Downloaded from GNOVELS.COM.NG This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG For feedback and support Facebook : https://facebook.com/gnovels Twitter : https://twitter.com/gnovels Telegram : https://t.me/gnovels S͆A͆N͆A͆D͆I͆N͆ B͆E͆S͆T͆Y͆ 💐💐 L͆a͆b͆a͆r͆i͆/R͆u͆b͆u͆t͆a͆w͆a͆✍️ R͆A͆B͆I͆'A͆T͆U͆ A͆H͆M͆A͆D͆ M͆U͆A͆'Z͆U͆ (R͆U͆B͆B͆Y͆) G͆a͆j͆e͆r͆e͆n͆ l͆a͆b͆a͆r͆i͆ (S͆h͆o͆r͆t͆ s͆t͆o͆r͆y͆) M͆y͆ t͆e͆l͆e͆g͆r͆a͆m͆ g͆r͆o͆u͆p͆ l͆i͆n͆k͆👇 https://t.me/+YyGNyl_PQv1iODdk M͆y͆ w͆a͆t͆t͆p͆a͆d͆ l͆i͆n͆k͆👇🏻 https://www.wattpad.com/1190086089?utm_medium=link&utm_source=android&utm_content=share_published 💐💐💐💐💐💐💐💐 Dᴇᴅɪᴄᴀᴛᴇᴅ ᴛᴏ Mʏ ʟᴏᴠᴇʟʏ ᴍᴏᴍ (Hᴀᴊ Rᴜᴋᴀɪʏʏᴀ), Aʟʟᴀʜ ʏᴀ ƙᴀʀᴀ ᴍɪᴋɪ ʟᴀғɪʏᴀ ᴅᴀ ɴɪꜱᴀɴ ᴋᴡᴀɴᴀ ❤️❤️ Sᴘᴇᴄɪᴀʟ ɢɪғᴛ ᴛᴏ Kᴀɪɴᴜᴡᴀ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀᴛɪᴏɴ Aʟʟᴀʜ ʏᴀ ƙᴀʀᴀ ʜᴀᴅᴀ ᴋᴀᴡᴜɴᴀɴ ᴍᴜ ᴀ ᴅᴜᴋ ɪɴᴅᴀ ᴍᴜᴋᴇ 🤗 *____________________________________* *🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼* *🇦SSOCIATION🤝🏻* ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation *_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻 https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association *____________________________________* B͆I͆S͆M͆I͆L͆L͆A͆H͆I͆R͆ R͆A͆H͆M͆A͆N͆I͆R͆ R͆A͆H͆E͆E͆M͆ Ɗu͆k͆k͆a͆n͆ y͆a͆b͆o͆ d͆a͆ g͆o͆d͆i͆y͆a͆ s͆u͆n͆ t͆a͆b͆b͆a͆t͆a͆ g͆a͆ A͆l͆l͆a͆h͆ m͆a͆i͆ k͆o͆w͆a͆ m͆a͆i͆ k͆o͆m͆a͆i͆, t͆s͆i͆r͆a͆ d͆a͆ a͆m͆i͆n͆c͆i͆n͆ A͆l͆l͆a͆h͆ s͆u͆ ƙa͆r͆a͆ t͆a͆b͆b͆a͆t͆a͆ g͆a͆ M͆a͆n͆z͆o͆n͆ m͆u͆, m͆a͆s͆o͆y͆i͆n͆ m͆u͆ a͆b͆i͆n͆ a͆l͆f͆a͆h͆a͆r͆i͆n͆ m͆u͆ A͆n͆n͆a͆b͆i͆ M͆u͆h͆a͆m͆m͆a͆d͆ S͆.A͆.W͆, d͆a͆ i͆y͆a͆l͆a͆n͆ s͆a͆ d͆a͆ S͆a͆h͆a͆b͆b͆a͆n͆ s͆a͆ b͆a͆ƙi͆ ɗa͆y͆a͆... Y͆a͆d͆d͆a͆ n͆a͆ f͆a͆r͆a͆ r͆u͆b͆u͆t͆a͆ w͆a͆n͆n͆a͆n͆ l͆i͆t͆t͆a͆f͆i͆n͆ a͆ s͆a͆'a͆, A͆l͆l͆a͆h͆ ka͆ b͆a͆n͆i͆ i͆k͆o͆n͆ k͆a͆m͆m͆a͆l͆a͆w͆a͆ a͆ s͆a͆'a͆, k͆u͆s͆k͆u͆r͆a͆n͆ d͆a͆ ƙe͆ c͆i͆k͆i͆ A͆l͆l͆a͆h͆ y͆a͆ y͆a͆f͆e͆ m͆i͆n͆, A͆l͆l͆a͆h͆ y͆a͆ b͆a͆m͆u͆ i͆k͆o͆n͆ y͆i͆n͆ a͆m͆f͆a͆n͆i͆ d͆a͆ a͆b͆i͆n͆d͆a͆ y͆a͆ƙe͆ c͆i͆k͆i͆... Gᴀʀɢᴀᴅɪ!! Gᴀʀɢᴀᴅɪ!!Gᴀʀɢᴀᴅɪ!!! Wᴀɴɴᴀɴ ʟɪᴛᴛᴀғɪɴ ƙᴀɢᴀɢɢᴇɴ ʟᴀʙᴀʀɪ ɴᴇ, ʙᴀɴ ʏɪ ꜱʜɪ ɗᴀɴ ᴄɪɴ ᴢᴀʀᴀғɪɴ ᴡᴀɴɪ ᴋᴏ ᴡᴀᴛᴀ ʙᴀ, ꜱᴀ'ᴀɴɴᴀɴ ʙᴀɴ ʏᴀᴅᴅᴀ ᴀ ᴊᴜʏᴀ ᴍɪɴ ꜱʜɪ ᴛᴀ ᴋᴏ ᴡᴀᴄᴄᴇ ꜱɪɢᴀ ʙᴀ, ʏɪɴ ʜᴀᴋᴀɴ ʙᴀʙʙᴀɴ ʟᴀɪғɪ ɴᴇ, ᴋᴜᴍᴀ ɪɴᴀ ʜᴀʀ ɴᴀ ᴋᴀᴍᴀ ᴍᴜᴛᴜᴍ ᴅᴀ ʜᴀᴋᴀɴ ᴢᴀɪ ғᴜꜱᴋᴀɴᴄɪ ʜᴜᴋᴜɴᴄɪ... PⒶⒼⒺ 1️⃣ Anty!! Anty!! Anty!! Mommy ta ce ki tashi daga bacci nan kafin ta zo da ƙanta. Dogon tsaki ta ja, ƙara gyara kwanciyar tayi ba tare da ta tashin ba, ganin haka ne yasa Arya fita daga ɗakin da gudu ta nufi parlour, wata mata ce a kalla zata kai shekara arba'in, tana zaune a kujera, waya ce a hannun ta da alama magana ta gama yi a wayar, ganin yar autar tata ta dawo ba tare da wacce ta aika a kira ma ta ba ne yasa ta cikin hassala ta ke faɗin "Arya, ina Raudar take? Ko baƙi je kin taso min ita bane"? Bude baƙi Arya tayi a shagwabe ta ce : To Mommy na je amma ta ƙi tashi kuma fa tana ji ina ce da ita Mommy na ƙiran ta, shine ta ƙara jan bargo bata kulani ba" Shikenan! Go and call Saleem" cewar Mommy ta fita a parlour'n tayi hanyar dakin Raudah, ita kuwa Arya da gudu ta fice compound din gidan dan kiran Saleem kamar yadda mommy ta aike ta. Mommy na shiga ɗakin Raudah ta hango ta nannaɗe a gado tana barci, charger ta cire a jikin socket ta nufi gaɗon, tana isa ta yaye bargon ta zuba ma ta a cinya, wani ƙara Raudah ta saki, ba shiri ta miƙe ta na sosa wajan ɗan taji zafi sosai, bacci ne fal a idon ta amma dole ta tashi ganin Mommy ce da ƙanta. "Yanzu fisabillilahi Raudah kin ma ƙan ƙi adalci kenan? Sau nawa ina aiko Arya ta tashe ki? Duk yau aikin gidan ni nayi abu na, wallahi idan ki ka ce da wannan lalacin zaƙi je gidan miji wahala zaƙi sha dan kuwa babu namijin da zai jure wannan halin na ki" Shiru ta yi tana shagwabe fuska ganin Mommy na ta sababi yasa ta yi shiru, ba ta ce komai ba, ita kuwa Mommy ci-gaba ta yi da fada, ɗan halin na Fauzah ya fara isar ta yarinya sai lalaci, sai da tayi mai isar ta sannan ta fice a ɗakin. Mommy na fita Raudah ma ta fice a ɗakin, tsakar gida ta je, ganin har rana ta fito sossai yasa ta hanzar ta daukan boƙiti wankan wanƙa ta nufi kitchen, ruwan zafi ya gani a kettle an tafasa, da hanzari ta juye ta shige bayi, koda ta fito daga wankan ba ta bi ta ƙan abin ƙaryawan da a ka ajiye ma ta ba ɗan tasan zuwa yanzu ya gama sanyi, wayar ta iPhone 7 plus da ke kan gadon ta ɗauka, ganin sha daya saura minti takwas yasa ta ce "Wayyo Allah na!! Allah yasa Bestynah bai yi fushi dani ba dan yau kwata_ƙwata ba muyi magana ba" tana fada tana kokarin kiran number BESTY ... Sai da ta ƙira sau biyu ana uku ya daga bai ce komai ba ta fara magana cikin shagwaba " Haba BESTY tin da kaga ban neme ka ba ai sai ka kira ni kuma ƙasan munyi da kai yau za ka raka ni wajan tela" Shi ma daga can ɓangaren shagwabe murya ya yi ya ce "Kiyi hakuri BESTY na ban tashi da wuri ba ne, kin ganni nan ko fitowa ban yi ba har yanzu ina daki, ban ma san wacce wainar aka toya a cikin gidan ba, tashi na kenan sai ga call ɗin ki". Narƙe murya tayi ta na faɗin " ba mun yi alƙawarin ba zamu dinga zama da yunwa ba, though nima tashi na kenan ɗan da charger waya ma Mommy ta tashe ni", har da yin shesheƙar ƙarya kamar yana gaban ta, da sauri Besty ya riki ce sai cewa ya ke "Kashhh!!amma dai Mommy bata ji miƙi ciwo ba ko? Ni fa da wani abu ya same ki gwara mulkin Buhari ya dawo farko, ya karshe maganar yana dariya, ita ma Rauda sai da ta ɗara jin abinda ya ce. Waya suka ci-gaba da yi cike da kulawa ganin call ɗin Ya Noor yana ta shigowa ne yasa ta ce " Ammm besty bani minti biyar pls, Ya Noor yana ta ƙira na ko me zai ce mun ohoo, ba na fada maƙa ba ranar, tunda ya kawo sadaki sai ya dinga min wasu abubuwa kamar iko _ iko, Ni wlh na gaji da halin shi, mutum sai shegen miskilancin masifa, mtseww", Shiru ya yi bai ce mata komai ba sai da ta karaci mitar ta sannan ya ce ma ta " kinga malama kin dame ni da maganar mutumin nan, ai tin ba yau ba nace ki rabu dashi ƙin ki ji, oh saboda ban isa dake ba ne, hmmm ai nasan matsayi na, mutumin da ko kallon arziki baya min, ta yaya ma zan ji dadi ace bestyna tana tare da wanda baya mutunta Ni? Indai har da gaske ni better half ɗin ki ne, to ya zama dole ki rabu dashi mu nemo wani saurayin" ya faɗa in a serious tone, Zufa ne ya fara karyo wa a jikin ta, tabdi!! tama isa ta ce ma Baba bata son Nura? Ai Wlh sai ya sumar da ita daga ita har Bestyn, gashi kuma bata son ɓacin ran besty'n na ta, ganin tayi shiru ne yana ta magana shi kaɗai yasa ya kashe wayar shi gaba ɗaya, ai kuwa sai ga kiran Noor ya sake shigowa a karo na uku wayar ta, tin da taga kiran da Noor yake ya yi yawa tasan wani abu zai fada ma ta mai muhimmanci ɗan shi Noor call daya yaƙe mata idan bata daga ba to ba zai kara kira ba har sai ta neme shi da ƙanta, ta inda BESTY ya fishi kenan sai ya mata missed call biyar ko shida koda kuwa hira kawai yake so suyi da ita. Sai da call ɗin ya kusa yankewa sannan ta daga, bata ce mai komai ba, hakan ba karamin fusata Noor ya yi ba, lallai ma Raudah ba karamin raina shi ta yi ba, ya zama dole ya yi maganin ta... Tana kwance a saman ƙirjin shi, wasa take da gashin da ƙe kwance a saman faffadan kirjin shi, hakan ba karamin nishadi yaƙe sa ka ta ba, kallon ta ya yi da rinanun idanuwan shi, da kyar ya ke iya kamo numfashin shi saboda wata sha'awar ta daƙe ƙara azalzalar shi, babu abinda yake so sama da ya ga ya yi sex da ita amma taƙi bashi hadin kai, tsawon watanni 5 kenan da haduwar su,kuma babu irin sabon da basu yi ba, ta yadda bata iya tsallake maganar shi, abu ɗaya ne ya kasa samu daga wajan ta, sai dai duk lokacin da suka haɗu suyi romancing ɗin junan su, a wanan lokacin hakurin shi ya ƙare, Hannun ta ya cire daga jikin shi, ganin hakan ne ya sa tayi saurin kallon shi "Haba mana Adnan, me yasa za ka hanani yin abinda nake matukar so da kauna" ta fada kamar zata fashe da kuka, Wata iska ya furzar da kyar ya aro jarumtar yin magana "Ya kike so nayi ne Fadeelah" ɗan baƙi san yadda na dauke ki bane, tin lokacin da muka fara abota har nasan damuwar ki da wancan tsohon saurayin na ki, na daukar wa kaina alkawarin share miƙi hawaye duk rintsi duk wuya, bani da burin da ya wuce na faran ta miƙi rai, amma ke kin gagara fahimta, ko da yaƙe dan kin ga na damu da ke ne shi yasa! Tabbas taga ɓacin rai a idanun Adnan, amma kuma fa ba zata iya bashi ƙanta ba, wannan tanadin sai gidan miji, to amma ya zata yi da rigimar da yaƙe neman ɓullo ma ta? Innaaa!! Ba abu bane mai yiwuwa, tab ai ba zata taba yadda ya aikata abinda yake so da ita ba, zina kenan fa, ta fada a ranta, shi kuwa Adnan yana nazartar yanayin ta ba tare da ya ce komai ba ya miƙe ya shiga toilet, bata yi ƙasa a gwiwa ba wajan tashi ta bi shi cikin toilet ɗin gudun kar ranshi ya ƙara ɓaci... Toh fa reader's da alama besty zai yi halin na shi🤣 VOTE COMMENTS SHARE ✍️ BADAWEEYERH 💐💐S͆A͆N͆A͆D͆I͆N͆ B͆E͆S͆T͆Y͆ 💐💐 L͆a͆b͆a͆r͆i͆/R͆u͆b͆u͆t͆a͆w͆a͆✍️ R͆A͆B͆I͆'A͆T͆U͆ A͆H͆M͆A͆D͆ M͆U͆A͆'Z͆U͆ (R͆U͆B͆B͆Y͆) G͆a͆j͆e͆r͆e͆n͆ l͆a͆b͆a͆r͆i͆ (S͆h͆o͆r͆t͆ s͆t͆o͆r͆y͆) M͆y͆ w͆a͆t͆t͆p͆a͆d͆ l͆i͆n͆k͆👇🏻 https://www.wattpad.com/1190086089?utm_medium=link&utm_source=android&utm_content=share_published 💐💐💐💐💐💐💐💐 Dᴇᴅɪᴄᴀᴛᴇᴅ ᴛᴏ Mʏ ʟᴏᴠᴇʟʏ ᴍᴏᴍ (Hᴀᴊ Rᴜᴋᴀɪʏʏᴀ), Aʟʟᴀʜ ʏᴀ ƙᴀʀᴀ ᴍɪᴋɪ ʟᴀғɪʏᴀ ᴅᴀ ɴɪꜱᴀɴ ᴋᴡᴀɴᴀ ❤️❤️ Sᴘᴇᴄɪᴀʟ ɢɪғᴛ ᴛᴏ Kᴀɪɴᴜᴡᴀ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀᴛɪᴏɴ Aʟʟᴀʜ ʏᴀ ƙᴀʀᴀ ʜᴀᴅᴀ ᴋᴀᴡᴜɴᴀɴ ᴍᴜ ᴀ ᴅᴜᴋ ɪɴᴅᴀ ᴍᴜᴋᴇ 🤗 *____________________________________* *🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼* *🇦SSOCIATION🤝🏻* ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation *_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻 https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association *____________________________________* Na gode da ganin comments ɗinku, Allah ya bar ƙauna... Besty yace na gaishe ku🤪 PⒶⒼⒺ 2️⃣ Ƙo a toilet ɗin ma sai da Adnan ya ƙara rage zafi , ganin hankalin shi ya kwanta ne ya sa tayi wanka ta fita daga toilet ɗin ta koma ɗaki, tana cikin sa ƙaya wayar ta dake ƙan bedside ta fara ringing, ganin sunan Anty baro_baro yasa gaban ta dukan tara_tara, ai ba zata iya dagawa ba, sai yanzu ta tuna da aikan da Anty ta ma ta, shine ta biyewa Adnan suka zo hotel, "Hubbey ka fito Anty nata kira na, kazo ka kaini inda ta aike ni" Fitowa ya yi yana goge gashin kan shi da towel, ganin ta ya yi a tsaye, matsawa ya yi kusa da ita ya kamo ƙugunta, ƙara narke masa tayi a jiki sai ta juyo ta ƙarbi towel din ta ƙara sa goge mai jikin shi, yana saka kaya ya ɗauki mulkin mashin din shi suka fice a ɗakin. A kasuwa ya ajiye ta ya wuce shagon shi bayan ya mata alƙawarin dawowa da daddare, da sauri ta shiga kasuwar, da kyar ta samu abinda Anty ta aike ta saboda yamma tayi, wajan ƙarfe biyar ta shiga gida. Ai kuwa titsiye ta Anty tayi bayan ta haɗe rai "Daga ina kike?" "Daga ƙasuwa nake Anty"cewar Fadeela muryar ta na rawa "Kasuwar ubanki!!, Awan ki nawa da fita daga gidan nan? Kin tafi yawon ta zubar ɗin ki ko? Wai Fadeelah me kike so ki mayar da kan ki ne? Ga maneman ki na arziki amma kin ƙi yadda, kin nace ma wannan shegen yaron mai kai kamar saman risho" Ai kuwa ɓaki na zumɓura jin munanan kalaman da Anty take jifan besty Adnan da shi, wallahi banda yayata ce da yau sai na sumar da ɓakin ta. Murfin kwanon da ke hannun ta ba tare da na lura ba ta buga min shi, ai kuwa sai da bakina ya fashe , ganin jini na zuba yasa na kwalla ihu tare da barin wajan ina tafiya ina ja mata Allah ya isa, ba baƙin da ya fashe bane ya ba ni haushi, a'a bestynah da ta zaga ne ya ƙona min zuciya, wajan rijiya na nufa na wanke bakina, bayan na gama na shige ɗaki abuna, ummahani yar Anty na gani a cikin ɗakin tana wasa da remote, ai kuwa sai da na mangare ta na ce "shegiya da ido kamar malmo, Allah ya isa dukan da babar ki tamin" ai kuwa ta sa kuka ta fita a ɗakin ganin haka yasa ni ma barin ɗakin kar Anty tazo ta kuma min wata masifar. Raudah ganin shima Noor bashi da niyyar magana yasa ta kashe wayar, ai kuwa ranshi ya baci, "Ba komai, zaki shiga hannuna ne" Noor ya fada yana dukan table din office ɗin shi. Ina kashe wayata na saka riga da skirt na wata jar atampha, ban shafa komai ba kasancewar ni fara ce sol kuma ni ba mai ra'ayin kwalliya bace, ko da yake besty ne ya cusa min ra'ayin nan wai shi yafi son ganin fuska na a haka, fita nayi zuwa dakin mom, ganin bata gyara ba yasa na gyara mata sa'annan na share dakin , ai kuwa nasha yabo a wajan ta "Iyeee!! Yau su Raudah anyi abun kai, chab da alama za'ayi ruwan sama da ƙanƙara, yau kece da gyara dakin nan?" Mommy ta fada cike da mamaki Murmushi nayi ina wasa da zoben hannuna na ce "Eh mom ya yi kyau ko?" "Ah sosai ma Allah ya miki albarka", Mommy ta fada, alamun jin daɗin abinda nayi sun bayyana a fuskar ta ganin ƙamar Raudah ta fara shiryuwa. Ɗaki na koma na saka gyale na, purse na ɗauka na fice a tsakar gida na iske Mommy na ma ta sallama ɗan zuwa wajan tela, ina fita ƙofar guda na ha motar Noor a waje a hankali na taka har wajan shi ina hu_hura hanci ɗan ban so ganin shi ba, "Maye", na furta a raina Cikin ɓacin rai Noor ya ce; "Raudah me yasa kika kashe min waya"? A dage nace mai " tambaya kake ko neman sani? Bai ƙara yin maganar ba, mun kai minti ɗaya a haka, ganin kamar bai da abin fada yasa na ce " kaga malam!! ni ina da wajan zuwa idan kai baka da shi", "Ina zaki je?" Noor ya tambaye ni, ko kafin na bashi amsa na hango bestyna yasha gayu cikin wasu kananun kaya jeans baƙi da jar riga yana ganin motar Noor ya haɗe girar sama da ƙasa ya samu gefe ta tsaya ya naɗe hannu a kirji yana kallona, Noor bai ga zuwan Besty ba, ganin ban bashi amsa ba yasa shi faɗin "Ki shiga na kai ki na ce " "No ka barshi za mu tafi da Dee dina" Juyawar da Noor zai yi sai ganin Dee ya yi a tsaye yana harar shi, ai kuwa a zuciye ya fito daga motar ya nufi inda yake... Hahahaha fan's din besty yau fa da alama zai sha ɗuka a wajan noor VOTE COMMENTS SHARE ✍️ BADAWEEYERH 💐💐S͆A͆N͆A͆D͆I͆N͆ B͆E͆S͆T͆Y͆ 💐💐 L͆a͆b͆a͆r͆i͆/R͆u͆b͆u͆t͆a͆w͆a͆✍️ R͆A͆B͆I͆'A͆T͆U͆ A͆H͆M͆A͆D͆ M͆U͆A͆'Z͆U͆ (R͆U͆B͆B͆Y͆) G͆a͆j͆e͆r͆e͆n͆ l͆a͆b͆a͆r͆i͆ (S͆h͆o͆r͆t͆ s͆t͆o͆r͆y͆) M͆y͆ w͆a͆t͆t͆p͆a͆d͆ l͆i͆n͆k͆👇🏻 https://www.wattpad.com/1190086089?utm_medium=link&utm_source=android&utm_content=share_published 💐💐💐💐💐💐💐💐 Dᴇᴅɪᴄᴀᴛᴇᴅ ᴛᴏ Mʏ ʟᴏᴠᴇʟʏ ᴍᴏᴍ (Hᴀᴊ Rᴜᴋᴀɪʏʏᴀ), Aʟʟᴀʜ ʏᴀ ƙᴀʀᴀ ᴍɪᴋɪ ʟᴀғɪʏᴀ ᴅᴀ ɴɪꜱᴀɴ ᴋᴡᴀɴᴀ ❤️❤️ Sᴘᴇᴄɪᴀʟ ɢɪғᴛ ᴛᴏ Kᴀɪɴᴜᴡᴀ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀᴛɪᴏɴ Aʟʟᴀʜ ʏᴀ ƙᴀʀᴀ ʜᴀᴅᴀ ᴋᴀᴡᴜɴᴀɴ ᴍᴜ ᴀ ᴅᴜᴋ ɪɴᴅᴀ ᴍᴜᴋᴇ 🤗 *____________________________________* *🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼* *🇦SSOCIATION🤝🏻* ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation *_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻 https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association *____________________________________* 💓💓вє тнє gιяℓ уσυ ωαит тσ вє 💃 αи∂ иσт тнє gιяℓ тнαт ρєσρℓє ωαитѕ уσυ тσ вє 🙅🏻 ✍️ яυвву PⒶⒼⒺ 3️⃣ Ran Noor a ɓace ya kara sa wajan da Besty yake, ganin haka yasa Raudah tayi saurin bin bayan shi kar yaje ya yi aika_aika, yana isa ya nuna Dee da ɗan yatsa "Wannan shine warning na ƙarshe da zan maka Kamaludeen, babu kai ba Raudah, ka fita a hanyar ta, tunda ba auren ta za kayi ba,ka bari na zauna lafiya, in kuma ba haka ba wlh!wlh! wlh! Kaji rantsuwa uku ko?za kayi dana sanin sanina!! A yatsine Besty ya kalle shi, sai kuma ya taɓe baƙi ya ce; "Lallai Nuradden, kana wasa da lamarin besty, to ga ka ga Raudah nan, ita ya kamata ka kafa ma wannan dokar ba ni ba" ya ƙara sa fada yana dariyar shakiyanci Tsananin haushi ya sa Noor kasa ce ma sa komai, kawai ya juya ya fisgi mota ya bar wajan, ita kuwa Raudah da ta tsaya kallon ikon Allah bata iya cewa komai ba sai da Noor ya tafi sannan ta juyo ta kalli Besty, dariya ta tuntsure da shi cikin sigar zolaya ta ce "Kaiii, dama Noor ya zane ka, yau da na sha dariya yadda naga ya zuciyan nan" ta fada tana dariyar kamar wata taɓaɓɓiya, hakan da tayi ba ƙaramin tunzura Besty ya yi ba, kasa ce ma ta komai ya yi a zuciye shima ya bar wajan ya juya ya fara tafiya, ai da wani irin sauri Raudah ta ke bin shi tana mishi magiya da fadin "Haba better half wasa fa nake maka, so nake kawai na tsokane ka", ganin ya ƙi kulata ne yasa ta fashe da kuka wanda hakan ya sa shi tsayawa chak yana toshe kunne, ƙara haɗe girar sama da ƙasa ya yi kai kace an aiko masa Sarkin garin su ya mutu ne, "To Malama ai sai ki mana shiru ko kada ki cire min doddon kunne", ƙafa ta fara bubbugawa cike da shagwaba take faɗin " To to ni ba zan dena ihun ba kuma ma .... bai bari ta karasa maganar ba ya kamo hannu ta suka tsallaka titi, da kyar suka samu abin hawa zuwa shagon tela. Noor yana barin wajan su ya nufi babbar kasuwa, shagon da mahaifin Raudah yake sigar da takalma da yadin maza gami da shadodi ya nufa, a kofar shagon ya ga Abba zaune da abokan shi suna hira, cikin girmamawa da kunya ya tsuguna ya gaishe su , ganin yanayin shi yasa Abba tashi yace su shiga shago "Nuru me yake damun ka na ganka wani iri, ko baka da lafiya ne?" Abba ya tambaya yana tsare shi da ido "A'a Abba , kawai na kasa hakuri ne ma shi yasa na ga ba zan iya jira ba har sai nazo na fada maka abinda ya faru yanzu, saboda banji daɗin abin ba" "Subhanallah, Nuru faɗa min mene ne ya faru ɗan Allah" "Abba dama ba wani abu bane so nake kawai ka ma Raudah magana akwai wani yaro sunan shi Kamaludeen tana ce masa Dee, to abokin ta ne, sam Abba bana son alaƙarsu kuma nasan da wuya idan kana da masaniyar suna tare, shi yasa nace bari na faɗa maka domin ayi wa tufkar hanci" cewar Noor yana kara russunar da kanshi ƙasa. Ran Abba ba ƙaramin baci ya yi ba kuma Noor ya kula da hakan , ƙara kwantar da murya ya yi "Abba ba wani abu bane fa kawai dai magana zaka ma ta" ya fadi haka ne ɗan ya ga Abba ya dauki abin da zafi dama yasan halin Alh Adamu