Downloaded from GNOVELS.COM.NG This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG For feedback and support Facebook : https://facebook.com/gnovels Twitter : https://twitter.com/gnovels Telegram : https://t.me/gnovels 71 & 72 __sunjima ahakan kamun sumayya tafara raba jikinta danashi d'agowa yayi suka had'a Ido gira d'aya yad'aga Mata tareda kashe Mata Ido d'aya Yana murmushi Aiko tayi saurin mayarda fuskarta akirjinshi Dan wata muguwar kunyace tarufeta shiko murmushi kawai yayi yamik'e tareda d'aukar ta cak kamar jinjira yayi bedroom d'inshi da,ita kamun yashiga bathroom yahad'a musu ruwan wanka yadawo yad'auketa atare sukayi wanka dudda wurin wankanma anbata lokaci ana Sha,ani bayan sungama yak'ara d'aukota suka dawo d'akin yashirta dakanshi cikin wasu k'ananun sleeping dress Riga da wando masu laushi kana shima yasaka nashi sukayi kwanciyasu Kamar basafiyaba..sunjima kwance cikin farin ciki da kaunar juna tana mak'ale ajikinshi kamun taji saukar muryarshi Dede kunneta Yana fad'ar ""Allah yayimiki albarka k'anwata..saurin d'agoda kanta tayi dangani tayi Kamar bashine yayi maganarba Ido suka had'a yasakarmata lallausan murmushi tareda lakace Mata hanci Yana fad'ar""yadai 🤨 Batace komaiba se kallanshi datakeyi shimadin dai kallanta yakeyi Wanda dagani kasan santa yakasa b'oyuwa aidonshi.."ngd sosai sumyyy Allah yayi muki albarka yadda Kika bani farin ciki kema Allah yafaran tamaki yafad'a Yana shafa lafaffen cikinta..itako kallan yadda Dan k'aramin bakinshi kejuyawa Yana magana Kamar ba,acin bakin take fitaba. takefitaba Kamun tanisa tana k'ara shigewa jikinshi tace "ameen y Allah mujina. Wani k'ayatatcen murmushi yazeed yayi yanashafa kwantaciyar sumar kanta kamun yace "rigi mammiya bacci zakiyi?baki taturo gaba tana fad'ar nidai Allah barigi mammiya bace tafad'a tanasan saka Masa kukan shagwab'a yazeed kuwa cikin dariyar dakesan kwace Masa yace "to shikenan naji yi hak'uri autar dady tashi kiji magana zamuyi yafad'a Yana Dan d'agota dagajikinshi kartayi bacci..itadai komai bataceba se gyara kwanciyarta datayi ajikinshi.."sumayya yakira asalin sunanta domin tasan dagaske yake maganar.."na,am ta,amsa cikin mmki Dan Bata tab'aji yakira sunanta ba..shiru yayi kamar bazeyi maganaba kamun yace ""Tashi kigayamun miyakaiki kunkiyar asiri? Yoshe Kika zama Yar jarida bawanda yasani agidannan? Waya koya Miki harbi? Aina kikasamu bindiga? Yak'arasa tambayar duka Yana had'e fuska irin bawasa d'innan kamun yace "Kuma kibani kowacce ansa basena K'ara nanata miki tambaya ba sabida hakan nayi mikisu atare yak'arasa zancen Yana lumshe kyawawan idanuwansa domin duk yaga maganar tayimasa tsayi becika sanyin doguwar magana kamar hakaba.. Shiru tayi tana kallanshi kamun tafara magana kamar hakan""yah yazeed aikine yakaini kungiyar alokacin danashiga aikin jarida Kuma Abba da abbe sunsan nid'in Yar jaridar sirrice Amma su suka Hana nagayawa kowa tin lokacin danazo musu dazancen inasan nayi karatun..nisawa tayi kana tace ""tin lokacinda naji Kuna zance akan kungiyar kaida su yah sulaiman tin lokacin nayi niyar tayaku bincikenta Koda ba,asakaniba agun aiki segaya Kuma suka bani aikinna nafarko akan k'ungiyar ne Wannan dalilin yasani shiga jikinsu tahanyar ogansu Wandani alokacin bansan matsayibshiba kawai dai Naga picture d'inshi acikin jerin way'anda akabani ahakan nafara bincike akansa harna gano wani company nasa daganan nad'auki takadduna naje neman aiki agunsa cikin sa,a kuwa inazuwa nasameshi bayan yaduba takadduna seyake cewa zebani aikin dayafi Wannan