDICATED TO.....* *Nafisa mrs dan malikin kawo* Page 31-32 Kallonshi tayi ya sakar mata murmushi tare da daga mata gira, yace jawaheer banso ana damunki sai yasa na canza miki sim nd kuma ban san any abu da zai daga miki hankali kin san abubuwan da suka faru na sanin basu mum bane iyayenki kin san tunda maganan nan ta fito kowa zaiji, nd kuma nasa wasu za suyi ta kiranki dan suji maike faruwa, banso wani koh wata su daga miki hankali har zuwa sanda zamu gano inda iyayenki suke, hannunta biyu ya kamo ya matse tare da fadin sai yasa na karya layin, murmushi tayi tare da fadin banyi fushi ba, kawai na dan damune akan mai yasa ka karya sim din ba tare da kamin bayani ba, amma yanzu da naji komai sai naji hankalina ya kwanta komai kuma ya wuce, yace dat my sister, yaushe zamu tafi abuja? Tace ba kace sai anyi kwana biyu ba,yace yes inaso in saba da kakanninmu gashi kuma bana jin yaranku, tace bari in fara koya maka, yace yauwa amma ba'a nan ba, kizo mu tafi waje, tace ok bari in canza kaya, yace ok ki sameni mota, daki ta shiga tasa wata jallabiya tare da yafa gyalen jallabiyan, ta nufi dakin adda taga tana bacci dan haka ta fita kawai tana shiga mota taga anja bata cemai komai ba har suka isa wani hadaddan restaurant babu kowa sai su kadai daka gani yasa an kama mai wajan ne duka, shiga sukayi suka zauna, kallonshi tayi tace mai za muyi a nan? Yace abinci zanci kin san ba komai na iya ciba, nd ke kuma baki damu damai naci ba, tayi narai narai da ido tace nifa kasan bani da lafiya ba yau na dawo gida bama, murmushi yayi yace hakane, my baby da sauri ta dago ta kalleshi hada ido sukayi ita tana mamakin sunan daya kirata dashi, shiko yana mamakin mai yasa kullum jawaheer take kara kyau, idan yaga ta mishi kyau yanzu anjima kuma sai tafi kyau,hura mata fuska yayi tayi firgit tasa hannunta ta rufe fuska tana dariya, dai dai lokacin masu saida abincin wajan suka zo suna tambaya mai za'a kawo musu, fada musu yayi ita tace tuwon semo miyan kuka, suka tafi, basu dade ba suka kawo abincin, sannan suka roqeshi akan su dauki hoto dashi, bai musa ba haka ya tashi suka dauka, suna ta murna, zama yayi yana kallon abunda jawaheer zata ci, lokaci daya kuma yayi dariya yace jawaheer miye haka? Tace mene? Yace wannan abun da zaki ci miye? Tace tuwo, kasa fadan sunan yayi, tace ka gwada ci akwai dadi sosai, kai ya girgiza alaman a'a, murmushi tayi ta fara ci, mai yakon yaci nashi saiya tsaya kallonta yanda take ci sai yaji abun ya burgeshi, dan haka shima yasa spoon cikin tuwan yaci ido ta kura mishi, taga ya cinye ya kara ci wasa wasa sai gashi ya cinye tuwan duka, saida ya gama yace ashe akwai dadi sosai dariya tayi tace abincin mu yana da dadi, murmushi yayi sannan ya fara cin farfesun kazan da aka hado mata dashi bai wani ci da yawa ba ya ajiye tare da kallonta yace ban taba cin abinci mai yawa irin haka ba, dariya tayi tace dan wannan abincin shine mai yawa? Yace eh mana, yace toh a fara koyamin hausa, tace mai kake so ka koya?? Yace komai amma nafi son in fara koyan gaisuwa, nan ta fara koya mai gaisuwa tana fada mai da turanci saita fassara mai, sannan ta koya mai tambayan abu, da wasu yan abubuwa, murmushi yayi tare da kunna wayanshi taji magananta ashe recording yayi, kokarin kwace wayan ta farayi wai zata goge garin haka ta fada jikinshi sukai qasa, wani irin yanayi dukansu suka shiga musamman ma shi, domin kirjinta ne ke kwance akan jikinshi, ganin irin kallon da yake mata yasa ta tashi da sauru tare da fadin kayi hakuri, baice mata komai ba harya tashi sannan yace baki ji ciwo ba? Kai ta daga mishi alaman eh, cikin sanyin murya tace muje gida dare ya farayi, tashi yayi yace muje, mota suka shiga aka sauketa kaman bazai fita ba komai ya tuna oho ya fito har kofan gidan ya kaita sannan yace mata saida safe, bata bashi amsaba ta shige, a falo ta tarar dasu mum harda dad, mum tana ganinta tace jawaheer daka ina kike maiya sami wayanki? Tace mum muna tare da m samir sannan na canza number ne, ido dad ya bita dashi yace saboda me kika canza number kuma baki bamu ba, tace dad m samir ya siya mana dazu nan ta fada musu number din suka saka, dad yace zai tafi hotel din daya sauka mum ta rakashi jawaheer kuma tayi dakin da take kwana ita da mum. M samir koda ya isa an kira sallah isha'i dan haka saida yayi sallah sannan yayi wanka ya kwanta, amma kuma sai me?? Tunanin jawaheer ne cike a ranshi, musamman dazu data fado mishi jiki ido ya lumshe tare da fadin maike damuna? Kanwata ce da sauri yace no bazan iya ba kanwata ce kawai sabuwan da mukayi ne yasa nake jin wani abu but zanyi dan nesa da ita, duk yanda yaso ya cire tunanin jawaheer ya kasa daka karshe recording din da yayi ya kunna yana jin muryanta yana dariya har bacci ya daukeshi. Itama ta gefen jawaheer tunanin nashi tai tayi ga wani irin azabban sonshi dake kara shiganta, Allah ya sani tana hakuri da irin son da take mishi amma ya kasa fahimta wani lokacin har tunani take inda zaice ta bashi jikinta zata iya bashi dan dai kawai yasan tana sonshi, duk da wani lokacin tana kokarin cire shi a ranta amma ina abun ya gagara sai dai kullum tayi sallah tana roqan Allah mafi alkhairi. Washe gari da safe jawaheer ta tashi da wuri, ita ta share tsakar gidan tare da hada kayan wanke wanke ta wanke su tas, adda ta fito tace jawaheer keda baki da lafiya inake ina aiki? Mai makon ta bata amsa saita gaidata da fadin ina kwana adda, murmushi adda tayi tace lfya ya karfin jikin naki? Tace alhmdlh naji sauki, adda tace haka akeso Allah ya kara mana lfya, tace ameen yar tsohuwa, dariya adda tayi tace aina fiki kyan jiki, jawaheer tace wa tab aida ban sami samari ba, adda tace ina samarin tunda kika zo banji anyi sallama ba, niko sanda ina budurwa zo kiga layi, jawaheer dariya take tayi tana fadin ba wani layi kakana kadai ke zuwa inna aureshi nasa ya sallameki dan kin mai tsufa, mum ce ta fito tana dariya tare da fadin ina kwana adda, adda ta amsa cikin fara'a tare da fadin kinga yar nema sauki ya samu zata damemu da surutu, mum dariya tayi dan harga Allah taji dadin yanda jawaheer ta sake yau har take ta fira, wanda rabonta data sake irin haka tunda tasan basu bane iyayenta amma yau gashi tana ta surutu, mum tace adda ina zan sami waina shi nake son ci yau, adda tace shine tun jiya baki magana ba aida anyi yau,kira abubakar ya siyo miki, tace toh daki ta koma ta dauko wayanta ta kira abubakar, sannan ta dawo tsakar gida inna adda da jawaheer keta kulla alale, suna fira, ita hannu tasa ta taya su, har suka gama jawaheer ta daura akan murhu, har alalan yayi suka faraci amma banda mum dan tana jiran waina, sallaman abubakar ne yasa su duka suka daga kai, amsawa sukayi sannan ya shigo ya ajiye cooler din tare da gaida adda, itama mum gaidashi tayi sannan itama jawaheer, bayan ya amsa yake tambayan jawaheer ina m samir bai zo bane? Tace eh bai zo ba uncle, murmushi yayi tare da fadin bari inje in shirya yau yace yawo zamu tare, mum tace yadai kamata shima yaga gari da irin al'adunsu, harya tashi zai fita ya dawi tare da tambayan ina mlm mahaifinsu kenan, adda tace yana bacci, yace mai gari jiya ya ganni yake tambaya na wai dagaske khausar ta dawo gari, nace mishi eh yace shine mlm bai fada mishi ba, nace toh nima ban san dalilin hakan ba nayi tafiya ta, mum tayi dan murmushin takaici tare da fadin naga kasar nan ta kowa ce kuma kowa zai iya zuwa inda yake so, koda can baya rashin sanin yanci nane yasa akamin haka, adda tace Allah dai ya kyauta suka amsa da ameen, sannan abubakar ya fita, jawaheer kam bayan ta tattare kayan da suka ci abinci ta wanke daki ta koma tayi kwanciyanta tare da tunanin m samir, haka taita zama a daki har wajan karfe daya ta fito tayi alwala ta koma tayi sallah, bayan ta idar taji mum na kiranta fita tayi tace mum gani, mum tace kije kici abinci mana, kin shige daki ko dai jikin ne? Tace a'a mum tashi tayi taje ta zuba abinci kadan ta zauna kusa da mum tana ci tana tunanin ina ma mum ce mamanta ta gaskiya da tafi kowa farin ciki, ajiye abincin tayi dan taji yana mata daci, mum tace badai wai har kin koshi ba? Tace eh mum bana jin yunwa sosai, shuru mum tayi dan tasan halin jawaheer ba'a matsa mata akan abu yanzu ta fara kuka, jawaheer damuwa ya mata yawa na rashin ganin m samir haka taita zama har yamma amma shuru bai leqo gidan ba, har mum da dad suka fita koda dad yazo yace ta bisu taki yarda ta bisu tace suje, tana zaune a falo adda ta zauna kusa da ita, duk tana lura da jawaheer tace jawaheer nikam wani irin so kikema wannan yaron haka? Jawaheer tayi dan murmushi tare da fadin adda niwa nake so? Adda tayi dariyan manya tace kaji ja'ira, bayan keda bakinki kin fada munji ko kin manta ne? Jawaheer tace kai ku tsofaffin nan bakwa mantuwa wlh, adda tace jawaheer naga kaman shi bawai yana sonki bane, irin yanda ke kike sonshi, amma zan baki shawara duk da nasan miye so ya kuma akeji dan nima auran so nayi duk da a lokacin ba'ayi, hada ku akeyi sai akaci sa'a muna son juna, ya kamata kibama wani namiji dama dan ya shiga cikin rayuwanki sannan ki nunama samir kema a matsayin dan uwa yake a wajanki yanda shima yake nunawa, ji jaraba wannan abun guda biyu idan kikayi zan kara miki wasu, jawaheer tayi dariya tace zan gwada yar tsohuwa suna zaune kam sai gashi wani yaro yayi sallama, wai ana kiran jawaheer, kallon juna sukayi ita da adda, sannan adda tace kaje kace tana zuwa, yaron ya fita jawaheer tace adda taya zani bayan ban san ko waye bane? Adda tace sai yasa nace kije ki gani, tashi tayi daka ita sai dogon wando da top amma yakai mata giwa sai wani dan shara sharan gyale ta yane kanta dashi, fita tayi taga wata mota kiran matrix tsayawa tayi sai taga an bude motar wannan dr din ta gani wanda ya dubata a asibiti, da murmushi akan fuskanshi yace bismillah ki shigo ciki mana, tace nan ma ya isa ai yace ba mutunci bane mu tsaya a waje...... Hasken mota ne ya hasko su, motocin m samir ne da security dinshi tun daka nesa ya hangosu suna tsaye, bayan motar ta tsaya ya fito zai wuce dr yace m samir tsayawa yayi tare da fadin dr ya aiki? Dr yace lfya tare da miga mai hannu suka gaisa hada ido sukayi da jawaheer wani irin kallo ya mata mai kama da harara, sannan ya shige ciki, dr yace shigo muyi magana, jiki a sanyaye ta shiga ciki,yace nazo inji ya jikin ki? Tace na warke nan ya fara mata surutai wanda gaba daya bama jinsa take ba, shiko m samir yana shiga yaga babu kowa sai adda ya gaidata da hausa tana ta mamaki tare sa fadin sai anjima kallo ta bishi dashi dan mamaki harya fice bata ce komai ba, koda ya fita yaga sun shige mota tsaki yayi tare da kawar da kanshi gefe ya shige mota akaja suka bar wajan....... *maryam obam* *JAWAHEER* *STORY AND WRITEEN BY......* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA* *(maryam Obam)* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝* *{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}* *wattpad @maryam-obam* *WWW.Maryamobamnovels.com* https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/ *DEDICATED TO.....* *Nafisa mrs dan malikin kawo* Page 33-34 Jawaheer kam bata Jin komai na abunda dr yake fada mata, shima kaman ya lura da hakan yasa yace mata bari ya barta yaga kaman ta gaji, hakan ya mata dadi yace ta bashi number dinta, bashi tayi sannan ya bata ledoji manya guda biyu daya kawo mata, amsa tayi tare dayi mishi godiya sannan ta fita tayi gida, a falo ta tarar da adda tana cin danwake, zama tayi kusa da adda tace adda samir yazo naga bai dade ba ya fita, adda tace hmm aini yau yaban mamaki, kinji hausa gaidani yayi da hausa harda cemin saida safe, jawaheer kam shuru tayi tana tunanin mai yasa ya tafi bai bari ta shigo ba, jin adda tayi ta katse mata tunani da fadin nasan ya ganki keda wani koh? Tace eh adda wannan dr din nanne yazo dubani, kinga yanda ya sakar min harara nan taba adda labarin abunda ya faru, adda tayi murmushi tace jawaheer inaso ki nutsu ki bama wannan dr din lokacinki dan ki nuna ma m samir kema fah akwai masu sonki, jawaheer tace adda shifa dr gaidani yazo yi ba sona yace yakeyi ba, adda tace aida haka zai fada miki, kedai kawai kiyi abunda nace..... Sallaman mum ne ya katse musu firan da sukeyi, jawaheer da fara'a tace mum har kun dawo sannu da zuwa, mum ta amsa tare da fadin dad dinki yace kije yana waje, tashi tayi ta fita ta sami dad a mota, dad yace jawaheer gobe ni zan koma ko akwai abunda kike bukata? Tace a'a dad babu komai sai dai ina son ka canza masu adda gida inda hali, dad yayi murmushi yace naso nayi hakan amma m samir ya rigani dan dazu abubakar yake fadamin fitan da sukayi gida yaje ya siyan musu cikin adamawa, abubakar yace gidan babba ne akwai komai da komai domin gidan wani barawon gwamnati ne wanda ya saci kudi shine gwamnati ta kama gidan ta saida, jawaheer tace kai Allah ya saka mishi da alkhairi, dad ya amsa da ameen, sannan yace an fara biyan kudin aikin haji, zan biya musu sai yasa zan koma ma gobe, sannan ina aiyuka, jawaheer tace Allah ya saka maka da alkhairi dad, murmushi yayi tare da kara son yar tashi ba ita yama abu ba amma tana ta godiya, kudi ya dauko ya bata ta amsa tare da fadin dad nida transfer kamin ma da yafi, dad yace toh riqe wannan din bari in miki transfer din ma, nan ya mata transfer tace kai dad kudin yayi yawa, yace jawaheer kudin da nayi ta sanadinki ne in baki ciba wa zaici, sannan million dari din da mum dinki ta bani lokacin data miqa mana ke, dasu na fara sana'a har nayi mugun arziki inada kalan kudin wajan sau million, na ware miki million dari na ajiye duk sanda naga mahaifiyarki zan bata kudin, wani hawaye ne ya zubo ma jawaheer tare da fadin dad idan na tuna baku kuka haifeni ba ina shiga cikin wani hali, wlh dad zuciya na yana zafi inna tuna hakan dan Allah dad kubar tunamin, ta karasa zancen cikin kuka, ya janyota jikinshi yana bata hakuri tare da fadin jawaheer ke yata ce har gobe, murmushi tayi tare da fadin ngd dad, yace bari inzo in tafi bacci nake ji, tace toh saida safe dad, gida ta koma inda ta sami adda ta fiffito da kayan da dr ya kawo kayan tea ne manyan gwangwani dasu milo sugar kwali dasu biscuit chocolate, mum tace ashe dr yazo dubaki? Tace eh mum, mum tace wannan hidima haka Allah dai ya saka mai, adda ta amsa da ameen, jawaheer kam haushin kayan ma taji tana yi, dan me yasa zai kawo mata suma, tashi tayi ta nufi daki, bata dade da shiga ba mum ta shigo, tace mum ashe samir ya siyama su adda gida? Mum tace eh wlh gobe zamu gidan ma muga in akwai abunda yake bugata duk da abubakar yace basai ansa komai ba, amma gobe zamu mu gani, jawaheer tace Allah ya kaimu, jawaheer ta kasa bacci babu abunda take son ji sai muryan m samir tashi tayi ta fita ta kira number dinshi amma taji ance switch off, tsaki tayi ta koma daki ta kwanta sai juyi take tayi. Washe gari tunda jawaheer tayi sallah asuba take ta kallon wayanta tana tunanin kota kira m samir ne, amma tana tunanin kaman bai dace ta kirashi yanzu ba, dan safiya ne, haka ta zauna akan dadduma harta fara bacci, bata farka ba sai wajan 9 ta ganta akan gado, murmushi tayi dan tasan mum ce ta kawota gadon, fita tayi ta nufi toilet, tana fitowa taga adda tace ga ruwan wanka nan dama yanzu zan kiraki, jawaheer tace toh yar tsohuwa, ansan ruwan tayi ta shiga toilet din, wanka tayi sannan ta fito ta shirya cikin atamfa riga da skirt ya mata bala'in kyau kaman ba itaba, adda tace kai jawaheer atamfan nan ta miki kyau amma na lura dake kaman ke bakya son irin wannan kayan kin fison kiyi ta shiga kaman ba musulma ba, dariya jawaheer tayi tace lah nice ba musulma ba? To a kunnen mai gidan, dai2 lokacin mlm ya fito yace kyaleta amarya ta kishi takeyi dariya adda tayi tace ni na yafe mata kai, jawaheer tace kaji kishin koh kaman dagaske take, dariya duka sukayi mlm yace yaushe zaku gidan? Mum tace anjima kadan abubakar muke jir..... Bata rufe baki ba saiga sallaman abubakar da m samir sun shigo, gaban jawaheer ne ya fadi kallo daya ya mata ya kawar da kanshi, gaida su mum yayi, itama jawaheer ta gaida uncle dinta, ya amsa sannan ta gaida m samir wanda ya amsa a dakile ba tare daya ko kalleta ba, mum tace ma m samir yaci abinci kuwa? Yace a'a tace ai naga alama murmushi yayi mum ta kalli jawaheer tace kema kije kici abinci kafin mu tafi, sannan ki dauko m samir kayan tea tace to, kitchen din adda ta nufa ta hada mishi kayan tea tare da soya mai akwai, falo takai mai shi daya ne a falon su mum na waje suna fira, ajiye mai tayi tare da fara kokarin hada mishi yace no leave it zanyi da kaina, sororo tayi tare da ajiye spoon din jiki a sanyaye, tana son yin magana taji yana fadin gobe zamu tafi abuja, da sauri ta dago tana kallonshi amma shi ba ita yake kallo ba, tace da wuri haka, bana tunanin zan biku gaskiya wani irin kallo ya mata da yasa tayi saurin yin qasa da kai, adda ce ta shigo tace jawaheer kuyi sauri mana, fada mishi dan Allah tunda baji nama yake ba, cikin sanyin murya tace ance kayi sauri muje, kai ya daga alaman yaji, tashi tayi itama ta fita waje da ido ya bita harta bace mai sannan ya lumshe ido, tana tafiya yaji abincin ya isheshi dan haka tashi yayi ya fita shima, uncle abubakar yace zaije kasuwa bada shi zasu ba, mum da adda suka shiga mota daya jawaheer da m samir kuma mota daya, sai security din dake mara musu baya, sai sharara gudu mota takeyi amma babu mai cewa komai, wayan jawaheer ne ya fara kara dan haka ta duba taga number ne, mamaki tayi toh wa yasan number dinta ita dai tasan bata kira kowa ba, har kiran ya tsinke wani kiran ya kara shigowa ta kalli m samir taga ba ita yake kallo ba dan haka ta dauka, tana dauka taji anyi mata sallama ta amsa yace nasan baki ganeni ba koh? Tace eh, yace dr ne, harga Allah ta manta ta bashi number dinta, tace eyya yaka koma gida? Yace lafiya qalau sai dai na tafi da tunaninki, tayi dan murmushi wanda a dai2 lokacin m samir ya waigo suka hada ido, wani irin kallo ya mata wanda yasa tayi saurin juyar sa kanta gefe, ci gaba tayi da wayan taji an fisge, da sauri ta waigo taga yana watsa mata wani irin kallo, yace dawa kike waya? Tace friend dina, yace ok daka yanzu in zakiyi waya a gabana karki karayin wani yare sai english, bata ce mai komai ba ya jefa mata wayan tare dayin tsaki kadan, bai kara ko kallonta ba balle ya mata magana wayanta ne ya fara kara, ganin number din dr yasa ta kashe wayan gaba daya, tafiya suke har suka karasa wani dangareren gida sukai horn mai gadi ya bude, suka shiga ciki bayan an faka suka fito, m samir yana fita baiko bi takan jawaheer ba ya nufi wajan su mum, jawaheer kam canjin da yake nuna mata ya fara damunta domin taga yana nuna halin ko in kula da ita tun jiya, amma koma dai miye yau sai taji miye dalili, shiga gidan sukayi wani dangareren falo suka shiga wanda yaji kayan more rayuwa, adda salati ta fara tana fadin ina zamu kai wannan gida? Dariya su mum suke ta mata suna fadin adda an zama yan gayu, gidan yayi bala'in haduwa gashi gidan sama, falo biyu ne a 'kasa sai daki daya a kasan, sama kuma falo daya ne sai daki uku a saman, fadin tsaruwan gidan bata bakine, adda harda hawaye tana ta sama m samir albarka tare dasu mum, tace jiba abunda muke ta kyama gashi yazo duniya ya bamu babban kyauta, haja taita mai godiya shidai murmushi yake tayi dan bai san mai take fada ba, adda tace babu abunda za'a sa a gidan hakan ya isa, mum tace shikenan dan itama taga babu abunda gidan yake bukata, haka suka fito da fadin zasu sa ranan dawowa, shiga mota sukayi dan tafiya gida, suna cikin tafiya jawaheer ta kalli m samir tace Allah ya biyaka gidan yayi kyau sosai, banza da ita yayi, ji tayi kaman tayi ihu dan takaici, ta bude baki zata kara magana taji yace mai adda take fada dazu? Dadi taji koba komai ya mata magana, tace godiya take maka tare da addu'a, dan murmushi yayi sannan yace ok, ya ciro wayanshi ya danna wasu numbers jim kadan yace dad yakake, shuru yayi sannan yace dad komai normal nan ya fara bashi labari dad din yaji dadi sosai tare da fadin ina jawaheer baice komai ba taga ya mika mata waya, amsa tayi tare da fadin hello dad yace yarinya ta yakike? Amsawa tayi tare da gaidashi nan suka taba fira tana ta dariya daka karshe sukai sallama, ta mika mai wayan sawa yayi a kunne ban san mai dad din ke fada mishi ba naji yace ok dad ba damuwa gobe zamu koma abuja muma, yana fadin haka sukai sallama, kallon jawaheer yayi suka hada ido murmushi ta sakar mai tare da fadin wai mai nayi maka kake shareni? Dan tsaki yayi tare da fadin babu komai, tace toh mai yasa kake shareni? Yace haka kawai bana son damuwa, sakan baki tayi tana kallonshi wato nice damuwa ma, dan tsaki tayi wanda bata san ya fito ba jin hannunshi tayi a bakinta yaja tare da fadin wa kike ma tsaki? Kasa magana tayi dan ya riqe mata lebe, ganin yanda tayi da ido kaman zatai kuka yasa ya sakan mata bakin tare da fadin karki kara min tsaki i hate it, bata ko kalleshi ba balle yasa ran zata bashi amsa, yau ce rana ta farko daya taba bata haushi, danme zai dinga wani shareta ba tare da tamai komai ba, inda yasan yanda ta shiga cikin damuwa aida bai mata haka ba, ido ta lumshe kaman mai bacci, bini bini ya kalleta ganin kaman tayi bacci yasa ya kura mata ido tare da fadin slp beauty, tafiya mota keyi tana sharara gudu, jin tsayuwar motar ne yasa ta bude ido mai yakon ta ganta a gidan adda saita ganta a hotel din da yake kwana, kallonshi tayi suka hada ido, kawar da kanshi yayi tare da fadin muje, kaman ba zata fita ba, komai ta tuna kuma ta fito suka shiga tana biye dashi a baya, dakin da ta sauka tai niyan nufa taji ya janyota sukai dakinshi akan gadon dakin ya ajiyeta, toilet ya nufa yayi wanka jim kadan sai gashi daka shi sai towel ga kuma wani karami yana goge kanshi dashi, kallonshi tayi, tayi saurin kawar da kai, murmushi yayi tare da matsawa kusa da ita ya mika mata karamin towel din yace gashi ki gogemin, kin amsa tayi ganin haka ya kamo hannunta ya mika mata towel din, yace tashi kimin, bata tashi ba sannan bata mai komai ba, yace saboda niba saurayinki bane? Da sauri ta dago kai ganin yanda ya kafeta da ido yasa tayi saurin tashi tare da fadin zan wuce gida, kafada ya daga alaman ke kika sani, ganin yanda ya mata yasa ta fara kokarin fita har takai bakin kofa taji ya riqota tare da fadin wa yace ki tafi? Tace na gaji da zama a nan ne, yace ok to babu inda zaki yau tare zamu kwana ni dake cikin wannan dakin....... *maryam obam* *JAWAHEER* *STORY AND WRITEEN BY......* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA* *(maryam Obam)* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝* *{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}* *wattpad @maryam-obam* *WWW.Maryamobamnovels.com* https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/ *DEDICATED TO.....