mahaifin Raudah baya ɗaukar raini kuma mutum ne da yaƙe tsaye tsam akan iyalinsa, sa'annan baya magana biyu idan yace eh to eh ne haka idan yace a'a to fa a'a nan ne, shi ya sa mutane su ke ganin girman shi da kimar shi" Abba ya ce " Kar ka damu Nuru, ai kai da Raudah duk ɗaya ku ke a wajena, insha'Allah zata gane ƙuskuren ta, kayi hakuri, ina ga ma zan kira mahaifin ka, idan ya shigo ƙarshen satin nan mu zauna a saka ranar auren kawai hankali na zai fi kwanciya" "To shikenan Abba Allah ya ƙara girma" "Amen Nuru, Kai kuma Allah ya maka albarka" "Amen Abba" Ganin ba wanda ya ƙara cewa komai a cikin su yasa Noor tashi ya ma Abba sallama, ya koma office. Ko a cikin adaidaitar hira suke cike da nishadi, tabbas suna jin daɗin kasancewar su tare a lokuta da yawa, koda suka sauka Raudah ce ta biya kuɗin, kasancewar shi Dee ba wani kudi ne da shi ba, ɗalibi ne ya na ajin karshe a jami'ar ATBU Bauchi, jakar hannun Raudah ya karba ya riƙe har suka karasa shagon tela, kai idan ka gan su zaka ɗauka masoya ne, dama telan abokin Besty ne haka suka zauna suka sha hira sai wajan ƙarfe uku na rana suka bar shagon a tare suka tafi, sai da ya rakata har ƙofar gida sannan ya juya ya tafi yana ta wurgo mata kiss da hannu, wasu samarin anguwan ne da su ke zaune a saman dakali su ke gulmar Raudah ƙasa_ƙasa, kallon su Raudah ta yi ɗan tabbas taji me suke faɗa a kanta, harara ta galla musu ta yi shigewar ta cikin gida. Gidan su Raudah matsakaici ne dai_dai zaman mutum daya, akwai flowers wanda aka ƙawata gefe da gefe compound din gidan, sai rijiya da pampo duk a waje ɗaya, daga chan gefe wajan ƙarshen gidan a nan toilet yake, flat biyu ne a gidan sai daƙin tsakar gida da kitchen madaidaici, a gefen kitchen ɗin store ne da yawanci tarkacen su suke ajiye wa, ba za'a ce da gidan su Raudah gidan masu kudi ba, amma suna da rufin asiri ɗan ba abinda suke nema su rasa a wajan Mommy da Abba, kasancewar Abba ɗan kasuwa, Mommy kuma malamar makarantar primary'n gwamnati ce. Raudah ce ƴa ta farko a wajan Alh Adamu sai Mubasheer da ke binta, sai Salem sannan auta Arya, Raudah nada shekara ashirin, tana zuwa school of nursing, shi kuma Mubasheer shekarar shi 17 yana SS 3 , sai Saleem ɗan shekara goma sannan auta Arya mai shekara biyar ta na nursery three, suna samun kulawa da tarbiyya yadda ya kamata kasancewar mahaifin su da mahaifiyar su basa ɗaukar wargi, suna da wasa da dariya da yara amma kuma hakan baya hana su tsawatar musu idan su ka yi ba dai_dai ba.. Wajen ƙarfe takwas na dare a lokacin Raudah ta iddar da Sallah, tana zaune suna chart da Besty, sai ga Salem ya shigo dakin ta "Anty Abba yana kiran ƙi" Damm gaban ta ya faɗi na ce "na shiga uku Salem me nayi?" Dariya Saleem ya sheke da shi ya na tafa hannu tare da faɗin "Kaiii Anty!! Kinga yadda kika zaro ido kuwa, sai kace an ka ma kaza za'a yanƙa" yana fadar haka ya fita ya bar ma ta ɗakin, jiki a sanyaye ta tashi bayan ta kashe data ta ajiye wayar a kan daddimar salla ta fice, a hankali ta ke tafiya kamar wata munafuka, kasancewar ba wuta, a haka ta karasa falon Abba. Da sallama ta shiga, ganin Mommy a wajan yasa gabanta kara faɗuwa, gefe ta samu ta zauna ta raƙube tare da cewa "Sannu da dawowa Abba" "Ba abinda na kira ki kimin ba kenan" Abba ya fada a hasale, ya cigaba da faɗin "dan ubanki waye Kamaludeen?" Cikin In inaa Raudah ta ce "A...a Abba ɗan makarantar mu ne, tare mu ka gama secondary" ta karashe zancen baƙin ta na rawa Mommy ta ce "Makarantar ubanki, yanzu Raudah kaf a cikin ƙawayen ki mata ki tasa wacce za kiyi ƙawa da ita sai namiji? Kisa mahaifin ki yana ganin kamar da haɗin bakina?" "Mommy dan Allah kuyi hakuri" Abba ne ya tashi a fusace ɗan jin zuciyar shi yaƙe kamar zata fashe saboda baƙin ciki ya kalle ta ya ce "Raudah abota!! Abotar ma da namiji", girgiza kai ta shiga yi ganin Abba na matsowa da bulala yasa ta fara ja da baya tana kuka da faɗin ya yi hakuri baza ta ƙara ba, ai kuwa sai da ya zane ta tas, ko hakuri Mommy bata bayar ba a cewar ta ita ta jama ƙanta, sai da Abba ya gaji dan kan shi ya kyale ta. Tana ta shesheƙar kuka Abba ya ce; "Yimin shiru!! Ba zaki mayar da ni mutumin banza ba kuma wlh babu ke babu wannan yaron, Kada na sake ji ko ganin ku tare" Yana gama fadar haka ya yi shigewar shi ɗaki, Mommy ma ta bishi bata ko kalle inda Raudah take ba.. Dafe kirji Raudah tayi ɗan kalaman Abba sun razana ta, kuma suna ma ta yawo a kwakwalwa, tashi ta yi tsaye tare da faɗin Kaiii!!! Innaaa!!! Wallahi ba zai taba yiwuwa ba ace na rabu da Dee, munafukin da ya faɗa ma Abba a kan shi zan sauke... 😂😂Toh fa da alama Noor ya jama soyayyar shi Ku ci-gaba da bin alƙalamina ɗan jin yadda zata ƙaya... VOTE COMMENTS SHARE ✍️ BADAWEEYERH 💐💐S͆A͆N͆A͆D͆I͆N͆ B͆E͆S͆T͆Y͆ 💐💐 L͆a͆b͆a͆r͆i͆/R͆u͆b͆u͆t͆a͆w͆a͆✍️ R͆A͆B͆I͆'A͆T͆U͆ A͆H͆M͆A͆D͆ M͆U͆A͆'Z͆U͆ (R͆U͆B͆B͆Y͆) G͆a͆j͆e͆r͆e͆n͆ l͆a͆b͆a͆r͆i͆ (S͆h͆o͆r͆t͆ s͆t͆o͆r͆y͆) M͆y͆ w͆a͆t͆t͆p͆a͆d͆ l͆i͆n͆k͆👇🏻 https://www.wattpad.com/1190086089?utm_medium=link&utm_source=android&utm_content=share_published 💐💐💐💐💐💐💐💐 Dᴇᴅɪᴄᴀᴛᴇᴅ ᴛᴏ Mʏ ʟᴏᴠᴇʟʏ ᴍᴏᴍ (Hᴀᴊ Rᴜᴋᴀɪʏʏᴀ), Aʟʟᴀʜ ʏᴀ ƙᴀʀᴀ ᴍɪᴋɪ ʟᴀғɪʏᴀ ᴅᴀ ɴɪꜱᴀɴ ᴋᴡᴀɴᴀ ❤️❤️ Sᴘᴇᴄɪᴀʟ ɢɪғᴛ ᴛᴏ Kᴀɪɴᴜᴡᴀ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀᴛɪᴏɴ Aʟʟᴀʜ ʏᴀ ƙᴀʀᴀ ʜᴀᴅᴀ ᴋᴀᴡᴜɴᴀɴ ᴍᴜ ᴀ ᴅᴜᴋ ɪɴᴅᴀ ᴍᴜᴋᴇ 🤗 *____________________________________* *🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼* *🇦SSOCIATION🤝🏻* ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation *_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻 https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association *____________________________________* 💓💓 ∂σи'т ¢αяє fσя тнσѕє ωнσ αяє ιgиσяιиg уσυ ¢αяє fσя тнσѕє ωнσ αяє ιgиσяιиg σтнєяѕ fσя уσυ ✍️ яυвву💓 PⒶⒼⒺ 4️⃣ Da kyar Raudah ta iya koma wa ɗakin ta, ko Arya da ta ke ma ta magana a falon Mommy bata kula ba, so kawai ta ke ta ƙira Noor ta mai rashin mutunci, ɗan kawai yaga tana son shi , shine zai fara hadata da iyayen ta, har ya sa Abba ya ɗake ta, to ba zata saɓu ba bindiga a ruwa. Haka dai ta yi ta kullawa da warware wa har ta isa ɗakin, ko kallon gaban ta ba ta yi ba,tsabar takaici da baƙin ciki, waya ta dauka ta na kiran Noor amma har wayar ta tsinƙe bai ɗaga ba, hakan ba ƙaramin ƙular da ita ya kuma yi ba, bata gaji ba ta ci-gaba da kira amma still bai dauƙa ba, sai da ta ƙira shi wajan sau goma sannan ta hakura, number Besty ta ƙira ringing biyu ya daga "Hello sarauniyar ya kike?" Jin tana shesheƙar kuka ne ya hana shi ƙara sa maganar da ya yi niyya tuni ya rikice da faɗin "Haba baby what's wrong kike kuka? Ko wani abu na miƙi? Dan Allah ki fada min" ganin Raudah taƙi dena kukan yasa Dee fadin "gani nan zuwa gidan tunda ba za ki faɗa min ba" Da sauri Raudah ta ce ,"a'a ba sai ka zo ba zan faɗa maka" Duk yadda suka yi da Abba Raudah ta faɗa ma Dee, ajiyar zuciya ya sauke yana faɗin " Wlh Raudah ban da kin nace da rabuwa ki ka yi da Nuru, mutum sai ɓakar zuciya da baƙin hali kamar kafuran farko, Ni wlh taurin kan shi ne ma na ke jiye miƙi" "To ya ka ke so nayi ne Besty" ni fa ba wannan bane damuwa ta, babbar damuwa ta maganar da Abba ya min ne, cewa fa ya yi wai bani ba kai, kuma kafi kowa sanin bazan iya rabuwa da kai ba" ta ci-gaba da shesheƙar kuka "To kiyi hakuri ki dena kukan mu yi magana ta fahimta, idan ina jin kukan ki har jijiyar ƙaina tashi ta ke yi" da kyar da kalamai masu ɗadi da ratsa zuciya Besty ya rarrashi Raudah ta dena kukan, "Ko kefa" ya faɗa cike da tsokana Murmushi ta sakar mai sauti kamar ta na tare da shi, dama tasan shi ne zai saka ta farin ciki, ɗan ba shi da burin da ya wuce hakan a ko da yaushe, in ta tsinci kan ta a damuwa, to wannan fa aikin Besty ne ya yi ƙoƙarin samar mata da farin ciki komai wahalar shi, shi yasa Raudah ba ta shayin fada mai ko mene ne ya same ta ko ya ke damun ta, abokin shawarar ta ne babu abinda ta ke iya boye mishi, ta riga ta sabar ma da ƙanta fada ma Besty damuwar ta ko farin cikin ta... "Kiyi hakuri kin ji Raudah!! insha'Allah ba zamu rabu ba, haba ni da ke ba rabuwa sai dai mutuwa ce za ta raba mu, muna nan tare har da ke har abada" Besty ya faɗa cike da son kwantar ma ta da hankali Ajiyar zuciya Raudah ta sauke, "Nima haka na ke fata my Better half, Allah ya ƙauda idon maƙiya" "Kaiii!! Raudah Abba'n ne maƙiya?lallai baki da hankali ashe" ya faɗa cike da fushi har ya na hura hanci kamar tana gaban shi Da sauri Raudah ta ce "a'a bestyna nifa ba da Abba na ke ba, da Noor na ke, ɗan nasan shine ya kai gulma wajan Abba kuma wallahi sai na mishi magana zai gane ya sa an dake Ni" Raudah ta faɗa cike da tsiwa Dariya Besty ya kwashe da shi, sai da ya yi mai isar shi sannan ya ce " Kar ki yadda ki mai magana, ki saƙa shakku a zuciyar shi, ko a fuska kar ki nuna mai anyi wannan maganar hakan zai rage mai ƙwarin gwiwar ƙara tarar Abba da irin wannan maganar koda wataran zai ƙara ganin mu tare, sannan maganar haɗuwa kuma zan san yadda za'a yi mu dinga haduwa ba a layin ku ba" Murmushi Raudah ta sake ɗan ta ji daɗin wannan shawarar, kuma ta gamsu da hakan, hira suka ci-gaba da yi har Arya ta shigo ta, dangwarar ma ta da book ɗin assignment ɗin ta tayi ta ce "Anty!! Mommy ta ce na kawo ki koya min kuma ta ce kar ki yadda ki dake ni" Sakkowa Raudah ta yi daga kan gadon ta fara koya mata assignment ɗin ba tare da ta ce ma ta komai ba kuma hakan bai sa ta yanke wayar ba... Misalin ƙarfe takwas da rabi Adnan ya iso kofar gidan su Fadeelah, sauka ya yi a kan mashin ɗin shi, kasancewar layin nasu shiru ne, ba shi da hayaniya sossai, karasa wa ya yi wajan wata barandar da ake kiwon shanu, akwai wani waje ta gefen barandar kamar lungu a inda ake ajiye abincin shanun, wayar shi ya zaro a aljihhu ya kira Fadeelah ya sanar ma ta ya iso. Bayan minti biyar sai ga Fadeelah ta fito daga gida da wani zumbulelen hijabi, taku taƙe cike da yanga dan dama ita akwai ƙaudi, iyayi, rawar ƙai, uwa uba kuma yanga, Idanu ya tsira ma ta har sai da ta ce "matsa mana na shiga ƙar wani ya ganni" ai da sauri ya matsa mata ta shige cikin lungun, tana karasa cire hijabin da ke jikin ta, daga ita sai pant da bra, ganin haka ya sanya Adnan sakin murmushi, janyo ta ya yi, ya fara aika mata da sakkoni, sun yi nisa cikin jin dadin su kawai sai ganin hasken wuta suka yi yana nufo wajan da suke da alama za'a shiga wajan abincin shanun ne... Toh fa reader's, 🤣😂 wannan shi ake kira da dirimm babban motsi!!! Yau fa ƙaryar Adnan da Fadeelah ta ƙare dan nasan zasu daku a wajan nan... VOTE COMMENTS SHARE ✍️ BADAWEEYERH 💐💐S͆A͆N͆A͆D͆I͆N͆ B͆E͆S͆T͆Y͆ 💐💐 L͆a͆b͆a͆r͆i͆/R͆u͆b͆u͆t͆a͆w͆a͆✍️ R͆A͆B͆I͆'A͆T͆U͆ A͆H͆M͆A͆D͆ M͆U͆A͆'Z͆U͆ (R͆U͆B͆B͆Y͆) G͆a͆j͆e͆r͆e͆n͆ l͆a͆b͆a͆r͆i͆ (S͆h͆o͆r͆t͆ s͆t͆o͆r͆y͆) M͆y͆ w͆a͆t͆t͆p͆a͆d͆ l͆i͆n͆k͆👇🏻 https://www.wattpad.com/1190086089?utm_medium=link&utm_source=android&utm_content=share_published 💐💐💐💐💐💐💐💐 Dᴇᴅɪᴄᴀᴛᴇᴅ ᴛᴏ Mʏ ʟᴏᴠᴇʟʏ ᴍᴏᴍ (Hᴀᴊ Rᴜᴋᴀɪʏʏᴀ), Aʟʟᴀʜ ʏᴀ ƙᴀʀᴀ ᴍɪᴋɪ ʟᴀғɪʏᴀ ᴅᴀ ɴɪꜱᴀɴ ᴋᴡᴀɴᴀ ❤️❤️ Sᴘᴇᴄɪᴀʟ ɢɪғᴛ ᴛᴏ Kᴀɪɴᴜᴡᴀ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀᴛɪᴏɴ Aʟʟᴀʜ ʏᴀ ƙᴀʀᴀ ʜᴀᴅᴀ ᴋᴀᴡᴜɴᴀɴ ᴍᴜ ᴀ ᴅᴜᴋ ɪɴᴅᴀ ᴍᴜᴋᴇ 🤗 *____________________________________* *🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼* *🇦SSOCIATION🤝🏻* ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation *_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻 https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association *____________________________________* Nα rαѕα dα wαccє írín kαlmα zαnчí αmfαní wαjαn nunα fαrín cíkí nα α gαrє ku mαѕσчα líttαfín ѕαnαdín Bєѕtч, ѕhαrhín ku nα ѕαkα ní níѕhαdí, nα gσdє ѕσѕαí, Allαh чα вαr mu tαrє Bαєѕtíєє'ѕ Dínα🤪 яєѕρє¢т fσя тнσѕє ωнσ ∂єѕєяνє ιт,иσт fσя тнσѕє ωнσ ∂ємαи∂ ιт 💓💓 яυвву✍️ PⒶⒼⒺ 5️⃣ Da sauri Fadeelah ta mayar da hijabin ta jiƙin ta na ƙyarma, gani haka shima Adnan ya rikice, dagan ganin hasken ya kusa ƙaraso wa wajan da suke, yana daga da karyo kwanar lungun wayar shi tayi ringing Tsaya wa Mallam Sule ya yi yana amsa ƙiran da aka mishi a waya, hakan ya bama Fadeelah damar fita da sauri ta bayan lungun kasancewar aƙwai maɓoya ta baya, Ganin haka yasa Adnan matsowa daga wajan lungun shima ya dawo dai_dai rumfar shanun, haska shi Baba Sale ya yi ganin yana zufa kamar sabon ɓarawo yasa ya kasa yadda da shi, gaba ɗaya Adnan ya ruɗe da ganin irin kallon da Baba Sale yaƙe mishi. "Saurayi me ka ke yi a nan? Baba Sale ya tambaye shi Cikin in ina da rawar murya Adnan ya ce; "Am im, da da dama amm ina jiran wani ne" Ƙara haska shi Baba Sale ya yi sannan ya ce " yaro alamun ka sun nuna kamar baka da gaskiya, kodai irin barayin yaran nan ne kai"? Da sauri Adnan ya girgiza mai ƙai yana faɗin "A'a Baba wlh ka yadda da ni, ni ba mugu bane wallahi kaji na rantse maka" Goro Baba Sale ya ɓantara tare da cewa "Ahaf!! Yoo mugu yana da kama ne? Ai da yana da kama da matsalar tsaro ta ragu a ƙasar mu" Ganin maganar ba zata ƙare ba ne ya sa Adnan ciro dari biyar a aljihu ya miƙa ma Baba Sale, Yana murmushi ya ce "Ga wannan ba yawa Baba, a siya goro" "Chabdi jam!! Niii na karɓi kuɗi a hannun ka? A'a ba haka nake ba, haka kurum ban san ka ba, ban taɓa ganin ka ba, kai ko me kama da ƙai ban taɓa gani ba, ai hakan ba zai yiwu ba" Baba Sale na gama faɗan haka ya shige cikin lungu ɗan dama ya manta bai saƙa ma shanun da yake kiwo abinci band shine ya fito sai kuma babban ɗan shi ya kira shi a waya. Adnan na ganin shigar Baba Sale lungun ya sauke ajiyar zuciya, bai ko tsaya ƙara neman Fadeelah ba ya yi tafiyar shi. Noor yana kwance a ɗakin shi da daddare, babu abinda yake yi sai tunanin halayen Raudah, shi dai yasan yana son ta so na haƙika, kuma itama ya tabbatar tana son shi, to amma wannan yaron da yake barazana da farin cikin shi yana kawo masa tsaiko da ruɗani a cikin soyayyar shi da Raudah, dole ne fa ya nemi mafita tun ƙafin dare ya mishi, wata zuciyar ce ta ce mishi; "Ai kuna yin aure zata dena tunda a lokacin ta zama mallakin ka gaba ɗaya, kaga sai yadda kayi da ita" Da wannan shawara da kwarin gwiwa da ya samu daga zuciyar shi ya saka hankalin shi kwanciya, ya ci-gaba da ayyukan shi a laptop hankali kwance... Sai da Raudah da Besty suka kwashe wajan awa uku suna chatting tare da alƙawarin za su haɗu washegari a shagon aɓokin shi tela, sannan suka kwanta bacci kowa zuciyar shi cike da farin ciki... Da safe tun da asuba Raudah ta tashi daga bacci, bata sake koma wa ba, kasancewar yau tasan Mommy na fushi da ita shiyasa ta fara ayyukan gidan da wuri, karfe takwas ta gama komai har Arya da saleem sun tafi school, Abba ya tafi kasuwa, Mommy ce kaɗai ta rage bata fita ba kuma ita ma yanzu take shirin fita. Mommy na tafiya maƙaranta Raudah ma ta shirya ta fita, dan tun wuri suka tsara haɗuwar su da besty kafin time ɗin da su Mommy za su dawo daga school tasan har ta dawo ta gama abincin rana tunda tasan ko mutuwa za tayi Mommy ba zata barta ta fita yau ba. A shagon Mansur tela suka haɗu, dan Besty ne ya buɗe shagon ma, Mansoor ɗin bai fito ba, sun shafe wajan awa 4 a shagon ba tare da sun farga ba, hirar su suka sha tamkar kar su rabu, tana duba agogon wayar ta taga ɗaya saura, ai da hanzari ta fara saka takalmi, cikin rudewa take fadin "Na shiga uku na lalace, besty Wallahi nasan Mommy ta dawo kuma zata ga gidan ba kowa" ta karashe zancen tamkar ta fasa kuka, "Ki kwantar da hankalin ki, insha'Allah ba ta dawo ba, zo muje na nema miƙi kake napep", Besty ya fada tare da kamo hannun ta, a haka suka jera har baƙin titi, hannun su na manne da juna, juyawar da Raudah za tayi ta hango Abba yana nufo wajan su, ai bata san lokacin da ta yi ihu ta hanƙada Besty ba, sannan ta kwasa a guje, ganin ta ruga da gudu shima Besty yabi bayan ta yana gudu tare da kiran sunan ta , ba tare da ya san gudun me take ba, dan shi bai san Abba ba sai a hoto kuma bai gane shi ba yanzu... Yau za'a sha gudun famfalaƙi, ga Raudah, ga Besty ga kuma Abba 🤣🤣 VOTE COMMENTS SHARE ✍️ BADAWEEYERH 💐💐S͆A͆N͆A͆D͆I͆N͆ B͆E͆S͆T͆Y͆ 💐💐 L͆a͆b͆a͆r͆i͆/R͆u͆b͆u͆t͆a͆w͆a͆✍️ R͆A͆B͆I͆'A͆T͆U͆ A͆H͆M͆A͆D͆ M͆U͆A͆'Z͆U͆ (R͆U͆B͆B͆Y͆) G͆a͆j͆e͆r͆e͆n͆ l͆a͆b͆a͆r͆i͆ (S͆h͆o͆r͆t͆ s͆t͆o͆r͆y͆) M͆y͆ w͆a͆t͆t͆p͆a͆d͆ l͆i͆n͆k͆👇🏻 https://www.wattpad.com/1190086089?utm_medium=link&utm_source=android&utm_content=share_published 💐💐💐💐💐💐💐💐 Dᴇᴅɪᴄᴀᴛᴇᴅ ᴛᴏ Mʏ ʟᴏᴠᴇʟʏ ᴍᴏᴍ (Hᴀᴊ Rᴜᴋᴀɪʏʏᴀ), Aʟʟᴀʜ ʏᴀ ƙᴀʀᴀ ᴍɪᴋɪ ʟᴀғɪʏᴀ ᴅᴀ ɴɪꜱᴀɴ ᴋᴡᴀɴᴀ ❤️❤️ Sᴘᴇᴄɪᴀʟ ɢɪғᴛ ᴛᴏ Kᴀɪɴᴜᴡᴀ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀᴛɪᴏɴ Aʟʟᴀʜ ʏᴀ ƙᴀʀᴀ ʜᴀᴅᴀ ᴋᴀᴡᴜɴᴀɴ ᴍᴜ ᴀ ᴅᴜᴋ ɪɴᴅᴀ ᴍᴜᴋᴇ 🤗 *____________________________________* *🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼* *🇦SSOCIATION🤝🏻* ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation *_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻 https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association *____________________________________* Ku yi hakuri da ni d'an Allah , biki ne ya sha kaina shi ya sa ku ka jini shiru, amma kuna raina a koda yaushe... Luv U oll... 