na company idan inabukata sabida inada hankali dadai sauran zancenshi.. Nima Sena nuna mashi nafibukakar kowanne aikine zebani Akan Wannan daganan kuwa seyad'an Fara bugar cikina akan matsafa dakunma masu garkuwa da mutane Duk inda yabullomun nunamasa nakeyi ai wayannan mutanen sune Dede Dan inda anamusu abunda yadace bazasu rik'a cutarda mutaneba..ahakan dai munfi wata d'aya Yana bugar cikina kamun yakaini k'ungiyarsu daganan nace bazanyi tsafiba Amma zanyi aikidasu duk wani k'alubale dazasu shiga zanyi maganin abun hakanko akayi domin duk hukomomin kasashe dake neman farmakarsu dazarar sungayamin nake masu hanyar dazusu salwancemasu shiyasa suka K'ara yadda Dani sosai. Niko abunda yasa nake Hana afarmakesu banasu sukub'utane nafiso afarmakesu inda za,ahukuntasu Wannan dalilin yasa lokacin dakukabawa su yah Sameer aikin bincike akan kungiyar nake turumusu komai nasirrin k'ungiyar da b'oyayyar nomber sabida nasan komai. Bindiga Kuma nakane ad'akinka nake d'auka.. Ko lokacin da suke bibiyar alhaji atiku bayan angayamun nice nazo nadakatardasu domin idan suka shiga k'ungiyar nasan kashesu zasuyi..shiru tayi tana jiran abunda yazeed zece ganin kusan minti 5 beyi maganaba yasa tad'ago dakanta suka had'a Ido domin shimad'in ita yake kallo cikin matsanancin mmkin kalamanta kallanda baka isakafassara ma,anarsaba..ganin tayi shiru tana kallanshi yayi murmushi tareda d'aga Mata gira d'aya 🤨 alamar tambaya? Sarai tasan miyake nufi tinda yayi hakan Yana nufin taci gabane Amma bazeyi maganaba..aranta tace Aiko bazanci gababa sekayi maganar afilikuwa turo baki tayi gaba tanafad'ar kaifa katambeni Kuma inagayama kayi shiru kashareni tak'arasa zancen cikin kukan shagwab'a.."ohh y salamm yazeed yafad'a Yana dafe kansa kamun yak'ara janyota jikinshi Yana fad'ar Yi hak'uri my Queen kinji bashareki nayiba Ina saurararkine cigaba dazancenki kinji jarumata waya koya Miki harbi to? Ranarda Kika Hana su Sameer bin Wannan mutumin ai since harbinsu kikeyi tako,Ina Kuma gashi nagani jiya kina harbi kamar a Indian film harmakinfimu iyawa yafad'a Yana murmushi.. Murmushin itama tayi tana dukan k'irjinshi kamuntace ""ai lokacinda naharbesu ko motarsu ban harbaba sabida nasan kosuwaye aciki dagangan nake goce seti gudun mistake..harbi kuwa Yaya sulaiman ne yakoyamun.."meee? Yazeed yatambaya Yana zaro ido 😳 yace sulaiman fa? "Eh shine yakoyamun ai Yaya sulaiman beyi mmkin ganina Ina farbiba sedai yayi mmkin ganina ak'ungiya sabida lokacin danakeso nakoyi harbi gidansu nasameshi nacemai Dan Allah yakoyamun harbi inasan yin aikin kakine Kuma konace kukoyamin alokacin Bazaku koyamunba shiyasa nasameshi dafarko yak'i ya,amincewa domin cewa yayi aikin kakikam ba,acin kaninsu Mata ba seda yaga Ina kuka kana yace zekoyamin Amma badan nayi aikin kakiba Hako akayi muka Ware Rana yafara koyamun harbi harna,iya yakasance inazuwa koyadakaina kobayanan to kaji yadda akayi.."hummm tab dijam lallai tetee wato mukika Bari Muna muki kallan biri kina Mana kallan ayiba humm kasgiya najijina muki jarumata kinri k'ok'ari sosai yafad'a Yana matseta ajikinshi kamun yace ahh to Ina Kika samo sunan mayah? Ainaji ahakan suke kiranki. Hhhhhh dariya tayi kamun tace mayah sunanane ai sumayya Sena cire su d'in nabarshi anakarshen mayah kawai domin b'adda Kama Amma sabida tsaro ne badan tsoroba yawwa.. murmushi yayi Yana dungure Mata Kai kamun yace Ina zuwa nayi mantuwafa a perlon yafad'a tareda saukowa yabar dakin da kallo sumayya tabishi tanajin Kamar tamayardashi ciki danso..Yana zuwa yadawo hanunshi