* *Nafisa mrs dan malikin kawo* Page 35-36 Kallonshi tayi da sauri tare da zare ido, hada ido sukayi yayi saurin kawar dakai tare da tamke fuska, dan murmushin takaici tayi tare da kokarin jan hannunta daka nashi amma ta kasa danya riqeta tam, ganin tana son ya saketa yasa ya kara janyota jikinshi ta fado kanshi, zama sukai akan gado ya kura mata ido na wani lokaci sannan yace miye tsakaninki da dr din nan?? Da sauri ta kalleshi, ganin babu wasa a tare dashi yasa tace babu komai, yace toh mai yazo yi wajanki? Tace yazo ya gaisheni ne kawai, kai ya daga alaman yaji, sannan ya tashi tare da fadin muje muci abinci sai a kaiki gida, da sauri ta tashi kallonta yayi tare da fadin saurin me kikeyi haka? Tace inaso ne inje gida na gaji, baice mata komai ba yayi gaba itama ta bishi, fadama security din inda zasu kaishi yayi, wajan wani hadaddan cin abinci suka nufa, bayan sun zauna a private waje ta kalleshi tace mai yasa baya cin abincin hotel din? Yace hakanan, masu kawo abincin ne suka zo suka tsaya suna jiran su fadi abunda suke so, kallonta yayi yace kalan abincin da kika ci rannan nake so, dariya tayi tace ma mai kawo abincin ya kawo tuwon semo, da farfesun kaza, ita kuma ya kawo mata rice nd stew da garden salad, tafiya yayi jim kadan saiga abincin ko wanne fara cin nashi yayi, ita kam ci take sosai dan sai yanzu ta tuna tun safe babu abunda taci suka fita, har suka gama ta tashi zasu fita ta riqe cikinta tare dayin yar kara, da sauri ya karasa wajanta tare da riqeta yana tambayanta lfya? Tace cikina ke murda min, cikin tashin hankali yace bari muje hspt, tace a'a zai daina bari in huta kad..... Bai gama sauraranta ba ya dagata cak ya fita da ita har mota yace suje hspt wani asibiti suka nufa, nan akai emergency da ita ganin yanda ya daukota yasa suka zata ko emergency ne, dr ne ya shigo dakin ya fara dubata, yace baki ci abinci da wuri ba da kika tashi ci kuma sai kika ci wani abun mai yakon ki fara shan tea, magani dr ya bata tasha, tana sha ko minti biyar batai ba cikin ya daina, sannan dr din ya sallamesu, suna mota ya kalleta yace ya cikin? Tace naji sauki sosai, ido ya kura mata can yace maganan tafiyan mu gobe saiki shirya dan da wuri zamu wuce, tace daka bari mun dan kara kwana biyu a nan, kuma banji mum tayi maganan tafiyan ba, yace dazu mukayi da ita so dan haka tace babu damuwa saiki shirya, shuru tayi ba tare data kara cewa komai ba, ita inda so samu ne ta zauna ta kara kwanaki a nan, suna karasawa kofar gida ta hango dr yana zaune akan motarshi yana danna wayanshi, m samir ya ganshi kallo daya ya mishi ya kawar dakai tare da kallonta yace sai yanzu nasan abunda yasa bakya son tafiya, nd kin dameni zaki tafi gida ashe shike jiranki, tace wlh ni ban san zai...... Shut up ya daka mata tsawa inma kin sani in baki sani ba wannan ba damuwa na bane, the only thing i hate shine karya, kince babu komai tsakaninku mai yazo yi yanzu??? Tace nima ban sani ba kuma bai cemin zaizo ba, yace bani phone dinki, mika mai tayi da sauri ya amsa ya duba yaga wayan a kashe, kallonta yayi tare da miqa mata wayan amma taki amsa ya ajiye mata a jiki tare da fadin mai yasa kika kashe wayan?? Tace hakanan kawai, yace ok tambaya na karshe miye tsakaninki da wancan dr din?? Tace babu komai yazo gaida nine ran nan, yace yanzu kuma mai yazo yi?? Tace nima ban sani ba, janyota yayi jikinshi tare da bude kofar gefenshi ya fito ita ya janyota ta fito ta kofar daya fita daura hannunshi yayi akan kafadanta tare da janyo dayan hannunta yana wasa dashi yajata suka fara tafiya, dr dake zaune m samir yace dr yakake? Dr ya dago yaga jawaheer maqale a jikin m samir nan idanshi ya canza launi dan tsabagen kishi, dakyar ya iya amsa ma m samir, sannan yaja jawaheer sukai ciki, dr kam wani irin takaici ne ya cika shi, suna shiga gidan ya saketa tare da tureta yayi ciki, binshi tayi da ido tana mamakin mai yasa yayi mata haka? Miye dan dr yazo wajanta, shiga itama tayi jiki a sanyaye ta samesu a falo har dashi, suna magana da mum ita kuma adda tana taba mlm labarin gidan, jawaheer gaidasu tayi bayan sun amsa adda tace dr yazo nemanki tun dazu, tace eh na ganshi, wani yaro ne ya shigo da kaya wai gashi a bama jawaheer inji dr, m samir jin an kira sunan jawaheer kuma ance dr ya gane sakon daka dr dinne, dan haka ya tashi da sauri ya amshi ledan, chocolate ne dasu biscuit tsaki yayi tare da bama yaron yace ya tafi dashi, yaron duk da baiji abunda yace ba ya gane ance yaje an bashi ne, mum tace ya zaka bashi bayan na jawaheer ne, yace mum kayan zaki ne kuma ita tana fama da ciwon ciki,so naga babu amfanin amsa, in kuma tana so sai in siya mata wasu, mum wani irin kallo tamai tare da fadin waya gaya maka cikinta na ciwo? Nan yaba mum labarin abunda ya faru da taci abinci, mum tace ai wannan ba komai bane kuma zata iya shan chocolate din, yanzu idan dr yaga yaron ya fito da kayan baziji dadi ba, yace mum wannan ba damuwan mu bane, ita kam jawaheer tana kwance akan cinyar adda ta daura akanta a kai, duk tana jin abunda suke fada tadai yi shuru ne, tana tunanin irin wannan sabon salon na samir, adda tace jawaheer abinci na kitchen fah, tace na koshi adda, mlm yace mai kika ci? Tace munci abinci kafin mu zo nan, nan mum ta basu labarin abunda ya faru da jawaheer cikin harshen hausa, nan suka fara mata sannu, shidai da ido yake ta kallonsu, dan baji yake ba amma ya dan fahimta ya gane mum ta fada musu abunda ya faru da jawaheer dinne, tashi tayi ta zauna tare da rungumo adda tace zanyi kewarki addata, banso tafiya gobe ba, adda tayi dariya tace nima haka idan aka tafi sai kuma yaushe? Ido suka hada da m samir ya sakar mata wani irin mugun kallo, tayi saurin kawar dakai tare da fadin bazan dade ba zan dawo adda ta, haka sukai ta fira daka sun hada ido dashi ya watsa mata mugun kallo, daka karshe dai tashi tayi ta shiga ciki, bata dade da shiga ba shima ya wuce, hada kayanta tayi tayi, lokaci kadan ta gama hada kayan sannan ta kwanta dan ta huta, tunawa tayi da wayanta dake kashe ta tashi ta dauko ta kunna tana kunnawa saqo ya shigo cikin wayan, budewa tayi dan taga dr ne ya mata saqon ga abunda yace nan *haba jawaheer keda nake daukanki mai hankali da nutsuwa mai yasa zaki biyema wannan farin fatan bayan kin san irin tamu tarbiyan ba irin tasu bace kalli yanda yake wani riqeki kaman wani maharraminki haba jawaheer, tunda na fara ganinki nake sonki kuma soyayyan aure nake miki bawai na wasa ba, inaso ki bani dama mu fahimci juna sannan iyaye su shiga ciki, ina fatan zaki amsa bukata ta ngd daka dr nazir* tana gama karantawa ta lumshe ido lallai dr nazir namiji ne da duk wata mace zatai burin samu a matsayin namiji sai dai ita kash m samir ya sace mata zuciyarta tare da ruhinta bata ganin kowa sai shi, ya kamata ta fadama dr nazir gaskiya.... Dan shuru tayi lokaci daya ta tashi ta fita mum ce kawai a falo, tace mum ina adda? Mum tace tana kitchen fita tayi ta nufi kitchen din inda ta sami adda na zuba dan wake a tukunya wanke hannu itama tayi tazo tana taya adda jefawa tare da fadin adda kina son danwake sosai, dariya adda tayi tace ai akwai dadi ne, jawaheer tace lallai nikam bai cika damuna ba, adda tace kin bar dadi, tace ya akayi keda mutumin naga kaman dazu yana ta miki mugun kallo sannan an aiko miki da kaya daka dr ya kyautar, nan jawaheer ta bata labarin abunda ya faru bata boye mata komai ba, adda tayi dan murmushi tace jawaheer kici gaba da kula dr tunda har yace yana sonki, tace adda shifa m samir din fa? Adda tace yace yana sonki ne?? Shuru jawaheer tayi adda tace kiban amsa mana, tace a'a bai ceba amma ina fatan yace min haka, adda tayi dan murmushi tare da fadin jawaheer ke yarinya ce har yanzu baki san mai duniya take ciki ba, kawai inason kiyi duk wani abu da nace miki indai kina son ki tabbatar da zaki sami m samir ko bazaki sameshi ba, kar ki zauna zaman jiranshi kiyi biyu babu, idan m samir yana sonki dole yayi kishin ki, inko baya sonki komai za kiyi babu ruwanshi, dan haka ji shigo da dr cikin rayuwanki sannan koda kun koma wani abu ya faru ki dinga fadamin tace toh adda ta, haka sukai ta jefa danwaken har adda ta tsame tasa musu suna fira suna ci. Shiko m samir ya rasa dalilin da yasa ya tsani dr, shidai abu daya ya sani bawai yana son jawaheer bane, kawai yana tausaya nata ne, dan shuru yayi lokaci daya kuma yace ba haka bane, kawai bana sonta da dr dinne dan ban yarda da hankalinsa ba, daukan wayanshi yayi ya doka mata kira, ringing biyu ta dauka, yace mata kin gama shirin mamaki tambayar tashi ya bata tasan dai dazu yana ta nuna mata halin ko in kula, yanzu kuma yana tambaya waiko ta shirya, tace eh na shirya komai duk da basan komawa nake gobe ba, yace saboda wannan dan iskan dr din koh?? Jawaheer ina tunaninki yake wai yaushe ma kika fara sonshi ne?? Shuru tamai tana jin ikon Allah daka cewa bata son komawa ya hakikance yana ta zagin mutum wanda baisan maike faruwa ba, tace kana cin hakkinsa domin shi bai san maike faruw....... Wani irin tsawa ya mata tare da fadin yimin shuru ban san haka kike ba, da tun farko ban daukeki a matsayin friend ba, wani irin takaici taji lokaci daya maganan da bata zata, zata fito ba taji ta fada nima fa budurwanka bace kace ni kawarka ce ina da right in kula duk wanda naga dama, jin ya kashe wayan yasa ta fara tunanin maita fada mishi haka, daura hannu tayi akai tana kuka tare da fadin Allah yasa ba fushi yayi da ita ba, daukan wayan ta tayi ta kirashi amma saiya saka mata busy alaman ya kashe wayan, daka karshe ma data kara kira sai taji switch off, kuka ta saki mai karfi mum dake kwance kusa da ita tana bacci ta farka tare da tanbayan lfya jawaheer? Tace mum wlh ina son m samir ban son in rasa shi, mum ta janyota jikinta tana fadin kiyi hakuri jawaheer idan Allah yasa shi zaki aura dole ya zama mijinki ance matar mutum kabarinshi, tace hakane mum, in ban sami m samir ba zan iya shiga cikin wani hal...... Toshe mata baki mum tayi tana ta rarrashinta, dakyar tayi shuru amma maganan bacci kam babu shi, dan ya gudu yanda taga dare haka taga safiya, tunda tayi sallah asuba, ta nufi dakin adda, adda tace jawaheer lafiya naga kaman idanki a kumbure? Kuka ta fara tare daba adda labarin abunda ya faru, adda tace ai gaskiya kika fada mishi baki Karya ba, aishi ba saurayinki bane, dan haka dole ji tsaya da wasu, jawaheer tace haba adda nifa shi nake so, adda tayi tsaki tare da fadin ai sai kiyi ta son nashi, kina son mutum yana miki wulakanci dan yaga ya hadu, shima yanda ya hadu haka kema kika hadu, babu namijin da zai ganki yaji bai sha'awar ya mallakeki, dan haka wlh kima cireshi a ranki tun kafin ya sa miki ciwon zuciya, gwara ki nemi mai sonki kibar wanda baya sonki, jawaheer cikin kuka tace adda bana son wannan magan ganun naki basu da dadin ji wlh, adda dariya tayi tare da fadin kaji ja'ira gaskiyan ne baki so? Tace adda taya zan cirshi a raina bayan kin san ba abu bane mai yihuwa? Adda tace ina zaune zanji kince kin cireshi a ranki amma fah kar kice na miki baki, kallon adda tayi sororo tace kaman ya adda? Adda tace nan gaba zaki gani badai namiji bane shi, jawaheer tashi tayi ta fita alaman taji haushin maganan adda, dariya adda tayi tace kai Allah ya yaye miki yarinya sai kace a kanfa aka fara soyayya ita ko zuciya ma taki yi, shiba sonta yake ba amma ta like mai, dakinsu jawaheer ta shiga taga mum na hada kaya mum tace yauwa jirgin 8 za mubi kizo ki shirya, jiki a sanyaye tace toh fita tayi ta nufi toilet tayi wanka da ruwan sanyi dan garin ana dan zafi, fitowa tayi ta fara shiri cikin wata doguwar riga na less yayi mata mugun kyau, duk da batai makeup ba, ta daura dankwali irin ture kaga tsiya ta yafa wani karamin gyale, sannan ta fita falo, inda adda tasa musu abinci kunu da alale da farfesun kayan ciki, zama sukai suna ci amma ita kam jawaheer tunani take saida mun ta lura da ita tace jawaheer tayi firgit mum ta girgiza kai tare da fadin kici abinci mana, bata ce komai ba ta fara ci, bata wani ci da yawa ba ta ajiye, adda tace zo muje ki rakani can gidan, tashi tayi suka fita ita kuma mum ta fara shiri itama, bayan sun fita tafiya sukai mai dan nisa jawaheer tace kai adda na gaji, adda tace muje mun kusa, kan wani dutse suka je suka zauna, jawaheer tace ina gidan? Adda tace jawaheer babu inda zamu nace muzo nan ne saboda mu sami daman magana ni dake, inaso kiji kuma ki duba ki gani, jawaheer idan kika duba rayuwa yanzu ya canza a baya kinyi kuskure kin nuna ma samir kina sonshi yaki yarda ya soki kaman yanda kike sonshi, idan kika duba zaki gane tun daka sanda kika furta kina sonshi zaiga bazaki iya rayuwa ba tare dashi ba, sannan namiji yace yana sonki yata kaya balle kece kika furta mishi kalman so, aikin bani, wlh indai kika bi yanda na fada miki zai fito yace miki yana sonki, jawaheer tace me kenan? Tace matso kiji, magana ta mata a kunne, jawaheer tace amma kina ganin hakan zaiyi? Adda tace insha Allah ki gwada, tashi mu koma ma dan nasan yanzu ke ake jira, kallon agogon hannunta tayi taga 8:30 tace adda lokaci ya wuce gashi wayana yana gida, adda tace kai muyi sauri toh, suna karasawa kofar gidan taga motocin m samir a kofar gidan, gabanta taji ya fadi ance jirgin 8 za subi gashi yanzu 9 ya kusa, tana shiga ta ganshi a tsakar gidan yana kaiwa da komowa,waigowa yayi ya ganta a tsaye wani irin kallo ya mata tare da fadin daka ina kike?? Tace mun fita ne da adda, yace karfe nawa yanzu?? Tace 8:49 yace what time zamu tafi? Tace 8 yace gud tawo muje fita sukayi suka hadu da adda, ya kira security dinshi ya mishi magana yace ya fadama adda, yace adda yace in fada miki mum ta wuce saboda jawaheer ta bata lokaci suma yanzu zasu tafi a mota, nan adda taita musu addu'an sauka lfya, jawaheer tace bari in dauko kayana, riqota yayi tare da turata mota suka tafi, tace mishi kayana fah? Yace keep quite karki dameni plz, shuru tayi tana kallon sa, lokaci daya tasa kuka waigowa yayi yana kallonta, yace driver ya faka, bayan driver ya tsaya yace mishi ya dan fita, driver na fita ya janyota jikinshi tare da rungumeta ido ya lumshe yace miye haka jawaheer? Tace haka aboki ya kamata yama kawarshi mai yasa kake fushi dani? Sakinta yayi da sauri kana kallonshi zaka gane ranshi a bace yake, nanata sunan yayi aboki wato yanzu bata sona, aboki ta daukeni........... *maryam obam* *JAWAHEER* *STORY AND WRITEEN BY......* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA* *(maryam Obam)* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝* *{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}* *wattpad @maryam-obam* *WWW.Maryamobamnovels.com* https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/ *DEDICATED TO.....* *Nafisa mrs dan malikin kawo* Page 37-38 Dago dakai tayi ta kalleshi sannan tace plz ka daina fushi dani, dan murmushi yayi tare da fadin komai ya wuce rungumeshi tayi tare da shafa mishi gashin kanshi, dariya yayi yace karki bata min gashin kai, tace sai in gyara maka, kiran driver yayi yaja suka wuce, tafiya suke kowa da abunda yake tunani, ita ta gefenta tana tunanin yaushe zai sota, yaushe zai fahinci irin son da take mishi, shiko ta gefenshi yana tunanin tunda sun bar yola babu ita babu ganin dr dama shine damuwanshi ya rasa mai yasa ya tsani dr din, dan waigowa yayi ya kalleta bacci yaga tanayi dan jiya batai bacci ba tunani ya hanata, ido ya kura mata yanda take bacci hankali kwance, yana cikin kallonta yaji ta fado jikinshi, murmushi yayi tare da kara gyarata ya mikar mata da kafa tare dasa kanta akan kafanshi, tafiya suke mota nata sharara gudu, bai taba long journey ba a mota sai yau, dan haka shima ya gaji sosai, amma yana jin dadin tafiyan, bude ido tayi taga anata gudu, tashi tayi daka jikinshi da sauri tana murmurza ido, murmushi ya sakar mata, tace har yanzu bamu kai ba? Kai ya daga mata alaman eh, tace kai wlh na gaji gaskiya da nisa, murmushi yayi tare da fadin matso nan, matsawa tayi kusa dashi yasa hannunshi akan kafadanta yace kefa kinyi bacci bai kamata kiga nisan wajan ba, tace ni nasha ina tashi zan ganni a gida, dariya yayi yace oh i see sai yasa kikai bacci, kai ta girgiza alaman a'a, yace toh miye? Tace jiya banyi bacci ba sai yasa nayi yanzu, kallonta yayi yace maiya hanaki bacci?tace babu komai kawai dai bana jine, shuru yayi tare da aiya nawa cikin ransa kodai tana tunanin wannan dr din ne? Tsaki yayi mara sauti amma duk da haka taji, dago kai tayi da sauri ta kalleshi ganin ya tamke fuska yasa tasa hannunta tana shafa mishi fuskan tare da fadin miye kuma? Hannunta ya cire daka fuskan nashi tare da fadin babu komai, bata kara cewa komai ba har suka zo wani kauye da ake ta siyar da abubuwa, tace driver dan faka, driver tsayawa yayi a gefen titi, kallonta yayi yace mai za kiyi tace yunwa nake ji abu zan siya, yace nop ki bashi ya amso miki, tace ai ban san mai zan siya ba saina fita na gani, kallon wajan ya farayi yana dubawa, tsaki yayi tare da cema driver yaja motar su wuce, driver ya tada motar suka tafi, tace ya zamu tafi ban siya komai ba, yace saboda abun wajan bai min ba, tace nifa yunwa nake ji, yace sorry in naga wajan da yayi min sai a tsaya kici, kai ta daga alaman toh, tafiya suke tayi babu wanda ya kara magana, har suka shiga cikin wani gari yace driver ya tsaya, bashi kudi yayi yace ya siyo mata kaza da drinks, amsa yayi ya fita jim kadan sai gashi ya kawo kaji har guda biyar, da drinks da yawa, amsa tayi ta fara budewa kudi ya kara ma driver yace kuma kuje kuci abinci tare da sauran security din, yace ok, bude kazan tayi tace kai yayi yawa, fara ci tayi tare da miqa mai kai ya girgiza tare da fadin nop bana ci, bata fuska tayi tace in baka ciba nima zan daina ci, kafada ya daga alaman bai dameni ba, ganin haka yasa ta ajiye naman wai tayi fushi, murmushi yayi tare da daukan naman yasa mata a baki ta kawar dakai yace plz kici ban san taurin kai, daukan naman tayi shima takai mai wajan baki ya kawar dakai ta kara matsawa kusa dashi zata bashi ya janyota jikinshi wanda yasa bakinta ya mannu a nashi, dukansu tsayawa sukai cak, sunyi wajan minti daya kafin ya danja baya, da sauri itama ta matsa tare dajin wani iri, shuru dukansu sukayi na wani lokaci sannan taji muryanshi yana fadin muci, bata musa ba suka fara ci, har driver ya dawo suka tafi baka jin karan komai sai wakan nicki minaj, sai wajan karfe hudu suka karaso garin abuja, tana ganin sun shigo taji wani irin dadi, gida suka nufa da sauri ta fita suka ci karo da khalil wani irin runguma sukai ma juna na murnan ganin juna, khalil yace sis sake ni mana inje inga samir, tace babu ruwana dakai dariya yayi yace sorry sis ai nafi jin dadin ganinki akanshi, dariya tayi tace mai wayau, sakinshi tayi ya nufi m samir dake tsaye yana kallonsu yana dariya hugging dinshi yayi tare da fadin bros u r wlcm, m samir yace thanks, ya umar ne ya fito shima cikin murna yayi hugging m samir sannan suka shiga ciki, jawaheer dakinta ta nufa tana shiga tayi toilet dan tayi wanka, bayan tayi wanka ta fito tasa wani wando 3quater da wata top mai bala'in kyau ta fito falo ta gansu su duka suna ta fira hawaye ne ya zubo mata tunawa da tayi bata hada komai dasu ba, wani irin zafi takeji daka zuciyarta, juyawa tayi zata koma daki dad ya kirata tsayawa tayi cak dan haka ya tashi ya nufi inda take, ya janyota jikinshi tare da fadin ina zaki, tace zani daki ne dad, yace no muje, kaita yayi har wajansu ta zauna kowa idanshi na kanta, tausayinta suke ji sosai, ga hawayen da take son boyewa ya kara zubowa, khalil yace sis miye haka? Bata bashi amsa ba sai kuka data saki tare da fadin mum plz muga kwalin da aka baku ni, kowa ya tausaya mata da turanci take magana kowa dake falon yaji mugun tausayinta, mum cikin sanyin jiki ta tashi ta nufi dakinta sai gata da kwali, miqa ma jawaheer tayi ta riqe kwalin tana kuka, budewa tayi taga international passport, dauka tayi taga wasu abubuwa akai budewa tayi tana kuka wani dan karamin passport ne ya fito, da sauri ta dauka tana kallon hotan fuskan matan sak mata da sauri ta nuna ma mum tana fadin mum kalla ki gani da sauri mum ta amsa tace wlh itace ta bamu ke jawaheer itace kuma duk yanda akayi mahaifiyarki ce dan ga kaman ku nan, ci gaba tayi da duba kayan ta dauko wasu riga da wando masu kyan gaske tana kallo, mum tace wannan sune kayan data bamu ke sune lokacin a jikin ki, rungume kayan tayi tana kuka mai ban tausayi m samir dake zaune yana kallonta cike da tausayi ya tashi ya nufeta tare da goge mata hawayen yace jawaheer kiyi hakuri ki daina wannan kukan nayi miki alkawarin haduwa da mum dinki bada dadewa ba wannan nauyin yana kaina, kuka ta kuma saki tare dayin hugging dinshi duk wanda ke falon saida tausayin jawaheer ya tsargo mai cikin zuciya, musamman khalil da sukafi sabawa dashi lokacin da yaji ba kanwar shi bace yayi takaici sosai dan yana son jawaheer, m samir amsan kwalin yayi tare da fadin mum a nan zan zauna ina daki na? Mum ta kalli jawaheer tace jawaheer kaishi dakin kusa dana khalil, mum tayi hakan ne dan jawaheer ta daina kukan, tashi tayi ta fara tafiya yana biye da ita a baya, bayan sunje kofar dakin taja jiki ta tsaya tare da nuna mai kofar da hannu alaman ga dakin nan, murmushi yayi tare da fadin tare zamu shiga, batai magana ba ta bude kofar ta shiga shima ya shigo, dakin akwai komai a ciki ga kamshi dake tashi daka ganin mum dazu tasa akasa komai dan tasan da babu komai a dakin, kallonta yayi yace wow dakin yayi kyau bari inyi wanka ki zauna ki jirani, kai ta daga mai alaman toh, yana shiga ta fita waje dakinta ta nufa ta kwanta tana kuka mai cin rai, yanzu basu mum bane suka haifeta ji take abun ya dawo mata sabo, musamman da taga bros umar khalil ga mum ga dad ga samir, amma ita bata hada komai dasu ba, mai yasa haka ya faru da ita mai yasa mum dinta ta bada ita, lallai tana bukatar jin amsa ada bata da burib haduwa da mum dinta amma a yanzu tana so, tashi tayi da sauri ta dauko wasu takardu tasa a jaka tare da daukan key din mota, har zata fita ta tsaya ta koma ta nufi wardrobe dinta ta dauko wata doguwar rigan atamfa tasa tare da yafa gyale akanta karami fita tayi ta nufi dakin m samir tare da fatan Allah yasa bai fito daka wanka ba, shiga tayi tako ci sa'a bai fito ba wajan kwalin ta nufa ta bude tare da kwashe kayan dake ciki tana kokarin fita taji ya kira sunanta da jawaheer tsayawa tayi cak, ba tare data waigo ba, ganin bata waigo ba yasa ya fara matsowa kusa da ita ji tayi ya riqota ta baya tare da juyo da ita, kallonta ya tsaya yi sannan yace wannan kayan fah? Mai zaki dasu? Kallonta ya kumayi daka sama har qasa sannn yace ina kuma kikë shrin zuwa? Wani irin hawaye ne ya gangaro mata sannan tace zan tafi zan tafi gaba daya zanje neman mahaifiyata lokacin da nake yola banji ina son ganinta ba, amma dawowa na nan gidan yau yasa naji ina son haduwa da ita, yau nasan miye iyaye bazan iya zama a nan ba dole in tafi in nemot..... Janyota yayi jikinshi tare da toshe mata baki yace ya isa haka jawaheer ya isa haka, karki kara tunanin barin nan gidan, kina tunanin kinyi adalci kenan yasu mum za suji in suka ga bakya nan?? Kinyi tunanin haka? Tace karka dakatar dani ka barni dan Allah yace jawaheer mai kike tunani kin san halin da kowa zai shiga kuwa? Nima kaina kin taba tunanin wani hali zan shiga idan aka nemeki aka rasa? Da sauri ta dago dakai suka hada ido lokaci daya kuma ta fashe da kuka tare da fadin koda na tafi kuna raina har abad......... Shhhhhhhhh ya dakatar da ita tare da fadin okey na fahimta amma kafin ki tafi inaso ki fadamin wani irin so kike min dahar kike tunanin barina gaba daya saboda wani dalili?? Zaki iya nesa da abunda kike so ba tare da kin sameshi ba?? Kasa magana tayi sai kuka da take tayi, shima shurun yayi tare dayin hugging dinta sosai yana mai jin kukan nata har cikin ranshi, ido ya lumshe ya rasa mai yasa yake jin abubuwa da dama akan jawaheer wanda baya ji akan ko wata mace, ko sonia da sukai zama tare na lokaci mai tsawo baya jinta kaman yanda yake jin jawaheer a halin yanzu sakinta yayi tare da janyota suka zauna akan gadon dakin yace jawaheer kiyi shuru kibar wannan kukan, nayi miki alkawarin neman miki mum dinki jibi zan koma spain muna da wasa bazan dawo kasar nan ba har sai na nemo miki mum dinki, inaso kimin alkawari ba zaki kara tunanin barin gidan nan ba, kai ta daga cikin kuka alaman eh, tare da rungumeshi tana fadin nagode sosai Allah ya baka abunda kake so, a hankali yace ke nake so jawaheer.......... *maryam obam* *JAWAHEER* *STORY AND WRITEEN BY......* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA* *(maryam Obam)* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝* *{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}* *wattpad @maryam-obam* *WWW.Maryamobamnovels.com* https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/ *DEDICATED TO.....* *Nafisa mrs dan malikin kawo* Page 39-40 Da sauri ta dago kai ta kalle shi, murmushi yayi tare da fadin yes jawaheer u r my sister bani da wata yar uwa mace sai ke, so kinga dole in soki, ajiye ajiyan zuciya tayi tare da lumshe ido dan ba haja tai zatan jiba, tashi tayi tare da fadin saida safe, shima tashin yayi yace sis bacci yanzu miye time? Tace na gaji ne sosai, yace ok good night, fita tayi ya bita da ido harta rufe mai kofar sannan ya lumshe ido tare da buga hannunshi akan dayan hannun yace damn, shima kwanciyan yayi tare da tunanin jawaheer din tare da alkawarin neman mata mum dinta a duk inda take a fadin kasar nan. Koda ta shiga daki kuka ta fashe dashi tare da fadin lallai na yarda m samir bazai taba sona ba, Allah ka jarabceni da son wanda baya sona amma ina roqanka kasa in cinye wannan jarabawan, shuru tayi tare da fadin lallai wannan shine maganin matsalata, wannan ne karo na farko data taba tunanin tayi aure ko zata cire m samir a ranta, lallai shine mafita amma komai zanyi sai naga mum dina zanyi aure inyi nesa dashi gaba daya da wannan tunanin bacci yayi gaba da ita. Washe gari m samir tun karfe 7 ya fita shida khalil da security dinshi, direct wajan hukumar shiga da fice suka nufa, inda suka basu international passport din mum din jawaheer, tare da kudi masu yawa akan su nemo bayanai akanta, ce musu sukayi su dawo nan da sati daya, hakan akayi suka tafi bayan yawan mutanen da suke ta cincirindon son daukan hoto da samir dakyar dai suka shiga mota suka bar wajan akan nanda sati daya zasu dawo ko kuma su zasu nemeshi sun daiyi exchanging number, yawo suka dinga yi ranan. Jawaheer kam tunda ta tashi tayi wanka, tasa wata atamfa mai ruwan ja da ash yayi kyau atamfar anyi dinkin riga da skirt saiya fito mata da surarta das a jikin kayan tayi bala'in kyau duk da ba makeup a fuskanta, wani karamin gyale ta yafa ta fito ta sami mum ita daya a falo, tace ina kwana mum? Amsawa mum tayi cikin sakin fuska tare da tambayanta ya gajiyan hanya, tace alhmdlh mum hanya babu dadi, mum tace ina zaki naga kaman fita za kiyi, tace eh mum yau zan shiga skul mun koma tun last week, mum tace kai jawaheer kina wasa da karatu tun last week kuka koma shine kikai shuru baki fara zuwa ba, yanzu kin san lecture nawa kikai missing? Tace mum karki damu attendance ne matsalan kuma nasa ana daukan min, mum tace toh shikenan dan Allah ki daina wasa kije kici wani abu kafin ki tafi, tace mum zanci a skul, babu yanda mum batayi ba amma taki ci tace bata jin yunwa, fita tayi ta wuce daya daka cikin motar gidan ta shiga mai kiran prado, ita da kanta take tukin har cikin makarantar,faka motarta tayi sannan ta nufi department dinsu, tun daka nesa ta hango yan class din nasu daka gani akwai lecturer a ciki domin duk sun bada hankalinsu wajan kallon waje daya, tana isa kam taga lecturer ne a ciki, dan haka ta shiga cikin sanyin jiki, kallonta lecturer din yayi kaman zaiyi mata magana sai kuma ya fasa, ji yayi tace mishi morning amsawa yayi sannan ta nemi waje ta zauna, kowa yayi mamakin dabai koreta ba dan yau kwananshi uku da fara basu darasi sannan duk wanda yazo idan ya shiga baya bari ya zauna, bayan jawaheer ta zauna ya kuma kallonta tare da sakin murmushin dashi kanshi bai san yayi ba, ganin itama ta mayar mai da martani yasa ya gane abun da yayi, da yake ya iya duniyanci saiya basar yaci gaba da lecture har lokacinsa yayi, sannan ya kalli jawaheer yace daka yau karki kara shigo min class indai na rigaki shigowa, kai ta daga alaman naji, sannan ya fita, tsaki tayi tare da dauko wayanta tana dan dannawa, kiran dr ne ya shigo kaman ba zata dauka ba, komai ta tuna kuma ta dauka tare da fadin hello, ajiyan zuciya ya sauke tare da fadin jawaheer wai nayi laifi ne aka daina daukan waya ta? Uhm kawai tace yaci gaba da fadin jawaheer naje adda tace min wai kin koma jiya, shine ko sallama babu, tace kayi hakuri tafiyan ne yazo a bazata, yace bakomai da fatan anga sako na, dan shuru tayi kafin tace uhm, murmushi yayi sannan yace ina fatan za'a bani dama? Tace Allah ya taimaka ya shige mana gaba, wani irin dadi yaji tare da fadin kenan an bani dama, kai yau ina farin ciki Allah ya dai daita mu, bata ce komai ba sai murmushi da tayi, wani lecturer ne ya shigo tace ina zuwa zamu fara lecture yace ok tare da kashe wayan, sai lecture ake musu amma ita sam bata san mai ake fada ba, domin tayi nisa cikin duniyar tunani ba komai take tunani ba sai na amince ma dr akan yaci gaba da nemanta har Allah yasa su fahimci juna tayi hakan ne da zuciya daya domin tana da burin ta sami miji tayi aure dan ta cire m samir a ranta duk da tun jiya take ta kokarin tusa ma kanta kin shi amma hakan ya faskara, lallai koda banga mum dina ba indai muka fahimci juna dole inyi aure in huta, ji tayi ana mata magana, wata yarinya ce kana ganinta kasan suma suna da arziki, jawaheer firgit tayi taga lecturer din ya fita tace kai ashe har an gama, yarinyar tayi murmushi tare da fadin sunana zarah, yau na fara zuwa lecture saboda nayi ciwo sai nayi differing da yanzu ina 3lv amma yanzu ina 2lv, jawaheer tace Allah sarki Allah ya baki lfya, murmushi zarah tayi tare da fadin baki fadamin sunanki ba, tace jawaheer murmushi zarah tayi tace suna mai dadi zarah ta amshi no din jawaheer tare da fadin in akwai lecture zata dinga fada mata, sannan tace duk abunda jawaheer bata gane ba ita zata dinga nuna mata, nan jawaheer tayi godiya tare da fadin an gama lecture din yanzu? Zarah tace a'a akwai wanda zai zo karfe hudu, jawaheer tace kai bari inje inci wani abu yunwa nake ji, zarah tace muje tare toh, fita sukayi tare suka je wani restaurant a cikin skul din, fried rice jawaheer tace a bata, ita kam zarah snacks ta amsa da drinks suna ci suna fira har suka gama, fita sukayi suka zauna wajan wata bishiya ko wacce na danna wayarta, wayan jawaheer aka fisge daka hannunta da sauri ta dago taga ko waye khalil ta gani dariya tayi tare da fadin bros mai kazo yi? Yace zo muje ki gani, zarah ta dago kai tare da kallon khalil gaidashi tayi jawaheer tace bros dina ne, tace ashe yayanmu ne, dariya yayi sannan yace ma jawaheer ga mota can kije ana jiranki ni bari in zauna a nan muyi fira da zarah, dariya tayi sannan ta nufi motar dan a zaton ta dad ne, tana budewa taga m samir zama tayi a cikin motar tare da rufewa shine a mazaunin driver daka gani shine ya tuka motar, kallonta yayi tare da fadin baki so gani na ba koh? Tace a'a , yace mai yasa kika daure fuska? Tace babu komai, murmushi yayi tare da fadin jawaheer yau baki damu da inda na shiga ba, baki kira niba, tace bani da abunda zance maka ne, yace ok toh bari in tafi, bata bude kofar ba sannan bata motsa ba, ya kuma cewa zan tafi, kallonshi tayi da idonta daya rine kadan kawai take jira tayi kuka, janyota yayi jikinsa yace karki sake kice zaki fito da wannan hawayen, jawaheer na rasa mai yasa ko kadan bana son ganinki cikin damuwa, bana son inyi nesa dake na saba dake cikin lokaci kadan, gobe zan tafi inaso plz koda na tafi kici gaba da riqemin kanki karki bama kowa daman shiga rayuwanki, dagowa tayi ta kalleshi dan bata gane mai yake nufi ba, murmushi yayi tare da fadin nan gaba kadan zaki fahimta abunda nake nufi, but yanzu ina son ki riqemin kanki ban son ko wani namiji ya shigo cikin rayuwanki, naso mu tafi tare sai naga koda munje banda tym nd ban son in barki cikin kadaici, shuru tayi tana tunani toh mai yake nufi kar inbar wani ya shiga rayuwa na? So yake in zauna banyi aure ba..... Katseta yayi da fadin zanyi missing dinki sosai, murmushi tayi tare da fadin nima haka, yace taya zan gane? Murmushi tayi tare da fadin komai kaji na fada a kanka dagaske nake kuma hakan nake ji, a musulunce mace zata iya fadama namiji tana son shi, amma a al'adance abun kunya ne, samir a kasar ku na fada maka ina sonka, amma ka nunamin inyi hakuri naji kuma nayi duk da ban cire raiba, amma a yanz..... Shuru tayi yace yanzu me?? Na hakura dakai ina son nima in sami mai sona inyi aure bada dadewa ba, kallonta yayi yana dan nazari kafin yace zaki iya auran namijin da baya sonki? Tace zan iya indai ni ina sonshi, murmushi yayi tare da fadin mai kike tunanin zai faru bayan auren? Tace zaman hakuri, yace har zuwa wani lokaci zaki ta zaman hakuri dashi, tace bazan iya sani ba, amma idan hakan ya faru zuciyata zata yanke a lokacin, yace ok naji zaki iya aurena bayan kin san bana sonki? Wani irin hawaye ga zubo mata, tace zan iya burina a kullum in kasance dakai a koda yaushe, yace jawaheer shikenan nayi miki alkawarin zan aureki amma inaso ki sani ban taba kallonki a matsayin budurwa taba, sai yar uwata, inaso kiyi tunani akai indai kin amince nanda wata biyu za muyi aure in kuma baki aminceba shikenan kiyi tunani akai, shuru tayi na wani lokaci sannan tace bana tunani akan sonka a kullum tunani na shine in sameka a matsayin miji dan haka na amince, yace ok zan fadama dad yau sai a fara komai duk abunda kike bukata sai ki fadamin, amma ina so ki sani indai kika shigo babu saki kar nan gaba kice baki son zaman, murmushi tayi tare da fadin bana tunanin baki na zai iya fadin haka,yace good zamu koma gida anjima sai mu karasa magana dama ke nazo in gani, tace ok sannan ta fara kokarin bude kofar amma yaki buduwa, kallonshi tayi alaman ya bude mata, yace haka zaki faramin babu wani abu sai kawai ki fita, rufe ido tayi tana dariya sannan ta matsa kusa dashi ta mishi peck a goshi, dariya yayi sannan ya bude mata motar ta fita, da ido ya bita har ta karasa wajan su khalil da suke ta fira shida zarah, tace toh saika tashi ku tafi dariya yayi tare da cema zarah sai munyi waya, tace ok, sannan ya tafi, jawaheer kallon zarah tayi tace badai har an kulla luv ba? Zarah tace haba luv a minti nawa, dariya suka sa dai2 lokacin wannan lecturer din yazo yace ma jawaheer tazo yana son ganinta, bayan ta matsa kusa dashi yace ga no dinshi yana son ta kirashi, bata yayi tasa sannan ta koma wajan zarah tana fada mata abunda yace mata, zarah tace haba nayi mamakin dabai koreki ba, ashe ya kamo fish, dariya sukayi har 4 yayi suka shiga lecture basu fitoba sai 6 gida ta nufa direct a gajiye ta shiga gida babu kowa a falo dan haka tayi dakinta, tana shiga toilet ta nufa tayi wanka wardrobe dinta a kusa da toilet dinta yake kaya tasa sannan ta fito tana fitowa taga mutum a dakin yana kalle kalle, kallonta yayi rai a bace sannan yace jawaheer jiba dakin ki duka pics dina ne harta carpet dinki, indai kina sona mai yasa kike kula wasu mazan?? Ido ta dan zaro alaman wana kula..... Tace ni yaushe kum...... Ya isa ban son jinki dazu waye naga yana baki number kina sawa?? Shuru tayi kaman ba zatayi magana ba, can tace lecturer dinmu ne fah, yace lecturer number din mai yake baki?? Tace yace in kirashi ne zai mun magana, ido ya lumshe ji yake kanshi na mishi wani irin tafarfasa lokaci daya idanshi ya kade yace mai zaki mishi idan kin kira shi? Tace nima ban sani ba, kallonta yayi kaman zaiyi magana sai kuma ya fasa ya fita fuuuuuuuu, dakinshi ya nufa zama yayi akan gadon dakin shidai yasan bawai son jawaheer yake ba, kawai yana tausaya mata sai yasa yake son ya aureta sannan baya son tana nesa dashi, to mai yasa nake kishi idan wani yana mata magana?? Wata zuciyar tace saboda kana sonta da sauri yace nop, kawai dai dan zan aureta ne dole kuma inyi kishi a kanta,karan wayanshi ne yasa ya dauka yaga dad din su khalil ne dauka yayi dad din yace mishi samir gani na dawo ina falo, yace ok dad ga ninan, tashi yayi ya fita ya nufi falon, samun dad yayi da mum akan dinning dad yace samir ya gida gobe ne tafiyan koh? Yace eh dad, dad yace masha Allah, Allah ya taimaka, yace ameen, yace dad dama inaso inyi maka magana nida jawaheer mun fahimci juna, kuma...... Dan shuru yayi dad yace inaji, yace muna son muyi aure in kun amince, dad cikin murmushi yace alhmdlh alhmdlh abu yayi kyau, mum tace toh yanzu ya za'ayi, amma inaga da an jira an duba iyayenta koh? Dad yace a'a in ba'a gansu ba fah, haka zatai ta zama? Kinga dole kuwa tayi aure, mum tace hakane, m samir yace dad plz ban son bikin ya wuce wata daya, mum harara ta sakar mai tare da fadin toh mara kunya, kai ya sosa tare da tashi yabar wajan suka bishi da dariya, dakinshi ya koma ya kwanta haka kawai yake jinshi cikin farin ciki da annashuwa, haka har bacci ya daukeshi,. Washe gari jawaheer nada lecture karfe 8, dan haka da wuri ta shirya duk da ranta a jagule yake, dan tasan m samir yana fushi da ita, gashi yau zai tafi, ji tayi ba zata iya tafiya ba har sai ta ganshi, dakinshi ta nufa taga baya nan, fita tayi ta nufi falo taga mum na gyara kayan abinci akan dinning, tace morning mum, mum tace har kin fito? Tace eh mum gashi har na kusa makara, na tafi sai na dawo, mum tace ok samir yace in fada miki ya tafi, sannan ga sako ya bayar a baki, dam taji kirjinta ya buga wato tafiya yayi shine bai mata sallama ba...... *maryam obam* *JAWAHEER* *STORY AND WRITEEN BY......* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA* *(maryam Obam)* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝* *{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}* *wattpad @maryam-obam* *WWW.Maryamobamnovels.com* https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/ *DEDICATED TO.....* *Nafisa mrs dan malikin kawo* Page 41-42 Mum ta dauko wani karamin bag ta bata, amsa tayi ta koma dakinta ta ajiye tare da fashewa da kuka, wato haka za'a fara kenan, kallon jakan tayi ta bude taga kudi masu uban yawa kuma duk dallar, sai wata takarda data gani a ciki, budewa tayi taga anyi rubutu kaman haka...... *ga kudi nan kisai duk abunda kike bukata kin san ban san ya al'adunku suke ba, ki fara siyayyan abunda kike bukata inna dawo sai mu karasa wasu abubuwan, sannan inaso ki sani ni bana daya daka cikin maza marasa kishi dan haka kisan wa zaki aura ina da kishin kaina dan haka dole inyi kishin iyalina, idan kika kara kula wani ban yafe ba sannan idan na sami labari zaki hadu da fishina bye* baki ta sake tana mamaki lokaci daya kuma tayi dan murmushin takaici, tare da tunanin yanda rayuwan aurensu zai kasance ita dashi, bata taba tunanin zata aura mijin da zai bude baki yace baya sonta ba har kuma ta yarda da auran, wani siririn hawaye ne ya silalo mata a fuska jin karan wayanta yasa tayi saurin goge hawayen zarah ta gani, dan haka ta dauka da sauri ban san mai zarah tace mata ba naji tace gani nan zuwa, har takai kofa ta tsaya tare da waigowa komawa tayi ta dauki jakar ta fita, a falo ta kara ganin mum tace yauwa mum gashi kudi ne a ciki yace in fara siyayya kafin ya dawo, murmushi mum tayi tare da fadin ok in kin dawo mayi magana tace ok tare da fita. Makaranta ta nufa direct bayan tayi parking ta kalli agogon dake manne a hannunta tare da fadin 8:03 Allah yasa bai shiga ba, jakarta ta dauka ta fita ta nufi department dinsu a tare da lecturer din suka shiga, kallonta yayi yace u r lucky 2day, murmushi kawai tayi ta nemi waje ta zauna, inda ya fara koyar dasu harya gama ya musu text, sannan ya kalli jawaheer yace sameni office dina yanzu, yana fadin haka ya fita, kallonshi tayi ta banga mai harara ta baya tare da fadin ko uban me zan mishi oho, zarah tazo kusa da ita tare da fadin sai ki tashi kije, hararan zarah tayi tare da fadin muje ki rakani, zarah tace wa? Ni din? Tab ai in kin ganni a lahira kaini akayi, ke yace kije dan haka babu inda zani, tashi tayi ta fita zarah tayi dariya tare da bin bayanta har kofar office dinshi zarah ta rakata amma taki yarda ta shiga, nocking jawaheer tayi taji shuru karayi tayi sannan akace come in, budewa tayi ta shiga, akan kujera ta sameshi yana duba wasu takardu, ganin ta shigo yasa ya saki murmushi, tare da fadin jawaheer right? Kai ta daga alaman eh, ya nuna mata kujera tare da fadin zauna mana, zama tayi fuskanta tamke, yace jawaheer mai yasa baki kira niba? Tace na manta ne, yace ok so yanzu ni sai ki bani number dinki, ko kuma ki kirani, tace zan kira inna koma gida, yace ok muga wayanki, kaman karta bashi amma babu yanda ta iya ta miqa mai, kiran layinshi yayi sannan ya mika mata wayan tare da fadin baki saving din number dina bama, dan murmushi tayi yace bari in gabatar miki da kaina sunana yusuf, ni dan garin kaduna ne wato dan zaria, ina da mata daya da yara biyu, jawaheer tunda na ganki naji Allah yasa min sonki sannan ni bada wasa nake ba da aure nake sonki, shuru tayi tana kallonshi, tare da takaicin kalaman da yake fada mata, amma ya dan burgeta dan da farko tayi zaton kalan lecturer din nanne masu bata yan mata, amma sai taji sabanin haka, sannan yusuf ba laifi yana da kyau sannan mijin nu nawa ne a ko ina, amma ita bata ganin kowa sai samir dinta kawai.... Katseta yayi da fadin jawaheer ya naji kinyi shuru, magana za tayi ta kasa ganin haka yasa yace kije zan kiraki zan baki lokaci kiyi tunani akai, da sauri ta tashi ta fita, wajan zarah ta nufa, zarah na ganinta ta tashi tare da fadin ya akayi? Tace hmmm muje kiji, suna tafiya tana bama zarah labarin abunda ya faru, zarah tace kai amma ni kam jawaheer mai zai hana ki yarda dan naga....... Tace dakata taya zan yarda bayan nanda wata biyu biki na, ido zarah ta bude tare da fadin ke dawa? Jawaheer tace m samir, shuru zarah tayi tana nanata sunan tare da fadin ni kam ina jin sunan, yauwa na tuna wani dan kwallon kafa ne mai irin sunan, jawaheer tace to ni dan kwallon zan aura, zarah kwashewa tayi da dariya tare da nuna jawaheer da hannu tace wannan wasan naki daban dariya yake, jawaheer tace kece kike da ban dariya amma banda lokacin miki bayani in lokaci yayi zaki gani, zarah dai dariya take tayi alama jawaheer wasa take mata, ganin tana kokarin mai data mahaukaciya ko kuma makaryaciya yasa jawaheer tace ni kinga tafiya ta, tayi gaba abunda zarah saboda dariya ma kasa binta tayi, ita kam jawaheer tayi gaba abunta. Jawaheer koda taje gida a wajan bukka taga mum dinta da dad suna fira ga kayan abinci nan a wajan kala kala, nufansu tayi cikin fara'a tare da fadin dad mum sannunku da hutawa, amsawa sukayi su duka da fadin yauwa, zama tayi tare da fadin mum ina khalil ne wai? Tace ya fita shida ozil, tace lah ya dawo ne? Mum tace eh ya dawo dazu, dad yace jawaheer kinci abinci kuwa? Tace a'a yace haba bakinki ya nuna hakan, mum ta fara zuba mata tare da fadin babu yanda banyi da itaba amma taki ci da safe, mutum yaita zama da yunwa in kika jajibo ma kanki ulcer aike kika sani, ita dai jawaheer shuru tayi tare da amsan abincin ta fara ci, taci sosai sannan ta ajiye, bayan ta kammala mum tace jawaheer nasa an canzo kudin da samir ya baki duka kudin million 200 ne, zamu tafi dubai muyi siyayya a can na kayan akwati kafin ya dawo muji yanda yake son a tsara dan kin san mutum celebrity bazai rasa yanda yake son bikinshi ya kasance ba, cikin jin kunya tace toh mum, dad yace amma kudi ai yayi yawa, mum tace baiyi wani yawa ba,yar tawa ai mai tsada ce, dariya dad yayi yace nima haka dan nawa, ita dai jawaheer tashi tayi dan wani irin kunyan mum taji tanayi yanzu, suna ganin ta tashi suka sa dariya. Dakinta ta shiga tare da ajiye jakarta, ta fada toilet tayi wanka, wani irin nishadi take ji sosai, duk da tana cikin damuwa na sauyin da samir yake nuna mata kafin ya tafi, gashi yau abunda ya mata ya bata mamaki tafiya babu sallama, wayarta dake kan gado taji tana ringing nufan wayar tayi tare da dauka taga zarah ce, dauka tayi taji zarah na fadin wlh jawaheer kin bani dariya dazu, tsaki jawaheer tayi tare da kashe wayan tace banda lokacin wannan tsokanan naki yanzu wlh zarah, kiran zarah dinne ya kuma shigowa dauka tayi tare da fadin miye kuma? Zarah tace miye na kashe wayan kuma? Tace naga kina son mai dani kaman mahaukaciya ne, zarah tace ko daya abun da kika fada ne kawai yake sani dariya, amma wai wasa kike koda gaske? Jawaheer tace akan mai zan miki wasa bari in turo miki saqo ta whtsapp yanzu, kashe wayan tayi ta tura mata pics dinsu da m samir kala kala, aiko tana gani ta doko ma jawaheer kira amma taki dauka daka karshe ma da taga ta dameta saita kashe wayan, tana fadin bari ke in manna miki haukan, batai minti shabiyar da kashe wayan ba taji ana nocking, tashi tayi ta bude kofar wa zata gani inba zarah ba, baki ta sake tare da fadin maiya kawo ki? Hararanta zarah tayi tare da fadin kinfi kowa sani ai, dariya jawaheer tayi tare da janyo hannuta suka shiga ta rufe kofar, zarah tace nazo inji gaskiyan lamari wlh tunda naga pics din nan na kasa zama, a ina kika sanshi? Jawaheer tace ai baki yarda ba kika sani mako editing nayi na pics din, zarah ta harareta tare da fadin ban san wulakanci fah, dan Allah ki fadamin, jawaheer tace toh bari kiji nan da wata biyu za muyi aure, zarah tace kai plz fadamin yanda kuka hadu, labari jawaheer ta fara bata tun daka sanda ta fara ganinshi a tv ta rude, har yanda suka hadu tare da fada mata dan mum ne, bata dai boye mata komai ba dan tasan wata rana kowa zai san gaskiya, zarah tace kai ikon Allah, wlh na tayaki murna kunyi mugun dacewa amma sai dai naji kince baya sonki? Jawaheer tace uhm, zarah tace nifa nasan yana sonki inda baya sonki wlh bazai yarda ya aureki ba, jawaheer shuru tayi can tace kai anya hakane kuwa, tausayina kawai yake, zarah tace tausayi alaman soyayya ne, jawaheer tace da kamar wuya, zarah tace nan gaba zaki gani, Allah ya bayyana miki iyayenki jawaheer ta amsa da ameen, nan suka ci gaba da fira yanda zasu tsara biki, zarah tace nasan a can kasar su za'ayi, jawaheer tace aini ko a ina ne buri na a daura dariya zarah ta saki tare da fadin Allah ya nuna mana zamu dauki hoto da manyan celebrity, dariya jawaheer tayi tare da fadin ke kuma shine damuwarki, tace eh din, tashi jawaheer tayi tare da fadin ina zuwa fita tayi jim kadan sai gata dasu snack da drinks ta kawo ma zarah, zarah tace ni a koshe nake drinks din zansha kawai, fira suka dinga yi har jawaheer ta dan manta da damuwanta duk da abun yana dan damunta na rashin jin m samir, zarah sai wajan 5 ta tashi zata tafi fitowa sukai tama mum sallama sannan suka fita tama mum sallama har wajan motarta jawaheer ta kaita wanda yayi dai2 da shigowan khalil fakawa yayi kusa da motar zarah, fitowa yayi cikin fara'a yana fadin kice da banzo da wuri ba dakin tafi tace wlh kuwa, ozil shima fitowa yayi jawaheer ta saki ihun murna tare da fadin manya an dawo garin, dariya yayi yace kai m samir kina kawo light fah, naji labarin kinyi nasara, dariya tayi tace haka yake, yace zamu sha biki, lallai Allah ya amshi addu'arki, dariya tayi sannan suka gaisa da zarah ta shiga motarta ta wuce su kuma sukai cikin gida. BAYAN SATI DAYA yau ake wasan su m samir tunda ya tafi basu waya da jawaheer ba, tayi mugun shiga danuwa sosai, a yanzu haka tana zaune a daki tana jiran lokacin wasan nasu yayi ta kalla, lokaci nayi ta kunna tv dinta, tana kunnawa taga sun jeru a fili ga mutane nata ihu, hangoshi tayi cikin kayan kwallo wanda yake kara fito mishi da kyanshi, wani irin murmushi tayi na ganinshi koba komai kallonshi da tayi yasa taji dadi,wasa aka farayi inda su m samir suka lashe wasan, jawaheer kam tayi murna sosai musamman da samir dinta ne ya lashe zaban, haskoshi akayi yana daga hannu mutane nata ihu, fitowa sukayi inda yan jarida keta cinjirindo tare da son yin magana dashi,tsayawa yayi yan jaridan suka zo, yace abu daya zance nasan yanzu someone is missing me alot, nasan komai nake kina kallo na i just want you to know that i miss you too, jawaheer dake kallon tv taji wani irin dadi tare da sakin dariya lokaci daya fuskanta ya canza ganin sonia tayi hugging dinshi......... *maryam obam* *JAWAHEER* *STORY AND WRITEEN BY......* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA* *(maryam Obam)* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝* *{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}* *wattpad @maryam-obam* *WWW.Maryamobamnovels.com* https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/ *DEDICATED TO.....* *Nafisa mrs dan malikin kawo* Page 43-44 *BABA BUHARI DODAR CONGRATULATION BABA BUHARI NEXTLEVEL NEXTNIGERIA ALLAH YAJA KWANA BABA BUHARI YA TAYAKA RIQO BABA BUHARI YACI ZABE KAI KUBAN KIDAN MASU GUDU SU GUDU💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃* Wani irin hawaye ne ya zubo mata tare da fadin dama har yanzu suna tare, gani tayi ya waigo domin ta baya tayi hugging dinshi da alama yana son ganin waye ya riqeshi, ganin sonia ce yasa ya saki dariya jawaheer na ganin haka ta kashe tv din tana kuka, wayanta keta faman ruri jin karan kaman ya dameta yasa ta duba dan taga ko waye, ganin sunan zarah yasa ta kura ma wayar ido, har ya tsinke, wani kiran ne ya kuma shigowa dan haka ta dauka, tana dauka zarah tace jawaheer kina kallon abunda ke faruwa? Jawaheer tace eh ina kallo, zarah tace amma wacece ita? Jawaheer cikin kuka tace itace sonia da nake cewa basa tare, ashe har yanzu suna tare nidai na shiga uku, zarah tace ina zuwa anjima kadan zan zo, jawaheer tace sai kinzo tare da kashe wayan, taci gaba da kukanta tare da jin wani abu na sukanta a zuciya, lallai tana son m samir amma bata tunanin zata iya hadashi da ko wace mace domin tana da bala'in kishi, ji tayi kirjinta har nauyi yayi dan tashin hankali, tana cikin wannan halin zarah ta shigo, tsayawa tayi tana kallon ta, matsawa tayi kusa da ita ta dafa mata kafada, firgit tayi dan bata san tama shigo ba, ganin zarah ce yasa ta goge hawayen dake fuskanta, zarah dan murmushi tayi tare da fadin jawaheer miye haka? Hararan zarah tayi tare da fadin ban sani ba, bayan kin gaka komai amma kina wani tambaya na, zarah tace haba jawaheer ke yanzu wannan abun kike ma kuka? Cikin kuka tace to mai zanyi zarah? Wlh ina son samir ina kishin shi ban san inga wata mace kusa dashi, wlh ji nake kaman zuciyata zata buga, zarah tace wlh jawaheer kina bani mamaki duk da nasan so ba karya bane kina ma samir mahaukacin so wanda bakya gane gabanki balle bayanki, namiji yace yana sonka ya ka kaya balle ke kika ce kina sonshi aiko kin san hakuri ya zaman miki dole akan duk abunda zaki gani, balle ma shi wanda kike so celebrity ne kinga baki da bakin magana, cikin kuka tace zarah nasan celebrity ne nasan bazan rabashi da mata ba, amma ki fahimta ita sonia budurwanshi ce, zarah tace eh na sani amma hakuri za kiyi ni in banda so sone aida nace wlh kiyi hakuri dashi tunda shi bawai yana sonki bane, jawaheer tace zarah idan na hakura dashi wa zan aura duk namijin dana aura toh ba zuciyata ya aura ba face gangar jiki na, domin zuciya na da ruhi na yana wajan samir ina gudun tarin zunubi domin wlh koda na auri wani tunanin samir zanyi tayi kinga kuwa haramun ne inyi tunanin namijin daba miji naba, zarah tace ikon Allah gaskiya Allah ya jarabceki, jawaheer tace hakane ina fatan Allah ya bani ikon juriya da hakuri, zarah tayi murmushi tace a hakan dan wannan abun da kika gani hankalinki ya tashi kin kasa sukuni, dariya tayi sannan tace zarah baki san kishi ba ina son samir fah wlh amma kin san wani abu kuwa? Zarah tace sai kin fada, jawaheer tace wlh bazan iya juran ganinshi da wata mace ba musamman sonia indai koh suna tare zan hakura dashi har abada, zarah ta kwashe da dariya tare da fadin kaman dagaske, jawaheer tace wlh kuwa dagaske nake gwara sonshi ya kashe ni akan inyi kishi da wata, zarah tace kawai ki yardan da yusuf musha biki hararanta tayi tare da fadin rufamin asiri ina zan kai mai mata harda yara biyu, indai zan iya auran mai mata inyi hakuri da samir dina mana, dariya zarah tasa tare da fadin kai jawaheer toh ba gwara ki aura mai sonki ba, jawaheer tace na bar miki shi, ni tashi ma mu dan fita ko zan danji dadi, zarah tace ok amma ya kira ki kuwa? Tace a'a bai kira ba na kira kuma yaki shiga, Zarah tace son maso wani....... Tsaki jawaheer tayi tare da fadin ke kika ga wahala, fita sukai cikin motar zarah wajan saida ice cream suka nufa. M samir bayan yaga sonia ce abun ya bashi mamaki itama ta lura da hakan dan haka taja hannunshi sukai mota, aka ja suka wuce, gidanshi aka kaishi suna shiga ta fara fadin baby mai yasa ka shareni dama baka so na? Ashe zaka iya barina ba tare daka neme niba? Yace to mai zan miki bayan ke kika tafi da kanki and kuma kin bani zabi wanda kin san bazan iya bi ba, toh mai yasa zan nemeki? Baki ta saki tana mamaki yanda taga yana mata magana, amma da yake yar duniya ce saita basar tare da matsawa kusa dashi tana shafa mai kirji tace haba dear kabar tunawa kasan bazan iya rayuwa ba tare dakai ba nasan kaima haka dan muna son junan mu, dan tureta yayi tare da fadin is too late now, tace ban gane bah, yace biki na saura 1month 2week, tace what? Lokaci daya kuma tayi dariya tare da fadin u r not serious, murmushi yayi tare da fadin dagaske nake miki, kuka ta saki tare da fadin kasan ina sonka mai yasa zaka min haka dama ba sona kake ba? Ganin yanda take kuka yasa ya janyota jikinshi ya fara rarrashinta tare da fadin sonia ina sonki amma kece kika gujeni, cikin kuka tace kayi hakuri koda na barka naji jiki na kasa hakuri dakai sai yasa nazo gareka gashi kana fadamin zakai aure nifa ya zakayi dani? Dan shuru yayi ba tare da yace mata komai ba, ta kara fadin plz answer me, yace muje ki huta z Muyi magana, dakyar ya jata yai toilet da ita dan tayi wanka, yana turata ya rufe mata kofar duk da tayi kokarin ta janyoshi wai suyi wankan tare amma yaci sa'a ya fita, koda ya fito falo ya koma ya zauna tare da tunanin ya zaiyi da sonia yasan yana sonta sosai domin ita ce first love dinshi, toh amma mai yasa baya jinta kaman da? Jin hannunta yayi a cikin riganshi tana wasa da kirjinshi, da sauri ya janyota tare da cire hannun nata daka kirjinshi kallo daya yayi mata ya kawar dakai domin daka ita sai towel, ta lura dashi amma saita basar ta kuma sa hannunta cikin riganshi tare da fadin i miss you my baby, plz let me feel you, kallonta yayi tare da fadin plz stop it kin san bana son irin haka, tace oh come on baby, ganin inya zauna tana shafa shi komai zai iya faruwa tashi yayi da sauri tare da fadin zan fita yana fadin haka yayi waje, sakan baki tayi sololo tana mamaki bayan ya fita tace uhm samir duk ka gama wayanka dole ni zaka aura bazan taba bari ka auri wata ba, sannan yau din nan sai munyi sex gwara ma ka daina wani guje guje, yar dariya ta saki tare da fadin na dade ina son jin kalan zumanka dan nasan ko kadan kai ba ragon namiji bane, hakuri na ya kare dan haka yau zan dana kalan baiwanka dariya ta saki sosai. Koda samir ya fita gidan dad dinshi ya nufa, bayan ya isa muhd ali yayi hugging din yaron nashi cikin fara'a tare da fadin my boy ya bubbuga mai kirji tare da daga hannu alaman yana alfahari dashi, sannan yace wasanku yayi kyau, samir yace nagode dad, tare da zama akan kujeran falon, dad din yace ya maganan tafiyan mu jibi? Yace tana nan dad, yace ok Allah ya kaimu, nan suka fara tattaunawa akan harkan kasuwancin da samir yake son farawa da nigeria inda mahaifinshi yayi na'am da batun tare dayi mishi addu'an samun nasara yaji dadi sosai ya dade suna fira sannan yamai sallama ya tafi gida. Yana shiga gida dakinshi ya nufa shi yama manta da sonia tana gidan, yana kunna wutar dakin ya ganta a zaune cikin wani shegen night gown wanda ya tsaya mata dai dai cinyanta ga nononta nan duk a waje gaba daya komai nata ana gani, ido ya dan kura mata lokaci daya kuma ya kawar da idonshi gefe gaba daya miyan dake bakinshi ya kafe magana yake son yi amma ya kasa, ganin haka yasa ta task tana karkada jiki ta karaso inda yake tare da hugging dinshi tana wani sauke numfashi, dan sakinsji tayi ganin yayi tsit yasa taji dadi dan tasan ya gama fadawa tunda ya kasa magana, hannunshi ta kamo ta fara janshi har gadon dakin ta zaunar dashi akai, shi kam jikinshi gaba daya yayi weak baya jin wani kuzahari a tare dashi dan sha'awa ce ta kamashi lokaci daya, jin bakinta yayi cikin nashi bai san lokacin daya biye mata ba ya fara tsotsan bakin nata shima, tare da shafa mata nononta wanda yafi daukan mishi hankali murza kan nononta yake tana wani irin nishi...... Karan wayanshi yasa ya dan tsagaita yayin da ita ta afka dan sakinta yayi lokaci daya kuma ya tashi da sauri tare da daukan wayanshi yabar dakin.... Har wayan ya tsinke bai dauka ba, falo ya nufa yana mamakin abunda yake kokarin aikatawa lallai Allah ya soni dubawa yayi domin yaga waye ya kira shi, jawaheer ya gani ido ya lumshe tare da fadin you are a darling u save me from zina, sonia kam tana kwance kan gado tana jira ya dawo sai wani irin nishi take saukar wa dan itama wani irin mugun sha'awa ne ya kamata gashi abunda take so gashi ya samu, jin shuru shuru bai dawo ba yasa ta tashi dakyar ta fito falo ganinshi tayi yana bacci akan kujeran falon ido ta bude tana mamaki tare da fadin mai yake nufi toh badai duk wannan abunda tayi mishi ace bai fada ba, kaman zata tashe shi sai kuma ta fasa, ciki ta koma ta bude jakarta ta dauko stick irin na maza amma na roba doguwa mai kauri, kwanciya tayi tasa a gabanta tana sawa tana cirewa tare dayin nishi tana lumshe ido lokaci daya kuma ta saki kara tare da cire stick din alaman tayi realising, zufa ne yake ta keto mata tako ina duk da akwai ac a dakin bata dade ba bacci yayi awon gaba da ita, shiko samir yana falo yana bacci abunsa bai san wata wainar take toyawa ba. Washe gari daya tashi da asuba, dakin ya koma ya ganta a kwance tana ta sharan bacci, dan tsaki yayi sannan ya shiga toilet yayi wanka tare da dauro alwala ya tafi masallaci, koda ya dawo kayanshi ya hada a cikin akwati yabar gidan, direct gidan dad dinshi ya nufa, koda yaje ya sami dad dinshi yana bacci, dakinshi na gidan yakai kayanshi sannan ya kwanta bacci ya kuma daukeshi. Jawaheer kam tunda ta kirashi taji ya shiga sai murna take tayi duk da bai dauka ba tasan yana cikin koshin lafiya tunda ya kunna waya, yau tana da lecturer karfe hudu, dan haka bata sauko kasa ba abinci tasa a kawo mata daki, sai wajan 3 ta fito cikin shiri inda ta samu mum bata nan, dan haka ta wuce skul kai tsaye, sai wajan 6 suka gama lecture gida ta dawo direct, ta sami su mum suma ta fira duk firan akan shirin bikinsu ne, sai wajan 10 ta nufi daki inda ta shiga toilet tayi wanka tana fitowa ta kwanta dan tana fashin sallah. Yau basu da lecture dan haka tunda ta tashi tayi wanka ta shirya cikin wani less mai shegen kyau dinkin riga da skirt ta dan shafa powder tare da lipstick, ta fito dan gidansu zarah take son zuwa tayi kyau sosai ko gyale bata yafa ba, a falo ta sami mum tana jera abinci akan dinning daka gani baki yau za'ayi dan taga cooler da yawa akai, mum ganin yanda tayi kyau yasa tace masha Allah, dariya tayi tare da fadin bari inje in dawo mum, mum tace ok sai kin dawo, fita tayi ba tare data tambayi waye ne zai zoba, tana fita ta shiga mota bude gate din gidan akayi itama lokacin ta tada motar ta, ido biyu sukayi dashi dam taji kirjinta ya buga tare da fadin anya shine, dan rufe idanta tayi tare sa budewa taga ana rufe gate din da sauri ta kalli wajan motocin da suka shigo taga dad din m samir da sauri ta bude motar ta fito, nufanshi tayi tare da fadin welcome dad cikin sakin fuska ya kamo hannunta tare da fadin jawaheer gaidashi tayi ya amsa cikin sakin fuska dai dai lokacin dad ya fito suka fara gaisawa ganin haka yasa tayi baya dan taga wani shegen kallo da samir ke mata, motarta ta nufa ganin su dad sunyi ciki, ji tayi an janyota ta dan saki kara dan taji zafi jan da akayi mata, waigowa tayi taga samir ne yace ina zaki a haka??? Sannan kina gani na dawo kike kokarin fita ina zaki??? *maryam obam* *JAWAHEER* *STORY AND WRITEEN BY......* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA* *(maryam Obam)* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝* *{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}* *wattpad @maryam-obam* *WWW.Maryamobamnovels.com* https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/ *DEDICATED TO.....* *Nafisa mrs dan malikin kawo* Page 45-46 Ji tayi ranta ya mata zafi tare da tunawa sanda sonia tayi hugging dinshi, kokarin jan hannunta tayi amma ta kasa dan ya riqeta da kyau, ganin irin kallon da yake mata yasa tayi kasa da kanta ranta na mata zafi tare da tunani kala kala, lallai namiji dan rai nin hankali ne wlh ya gama runguman budurwanshi zai zo ya dameni a nan,dan tsaki tayi jin hannunshi tayi akan bakin nata yaja da karfi kara ta saki tare da hawaye dan taji zafi sosai, ganin tana hawaye yasa ya barta tare da wucewa, bakin ciki ne ya isheta tare da takaici ji tayi kaman ta koma gida amma saita fasa ta shiga motarta taja ta fita, direct gidansu zarah ta nufa, sun gaisa da mum din zarah cikin sakin fuska sannan sukai ciki ita da zarah din, suna shiga jawaheer kwanciya tayi tare da fadin bacci nake ji bari in kwanta, zarah ta tabe baki tare da fadin kedai kika sani sai kiyi tayin baccin, dariya jawaheer tayi tare da fadin naji din, bata dade ba bacci yayi gaba da ita*JAWAHEER* *STORY AND WRITEEN BY......* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA* *(maryam Obam)* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝* *{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}* *wattpad @maryam-obam* *WWW.Maryamobamnovels.com* https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/ *DEDICATED TO.....* *Nafisa mrs dan malikin kawo* Page 45-46 Ji tayi ranta ya mata zafi tare da tunawa sanda sonia tayi hugging dinshi, kokarin jan hannunta tayi amma ta kasa dan ya riqeta da kyau, ganin irin kallon da yake mata yasa tayi kasa da kanta ranta na mata zafi tare da tunani kala kala, lallai namiji dan rai nin hankali ne wlh ya gama runguman budurwanshi zai zo ya dameni a nan,dan tsaki tayi jin hannunshi tayi akan bakin nata yaja da karfi kara ta saki tare da hawaye dan taji zafi sosai, ganin tana hawaye yasa ya barta tare da wucewa, bakin ciki ne ya isheta tare da takaici ji tayi kaman ta koma gida amma saita fasa ta shiga motarta taja ta fita, direct gidansu zarah ta nufa, sun gaisa da mum din zarah cikin sakin fuska sannan sukai ciki ita da zarah din, suna shiga jawaheer kwanciya tayi tare da fadin bacci nake ji bari in kwanta, zarah ta tabe baki tare da fadin kedai kika sani sai kiyi tayin baccin, dariya jawaheer tayi tare da fadin naji din, bata dade ba bacci yayi gaba da ita. Shiko m samir tunda ya shiga yake ta dubawa ko zata shigo amma yaji shuru su dad nata fira amma shi hankalinshi baya wajansu ganin taki shugowa yasa ya tashi ya fita amma yaga babu motarta alaman ta fita kenan hannunshi ya buga da karfi tare da fadin damn, ciki ya koma rai bace wato batai murnan ganinshi ba tunda har zata iya fita ta barshi bayan tasan ya dawo, ina taje da har ya fini muhimmanci? Doka mata kira yayi harya tsinke ba'ai picking ba, tsaki yayi dad dinshi yace samir lafiya? Yace lafiya dad na gaji ne, dad din su khalil yace toh sai kaje ka huta tashi yayi yabar falon ya nufi dakinshi na gidan kara kiranta yayi harya gama ringing ba'a dauka ba, toh ina taje? Mai takeyi da taki daukan waya na? Tashi yayi yana ta sintiri a dakinshi daka yaji kaman motsin bude gate saiya leqa yaga koh itace ta dawo jin shuru2 gashi har yamma tayi dad dinshi yasa a kira shi dan ya rakashi masaukin shi, hakan suka fita shida khalil suka kai dad din nashi hotel sai bayan isha'i suka tawo gida suna shiga jawaheer na shigowa abun ya bashi mamaki sosai bayan sunyi parking khalil ya wuce ciki dan yana waya ne, shiko wajan motarta ya nufa ya bude dayan gefen ya shiga tare da rufewa, kallonta yayi tare da fadin sau nawa na kiraki? Tace ban gani ba, yace muga wayanki amsa yayi yaga alaman bata bude ba yace daka ina kike? Tace gidan kawata, dan shuru yayi sannan yace daka yau banso ki kara fita saida izini na, dan bazan dauki wannan yawace yawa cen ba, tace ai ba'a daura auren ba, kallonta yayi ya saki wani irin murmushi tare da fadin ko dai miye ki shiga ciki kiji daka yau saida yarda na zaki ko kofar gida, wayanta ne yayi kara ta duba taga zarah ce dauka tayi tare da fadin zarah na dawo yanzu, fisge wayan yayi tare da sawa a kunnenshi dan yaji ko waye jin muryan mace yasa yayi magana zarah tace badai ango bane? Yace eh nine cikin harshen turanci tace wow ashe kuna tare na kira toh asha luv lafiya zan kira anjima yayi dan murmushi tare da kashe ma jawaheer ido daya, sannan ya kashe wayan, ganin yanda ta tamke yasa ya janyota jikinshi tare da fadin haka ake tarban miji yau sati nawa bana gari amma na dawo babu wani tarba mai kyau, tace da zaka tafi ka fadamin? Aini na dauka ma kana gari, dariya yayi tare daja mata hanci yace ai naga fada mikin bashi da amfani, tace ok nima sannu da zuwan da kake so inyi maka kaga kenan baida amfani, hararanta yayi tare da fadin kinma isa, tun dazu banci komai ba ke nake jira ki dawo kiban, uhm tace tare da fadin nifa bacci nake ji, kwai kwayan magananta yayi tare da fadin kice yau zan kwana da yunwa ido ta zaro tare da fadin saboda me? Yace saboda ba zaki bani ba, tace uhm muje kaci toh fita yayi saida suka shiga falo yace takai mai dakinshi tace toh, hada mai kayan abinci tayi ta haura dashi dakinshi, bata ganshi ba amma taji motsinshi a toilet kuma daka ji wanka yake yi, dan haka ta fita tana shirin zuwa dakinta taga dad, yace yauwa jawaheer zo mana dakim mum suka shiga inda taga mum a zaune itama, zama tayi a kusa da mum, dad yace jawaheer gashi amsa tayi taga kudi yan dubu daya daya, sai kuma wasu dollars, dad yace naira din da kika gani kudin sadakinki ne dubu dari sannan sauran dollars din kudin na gani ina so ne,duk da sunso sadakin yafi haka amma nace a'a hakan yayi,wani irin hawaye ne ya fara silalo mata tare da mamakin yanzu wannan sadakinta ne a hannunta, miqa ma dad tayi tace gashi ka riqe dad, kai ya girgiza tare da fadin naki ne, dan haka sai ki adana, kuka ta saki mum ta fara rarrashinta tashi tayi ta nufi dakinta, ajiye kudin tayi tare da fadawa toilet tayi wanka yasa night gown, tazo zata kwanta taji ana mata nocking hijab tasa sannan ta bude kofar samir ta gani saida ya kalleta sama da kasa sannan yace ke nake ta jira, bata ce mai komai ba tabi bayanshi, bayan sun shiga ya kura ma fuskanta ido yace kinyi kuka koh? Kai ta girgiza alaman a'a yace karya ne, idan nan yayi kuka, wani hawayen ne ya gangaro mata tare da fadin ina kukan rabuwa da mum da dad ne plz idan mukai aure a ina zamu zauna? Murmushi yayi tare da fadin spain mana, tace nidai plz ka barni a nan nafi son zama a nan, tamke fuska yayi tare da fadin plz bani abinci inci yunwa nake ji, bata kara magana ba sai tray din data dauko ta ajiye mai, kallonta yayi tare da fadin waye zai bani? Baki ta dan turo tare da bashi abincin dambun cous cous ne, bayan yaci yace woa delicious wannan miye? A hankali tace cous cous yace akwai dadi abun bashi tai tayi daka sun hada ido ya kanne mata ido daya tana cikin bashi taji ya janyota tare dayin hugging dinta yana son kamshin turarenta ido ya lumshe yana shakar kamshinta dan tureshi ta farayi tare da fadin ka barni plz, sakinta yayi tare da hura mata iska a fuska yace jawaheer saura lokaci kadan ki zama tawa har abada,da sauri ta dago da kai ta kalleshi hancinsu ya hada waje daya yana girgizawa jan fuskanta tayi tare da tashi tsaye tace saida safe, harta fara tafiya ya janyo mata hijab wanda yasa dole ta tsaya tashi yayi ya shiga gabanta yace jawaheer zan miki wani babban kyauta ranan bikin mu, amma ke me zaki bani? Shuru tayi na wani lokaci sannan tace komai kake so zan baka, yace komai fah kika ce? Tace eh yace ok Allah ya kaimu saura kwanaki ai, tace kwanaki kuma? Yace eh an canza komai kin kusa zama matar aure yana fadin haka ta fara kokarin ta fita janyota yayi tare da manneta a jikinshi har suna shakan numfashin juna, lokaci daya yasa bakinshi cikin nata ya fara kissing dinta...... Yayi wajan minti daya sannan ya saketa gaba daya ta dauke huta shima wani irin mugun sha'awa yaji ya kamashi wanda bai taba jiba, saida tayi wajan 2mnt kafin ta dawo hayyacinta fita tayi da sauri, shiko cikinshi ya fara ciwo dan haka ya riqe cikin tare da matsawa kan gadon dakin ya kwanta yana juye juye. Ita kam tana shiga daki ta rufe tana sauke ajiyar zuciya, ido ta lumshe tana murmushi tare da tuna abunda ya faru, kwanciya tayi tana tunani wayanta data bari a daki ya fara kara dubawa tayi taga dr nazir ne mamaki ya kamata dan yayi kwana biyu bai kirata ba, har kiran ya tsinke bata daga ba, wani kiran ne ya kara shigowa dan haka ta dauka, yace barka da dare sarauniyar mata, tace ina wuni dr, ya amsa da fadin lfya gani a abuja kuma danke nazo ido ta dan zaro tace danni? Yace eh danke, tace shine baka kirani ba ka fadamin zaka zo ba, yace nasan idan na fada miki ba yarda za kiyi ba amma tunda nazo nasan za'aji tausayina a barni inga sarauniya,tace uhm amma dai ba yanzu bako? Yace eh gobe, tace Allah ya kaimu nan yace ta bashi address ta fada mishi yace ya gane gidan, sukai sallama, tashi tayi da sauri tare da fadin mai na aikata samir na gari gashi ya tsani dr, kaiwa da komowa tai tayi domin neman mafita tama rasa mai yasa ta yardan ma dr yazo tsaki tayi mai karfi, shiko samir ciwon ciki ya sashi gaba ga zazzabi ya kamashi sosai yama rasa abunyi dakyar ya janyo wayanshi ya kira jawaheer dauka tayi taji yace kizo plz, jin muryanshi wani iri yasa ta fita da sauri, dakinshi ta nufa taga yana ta shure shure da sauri ta nufeshi tana fadin samir maiya sameka? Jin jikinshi da zafi yasa tace fever bari in kira dr kamo mata hannu yayi tare da janyota jikinshi yace nop bana bukatar dr ke nake bukata dam taji kirjinta ya buga, wani irin runguma yayi mata tare da kokarin shafa mata jiki tako ina, cikin sanyin murya tace ka bari..... Yace plz jawaheer karki dakatar dani nine zan aureki na biya sadakinki plz allow me hawaye ne ya fara gangaro mata a fuska mai yake damun samir haka?......... Ku biyo ni danjin yanda zata kaya.....plz ina bukatar comment da sharhi *maryam obam* *JAWAHEER* *STORY AND WRITEEN BY......* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA* *(maryam Obam)* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝* *{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}* *wattpad @maryam-obam* *WWW.Maryamobamnovels.com* https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/ *DEDICATED TO.....* *Nafisa mrs dan malikin kawo* Page 47-48 Jin hannunshi tayi akan nononta yana matse mata su da karfi alaman yana matukar bukata ido ta lumshe ga kirjinta dake ta faman bugawa da karfi, bata ankara ba taji bakinshi cikin nata kissing dinta yake sosai yana tsotsan bakinta kaman yana shan sweet duk da ita bata mayar mishi da martani, dan sakin bakinta yayi tare da kokarin cire mata riga kuka ta saki mai karfi tare da fadin samir kar son zuciya ya sa mu aikata aikin dana sani, ina sonka bazan iya hanaka jiki naba, amma ina gujewa sabon Allah da aikin dana sani, kar mu aikata abun da zamu haramta ma juna auran mu dan Allah kayi hakuri har zuwa ranan da...... Wani irin runguma yayi mata ya matseta da karfi a jikinshi har tana jiyo stick dinshi domin ta riga ta tashi, kwanciya yayi ya kara janyota ta kwanta a jikinshi, ido ta lumshe domin abunda take ji yana tabata ya fara bata tsoro shafa mata baya yake tako ina tare da sauke nishi kadan kadan, kwanciyan da tayi yaga kaman batai mishi ba ya kara juyar da ita ta koma kasa shi kuma yahau samanta goga jikinshi yai tayi akan nata yayi wajan minti goma yana abu daya lokaci daya ya saki wani irin nishi tare da kara kankameta da karfi, zufa ya fara keto mishi ita kam babu abunda take sai kuka tare da fargaban karya aikata mata abunda take tsoro, sakinta yayi tare da tashi ya shiga toilet ganin ya shiga toilet itama tayi kokarin tashi taga jikinta ruwa ya jiqata dubawa tayi taga sperm ne, da sauri ta tashi tabar dakin tayi dakinta da gudu tana kuka, koda ta shiga daki rufe kofa tayi tana ta kuka tare da godema Allah da yasa babu abunda ya shiga tsakaninsu lallai dole tayi nesa dashi kar wani abun ya shiga tabbas duk wanda ya kauce ma hanya yana tare da aikin daya sani, shigewan da sukema juna yayi yawa sosai gashi sun maida taba junansu kaman ba komai ba, ido ta lumshe tare da fadin tabbas dole inyi nesa dashi, inko ba haka ba muna gab da aikata aikin dana sani, ranan haka ta kwanta sai juyi take, shiko koda ya fito daka toilet bai ganta ba murmushi yayi tare da fadin Allah na gode maka daka bani mace mai tsoran Allah yasan inda sonia ce da yau sai sun aikata aikin sabo da ita bazata taba kokarin hana shiba, lallai sai yasa kayi soyayya da mace mai addini kwanciya yayi yana tuna abunda ya faru yana dan murmushi gaba daya tsoro ya bayyana a fuskan jawaheer din ido ya lumshe tare da fadin kina da kyau jawaheer da haka har bacci ya daukeshi. Tunda jawaheer tayi sallah asuba, take ta fargaban zuwan dr gashi ta bashi address, yanzu idan yazo suka hadu da samir ya zatayi? Wani zufa taji yana keto mata, tasan muddin dr yazo suka hadu da samir tasan akwai kura namiji ya ganta ya mata magana bai masan miye tsakaninsu ba yayi fushi da ita balle shi wannan da yasan sonta yake yi, daukan wayanta tayi ta doka ma zarah kira ringing hudu ta dauka cikin muryan bacci, jawaheer tace baki tashi ba kenan? Tace na tashi nayi sallah na koma, aike nasan kina fashin sallah, jawaheer tace jiya nayi wanka na fara, zarah tace toh wannan kiran fah da sassafe, jawaheer tace ban sani ba, zarah tace wlh bacci nakeji fadamin miye, jawaheer tace mata dr da nake baki labari yace yana abuja anijma kuma zai zo wajena, wlh nama rasa abunyi na rasa mai yasa nace yazo har ina bashi address, zarah tace toh miye dan yazo? Tsaki jawaheer tayi tace kin manta samir na gari, da sauri zarah ta tashi tace kai wlh na manta yanzu miye abunyi, jawaheer tace shine nake so ki fadamin dan shuru zarah tayi sannan tace yauwa ki kira shi kice ku hadu a wani waje, jawaheer tace hmmm samir ya kafa min doka akan in zan fita saina tambayeshi, nidai na shiga uku, zarah tace toh zanzo anjima saimu fita tare nasan bazai ce komai ba, jawaheer tace hakane sai kinzo toh, zarah tace ok sai ki kirashi ki fada mai inda zaku hadu tace anjima kam zan kira shi. Tun wajan 11 zarah tazo gidan su jawaheer bayan sun gaisa da mum da dad sannan ta haura dakin jawaheer, buga kofar tai tayi saida ta dade tana bugawa sannan jawaheer tazo ta bude mata zarah tace sannu ke bacci ma kike yi, jawaheer ta saki hamma tare dayin miqa tace wlh kuwa gwara in kwanta in huta jiya banyi wani baccin arziki ba, zarah tace dakyau yau ma in bakiyi wasa ba baccin saiya gagareki kin kira dr din kuwa? Tace karfe nawa yanzu zarah tace oho, dauko wayanta tayi tace kai 11:22 bari in kirashi yanzu tsaki zarah tayi tace in kika bari har yazo ai matsalanki ce, jawaheer bata ce mata komai ba sai kiranshi data farayi taji a kashe, kallon zarah tayi tace kinji number dinshi baya zuwa a kashe yake, zarah tace toh mu bari zuwa anjima basai mu kira shiba, tace toh, bari inyi wanka sai mu fita kinga inna sameshi sai in fada mishi inda nake, zarah tace ok hakan yayi, toilet jawaheer ta fada tayi wanka tasa wata doguwar riga na yar kanti tare dasa wani hula mai kyau ta feshe jikinta da turare tayi kyau sosai duk da ba makeup takeyi ba, amma komai yayi kyau, daukan jakarta tayi karama tare da wayarta, a falo ta tarar da mum gaida mum tayi tare da cema mum zan raka zarah ansan sako, mum tace ok jibi zamu dubai fah, tace mum da huri haka? Tce eh wlh an canza date din bikin ne, zarah bani number din mum dinki zanje gidanku anjima koh gobe ta bari muje tare dake kina da international password koh tace eh mum ina dashi, mum tace ok anjima zan zo gidan naku, bata number din mum din tayi tare da mata kwatancen gidansu, sannan suka fita. Jawaheer sai trying number din dr take amma taji switch off, zarah tace may be ma ya fasa zuwa gashi yanzu har 4 yayi, jawaheer tace nifa ina jin tsoro kar ace yazo tunda na mishi kwatance kuma wlh idan suka hadu da samir akwai matsala sosai, zarah tace ni nama rasa miye mafita wlh, amma tunda wayanki a kunne yake ai dole in yazo gidan ya kiraki, jawaheer tace hakane, tunda taji zarah ta fadi haka sai taji hankalinta ya kwanta, suka barke da fira har 6 yayi jawaheer tace kinga dr ba zuwa zaiyi ba bari inzo in tafi gida, zarah tace kai tun yanzu ai kya bari anjima koh, tace wank anjima ni tashi muje ki kaini, tashi zarah tayi suka fita tama mum din zarah sallama mum din zarah tace dazu mamanki ta kirani jawaheer tace zata zo anjima, jawaheer tace eyya sannan suka fita, zarah na driving cikin kwanciyan hankali suna ta fira har suka karasa cikin gidan samir ta gani akan mota yana zaune yana danna waya, baiko dago kaiba balle yaga suwa suka shigo, zarah tace kai amma gaskiya a fili ma ashe yafi kyau sosai, zarah tace bari inje mu gaisa fita tayi itama jawaheer ta fita, bayan sun isa wajanshi ya dago zarah tana gaidashi cikin sakin fuska yace zarah right? Tace eh hakane ashe ka sanni yayi dan murmushi tare da fadin eh, kallon jawaheer yayi fuska daure tare da fadin kinyi baqo yana ta jiranki, dam taji kirjinta ya buga, amma saita daure tace baqo kuma anya ni? Bai kuma kallonta ba balle ya bata amsa, saima tashi da yayi ya kalli zarah yace sai mun hadu next time shiga motar yayi yabar gidan, ita kam jawaheer jikinta har rawa yake dan takaici kallon zarah tayi tace amma wannan dr din wlh baiyi ba dan wulakanci in zaka zo wajan mutum ai saika fada mai gani a hanya amma ya tashi ya kashe waya tsaki ta saki tare da fadin muje dallah ni in sallameshi, zarah tace kai ki nutsu mana, hararanta tayi ta wuce gaba abunda tana zuwa falon baki taga professor yusuf a zaune mamaki ne ya kamata dan batayi expecting ganinshi ba, itama zarah mamakin ne ya kamata na ganin professor a zaune, kallon juna sukai ita da zarah murmushi yayi tare da fadin kuna mamakin gani na koh? Mai makon amsa sai suka gaidashi su duka har suna hada baki, amsawa yayi sannan suka shiga zarah tace ni bari in tafi, yace no zauna nima ba dadewa zanyi ba yanzu zan tafi, kallon jawaheer yayi da yaga ta tamke fuska yace my dear i just come to see you sannan inji anyi approving dina? Dan shuru tayi kaman tace mishi dallah ban sani ba amma yana mata kwarjini, dan haka tace kayi hakuri za muyi magana ta waya, murmushi yayi yace amma ai inaga duk maganan waya bata taso ba komai za'ayi muyi ta nan kaman zaifi, tace hakane inaso in baka hakuri an amshi kudin sadaki na a halin da ake ciki yanzu kudin ma yana hannu na, kuma kaga babu kyau neman aure akan wani, dan shuru yayi na wani lokaci sannan yace hakane naji dadi da kika fadamin gaskiya Allah yasa ma aurenki albarka ya bada zaman lafiya, nima Allah ya bani hakuri, ta ansa da ameen, sannan ya tashi har mota suka raka shi ya dauko wasu ledoji guda biyu ya bata tayi mishi godiya sannan ya wuce zarah tace wlh yaban tausayi sosai, amma gwara da kika fada mishi gaskiya koba komai kinga kin rage saura dr, tace hakane mu shiga ciki mana, zarah tace ke tafiya zanyi, muga maiya kawo amsan ledan tayi taga su turare ne da kayan chocolate, daukan wani chocolate zarah tayi ya fara ci, tare da shiga mota dai dai lokacin mum ta fito tace har kun dawo nima gidanku zani zarah bari mu jera toh, mum shiga mota tayi driver ya tada itama zarah shiga tayi aka bude musu gate dai dai lokacin shima samir ya dawo gidan, parking yayi jwaheer ta shige ciki da sauri ya fito ya sameta a falo, kallonta yayi tare da fadin waye yazo nemanki? Tace lecturer dinmu yace maiya kawo shi? Tace yazo mu gaisa ne, wani irin kallo ya watsa mata tare da nufanta ya dauki ledojin dake gabanta ya bude ya gani fuska ya tamke tare da kiran masu aikin gidan ya basu, kallonshi tayi kaman zatai magana amma saita fasa ta wuce cikin dakinta binta yayi da ido harta bace mai, koda ta shiga wanka tayi tare dayin alwala tayi sallah sannan ta kwanta abunta, karan wayanta taji alaman saqo ya shigo dubawa tayi taga samir ne ga abunda yace...... *jawaheer inaso ki sani daka yau shine na farko na karshe da wani dan iska zai kara zuwa gidan nan da sunan nemanki, nd kuma na fada miki ban son yawo amma baki jiba nace in zaki fita ki fadamin amma baki jiba daka yau shine na karshe in kika kara only god knws what wil going to happen* bayan ta gama tayi dan murmushin takaici tare da jefar da wayan, bata dade ba bacci ya dauketa. Sonia tunda ta farka taga m samir baya nan, tace may be yaje ya dawo ne amma taji shuru data bincika sai ake fada mata ma yabar kasar, ranta yayi mugun baci tayi alwashin saita sameshi tako wani hali, sannan duk wacce yake tare da ita ko waye sai taga bayanta domin indai bata sameshi ba toh babu wata mace da zata bari ta sameshi dan tsaki tayi tare da fadin dole inyi mishi black magic in bai dawo hankalinshi ba........ Kuyi manage *maryam obam* *JAWAHEER* *STORY AND WRITEEN BY......* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA* *(maryam Obam)* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝* *{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}* *wattpad @maryam-obam* *WWW.Maryamobamnovels.com* https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/ *DEDICATED TO.....* *Nafisa mrs dan malikin kawo* Page 49-50 Washe gari tunda jawaheer tayi sallah asuba ta koma bacci dan kwana biyu bata samun bacci gashi tana da lectures karfe goma, karan wayanta ne ya tasar da ita, tsaki tayi ta dauka ba tare data duba ko waye mai kiran taba, tana dauka taji muryanshi yana fadin plz kimin wannan abun da mukaci a yola rannan white din nan da miya mai yauki, bata san lokacin da dariya ya kubce mata ba dan ta gane tuwan semo yake so miyan kubewa, yace miye abun dariya? Tace babu komai, kashe wayan yayi taci gaba da dariya, tashi tayi ta fita kitchen ta nufa ta daura karamin tukunya tasa ruwan tuwan gefe kuma tasa kayan miya da manja da nama dasu dry fish, bude wata cooler tayi taga akwai farfesun kaza tace yauwa basai nayi ba, cikin minti arba'in ta gama komai ta shirya a try ta ajiye mai akan dinning saida ta shiga dakinta sannan ta kirashi tace ta gama yana dinning tana fadin haka ta kashe dariya yayi dan yasan bata son taji yace ki kawo min daki na sai yasa ta kashe, toilet ta fada tayi wanka dan ta kusa tafiya skul koda ta fito shiryawa tayi cikin wata jallabiya mai ruwan baki da maroon yayi mata bala'in kyau ta yafe gyalen jallabiyan kallo daya zaka mata kace ba yar kasar nan bace domin kyau iya kyau ne ya hade a wajan, feshe jikinta tayi da turare sannan ta fito a dinning ta sameshi yana cin tuwan tunda ta fito ya kura mata ido harta karaso inda yake, yace kinyi kyau sosai amma ki koma kisa abunda zai rufe miki jiki danni kadai ya kamata inga wannan kwalliyan, baki ta dan turo tare da fadin nifa nayi late banza da ita yayi yaci gaba dacin abincin shi, ganin bashi da niyan tanka mata yasa ta juya tana gun guni ni mutum ba aurena yayi ba amma ya dinga matsa min ina da anyi auren aina shiga uku, kayan ta cire tasa dogon wando da wata top mara hannu sannan tasa hijab, fitowa tayi idonshi na kanta harta karaso yace wannan ma yayi kyau ni skul din nan dole ne ki dinga yi ta online mana, ganin so yake ya hanata zuwa yasa tace dan Allah ka barni in tafi ina da test karfe goma dai dai kuma gashi yanzu saura 30mnt, yanda ta marai raice mai take magana sai yaji ta bashi dariya yace ki zauna in gama sai muje tare dan ban yarda da zuwa wannan skul din ba, babu yanda ta iya dole ta zauna bini bini ta kalli agogo, gashi yana cin abincin kaman baya ci, duk abunda takeyi yana kallonta amma sai yake nunawa kaman bai masan tana yiba, ganin bashi da niyan tashi tace lokaci na tafiya fah, bai ko kalleta ba balle ya tanka mata ba, saida ya gama bata mata lokaci sannan ya tashi yace muje tana ta zunbure zunbure suka fita, bude mata gidan gaba yayi ta shiga shi yake tuki har cikin skul din nasu, bayan yayi parking ta bude kofar amma taji a rufe kallonshi tayi alaman ya bude mata, tambaya ya jefo mata wannan fushin fah? Bata ce mishi komai ba kuma bai bude kofar ba, ganin goma saura minti hudu inta biye mishi zata rasa test din yasa tace dan Allah ka bude min inje inyi test din nan, yace sai kin fadamin dalilin da yasa kike fushi, tace nifa ba fushi nake ba kawai na kosa inzo skul inyi test ne banso inyi missing, bude mata kofar yayi tare da fadin ina jiranki in kin gama tace toh ta fita da sauri, tana koh shiga lecturer din ya shigo ya basu test. Tunda ta fita ya kwantar da set din motar ya kwanta bai kashe motar ba dan ya kunna ac, pictures din jawaheer yake ta kallo a wayanshi yana murmushi lokaci daya ya furta u wil be mine very soon, jin kaman ana kokarin bude motar yasa ya dago dakai ya ganta ita da zarah, bude mata yayi ta shigo zarah ta gaidashi ya amsa tare da fadin gobe zaku tafi koh? Tace eh insha Allah, yace ok ki kulan min da ita fah sosai, dariya zarah tayi tace baka da damuwa indai dan wannan ne, yace ya gode tare da fadin in kun dawo sai inji ya kuke irin naku bikin zarah tace ok zaka ji komai da komai dariya yayi sannan sukai sallama, jan motar yayi suka bar skul din, mai makon suje gida saiya biya dasu wajan wani shan ice cream wanda turawa da manyan masu kudi suke zuwa wajan, mutane na ganinshi suka rugo da gudu suna daukan hoto dashi tare da basu takarda yayi musu signing saboda yawan mutane ko ice cream din ma basu shaba ya samu ya kubce ya shige mota, ita kam jawaheer dariya tai tayi yanda taga ya silale ya shige mota, kallonta yayi yace wannan dariyan fah? Tace babu komai kawai naji ina son yi ne hancinta yaja tare da fadin saina cire miki shi, dan kara ta saki tare da fadin akwai zafi fah, hararanta yayi tare da fadin ai na sani, baki ta turo, tuki yaci gaba dayi yana fadin mutum bashi da daman yin rayuwan da yake so sai mutane sun dameka, mtsww ya saki dan gajeran tsaki, jawaheer tace uhm toh ai mutane rahma ne, yace haka ne amma ai ba irin haka ba, sunyi tafiya mai nisa ta daiga bashi da niyan zuwa gida tace wai ina zamu? Yace zan sai daki ne, dariya ta saki tare da fadin tab lallai ma, cikin wani hotel suka isa, yace fito muje. Bata musa ba ta fito suka shiga wani daki suka shiga inda ya tsaya yana nocking, jim kadan aka bude dad dinshi ne hugging dinshi yayi tare da fadin dad yakake? Dad mai makon amsa sai kiran sunan jawaheer yayi da fadin shigo mana, shiga tayi cikin jin kunya ta sami waje ta zauna cikin kujeran dakin, hotel din ciki da falo ne, gashi ya hadu sosai, gaida dad tayi ya amsa cikin fara'a cikin jin kunya tace dad tun tuni nace ya kawo ni yace wai ka koma, wani irin kallo samir ya mata wanda yasa tayi saurin kasa dakai, dad kuma yace baka kyauta ba samir, shuru yayi ba tare da yace komai ba sunyi fira sosai dad dinshi yana son jawaheer sosai dan ya yaba da tarbiyanta da hankalinta uwa uba rainan bilkisu ce, dad din yace yaushe zaka spain din? Yace ran friday zan tafi inna gama kuma sai in tafi saudiya bazan dawo ba sai an daura auren daka nan sai mu koma spain din dan acan za muyi dinner, dad yace Allah ya taimaka an kawo card din ne? Yace eh an kawo dad yace ok nima idan aka daura auren zan tafi kwa sameni can, samir yace dad tare zamu tafi akwai private jet da za'a diba kowa mai cin mutane 120 dad yace ok ba damuwa, sai wajan karfe daya dad ya tashi shida samir dan zuwa masallaci, bayan sunyi sallah sun dawo suka tarar da ita tana sallah itama, bayan ta idar suka ma dad sallama suka tafi, suna tafiya cikin mota ya dan kalleta tare da fadin yaushe kika ce in kaiki wajan dad? Tace toh ai baka fadamin wajanshi zamu ba kuma ya kamata ka fadamin inyi mishi wani abu, tace yauwa mu ma bar wannan maganan tafiya za kayi shine baka fadamin ba, yace eh haka naga dama, shuru tayi ba tare data kara cemai komai ba, har suka karasa gida, a falo ta tarar da khalil da kabeer ozil da mum suna fira, tace ozil kai fa yanzu kayi wuyan gani, yayi dariya yace aikin dana samu akwai wuya wlh, tace sannu da gida mum, dai dai lokacin shima ya shigo falon zama yayi kusa da mum ozil ya fara tsokananshi da ango indai za'a ganka toh tare za'a ganku, dariya kawai yayi, kallon yanda yake da ido yasa jawaheer ta gane yana jin yunwa dan haka ta nufi dinning ta zubo mai abinci ta daura a plate ta daura a center table ta janyoshi gabanshi kallonta yayi yace thanks, sannan ya fara ci, mum kam tana jin dadin yanda suke nunawa juna kulawa sosai, khalil yace sis idan kun tafi ki siyomin phone a can naso muje tare amma banda time, jawaheer tace ok ka dauki excuse mana sai mu tafi, yace dad ai ba barina zaiyi ba wlh aikin nan akwai wuya shi bros umar ya huta wlh, dariya kabir yayi yace kalleka ai gwara naka aikin akan nawa, mum tace kun daiji jiki yara sai son jiki miye wahalan aikin zama ne fa a office ga ac sai signing shike nan fah, dariya jawaheer tayi tare da fadin mum wlh ni nama fi su dauriya, samir dai jinsu kawai yake yana cin abincinshi amma bini bini ya kalli jawaheer, ya rasa mai yasa ako da yaushe yake son ya kasance kusa da ita, jawaheer tashi tayi ta shiga kitchen ta hada ma dad abinci kalan na kasar su, dana nigeria kuma, mum ta shigo kitchen din tace baki za muyi yau kenan? Tace a'a mum za'a kaima dad ne, mum ta gane wanda take nufi dan haka tayi dariya ta fita, bayan ta kammala ita da kanta ta fita taje takai mai yana ta sa mata albarka, gida ta dawo ta shige dakinta, tana kwance taji nocking dan haka ta tashi ta bude, kallonta yayi daka sama har kasa ya dan cije baki, sannan ya shigo dakin binshi tayi a baya, zama yayi akan kujeran dakin mai dauke da hotanshi, yace nazo yin godiya ne, tace name? Yace dad yace kin kai mai abinci mai dadi, nagode, bata fuska tayi tare da fadin kaman ya ka gode nima fa dad dina ne, yaji dadin yanda tayi magana dan yana son dad dinshi yana kuma son mai sonshi, tashi yayi yazo kusa da ita ya zauna tare da janyota jikinshi yace hakane sorry na tuba a daina fushi murmushi tayi tare da kokarin matsawa, janyota ya kuma yi tare da fadin haka za muyi sallama din kin san fah gobe zaki tafi in kin dawo kuma ba gani na za kiyi ba sai ranan biki, baki ta dan turo tare da fadin Allah ya taimaka, yace ameen tare da ja mata hanci ta saki kara mai dan sauti tace akwai zafi fah, yace dagaske? Daure fuska tayi alaman taji haushi yace idan kina fushi kinfi kyau, dariya tayi tace ba wani nan, shima dariyan yayi yace dagaske nake, jawaheer kina da kyau tako ina, murmushi tayi cikin jin dadin yabon da yake mata, duk da tasha jin ana fadin tana da kyau ita da kanta tasan ta hadu, amma idan taji a bakin samir tafi jin dadi, jin hannunshi tayi akanta yana shafawa ido ta lumshe, jin muryanshi tayi yana fadin saida safe tunda ba za'ayi min sallama ba, da sauri ta bude ido tare dayin hugging dinshi tace gashi nayi maka ko akwai wata sallama da tafi wannan? dariya yayi tare da girgiza kai yace bazan ce komai ba yanzu, itama dariyan tayi tare da kokarin jan jikinta daka nashi, tashi yayi ya mata peck a goshi yace sai da safe naji mum tace 10 zaku tashi zanyi kokari in tashi muyi sallama, tace ok fita yayi ta rufe kofarta ta kwanta tana tunanin irin kulawan da zata bashi in sunyi aure, har bacci yayi awon gaba da ita. Tunda yayi sallah asuba bai koma ba, wajan 8 ya fito ya nufi dakinta yayi nocking ta bude kallonta yayi yaga tayi kyau tasa wata jallabiya pink, yace har kin shirya? Yace eh tare da fadin barka da safiya bai amsa ba sai jakar daya mika mata yace gashi saiki kara nasa an canza miki kudin dubai ne, tace wanda ka bani ya isa fah, fuska ya tamke yace bana son musu inna baki abu ki amsa kawai koda bakya so inna tafi saiki kai bola, amsa tayi tare da fadin kayi hakuri ba haka nake nufi ba, kafada ya daga alaman ke kika sani, yace in kin dawo zaki sami card a gida tace ok, tare da fadin nagode, kallonta yayi ji yake kaman yayi hugging dinta ko ya dan sami saukin abunda yake ji a halin yanzu, ganin inya ci gaba da kallonta komaj zai iya faruwa yasa yace in kun tashi tafiya saiki fadamin tace ok, falo ta nufa lokacin yayi dai dai da shigowan zarah da dan karamin akwatinta rungume juna sukayi sannan suka sami waje suka zauna, suna fira basu dade ba mum ta shigo falon gaidata sukayi tace saiku kai kayanku mota 10 zamu tashi kafin mu kai yayi, suka amsa da tam jawaheer itama ta shiga ta dauko kayanta tasa a mota sannan sukai breakfast, bayan sun gama ta kira samir tace zasu wuce falo ya fito ya gaida mum sukai sallama su mum suka fita jawaheer ce kadai a falon tace mun tafi janyota yayi yasa bakinshi cikin nata ya tsotsa na wajan second biyar sannan ya saketa tare da fadin ki kulan min da kanki, jiki a sanyaye ta fita dan ya kashe mata jiki, shima daki ya koma driver yaja su har airport suna zuwa suka shiga jirgi karfe goma dai dai suka daga zuwa kasar dubai siyayyan kayan akwati. Kwanan su jawaheer 7 a dubai suka dawo ba kayan akwati suka siya ba kawai harda kayan daki dan mum tace mata ya siya gida koda sunzo nigeria, akwati talatin da shida suka siya, ko wanne makil yake da kaya, atanfa materia english wear etc... Jawaheer tana kewan samir sosai gashi tunda suka tafi sau biyu sukai waya, taga katin bikin saura sati daya tayi mamaki ita ba kawaye gareta ba dan haka zarah ce taita rabo ta dai bama yan class dinsu, mum ta dauko mai gyara ta fara gyara mata yar tata, kun san farar mace babu wuya abu ya amsheta fatar jawaheer tayi laushi tayi silbi gwanin sha'awa har wani sheki takeyi da walkiya, ga kirjinta ya kara cika domin masu gyaran gaske mum ta dauko mata, anata hidiman biki ita jawaheer abunda yake damunta shine rashin wayan da basayi tunda sukayi a dubai yace mata shima yana spain zai raba kati, basu kara waya ba, gashi wayanshi baya shiga..... Yau za'ayi mothers day wanda mum ta shirya a wani haddan hall wanda saika amsa sunanka zaka iya kamashi manyan mata sun taru sosai masu hannu da shuni amarya saboda bala'in kyau dakyar na ganeta yan class dinsu sunyi mata kara sunzo matan dan event din na mata ne, sannan sunce zasu spain din harda mazan, anyi taron mothers day wanda mawaka daban daban suka baje basirar su, anci ansha kowa yaji dadi ga calender da aka raba wanda zarah ce ta hada musu cikin pics dinsu da jawaheer ta tura mata kwanaki sunyi kyau sosai mutane da dama sunyi mamaki da suka ga mijin nata suna ta fadin sun dace ashe dan kwallo ne kai ta sami mai mugun kudi, bayan sun koma gida saiga kiran samir da sauri ta tashi tayi toilet dan akwai kawayensu na class dinsu a dakinta dauka tayi cikin murya kaman zatai kuka tace hello, yace dear maiya sameki? Tace bakai bane kaki kirana ka kuma kashe waya, yace sorry dear jibi ina nan tafe uwar haka jibi kin zama tawa koh? Dariya tayi tare da fadin insha Allah ina ma auren soyayya mukayi kana so na kaman yanda nake sonka aida abun yayi armashi dariya yayi yace wani irin armashi? Tace mai zaka siyomin? Yace mai wayau kiban amsan tambaya na, dariya tayi danya gano ta tana son canza maganan ne, tace nima ban san amsa ba, yace zaki sani inna dawo bada wasa zan miki ba, dariya tayi tare da kashe wayan...... Jawaheer na gayyatar kowa da kowa daurin aurenta fans😀 *maryam obam* *JAWAHEER* *STORY AND WRITEEN BY......* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA* *(maryam Obam)* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝* *{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}* *wattpad @maryam-obam* *WWW.Maryamobamnovels.com* https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/ *DEDICATED TO.....* *Nafisa mrs dan malikin kawo* Page 51-52 Kiranta ya kuma yi dauka tayi yace naga pics kinyi kyau sosai, tace waya turo maka? Yace zarah nasa ta tura min pics din duk event din da akayi dariya tayi tare da fadin nasan banyi wani kyau ba zolaya na kake, yace uhm idan na dawo zan tabbatar miki da kyan da kikayi dariya ta kara saki tare da fadin sai anjima nabar mutane, yace mutanan sun fini ne? Tace a'a yace gud sai ki tsaya dan ban gama jin muryanki ba, tace uhm janta yayi da fira sosai sannan ya barta sukai sallama fita tayi zarah tace har an gama soyewan dan gulma waya shine a bayi, dariya tayi tare da fadin ehdin ina ruwanki ban san gulma, sauran sukai dariya tare da tashi suka mata sallama ita dama zarah yau tazo sai bayan biki zata koma, tare zasu kwana, raka su sukai har wajan gate akan sai sunzo gobe kamu, ciki suka koma jawaheer tace wai miye tsakaninki da khalil ne? Zarah tace mutunci jawaheer tace uhm in tayi wari maji, dariya zarah tayi suna cikin haka mum ta shigo dakin hannunta dauke da wani cup taba jawaheer tace ta shanye amsa tayi ta shanye sannan mum ta amshi cup din ta fita jim kadan sai ga kayan fruit an kawo musu, zarah ta amsa suka fara sha. Yau za'ayi kamu tun karfe biyu aka farama jawaheer makeup ba'a gama ba sai wajan 5 danma tayi alwala kafin a fara saida tayi sallah kafin aka fita zuwa wajan kamu kwalliyan yau tafi ta jiya, a wajan taga adda dariya tayi domin taji dadin zuwanta haka aka sa lalle duk abunda akeyi zarah na daukan ma samir tare da videos anci ansha an kashe naira kaman ba gobe, harda mutanan da ba'a gayyata ba sunzo yau domin kawai ansan dan kwallon kafar da duniya takeyi dashi shine zai auri yar nigeria abun yaba ma mutane da dama mamaki amma duk wanda yaga amaryan sai yace eh gaskiya sun dace domin itama ba'a baya ba wajan kyau koda zarah ta tura ma samir hotuna ganin yanda tayi wani irin bala'in kyau abun ya bashi mamaki uwa uba yaga ta kara girma da cika, ji yake kaman yayi tsuntsu ya dawo gida amma ba hali sai gobe, ranan gani yayi lokaci baya mishi sauri burinshi kawai ya dawo yaga jawaheer dinshi, bayan an gama komai aka koma gida jawaheer dakin da adda ta sauka ta tare tace adda shine sai yau zaki zo? Adda tace ni rabu dani ja'ira sai inji shuru tunda kika tafi sai kawai naji ance wai zakuyi aure shin yaushe kuka fara soyayya ne haka har abun yayi karfi? Dariya tayi tare da fadin to ni ta ina zan fara bada amsa? Adda tace tako ina, labari taba adda yanda abubuwa suka kasance har da amincewan da yayi zai aureta, adda ta nisa tare da fadin hmmm samir kenan ni nasan yana sonki idanshi kawai za'a kalla a ga sonki a ciki, dariya jawaheer tayi tace uhm adda nidai banga komai ba, wai ni kam adda ina dr ne? Adda tace kwanki yazo gida na, nake fada mishi maganan aurenki ai, jawaheer tace eyya kwanaki ya kirani yace min zaizo bai zoba na kirashi lokacin wayanshi a kashe, adda tace kai mutumin nan yana sonki shima sosai Amma zabin Allah koda yaushe muke nema, jawaheer tace haka ne adda tah, adda tace ni karki samin ciwon jiki miko min jakata, tashi tayi ta dauko mata jakar tata, adda ta bude ta ciro wata leda, gora ne guda hudu, taba ma jawaheer gora daya tace gashi maza shanye, tace miye wannan kuma? Adda tace dallah shanye ban son surutu dariya tayi tare da fadin toh mutum zaisha abunda bai sani bane, tsaki adda tayi tace kyaji dashi, bude goran tayi ta kafa kai ta shanye, adda ta kara mata wani, duka gora uku ta shanye, ya rage saura daya adda tace wannan kuma gobe zan baki shi, tace toh yar tsohuwa, nan sukai ta fira tare da bata shawarar yanda zata biyar da mijinta....... Adda tace jawaheer aure ba abun wasa bane, ba abunda za kayi bane yanzu anjima kace bakayi, shi aure anayin shine har abada, dan haka ina mai baki shawara da kiji tsoran Allah ki riqe mijinki da hannu bibbiyu kiyi mishi biyayya yi nayi bari na bari domin aljannarki na karkashin kafarshi yin biyayya ga miji na kara mishi son matarshi, sannan duk inda kike ki zamto mai riqema mijinki mutuncinsa, zaisa mijinki ya yarda dake karki kuskura ki bashi hanyar da zai fara zarginki, domin zargi yana lalata aure, tayi ma jawaheer nasiha mai ratsa jiki inda daka karshe tace mata shi zaman aure hakuri ne gaba dayanshi kin san duk abunda akace bauta sai anyi hakuri, sun dade suna fira kafin ta tafi dakinsu taga zarah nata bacci abunta wayanta taga yana wuta da sauri ta duba taga 11 miscall sa sauri ta bude taga duka na samir ne, kiranshi tayi kashe wa yayi ya kirata da sauri ta dauka tambaya ya jefo mata da fadin ina kika shiga? Tace ina dakin adda, yace tazo ne? Tace eh dazu tazo shine naje muna ta fira, murmushi yayi tare da fadin shine kika manta dani koh dan kinga adda, tace ko daya kana raina koda yaushe kasan ni ce nake sonka kaga kenan bazan manta dakai ba, yaji dadin magananta sannan yace wani irin so kike min? Tace sonda nake maka bazai iya misaltuwa ba, amma ka bari a hankali zaka fahimta, ajiyan zuciya ya sauke tare da fadin gobe ina nan tafe mai zaki tanadar min? Tace mai kake so? Yace ke kawai nake son gani dariya tayi tare da fadin saurin mai kakeyi? Yace nayi missing dinki sosai uhm kawai tace, murmushi yayi tare da fadin bari in barki sai na dawo goben, tace ok Allah ya kawo min kai lafiya ya amsa da fadin ameen, itama kwanciya tayi tana tunanin samir dinta yanzu gobe shikenan mun zama mata da miji. Rana dai bata karya sai dai uwar diya taji kunya inji masu iya magana, yau take friday ranan daurin auren jawaheer da samir da misalin karfe daya da rabi aka daura auren akan sadaki naira dubu dari wanda dubbanun mutane suka shaida cikin daurin auren harda shugaban kasar spain da manyan yan kwallon kafa da abokan arzikin samir duk sunzo tare da masoyanshi shugaban kasar nigeria shine wakilin jawaheer, an daura aure mutane sun watse ana ta san barka, tunda aka daura auren aka fadama jawaheer wani irin faduwa taji gabanta nayi ga jikinta yayi mata wani irin nauyi ta rasa gane wani irin yanayi take ciki farin ciki take ko akasin hakan, tana zaune a dakin adda ta kwanta adda ta shigo tana fadin kinzo kin kwanta a nan ga mutane can anata tambayanki har samir dinma ya dawo ashe kina nan, bata motsa ba balle tayi magana, jin muryanshi tayi ya shigo dakin lumshe ido tayi yau itace rana ta farko da take jin kunyan hada ido dashi, kiran sunanta yayi da jawaheer tashi kiga kyautar da nace zan baki ranan daurin auren mu, kamar karta tashi amma ta tashi taga wata mata amma tasa nikaf da wani namiji kallo daya zaka masa kasan balarabe ne, namijin ya fara fadin Allahu akbar wlh wannan yarki ce nadia ga kaman ku nan sak, jawaheer kam ta shiga rudani, matar ta cire nikaf jawaheer bata san lokacin data saki ihu ba tare da nuna matar da hannu dan tabbas itace a wannan hotan na passport lokaci daya kuma tasa kuka tare da fadin dama kina raye shine baki taba nema naba? Matar ta matso kusa da ita tana kuka dai dai lokacin mum da dad suka shigo dad yace tabbas itace ta bamu jawaheer, matar tace jawaheer shekaru ishirin da biyu yanzu ina fama da ciwo wanda ba komai yaja min ba sai tunanin kina wani hali, a ina zan ganki na bata tsawon wannan lokacin da tunanin inda zan ganki iyayena sunce in cireki a raina dan sun san hala kin mutu amma naki yarda da hakan, sai gashi a yau tunani na ya zama gaskiya ta nuna m samir tace lallai jawaheer kinyi dacen miji shine ya sadani dake Allah yayi ma aurenku albarka, jawaheer cikin kuka tace mai yasa kika bayar dani mai yasa kika gujeni tun ina yar karama ta? Matar ta nisa sannan ta sauke ajiyan zuciya tace yanzu zan fada miki..... TUNA BAYA..... sunana nadia ahmad yar kasar saudiya iyayena mu biyu suka haifa nida yayana muhd, mun taso cikin gata da kulawa kasancewan mahaifina mai kudi ne shi sosai, ummi na tana ji dadi fiye da komai nata tun ina yar karamata ake fadamin inada kyau, tun banyi wayau ba nake da burin zama doctor sau tari in ummi ko abba na tambaya na mai zan zama sai ince doctor haka na taso da son zama dr har na gama secondary skul dina na fara jami'a inda na sami course din da nake so wato dr, zan karanci fannin zuciya hawan jini da suger, a lokacin maza da dama suna rubibina amma bana basu dama, domin karatu nasa a gaba, gashi iyayena duk abunda nace shi sukemin har yayana yayi aure amma ni ban taba tunanin yin aure ba harna kammala karatu na fita da first class gwamnatin saudiya ta bani aiki duk da dad dina yaso ya gina min asibiti na kaina nace a'a kasata zanma aiki, ana cikin haka wani dan uwan abba na yazo yace yana sona naki yarda abba na har yayi fushi tare da fadin ya kamata ace nayi aure, nace mishi zanyi amma ba yanzu ba, ana cikin haka shugaban kasar nigeria a lokacin yazo da mahaifinshi asibitin da nake aiki wanda a lokacin ciwon zuciya yake nice dr din da zan dubashi, cikin ikon Allah na fara dubashi yana samun lafiya, ashe president muktar kabir sona yake lokacin kasancewan mahaifin nashi ya dade a asibtin yasa muka saba dasu, harya samu sauki aka sallameshi bayan sun koma muna waya akai akai harya fito ya fadamin abunda ke ranshi a lokacin nima banyi musu ba na amince mukai ta soyayya har magana taje wajan iyayena inda suka nuna su sam bazan auri dan nigeria ba sai dai in auri dan kasata, haka naki yarda na bijire musu har abinci na daina ci na daina sha na rame sosai, ganin haka yasa sukace sun amince amma duk abunda ya biyo baya babu ruwansu, hakan yamin dadi ba tare da tunanin komai ba nace na amince, haka akayi bikin mu aka tawo dani nigeria muka sauka a villa, inda matarshi take mai suna hauwa, matarshi ta amsheni hannu bibbiyu hakan yamin dadi, saida mukai sati biyu muna amarci kafin ya koma kan kujeransa wanda yaba mataimakinsa na wucen gadi, mutane da dama suna ta bani kyauta dan inyi musj hanya wajan mijina, daka baya ya hana dan baya son kowa ya sanni, haka na daina fita amma ita uwar gidanshi kowa ya santa, haka muke zama dashi bai taba haiyuwa ba, ina zuwa kam na sami ciki, tun daka lokacin na fara ganin sauyi wajan kishiyata yayin da mijinmu ke murna, a lokacin ta fito da kishinta karara harda kanin mijinmu yake biye mata ita tana tsoran in haiyu in mijin mu ya mutu in fita gado tunda ita ance ba zata taba haiyuwa ba, shiko kanin mijinmu yna tsoron in haiyu a hanasu gado, hka suka tsangwameni, wata rana president yayi tafiya suai hatsari a jirgi babu wanda ya rayu, gashi a ranan na haiyu, a gida aiko inata wajan window din daki na naji hauwa da kanin mijinmu suna fdin suje su kashe abunda na haifa, babu shiri naje dakina na dauko kudade nasa da password dina nayi sauri nayi rubutu, na fita daka gidan ashe sun ganni suna ta bina shine na hadu da wa innan bayin Allah na basu ke da nufin koda sun kama ni, ni daya zasu kashe, amma Allah bai basu sa'a ba na tsere, dakyar na samu akamin password da wuri nabar kasar na koma saudiya wajan dangina, koda na fada musu abunda ya faru, abba ya fadama gwamnatin saudiya ta kwatar min yancina yanzu hauwa da kanin mahaifinki suna bursuna za suyi shekara hamsin da aiki mai tsanani tunda sunyi niyan kisan kai Allah bai basu dama ba, har yanzu ba'a raba gadon mahaifinki ba saboda baki dawo ba kuma hauwa na prison, nasha zuwa nigeria ko zan ganki amma babu wani labari sai shekaran jiya wannan bawan Allah yazo min da maganarki da farko ban yarda ba saida muka ga pics dinki ya kuma fadamin shine zai aureki, naji ddi sosai domin shiba karamin mutum bane sananne ne, kuma naji dabi'unsa masu kyau ne ta nuna mutumin da suka zo tare tace ga yayana , rungumeta jawaheer tayi tana kukan murna tare da kara godema Allah da aka haifeta ta hanyar aure nadia taita ma su dad godiya bayan an kimtsa dad ya dauko kudi yaba nadia yace ga kudin da kika bamu lokacin, kai ta girgiza tare da fadin dawainiyar da kukayi da jwheer banda abunda zan biyaku wannan kudin naku ne halak malak, dad yana ta mata godiya, samir kam sai kallon jawaheer yake yana bukatar su kebe amma taki tashi kuma ta lura da hakan....... *maryam obam* *JAWAHEER* *STORY AND WRITEEN BY......* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA* *(maryam Obam)* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝* *{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}* *wattpad @maryam-obam* *WWW.Maryamobamnovels.com* https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/ *DEDICATED TO.....* *Nafisa mrs dan malikin kawo* Page 53-54 Mum din jawaheer ta kalli samir tace wani shirye shirye za kuyi kuma yanzu? Yace dinner ne amma a spain za ayi da yau kuma so mu wuce can ma dan dinner din gobe ne, nadia tace eh toh sai a shirya koh tunda kun tsara hakan, hakan ko akayi aka fara hadama jawaheer abubuwan bukatanta harda kawayenta aka akai airport cikin masu tafiyan harda adda😀 jawaheer ita da m samir suna mota daya driver na jansu, hannunta ya riqe tare da matsewa yace kin kara kyau da girma miye sirrin? Fisge hannunta tayi dariya yayi yace nayi laifi kenan? Kai ta girgiza alaman a'a, tace ban san da wani baki zan maka godiya ba, amma zan dan gwada nagode daka sadani da mum dina yau ya kasance min ranan farin ciki ranan da aka daura min aure kuma ranan daka kara min wani farin cikin nima Allah ya bani ikon faranta ma.... Toshe mata baki yayi da hannunshi sannan ya matsa kusa da ita yace yau nima zaki bani abunda nake so, tureshi tayi ya fara dariya ita kam ta rufe fuska har suka isa airport suka shiga jirgi, jirgi biyu ne aka basu dan mutanan sunyi ma jirgi daya kadan dan naga harda yan jawaheer fans group a tafiyan da yan hausa novels da yan maryam obam novels da sauransu...... Kowa ya shiga jirgi aka daga zuwa kasar spain duk yawan mutanan nan a hotel aka saukesu sannan ance suci komai kyauta duk abunda sukeso ga kudi da aka basu gaskiya sudai shar yan biki, ita kam jawaheer da mum, dinta da dad dasu adda gidansu na kasar suka sauka, jawaheer da mama take kiran mum dinta, jawaheer na makale da mamanta shiko samir gidanshi ya nufa yana shiga yaga sonia abun ya bashi mamaki hugging dinshi tayi tare da fadin congratulations na tayaka murna, abun ya bashi mamaki musamman da bata nuna komai ba akai, dakinshi ya nufa ya fada toilet dan yayi wanka bai dade ba ya fito yasa wasu kananan kaya sunyi mishi kyau sosai, ji yayi yana son jin muryan jawaheer dan haka ya dauki wayanshi ya doka mata kira, amma a kashe dan tsaki yayi tare da fadin bata sa sim dinta na nan ba, tashi yayi ya fito baiga sonia ba dan haka ya fice direct gidansu jawaheer din ya nufa inda ya samesu su duka a falo suna ta fira, shima zama yayi aka fara firan dashi, mama ta lura da jawaheer yake son gani dan haka ta kalleta tare da fadin jawaheer tashi ku dan zaga mana, tashi tayi shi kam dadi yaji, tashi yayi shima suka fita, wajan wata bishiya suka je a bayan gidan, zama sukai a kasa ya janyota jikinshi tare da fadin na rasa mai yasa bana son inga ina yin nesa dake, in nayi nesa dake sai in dinga jin wani iri, dariya tayi tare da fadin toh fah, toh mai yasa hakan ke faruwa? Yace shine nake so ki fadamin miye sirrin abun, hannunta ya riqo yana shafawa bata ce komai ba ganin haka yace jawaheer yau zan tafi dake koh? Da sauri ta dago tare da fadin dan Allah ka rufa min asiri, tamke fuska yayi yace kaman ya keba matata bace? Ina da iko inyi duk abunda naga dama dake babu wanda zaice min danme, tace hakane amma ai saika bari a kawo ni kaman yanda al'adanmu yake, yace ni bana son wani al'ada tunda ba addini bane, baki ta dan turo alaman taji haushi bata ankara ba taji bakinshi cikin nata, kissing dinta yake sosai tun bata mayar mishi da martani harta fara, sunyi wajan minti biyu suna tsotsan bakin junansu sannan ya saketa ta lumshe ido, ido ya zuba ma fuskanta yana kare mata kallo, lallai nayi dacen mata kyakyawa mai addini yar gidan mutunci, Allah na gode maka daka bani jawaheer a matsayin mata, gaba daya jikinta yayi weak bude idonta tayi taga ita yake kallo tayi sauri ta kuma rufewa dariya yayi tare da dagota daka jikinshi yace oya tashi muje yunwa nake ji, tace akwai abinci a ciki bari in kawo ma, yace nop muje akwai inda zamu ci, tace ok ina zuwa ciki ta shiga jim kadan sai gata ta fito ta canza kaya ido ya bita dashi komai jawaheer tasa yana amsanta, motarshi suka shiga shike tukawa har wani katon hotel ciki suka shiga, direct restaurant din hotel din suka nufa, masu abincin suka basu list na abincin suka nuna ba'a dade ba aka kawo musu, sunci sunsha sannan suka tashi wani daki taga ya bude gabanta taji ya fadi, amma haka ta daure ta shiga, bayan sun shiga kwanciya yayi akan gadon dakin tare da kallonta yace kunna min ac din, kunna mai tayi sannan ta sami waje ta zauna cikin kujeran dake dakin, kallonta yayi tare da bude mata hannunshi alaman tazo inda yake yi tayi kaman bata ganshi ba, ya lura da hakan yayi dan murmushi tare da tashi ya dauketa cak ta fara zillo amma ko a jikinshi kan gadon ya ajiye ta, tazo zata tashi ya janyota jikinshi tare da fadin muyi bacci, a hankali tace ni bana jin bacci, bai kulata ba sai kara manneta da yayi a jikinsa, bai dade ba bacci ya daukeshi yayi bacci sosai har wajan magrib tashi yayi tare da salati jin ana kiran sallah yasa ya tasheta da sauri tare da fadin tashi kiyi sallah, fita yayi ya nufi masallaci shima, koda ya dawo yaga ta ciro wani zanin gado ta yafa tayi sallah dashi, bayan ta gama yace su tafi, shiryawa tayi suka fita, bayan sun shiga mota yace mata gobe karfe hudu masu gyaraki za suzo, saiki zama ready suna tafiya yana mamin wakar da yasa na nicki minaj, har suka karasa kofar gidansu ya sauketa shima ya karasa nashi, koda ta shiga ta gansu a falo sai taji kunya amma sai basu nuna sun sam tana yiba, sai adda da tace sai yanzu bata ce komai ba ta sami waje ta zauna kusa da mum, tace mum gobe 4 masu makeup za suzo yace in shirya mum tace Allah ya kaimu, tashi tayi ta musu saida safe sannan ta wuce dakinta, tana sallah isha'i ta kwanta bacci. Washegari tun da safe gidan ya kacame anata gyare gyare duk da ba taro za'ayi a gidan ba, lokaci kadan gidan yayi kyau ga kamshi na tashi tako ina, jawaheer sai wajan 10 ta fito adda ce ma take ta buga mata kofa sai yasa ma harta fito, bayan ta fito adda tace mutum ya kwanta yaita bacci har yanzu, tace kai adda bazaki bar mutum ya huta ba wlh, adda tace malalaciya ni ban taba ganin amarya mai son jikinki ba anya ma zaki dinga dafa mai abinci kuwa? Jawaheer tace haba girki sai kace zamaninku salati adda ta saki tace amma ko wannan zamanin naku ba abun arziki kuka koya ba, toh a ina zai dinga cin abincin? Tace wajan saidawa adda taita bala'i wai taya zata bae mijinta ya dinga cin abincin saidawa saboda lalaci, su mum kam babu abunda suke sai dariya, dinning ta nufa ta zuba abinci ta fara ci, sallamanshi taji idonshi na kanta ganin irin kallon da yake mata yasa ta sakar mai murmushi, adda data lura dasu tace mutum dai ya kalli gabanshi kar yaje ya fadi, shi kam ba hausa yake jiba, jawaheer kam ta gane dasu take, dan haka ta kawar da kanta daka kallonshi, taci gaba dacin abincinta, gaida su mum yayi da mama suka ansa sannan ya gaida adda da fadin ina kwana adda? Amsawa tayi da lafiya qalau, itama jawaheer gaidashi tayi da fadin morning, amsawa yayi ba tare daya kalleta ba, zama yayi kusa da mama yace ya kwanan kasar? Mama tace alhmdlh ya shirye shirye? Yace an gama komai babu abunda ya rage, tace toh alhmdlh Allah ya taimaka, ya amsa da ameen khlil da dad da muhd da kabir da umar ne suka shigo cikin gidan, gaisawa sukayi sannan suka zauna anata tattaunawa yanda abun zai kasance samir yace ya gama shirya komai karsu damu, jawaheer bayan ta gama cin abinci barin falon tayi ta nufi dakinta, kwanciya tayi dan bata koshi da baccin ba adda ta tashe ta, amma sai dai kuma me gaba daya ta kasa baccin sai tunani, yau itace a matsayin matar m samir, tashi tayi ta fito falon ta kalli samir tace plz ina aka sauke baki zarah na can tace tare da kawayenmu zasu zauna, gashi ina bukatarta a nan, yace zaku hadu ai daka wajansu nazo nan, na bada kayan da za susa ankai musu ma, tace ok tare da komawa ta zauna akan kujera kusa da adda, m samir tashi yayi ya wuce haka sukai ta fira. Wajan 5 masu makeup suka zo, saida tayi alwala kafin ta zauna aka fara mata, ana cikin makeup din aka kira sallah, saida tayi sallah akaci gaba, kwalliya ake mata na kece raini, wedding gown aka sa mata, jin kiran sallah isha'i yasa tace a cire mata abun kanta tayi sallah, haka suka cire tayi sannan suka kara gyara mata, wow fadin irin kyau din da tayi bata lokaci ne, bazai ma iya faduwa ba, bayan an gama aka rufe mata fuska suka fita cikin wata dangareriyan mota suka shiga da ita, a ciki ta sami samir shima yasha suit fari irin kayanta fari, kallonta yayi tare da fadin wow my princess kinyi kyau sosai, murmushi tayi ba tare da tace komai ba, driver yaja mota suka tafi bayan sun karasa dangareren hall din tare suka jera da kawayenta da suka sa black gown mazan ma haka har cikin hadaddan hall din, zama kowa yayi inda karan kida ke tashi masu rawa nayi, amarya da ango akace su fito su zo suyi rawa, hannu ya miqa mata ta miqa mai nata suka fara rawa gwanin sha'awa zarah taki yarda tayi rawa da kowa saboda khalil na wajan, bayan amarya da ango sun zauna nan aka fara basu gift suna amsa, cikin masu bada gift din harda sonia wacce taba zarah ta amsa tayi godiya, murmushi sonia tayi tare da komawa ta zauna, anci ansha gaba daya kayan aka kwashe akai mota dasu, yanda aka tsara daka dinner zai tafi da ita, ita bata ma san hakan aka tsara ba, saida aka gama suka shiga mota, wani dangareren gida suka nufa bayan mota ta faka yace ta fito fita tayi sukai ciki, gidan ya hadu sosai a falo suka tarar da gift din da aka basu, gaba daya anyi raping dinsu, gasu manya wanda sonia ta bata ta dauko shine karamin ciki, zata bude samir ya amsa ya fara budewa zobuna ne guda biyu masu shegen kyau ko wanne an rubuta S&J ma'ana samir da jawaheer kamo hannunta yayi yasa mata daya shima yasa nashi, tunda yasa mata ta zauna a kasa murmushi yayi tare da kokarin dagata amma tayi wani irin wurgi dashi wanda saida ya bugu da bangon dake kusa dashi, cikin tsoro da mamakin irin tureshi din da tayi ya fara kokarin tashi nufanshi tayi ta shake mai wuya tare da fadin yau zan kashe ka, lokaci daya kuma ta saki dariya tare da kara jefar dashi wannan karan akai ya bugu harda jini ya fara zuba, dariya ta saki mai karfi tare da sauti gashin kanta duk ya mimmike tsaye........ Toh fah muje zuwa *maryam obam* *JAWAHEER* *STORY AND WRITEEN BY......* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA* *(maryam Obam)* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝* *{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}* *wattpad @maryam-obam* *WWW.Maryamobamnovels.com* https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/ *DEDICATED TO.....* *Nafisa mrs dan malikin kawo* Page 55-56 Riqe kanshi yayi da yake ta zubar da jini, a wannan karan baiyi yunkurin tashi ba, sai kallonta da yake da ido, yana mamakin maiya sameta lokaci daya haka, kodai aljanu gareta? Kai anya inma aljanu ne...... Ganinta yayi a tsugunne a kusa dashi tana dariya mai karfi magananta yaji ya canza kaman ba nata ba, gashin kanshi ta danqo da karfi duk da yana jin zafi baiyi kokarin hanata ba, haka ta dagashi sama ta kuma yin wurgi dashi tare da fadin zan kashe ka, ka shiga gonar daba taka ba duk cikin turanci take maganan, lokaci daya kuma tasa kuka mai ban tausayi, samir kam tunda tayi wurgi dashi ya bugi wani glass bai san inda kanshi yake ba, jin ruwa yayi a kanshi da sauri ya bude ido ganinta yayi tana dariya ga idonta ya rune yayi baki sosai, ga gashin kanta duk ya mimmike a hankali ya sauke idanshi akan komai na falon duk ta faffashe komai na falon komai ya wargaje ga jini itama na zuba a jikinta alaman taji ma kanta ciwo, da sauri ya tashi da nufin ya riqota amma ina wani irin ihu ta saki tare da shako mai wuya lokaci daya kuma tayi 'kasa tana surutai ganin ta sakeshi yasa yayi kokarin fita dan ya kira security dinshi su taimaka a kamata ji yayi ta janyo shi tare da wurgar dashi a kasa, tace kar kayi tunanin yin wani abu duk wanda ya shigo cikin gidan nan saina kashe shi, matsawa tayi daka inda yake ta zauna akan kujeran falon tana kallonshi tana dariya, shi kam gaba daya ya firgita da ita ya rasa ma abun yi, bai kara yinkurin tashi ba ga dariyan da takeyi babu dadin ji, ga tsoro, ganin karan ya isheshi yasa ya yankura ya tashi ganin ya mike yasa ta nufoshi amma wannan karan addu'a ne a bakinsa harta karaso inda yake tana kamashi ta sulale kasa tabata yayi yaga alaman kaman ta sumene da sauri ya dauketa yayi wani daki da ita ya rufe da key, fita yayi daka gidan cikin daren direct gidansu ya nufa, nocking yayi aka bude mai, mum ta tsorata da ganin dan nata jiki duk jini, tace samir lafiya maiya sameka? Bai iya furta komai ba sai shiga falon da yayi ya zauna yana maida numfashi kowa dake gidan ya fito, hankalin kowa ya tashi na ganin irin halin da yake ciki, mama ta matsa kusa dashi tana fadin samir maiya sameka ina jawaheer accident kukayi? Kai ya girgiza alaman a'a yace mama jawaheer ta sami tabin hankali itace tamin duk wannan abun, kowa dake wajan ya tsorata mum tace kaman ya labarin abunda ya faru ya basu, kowa yayi shuru yana jimami, mum tace ai sai muje gidan muga halinda take ciki sannan a kira dr, tashi sukayi da mum da dad da muhd da mama sai adda, suka shiga mota samir na tuki har gidan, salati kowa yasa da suka ga yanda falon ya dawo an wargaza komai dake falon, jin karan ihunta yafi komai daga musu hankali tare da gunjin kukanta, dr yace bari ya dubata, dakin suka nufa samir ya bude kofar, aiko suna shiga idonta ya sauka akan na samir da gudu ta cafkeshi tana fadin saina kashe ka wa yace ka kira mutane? Sakinshi tayi kuma ta saki dariya tare da kallon dr ta nunashi da hannu alaman ya fita daka dakin, ganin haka dr yayi saurin fita har zufa yake dan tsoro, kowa dake wajan ya tsorata da ganin yanayin data shiga, musamman ma da sukaji yanda take magana kaman ba ita ba, samir kam kuka yakeyi ganin yanda jikinta yake zubar da jini duk taji ma kanta ciwo sosai, matsawa yayi kusa da ita amma tayi baya da karfi tare da kwashewa da dariya mai sauti, kara nufanta yayi wannan karan bata matsa ba yana tabata tayi wurgi dashi su dad sukayi saurin riqoshi, fita sukayi sukai sauri suka sama dakin key, buga kofar tai tayi da karfi, shuru sukai a falo su duka, maman jawaheer kam ita da mum babu abunda suke sai kuka, adda ce tayi gyaran murya tace kunyi shuru ku dukanku ya kamata a nema mafita fah, dad yace inaga mu kaita asibiti, mum tace kana ganin yanda take fusge fusge ba bari zatai a kamata ba, shuru sukai kowa yana tunanin yanda za'ayi samir yace ina zuwa dad tashi yayi ya bude kofar shiga yayi tare da addu'a a bakinsa kaman dazu tana tabashi ta sume da sauri ya ciccibeta akai mota da ita suma tashi sukayi suka shiga akai asibiti da ita, ana zuwa aka sata akan gado, aka daure mata hannu da kafa dan dr din yaga yanda takeyi kafin yabar gidan, ana gama daureta kam ta fara fisge fisge, tare da ihu, kowa dake wajan saida ya tausaya mata, dr suka mata alluran bacci amma sam baccin yaki zuwa haka taita ihu mai karfi, dukansu haka suka kwana babu bacci, hankalin kowa a tashe yake musamman ma samir da yake jin jawaheer din kaman ranshi a yanzu, har rama yayi na lokaci daya, haka itama ta kwana tana ihu, duk wani abu an mata ba'a ga wata matsala ba kwakwalwanta an gwada lafiya qalau babu wani ciwo, hankalin kowa ya tashi sosai, adda tace nifa wannan ciwon ban yarda na asibiti bane gaskiya a kira malami, mum tace adda bari muga mai za suce, adda ta fara masifa ai matsalanku kenan abu gashi a fili inba aikin sihiri ba taya magananta zai canza sannan kuce ciwon asibiti ne ni wlh ku kira malami tun kafin abun ya girma, ganin yanda take ta bala'i yasa dad yama samir magana akan a kira malami, samir dad dinshi ya kira dabai san maike faruwa ba, bayani ya mishi a waya dad din yana ta salati, yace gashi nan zuwa, bai dade ba sai gashi da mlm sun zo, malamin yana daya daka cikin manyan malaman kasar spain, dakin da jawaheer take aka kaishi kallo daya ya mata yayi murmushi tare da fadin a kwance ta, dr din sukace a barta in aka kwanceta akwai matsala, yace toh su basu ita a mayar da ita gida, suka ce sam saita sami lafiya tana karkashin gwamnati ne yanzu tunda a kasar ta fara ciwon, saida samir yayi magana aka kwanceta ta fara zabure zabure mlm ya fara addu'a ihu ta fara tare da sumewa, yana ganin haka ya kalli samir yace dauketa ka kaita mota, hakan yayi suka bar asibitin gidan suka koma, akan kujeran falon ya ajiyeta malam din yace ya kwantar da ita a kasa, yace a bashi cup da ruwa samir da sauri yayi kitchen ya dauko cup da ruwan roba, ya miqama mishi, budewa yayi ya zuba a cup din yayi addu'a sannan ya miqama samir yace gashi ya shafe mata jiki dashi, amsa yayi ya fara shafa mata a jiki wani irin nishi takeyi mai karfi tana jijjiga jikinta malam din yace yaci gaba karya tsaya har sai yace ya daina, haka yaita shafa mata tana nishi daka karshe ihu ta fara mai karfi malam din yana ta addu'a yana tofa mata shi kuma, lokaci daya ta fara ihu mai karfi kowa dake falon ya tsorata dajin irin ihun da takeyi musamman m samir dake jin ciwon kaman a jikinshi yake, ido ta bude daya kara kadawa yayi baki, hannunta take ta kokarin dagawa amma ta kasa idon malam din ya sauka akan hannun zoben hannuta ya gani da yake kaman hayaki da sauri ya kamo hannun ya cire mata zoban wani irin ihu ta saki tare suka suma ita da m samir yana tsaye ta fadi tim, a kasa hankalin kowa ya kara tashi malam ya koma kan m sami yana shafa mai ruwan addu'a shima yana karatu shima hannun nashi ya kalla yaga zoben irin na jawaheer din cire mai yayi wani kara dakin yayi mai karfi, zuba ya fara keto musu su duka mlm din ya kalli su mum yace bari su farka mu gani anyi musu mugun sihiri ne, amma mun godema Allah abun ya hada da zoben dake hannunsu a ciki akasa sihirin bayan sun sa ne abun ya kamasu yanzu sai su dinga kula sosai domin inda abun ya dade samir zaiji tsanan jawaheer a ranshi sai su kara dagewa da addu'a, sai fadin alhmdlh suke bacci suke sosai mum tace bari ta kira masu aikinta suzo su gyara falon haka akayi aka gyara falon wajan da suke kwance kuma a haka aka barshi har su tashi, mlm din yace zai tafi yayi addu'a yace gashi in sun tashi a basu susha sannan yace a hadashi da wani ya amso musu maganin da zasu dinga shafawa na wani lokaci. Sonia dake zaune a gaban wani farin glass taga yayi baki ihu ta saki domin ance indai ya canza kala to komai zai lalace da sauri ta shiga daki ta dauko wasu allura ta fara ajiyewa akan glass din lokaci daya ya fara washe wa yana haske dariya ta farayi tare da fadin tunda ka yaudareni bazan taba bari kaji dadin aurenka ba saina lalata muku rayuwa, wannan sihirin har china naje dan inyi maganin ku, bazan taba barinku ba kuda jin dadin aure har abada dariya ta saki mai karfi........ Toh masu karatu muje zuwa muga ya farkawan su jawaheer zai kasance mu hade a next page *maryam obam* *JAWAHEER* *STORY AND WRITEEN BY......* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA* *(maryam Obam)* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝* *{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}* *wattpad @maryam-obam* *WWW.Maryamobamnovels.com* https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/ *DEDICATED TO.....* *Nafisa mrs dan malikin kawo* Page 57-58 Gaba daya kowa dake falon yayi jigum, kowa jiran tashinsu yake, har wanda yabi mlm ya dawo ya basu abunda ya bashi ya kawo ya karayi musu bayani, adda tace a shafa musu mai din kafin su farka, hakan akayi aka shafe musu jiki dashi, sunyi a kalla wajan awa uku suna bacci, jawaheer ce ta fara farkawa tare dayin salati, ganin samir kusa da ita jikinshi duk jini yasa ta rude tare da fadin sunanshi da samir maiya sameka haka, su mum ne suka karaso inda take suka riqeta kuka take sosai tare da fadin mum maiya sameshi dan Allah kuce ya tashi, karan hayaniyarta ne yasa ya farka ido ya kura mata yanda take kuka bai san lokacin da yayi hugging dinta ba dukansu sauke ajiyan zuciya sukeyi, lokaci daya kuma suka saki juna suna murmushi gaba daya sai yanzu yaji ciwon jiki na damunshi na wurgin da yasha haka itama gaba daya jikinta ciwo yake, adda tace sai kuje kuyi wanka aje asibiti wannan ciwukan a baku magani tunda jini na zuba, taimaka mata yayi ta tashi mum ta amsheta tace mishi ina ne dakinta? Nuna mata yayi mum ta riqeta sukai ciki, bayan sun shiga shima yayi nashi dakin, mum ce ta tayata cire kayan jikinta sannan tace toh maza kije kiyi wankan shiga toilet din tayi bata dade ba ta fito fuskanta duk a jagule mum tace yadai? Ko jikin ne? Tace mum bazan iya wankan nan ba wlh nasa ruwa a jiki na kaman nasa garwashi zafi jiki na yake ni na rasa garin yama naji ciwon nan ba, mum tace toh kisa kaya muje haka, bude wardrobe din dakin mum tayi ta dauko mata riga da wando tare da after dress mum ta dauko turare ta feshe mata jiki dashi, sannan suka fito koda suka fita basu ga samir ba zama sukayi suna jiranshi, basu dade ba sai gashi ya fito cikin wani riga mai gajeran hannu na yan kwallo, da dogon wando, yayi kyau goshin shi dai ya fashe amma wankan da yayi yasa jinin ya dan rage zuba, fita sukayi su duka bayan sunje asibitin aka duba su aka basu magani, mum tace suje gidanta hakan akayi mum tace abar jawaheer a nan harta warke, samir bai so haka ba amma babu yanda ya iya dole ya hakura, mum ta bashi maganinshi tace ya dinga amfani dashi kullum ta mishi bayani sosai yanda zai dinga yi, amsa yayi sannan yace zashi gida yaje ya huta, fita yayi ya nufi gidan, dakinshi ya nufa ya shafe maganin a jikinsa sannan ya kwanta bai dade ba bacci yayi awon gaba dashi, itama haka ta gefen jawaheer bata dade ba bacci yayi awon gaba da ita. Jawaheer na samun kulawa sosai wajan mum, ga zarah itama ta dawo gidan dan duk an tafi da yan bikin kowa ya koma sai zarah ce kadai ta rage wacce zasu koma tare dasu mum jibi, jawaheer na zaune a falo tana shan kankana da adda ta bata, samir ya shigo babu kowa a falon sai ita dan haka ya kura mata ido yanda take shan kankanan kaman ba zata shaba, ji tayi kaman ana kallonta ta dago dakai suka hada ido, murmushi ta saki shima mayar mata da martani yayi tare da nufanta ya zauna kusa da ita yace dear ina mutanan gidan? Tace suna ciki mama da mum kuma sun shiga kasuwa kai ya daga tare da fadin wai yaushe zasu bani matata ne? Dariya tayi tare da fadin tare dasu zan tafi nigeria tunda kasan har yanzu bawai na gama warkewa bane, wani irin kallo ya mata wanda ya sata yin dariya mai sauti,yace wasa ma kike yi, ni hakuri na ya kare kawai aban matata mu tafi yau tare,kamo mata hannu yayi yace ke bakya jin tausayina yanda nake kwana ni daya? Abun dariya ma ya bata sai kace sun saba kwana tare toh da dawa yake kwana, in banda fitina irin nashi miye na kosawa su koma gida shida bawai sonta yake ba kawai dai ya aureta ne, katse mata tunani yayi da fadin plz kice masu mum zaki bini yau, ido ta zaro tare da fadin rufamin asiri, yace ok to ni zan fada musu, dariya tayi tace uhm Allah ya taimaka, jan hancinta yayi tare da fadin tunda bakya so nima bazan yi magana ba suna cikin haka saiga su mum sun shigo tashi yayi daka kusa da jawaheer tare dajin kunyan yanda su mum suka gansu dan hannunshi nakan kafadanta, yi sukai kaman basu gani ba,gaida su mum sukayi bayan sun amsa mum tace mishi ya jikin yace da sauki, itama mama tambayarshi tayi ya amsa mata da jiki da sauki, mama tace jawaheer sai ki shirya kibi mijinki yau, mum tace mai makon ki bari ta kara warwarewa, mama tace a can ta warware ni banga amfanin zaman nata ba a nan tunda mu jibi zamu wuce, zarah ce ta fito mama tace yauwa zarah hada mata kayanta suzo su tafi gida, zarah ta amsa da toh tare da gaida samir sannan ta wuce ita kam jawaheer fuska ta tamke ya lura da hakan amma saiya basar sai sun tafi zaiji dalili, zarah bata dade ba ta gama hada mata kaya tare da adda suka fito tace ma jawaheer tazo, bayan sun shiga ta miqa mata gora tace oya shanye amsa tayi tana fadin ni ban cika son irin wannan abun ba wlh aita bama mutum tarkace, adda tace ke kika ga tarkace ni ban ganshi ba ja'ira, bayan ta shanye ta miqa ma adda goran, adda tace toh kardai a manta da addu'a sannan a riqe ibada sallah akan lokaci kuma banda wasa, tace insha Allah sannan ta fita, sallama tama su mum suka karayi mata nasiha sannan zarah ta rakata har mota bayan ta bude mata ta shiga sukai sallama yaja suka wuce. Bayan sun karasa gida ya kalleta yace saiki fito, fita tayi ta shiga ya dauko mata jakarta gidan ya canza mishi abubuwa yayi kyau sosai har yafi da haduwa, dakinta ta nufa ta fada toilet tayi wanka tare da alwala, shafa jikinta tayi da mai din da mln ya basu sannan ta shafa nata man a kai ta feshe jikinta da turare tasa wata doguwar riga daka sama ta kama kasan kuma ya bude, sallan la'asar tayi bayan ta idar ta kwanta akan gadon dakin, shigowa yayi ya ganta a kwance shima kwanciya yayi a bayanta tare da janyota jikinshi yace kin bar mijinki shi daya kinzo kin kwanta, bata cemai komai ba sai dan murmushin da tayi jin tayi shuru yasa ya juyo da ita ta gabanshi idonta a lumshe yace ina son a bani alkawarin da akamin, bude ido tayi tace name? Yace wanda kika min komai nakeso kince zan samu, dariya tayi tare da fadin mai kake so toh? Bakinshi yasa a nata ya fara tsotsa yayi wajan minti uku yana tsotsa gaba daya jikinta ya mutu sakinta yayi yace bari inje in dawo inna dawo zan fada miki coach dinmu yana nema na, bata iya magana ba sai kai data daga mishi alaman ok, fita yayi bayan ya manna mata peck a goshi, ido ta lumshe tana tuna abunda ya mata, ta dade tana kwance kafin ta tashi ta fito falo kitchen ta nufa dan ta duba abun ci,fridge ta bude ta dauko wani milk ta xuba a cup ta fara sha, saida tasha da yawa sannan ta dauko kaza a fridge din ta wanke tare da barbada mishi maggi da sauran kayan hadi tasa a oven baiyi 30mnt ba ya gasu ta ciro shi, tasa a cikin wani plate ta rufe da full paper, sannan ta dafa indomie da egg, bayan ta gama taci ta koshi jin kiran sallah magrib yasa ta shiga toilet tayi alwala tare dayin sallah, bayan ta idar ta koma ta karayin wanka tare da dauro alwala saida tayi sallah isha'i sannan ta zauna ta fara shafe jikinta da man da aka basu sannan ta shafa nata akai dasu turaruka masu dadin kamshi dakin ya bide da kamshi tako ina, wata shegiyar rigar bacci ta dauko mai daukan hankali, tana kokarin sawa taji an rungumota ta baya ihu ta saki tare daja da baya dariya yayi sosai ita kam sai sauke ajiyan zuciya take, cikin wani wando yake 3quater da singlet daka gani ya dan jima da dawowa nufanta yayi yana fadin sorry my dear tsoranki yayi yawa, kukan shagwaba tasa mishi tare da fadin shine ka bani tsoro in zaka shigo basai kamin sallama ba, yace sorry na tuba, tare da share mata hawayen data fara, yace kawo insa miki rigan, mika mishi tayi ya cire mata towel din dake jikinta idanshi ya sauka akan kirjinta dake tsaye kyam dasu, gaba daya jijiyoyin jikinshi suka fara harbawa da karfi, ganin haka yasa ta amshi rigan tasa da sauri tare da janshi tace muje kasi kazan dana maka, binta yayi kaman wani karamin yaro har dinning sukaje ta bude mai kazan ta yago ta bashi ci yayi tare da lumshe ido, tace yayi dadi kai ya daga mata alaman eh, haka taita bashi ganin bataci yasa shima ya fara bata har suka gama suka wanke hannu dakinta ta koma shima yayi nashi dakin jim kadan sai gashi ya shigo lokacin tana kwance akan gado, kallonta yayi yace tashi muyi sallah, bata musa ba ta tashi sukai raka'a biyu domin nuna godiya ga uban giji, bayan sun idar ya kama kanta yana addu'a gabanta taji ya fara fadi domin tasan yau mai cetonta sai Allah, bayan ya gama ya dauketa cak sai dakinshi akan gadon dakin ya kwantar da ita, cire mata hijab din yayi idonshi ya sauka akan nononta da suke rudashi a hankali ya furta i love it, ido ta lumshe gabanta na bugawa, hannunshi taji akan nononta yana shafawa tare da murza kan nipple dinta, idanta a lumshe amma tana jin abunda yake mata har cikin tsakiyan kanta, bakinshi taji akan nononta yana sucking tun tana dauriya harta fara saukar da numfashi tare da nishi mai sauti lokaci daya ya saka bakinshi cikin nata tare da murza mata nononta da hannunshi wani irin nishi takeyi mai sauti, kokarin saka hannunshi yake a gabanta tayi sauri ta juya tare da matsawa gefe tana hawaye tare da sauke ajiyan zuciya, ido ya kura mata yana kallonta ba tare da yace mata komai ba, ganin kuka take sosai yasa ya tashi ya matsa kusa da ita yana fadin jawaheer mai yake damunki? Cikin kuka tace ina jin tso........ Bakinshi yasa ya fara kissing dinta wanda shine ya hanata fadin abunda tai niya, duk yanda tai kokarin ta kwaci kanta abun yaci tura ita burinta ya furta mata kalman so kafin wani abu ya shiga tsakaninsu amma gashi bata ji hakan ba kuma yana kokarin yi mata aika aika, tun tana kokarin tureshi harta gaji ta sallama mai, cire mata rigan baccin yayi gaba daya babu komai a jikinta hannunshi daya yasa yana murza mata nononta dayan kuma yana wasa da gabanta dashi ta wajan dan kunlutun ta, wani irin nishi takeyi wanda bata san tanayi ba bakinshi yasa a gabanta ta wajan tsinin wato dan tsaka, wani irin kara ta saki tsotsa yake tana kankame jikinta saboda yanda takeji wani irin abu takeji yana mata yawo tun daka saman kanta har tsakiyan kwanyanta, tsotsa yake taa nishi tare da kara ruwa ne ya fara zuba daka gabanta ya fara bi yana shanyewa, saida yaga ta fita hayyacinta gaba daya bama ta gane a wace duniyar take sannan ya saka stick dinshi cikin gabanta ihu ta saki da karfi lokacin da yake kokarin shiga dakyar ya samu ya shige saboda matsin wajan, jawaheer kam bata jin komai sai azaba shi kam bai masan wace duniyar yake ba sai surutai yake ta mata tare da gaya mata kalamai na soyayya wacce ita bata na san yanayi ba dan azaba, tun tana maganan ya barta tare da kokarin tureshi harta kasa ta hakura domin jikinta ya mutu nishi take sama sama a kalla yayi awa biyu kafin yayi realising ganin jini na zuba a gabanta yasa ya rude gashi ko motsi batayi dan azaba, da sauri ya ciccibeta yayi toilet da ita, yasata cikin bab kankameshi tayi tana kuka, tausayinta ya kamshi da wani irin sonta sa yaji yana shigarshi, shiya mata wanka sannan yace tayi na tsarki fita yayi ya barta tashi tayi taji wani irin zafi babu shiri ta kara zama cikin ruwan zafin, shigo zanin gadon ya canza ya nufi dashi washing machine ya wanke tare da bussar dashi, dakinshi ya dawo dashi yasa shi cikin wardrobe dinshi, jinta shuru shuru bata fito ba yasa ya koma toilet din ganinta yayi tana ta baccinta, murmushi yayi tare da nufanta ya watsa mata ruwa a fuska tayi firgit ta tashi tsaye tare da sosa ido, shiya taimaka mata tayi wankan tsarkin sannan yace ta fito kuka ta saka mishi ba tare data daga koda kafarta ba, ganin haka yasa ya dauketa cak yayi kan gado da ita, dakinta ya koma ya dauko mata rigan bacci yasa mata sannan ya kwantar da ita tare da fadin plz kibar kukan haka ki kwanta ki huta, kwanciya tayi tana mai jin haushin abunda yayi mata bata dade ba baccin wahala yayi awon gaba da ita, wani irin tausayinta yake ji shida kanshi yasan bai mata da wasa ba gata virgin, daga hannu yayi yana karayi ma Allah godiya daya sami matarshi a matsayin budurwa, lallai ya kasance cikin maza masu sa'a wanda yanzu mata masu kai budurci gidan aurensu sunyi karanci an maida zina kaman ba komai ba, kira ga yan mata wlh budurcinki shine kimarki idan kika bama wani kato kanki wlh idan kikai aure baki ba mutunci wajan miji har abada bama lallai bane yaci gaba da zama dake dan yasan yar iska ya aura, kai budurci gidan miji yana kara ma mace kima daraja da soyayya a wajan miji tare da yarda dake, mata da yawa suna yaudaran kansu wajan bama saurayi jikinsu da sunan shi zamu aura ko ya kawo sadaki na ai, wlh yar uwa karki kuskura ki fara yarda daka ranan da yayi zina dake wlh ya barki kenan koda ma bai barki ba zaki ga maganan aure ya zama yana yawo, domin fah shi a kullum zarginki zai dinga yi yana ganin tunda kika bashi zaki bama wani, kar so ya kaiku ya baro, sannan akwai gwajin da maza da dama suke yima mace kafin aure banda lokacin yin bayani amma gamai bukatar bayani ya iya min magana ta pc ko kuma masu number ta, Allah yasa mu dace. Jawaheer bata farka ba sai da taji ana kiran sallah asuba, bata ganshi ba dan haka ta tashi taja jiki tayi dakinta alwala tayi tazo tayi sallah, wani irin sanyi take ji domin jikinta akwai zazzabi sosai, kwanciya tayi akan darduman,koda ya dawo daka masallaci ya nufi dakinshi bai ganta ba dakinta ya nufa ya ganta a kasa tana bacci daukanta yayi yaji jikinta da zafi, jin an dauketa yasa ta bude ido ajiyeta yayi tare da fadin fever kikeyi? Kafin ta bashi amsa ya fita jim kadan sai gashi da tea tashinta yayi ya bata kadan tasha sannan ya bata paracetamol bayan tasha ta kwanta bacci ya kara dauketa, shima kwanciya yayi a bayanta. Sai wajan karfe goma ta tashi taji jikinta yayi mta wayam kaman an cire maa wani abu daka jikinta hka take ji, toilet ta nufa tayi wanka bayan ta fito ta shafe jikinta da maganinta sannan ta shafa manta wata doguwar riga tasa yar kanti kafanta har yanzu yana mata zafi in mutum ya lura da yanda take tafiya zai gane anyi wani abu, falo ta nufa tana zuwa taga an zagaye falon da stikers masu wuta da marasa wuta ko wanne an rubuta i love you jawaheer thanks for yesterday night, ido ta lumshe tana kara nanata kalman i love you jawaheer, bude ido tayi ta ganshi a gabanta a hankali yace ina sonki jawaheer kece farin ciki na, zan baki farin cikin da duk wani namijin bana tunanin zai iya baki, wani irin hawaye ne yake zuba a idonta wanda zan iya dangantashi dana farin ciki ne, a hankali tace yaushe ka fara sona? Yace tun sanda na fara ganinki naji ina sonki ban dai nuna miki bne dan a lokacin ina tare da sonia, ki yarda dani ina sonki har cikin raina kuka ta saki tare dayin hugging dinshi......... Ina labarin sonia ku biyo ni a next page wanda zan warware muku komai. *maryam obam* *JAWAHEER* *STORY AND WRITEEN BY......* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA* *(maryam Obam)* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝* *{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}* *wattpad @maryam-obam* *WWW.Maryamobamnovels.com* https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/ *DEDICATED TO.....* *Nafisa mrs dan malikin kawo* Page 59-60 *LAST PAGE* Cikin kuka take fadin mai yasa kaki fadamin tun tuni bayan baka tare da sonia, lallai yau nafi ko wace mace farin ciki a duniya, idan ka barni da wannan kadai ya isheni, peck ya mata a goshi tare da fadin jawaheer ina jinki cikin raina da zuciyata lallai nafi ko wani namiji sa'a dana mallake ki, zan nuna miki gata zan mayar dake sarauniya na gode da babbar kyautar da kika bani, wanda bazan iya biyanki ba, lallai jawaheer a jiya zuwa yau sonki ya kara nunkuwa a raina ninkin baninki ban taba zaton akwai budurwa virgin ba a wannan duniyar tamu data lalace ba, sai gashi tunani na ya zama karya tunda na sami matata a virgin, hannunta tasa ta rufe fuskanta alaman taji kunya, dariya yayi ya dauko wasu takardu ya bata yace wannan na kamfanin motoci na ne dake kasar london na baki halak malak, ya kuma bata wani takardan yace wannan na gidan da nasiya a nigeria ne guda biyu na baki dayan, check ya bata wanda yayi signing yace gashi ki rubuta iya adadin kudin da kike bukata na baki kyauta, kuka ta farayi tare da girgiza kai tace nagode amma bazan amshi wannan kyautar ba, bana bukatar komai a gareka burina in kasance dakai har abada duk rintsi duk wuya banso kayi nesa dani koda kuwa mai zai faru in kamin haka shine kamin babbar kyauta a duniya ta, murmushi yayi tare da fadin nayi miki alkawari bazan taba barinki ba jawaheer yanda bazan iya rayuwa babu ruwa ba haka bazan iya rayuwa babu ke ba, sannan wannan kyautar na riga nayi niya bazan amsa ba, saiki adana zai miki amfani sannan daka yau za'a fara turo miki duk wata riba da aka samu cikin acct dinki na company din motar, kara rungumeshi tayi tace mai yasa zaka matsamin in ina tare dakai bana bukatar komai, kai daya ne jin dadin rayuwa na, kara matseta yayi cikin jikinsa yana fadin i love you my angel, sun dade a haka kafin ya saketa yace karta kara cemai bata son abunda ya bata, hannunta yaja sukai dinning abinci ya zuba mata, kallonshi tayi tare da fadin wa yayi? Yace ni mana, dariya tayi ta faraci tace wow ashe ka iya abinci yace yes da mai kika daukeni, dariya tayi taci gaba daci har ta koshi, shida kanshi ya kwashe kayan tare da fadin anjima masu aiki za suzo su farayi, tace ok, ranan suna tare daka tayi motsi yace mai nene haka yaita tarairayanta cikin so da kauna. Yau su mum za subar kasar dan haka yace jawaheer ta shirya su rakasu airport, cikin sauri ta shirya tana ta murna, bayan sunje ta rungume zarah ta gaida iyayenta adda kam sai kallonta take tayi dan ta gano yanzu jikar tata ta zama babbar mace, karfe 11 ta musu a airport 11:30 jirginsu ya daga jawaheer ji tayi kaman ta bisu, amma babu dama dan yace shida suzo nigeria saiya gama wasanshi da zaiyi, wani supermarket sukaje ganin mutane sun fara ihu yasa yabar wajan tare da fadin ita taje ta dauki abunda take so, tace a'a haka suka dawo gida, samir yana nunama jawaheer so da kauna tunda sukai sex sau daya har yau babu abunda ya kara shiga tsakaninsu duk da yana matukar bukatanta amma yana tausaya mata dan yaga har yanzu tafiyanta bai koma normal ba, amma hakurinshi ya kare a matse yake sosai, gashi sai taita saka kaya masu fito mata da sura, yau yana zaune akan kujera yana danna laptop sai gata ta fito cikin riga da wando rigan rabin nononta a waje, idanshi ya sauka akan nononta gashi ta matso kusa dashi tana manna mishi jikinta tun yana kokarin ya mayar da sha'awar shi har abun yafi karfinshi bai san lokacin daya saka bakinshi cikin nata ba tare da yage mata riga ya fara murza mata nono yana shafawa a hankali ita kam tsoro ne ya kamata dan har yanzu bawai ta daina jin zafi bane,duk yanda taso ta hanashi amma abun ya faskara domin bada wasa yake ba, duk da itama tana jin dadi amma tana tsoran yasa stick dinshi cikin gabanta, saida ya bari ta saki jiki ta fara fita hayyacinta sannan ya saka sandar girma cikin gabanta, ido ta fara lumshewa tana dan nishi sai dai abunda ya bata mamaki wannan karan bata ji zafin da take tunani ba duk da akwai zafin amma tana jin dadi, sai surutai yake ta mata tare da fada mata kalaman soyayya, tayi realising yakai sau uku amma shi ko sau daya baiyi ba, tun tana daurewa dan gajiya harta fara tureshi amma ina ko gezau baiyi ba saida yayi wajan awa uku yana abu daya, sanda ya cire stick dinshi daka gabanta har wani zugi taji yanayi dan tsabagen ciyuwa, lallai ta dade tana jin labarin akwai maza harijai masu yin awa biyar shida fiye da haka suna sex har karyata take sai gashi ita nata mijin abun nashi sai a hankali inda zata barshi to shi tana ganin saiya wuce awa takwas yana abu daya, baccin wahala ne ya dauketa, shiko janyota yayi jikinshi yana mai kara sonta. Sonia lokacin da taga abun ya washe tana cikin murna taga ya kuma dawowa baki, cikin tashin hankali take ta sintiri a dakin, kuma dawowa tayi ta fara cire alluran lokaci daya glass din ya fashe ya tarwatsan mata a fuska, sai farkawa tayi ta ganta a hspt, glass ya shigan mata ido bata gani gaba daya, tayi kuka kaman ranta zai fita ga takaicin bata samu abunda take soba ga idonta ya nakasa, kasarta tasa aka mayar da ita dan tasan kam a yanzu samir ko kallo bata isheshi ba dan tasan yasan ita ta musu magic dole ma tayi nesa dashi inma batayi ba da wani idon zata ganshi, hmmmm lalli in zaka gina ramin mugunta gina shi gajere wata kila kaine zaka fada wanda gashi ya faru akan sonia, a yanzu babu abunda take saida na sani inda batai magic ba da tasan yanzu da idonta bai makance ba, gashi yanzu bata gani komai sai anyi nata babu asibitin da ba'a kaita ba amma ance glass din ya nakasa idon haka dole aka hakura. Jawaheer yanzu ta saba da mijinta kuma duk wani bukatarshi tana kokarin jurewa shima da kanshi yasan tana daurewa ne amma bukatarshi yafi karfinta dan yana da yawan sha'awa tunda yayi aure, sannan ita duk wata hanya da za tabi dan ta nuna mishi bata gaza ba ko gajiya tana bi, yanzu watansu biyu duk ya buga match dinsu kuma sunci cup din, yanzu ana shirin yin world cup ne wanda za'a buga a kasar canada, ita burinta a kullum suje nigeria amma yace babu inda zasu sai ta sami ciki, yanda ya lura da ita kaman bata son ana mata maganan haiyuwa daka ya fara zata canza maganan sannan kullum akwai maganin da yaga tana sha, ya tambayeta kona miye tace na karin jini ne dana sa mace ta sami ciki da wuri, yaji dadin hakan duk da ya nuna mata ta daina sha tunda ba dr bane ya bata, tace dr ya bata tun a nigeria, bai kara bi takan maganin ba, yau tana zaune ita daya a dakinta tana chatting ita da zarah tana fada mata suda khalil sun fahimci juna har manya sun shiga zancen, dariya jawaheer tayi tare da doka mata kira bugu daya ta dauka, jawaheer tace dama nace da wani abu aketa min rufa rufa ashe dai da walakin goro a miya, dariya zarah tayi tare da fadin lokaci yayi kin sani yanzu ai, jawaheer tace a ina aka tsaya da zancen? Tace ansa rana nan da wata biyu, jawaheer tace kai Allah ya kaimu sai a fitar mana da anko mai kyau, zarah dariya tayi tace kafin lokacin cikin ki yayi girma, tace uhm su ciki manya rufamin asiri ban gama cin amarci ba, maza yanzu daka ja haiyu zaka ga canji, zarah tace babu wani canji shine ma zai karasa ya soki, jawaheer tace mubar zancan ya maganan skul? Zarah tace alhmdl, ke naji ai sun yarda kinayi ta online, jawaheer tace eh ai nayi sa'a wlh, sunce exam kawai zan dinga zuwa, zarah tace ina ma nice dariya suka sa sunyi fira sosai daka karshe sukai sallama, tana kashe wayan taga samir a tsaye yana kallonta yana sakar mata murmushi ita kam tamke fuska tayi tare da juya mishi baya, dariya yayi dan ya gano yau rigima take ji tun dazu, wajanta ya nufa tare da kwanciya akan gadon yasa kanshi akan cinyanta, yace baby waya tabamin ke ne wai? Cikin shagwaba tace bakai bane, yace ni mai nayi? Tace kaki bari muje nigeria kuma in an fara world cup nasan baka da lokaci, yace ai world cup zai kai nanda 3 to 4 month kafin a fara, ni nafi son muje wajan su mum lokacin cikin ki yayi girma, baki ta turo tare da fadin nifa bani da wani ciki kawai muje, kallonta yayi tare da fadin baby wannan maganin da kike sha plz ki daina ni ban yarda dashi ba, may be shine yake hanaki ma daukan ciki, dan shuru tayi can tace amma ai na daukan ciki ne tunda baka so zan daina, yace gud ki shirya cikin week din nan sai muje nigeria din, wani irin ihu tasa tare dakai bakinta cikin nashi ta fara kissing dinshi, shima dai biye mata yayi dan dama shi baiki koda yaushe yayi sex da ita ba, kokarin cire bakinta tayi daka nashi tana kokarin tashi rigota yayi tare da fadin ai baki isa ba tunda kika fara sai kinje karshe tace nifa bana so, ya kwaikwayi magananta da fadin ni kuma inaso, dariya tayi ya janyota ta fado kanshi, nan ya fara wasa da nononta da harshenshi tana wani karkashe ido tana lumshewa tana budewa, wasa yake da nononta sosai yana lasa yana tsotsewa wani irin abu takeji tun daka kan kanta har kasan maranta, cire mata kayanta yayi a hankali lasanta ya farayi da harshe tun daka sama har gabanta wajan dan kullutun gabanta ya tsaya inda ya cafkeshi yana tsotsa kaman sweet wani irin kara take saki mai ciki da dadi tare da nishi mai sauti, gaba daya ta fita cikin hayyacinta sai shafa mishi kai take tayi yayin da bakinshi yake tsotsan mata tsinin gabanta, kafanta ya daga duka biyun ya ware su yanda zaiji dadin sha, tayi realising yakai sau biyu amma bai daina shafa saida tayi sauri ta juya da karfi kafin tayi baya tana mai sauke ajiyan zuciya, janyota ya kuma yi yasa hannunshi cikin gabanta ya fara fingering nata ihu takeyi tana lumshe ido lokaci daya tayi baya tare da cafko stick dinshi tana wasa dashi, tashi tayi daka kwancen da take tasa bakinta akai ta fara tsotsa ido yake lumshewa tare da kara tura mata kanta ciki ruwa ne ya feso mata daka ciki bi tayi tana shanyewa tare da kashe ido jan stick dinshi yayi ya fara watsa mata ruwan sperm din a fuska, tana bi da harshenta tana son ta lashe sun dade suna haka kafin ya saka mata sandar cikin gabanta dan kara ta saki shigo sambatu yake ta mata tare da nishi itama ta gefenta haka wani irin nishi take saki mai sauti samir ya iya juya mace suna style kala kala sai yayi wajan realising sau biyar a kalla yayi wajan awa uku da wani abu kafin ya barta, wani irin nishi take saki mai kara, bacci ya daukesu gaba dayansu. Yau su jawaheer za'a zo nigeria tun da asuba da tayi sallah bata koma bacci ba take ta kara shirye shirye shiko koda ya dawo daka masallaci bacci ya koma, bai farka ba sai wajan 9 wanka yayi ya fito falo yaga ta shirya harda akwatinansu a gabanta dariya ma ta bashi yace tafiyan nan an fasa sai wani week din, da sauri ta tashi ta tareshi tare da fadin plz kayi hakuri wlh kirjina zai buga, dariya yayi tare da fadin muga kirjin, kokarin budemai take yace muje wani irin ihu ta saki sannan yaja akwatin suka fita security dinshi suka amsa suka jera a mota, sannan suka kama hanyar airport, jirgin 10 suka hau suna zuwa jirgi ya daga zuwa nigeria, koda suka sauka daka airport sun tarar da driver din gidan mama yazo daukansu, shiga sukai direct gidan mamanta suka nufa, jawaheer tayi mamakin ganinta a nigeria mama tayi musu abinci kala kala, bayan sun kimtsa samir yace zaije gidan mum a can zai kwana sukai sallama jawaheer ta rakashi har mota inda yake fada mata zaiyi missing dinta itama hakan tace mishi ya mata peck sannan tace ya gaida su mum kafin tazo, ciki ta koma inda ta sami mamanta a ciki, tambayan mamanta tayi mai takeyi a nan? Tace ta dawo nan da zama labari ta fara bama jawaheer bayan bikinta an raba gado sun sami company da yawa ga tarin dukiya sai taga gwara ta zauna a nan ta dinga juya kudin ita da dan uwanta muhd daya dawo nan shida iyalanshi, jawaheer tace ina kakanninta wato iyayen mamanta, maman tace mamanta ta rasu saura babanta shiya bata shawaran ma ta dawo nan, jawaheer taji dadi sosai suna ta fira ita da mamanta wani irin shakuwa ya kara shiga tsakaninsu. Washe gari tun karfe 11 samir yazo gidan dan yana kewar matarshi bayan sun gaisa da mama ta kawo mai abun taba baki sunyi fira sosai sanda zai tafi tace ma jawaheer tabi mijinta su tafi, wani irin dadi yaji da mama ta fadi hakan ita ko jawaheer bata so binshi yanzu ba amma babu yanda ta iya, kayanta ta hado aka kai mata mota suka wuce, tasha ko gidan mum zasu sauka amma sai taga sunje wani gida mamaki ya kamata tace nan ina ne kuma? Yace gidanmu a nan zamu dinga sauka in munzo, gidan ya hadu sosai tace nasha koh gidan mum zani in kwana hararanta yayi tare da fadin bazan kara yarda ki kwana a ko ina ba, jiya naji jiki, bata fuska tayi tace nidai gaskiya ka kaini gidan mum, wucewa yayi ya barta tare da fadin wasa ma kikeyi, ganin ya shige ciki yasa ta bishi a kan gado ta ganshi daka shi sai boxer babu riga a jikinsa, zama tayi a gefen gadon tana bata fuska, a hankali yace mata anjima zan kaiki ku gaisa sai mu dawo, tace plz ka barni in kwana daya mana, yace ban yarda ba in kika karamin maganan kwana zuwan ma ba zaki ba, tunda taji haka taja bakinta ta tsuke tayi shuru, sai wajan karfe 2 suka fita zuwa gidan mum, mum taji dadin ganin yanda jawaheer ta kara kyau da girma, dad shima yaji dadin ganin yar lelen tashi, haka ma su khalil inda jawaheer take ta tsokananshi da angon kawata, yace kuma dole kice mata anty ba, mum tace rabu da khalil kizo kici abinci, zama tayi akan dinning ta fara cin abinci samir yace mum ni baza'amin tayi ba, mum tace ai naga cikin kane in kaga dama zaka ci, dariya yayi tare da fadin shikenan nama koshi zani gidan mamana inci, mum tace kai ka sani ai, dad yace zoka zauna kaci kaji yarona, zama yayi kusa da jawaheer tashi tayi ta bude cooler tasa mai tare da ajiye mai mum tana jin dadin yanda suke nunama juna kulawa, sun dade a gidan sai wajan 10 suka bar gidan suka koma gidansu. Bikin su zarah ya gabato zarah da jawaheer suna ta shirye shirye na shirin biki, suna zaune a falo samir ya shigo ya kalli zarah yace bride to be, dariya tayi tace insha Allah, jawaheer takai mata dukan wasa tace yayan mijinki nefa, ko yar kunyan nan bakyaji, dariya zarah tayi tace eh din, zama yayi sukai ta fira tare, samir yace ana gama bikin su zarah zasu koma spain, gaba daya iyayensu suna zargin ciki jawaheer gareta amma basu sam wayam bane bata da komai samir shima ya kosa ta samu ciki domin yana masifar son yara, an shiga hidiman bikin su khalil jawaheer kam gaba daya ta shiga busy bata da sakat yau za'ayi arebiyan night su jawaheer dama jinin larabawa ne sai ta fito sak balarabiyanta sunyi kyau sosai ita da gogan nata, tare suka tafi anci ansha taro ya watse, biki ya rage kwana biyu akai dinner, jawaheer gaba daya bata da lokacin kanta balle na wani, shima samir bai matsa mata ba ya barta dan yasan yanda take da zarah gashi kuma dan uwansu zata aura, ranan friday aka daura auren zarah da khalil, maitama aka kai zarah gidanta yayi mugun haduwa sosai da sosai, dad din m samir shima yazo tunda yaga maman jawaheer ya tabbatar bata da aure ya fadama dad shifa yana son aurenta, dad yaji dadi dan dama yace zama babu aure babu kyau, koda aka fada mata da farko tace a'a saida dad da yayanta muhd suka mata nasiha harda mum cikin masu yin campaign dakyar dai ta amince ba karamin dadi dad din m samir yaji ba, samir da jawaheer basu san da zancen ba sai dai sukaji ana fadin daurin aure ranan friday sunyi mamaki sosai amma sunji dadin hakan, dole suka kara daga tafiyansu sai bayan bikin baban mum din jawaheer shima yazo daka saudiya jawaheer taji dadin ganinshi inda aka daura aure ranan friday kowa ya watse mama tare suka tafi spain ita da mijinta inda tabar komai nata a hannun dan uwanta, sai muce Allah ya bada zaman lafiya, suma su jawaheer sun koma. Rannan samir ya dawo gida ya tarar da jawaheer nashan wannan maganin daukewa yayi tare da fadin bana hanaki shaba, tace toh naga har yanzu ban sami ciki bane sai yasa nake sha, fita yayi da maganin gidan ya bari gaba daya sai da yamma ya dawo, sai gashi ya shigo ranshi a bace kallonta yayi idonshi har rinewa yayi saboda bacin rai, yace nagode da abunda kikai min ban taba tunanin bakya kaunata ba sai yau, ashe dama ba sona kike ba duk karya ne, kullum kina fadin wannan maganin na daukan ciki ne ashe duk karya ne, ashe maganin hana daukan ciki kike sha, hawaye ne ya fara zubar mishi tare da fadin maina miki maina aikata miki dana fuskanci wannan hukuncin, ta bude baki zatai magana ya dakatar da ita tare da fadin ya isa haka ban son jin komai ki tafi bana son ganinki i hate you jawaheer plz ki tafi ki barni, kuka take sosai tare da kokarin bashi hakuri ganin haka yasa yabar gidan gaba daya cikin bacin rai, zama tayi a kasa tana kuka toh ina zata ma inta tafi sai yanzu tayi nadama akan maganin da take sha, ita a tunaninta tunda mijinta celebrity ne kaman bazai so haiyuwa ba, sannan tana ganin inta haiyu zai canza mata hmmm kunji jawaheer da wani irin tunani, kuka take sosai tashi tayi zata daki jiri ya dibeta ta fadi, tadai farka ta ganta a gadon asibiti ga mum dinta ga samir a kusa da ita, kuka ta saki tare da fadin dan Allah kayi hakuri wlh bada nufin kuntata maka nayi b...... Hannu yasa ya toshe mata baki mamanta ta mata sannu sannan ta fita ta basu waje, kallonta yayi yace jawaheer kina shan maganin planing dan karki haiyu gashi Allah ya kamaki yanzu kina da cikin wata biyu, ido ta lumshe tabbas hakan zai iya faruwa kwanaki tayi missing din kwana daya bata shaba, kuma lokacin bata dade da gama period ba, katseta yayi da fadin idan kikai gigin zubar min da ciki sai nayi shari'a dake, cikin kuka tace kayi hakuri na tuba wlh nayi nadama bada nufi nayi ba wlh saboda sonka nayi haka tace nasha koh ba zaka so haiyuwa yanzu ba sannan ina tsoran in haiyu ka rage sona, hancinta yaja da karfi yace jawaheer karki kara wannan tunanin bana daya daka cikin maza marasa son yara ina matukar kaunan yara,jawaheer karki kara yin wani mummunan tunani a kaina komai zai faru sonki bazai taba raguwa a cikin raina ba, matse hannunshi tayi tana kuka tare da bashi hakuri tace mum ta sani? Yace a'a bata san komai ba ta dai san kina da ciki komai za kiyi min zan jure bana daya daka cikin maza masu yawan kai kara, peck ya mata a goshi tare da fadin mai zaki ci? Tace babu komai bana bukatar cin komai, kwanan jawaheer uku aka sallameta, suka dawo gida samir na nuna mata kulawa sosai daka tace wash zaice mai nene mai yake miki ciwo mai za kici, haka zaiyi ta tambayanta,mum tazo taga jawaheer din ita da dad sati daya sukayi suka koma, mama kullum ita take kawo musu abinci dan tace ta daina girki. An fara world cup samir shi daya ya tafi canada domin da spain za'a fara bugawa, jawaheer kam gidan mama ta koma da zama, kullum tana kan tv tana kallon kwallo, saida yayi wata biyar a can lokacin jawaheer ta kusa haiyuwa an gama world cup kasar spain taci kofi anyi ma yan wasan mugun manyan kyauta musamman ma m samir daya zama zakaran kwallon kafa, tunda sunci world cup kuma duk shi yake zura ball din, m samir ya kara samun mahaukatan kudade sosai, ranan daya dawo gida ba karamin dadi yaji ba na ganin matarshi a gida, tun daka falo ya fara nuna nata soyayya tare da nuna mata yayi kewarta cikin ta yayi girma sosai, tunda ya dawo baya fita yaba mama kudi masu uban yawa a musu siyayyan kayan babys. Wata ranan monday jawaheer ta tashi dana kuda, ama bata bari ya ganeba, tunda yaji ta shuru taki fitowa daka daki ya kira mama, ba'a dade ba mum tazo, dakinta mama ta shiga taganta tana cije baki tare da kuka, da sauri mama ta karasa wajanta tana fadin lafiya jawheer, tace mama ciki na ke ciwo, dauko mata hijab tayi tasa mata dai dai lokacin samir yazo shiya kamata suka fita har mota akai asibiti da ita, ana zuwa akai labour room da ita, samir kasa zama yayi batai doguwar nakuda ba ta haiyu ta haifi yan biyu duka maza lokacin da aka fada musu ba karamin murna yayi shiga dakin yayi yaga yaran kyawawa sak shi, farin ciki yake tayi har baya iya boyewa, mum washe gari suka iso harda zarah kwananta biyu aka sallamesu, gaba daya gidan jawaheer din suka nufa, mum ce ta zauna da ita take mata wanka, samir zama yake ya tasa yaran gaba yaita kallo, wani irin so yake ma yaran tare da mamansu. Ranan suna yaran suka sukaci sunan dad dinshi muhd ali da muhd jibrin sunan dad din jawaheer ana kiran yaran da suhail da suhal, ranan suna an kashe naira dad ya kashe kudi sosai haka dad din samir ma, saida jawaheer tayi arba'in sannan mum ta koma. BAYAN SHEKARA BIYAR Abubuwa da dama sun faru ciki harda kammalawan karatun jawaheer gashi ta kara haifan yan biyu mata, akasa nadia da bilkisu, suna kiransu da ummi da ma-ma, mum din jawaheer ta haifi yarinya mace mai suna fatima, haka zarah ma ta haifi mace mai suna aysha, samir ya kara samun arziki fiye da nada yana bala'in ji da iyalanshi, jawaheer na zaune a daki samir ya shigo yace ina yara? Tace suna bacci, yace bari in kara baki yan biyu, koda yake wannan karan yan uku zan bayar dariya tayi tare da fadin na yaf..... Bata karasa ba ya cafkota tare da kissing dinta, kashe wuta samir yayi alaman in fita daukan rahotan ya isa haka.......... Toh anan zan dakata ALHAMDULILLAH SAI MUN HADE A SABON NOVEL DINA GODIYA GA MASOYANA MASU BIBIYAR NOVELS DINA MARYAM OBAM NA MATUKAR YINKU SOSAI Downloaded from GNOVELS.COM.NG This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG For feedback and support Facebook : https://facebook.com/gnovels Twitter : https://twitter.com/gnovels Telegram : https://t.me/gnovels