💓💓∂σи'т ωαѕтє уσυя тιмє ωιтн ρєσρℓє ωнσ ѕєєк αттєитισи тнєу αяє נυѕт вσяє∂ ωιтн тнєяє ℓιfє. ✍️ яυвву PⒶⒼⒺ 6️⃣ Ganin irin gudun da su raudah su ke yi ne ya sa Abba ya koma wajan motar shi, shiga ya yi shima ya tayar a dari ya bar wajan, ɗan yana da tabbacin gida Raudah za ta je . Ganin Raudah ta ƙi dena gudun ne ya sa Besty fara yin ihun a tare_ a tare ɗan duk a na shi tunanin aljannun ta ne su ka tashi, ganin babu wanda ya yi yunkurin tare tan ne ya saka shi neman waje ya zauna ɗan shi dai Allah ya gani ba zai iya gudu da aljannu ba, koma mene ne ya je gidan su kawai. Abba yana barin wajan gida ya nufa, dama yazo bada sako ne, saukar shi kenan a mota ya ga Raudah da wannan yaron da take cewa ɗan ajin su ne, Abin da ya ƙara mishi takaici shine ganin hannun su manne da juna. Raudah kam duk nisan wajan nan bata gani ba sai da tayi rabin tafiya, gajiyar da ta yi ne ya sa ta tsugunna a gefen titi tana kuka, wayar ta ce ta ke ta ringing amma ba ta da nutsuwar duba wa balle ta iya ɗauka, yanke shawarar koma wa gida ta yi, d'an haka da sauri ta tsayar da me keke napep, da kyar ta iya faɗa mai inda zata je. Ko a cikin keken ma babu abinda Raudah ta ke yi sai kuka, shi dai mai keke ya tsaya yana kallon ikon Allah, ganin budurwa santalelliya son kowa ƙin wanda ya rasa, amma ta zauna tana zubar da hawaye, koma me yake damun ki Allah ya yaye miki yan'mata, ya fada a zuciyar shi. Raudah kam ba ta ma san ya na yi ba, gaba ɗaya hankalin ta baya jikin ta, addu'a ta ke yi Allah ya sa Abba ya koma kasuwa, babban tashin hankalin ta ma Mommy ce, in dai Mommy ta dawo ba ta same ta a gidan ba to ta kaɗe, ɗan yau ta san mai ƙwatar ta a hannun iyayen ta sai Allah, ƙara sautin kukan ta yi, ba ta biyo ta titi ba, sai ta saka mai adaidaitar bi ta saman layin su, hakan ne ya sa bata ga Abba ba, d'an shi har ya zai yi kwanar shiga gida wani abokin shi ya tare shi, akan wata muhimmiyar magana da za su yi, hakan ya sa Abba ya shiga gidan abokin d'an su tattauna, amma gaba ɗaya hankalin shi na kan Raudah. A dai_dai kofar gidan su, Raudah ta ce mai adaidaitar ya sauke ta, sallamar shi ta yi, duk da gaban ta na dukan tara_tara hakan bai hana ta tunkarar gidan ba kai tsaye, da sanɗa ta shiga da saleem ta fara cin karo a bakin pampo ya na wanke hannu, da sauri ta karasa wajan da ya ke ta na tambayar shi "Saleem, Mommy ta dawo?" Bai amsa ma ta ba illa ɗaga ma ta kai da ya yi alamar eh "Na shiga uku Saleem, ta riga ku dawowa" Raudah ta ƙara tambayar shi, duk ta bi ta rikice, har yanzu jikin ta bai bar rawa ba, kasa motsi ta yi jin muryar Mommy kamar daga sama ta na faɗin "Daga gidan uban wa ki ke" Tsaya wa ta yi, ta gaza furta komai sai rawar jiki, bata iya bama Mommy amsa ba d'an ta san ko giyar wake ta sha ba zata iya ma Mommy ƙarya ba, ganin ta yi shiru ne ya sa Mommy ta fara nufo wajan da ta ke ai da sauri bakin ta ya fara magana "Mommy kar ki ƙara so wallahi shagon tela na je, kira na ya yi wai bai ga kayan da na kai ba, kuma ban dade da fita a gidan ba", Ganin Mommy ta ki ce mata uffan ne ya sa ta ci-gaba da rantaɓa bayanai kamar an kunna rediyo kaduna "Wallahi Mommy kuma da na je sai na samu ya fita,shi ne na kira shi ya ce na jira shi, shi yasa na dade" Wata uwar tsawa mai sa yan hanji su kaɗa Mommy ta ma Raudah "Dan uban ki ni sa'ar ki ce? Ni za ki kalla ki shirya ma karya Raudah? Tun sha daya da rabi na dawo gidan nan ba kya nan, kuma na kira wayar ki baki daga ba, to tukunna ma a ina Abba'n ku ya ganki?" Ai tuni Raudah ta ji wani gudawa ya taho ma ta, jin ashe ma daddy ya dawo gidan, to amma ai ba ta ga motar shi s kofar gida ba, ƙila ya ajiye ne a kasuwa ya zo a mashin, ganin gudawar da ta ke rike wa na ƙoƙarin zubo ma ta a wando ne ya sa ta suri butar da ke kusa da Saleem wanda ya tsaya kallon su, ai Raudah ba ta tsaya a ko ina ba sai saman toilet, me Saleem zai yi in ba dariya ba, ana cikin haka sai ga Abba ya shigo gidan, a fusace ya ce ma Mommy "Mommy'n yara Raudah'n ta dawo kuwa?" Juyawa Mommy ta yi ta na ma Abba nuni da toilet, sannan ta ce "Abba ta dawo ina mata magana ta shiga bayi, cemin tayi wai daga shagon tela ta ke", Mommy ta karashe maganar cike da takaici dan ita fa halayen Raudah yanzu sun fara ba ta tsoro". Abba ya ciro wayar shi yana dannawa, sako ya tura sannan ya dago ya kalli Mommy, ya ce " Kwarai daga shagon tela ta ke, amma ita da wannan ɗan iskan yaron da na raba ta da shi jiya, saboda ta nu na min ban isa ba shine ta je wajan shi har su na rike ma juna hannu" "Innalillahi wa inna ilaihir rajiun!! Alh!! rike hannu fa? To Allah ne kaɗai ya san me yaron nan yake aikatawa da Raudah tunda a idon duniya ma sun iya riƙe ma juna hannu, to wa ya san me suke a ɓoye? Tin da dai ba'a shedar yaran yanzu" kana ganin Mommy ka ga wacce hankalin ta ya tashi, to ba dole ba ace an ga y'ar ka da wani hannun su manne da juna... Ƙasa hakuri Mommy ta yi, dama Mommy ba sai zuciya ba, dan ba ta iya ɓacin rai ba, hanyar toilet ta nufa a zuciye, cikin ɓacin rai ta fara buga ƙofar, d'an Raudah da ta shiga sakata ta sa ka ta ciki, bugawa Mommy ta ke da ƙarfi tana ce wa "Ki bude ki fito, yau sai kin faɗa min abinda kuke yi ke da wannan shegen yaron da ku ka ƙasa rabuwa da juna" Jin Mommy na buga kofa kamar zata balla ne ya ƙara hautsina cikin Raudah, ai kuwa tana gudawar ta kara taho wa kamar pampo, ta na yi tana rusa ihu tare da magiya... 😂😂 Fan's ɗin Raudah yau fa besty ya ja ma mutuniyar ku gudawa, da alama sai Mommy ta ɓalla ƙofar za ta bude, Ni dai na tafi kiran besty mu kai agaji gwanda mu haɗu mu rarrashi Abba da Mommy kar su dakan ma na matar besty.... VOTE COMMENTS SHARE ✍️ BADAWEEYERH 💐💐S͆A͆N͆A͆D͆I͆N͆ B͆E͆S͆T͆Y͆ 💐💐 L͆a͆b͆a͆r͆i͆/R͆u͆b͆u͆t͆a͆w͆a͆✍️ R͆A͆B͆I͆'A͆T͆U͆ A͆H͆M͆A͆D͆ M͆U͆A͆'Z͆U͆ (R͆U͆B͆B͆Y͆) G͆a͆j͆e͆r͆e͆n͆ l͆a͆b͆a͆r͆i͆ (S͆h͆o͆r͆t͆ s͆t͆o͆r͆y͆) M͆y͆ w͆a͆t͆t͆p͆a͆d͆ l͆i͆n͆k͆👇🏻 https://www.wattpad.com/1190086089?utm_medium=link&utm_source=android&utm_content=share_published 💐💐💐💐💐💐💐💐 Dᴇᴅɪᴄᴀᴛᴇᴅ ᴛᴏ Mʏ ʟᴏᴠᴇʟʏ ᴍᴏᴍ (Hᴀᴊ Rᴜᴋᴀɪʏʏᴀ), Aʟʟᴀʜ ʏᴀ ƙᴀʀᴀ ᴍɪᴋɪ ʟᴀғɪʏᴀ ᴅᴀ ɴɪꜱᴀɴ ᴋᴡᴀɴᴀ ❤️❤️ Sᴘᴇᴄɪᴀʟ ɢɪғᴛ ᴛᴏ Kᴀɪɴᴜᴡᴀ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀᴛɪᴏɴ Aʟʟᴀʜ ʏᴀ ƙᴀʀᴀ ʜᴀᴅᴀ ᴋᴀᴡᴜɴᴀɴ ᴍᴜ ᴀ ᴅᴜᴋ ɪɴᴅᴀ ᴍᴜᴋᴇ 🤗 *____________________________________* *🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼* *🇦SSOCIATION🤝🏻* ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation *_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻 https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association *____________________________________* 💓💓ѕмιℓє ιи fяσит σf ρєσρℓє ωнσ нαтє уσυ… υя нαρριиєѕѕ кιℓℓѕ тнєм… ✍️ яυвву PⒶⒼⒺ 7️⃣ Abba ne ya umarci Mommy da ta bar Raudah ta ƙara sa uzurin ta, tunda ai dole zata fito a bayan gidan komai daɗewa, badan Mommy ta so ba ta shige cikin gida ba tare da ta ce uffan ba. Bin bayan ta Abba ya yi da kallo mai ma'anoni daban_daban, shi dai yana jin daɗin yadda Mommy ta ke tsaye a kan tarbiyyar gidansa, a kullum yana ƙara gode ma Allah da ya ba shi mata ta gari, ba kamar wasu matan ba da za kaga suna goyon bayan ya'yan su idan sun yi laifi, wasu iyayen ma idan an ma yaran su faɗa ko an hukunta su, koda kuwa mahaifin su ne ko yayun su, kai koda wani ne daban sai kaga sun ji haushi ko su nuna ran su bai so ba, wasu marasa hakuri ma sai sun mayar da martani. Saleem dake tsaye har yanzu shima ya bi Abba da Mommy ciki ɗan daga shi sai Arya ne a gidan Mubasheer bai dawo ba, su sai karfe biyu da rabi suke tashi saboda lesson ɗin da suke tsayawa yi, tunda a shekarar nan zai zana SSCE. Dee kam gajiya ya yi da zama a baƙin titi, gashi ya gaji sosai, shi anya ma zai iya zuwa gidan su Raudah yanzu? tashi ya yi jiki a sanyaye ya koma shago da zummar ya kwanta, in yaso zuwa yamma sai ya je gidan su Raudah. Mahifin Noor na office ya ci karo da sakon Abba'n Raudah, hakan ne ya sa ya yanke shawarar kiran shi a waya, domin maganar ta shi mai muhimmanci ce, amma bai daga ba, ganin ya kira sau biyu bai dauƙa ba yasa ya hakura, ya san idan yaga ƙiran shi zai biyo baya, yanke shawarar kiran Noor ya yi, ringing biyu ya ɗaga wayar "Assalamu alaikum Baba, Barka da rana" Daga ɓangaren mahaifin Noor ya amsa cike da jin daɗi, yana son ɗan shi, kasancewar Noor yana da biyayya da sauƙin kai, cikin farin ciki Baba ya ce "Son kana lafiya?". "Lafiya lau alhamdulillah Baba, ya aiki?". "To Alhamdulillah, komai na tafiya yadda ake so, amm...dama saƙo ne naga sirikin ka, ya turo min aƙan maganar bikin ku, to amma dai maganar ba ta waya bace, zan shigo a weekend ɗin nan insha'Allah, kai dai ka kasance cikin shiri". Duk da Noor bai fahimci maganar ba, sai kawai ya sosa ƙeya tamkar yana gaban Baba, cike da ƙunya ya ce "Allah ya dawo da kai cikin koshin lafiya da aminci Baba". Sosai mahaifin Noor ya ji daɗin wannan addu'ar da gudan jinin shi ya yi, murmushi ya yi cike da farin ciki ya ke faɗin "Amen Nuradden, Allah ya yi maka albarka, ka gaishe min da yan gidan , ko da yake kafin nan ma zan kira mahaifiyar taka". "To shikenan Abba". Noor ya amsa cikin ƙwantar da kai da nuna tsan_tsar biyayya ga Baban shi, ko wannen su ya ajiye waya cike da kewar junan su, ɗan akwai soyayya da shaƙuwa mai ƙarfi tsakanin iyalan Alh Mukhtar Baba, kan su a haɗe ya ke. Nuradden shine ɗan su na fari sai Khadijah dake bin shi, sannan Hauwa'u ɗuk matan suna da aure Noor ne kaɗai ya rage ( shima kuma zai amarce da Raudah'n Besty🤣), mahaifiyar su, Mama Hajara mace ce mai dattako da mutunci, tana mutunta kowa, amma fa bata iya ɓoye soyayyar da take wa yaran ta a ko'ina, bata son Abinda zai taba su, duk da haka ba ta lalata yaran ba, ta basu tarbiyya dai_dai gwargwado, ɗuk gidan Alh Mukhtar Baba kowa yafi son Noor, ko dan kasancewar shi kaɗai ne namiji, shi yasa ake ma bikin shi tanadi na ban mamaki... Sai da Raudah ta share wajan mintuna arba'in a toilet sannan ta iya fitowa, a hankali ta ke taƙawa tamkar wacce ta yi nakudar yan uku, Arya ce kaɗai a kofar kitchen da alama wani abin ta ke yi, ɗauke kai ta yi daga kallon Arya ta nufi hanyar shiga parlour'n su, a baƙin ƙofa ta ja ta tsaya jin Muryar Abba da Mommy suna magana "Tabdijam! Yanzu Abba bai fita ba?, Innalillahi wa inna ilaihir rajiun, wallahi na san yau ba mai ƙwata na a gidan nan". Raudah ta faɗa, wasu hawayen baƙin ciki na zubowa a Idanun ta, jin an rangaɗa sallama ne ya sa ta juyo da sauri ɗan ganin waye Ai kuwa da gudu ta karasa shigewa cikin parlour'n tamkar wacce ta ga mala'ikan mutuwa, ganin wanda Abba ya kira, ta san yau za taci ubanta..... VOTE COMMENTS SHARE ✍️ BADAWEEYERH 💐💐S͆A͆N͆A͆D͆I͆N͆ B͆E͆S͆T͆Y͆ 💐💐 L͆a͆b͆a͆r͆i͆/R͆u͆b͆u͆t͆a͆w͆a͆✍️ R͆A͆B͆I͆'A͆T͆U͆ A͆H͆M͆A͆D͆ M͆U͆A͆'Z͆U͆ (R͆U͆B͆B͆Y͆) G͆a͆j͆e͆r͆e͆n͆ l͆a͆b͆a͆r͆i͆ (S͆h͆o͆r͆t͆ s͆t͆o͆r͆y͆) M͆y͆ w͆a͆t͆t͆p͆a͆d͆ l͆i͆n͆k͆👇🏻 https://www.wattpad.com/1190086089?utm_medium=link&utm_source=android&utm_content=share_published 💐💐💐💐💐💐💐💐 Dᴇᴅɪᴄᴀᴛᴇᴅ ᴛᴏ Mʏ ʟᴏᴠᴇʟʏ ᴍᴏᴍ (Hᴀᴊ Rᴜᴋᴀɪʏʏᴀ), Aʟʟᴀʜ ʏᴀ ƙᴀʀᴀ ᴍɪᴋɪ ʟᴀғɪʏᴀ ᴅᴀ ɴɪꜱᴀɴ ᴋᴡᴀɴᴀ ❤️❤️ Sᴘᴇᴄɪᴀʟ ɢɪғᴛ ᴛᴏ Kᴀɪɴᴜᴡᴀ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀᴛɪᴏɴ Aʟʟᴀʜ ʏᴀ ƙᴀʀᴀ ʜᴀᴅᴀ ᴋᴀᴡᴜɴᴀɴ ᴍᴜ ᴀ ᴅᴜᴋ ɪɴᴅᴀ ᴍᴜᴋᴇ 🤗 *____________________________________* *🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼* *🇦SSOCIATION🤝🏻* ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation *_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻 https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association *____________________________________* Ina godiya sosai da addu'oin ku a gare ni bisa rashin lafiyar da nayi na kwana biyu, Allah ya saka muku da alkhairi, ina son ku sossai Sanadin Besty Fan's 1&2, Allah ya bar zumunci 👍 вєαυту fα∂єѕ αfтєя тιмє, вυт ρєяѕσиαℓιту ιѕ fσяєνєя! ✍️ яυвву PⒶⒼⒺ 8️⃣ Ko da Raudah ta shiga parlour'n ma rasa inda zata nufa ta yi, gaba ɗaya ta rikice, cikin ta ne ya kuma kaɗawa ganin Mommy da Abba na bin ta da wani irin kallo, Allah ya so ta ma a iya kaɗawar ya tsaya. Sallamar shi ce ta kuma ratsa dodon kunnen ta, ya na neman izinin shigowa cikin parlour'n, ai bata san lokacin da ta karasa gaban Abba ba, ƙafafuwan Abba ta kamo tana kuka tamkar ranta zai fita, hakan ya yi dai-dai da karasowar shi cikin parlour'n yana faɗin "Yaya ai da tura ta kayi chan gidan ma ba sai na zo ba" Murmushi Abba ya yi ya ce "A'a Babangida, gata a nan ai ba inda ta isa ta je, naga ni ta raina ni ne shi yasa na ƙira ka, jiya-jiyan nan na gama mata kashedi a kan wannan ɗan iskan yaron, dake ban isa da ita ba shine ko awa ashirin da hudu ba a rufa ba ta tsallake maganar" Kai da ganin yadda Abba yake magana kasan ran shi ya ɓaci sosai, yasan idan yace zai kuma mata hukunci to zai loosing control ɗin shi ne a kanta, baya son magana sau biyu, amma Raudah na neman chanja shi daga tsarin shi. Babangida ne ya kalli Raudah da har yanzu jikin ta bai bar mazari ba , ya daka ma ta tsawa!! "Za ki zo ne ko sai na zo wajan dan ubanki?". Da rarrafe ta ƙara sa wajan da ya ke, tana gunjin kuka, hannaye biyu ta haɗa alamar roko cikin rawar murya ta ke faɗin "Uncle dan girman Allah kar ka dake ni, wallahi ba zan kara ba na maka alkawari, kuma idan na kara..." Ai uncle bai bari ta ƙara sa maganar ba ya buge baƙin ta da bayan hannun shi, kan kace kwabo kuwa bakin Raudah ya fashe sai jini da ke zuba, hannu ta sa ta tare jinin tana kuka, belt ɗin jikin shi ya kunce, ganin haka Raudah ta ƙwalla uban ihu tana ƙara bashi haƙuri, nufar in da Mommy ta ke zaune ta yi, "Mommy wallahi zai kashe ni, Mommy dan Allah ki bashi haƙuri ba zan sa ke ba, Please Mommy". Duk da Mommy ta tausaya ma ta ganin irin kukan da ta ke yi, amma bata nuna tausayin na ta a fili ba, saboda ko ba komai gidan miji za su kai Raudah, kuma ba zata so ta bar musu abin kunya ba, ko ta janyo musu magana a gari tunda har sun iya riƙe ma juna hannu da namijin da ba muharramin ta ba, to gwanda su yi wa tufkar hanci tun wuri, to idan Raudah ba ta dena waɗannan halayen da ta tsiro da su ba ai kuma ba'a san a inda abin zai ƙare ba, tashi Mommy ta yi ta bar parlour'n dan ba zata iya zama ba, shima Abba miƙewa ya yi ya bi bayan Mommy, ɗan ya lura da halin da ta ke ciki, kuma shima hakan ya ke ji a ranshi, sai dai fa ba zasu ƙi hukunta Raudah ba saboda suna son ta, inaaaaa!! Ai a irin tsarin gidan ma babu ɗan da zai gagare su hukunci ko da nan gaba ne, saboda idan suka goyi bayan yara a kan rashin gaskiya to fa a karshe sune za suyi kuka, tare da dana sani mara amfani. A mamakin Raudah sai ta ga uncle ya zauna, ajiye belt ɗin ya yi a gefen kujera, ganin ta ƙura mai ido ya sa shi faɗin " Ba za ki zo ba sai na zo wajan na cire Waɗannan shegun idanun na ki masu kama da na mujiya". Ai da sauri Raudah ta tashi, ƙaraso wa ta yi wajan da ya ke ta tsugunna tare da sunkuyar da kai ƙasa kamar wata ta arziki... "Waye wannan yaron da ki ka maƙale mai, wanda har yaya da kanshi zai raba ku amma kiyi kunnen uwar shegu?" Uncle ya tambaye ta cikin daka tsawa Cikin shesheƙar kuka ta fara magana "Uncle wallahi ba komai a tsakanin mu da shi, class mate ɗina ne lokacin muna secondary school, bayan haka babu komai, kaji na rantse". Kallon ta uncle ya ke cike da son gano gaskiyar abinda ta ke faɗa, ya yi tunanin ba iya dukan bane kadai zai wadatar musu, dole sai an hada da yi ma ta nasiha da tunatar wa, gyaran murya ya yi sannan ya ce "Raudah kin ga wannan abun da muke miƙi? Wallahi shine gatan ki, baki da waɗanda suka fi iyayen ki duk duniyar nan, riƙe mutuncin ki abin alfahari ne a wajan su kamar yadda zubar da mutuncin ki abin takaici ne da tozarci a gare su, dan haka kece kadai mafitar gidan nan, darajar gidan nan ke zaki daga ta a wajan al'ummar da suke ganin ƙima da darajar iyayen ki, kuma ke kan ki kin sa ni, wanda za ki aura wato Nuradden ɗan manyan mutane ne, to da'a ce yau mahaifin Nuruddeen ne ya ganƙi a yanayin da Abba'n ki ya ganki ya zai ji? To wallahi fasa auren za'a yi duk kuwa son da kuke ma juna da yaron na shi, kuma shi wannan sha-sha-shan ba da kuke yawon gantali a gari ba zai taɓa auren ki ba". Haƙika maganganun sa sun ratsa zuciyar Raudah, jikin ta ya yi sanyi laƙwas, cikin sanyayyar murya wadda har ta fara dashewa saboda kukan da ta yi, ta ce "Uncle kayi hakuri insha'Allah ba zan ƙara ba, kuma zan bama Abba da Mommy hakuri, kai ma ɗan Allah ka taya Ni basu haƙurin". Jin-jina kai uncle ya yi, ganin jikin Raudah ya yi sanyi fiye ma da yanda yake tunani, kamo ta ya yi ya zaunar da ita ɗan da a tsugunne ta ke, "To shikenan Raudah in dai kin kiyaye babu wanda zai kara taba lafiyar jikin ki, kuma zan taya ki bama Abba da Mommy haƙuri, sai dai Raudah akwai wani hanzari ba gudu ba..." Ba'a iya haka Adnan ya so su tsaya da Fadeelah ba amma wannan Mallam Sule'n ya kwafsa mishi, ko da ya koma gida kiran ta ya yi a waya ta na daga wayar ya sauke ajiyar zuciya "Fadeelah Baba Sule ya kwafsa min wallahi, ba ki ji yadda na ji ba, ko kaɗan ban ji daɗin yadda ya katse mana jin dadi ba, a hannu na ke". Fadeela ma cikin yanayin rashin jin dadi wanda daga muryar ta ma zaka fahimci hakan ta ce " Wallahi kuwa Bestynah, amma fa na ji dadi da Allah ya rufa mana asiri bai gan mu ba, ɗan wallahi da ya gan mu tare sai ya tara mana jama'ar anguwa" Shi dai Adnan a zuciyar shi yasan yau tarkon shi zai iya cimma Fadeelah, dama haka ya ke so ta fara muradin shi da ƙanta, yasan dama wataran da ƙanta za ta kawo mishi kanta a ruwan sanyi, cikin nuna isa ya ke faɗin "Kinga Fadeelah gobe ki fito mu hadu, kuma ba romancing na ke so ba, so na ke na karɓi budurcin ki a gobe, idan ba haka ba ki manta da ni a rayuwar ki, kuma ko a hanya kar ki nuna kin sanni saboda ba kya sona kamar yadda na ke son ki" Yana gama faɗar haka ya kashe wayar Chabdi jam!!!!