d'aukeda ledojinda yashigo dasu d'azu yazube akan bed tarkacen kayan makulashene aciki irin namasu ciki se Wannan abun daya saka acikin aljihunsa. Kwaso kayan sumayya tayi tasomaci tanamishi surutu shiko yazuba Mata Ido kawai yanakallonta seda yaga hankalinta yadan dawo kana yazaro key biyu acikin aljihunsa yakama hannun sumayya yasamaka kamun yabud'e Wannan kyakkyawan k'ok'on yafitoda wani had'd'en zoben gold se k'yalli yakeyi yasaka Mata ayatsa..dubawa tayi ganin cer key ne d'ayan Kuma batasan makullin miyebane yasa tad'ago tana kallanshi..shima kallanta kawai yayi tareda d'aga Mata gira d'aya 🤨 "Namiye yah yazeed? ""Murmushi yasakeyi kana yace Wannan gift d'in killacemun kanki dakijayine har izuwa gidana nasamu abuna lpy Ina alfahari dake matata Allah yayi miki albarka..itadai sumayya takasa cewa komai se Ido kawai datake binshi dasu..kallan d'ayan key d'in yayi kana yace Wannan Kuma gidan Dana ginane sabidake Kuma se Babu yabamu Wannan shine na mallakamiki abunki nabakishi sabida kinbani farin cikin dazan,iya saka Miki dakomaiba sedai addu,ata agareki bazata yankeba hark'arshen numfashina I love you so very much my tetee I really love you so much my happiness much love you more & more my life yafad'a Yana rungumeta tsam ajikinshi... Autar alheri ✍️✍️ 73 & 74 __wani irin farinciki ne yamamaye zuciyar sumayya Wanda yakasa b'oyuwa agareta yau itace yah yazeed kefurtawa kalmar so yau itace ajikin ya yazeed amatsayin matarsa Kuma abun alfaharisa itakuwa mizatayi wurin nunawa Allah godiyarta.. Shiru duk sukayi kowanne na sauraren numfashin D'an uwansa kamun yazeed yaji saukar hawanyen Sumayya ajikinshi..d'agota yayi cikin sauri Yana fad'ar ohh my God my tetee are you crying? Mayarda fuskarta tayi jikinsa tab'oye tana murmushi..shima shiru yayi Yana kallanta...sunjima ahakan harya fiddaran zatayi magana sekawai yaji saukar dadd'an muryarta tana fad'ar "I love you too ya yazeed I really love you so very very much ya sweet dream banada kalaman dazanyi anfani dasu wurin yimaka godiya ngd sosai mijina Allah ya barmun Kai har muk'arasa wayuwarmu Yayana Kuma abun alfaharina akowanne lokaci tak'arasa zancen tana k'ara shigewa jikinshi kamar Takoma cikinshi kamin tanisa tacigabada fad'ar"""My heart beat only for you sweetheart yayana tak'arasa zancen tana kissing d'in kunnenshi..wani numfashi yazeed yaja cikin matsanancin farin cikin kalamanta da mmki yake kallanta wani irin kallo yake bintadashi me wuyar fassarawa kallota yakeyi yanajin jini da zuciyarshi yadda suke k'ara bud'e duk wata gab'a data rage daga cikinsu suna Ida toshewa da soyayyar ta cikin zallar so k'auna shauk'i yake fad'ar""thank you so much babyna ked'in rayuwata sumayya nasoki tinkina cikin zanen goyonki nasoki tinbansan so nasoki tinbansan cewa kid'in mahad'in rayuwata bace duk abunda kikaga Ina muki lokacin sabida banaso kukusanceni ne muddin Kika rab'eni ko kad'an ne Sena Sha wahala narasa miyasa nakejin matsanancin feeling akanki tinbakida wayo ko hannuna Kika rik'a senayi wanka zanyi sallah kekuwa alokacin ba,abunda kikeso Kamar kihau jikina shiya nake d'aure miki fuska gudun Kar watarana girma yafad'i yak'arasa zancen Yana murmushi sa,annan yace kitina lokacin da Kika tsokano Khadija Kika hau bayana? d'agowa tayi fana kallanshi kamun tace "eh natina tana dariya..""humm ranar kinkusa kasheni domin kwana nanane akwai agaba Amma na azabtu aranar yafad'a Yana shafa kanta.."baki taturo gaba tana fad'ar ainima kadakeni Kuma naji zafi Sosai tafad'a cikin shagwab'a..murmushi yayi yanafad'ar