🤣🤣🤣 Chakwalkwalin chakwakiya kenan, shin Fadeelah zata amince ta mallaka wa Besty Adnan budurcin ta kafin Aure kuwa? Ga kuma Raudah'n Besty an ce akwai magana a kasa... Ko me Uncle zai faɗa ma ta.... Ku ci-gaba da bina dan jin yadda za ta kaya..... VOTE COMMENTS SHARE ✍️ BADAWEEYERH 💐💐S͆A͆N͆A͆D͆I͆N͆ B͆E͆S͆T͆Y͆ 💐💐 L͆a͆b͆a͆r͆i͆/R͆u͆b͆u͆t͆a͆w͆a͆✍️ R͆A͆B͆I͆'A͆T͆U͆ A͆H͆M͆A͆D͆ M͆U͆A͆'Z͆U͆ (R͆U͆B͆B͆Y͆) G͆a͆j͆e͆r͆e͆n͆ l͆a͆b͆a͆r͆i͆ (S͆h͆o͆r͆t͆ s͆t͆o͆r͆y͆) M͆y͆ w͆a͆t͆t͆p͆a͆d͆ l͆i͆n͆k͆👇🏻 https://www.wattpad.com/1190086089?utm_medium=link&utm_source=android&utm_content=share_published 💐💐💐💐💐💐💐💐 Dᴇᴅɪᴄᴀᴛᴇᴅ ᴛᴏ Mʏ ʟᴏᴠᴇʟʏ ᴍᴏᴍ (Hᴀᴊ Rᴜᴋᴀɪʏʏᴀ), Aʟʟᴀʜ ʏᴀ ƙᴀʀᴀ ᴍɪᴋɪ ʟᴀғɪʏᴀ ᴅᴀ ɴɪꜱᴀɴ ᴋᴡᴀɴᴀ ❤️❤️ Sᴘᴇᴄɪᴀʟ ɢɪғᴛ ᴛᴏ Kᴀɪɴᴜᴡᴀ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀᴛɪᴏɴ Aʟʟᴀʜ ʏᴀ ƙᴀʀᴀ ʜᴀᴅᴀ ᴋᴀᴡᴜɴᴀɴ ᴍᴜ ᴀ ᴅᴜᴋ ɪɴᴅᴀ ᴍᴜᴋᴇ 🤗 *____________________________________* *🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼* *🇦SSOCIATION🤝🏻* ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation *_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻 https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association *____________________________________* PⒶⒼⒺ 9️⃣ Kallon mamaki Fadeelah ta bi wayar hannun ta da shi, a iya zaman da suka yi da Adnan bai taɓa mata haka ba, Ita dai ta san ba soyayya suke ba amma kuma ta bashi muhimmanci sossai a zuciyar ta, ta yadda ko ɓacin ran shi ba ta so ballantana kuma a ce ita ce sanadi, number shi ta ƙara gwada wa amma sai ta ji a kashe, saƙo ta rubuta mai sanan ta kashe wayar ta gaba ɗaya, shirin bacci ta yi, sai da ta gama shirin ta hau gado, wata sha'awa ce ta fara damun ta hakan ya sa ta dauko wayar da ta kashe ta kunna, wani group ɗin su na mata da maza ta shiga, babu abinda ake yi a group ɗin sai batsa, ai kuwa tana hawa ta ci karo da wani hira da a ke yi mai ta da hankali, karantawa ta shiga yi cikin nutsuwa da mayar da hankali, tana cikin karatun kuma aka sako wasu zafaffan vedio masu ɗaga hankali, da kallon da tayi ne dai har ta samu relief sannan bacci mai daɗi ya kwashe ta. A ɓangaren Adnan kuwa shima bai samu bacci ba ɗan yana cikin yanayin da in dai bai rage abinda yake damun shi ba to tabbas akwai matsala, ganin lokaci na tafiya ne ya sa ya shirya cikin kananun kaya masu kyau da daukar hankali, wayar shi ya dauka ya kira Farouk, sai da ya kira sau uku sannan ya ɗaga wayar "Hello freind kana ina ne ina ta kiran ka baka ɗauka?" "Mtseww kaii dan iskaa ne mutum yana tsakiyar jin dadi ka katse shi, ai dai kasan ina gida ko?" Farouk ya faɗa cike da jin haushi ɗan da yasan wannan banzar tambayar zai mai da ba zai ɗauki wayar shi ba. "Ah lallai shine ɗan ka samun jin dadi ko ka kira ni muyi kashe mu raba kamar yadda aka saba, to gani nan zuwa dan wallahi a hannu na ke". Bai ma jira cewar Farouk ba ya kashe wayar, ɗakin ya kulle ya fita, tunda yasan babu mai neman shi a cikin iyayen na shi koda kuwa zai kwana uku baya gida ne, ɗan iyayen shi basu cika damuwa da inda yaro yaje ba, a cewar su ai ya na da hankali zai iya kare kan shi, shi yasa bai cika kwana a gida ba. Mashin ya dauka ya nufi gidan su Farouk, babban gida ne sosai, dake me gadi ya san da shi bai sha wahalar shiga ba tunda dama sun saba kwana a gidan, direct sashen Farouk ɗin ya nufa sai dai a kulle kofar ta ke, door bell ya danna har tsayin mintuna biyar amma ba alamar za'a bude mishi kofar, a ran shi ya ce "Lallai Farouk ɗan iska ne ya, wato ya samu mace ai dole ya manta da ni", wayar shi ya ciro ya kira shi, ganin kiran Adnan ya sa Farouk miƙewa da wayar a hannunsa dan ya san ya zo ne shiyasa ba zai daga wayar ba, kofa ya je ya bude mishi, kutsa kai Adnan ya yi shiga "Kaii ka ga idanun ka kuwa lallai yau akwai tada ƙura..." Adnan ya faɗa cike da zolayar abokin na shi. Wata uwar harara Farouk ya mishi yana faɗin "Eh ba gwanda ni ba duk jarabata ai ban kai ka ba, kai kam wallahi matar da zaka aura, oh sorry Fadeelah da zaka aura ta shiga uku", ya karashe maganar yana dariya ƙasa-ƙasa, ai kuwa a ƙufule Adnan ya ce "Kar ka ɓata min rai Mallam, na taɓa ce maka Fadeelah ce matar da zan aura? Allah ya sawwaka!! Me zan yi da wannan balagazar yarinyar da bata jin maganar kowa, kada ma ka sake haɗa ta da matar da zan aura, domin ni matata mai nutsuwa ce kuma mai tarbiyya, kamila sannan Malama, irin matar da zan aura kenan, so you better stop comparing me with that stupid" Tin da Adnan ya fara magana Farouk ya ke kallon shi, dake a tsaye suke a cikin parlour'n, basu Karasa ciki ba suka fara wannan hirar, shi wallahi Adnan mamaki ya ke ba shi, ba wani mamakin wacce yake da burin aure ba a'a mamakin yadda ya ke deceiving yarinyar mutane kuma a bayan idon ta yazo yana zagin ta, girgiza kai kawai Farouk ya yi bai ƙara ce masa uffan ba ya nufi hanyar bedroom, ganin haka ya sa shima Adnan jan dogon tsaki ya bi bayan shi, saboda ya lura Farouk na son lalata mishi mood ɗin shi ne. Yana shiga ɗakin yaga wata budurwa a kwance, dama Farouk ya riga shi shiga hango su ya yi a kwance cikin bargo, kallo daya ya ma yarinyar ya ga idon ta a soye ya ke, zama Adnan ya yi a kujerar da ke bedroom ɗin, yana iya ganin kallon da yarinyar take mishi, a ranshi ya ce "mayya kar ki cinye ni". Adnan ne ya kalli Farouk ganin bashi da niyyar tashi ya basu waje gashi dama shi a mugun matse yake ya ce "Guy ka ɗan bamu waje mana". Ko kallon shi Farouk bai yi ba sai ma baya da ya juya musu yana faɗin "Hmmm bana son munafurci yau ka saba yi a gabana? Nifa iyayi ne bana so, kasan dama haushin ka nake ji, idan kaga dama ka ɗauke ta kuje parlour amma nikam ba inda zan je" yana gama faɗar haka ya ƙara jan bargo ya rufe jikin shi, shi kuwa Adnan jawo hannun yarinyar ya yi wadda ko sunan ta ma bai sani ba, yasan ita ma ba baƙuwa ba ce a harkar daga ganin yanayin ta, ai kuwa narke mishi ta yi a jiki , daga haka dai labari ya chanza ( ban ga komai ba Fan's kar Fadeelah ta soka min wuka 😜). Shiru Raudah ta yi ta bama uncle dukkan nutsuwar ta, da alama maganar da zai faɗa mata tana da muhimmanci sossai, qasa ta kara yi da kanta ta ce "Uncle mene ne ya faru, Ko laifin nawa ba daya ba ne?". Girgiza mata kai uncle Babangida ya yi, ganin hankalin ta ya tashi ne ya sa shi faɗin "Ki kwantar da hankalin ki Raudah, dama Abba'n ki ne ya bani sako na baki, akan maganar auren ku da Nuradden, kin san dama kowa a shirye yake, kuma da tuni an dade da yin auren naku sai aka miki uzurin ki kammala jarrabawa a makaranta tunda kun zo ƙarshe, haka ne?" Daga mishi kai Raudah tayi ba tare da tayi magana ba, ya ci-gaba da faɗin "To mahaifin ki ya tsayar da bikin ku nan da sati Biyar masu zuwa idan Allah ya kaimu, sai kije ki fara shirye-shirye, kuma shima a ban'garen Nuruddeen ɗin Abba ya sanar da mahaifin shi". Dammm!!! Raudah taji.ƙirjun ta ya buga, rasa wanne yanayi take ciki ta yi, murnar auren ta da masoyin ta da za'a yi ko kuma baƙin cikin an raba ta da Besty ɗin ta, kawai sai ta faɗa jikin kujera ta fashe da matsanancin kuka... 😂😂🤣 Raudah'n Besty Meye na kuka? Fan's ɗin Raudah ku ce mata amarya bata kuka fa ahto kar tayi ma Noor asarar hawaye..... VOTE COMMENTS SHARE ✍️ BADAWEEYERH 💐💐S͆A͆N͆A͆D͆I͆N͆ B͆E͆S͆T͆Y͆ 💐💐 L͆a͆b͆a͆r͆i͆/R͆u͆b͆u͆t͆a͆w͆a͆✍️ R͆A͆B͆I͆'A͆T͆U͆ A͆H͆M͆A͆D͆ M͆U͆A͆'Z͆U͆ (R͆U͆B͆B͆Y͆) G͆a͆j͆e͆r͆e͆n͆ l͆a͆b͆a͆r͆i͆ (S͆h͆o͆r͆t͆ s͆t͆o͆r͆y͆) M͆y͆ w͆a͆t͆t͆p͆a͆d͆ l͆i͆n͆k͆👇🏻 https://www.wattpad.com/1190086089?utm_medium=link&utm_source=android&utm_content=share_published 💐💐💐💐💐💐💐💐 Dᴇᴅɪᴄᴀᴛᴇᴅ ᴛᴏ Mʏ ʟᴏᴠᴇʟʏ ᴍᴏᴍ (Hᴀᴊ Rᴜᴋᴀɪʏʏᴀ), Aʟʟᴀʜ ʏᴀ ƙᴀʀᴀ ᴍɪᴋɪ ʟᴀғɪʏᴀ ᴅᴀ ɴɪꜱᴀɴ ᴋᴡᴀɴᴀ ❤️❤️ Sᴘᴇᴄɪᴀʟ ɢɪғᴛ ᴛᴏ Kᴀɪɴᴜᴡᴀ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀᴛɪᴏɴ Aʟʟᴀʜ ʏᴀ ƙᴀʀᴀ ʜᴀᴅᴀ ᴋᴀᴡᴜɴᴀɴ ᴍᴜ ᴀ ᴅᴜᴋ ɪɴᴅᴀ ᴍᴜᴋᴇ 🤗 *____________________________________* *🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼* *🇦SSOCIATION🤝🏻* ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation *_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻 https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association *____________________________________* PⒶⒼⒺ 🔟 Ganin Raudah ta ƙi dena kukan ne ya sa uncle haɗe rai, yaga yarinyar na neman raina shi, to in ba raini ba daga magana sai ta kama yi masa kuka? Tsawa ya daka mata hakan ya sa ta yi gum da baƙin ta "Kukan me kike yi?" Ya tambaya yana zaro mata dukkan idanuwan shi, dama a kaf cikin familyn su babu wanda ake tsoro kamar uncle Babangida, yana da sauƙin kai amma yana da zafi, kuma a jinin su ne shi da Abba'n Raudah Allah ya basu baiwar kwarjini a idon mutane, shiyasa a lokuta da yawa su ne masu hukunci a cikin familyn... Ƙasa bashi amsa ta yi hakan ya sa uncle tashi ya fita a parlour'n yana faɗin "Kya ji da shi munafuka, ki na son mutum amma kin saka shirme da wasa a maganar aure kina son ki mayar da mu ƙananan mutane". Haka dai ya ci-gaba da mita har ya bar parlour'n gaba ɗaya ba tare da ya nemi Abba da Mommy ba, Raudah na ganin ya fita ta miƙe, ta nufi ɗakin ta, zama ta yi a kan bed sai kuma tunanin besty ya faɗo mata a rai, kawar da tunanin ta yi ta hanyar tunawa da nasihar da uncle ya ma ta, ganin kanta na ciwo ne ya sa ta dauƙo magani ta sha, sannan ta ƙwanta, ko a baccin ma babu abinda ta ke yi sai mafarkin Besty, wai gasu a wani lambu mai korayen ganye, tana zaune a saman cinyar shi yana bata hollandia milk a baki sai zuba shagwaba ta ke yi shi kuma yana biye ma ta, suna cikin wannan yanayin ne sai ga Abba da Noor ai kuwa ta ƙwalla ƙara ta farka a gugice ta na share zufa, jin ihun Raudah ya sa Mommy shigowa da gudu cikin ɗakin tun da ta tabbatar Uncle Babangida ya tafi, saboda yana fita ya kira su a waya ya shaida musu yadda su kayi da Raudah'n da kuma roƙar su yafiyar ta, kuma suna gama wayar shima Abba ya koma shago, a guje Mommy ta ƙara so ɗakin, ganin Raudah na zaune a bakin gado tana haɗa zufa ne ya sa ta jingina da jikin Mirror, kallon mamaki Mommy ta ke bin Raudah da shi, a ranta ta ke tunanin ko dai yarinyar nan tana da aljannu ne? Saboda abubuwan da ta ke yi wasu lokutan na bata mamaki ko kuma dai tsabar iskanci ne ohooo, cike da mamaki Mommy ta kalli inda Raudah ta ke zaune, har yanzu bata bar haɗa zufa ba, duk da ta ga shigowar Mommy, sai da Mommy ta gama nazartar ta sannan ta ce "Wai ke Raudah me yasa kike abu kamar ƙaramar yarinya ne? Ko Arya ba zata yi abinda kike yi ba, ke kenan kullum sai an miki magana? To wallahi ba zan iya ba na gaji da halin ki gwara ma ayi-ayi auren kowa ya huta ki tattara kayan ki ki bamu space ni da mijina ni ma". Karshen maganar da Mommy ta yi ne ya sa Raudah kallon ta gami da sakin murmushi tana faɗin "Kai Mommy kun gaji da ni kenan?" Harara Mommy ta galla ma ta, gaba ɗaya lamarin na Raudah sai addu'a "Eh ba dole muyi Allah-Allah ki tafi na ki ɗakin ba, Raudah yanzu kin fara chanza halin ki, tun da ki ka haɗu da wannan ɗan iskan yaron ni ƙaina hakuri na ke yi da ke, Ni dai shawarar da zan baki ita ce gwara ki rufa ma kan ki asiri ki rufa mana mu ma iyayen ki, ki samu ayi auren ki lafiya qlau ba tare da an samu wata matsala ba" Murmushi Raudah ta yi har da rufe idanu alamar kunya, ganin haka ya sa Mommy girgiza kai kawai ta fita a daƙin tana addu'ar Allah ya raba Raudah da wannan Besty'n, Mommy bedroom ɗin ta ta koma ta fara ninke kayan Arya da almajirin gidan ya wanke. Mommy na fita Raudah ta tashi, parlour ta fito bata ga kowa ba, hakan ya tabbatar mata da yaran sun tafi madrasah, tunowa ta yi da wayar ta, da sauri ta nufi tsakar gida, a gefe kusa da pampo ta hango jakar ta a yashe a wajan ba zata iya tuna lokacin da ta yar da jakar ba tsabar ƙiɗimewa da ta yi, Allah ya so ta ma ba'a mata dukan da tayi tsammani ba, ai kuwa da Uncle Babangida dukan ta ya yi yau ta san sai an ƙwantar da ita a asibiti dan bata mantawa akwai lokacin da ya daki Sadiya yarinyar shi akan ta yi laifi sai da ta kwana uku a asibiti kafin ta dawo dai-dai. Nufar wajan da jakar ta ke ta yi, ta da ɗauka sannan ta shiga kitchen, dube-dube ta fara yi, wata food flask blue ta buɗe ɗan ba karamin yunwa ta ke ji ba daurewa kawai ta ke yi, jallof ɗin taliya da macroni ta gani, tsaki Raudah ta ja ɗan a duniyar nan babu abincin da ta tsana kamar taliya da macroni, rufe abincin ta yi, parlour ta koma, ta zauna a kujera, ganin yunwa ba zata bar ta ba ya sa ta haɗa tea. Wayar ta ta jawo taga twenty missed calls da massages guda biyu, sai da gaban ta ya faɗi, da kyar dai tayi ta maza ta buɗe, ganin Dee ne ya sa ta tura baki gaba ta bude massage ɗin, tambayar ta yake yi tana ina ne? Hankalin shi ya tashi sossai da rashin daga wayar ta, sai da ta gama karantawa sannan ta kunna data, massages ne suka fara shigowa, na besty ne a sama, ya mata massages ya fi goma a WhatsApp, bayan ta buɗe ta gama karantawa sai tayi murmushi mai kayatarwa saboda ko ba komai he really cares kuma ita ma ta san ya zama wani ɓangare na jikin ta, voice note ta mishi, bayan ta labarta mai abinda ya faru ta kara da cewa su rabu kawai tunda ta ma iyayen ta alƙawari kuma gashi sun yanke shawarar auren da ita nan nan da sati biyar, tura mai da voice note din ta yi sannan ta koma gefen status, emoji na kuka ta uploading, tana gama wa ta sauka, cup ɗin da ta sha tea ta ɗauka ta nufi kitchen, wanke-wanke ta hada, da kyar ta iya gamawa, ta na yi tana zumɓura baƙi, har lokacin da ta gama Mommy ba ta fito ba. Gari na wayewa Fadeelah ta gyara gidan tsaf, suna cikin breakfast da Antyn ta take shaida mata yau za ta je shagon saloon, abin ya ba ma Anty mamaki dan tun da aka saka ta a shagon da zummar ta koyi aiki ba son zuwa ta ke ba, sai Anty tayi ta magana ta ke zuwa shi yasa ta kyale ta taci karen ta ba babbaka tunda ita a rayuwar ta bata san inda ya ke mata ciwo ba, "Yau kin ga dama za ki je shagon ne"? Anty ta tambaye ta bayan ta gutsuro bread zata saka a baƙi "Eh Anty jiya ne da daddare nayi tunanin na koma tunda ba wani abun na ke yi a gida ba" "To Allah ya bada sa'a" cewar Anty, daga haka babu wanda ya ƙara cewa komai har suka gama breakfast, yaran Antyn guda biyu Areef da Areefa Fadeelah ta kai school, bayan ta kaisu ne ta tsaya a hanya ta kira Adnan yana dagawa ta fara kora mai bayani cike da murna "Haba Bestynah me yasa ka ke wasa da numfashi na"? Wata iska mai sauti da jan hankali Adnan ya furzar, sai da tsiƙar jikin Fadeelah ta tashi, wani yanayi ta ji ta a ciki mai wuyar musaltuwa, jin ya yi shiru ne ya sa cikin shagwaba ta ƙara faɗin "Umm ummm wallahi zan maka kuka kaga bana son ina maka magana kana banza da ni, kuma ai na maka text na ce yau za mu haɗu kamar ƙarfe koma, shine kake son daga hankali na ko?" Tun da ta fara magana har ta gama bai ce mata komai ba sai da ta saka mai kukan gaske sannan ya fara magana "Am shikenan bana son kukan na hakura shikenan?, Allah ya kaimu ƙarfe goman mu hadu a dai-dai junction din anguwan ku saii na ɗauke ki" "To shikenan sai mun haɗu" ta na gama faɗar haka ta koma gida, sauran aikace-aikacen ta ƙarasa, tana ganawa ta shiga wanka, duk da gaban ta na faɗuwa amma ya za ta yi? Ba zata iya jure fushin Besty ba, kuma ma tasan ba abinda zai faru tunda shima yana ƙaunar ta, da wannan tunanin hankalin ta ya kwanta har ta gama wanka... Shirya wa Fadeelah ta yi cikin wata jar after dress yayin da ciki bata saka komai ba daga ita sai pant da bra, bayan ta bi ko wanne lungu da saƙo na jikin ta da turare mai sanyin kamshi, baƙar jaka ta dakko ta saka wayar ta a ciki da yan kuɗaɗen ta sannan ta ɗauko wani bakin flat shoe ta saka, Masha Allah tayi kyau sosai, dan Fadeelah kyakkyawa ce kuma irin dogayen matan nan ne, sai dai ba Siriya ba ce tana da cikar kirji, kallon kanta ta yi a madubi sannan ta fice zuwa ɗakin Anty, guga ta tarar da ita tana yi, zama ta yi a hannun kujera ta ce "Anty ni zan tafi, sai na dawo" Tashi Anty tayi zuwa gefen TV stand ta dakko dari biyar ta bata, ta ce " Ga wannan ki yi kuɗin mota kuma ki siya abinci, ɗan Allah Fadeelah ki kiyaye bana son na ji wani abu, ki kula da kanki kuma ki tsare mutuncin ki, banda surutun banza da kuma kule-kulen samari, ki gaishe min da Madam Cynthia". Da to Fadeelah ta amsa ma Anty ta fice da sauri a gidan, tana isa junction ta hango Adnan a tsaye yana waya, yana ganin isowar ta ya yanke wayar, bata nuna mai komai ba ta hau mashin din suka nufi hotel din da suka saba zuwa, dakin da ya kama suka nufa, suna shiga ya ɗaga ta chak zuwa toilet ya cire mata kaya, wanka suka yi a tare sannan ya dawo da ita kan gaɗo suna rungume da juna, Adnan ya ce "Fadeelah ba ki san yadda na ke ji a kan ki bane, ke kin san inda bana son ki ma ba zan dinga sha'awar ki ba, to amma bana iya jurewa a duk sanda na gan ki, na kan zauce na rasa tunani na, bana iya samun nutsuwa sai na ji ki a jiki na, dan Allah Fadeelah ki dena mun rowa, mun fa daɗe da zama ɗaya ni da ke" ya ƙarasa maganar yana shafa gashin kanta... Lumshe ido ta yi saboda ba karamin dad'i maganar shi ta ma ta ba, sai ta ji ta kamar wata sarauniya, gashin ƙirjin shi ta fara shafawa dan ba karamin burge ta suke yi ba yadda suke a kwance luf, gashi jikin na shi a jiƙe yake, shi yasa wajan ya ƙara armashi, kwantar da ita Adnan ya yi ya fara bata wasu hot kisses, dake sun saba da romancing ɗin juna sai ta biye mai, sai dai wannan ƙaran ya sha ban-ban da sauran domin kuwa da alama a hannu ya ke, gangarowa ya yi dokin wuyan ta ya fara lasa, ai tuni ta birkice, romancing ɗin juna suke sossai, shikam oga Adnan baya hayyacin shi domin kuwa yanzu so yake kawai ya jefa ƙwallo a raga, cikin kiɗimewa ya shige ta. Wani razanannen ihu Fadeelah ta ƙwalla, amma inaaa Adnan kam bai ma san tana yi ba, sai da ya kwashi kusan mintuna talatin yana abu daya sannan ya samu nutsuwa, sai a lokacin ya dawo hayyacin shi, yana dubawa ya ga Fadeelah bata numfashi... VOTE COMMENTS SHARE ✍️ BADAWEEYERH💐💐S͆A͆N͆A͆D͆I͆N͆ B͆E͆S͆T͆Y͆ 💐💐 L͆a͆b͆a͆r͆i͆/R͆u͆b͆u͆t͆a͆w͆a͆✍️ R͆A͆B͆I͆'A͆T͆U͆ A͆H͆M͆A͆D͆ M͆U͆A͆'Z͆U͆ (R͆U͆B͆B͆Y͆) G͆a͆j͆e͆r͆e͆n͆ l͆a͆b͆a͆r͆i͆ (S͆h͆o͆r͆t͆ s͆t͆o͆r͆y͆) M͆y͆ w͆a͆t͆t͆p͆a͆d͆ l͆i͆n͆k͆👇🏻 https://www.wattpad.com/1190086089?utm_medium=link&utm_source=android&utm_content=share_published 💐💐💐💐💐💐💐💐 Dᴇᴅɪᴄᴀᴛᴇᴅ ᴛᴏ Mʏ ʟᴏᴠᴇʟʏ ᴍᴏᴍ (Hᴀᴊ Rᴜᴋᴀɪʏʏᴀ), Aʟʟᴀʜ ʏᴀ ƙᴀʀᴀ ᴍɪᴋɪ ʟᴀғɪʏᴀ ᴅᴀ ɴɪꜱᴀɴ ᴋᴡᴀɴᴀ ❤️❤️ Sᴘᴇᴄɪᴀʟ ɢɪғᴛ ᴛᴏ Kᴀɪɴᴜᴡᴀ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀᴛɪᴏɴ Aʟʟᴀʜ ʏᴀ ƙᴀʀᴀ ʜᴀᴅᴀ ᴋᴀᴡᴜɴᴀɴ ᴍᴜ ᴀ ᴅᴜᴋ ɪɴᴅᴀ ᴍᴜᴋᴇ 🤗 *____________________________________* *🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼* *🇦SSOCIATION🤝🏻* ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation *_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻 https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association *____________________________________* I lack proper words and adjectives to express my gratitude enough for the lovely birthday wishes I have received from you all! You have all shown me so much love and for that, I am very grateful! I’m being totally truthful when I say that each and every message brought a smile to my face and made my day that much more special! I appreciate. Thank you for making my day as special as it could be. Allah yabar zumunci🥰. PⒶⒼⒺ 1️⃣1️⃣ Salati kawai Adnan ya ke yana kiran sunan ta Fadeelah! Fadeelah!! Fadeelah!!!, Ki tashi dan allah, ganin ko gezau ba ta yi ba ya sa ya tashi da sauri ya saka kaya ya nufi toilet ya ɗibo ruwa ya fara shafa mata, sai da ta kusan minti biyar sannan ta ja wani numfashi, har a lokacin ba ta daina kuka ba, rarrashin ta ya ke ta yi, da kyar ya samu ta yi shiru, dan ma sun saba romancing kuma yana saka mata yatsa, amma ba dan haka ba ai shima yasan ba karamar wahala za ta sha ba tunda ba'a taba shigar ta ba, hawaye ne suke tsiyaya a idanun ta, ba tare da ta ce mai komai ba ta miƙe, ai kuwa wata ƙara ta ƙara sakawa saboda wani zafi da ta ji ƙasan ta yana yi, dake shi Adnan kwararre ne a fannin kawai ya tashi ya nufi toilet ya haɗa mata ruwa mai zafi, yana fitowa ya ɗauke ta sai cikin bathtub, ai kuwa ƙankame shi ta yi, da kyar ta zauna ruwan ya ratsa ta, sai da ya mata hakan sau uku sannan ta ji wajan ya rage zugi, da kanta ta fito tana ɗingisa ƙafa, ko kadan ba ta ji haushin abinda ya ma ta ba, a ganin ta ai duk soyayyar da ya ke ma ta ne ya janyo hakan, kuma ta yadda da shi ɗari bisa ɗari cewa ba zai ci amanar ta ba ko kuma ya juya ma ta baya komai daren daɗewa.. Da kyar ta iya zama a kan stool ɗin da ke gefen gadon, shi kuwa Adnan sai murmushi ya ke zuba ma ta, tashi ya yi zuwa wajan da kayan ta su ke ya dauko, a gaban ta ya tsugunna ya fara saka ma ta kayan yana kara yi ma ta kalamai masu ratsa zuciya, abinci ya musu order, amma fir Fadeelah ta ki ci, sai da ya lallaɓata tukunna ta ci kaɗan, ruwa ya bata ta sha, sai da ta sha mai isar ta sannan ta kwanta tana bin shi da kallo, nan da nan kuma zazzaɓi mai zafin gaske ya rufe ta, hakwaran ta ne ya fara haɗuwa waje ɗaya, ganin haka ya sa Adnan tashi da sauri ya rufe ta da blanket, key din mashin ɗin shi ya ɗauka ya fice a ɗakin, bayan kamar mintuna ashirin ya dawo ɗauke da magani, har a lokacin babu abinda ta ke sai kakkarwa, kuma ba bacci ta ke ba saboda duk abinda ya ke yi tana jin shi amma ko ido ta kasa buɗe wa. "Fadeelah tashi ki sha magani" Ƙasa tashi ta yi saboda yadda ta ke ji, ganin tana bata mai lokaci ne ya sa ya hau gadon ya tallafo ta, maganin ya ɓalla ya bata ta, tana yamutsa fuska alamar bata, da kyar nan ma ya lallaɓata ta sha, har yanzu bata buɗe ido ba kuma bata ce da shi uffan ba, ganin haka ne ya sa ya ƙara kwantar da ita ya shiga wanƙa, nan da nan bacci mai nauyi ya kwashe ta saboda a cikin maganin ya sa an haɗa mata har da na bacci, addu'ar shi daya Allah ya sauƙaka musu ta yadda tana tashi ya kasance babu zazzaɓin a jikin ta ya mayar da ita gida. Ya kai kamar minti goma a cikin bayan gidan yana wanƙa, yau jin shi ya ke yi kamar sabon ango, duk da ba yau ya fara mua'mala da ya mace ba amma yau ɗin na musamman ne a wajan shi, shi ya sa yake ta zabga murmushi kamar an mai kyautar agogo (agogon Mommy'n Ahlan da gwaggo Indo ta aro ta je biki😜). Ko da ya fito kayan shi ya mayar ya tsaya yana kallon yadda Fadeelah ta ke sauke numfashi a wahale, wani tunani ya yi sai ya saka murmushi mai sauti harda girgiza kai ( na ce lallai Adnan ya san kan bariki), kayan jikin shi ya ƙara cire wa shima ya haye gadon ya manne da Fadeelah har da ƙara ja masu blanket, (asuba ta gari besty'n Fadeelah 😂)... Kwanan Raudah uku bata yadda ta yi magana da besty ba duk da zuciyar ta na mata raɗadi amma ta daure, ta ƙi daga wayar shi, ga saƙon da ya ke aiko mata da su a ko wanne lokaci ta Massage da ta WhatsApp wanda ita kanta bata dan adadin su ba, kuma a kwanakin nan kullum sai ya saka hotunan ta a status tare da kalmomi na nuna tsantsar damuwa na rashin ɗaukar wayar shi da ta ke yi, gallery ta shiga ta fara kallon hotunan da suka ɗauka tare, hawaye ne ya ke gangarowa a fuskar ta, tana cikin wannan yanayin ne kiran Noor ya shigo wayar ta, rabon da su yi waya tun ana gobe Abba zai ganta da Besty, ta rasa matsalar Noor, gaba ɗaya shi he is not a caring type, shi ya sa ta fi jin Besty a ranta, duk da tana son Noor kuma tana fatan su kasance tare har abada amma Besty ya fi shi kula da ita, ya fishi nuna damuwa a kanta, har kiran ya katse bata iya dagawa ba sai da ya ƙara kira a karo na biyu ta ɗauka, cikin murya mai sanyi ta ce "Assalamu Alaikum" "Wa'alaikumus Salam Amarya ba kya laifi, ashe an saka bikin mu shine ko ki kira ni na taya ki murna?" Noor ya faɗa cike da zolaya Kallon mamaki Raudah ta bi wayar da shi ɗan bata taɓa jin irin wannan wasan a wajan Noor ba, ciro wayar ta yi a kunne ta ƙara dubawa number a ganin ga ko bata ga sunan da kyau ba ne, tabbas dai shine ba wani ba... "Tabdijam" ta furta a ranta "Ko azumin magana matar tawa ta fara yi ne"? Ai kusan daskarewa Raudah ta yi a wajan cikin in-ina ta ce "Ina-ina wuni ya Noor"? "Ba zan amsa gaisuwur ki ba har sai kin bani amsar abinda na tambaye ki". Rasa me zata ce mai ta yi kawai ta yanke kiran saboda jin abin ban-barakwai da ta yi, a ranta tana tunanin anya Noor ne kuwa? To me ya sa ya ke mata wasa yau bayan tafi kowa sanin murdaɗen halin shi?, Bata gama mamaki ba kiran ya ƙara shigowa, tana dagawa ya ce "To amarya ina nan zuwa bayan magrib, za muyi magana, ki min kwalliya sossai". Yana gama faɗar haka ya kashe wayar, ita kuwa Raudah banda juya wayar babu abinda ta ke yi, sam mamakin ƙiran da Noor ya yi ya ƙi barin ta ranta, a sukwane ta tashi daga kan gadon ta nufi daƙin Mommy, bacci ta tarar tana yi tunda duk yaran gidan suna makaranta, daƙi ta koma ta ɗauko mayafi da kuɗi da zummar ta siyo kati a shagon da ke ɗan gaba da gidan su, kai tsaye shagon ta nufa ta siyo katin, fitowar ta daga shagon kenan ta ci karo da Dee, da sauri ta dafe ƙirji ta ja da baya tana faɗin "Innalillahi wa inna ilaihir rajiun" Raudah ta faɗa da ƙarfi kamar wacce ta ga mutuwa, mamaki ne ya kama Dee ganin reaction ɗin ta, tunanin shi ɗaya dai Allah ya sa aljannun ƙanta basu shiga tsakanin alaqar shi da ita ba saboda shi fa ya rasa gane kanta kwata-kwata dan ko a waya da ta ce mai sun rabu ma kasa yadda ya yi, bai ma bar abin ya darsu a zuciyar shi ba saboda a nashi ganin sharrin aljannun da suka kamata ranar da ta yi wannan gudun ne, duk da ta faɗa mai abinda ya firgita ta yi, amma shi ya fi alaƙanta hakan da aljannu ne ta gani, sai ka ce wanda aka musu farraƙu, kasa ce mata komai ya yi, sai bin ta ya ke da idanu, samun kan shi ya yi da zubewa a ƙasa ya na hawaye, kallon shi Raudah ke yi alamar tausayi da nadamar abinda ta mishi fal ranta, Allah ya so su ma babu mai kallon su ɗan anguwar ba kowa, maza na kasuwa yara kuma na makaranta, dama haka anguwar ta su ta ke ko a weekend's ma anguwar shiru ta ke yi saboda kowa na cikin gida, ganin babu mutane ne ya sa ita ma ta tsugunna ta kamo hannun shi ta fashe da kuka, mai shago ya na cikin shagon shi bai san wainar da ake toyawa a waje ba, shi rediyo ma ya ke ji. "Raudah me na miki? Me ya sa ki ke barazana da numfashi na? Ko dan kinga na damu da ke ne shi ya sa kike min haka?" Cewar Dee yana ƙara damƙe mata hannu kamar wacce za'a kwace mai ita. Kuka Raudah ta ke yi wanda ita kanta ba zata iya cewa ga dalilin ta ba, sai dai zuciyar ta na ma ta zafi, tabbas Besty bai cancanci haka daga gare ta ba, ita kanta ta a yan kwanakin nan da basa magana azabtuwa ta ke yi, tunani ta ke yi ma anya zata iya rayuwa ba tare da Dee ba? Kaii da kamar wuya, tsagaita kukan ta yi ta share hawaye tana ƙara kallon shi kuma har a lokacin hannun su na like da juna, Chan kuma kamar an tsigare ta sai ta miƙe ta ce "Besty an saka auren mu da Noor kamar yadda na faɗa maka kuma Abba ya raba ni da kai, sai dai a wannan karon hakuri na ya ƙare, Nima ba zan iya jurewa ba". Tana gama faɗar haka ta ƙara jan wani dogon numfashin sannan ci-gaba da faɗin " Ni ta ka ce, ko da nayi aure ma babu wanda ya isa ya raba ni da kai Dee, ka rubuta ka ajiye, ina tare da kai har ƙarshen numfashi na!!!". Tana gama faɗar haka ta sake mai hannu ta yi shigewar ta gida tana kuka, murmushin nasara da farin ciki Dee ne ya kuɓce a fuskar Dee, cike da ƙwarin gwiwa shima ya miƙe ya bar wajan... Tabdijam lallai Raudah kin ɓallo ruwa ni dai babu ruwana idan Abba da uncle Babangida suna miki lugude, Fan's dinki sa kwace ki ah to ni kam na yi nan🏃🏃 VOTE COMMENTS SHARE ✍️ BADAWEEYERH 💐💐S͆A͆N͆A͆D͆I͆N͆ B͆E͆S͆T͆Y͆ 💐💐 L͆a͆b͆a͆r͆i͆/R͆u͆b͆u͆t͆a͆w͆a͆✍️ R͆A͆B͆I͆'A͆T͆U͆ A͆H͆M͆A͆D͆ M͆U͆A͆'Z͆U͆ (R͆U͆B͆B͆Y͆) G͆a͆j͆e͆r͆e͆n͆ l͆a͆b͆a͆r͆i͆ (S͆h͆o͆r͆t͆ s͆t͆o͆r͆y͆) M͆y͆ w͆a͆t͆t͆p͆a͆d͆ l͆i͆n͆k͆👇🏻 https://www.wattpad.com/1190086089?utm_medium=link&utm_source=android&utm_content=share_published 💐💐💐💐💐💐💐💐 Dᴇᴅɪᴄᴀᴛᴇᴅ ᴛᴏ Mʏ ʟᴏᴠᴇʟʏ ᴍᴏᴍ (Hᴀᴊ Rᴜᴋᴀɪʏʏᴀ), Aʟʟᴀʜ ʏᴀ ƙᴀʀᴀ ᴍɪᴋɪ ʟᴀғɪʏᴀ ᴅᴀ ɴɪꜱᴀɴ ᴋᴡᴀɴᴀ ❤️❤️ Sᴘᴇᴄɪᴀʟ ɢɪғᴛ ᴛᴏ Kᴀɪɴᴜᴡᴀ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀᴛɪᴏɴ Aʟʟᴀʜ ʏᴀ ƙᴀʀᴀ ʜᴀᴅᴀ ᴋᴀᴡᴜɴᴀɴ ᴍᴜ ᴀ ᴅᴜᴋ ɪɴᴅᴀ ᴍᴜᴋᴇ 🤗 *____________________________________* *🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼* *🇦SSOCIATION🤝🏻* ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation *_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻 https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association *____________________________________* PⒶⒼⒺ 1️⃣2️⃣ Ko da Raudah ta shiga gida ɗakin Mommy ta nufa, bata gadon kamar yadda ta ganta dazu, dammm gabanta ya faɗi "Kar dai a ce Mommy ta tashi bata ganni ba?" Ta faɗa tana zama a kan stool ɗin da ke gefen gadon, maganganun Besty ne suke yawo a cikin zuciyar ta, da kuma yanayin da ta ganshi, fuskar shi kaɗai zaka kalla kasan baya hayyacin shi, gaba ɗaya tausayi ya bata, ya zama dole su koma kamar yadda suke da, sai su gyara salon su ta yadda babu wanda zai gane suna tare har tayi aure ta bar musu gidan. Mommy ce ta fito daga toilet, ganin Raudah a zaune ya sa ta ɗan dakata bata karaso ba, karantar yanayin da ta ke ciki ta yi, chan kuma sai ta ce "Raudah lapiya? Tunanin me ki ke yi"? Firgigit ta dawo cikin hayyacin ta, murmushin dole ta ƙirƙiro, ta ce "Ah haba Mommy tunanin me zan yi ina da ke", dariya Mommy ta yi koba komai akwai shaƙuwa mai ƙarfi tsakanin ta da ƴaƴan ta duk da ba ta musu goyon sakalci ba amma dai sun shaƙu sossai, kuma duk wanda ya yi laifi suna hukunta shi dai-dai da laifin shi. "To ko an fara tunanin rabuwa da mu ne?" Mommy ta tambayi Raudah cike da zolaya Rau-rau ta yi da idanuwa, kamar zata yi kuka ta ke faɗin "To ni Mommy ki dena cewa za mu rabu, ba kiji yadda gabana ya faɗi ba, Allah na ji wani iri" ta karashe maganar cike da shagwaba... Shiru Mommy ta yi bata kuma cewa komai ba, zama Mommy ta yi a bakin gado ta dauko waya tana dannawa, wayar ta kara a kunne jim kaɗan ta fara magana "Assalamu Alaikum, Hajiya Salimah, fatan kina lapiya"? Daga chan ɓangaren Hajiya Salimah ta yi murmushi mai sauti sannan ta ce "Lapiya qlau, Mommy Mubasheer ya gida da yaran?" "Alhamdulillah, sai dai fa kar ki bari Arya ta ji kina cemin Mommy'n Mubasheer, ɗan ta ce ni Mommy'n ta ce ita kaɗai", Mommy ta faɗa tana dariya Hajiya Salimah ma dariyar ta yi sannan ta ce "Ah ah ai kuwa na tuna kam, na dena faɗa afuwa Mommy'n Arya", su duka biyun dariya suka saka, sai da suka ɗan taɓa barkwanci sannan Mommy ta ce "Hajiya maganar da na mukayi jiya ne akan bikin Raudah, na ji ki shiru kuma kince da azahar za ki zo har nayi bacci na tashi ban ji ki ba, shine na ce bari na kira ki baeki ko lapiya"? "Ohhh!!! Na manta ne ban kira ki ba, dama so na ke ayi la'asar sai na zo saboda nima baƙi na yi yanzun nan suka tafi" cewar Hajiya Salimah "Toh shikenan, Hajiya sai kin zo". Mommy na gama faɗar hakan ta kashe waya, juyowa ta yi tana kallon Raudah ganin itama ita ta ke kallo ya sa ta ce "Wai mene ne ki ka saka ni a gaba kina kallo na"? Ba komai Mommy cewar Raudah, "emmm dama dazu fa'iza ta kira ni wai maganar anko shine na ce ma ta zan kira ta anjima", Kallon mamaki Mommy ta bi Raudah da shi, rasa me za ta ce ta yi kawai ta mata daƙuwa "Ungo naki Raudah, na ce ungo na ki, yanzu dani za kiyi maganar ankon ƙawayen ki? Ah lallai kam zamani, sai ki jira idan angon ya zo kuyi maganar tun da ku ta shafa" Mommy na gama faɗar haka ta fice a ɗakin, tashi Raudah ta yi ta nufi daƙin ta, gado ta haye ta buɗe data, sai gani kawai tayi an saka ta a wani group mai suna "Raudah's bride maid's", murmushi ta yi ɗan ta san wannan aikin fa'iza ne, ai kuwa tana shiga ta duba ta ga duk ƙawayen da take bukata ne a ciki, cousin's ɗin ta kawai ta adding a ciki, sannan suka fara shirye-shiryen yadda biki zai kasance. Misalin ƙarfe takwas na dare Raudah ta shirya cikin wata maroon color ɗin abaya, stones ne a jikin ta tun daga sama har ƙasa,sai walwali ta ke yi da ɗaukar ido, ba ta yi kwalliya ba domin bata da ra'ayin hakan duk da Noor ya ce ta yi amma fa ita ba zata yi ba, kawai so ya ke ya takura ma ta, head band ta dakko shima maroon ta saka, da ɗan kunne, sai gyalen abayar da ta yafa, maroon ɗin flat shoe ta saka sannan ta fashe jikin ta da turarruka masu ƙamshi, Masha Allah dan ba karamin kyau ta yi ba, kamar ka sace ta ka gudu, fitowa ta yi parlour, a nan ta tarar da Mommy, Arya da saleem, Mubasheer ne kaɗai baya nan, Arya littafi ne a hannun ta, Mommy ma haka, da alama assignment ta ke koya musu ganin ba'a kunna tv ba. "Mommy bari na je Noor na jira na a waje". A dawo lapiya Mommy ta ma ta, Arya ce ta ajiye littafin da ke hannun ta, ta je kusa da ita ta na cewa "Anty zan biki", ba tare da Raudah ta ce komai ba ta kama hannun ta suka fita waje, yana tsaye a jikin motar shi ya saka kaftan Black colour, ba karamin kyau suka mai ba, saboda shima Noor kyakyawa ne, jingina ta yi da jikin motar ita ma tana gaishe shi, amsa wa ya yi ya miƙa ma Arya hannu yana faɗin "Little zo mana mu gaisa", da sauri Arya ta karasa kusa da shi, hirar su suke ta yi da Arya, hirar ba ta komai ba ce face school, satar kallon Raudah ya yi, yaga tana ta lanƙwasa ƙafa alamun ta gaji, motar ya buɗe ya ciro chocolate ya ba Arya, cike da farin ciki ta ce "Thank you uncle" tana gama faɗar haka ta shige cikin gida da sauri tana ƙwalawa Saleem kira. Juyowa ya yi ya kalli Raudah, ba karamin kyau ta mai ba, murmushi mai sauti ya yi, bai ce mata komai ba, kuma a irin yanayin shi ba zai ce ta yi kyau ba, dama ta saba in dai Noor ne, da wuya kayi abu ya yaba, shi yasa ta ke jin daɗin Dee komai ya gani ya yi ta koɗawa kenan, koda abin bai ma ta kyau ba har sai ta ji ya shiga ranta, gaishe shi ta yi amma sai da ya ja wasu seconds sannan ya amsa, shiru ne ya biyo baya daga bisani ya ce "Amarya ba kya lefi, ko kin kashe dan masu gida inji hausawa", murmushi Raudah ta yi da jin maganar da ya faɗa sannan ta ce "Uhmmm su ango manya", dariya ya yi sannan ya ci-gaba da faɗin "Dama nazo ne muyi magana na ji mene ne shirye-shiryen ki, kwana biyu ban samu zama ba ne, tunda daddy ya zo, sai da ya tafi yau da safe sannan na dawo dai-dai, kin san daddy sai a slow, sai ya saka ni a gaba ya ce duk inda za shi sai na raka shi, bayan ya san ina da schedules ni ma" "Allah sarki ashe daddy ya zo, ban ma sani ba, ko da yake na ma manta yaushe rabon da muyi waya da kai", Raudah ta faɗa cike da damuwa "Kiyi hakuri Amarya, abubuwan ne sai a hankali kema kin sani" Noor ya bata amsa cike da ƙwarin gwiwa, da uhmmmm kawai ta amsa daga nan bata ƙara cewa komai ba, shima shirun ya yi, sai da suka kwashe wajan minti biyar a haka sannan Noor ya katse shirun da cewa "Raudah mene ne shirye-shiryen ku? Ina so na sallame ki ne gaba ɗaya tunda kinga yadda abin ya zo, ko da ya ke ai dama chan exams din ki ne ya ke ja mana delay, amma komai ya zama ready, amarya kawai na ke jira ko da yake inaga da yanzu kin aihu" Mamaki ne ya kama Raudah ganin irin zumuɗin da ya ke yi, tunowa ta yi da wani lokaci da suka taɓa hirar event da Besty ya ke faɗa ma ta abinda ya ke so ta yi a bikin ta, murmushi ta yi sannan ta ce "Anko za mu cire jibi, za muyi henna party, friends of honour, kamu shikenan, kai mene ne shirinka?" "Ah ni ba abinda zanyi, friends ɗina ne za su haɗa mana dinner, daga nan shikenan, amma ba damuwa ki tura min list ɗin abubuwan da kike so sai na tura miƙi kuɗin, shikenan"? Bata ce komai ba ta illa ɗaga kai da ta yi, daga nan suka ci-gaba da hirar su, sannan ta mai sallama ta shigaa gida ganin dawowar Abba tun dazu. Fadeelah bata farka ba sai karfe uku, salati ta yi sannan ta miƙe zumbur kamar wacce aka tsikara da allura, kallon ɗakin tayi bata ga kowa ba, tashi ta yi sai taji wajan ya ɗan rage zugi amma dai tana ɗingisa ƙafa, toilet ta shiga ta ƙara gasa wajan kamar yadda taga ya mata dazu sannan ta yi wanka, a ranta tana tunanin a haka zata koma gida? Kar fa Anty ta gane, da wannan tunanin ta gama wanka ta fito, ganin Adnan ta yi a kujerar da ke chan gefen ɗakin, ba ta ce mai komai ba sai ya taso ya nufo inda ta ke "Besty har kin tashi? Nima na gangara ƙasa siyan kati" "Eh na tashi ka mayar da ni gida kaga yamma tana yi" "To shinkenan shirya mu tafi" Bayan ta gama shirya wa ne suka fito, duk da haka tana ɗingishi, kallon ta ya yi sannan ya ce "Sai fa kin gyara tafiyar ki Fadeelah kada Anty ta fahimci wani abu" da kyar ta saita ƙafar saboda ko yaya ta haɗa su sai wajan ya ma ta zafi, amma haka ta daure suka tafi, suna isowa junction ya ajiye ta kamar yadda ya ɗauke ta, godiya ya mata tare da kalamai na soyayya sannan su kayi sallama ya tafi, da kyar ta iya karasa wa gida. Da sallama ta shiga, a tsakar gida ta iske Anty na