to tuba nakeyi dad'ina.. murmushi itama tayi taba dukan k'irjinshi sukayi kwanciyasu ahakan can yazeed yace..""tetee..na,am tafad'a tana kallanshi.."uhnmm mimakikace? yafad'a kamar mesan tino wani abun kamun yace ""okay kikace Kinga tabo ajikina ko?kozaki nunamun inda yake nidai naduba banganshiba yafad'a cikin shagwab'a Kamar wani yaro..dariya sumayya tasaka tana fad'ar Allah ya yazeed shagwab'a namaka kyau kaid'in kyakkyawane Yayana 🙈 ""Humm rufamun asiri aibaikaiki kyauba.."Allah bawani ai duk gidannan kafi kowa kyau acikin maza..😲 har Ahmad? Yazeed yatambaya..""eh Mana harkowama..dariya yayi kamun yace keko kinfi kowa amata ba nidai ba Wannan ba gayamun inda tabon yake kokizo kinunamun.. "Wanne tabo?""au kinmanta ne?"eh wlh.."okay zona Tina Miki yafad'a Yana kaibakinshi kunneta yace""tabon dakikace inadashi a d'uwawu Mana..aibe k'asaraba sumayya tadunk'ule tana dariya tace..ah,ah fa ya yazeed nidai Allah banfad'a ba..shima dariyar yayi wadda idan kikaganshi baza,ace yazeed ne Wanda maganama kemsa wahalaba cikin tsokana yace "tofa 🤔 abunda kikace dama akwai fari kinaso kik'ara gani taso Mana kiyita kallah aiyazama naki Kinga yanzu ba d'uwawuba har abun dad'inki kinganiko yak'arasa zancen Yana kashe Mata Ido d'aya..wata muguwar kunya sumayya taji Wanda yasata mik'ewa dagudu tabar d'akin tana dariya shima dariyar yake yajuya yayi kwanciyarsa domin yasan idan yabita gudun zata k'arayi kumaga sabon ciki ajikinta.. Tofa sannu2 Bata Hana zuwa sedai adad'e ba,akaiba..rayuwa juyawa takeyi kullun kwanan duniya inda ayanzu cikin sumayya da safnah yakai wata bakwai Kuma ahakan suke rayuwarsu cikinso da kaunar juna yayinda iyayensu basusan Ina suke d'orawa dasuba hajiya Nene kuwa kamar tafi kowa murnada Wannan cikin nasu domin kullun seta dafa musu wani abun irin nasu natsofaffi namusu ciki takai musu hakama anty amarya da ammy zamansu suke hakali kwance suna zuba soyayya San ransu yayinda su yazeed tuni aka k'ara musu girma Wanda shugaban k'asa alhaji abdurahman kafiya dakanshi yakarramasu tareda K'ara musu girman anyi taro lpy anwatse inda matansu sukace bazasuyi bikiba sebayan su haihu suhad'a suyishi lokaci d'aya saurat ma yanzu tanada yaron ciki inda yazo Mata sab'anin nasu safnah domin ita laulayi takeyi sosai duk tarame tanashan wahala acikin..ahakan sadeeq kekulada,ita sosai. Fannin marwan kuwa yakusan zuwa hutun shekara yanacan Yana karatunsa Amma hankalinsa na wurin iyayensa. Yau asabar tinsafe safnah kefad'awa Ahmad gabanta ke fad'uwa gatsinkewar zuciya datakeji..yace tayita addu,a insha Allah bakomai ahakan har 12 tayi suka shirya dukansu zuwa gidan anty lele Ahmad ne yakaisu yanazuwa yayi hold megadin gidan yabud'e musu get suka shiga ahankali kowaccensu tafito da katon cikinta agaba saurat ce kawai natabeyi girmaba wucewa sukayi cikin gidan yayinda megadin yabisuda kallo ko kiftawa Babu Ahmad nata Masa magana Amma bejiba harseda yadakeshi tukunnah..shikin sauri yamarda hankalinshi..""mikake kallon ne haka anama magana bakaji? Ahmad yatambaya fuska ahad'e..bakomai yallabai wlh wani tinanine yashigeni shiyasa banjiba Amma kayi hakuri Dan Allah.."no bakomai Amma kakula yafad'a tareda shigewa motarsa yabar wurin yayinda suko sundad'e dashigewa harsunfara bajewa anty lele tab'ararsu domin kowa suka had'ewa su ukkun tofa sebuzunsa inwannan tayi nata saib'in anjima Wannan zatayi su adoli masu ciki.. Shiko megadi Yana ganin tafiyar Ahmad yafiddo waya a aljihun rigarsa yasakawa wata nomber Kira tareda shigewa d'akinsa. Achan gida kuwa Nene ce Kate