wanke-wanke, karasa wa tayi ta ƙarba, taba faɗin "Sannu da gida Anty" "Sannu Fadeelah kin dawo?" "Eh na dawo", ta bata amsa suka ci-gaba da wanke-wanken, suna gamawa Fadeelah ta tashi ta nufi hanyar ɗakin ta, kamar daga sama ta ji muryar Anty tana cewa "Keee Fadeelah me ya same ki? Wacce irin tafiya kike yi haka?".... Fan's yau fa asirin Fadeelah zai tonu, chabb ko yaya zata kaya gashi Anty kamar ta gano an ɓarar da darajar...... VOTE COMMENTS SHARE ✍️ BADAWEEYERH 💐💐S͆A͆N͆A͆D͆I͆N͆ B͆E͆S͆T͆Y͆ 💐💐 L͆a͆b͆a͆r͆i͆/R͆u͆b͆u͆t͆a͆w͆a͆✍️ R͆A͆B͆I͆'A͆T͆U͆ A͆H͆M͆A͆D͆ M͆U͆A͆'Z͆U͆ (R͆U͆B͆B͆Y͆) G͆a͆j͆e͆r͆e͆n͆ l͆a͆b͆a͆r͆i͆ (S͆h͆o͆r͆t͆ s͆t͆o͆r͆y͆) M͆y͆ w͆a͆t͆t͆p͆a͆d͆ l͆i͆n͆k͆👇🏻 https://www.wattpad.com/1190086089?utm_medium=link&utm_source=android&utm_content=share_published 💐💐💐💐💐💐💐💐 Dᴇᴅɪᴄᴀᴛᴇᴅ ᴛᴏ Mʏ ʟᴏᴠᴇʟʏ ᴍᴏᴍ (Hᴀᴊ Rᴜᴋᴀɪʏʏᴀ), Aʟʟᴀʜ ʏᴀ ƙᴀʀᴀ ᴍɪᴋɪ ʟᴀғɪʏᴀ ᴅᴀ ɴɪꜱᴀɴ ᴋᴡᴀɴᴀ ❤️❤️ Sᴘᴇᴄɪᴀʟ ɢɪғᴛ ᴛᴏ Kᴀɪɴᴜᴡᴀ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀᴛɪᴏɴ Aʟʟᴀʜ ʏᴀ ƙᴀʀᴀ ʜᴀᴅᴀ ᴋᴀᴡᴜɴᴀɴ ᴍᴜ ᴀ ᴅᴜᴋ ɪɴᴅᴀ ᴍᴜᴋᴇ 🤗 *____________________________________* *🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼* *🇦SSOCIATION🤝🏻* ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation *_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻 https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association *____________________________________* PⒶⒼⒺ 1️⃣3️⃣ Kiɗimewa Fadeelah ta yi cikin in ina ta ce "Anty ogan mu ce ta sani mopping shine na zame a kan tyles na faɗi" gaba ɗaya ta ruɗe da kyar ta iya haɗo ƙaryar ta bada amsa, kallo Anty ta bita da shi cikin tausayi ta ke faɗin "Subhanallah!!! Sannu Allah ya ƙara sauki, akwai pain relief a ɗaki ki ɗauka ki sha sai ki kwanta". Da to ta amsa ta wuce ɗakin Anty ta sha maganin, fitowa ta yi ta koma ɗakin ta, ta chanza kaya, sai da tayi sallar la'asar sannan ta kwanta nan da nan wani baccin ya kuma kwashe ta. Adnan yana kan hanayar shi ta koma wa gida ya haɗu da wata yarinya sanye da hijabi har kasa, yarinyar Black beauty ce tana goye da jakar baya, kallo ɗaya Adnan ya ma ta ya ji zuciyar shi ta kamu da sonta, tafiya ta ke cikin nutsuwa wanda hakan ya ƙara jan hankalin Adnan, kokarin tsayar da ita ya ke yi amma sam ta ƙi tsayawa, a haka ya dinga bin ta a baya har ta iso wata unguwa ta masu rufin asiri, dai-dai wani matsakaicin gida ta tsaya, knocking ta yi aka buɗe ma ta, ta shiga, duk da ta ga wannan mai mashin ɗin yana bin ta hakan bai sa ta tsaya ba, wani yaro Adnan ya gani ya kira shi yana tambayar shi, "Ɗan samari wannan yarinyar a anguwar nan ta ke?" "Eh nan ne ma gidan su" yaron ya faɗa yana nuna gidan da ta shiga, "Mene ne sunan ta"? Adnan ya ƙara tambaya "Zeenat" yaron ya faɗa har a lokacin yana wasan shi, godiya Adnan ya ma yaron, sannan ya juyar da mashin ɗin shi ya tafi, a zuciyar shi yana ta murna da zumuɗi, shifa ya samu matar aure, ɗan gaskiya wannan yarinyar yaga alamun tana da tarbiyya kuma irin macen da ya ke so ce, cikin farin ciki ya karasa gida ba tare da ya anƙara ba. Washe gari da safe Noor ya tura ma da Raudah ƙuɗaɗe masu yawa, sai da ta faɗa ma Mommy dukkan shirye_shiryen su ita da ƙawayen ta, Mommy ta ƙara bata wasu shawarwari, Hajiya Salimah bata samu zuwa a ranar da ta ce zata zo ba, washe gari sai gata niƙi-niƙi da kayan mata ingantattu da magungunan sanyi masu kyau da inganci,wanda ta saka a ka haɗo musu a wajan shahararriya kuma ƙwararriyar likitar mata, wadda ta shahara wajan sanin duk wani magani mai saka ni'ima da kuma ɗanɗano,gwana ce sosai a fagen sanin sirrin kula da jiki ciki da waje ma'ana mai kara mayar da mace cikakkiyar mace ta hanyar ƙwato ma ta daraja da ƙima a wajan oga, a gefe guda kuma maganin sanyin ta ma ba'a bar shi a baya ba wajan magance ko wanne irin nau'in sanyi, sanyi na ciki da na waje duk tafiya su ke yi su bar ki ki shana, ba wata bace face MAMAN YUSUF wacce ake ma laƙabi da (Dr mata ko kuma likitar Mata) ƴar mutan sokoto, (duk mai bukatar kayan ta ya tuntuɓe ni). Cikin kwanaki ukun da Raudah ta yi tana amfani da maganin sanyi ba ƙaramin daɗin jikin ta ta ji ba, ita ƙanta ta ji chanjin da bata sani ba a tattare da ita, dama da maganin sanyin zata fara amfani kafin tayi amfani da sauran, a cikin satin suka je cire anko ita da fa'iza da kuma Maryam, fa'iza ƙawar ta ce Maryam kuma cousin ɗin ta ce, sun ciro anko masu kyau sossai, ko a cikin group ɗin bikin ta da suka tura ma freind's din santi suka dinga yi, dama kwata-kwata su goma ne ƙawayen, cousin's din ta huɗu sai sauran kuma freind's ɗin ta, duk abinda ta ke yi sai ta tuntuɓi besty sun yi magana, ko da Noor ya turo ma ta da outfit ɗin dinner sai da ta tura ma Besty, amma Besty na gani ya ce basu mai kyau ba, haka ta kira Noor ta ce a chanza basu ma ta kyau ba, "Haba Raudah basu miki ba fa ki ka ce? Ai naga is one of Ur best colour" Noor ya faɗa cike da ɓacin rai "Eh kawai bai min ba ne" ta bashi amsa a taƙaice, bai ƙara ce mata komai ba ya kashe wayar, wayar ta bi da kallo sai chan kuma ta girgizar kai tana faɗin "Ohoo dole a chanza min ɗan bai ma Besty kyau ba, tunda bai mishi kyau ba nima bai min ba", chatting ta ci-gaba da yi chan ta ji massage ya shigo tana buɗe wa ta ga wasu colours ɗin Noor ya turo ma ta, ba ta mai reply ba kawai ta tura ma Besty ta ce ya zaɓar musu duk wanda ya mishi... Sai da Fadeelah ta kwashe kwanaki biyu ta na jinyar jikin ta tukunna ta dawo dai-dai, tunda wannan abun ya faru Adnan sau biyu ya kira ta, ba kamar da ba, da a rana sai ya kira ta sama da sau biyar, wannan abu ba ƙaramin ɗaga ma ta hankali ya yi ba amma ta daure bata mai magana ba. Yau bayan ta gama aiki da safe ne ta kira shi, sai da ta kusan katsewa sannan ya ɗaga "Besty wai me na maka ne ka share ni? Tun ranar da abin nan ya faru sau biyu ka kira ni"? Fadeelah ta faɗa tana fashewa da kuka, shiru ya yi bai ce komai ba, sai da ta yi mai isar ta sannan ya bata haƙuri ya ce idan ta fito ta kira shi za su haɗu, ai kuwa jiki na ɓari ta shirya, Anty tayi ma sallama ta ce ta tafi shago, tana fita ta kira Adnan, nan da nan ya zo ya ɗauke ta zuwa hotel kamar yadda suka saba, wannan ƙaron ma sai da ya ƙara yin sex da ita, sai dai bataji zafi ba kamar na farkon, haƙuri ya bata na rashin kiran ta da bayayi saboda aiki ya mai yawa a yan kwanakin nan, sai yamma ya mayar da ita gida tare da alƙawarin zai zo gobe da daddare. Washe gari ne Fadeelah ta koma shago gudun kar Anty ta je shagon watarana bata ganta ba ko a ce bata zuwa, dan ta san Anty da bin ƙwaƙwafi, ai kuwa ta sha faɗa a wajan Madam Cynthia, aikin ranar gaba ɗaya ita ta yi shi, sai karfe shida ta koma gida, gaba ɗaya a gajiye ta ke, da kyar ta iya yin sallar magriba ta ci abinci, Adnan ta kira ya tabbatar ma ta da zai zo bayan isha'i, har zata katse wayar ya ce "Emm Baby yau kar ki saka kaya, hijab kaɗai za ki saka ɗan yau a matse na ke" Adnan ya faɗa har da kashe ido kamar tana gaban shi, da to kawai ta amsa mai sannan ta yanke kiran, tashi tayi ta nufi daƙi ta gabatar da Sallar isha'i, sannan ta saka wasu pant da bra masu kyau da ɗaukar hankali, katon hijab ta saka ta fesa turare a jikin ta. Misalin takwas da rabi Adnan ya kira ta ya sanar ma ta yana waje, sallama ta ma Anty ta fice, wajan rumfar shanu suka nufa ganin anguwar ba mutane kamar kullum, ciki ta shiga shi kuma ya tsaya ta waje, matsowa ta yi ta ɗaga hijabin, ai kuwa yana kyalla ido ya ganta hankalin shi ya tashi, wasanni suka fara yi sai da ya samu nutsuwa da ita ya ma ta sallama ya koma gida, itama gida ta koma cike da farin ciki domin tana son kasancewar su a irin wannan yanayin... VOTE COMMENTS SHARE ✍️ BADAWEEYERH 💐💐S͆A͆N͆A͆D͆I͆N͆ B͆E͆S͆T͆Y͆ 💐💐 L͆a͆b͆a͆r͆i͆/R͆u͆b͆u͆t͆a͆w͆a͆✍️ R͆A͆B͆I͆'A͆T͆U͆ A͆H͆M͆A͆D͆ M͆U͆A͆'Z͆U͆ (R͆U͆B͆B͆Y͆) G͆a͆j͆e͆r͆e͆n͆ l͆a͆b͆a͆r͆i͆ (S͆h͆o͆r͆t͆ s͆t͆o͆r͆y͆) M͆y͆ w͆a͆t͆t͆p͆a͆d͆ l͆i͆n͆k͆👇🏻 https://www.wattpad.com/1190086089?utm_medium=link&utm_source=android&utm_content=share_published 💐💐💐💐💐💐💐💐 Dᴇᴅɪᴄᴀᴛᴇᴅ ᴛᴏ Mʏ ʟᴏᴠᴇʟʏ ᴍᴏᴍ (Hᴀᴊ Rᴜᴋᴀɪʏʏᴀ), Aʟʟᴀʜ ʏᴀ ƙᴀʀᴀ ᴍɪᴋɪ ʟᴀғɪʏᴀ ᴅᴀ ɴɪꜱᴀɴ ᴋᴡᴀɴᴀ ❤️❤️ Sᴘᴇᴄɪᴀʟ ɢɪғᴛ ᴛᴏ Kᴀɪɴᴜᴡᴀ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀᴛɪᴏɴ Aʟʟᴀʜ ʏᴀ ƙᴀʀᴀ ʜᴀᴅᴀ ᴋᴀᴡᴜɴᴀɴ ᴍᴜ ᴀ ᴅᴜᴋ ɪɴᴅᴀ ᴍᴜᴋᴇ 🤗 *____________________________________* *🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼* *🇦SSOCIATION🤝🏻* ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation *_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻 https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association *____________________________________* PⒶⒼⒺ 1️⃣4️⃣ Yau ya rage saura sati ɗaya bikin Noor da Raudah, kuma a yau ne aka kawo lefen Raudah gidansu, lefe ne na gani na faɗa, sosai Raudah ta ji daɗin kayan domin Noor ya gwangwaje ta, a waya ta kira shi ta mai godiya, ko da ta nuna ma Besty bidiyon kayan ta waya shima ya taya ta farin ciki ga shi dama duk wani kayan da ta ɗinka sai da ta siya ma Besty shadda colour ɗin kayan, wasu kuma ƙananan kaya ta siya mishi saboda ta ce bikin nasu ne. Ranar Laraba aka yi henna party inda ƙawayen suka saka lifaya bayan an kammala musu lalle ja da baƙi, sosai suka yi kyau cikin lifaya kalar sararin samaniya, ita kuma amarya ta saka baƙa, musamman aka kira Bebeji mai hoto ya zo ya musu hotunan, Masha Allah don duk wanda ya ga hotunan sai ya yaba domin sun yi komai cikin tsari da wayewa, a gidan Anty Salimah suka yi henna party ɗin, tun da Besty ya ga hotunan Raudah ya ke koɗawa cewar tayi kyau, ba abin da ta ke yi illa murmushi da jin daɗi ko ba komai ya wanke mata baƙin cikin Noor domin shi da ta tura masa emojin murmushi kawai ya aiko mata wanda hakan ba ƙaramin baƙanta ranta ya yi ba, washe gari Alhamis su kayi freind's of honour, nan ma amarya da ƙawayenta sun sha kyau har sun gaji, kuma Besty ya halarta, ko da Noor ya ga hotunan su tare da Besty ran shi ba karamin ɓaci ya yi ba amma ya danne a cewar shi kwana nawa ne ta zama mallakinsa. Ranar Juma'a suka yi kamu a flourish event center, amarya Raudah da angonta Noor sun sha kyau sosai, duk motsin da Noor zai yi sai ya galla ma Besty harara, shi kuma sai ya yi murmushi ya waske, Raudah na kula da yanayinsu amma ba ta ce komai ba, a haka aka saka Raudah a lalle, sai a lokacin ne gabanta ya fara faduwa ganin fa da gaske gobe ne auren, nan da nan jikin ta ya yi sanyi, a haka dai aka yi kamun aka gama amarya ta koma wata shiru-shiru, ai kuwa dangi suka saka ta a gaba da tsokana wai munafurci ne ita dai bata iya cewa komai, sai wata matar abokin Abba ce mai tare ma ta. Washe gari ya kama Asabar da misalin ƙarfe biyu da rabi dubanin jama'a suka shaida ɗaurin auren Nuradden Mukhtar Baba tare da amaryar sa Raudah Adam a babban masallacin ƙofar fada, a kan sadaki naira dubu ɗari da hamsin, bayan an gama ɗaura auren ne ango ya dinga gaisawa da jama'a yana washe baki kamar wanda aka ma gafara, can na hango Besty shima ya sha shadda blue sai ɗaukar ido ta ke yi yana ta hura hanci, a lokacin ne kuma Besty ya kira Raudah ya sanar da ita an daura, "Amarya ayuriri!!! Yau kin zama matar aure" Besty ya faɗa cike da zolaya, kuka Raudah ta fashe da shi hakan ya sa ya kashe kiran saboda ba zai iya jurar jin kukanta ba, daga nan wajen cin abinci aka nufa inda aka ci aka sha aka yi hani'an.... Misalin ƙarfe biyar na yamma jerin motocin ɗaukar amarya suka tsaya a daidai ƙofar gidansu Raudah, a lokacin tana tsugunne gaban dangi tana rusa kuka, addu'ar zaman lafiya mai ɗorewa ake mata daga nan Anty Salimah da Anty Hassana ƙanwar Abba suka kama ta suka kai ta ɗakin Abba, shi da abokansa da kuma yan'uwansa ne a ciki, nasiha mai ratsa jiki suka yi mata sannan aka fito da ita aka nufi wajen Mommy, addu'ar zaman lafiya da zuri'a ɗayyiba Mommy ta bi 'yarta da shi, da ƙyar aka ɓamɓare Raudah daga jikin Mommy zuwa cikin mota, har aka dangana ta da katafaren gidanta da Noor ya gina mata ba ta daina kuka ba, kowa sai santin gidan ya ke yi, a haka aka shigar da ita, daga nan kuma aka fara shirin sallar magriba saboda daga gidan za a shirya tafiya wajen dinner. Wajen dinner ya cika da yan'uwa da abokan arziƙi ta kowane ɓangare, ango da amarya sun sha kyau har sun gaji, ranar kam an yi rawa da kuma watsi da kuɗi, da gangan Noor ya taka ma Dee ƙafa lokacin da ya shigo yi ma Amarya manni, shi har ga Allah ya tsani yaron, amma ba komai ai ya zo ƙarshe, abinci serve your self ne, can na hango Sanadin Besty Fan's 1 sun sha anko suna ta ɗibar kaza har da masu sakawa a leda nace to! Su kuma waɗannan gayyar wa? Ban gama mamaki ba na hango Sanadin Besty Fan's 2 suma an ba su fili suna taka rawa na ce yau kam Raudah'n Besty an sha gata, ta ba da Sanadin Besty Fan's sun miki kara, sai dai fa sun kwashi gara. Ba'a tashi a dinner ba sai ƙarfe shabiyu na dare daga nan kowa ya watse ya koma inda ya fito, ƙawayen amarya kuma aka mayar da su gidansu Raudah saboda Abba ya ce babu mai kwana ba ya son wanan ƙaƙalen kawai a bar ango ya shiga gidanshi... Adnan kam soyayya mai ƙarfi ce ta ƙullu a tsakanin shi da Zeenat, domin har ya kai kuɗin aure an saka rana, bai da wani buri da ya wuce ya same ta a matsayin mata, ya ma manta da wata Fadeelah don ko ta kira shi a waya ba ya ɗagawa, shi ya sa ta ɗan daga mai ƙafa kwana biyu. Yau Fadeelah ta tashi da matsanancin ciwon kai, ga zazzabi, ko'ina a jikinta rawa yake, ga shi komai ta ci sai ta amayar, gaba ɗaya ta galabaita, ganin zazzaɓin ya ƙi sauka ne ya sa Anty ta shirya ta suka tafi asibiti, bayan likita ya gama mata aune-aune ya miƙa ma Anty result yana faɗin "Congratulations, tana ɗauke da ciki tsawon sati shida" "Ciii meee?" Cewar Anty ta faɗa tana zazzaro ido, tabbatar mata da cewa Fadeelah na da ciki likita ya yi, jin haka ya sa Fadeelah ƙwalla wani uban ƙara ta faɗi ƙasa sumammiya... **** **** **** A daren da aka kai Raudah Noor bai mata komai ba saboda kulle ƙofar ɗakinta da take yi kamar yadda Besty ya ba ta shawara, ai kuwa ba ƙaramar ƙuluwa Noor ya yi ba, amma ya tabbatar da cewa duk randa ta shiga hannunsa za ta gane ba ta da wayo, a haka sai da ta shafe sati ɗaya tana kulle ƙofar idan dare ya yi, ranar kuwa da ya sace ta ya riga ta shiga sai da ta faɗa ma masu anguwan garinsu, don sai da ya sauke ma ta sannan ya samu nutsuwar, kwana Raudah ta yi tana kuka, daga bisani kuma ta warware suka ci gaba da shan soyayyarsu kamar za su mayar da juna ciki, sai yanzu ne ta kuma tabbatar ma da kanta cewa tana ƙaunar Noor fiye da tunaninta, duk da halayen shi na i don't care ba wai ya daina ba ne, ganin shi ba mai irin wannan ra'ayin ba ne ya sa ta rage damun kan ta.... Satin su uku da aure kullum sai ta yi ma Besty ƙorafin ya ƙi zuwa, yau dai ya yanke shawarar zai zo, bayan ya sanar da ita, murna fal a ranta ta tashi ta hau gyare-gyare da soye-soye, wanda tun da aka kawo ta ba ta taɓa yi ba, bayan ta kammala komai ne ta sakawa gidan turaren wuta ai tuni ya baɗe da ƙamshi, wanka ta yi a gurguje sannan ta shirya cikin wani material, ɗinkin gown ne amma ya mata kyau sosai, ba ta daɗe da zama ba sai ga kiran Dee a wayarta, gate ta je ta buɗe mai kasancewar har yanzu ba su da mai gadi, tun daga wajan gate ta fara zuba mai shagwaba har suka yada zango a parlour'n, bayan ya huta ne ta zuba musu abinci suka fara ci a tare, a dai-dai lokacin ta ji kar'ar buɗe gate, dammm gabanta ya faɗi ta ce "Innalillahi wa inna ilaihir rajiun, na shiga uku Noor ya dawo" gaba ɗaya ta rikice domin zuwan ta da kwana biyu a gidan ya ji tana waya da Besty, ai kuwa ya zaunar da ita ya zana ma ta serious warning, kuma ta masa alƙawarin ba ita ba Dee, wannan dalilin ne ya sa hankalin ta ya tashi saboda ba ta yi tsammanin zai dawo da rana ba tunda sai biyar suke tashi a office . Shi kam Dee bai ma san tana yi ba kazar shi kawai ya ke ci kamar wani sabon mayunwaci, ci ya ke cike da kwanciyar hankali, cikin siririyar murya Noor ya yi sallama ya buɗe kofar parlour'n ya shigo, kasa ko da ƙwaƙwaran motsi Raudah ta yi jin har ya gama shigowa, bin inda ta ke Noor ya yi da ido ganin ko sallamar tashi ma yau ta kasa amsawa, kallon gafenta ya yi ai bai san lokacin da ya yar da jakar hannun shi ba, ƙarawa ya yi bakin shi na rawa ya ce "Kai me ya kawo ka gida na wajan matata"? Noor ya tambaya yana nufar inda Dee ya ke, bai tsaya wata-wata ba ya shaƙo wuyan shi yana ci gaba da faɗin: "Oh ƙawancen naku bai tsaya a waje ba har sai ka biyo ta cikin gidanta na aure? Ko da ya ke ba laifinka ba ne laifinta ne da ta ba ka wannan damar" nufar inda Noor ya ke Raudah ta yi, tana ƙoƙarin cire hannun shi a wuyan Dee da ya shaƙe saboda ta lura Besty'n ma ya kasa magana sai numfashi da ya ke fitarwa sama-sama, tsoron kar ya illata shi ne ya sa ta je ceton shi, ai kuwa tana saka hannu Noor ya wanka mata mari, sannan ya hankaɗa Dee saman kujera ya fara jibgar shi kamar wanda Allah ya aiko, sai ihu ya ke kwararawa sai da hannun Dee ya bada sautin ƙas alamun ya karye kenan, a gigice Raudah ta nufi inda Noor ya ke ganin dukan da ya ke mai kamar baya cikin hayyacin shi, ai kuwa idon shi ya rufe ba ya ji ba ya gani, kamo hannunsa Raudah ta yi tana cewa: "Yanzu Noor so kake yi ka kashe shi? Haka kawai babu abin da ya maka ka rufe shi da duka? Wannan ai zalinci ne.." Ai ko kafin ta ƙarasa sai jin duka ta yi, dukan ta ya ke ba ji ba gani yana faɗin: "Ni ne azzalumin? A kan wannan ɗan iskan ki ke kira na da azzalumi? Oh wato bai min komai ba na dake shi? To ki rama mai, na ce ki rama mai"! A zafafe ya ƙarasa maganar yana ƙara marin na ta, ihu take yi iya ƙarfinta amma ba mai ceto, sai da ya yi mai isar shi sannan ya zauna ya na mayar da numfashi, shi yasa baya so ranshi ya ɓaci saboda bai iya ɓacin rai ba, duk abin da aka mai yana ƙoƙarin danne fushinsa, saboda idan ya yi fushi shi kanshi yana shan wahala, da ƙyar ya iya tashi ya je wajen fridge ya sha ruwa sannan ya dawo ya kwashe su zuwa asibiti.... *** *** *** Zeenat amarya sai chushe-chushe ake yi, ga wani rashin kunya da ya ke ƙaruwa a kanta, sai rawar kai ta ke yi ita ga amarya, ita da ƙawayenta sun haɗa party a ɓoye, wanda za a fara tun takwas na dare har safiya wanda suke kira (till down), a ɓangaren ango Adnan ma sai rawar kai ya ke yi shi da su Farouk da sauran abokansa, iyayensa kuwa sun saki bakin aljihu sun haɗa lefe na gani na faɗa an kai gidan su Zeenat, iyayen Zeenat irin masu son abin duniyan nan ne kuma ba sa ma Zeenat faɗa, sosai iyayenta suka gwangwaje ta da furniture's na gani na faɗa, sosai suke shirye-shiryen bikin. Ranar Asabar da misalin ƙarfe sha ɗaya da rabi dubanin jama'a suka shaida ɗaurin auren Adnan da Zeenat a kan sadaki naira dubu ɗari, farin ciki ne kwance a fuskar Adnan, sai dariya ya ke yi domin kuwa yau mafarkin shi ya zama gaskiya, Zeenat ta zama mallakinsa, Allah ne kaɗai ya san yawan son da ya ke wa yarinyar domin tana da nutsuwa da kamun kai abin da ya fi fisgar shi a wajen mace kenan, shi kam ya gama dacewa da mace a duniya. Ƙarfe biyar na yamma aka raka amarya Zeenat zuwa ɗakin mijinta tare da rakiyar manyan gogaggun ƙarshen ta, sai santin gidan su ke yi tare da ma ta lakca da huɗubar banza wanda ta hau kai ta zauna to dama abu ya haɗu da halinta, ba su bari an rako ango ba suka watse bayan sun ja gefe da wata babbar ƙawar ta ta bata kwalli da wasu ƙwayoyi, daga ita sai cousin's ɗinta aka bari saboda Adnan bai san ta da ƙawaye ba. Basu wani ɓata lokaci ba aka tafi kai ango domin ya matsa musu ayi a raka shi wanda zumuɗin da yake yi sai da ya ƙular da Farouƙ, tsaki kaɗai Farouƙ ɗin ya ke ja yana faɗin: "Dalla Mallam kar ka dame mu! Ai ba a kanka aka fara aure ba ka zo sai wani rawar kai kake kamar kwaɗo". Cikin haɗe gira da jin haushin abin da ya faɗa Adnan ya ce: " Kawai ka ce haushin rashi ne, ko da ya ke yau kai ba sa'a na ba ne, i pass Ur level so I don't have Ur time, ai ban ce dole ka raka ni ba ko?" Farouk bai sake magana ba ya tashi ya shiga mita sauran abokan suka rufa musu baya, hira suke yi cike da nishadi har suka ƙarasa gidan Adnan, bayan raha da barkwanci a tsakanin su da yan'uwan Zeenat, kuɗi suka basu sannan suka mayar da su gidan iyayen Zeenat ɗin kasancewar a can za su kwana, Adnan na ganin tafiyar su ya rufe get, ya koma ciki, har yanzu Zeenat na zaune a kujerar da ya bar ta, bakinsa ya ƙi rufuwa, cike da jin daɗi ya ke faɗin: "Amarya ba kya laifi, to ki tashi ki shiga toilet ki canja kaya mana na ga waɗannan sun miki nauyi, ni ma bari in je ɗakina in shirya kar na takura miki ko?". Kai ta ɗaga ba tare da ta ce komai ba shi kuma ya juya ya fice, tana ganin ya fita ta shiga toilet ta gama abin da za ta yi gudu-gudu ta shafa kwallin da ƙawarta ta ba ta sannan ta fesa wani farin abu a gabanta, fitowa ta yi ta ƙara buɗe jakarta ta ciro wani garin magani ta zuba a cikin humra ta jijjiga sannan ta bi kowanne lungu da saƙo na jikin ta da humrar, wasu fingilalun kayan bacci ta saka, komai na jikin ta ana gani sannan ta ɗora hijabi a kai, zama ta yi a bakin gado tana dakon jiran ango Adnan. Ko da Adnan ya gama abin da zai yi, ɗakin Zeenat ya koma cike da murmushi, a bakin gado ya tarar da ita tana danna waya, cike da kulawa ya ƙarasa gefen ta yana kamo hannunta haɗe da shafa cikin ta yana faɗin: "Baby babu komai a cikin nan na ki, farin ciki ya hana ki cin abinci ko?" Ya ƙarasa maganar yana lakuce ma ta hanci. Murmushin jin daɗi Zeenat ta yi domin kuwa yadda ya ke ma ta yawo da hannayen shi a cikin ta ba ƙaramin daɗi ta ke ji ba, tun daga tsakiyar kanta har tafin ƙafarta saƙon yake isa, zamewa ta yi ƙasa ta zauna ganin haka ne ya sa ya sakko shi ma ya fara bata abinci ita ma tana bashi, ko kunya ba ta ji ba, a nata ganin ai anyi mai wuyar tun da an yi auren, sai da suka ƙoshi sannan ya kwashe plates din zuwa kitchen ta shiga toilet ta kuskure baki, yana shigowa shima ya je ya wanke baki, kafin ya fito ya iske har ta kwanta, wutar ɗakin ya kashe ya kunna mara haske sosai sannan ya haura saman gadon ya janye bargon da ta rufa, hijabin jikinta ya cire ai kuwa idanun shi suka ci karo da ƙirjinta, tuni idanunsa suka kaɗa, kuma turaren da ta shafa ya fara fisgar shi, lumshe idanu Zeenat ta yi cike da jin daɗi, Allah-Allah ta ke yi ya jefa ƙwallo a raga ta ji ya yake, shima gaba ɗaya ya gigice a haka ya rabata da komai na jikin ta ya ci-gaba da ma ta wasanni masu tada hankali, ganin ba za ta iya jurewa ba ya sa ta fara mayar mai da martani, bai ma kula da abin da ta ke mai ba saboda gaba ɗaya ya fice a hayyacin shi, ga wani soyayyarta da ke ƙara ƙaruwa, a haka ya samu ya shige ta, sai dai ya tsaya jimm jin ƙofar a buɗe, ko da an yi wasu kwaskwarima hakan ba zai hana shi gane macen da aka taɓa buɗewa ba, wani nauyi ya ji a zuciyar shi, ji ya ke kamar ya fasa ihu amma ina ya kasa ƙarasawa, haka ya zare jikin shi, kamo shi ta ƙara yi suka haɗa ido, nan da nan- ya ji komai ya gudu a ƙwaƙwalwarsa, ci gaba ya yi da sarrafa ta yadda ya ke so ita kuma sai jin daɗi ta ke yi na ganin komai ya tafi yadda ta tsara.. Taimakon gaggawa likitan ya fara ba ma Fadeelah, sai da suka kwashe tsawon awa ɗaya sannan aka samu numfashinta ya dawo, ban da kuka ba abin da Anty ta ke yi tana faɗin: "Shikenan Fadeelah kin cuce ni, yanzu sakayyar da za ki min kenan? Duk irin yadda na ke faɗi-tashi a kanki amma sai da kika ɗauko mana abin kunya? Innalillahi wa inna ilaihir rajiun, Allah na tuba ", haka Anty ta ke ta maimaitawa cikin baƙin ciki da ƙunar zuciya, ita kaɗai ta san me ta ke ji a cikin zuciyarta, da ƙyar wata nurse ta ja ta gefe ta rarrashe ta sannan ta tsagaita da kukan, jira kawai take yi Fadeelah ta farka ta faɗa ma ta wanda ya aikata ma ta wannan aika-aikar, ko da ya ke ai ba laifin shi ba ne, da ba ta ba da kanta ba ai hakan ba za ta faru ba, ga shi yanzu ta ja musu masifa suna zaman-zaman su cikin rufin asiri. Sai da Fadeelah ta kwashe awanni wajen biyar sannan ta farka, cikin firgici da ihu, bubbuga gadon take yi tana miƙewa jin hakan ya sa Anty da ke bakin ƙofa ƙarasowa da sauri, tana shiga ta tarar da ita a wannan yanayin tsawa ta daka ma ta tare da faɗin: "Dalla ki mana shiru munafuka, koma mene ne ai ke kika jawo, tun da kin zama ballagaza jaka, wallahi Fadeelah kin cuce mu", ta ƙarasa maganar kuka na kufce ma ta, ita ma Fadeelah kukan take yi ta na cewa: "Tabbas Anty na cuci rayuwata, Adnan ya cuce ni, Innalillahi wa inna ilaihir rajiun wannan wace irin masifa ce?" Matsowa Anty ta yi gadan-gadan kamar zata dake ta ko me ta tuna kuma sai ta fasa, juya wa ta yi ta tsaya a dai-dai saitin window hawaye na zubowa a idanunta, yadda take ji a zuciyarta ko ta daki Fadeelah ba hucewa za ta yi ba, babban abin takaici ma wai wannan ɗan iskan yaron mai ido a tsakar ka, yaron da ba ya ganin mutuncin mutane, ita kam ina zata saka rayuwarta? Haka dai ta yi ta saƙe-saƙe a cikin zuciyarta, ganin ta rasa mafita ya sa ko kallon inda Fadeelah take kuka ba ta yi ba ta fice gaba ɗaya a ɗakin. Waya ta ɗauka ta kira mijinta kasancewar ba mazauni ba ne ta faɗa masa abin da ya faru, cikin kuka take faɗin: "Yaya Fadeelah ta cuce mu, ta kasa riƙe mutuncinta, ciki fa ta yi, ina zamu kai wannan abin kunyan? Ni wallahi na rasa yadda zan yi ma". Daga ɓangaren shi shiru ya yi sai da ta gama bayani sannan ya ce: "Ki yi haƙuri ki daina kuka, ƙaddara ce amma kuma duk da ganganci, ki kwantar da hankalin ki insha'Allah gobe ko jibi zan taso sai mu san yadda za a yi, amma kafin nan dan Allah kar ki ce ma ta komai", sai da ya tabbatar da hankalin ta ya kwanta sannan ya ma ta sallama ya ajiye wayar cike da mamakin abin da ƙanwar matar ta shi ta aikata, yana ma ta kallon mai wayo ashe shashasha ce... Kwanan Fadeelah uku a asibiti a ka sallame ta a ɗan wannan lokacin jikin na ta ya yi kyau sai dai damuwa da ya ramar da ita, tsakanin ta da Anty kuwa sai dai kallo don ko ta ma ta magana ba amsawa ta ke ba, a haka dai suka tattara suka koma gida, kuma har a lokacin mijin Anty bai dawo ba, rayuwa ta ma Fadeelah tsauri, ko kaɗan Anty ba ta raga ma ta... Ango Adnan kam sai zuba soyayya a ke yi da Amarya Zeenat, ba ta bari ya fita ko nan da can, gaba ɗaya gajiyar da shi take amma ya kasa ce ma ta komai, tsabar tsanar ta ce a kwance a ƙasan ranshi amma bakinsa na mai nauyin furta ma ta, ga shi bai isa ya sa ta abu ta yi ba sai dai ta balbale shi da masifa ta na faɗin ita fa ba 'yar aiki ba ce, ko girki ba ta yi sai dai kullum ya siyo musu, ga ƙazanta kamar me, cikin wata ɗaya da aure Adnan ya rame, sai idanu, kana ganin shi ka ga mai damuwa amma ba zai iya furta wa ba, wani sabon abu ma da Zeenat ta tsira shine fita da ta ke yi kullum ba tare da izinin shi ba, ga shi bai isa ya ma ta magana ba sai ta hau shi da masifa wai yana takura ma ta, tsakanin shi da ita yanzu sai idanu... Noor na isa asibiti ya kira Abba ya sheda mai abin da ya faru sannan ya ƙarasa ya kira nurses, ba ɓata lokaci aka karɓe su kasancewar asibitin mahaifinsa ne, cikin ƙanƙanin lokaci aka ba su taimakon gaggawa, Besty kam ya jigata sosai kasancewar ya bugu da gefen kujera ga kuma karaya a hannun shi na dama, naɗe wajen aka yi da bandeji bayan an gyara karayar hannun da ƙyar, sannan aka mai allura ya koma baccin wahala, ita kuwa Raudah allura kaɗai aka ma ta kasancewar suma kaɗai ta yi, Noor ya na ƙofar ɗakin da Raudah ta ke a tsaye, haushin ta yake ji sosai, gani yake kamar wani abu ya shiga tsakanin ta da Dee, sam ya ji ba ya ƙaunar ganin ta, ana cikin haka Abba da Mommy suka ƙaraso asibitin a tare, don Noor na gama faɗa wa Abba a lokacin ya na kasuwa shi ma ya kira Mommy hankali tashe, a bakin titi Mommy ta jira shi ya zo ya ɗauke ta suka wuce cike da fargaba, ran Abba ba ƙaramin ɓaci ya yi ba, wato Raudah ba ta jin maganar shi kenan, duk faɗan da ya ma ta a banza ta yi auren ma ba ta rabu da wannan tantirin yaron ba, haka su ka tsaya cirko cirko a asibitin ba wanda yake iya magana, sai bayan isha'i sannan Raudah ta farka, ƙin shiga ɗakin Noor ya yi sai mommy ce ta shiga a lokacin Abba bai dawo daga masallaci ba. Ko da Mommy ta shiga ta tarar da Raudah a kwance idanunta biyu amma hawaye na tsiyaya a fuskarta, ko a mafarki ba ta taɓa zaton Noor zai iya dukan ta ba, lallai ta san ta kai shi maƙura, tsinkar muryar Mommy ta yi ta na cewa: "Ai ba ki ma yi kuka ba, bari Abbanku ya shigo za ki faɗa mana uban me wannan yaron ya je yi gidanki na aure", Ƙara sautin kukan Raudah ta yi don ta tabbatar yau kashinta ya bushe, babu abin da zai hana Abba dukan ta, ita babbar damuwar ta ma Noor ganin ba ta gan shi a ɗakin ba, tunowa ta yi da abin da ya faru sai ta ji duk duniya ba wanda ta tsana kamar Dee don ko sunan shi sai ta ji ya ma ta ɗaci, yau a kan shi mijinta da take matuƙar so kuma yake son ta, mai haƙuri da kawaici ya sa hannu ya dake ta? Ko da ya ke ba ta laifinsa ba ne, don ko ita ce abin da za ta yi kenan ko zuciyarta za ta ji sanyi, babbar damuwarta ma shi ne kallon da Noor zai ma ta, ba ta da wata mafita, kuma duk abin da za ta faɗa ba lallai su yarda da ita ba, ita yanzu babbar matsalar ta ma bai wuce Noor ba ta ga har yanzu bai shigo ba, numfashi mai ƙarfi ta ƙara ja tana mai kallon Mommy, ganin Mommy ta ƙi kallon ta ne ya sa ta rufe ido tamkar mai bacci. Ko da Besty ya farka ba wanda ya zo ya duba shi sai nurses da ke sintiri, kanshi har yanzu bai daina sara mai ba, ya yi nadamar kasancewar shi Besty, a ranshi yake faɗin "me ma ya kai ni gidanki Raudah? Ga shi nan na ja ma kaina" ganin ya kasa ɗaga hannun shi ne ya duba ya ga hannu a nannaɗe hakan ya tabbatar mai da har karya shi Noor ya yi, nurse ce ta shigo ta ƙara duba shi sannan ta ƙara mai allura, roƙon ta ya yi ta kira mai mahaifiyar shi, bayan ta kira ne ya shaida ma ta yana asibiti, ba shiri ta tashi ta yafa gyale ta taho wajen Dee kasancewar shi ne yaron su ɗaya tal da Allah ya ba su, ko da ta iso ta ga yadda jikin nashi ya yi bayan ya labarta ma ta abin da ya faru faɗa ta hau shi da shi tana faɗin: "Innalillahi wa inna ilaihir rajiun!! Kamaludeeni yaushe ka zama kwarto?" Ta tambaya cike da mamaki, da ƙyar Dee ya iya ɗago idanunsa da suka kumbura saboda yadda kan shi ya ke mai ciwo ya ce: "Haba Mama kwarto kuma? Kawai ƙawata ce fa shi ne na je na gan ta" ya faɗa yana juyar da kan shi gefe domin ba ma ya son ƙara tunawa, faɗa sosai Mama ta dinga mai kamar ta aro baki sannan ta fita waje ta kira mahaifinsa ta sanar da shi, shima ba shiri ya bar aikin ginin da ya ke yi ya taho asibitin, ko da mahaifiyar Dee ta labarta mai abin da ya faru tashi ya yi ya fice daga ɗakin yana cewa "Allah shi ƙara" tun da shi ya ja wa kan shi. A haka suka kwashe tsahon kwana uku a asibitin kuma har yau Noor bai shiga ya ga jikin Raudah ba, Abba dai ya duba ta sau biyu amma har yanzu bai ce komai ba, babu wanda ya san tana asibiti a cikin familynsu saboda Abba ya ce wanann labarin ba abin sanarwa ba ne, Mommy na kula da rashin shigan Noor duba Raudah amma ba ta ce mai komai ba, kullum a asibitin yake wuni kuma duk abin da ake buƙata shi yake yi, shima a ɓangaren 'yan gidansu bai sanar da kowa ba, kullum Raudah sai ta yi kuka tana ce ma Mommy dan Allah ta kira ma ta Noor amma ko kallo ba ta ishi Mommy ba sai dai ta bata amsa da cewa "ai ke kika ja ma kanki ba wani ba" . A zaman da suka yi a asibitin ne mahaifin Raudah suka haɗu da mahaifin Dee har suka tattauna sosai, ɗan zaman da suka yi har sun saba tare da samar wa da kan su mafita, mahaifiyar Dee ce ma ta lura da shige da ficen su Abba a asibitin shi ne ta tambayi wata nurse, yadda nurse din ta ma ta kwatance cewa tare wani ya kawo su da wata mace hakan ya tabbatar ma ta da ita ce matar da Dee ya je gidanta, shi ya sa ta faɗa wa mahaifinsa shi ne ya nemi Abba suka yi magana kuma alhamdulillah domin kuwa sun fahimci juna yadda ya kamata, mahaifin Dee ya so su haɗu da, shine Abba ya sanar wa da Noor din amma da ke har yanzu bai huce ba, ya na ganin mahaifin Dee sai ya canza waje . Ko da aka sallami su Raudah gidansu Abba ya mayar da ita da kan shi, ta ji sauƙi ba laifi, a ranar shi ma Dee mahaifinsa ya ce a sallame su saboda sun gaji da zaman asibitin shi dama karayar da ya yi ne da buguwar da ya yi a kai ba su warke ba wannan kuma sai a hankali, Abba ne ya biya ma Dee kuɗin asibiti saboda Noor ƙin biya ya yi na matarsa kaɗai ya biya ya juya ya bar asibitin, shi kaɗai ya san yadda yake ji a zuciyarsa. Yana son ganin Raudah amma fushin da yake yi da ita ba zai bar shi ya iya ganin ta ba... Bayan kwana biyu da dawowar su iyayen Dee suka zo tare da Dee gidan domin yin zama na musamman a tsakanin su, da ƙyar Noor ya yarda ya zo don ma yana jin kunyar Abba ne, a babban falon Abba suka zauna, bayan zaman su da kamar minti goma sai ga Raudah ta shigo sanye da farin hijabi har ƙasa, suna haɗa ido da Noor gabanta ya faɗi ganin yadda ya rame sosai kamar ba shi ba, sauke idanunwan ta tayi ƙasa tana tafiya a hankali har ta kai gefen da Noor ya ke ta zauna a ɗan gaba da shi, juyawa ta yi ta hango Dee a ƙasa a gefen ƙafar mahaifin shi dama ta san iyayen shi domin yana saka su a status, kallo ɗaya Noor ya ma ta ya ɗauke kai kamar bai ganta ba, haka kawai sai ya dinga jin haushin ta, Uncle Babangida ne ya buɗe taro da addu'a sannan ya fara da musu nasiha tare da nunar musu yadda addini ya tsara macen da ya kamata ka yi mu'amala da ita da kuma namijin da ya kamata ka yi mu'amala, da haramcin kula wadda ba muharramarka ba da kuma wanda ba muharraminki ba, kuka kawai Raudah take yi saboda jin yadda Allah ya tanadar ma da masu irin halayen ta azaba amma ta biye wa son zuciya, jikin Dee ya mutu murus kuma tun ba yau ba ya yi nadamar abin da ya yi, Abba ne ya katse Uncle Babangida da faɗin: " Raudah kin ba ni kunya, tun da ki ka taso a gidan nan har kika mallaki hankalin kan ki kin taɓa ganin wani wanda ba ki sani ba ya zo da sunan shi abokin mahaifiyarki ne?" Girgiza kai Raudah ta yi ba halin magana Abba ya ci-gaba da cewa: "Ko kin taɓa gani na da wata da sunan ita ɗin ƙawata ce?" Nan ma dai girgiza kai ta yi sannan ya ce: "Oh to sai ke tsabar shashasha ce ke, ba ki san inda yake miki ciwo ba shi ne za ki biyewa son zuciya da wata shegantaka da sunan wayewa wai Besty ko? To ai gashi nan kina nema ki ɓalle auren ki da hannunki, kuma wallahi wallahi wallahi kin ji rantsuwar musulmi in dai Nuruddeen ya rabu da ke to sai dai wani gidan ba nawa ba". Yana gama faɗar haka ya ja bakinsa ya yi shiru ai Raudah na jin kalmar rabuwa ta ƙara fashewa da kuka ba wanda ya ce mata komai sai da tayi mai isar ta sannan ta yi shiru, mahaifin Dee ya ɗora da faɗin: " Ni na rasa me zan ce ma wallahi, Alhaji, Hajiya dan Allah kuyi haƙuri dama shi ya sa na ce gwara mu taru mu yi magana ta fahimta, waɗannan yara sam ba su kyauta ba sun yi rashin hankali kuma wannan ba tarbiyyar musulmi ba ne kuma ni wallahi abin da mijin yarinyar nan ya yi ya min daidai domin kuwa ko ni ne zan yi fiye da haka ma" sai ya juya wajen da Dee ya ke ya ce " kai kuma na dawo gare ka mutumin banza mutumin wofi, wallahi wallahi idan baka fita a harkar 'yar mutane ba sai ranka ya ɓaci kai kasan karon mu da kai ai, ba kai ba ita na faɗa maka, ko da wasa na sake jin makamanciyar hakan kai ko ba a kan ta ba ko a kan wata ce na haramta maka zama Besty idan ka ƙi kuwa za ka gane ba ka da wayo". Share hawaye Dee ya yi sannan ya ce " don Allah don Annabi ku yafe min insha'Allah ba zan sake ba tun daga ranar da abin ya faru na yi nadama kuma insha'Allah ko a kan wata ma ba zan ƙara zama Besty ba domin a "SANADIN BESTY" aka karya min hannuna, hannun da har yanzu ya ki ɗauruwa", ya ƙarasa zancen hawaye na ƙara zubo mishi, rarrafawa ya yi ya je wajen Noor ya roƙe shi gafara a taƙaice, ya amsa mai sannan ya nemi yafiyar Raudah da iyayenta, shi da zama Besty har abada, haka aka musu katangar ƙarfe mai ƙarfi tare da gindaya musu sharuɗa na musamman, sannan ita ma Raudah ta nemi yafiyar iyayen ta da mijinta saboda ta san ta kai su bango tun da har suka iya jure yin fushi da ita, tana hango fushin da Noor ya ke yi a cikin ƙwayar idanunsa amma ya ta iya? Ba ta ankara ba ta ga ba kowa a ɗakin daga ita sai Noor ashe duk sun watse, gefen Noor ta je ta kamo hannunsa tana kuka a lokaci guda ta na cewa: "Ka yi haƙuri mijina sharrin shaiɗan ne ba zan sake ba, Please forgive me" kallon ta ya yi da rinannnun idanunsa ya ce: "Why Raudah? Why? Me na miki haka da za ki saka min da wannan? Na dawo gida na na ganku da wani, wani fa Raudah?" Fashewa Raudah ta yi da matsanancin kuka ganin ba zai iya jure saurarar kukan nata ba ya sa shi ficewa daga parlour'n ya bar ta a wajen... Bayan dawowar mijin Anty da kwana biyu suka tusa Fadeelah a gaba zuwa gidansu Adnan da ke ya taɓa kai ta gidan ta jira shi ya ɗauko abu ya fito, korar kare iyayensa suka musu kasancewar suna da kuɗi sosai, sai a wajen mai gadi suka samu lambar Adnan ɗin da ƙyar, a ƙofar gidan mijin Anty ya mai kira har guda uku amma bai ɗaga ba hakan ya sa suka tafi zuwa police station kai ƙarar Adnan, motar police ɗaya aka haɗo su da shi ta biyo su har gidansu Adnan ɗin aka sanar da mahaifinsa, motar shi ya shiga ya bi su station ɗin yana iƙirarin duk wanda ya ma ɗansa sharri sai ya yi Shari'a da shi, 'yan sandan ne suka ba shi umarnin ya kira Adnan ai kuwa yana liƙe da Zeenat suna ta faman abu ɗaya kiran Daddyn ya shigo da ƙyar ta bari ya fito a gidan bayan ta gindaya mai sharuɗa..... VOTE COMMENTS SHARE ✍️ BADAWEEYERH 💐💐S͆A͆N͆A͆D͆I͆N͆ B͆E͆S͆T͆Y͆ 💐💐 L͆a͆b͆a͆r͆i͆/R͆u͆b͆u͆t͆a͆w͆a͆✍️ R͆A͆B͆I͆'A͆T͆U͆ A͆H͆M͆A͆D͆ M͆U͆A͆'Z͆U͆ (R͆U͆B͆B͆Y͆) G͆a͆j͆e͆r͆e͆n͆ l͆a͆b͆a͆r͆i͆ (S͆h͆o͆r͆t͆ s͆t͆o͆r͆y͆) M͆y͆ w͆a͆t͆t͆p͆a͆d͆ l͆i͆n͆k͆👇🏻 https://www.wattpad.com/1190086089?utm_medium=link&utm_source=android&utm_content=share_published 💐💐💐💐💐💐💐💐 Dᴇᴅɪᴄᴀᴛᴇᴅ ᴛᴏ Mʏ ʟᴏᴠᴇʟʏ ᴍᴏᴍ (Hᴀᴊ Rᴜᴋᴀɪʏʏᴀ), Aʟʟᴀʜ ʏᴀ ƙᴀʀᴀ ᴍɪᴋɪ ʟᴀғɪʏᴀ ᴅᴀ ɴɪꜱᴀɴ ᴋᴡᴀɴᴀ ❤️❤️ Sᴘᴇᴄɪᴀʟ ɢɪғᴛ ᴛᴏ Kᴀɪɴᴜᴡᴀ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀᴛɪᴏɴ Aʟʟᴀʜ ʏᴀ ƙᴀʀᴀ ʜᴀᴅᴀ ᴋᴀᴡᴜɴᴀɴ ᴍᴜ ᴀ ᴅᴜᴋ ɪɴᴅᴀ ᴍᴜᴋᴇ 🤗 *____________________________________* *🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼* *🇦SSOCIATION🤝🏻* ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation *_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻 https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association *____________________________________* 💐💐S͆A͆N͆A͆D͆I͆N͆ B͆E͆S͆T͆Y͆ 💐💐 L͆a͆b͆a͆r͆i͆/R͆u͆b͆u͆t͆a͆w͆a͆✍️ R͆A͆B͆I͆'A͆T͆U͆ A͆H͆M͆A͆D͆ M͆U͆A͆'Z͆U͆ (R͆U͆B͆B͆Y͆) G͆a͆j͆e͆r͆e͆n͆ l͆a͆b͆a͆r͆i͆ (S͆h͆o͆r͆t͆ s͆t͆o͆r͆y͆) M͆y͆ w͆a͆t͆t͆p͆a͆d͆ l͆i͆n͆k͆👇🏻 https://www.wattpad.com/1190086089?utm_medium=link&utm_source=android&utm_content=share_published 💐💐💐💐💐💐💐💐 Dᴇᴅɪᴄᴀᴛᴇᴅ ᴛᴏ Mʏ ʟᴏᴠᴇʟʏ ᴍᴏᴍ (Hᴀᴊ Rᴜᴋᴀɪʏʏᴀ), Aʟʟᴀʜ ʏᴀ ƙᴀʀᴀ ᴍɪᴋɪ ʟᴀғɪʏᴀ ᴅᴀ ɴɪꜱᴀɴ ᴋᴡᴀɴᴀ ❤️❤️ Sᴘᴇᴄɪᴀʟ ɢɪғᴛ ᴛᴏ Kᴀɪɴᴜᴡᴀ ᴡʀɪᴛᴇʀ'ꜱ ᴀꜱꜱᴏᴄɪᴀᴛɪᴏɴ Aʟʟᴀʜ ʏᴀ ƙᴀʀᴀ ʜᴀᴅᴀ ᴋᴀᴡᴜɴᴀɴ ᴍᴜ ᴀ ᴅᴜᴋ ɪɴᴅᴀ ᴍᴜᴋᴇ 🤗 *____________________________________* *🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼* *🇦SSOCIATION🤝🏻* ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation *_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻 https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association *____________________________________* PⒶⒼⒺ 1️⃣5️⃣ (Last page) Ko da ya iso police station ya ga Fadeelah sai da gabansa ya faɗi, shi ya ma manta da ita Wallahi, tana ganin shi ta tashi ta cukume rigarsa tana ihu tana faɗin: " Ka cuce ni Adnan haƙiƙa na ga "SANADIN BESTY" Wannan abin kunyar ina zan kai shi?" Haka dai take ta sambatu da ƙyar aka ɓamɓare ta a jikinsa, bayan DPO ya saurari bayananta ne ya tambayi Adnan shin da gaske ne? Shiru ya yi bai ce komai ba Daddy ya ce: "Ka yi magana Adnan ba shiru za ka yi ba mutanen nan so suke su ƙulla maka sharri, shirun ka ba mafita ba ne don wallahi muddin sharri suke maka sai na ɗaure su", mahaifin Adnan na ta kumfar baki ya tsinkayi muryar ɗansa yana faɗin: "Daddy ciki na ne, tabbas Fadeelah budurwa ta ce kafin na yi aure". "Aure? Aure fa ka ce ?" Fadeelah ta faɗa da ƙarfi saboda kalmar ta razana ta, Adnan ya ci gaba da cewa: "Gwara na faɗa maka gaskiya daddy cikina ne a jikinta ba sharri take yi min ba" A zabure Daddy ya tashi yana cewa "ko ka sha ƙwaya ne Adnan? Ina kai ina yarinyar nan mai zubin mayu? To wallahi ka dawo cikin hayyacinka don ba a gidana ba", yana gama faɗin haka ya miƙe zai tafi, DPO ne ya tsayar da shi ta hanyar nuna masa illar abin da yake yi gwara a bi komai a hankali kada mutuncinsu ya zube, da haka ya koma ya zauna suka tattauna yadda zasu ɓullo ma lamarin, shi dai Adnan ban da ƙyarma babu abin da jikinsa ya ke yi domin minti talatin Madam Zeenat ta ba shi ga shi an hura awa ɗaya yanzu, yana ta jin vibration ɗin wayarta amma ya kasa ɗagawa, matsaya aka samu a kan cewa zai ɗauki nauyinta har sai ta haihu, kuma duk wani dawainiya shi ne zai yi, godiya mijin Anty ya yi wa DPO suka koma gida, ita kam Fadeelah kuka kawai take yi da nadamar abin da ta aikata , ko a yanzu Adnan ya gama da ita ya ma ta illar da ba za ta taɓa gogewa a jikin ta ba, ta bi son zuciya ai kuwa yau ta tabbatar da "SANADIN BESTY" ta ga babban darasi a rayuwarta. A haka rayuwa ta ci gaba da tafiya yau da daɗi gobe babu har cikin Fareedah ya shiga wata huɗu, ba ƙaramar wahala cikin yake bata ba, ga shi mijin Anty ya koma, tsakanin ta da Anty kam abin ba sauƙi, tana gida babu inda take zuwa kuma tun daga ranar da suka je police station har yau Adnan bai sake zuwa ba, tsananin da ta ke ciki ne ya sa ta fara tunanin hanyar da za ta bi ta zubar da cikin, Google ta shiga ta fara browsing ai kuwa ta ci karo da magani kala-kala ba tare da tayi tunanin komai ba ta rubuta su a wata yar ƙaramar takarda ta ɓoye, tunanin inda za ta samu kuɗi ta yi, can sai ta miƙe tana murmushi ta nufi dakin anty domin ta ji fitar ta daga gidan, purse dinta ta buɗe ta ga kuɗi a ciki dubu biyu ta zara sannan ta fice a gidan, machine ta hau ta tafi wani babban pharmacy ta siyo maganin ta dawo, dama sun saba siyar da illegal magani a wajen shi ya sa ba tare da tunanin komai ba suka bata, gida ta koma ta ƙara duba yadda ta ga an rubuta a wayar yadda za tayi amfani da shi ai kuwa haka ta yi amfani da shi tana mai farin cikin za ta rabu da wahala.. Zaman Zeenat kam da Adnan abin ya ci tura, ba wanda yake iya zuwa gidan domin amarya ta hana, shi kam ya ma zama mijin kan ta ce domin kuwa mugun tsoron ta yake ji, ko ba ta ce ya yi abu ba sai ya yi jikinsa na rawa, sai dai ta tara ƙawayen banza su yi ta shaye shaye har maza suke tarawa a gidan, tun da an mayar da mai gida hoto, Farouk ne ya yanke shawarar zuwa ya ga abokin nasa tunda ko wajen aiki ma ba ya zuwa, ai kuwa zuwa ya yi ya tarar da shi kwance ba lafiya ita kuwa uwar gantali ta fita da ƙawaye ta bar shi jiran gida. Asibiti Farouk ya kai shi, a nan aka ba shi gado sannan aka diɓi jininsa don a yi masa gwaji domin gano me ke damun shi, sai dai gwajin farko likita ya tabbatar wa da Farouk cewa abokinsa na ɗauke da cuta mai karya garkuwar jiki wato (HIV), ƙiris ya rage Farouk bai faɗi a gaban likita ba, haka ya kira Daddyn ya sanar da shi suna asibiti, ko da suka iso shi da mahaifiyar Adnan results ɗin ya basu ba tare da ya ce komai ba, zufa daddy ya shiga sharewa yana maimaita kalmar innalillahi a fili, ɗakin da aka kwantar da Adnan suka shiga yana bacci shi kam bai ma san wainar da ake toya wa ba, zaune suke jugum jugum, can mahaifiyarsa ta ce: "Farouk ni kam ina Zeenat? Na ga tun da muka zo ban gan ta ba?" "Mommy wallahi ni ma ko da na je gidan ban tarar da ita ba, shi na samu zazzaɓi ya rufe shi, shi ne na kawo shi asibiti. Ina ganin ta je unguwa ne" Farouk ya ba ta amsa domin shi kam ya san halin da abokinsa yake ciki, kawai ba zai iya faɗa musu ba ne. Haka suka zauna a asibitin cike da damuwa don mahaifiyarsa sai kuka take yi, jira kawai suke ya farka su ji daga gidan uban wa ya kwaso wannan ciwo, ai shi Farouk tun da ya ji wannan maganar hankalinsa ya dawo jikinsa, sai istigfari yake yi yana neman gafarar Allah , shi kam ma aure zai yi kar shima ya jono ma kansa masifa. Raudah na zaune a gidansu tsawon lokacin nan ba wanda ya ce mata koma gidanki, abin duniya duk ya ishe ta ta rasa makomar aurenta, ko ta kira Noor ba ya ɗagawa, kullum sai ta tsine ma Besty a fili da zuciya, ta yi nadama mara adadi ga shi ba ta jin daɗin jikinta, komai idan ta ci sai ta yi amai, lura da haka ne ya sa Mommy ta sanar da Abba suka kira wata likita a unguwarsu mai suna DR. Zainab ta gwada ta, ai kuwa gwajin farko ta tabbatar musu da zaman ciki a jikinta, farin ciki a wajen Mommy da Abba ba a magana, nan da nan suka rungumo 'yarsu suna saka mata albarka kuka ta fashe da shi, bayan DR. Zainab ta tafi take ce musu: "Shikenan Abba Noor ya tsane ni, ga shi ina ɗauke da cikinsa, na san ya daina so na, kuma komai daren daɗewa zai rabu da ni" ta faɗa tana kuka kamar ranta zai fita , Mommy ce ta buga bayanta tana cewa: "Ki yi haƙuri Raudah, Noor yana son ki, ya yi hakan ne don ganin kin shiryu kuma mu ma mun ba shi goyon baya don mu ga ko kin hankalta, kuma tabbas kin yi nadama insha'Allah Noor zai zo ya gan ki kuma za ki koma ɗakinki kin ji? Gata muke miki" hannu Mommy ta sa ta share mata hawaye sannan Abba ya fita ya siyo maganin da Dr ta rubuta mata, kunu Mommy ta dama mata ko da ta sha sai ta ba ta magani sannan ta kwanta , nan da nan barci ya yi awon gaba da ita. Abba ne ya kira Noor ya shaida masa albishir, ai ba shiri ya taho gidan cike da farin ciki, Mommy ce ta ce ya shiga ɗakin Raudah'n don ya sa Mommy a gaba yana ta sunkuyar da kai, ai kamar jira yake yi ya miƙe har da ɗan gudunsa ya shiga, barci ya tarar da ita tana yi , hayewa saman bed ɗin ya yi ya kama kissing ɗin ta, kamar a mafarki Raudah ta ji ana ma ta kiss, tana buɗe ido ta ga Noor nan da nan hawaye suka fara zubo ma ta, harshe ya sa yana lashe mata yana faɗin: "Haba maman baby kar ki sa baby ya ce na ci zalin mamansa, i am sorry! ko kishi ne ya rufe min ido na yi abin da na yi amma ki yi haƙuri komai ya wuce tashi mu koma gida", ƙoƙarin miƙar da ita yake yi ta noƙe, fita ya yi ya je ya samu Mommy ya ce "umm amm...Mommy zan tafi da ita gida tana buƙatar kulawa", ya faɗa yana sosa kai, murmushi Mommy ta yi tana faɗin Allah ya tsare hanya ga ka ga ta nan, tashi ya yi ya koma ɗakinta ya haɗa mata kayanta da maganin da Dr ta bata suka yi wa Mommy sallama ya mayar da ita gidansa, ai kuwa a ranar ta durzu kuma ta sha gata, ita ma ta zage ta nuna mai soyayya domin ƙara samun matsayi a zuciyarsa, Noor haka ya dinga kiran yan'uwansa yana sanar da su labarin cikin Raudah kowa ya yi farin ciki har mahaifinsa da mahaifiyarsa da kansa ya faɗa musu, addu'a suka musu da fatan Allah ya sauke ta lafiya, haka dai suke rainon cikinsu cike da soyayya da tattalin juna. A gadon asibiti Fadeelah ta farka, ganin hannunta ana mata ƙarin jini ya sa ta rufe ido tana ƙoƙarin tuno abin da ya faru, ta dai san ta sha magani ta kwanta, can kuma ta ji mararta kamar za ta fashe daga nan ta ƙwalla wata ƙara ba ta sake sanin inda take ba sai yanzu, Anty ce a gefenta tana share hawaye, kamo hannunta Fadeelah ta yi tana faɗin: "Anty da kin bar ni na mutu, rayuwata ba ta da amfani sam, na cuci kaina, kullum cikin baƙin ciki nake, rayuwata ba ta da wani amfani" ita kan ta Anty kuka take yi sai yanzu ta yi nadamar ƙin jan ƙanwarta ta a jiki da ba ta yi ba, ga shi nan a garin zubar da cikin ta sha magani ba bisa ƙa'ida ba har ta rasa mahaifarta gaba ɗaya, nasiha mai ratsa jiki Anty ta yi mata tare da nuna ma ta muhimmancin yarda da ƙaddara, sannan daga bisani ta faɗa mata matsalar da zubar da cikin ya ja ma ta, domin ita ma Anty ta shigo kenan daga unguwa ta gan ta kwance cikin jini shi ne ta kwaso ta zuwa asibiti da ƙyar aka tsayar da jinin, Allah Ya yi tana da nisan kwana ne amma da yanzu wani labari ake ba wannan ba, sosai jikin Fadeelah ya ƙara sanyi da lamarin duniya ta san Adnan ya gama da ita ya kuma cuce ta, haka dai ta zauna a asibiti aka yi ta jinya har ta samu sauƙi suka tattara suka koma gida ... A ɓangaren Adnan kuwa ko da ya farka babu wanda ya iya faɗa masa halin da yake ciki, sai dai mahaifiyarsa ta saka shi a gaba ta yi ta kuka, ya rasa abin da zai ce ma ta, idan ya tambaye ta sai ta ce ba komai, Zeenat neman shi take cike da tashin hankali, don babu wanda ya sanar da ita inda yake ga shi boka ya ce kada ta yarda ya yi nisa da ita na tsawon awa arba'in da huɗu, komai zai iya lalacewa, hankalinta sam baya jikinta, shi kam jin shi yake sakayau, ko da mahaifiyarsa ta tambaye shi ina Zeenat ɓata rai ya yi domin ba ya son jin ko sunanta, sai da ya cika sati ɗaya a asibiti aka sallame shi, Farouk ne mai kwana da shi, direct gidansu aka wuce da shi sannan Daddy ya zaunar da Adnan ya faɗa masa halin da yake ciki, cikin firgici yake kuka da maimaita kalmar innalillahi a bayyane, ihu yake yana cewa Zeenat ta cuce shi, bai tsaya jiran kowa ba ya miƙe ya zari key ɗin motar Daddy da ke gefen kujera ya fice daga gidan a ɗari da talatin, bai tsaya a ko'ina ba sai cikin parlour'n gidansa, ai kuwa ya iske Zeenat da ƙawayenta suna ta rawa kamar yadda ya saba, ido rufe ya yi kanta gadan gadan bayan ya kunce belt din jikin shi, karfe belt ɗin ya samu ya dinga dukan ta da shi har sai da gefen idon ta ya fashe, ihu take amma babu mai taimako domin ƙawayen nata ma tuni sun tsere, sai da ya tabbatar ya mata illa sannan ya rubuta mata saki uku ya cilla ta wajen gidan ya rufe gidan ya yi gaba abin shi .... A haka dai rayuwa ta gangara abubuwa da dama sun faru ciki har da rasuwar Zeenat wadda ta yi hatsarin mota a yawon bin bokaye don su mayar da ita gidan Adnan, iyayenta sun yi baƙin ciki sosai da mutuwarta, shi kuma Adnan yana nan yana karɓar magani, kuma ya je gidansu Fadeelah ya roƙe ta gafara bayan ya sanar da ita halin da yake ciki, tana kuka ita ma take faɗa mai abin da ya same ta na rasa mahaifa da ta yi gaba ɗaya, yanzu ma wani ɗan maƙocin su Baba Saleh ne zai aure ta a unguwar yake matansa biyu ita ce ta uku, kallon ta Adnan ya yi ya ce: "Hmmmm lallai Fadeelah SANADIN BESTY bai haifar mana da komai ba sai sharri, har yau ina nadamar kasancewa ta a matsayin Besty domin na san abin da muka shuka a lokacin da muke ƙawance shi muke girba yanzu", a haka dai suka gama hira suka yafi juna ta koma gida... Bayan wata tara Raudah ta haihu inda ta haifi 'yarta mace santalleliya mai kama da Noor, shagali kam an sha a ranar sunan yarinyar nan, inda SANADIN BESTY FANS suka taka rawar gani a sunan nan, don kuwa shinkafar Noor kam haka suka saka buhu guda a gaba suka cinye, ko da Noor ya gan su a gefe suna harraka abinci harara ya dinga zabga musu, a haka aka yi shagali aka watse inda yarinya ta ci suna Hafsat wato ƙanwar Mamman Noor kenan.... Bayan shekaru goma, Wani na hango sanye da kakin soja da wata mace a gefensa sun shiga shopping mall, wata yarinya ya gani kyakkyawar gaske tana bin wani yaro da gudu za ta amshi teddy, buge shi yaron ya yi ganin ya buge baban mutum ya saka shi yin rau-rau da idanu yana cewa: "Sorry uncle, Hafsa ce ta ture ni", murmushi wanda aka kira da uncle ya yi ko kafin ya yi magana ya hango wata hamshakiyar mace a tare da wani babban mutum suna ƙarasowa wajan da suke, kallo ya bi ta da shi ya ce: "Raudah?" Tana dago kai ta ce "Dee" harara Noor ya zabga musu yana cewa: "Malama ki zo mu tafi ko?" Hannu Dee ya ba shi suka gaisa cikin wasa da dariya bayan sun gaisa yake tambayar Noor waɗanan yaran fa? Noor ya ce mai yaransu ne macen sunanta Hafsa, namijin kuma Muhammad, albarka ya sanya musu sannan shima ya gabatar musu da Fa'iza yarinyar da ya aura wata uku da suka wuce kuma yanzu two star ne shi a aikin soja, murmushi suka yi, nan take Raudah da fa'iza suka ƙulla zumunci, Dee ne ya biya musu kuɗin siyayyar gaba ɗaya sannan suka fito a tare kowa ya shiga motarsa zuwa inda ya fito... Anyi bikin Fadeelah da maƙocin su Sani kuma suna zaune lafiya da shi, duk da wani lokacin matansa na mata gorin haihuwa sai dai ta shiga ɗaki ta yi ta kuka, shi ma Adnan ya damu wata mata ya aura a asibitin da ya ke karɓar magani.... Zaman Raudah da Noor kam sai son Barka hankalin iyayenta a kwance, ƙannenta ma duk sun girma, wani lokaci idan suna zaune da Noor sai ta tuno da lokacin da Abba ya biyo ta ta shige bayi ta dinga zawo, sai Raudah ta yi dariya tana faɗin: "Ai SANADIN BESTY ya so ya raba soyyayya, da mun bi ta BESTY da yanzu Allah bai bamu yaranmu sanyin idaniyarmu ba". Dee ya ce "ai da kuwa na ga asalin SANADIN BESTY dan ni za a cuta, duk abin da Allah da ManzonSa suka hana to guje mai ya fi wayewar duk na banza ne". Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Alhamdulillah!!! Allah na gode maka da Ka ba ni ikon kammala wannan littafin, kuskuren da na yi a ciki Allah Ka yafe min, alkhairin da ke ciki Allah Ya sa da ni da ku duk mu amfana.. Waɗanda suka bibiya tun da na fara har na kammala ina godiya a gare ku matuƙa, Allah Ya bar zumunci.... Ina son ku sosai Fan's ɗina Sai mun haɗu da ku a sabon novel ɗina mai suna " SOYAYYATA DA KWAMARET" Kada ku sake a ba ku labari domin nashi salon daban yake .... ✍️ ᏒᎪbᎥ'ᎪᏆu ᎪhmᎪᎠ mu'ᎪᏃu (ᏒubbᎽ)💙 Downloaded from GNOVELS.COM.NG This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG For feedback and support Facebook : https://facebook.com/gnovels Twitter : https://twitter.com/gnovels Telegram : https://t.me/gnovels