mita akan doline Salman yakira Mata yazeed ko Ahmad domin sukowo matansu zata Basu magani kuma itabazataje dakantaba..""nifa gaskiya Nene banada credit awaya sekiyata Mita akan Abu d'aya kibawa su ya yazeed d'in sukaimasu Mana.."nashiga aljannah da izzinin ubangiji 🤔 Ashe bakada kunya? Yota,Ina zabawa wad'annan marasa hankalin maganin miki sokakiyi nabasu suje azubarko shikenan Dan an mayardani gantalalliya to badaniba Kuma doline kakira korona rod'ema Kai yanzu marar kunya kawai bawani kejin dabakada Dan karkakirasune tomaza inajinka kabani kosena sanbad'a maka sandarnan tafad'a tana d'ago sandar karfen dake gefenta.. Dariya salman kesanyi Amma yasanda yayita zatace yazagetane ba,abunda zehanata dokamai sandar dake hanunta gashikuma shine k'urya balle yagudu wayar yajanyo Yana fad'ar nifa Nene ba keji naceba credit wannne keji kuma yafad'a Yana dannawa Ahmad Kira har sau ukku Amma be d'agaba kallanta yayi yace""togashi nakira yah Ahmad Amma bed'aga.."to shi yazeedu fa tafad'a tana wulgamai harara.."Nene yah Ahmad ma be d'agaba Belle yah yazeed ni wlh inba doliba banasan kiranshi awaya sekayita magana yayimaka banza.."yo ba miskilanci banza dawofibane ainima inada cikinshi wlh Nan yazo shekaran jiya na sameshi har d'akin uwarsa nace yaxo yakarb'a musu kwad'on zogalar danayi masu yayi banza Dani seda uwarsa tayi Masa magana Kana ya,amsa danya mayardani gantalalliya irinsa yau inbanda tonon asiri ba kyau ba Aidana dad'e da wanke Masa allonsa d'anbanzan yaro Nan duk Wannan miskilanci na banza da wofi ainan yazo Yana k'wak'wular k'anwarsa Yana surfar kuka da ihu kamar Wanda ake zagewa rayuwa Amma inyazo ana magana Yana kallan mutane d'age Kamar bashiba Amma bakomai aikuma hakan dayayi Dede ne Dan naji dadi sosai shiyasa bazan Tona Masa asiriba idan yazo Yana kyale mutane tinda yanzu Masha Allah noma yayi harzamu Fara girbi tak'arasa zancen tana washe baki. Shidai salman nomber yazeed d'in yasakama Kira Yana dariya aransa yake fad'ar kaji Nene dawani shirme shi ya yazeed d'inne zeyi kuka sabida mace kumawai macenma sumayya ai wlh naso yanan Kika Fad'i hakan Naga yadda zakuyi..afili Kuma seya mik'a Mata wayar Dan yazeed d'in ya d'aga..amsa tayi tana k'arawa akunne tareda fad'ar""assalamualaiku yazeedu kana inane tokumadai Ina kake kakawomin matanku yanzu yawwa Kuma wlh inbaka kawosuna nakirawo ubanku nafad'a Masa tinda kunzama sallamammi..ab'angaren yazeed kuwa Jin Nene ce akan layin dakuma abunda take fad'a yasashi lumshe kyawawan idanuwansa seda yagamajin sak'onta sa,annan yace okay kawai tareda yanke wayarsa..yanufi gidan anty lele damashine ze d'aukosu tinda sunyi nauyi basasan yin driving Kuma kowaccensu nada motarta da mijinta yasiya Mata tsabar fitinace kawai irin tasu. Yana zuwa yakira sumayya yace sufito sutafi haka suka fito badan sunsoba sunata kunbura dukansu ukku yayinda anty lele ke dariyarsu tahad'o muzu kayan makulashe kala2 namasu ciki kana sukayi Mata sallama suka tafi.. safnah dai gabanta se tsananta fad'uwa yakeyi haryanzu bedenaba gashikota Kira Ahmad baya d'auka ahakan take cikin fargaba har suka Isa gidan dakanshi yafito yabud'e musu mota duk sukafito suka nufi pert d'in Nene. Achan gidan anty lele kuwa wayar megadi ce tayi k'ara yana d'auka yace wlh yanzu sukabar gadannan Kuma bansan gidansuba..bangaren Wanda megadi kewaya dashi kuwa cewa yayi kosune yanzu sukafice dawata mota fara? ""Eh sune kungansu ne? Kungansu bara mubisu yafad'a tareda yanke wayar Yana cewa me npp yabi waccan motar..hakako sukarik'abin su yazeed haryazo Nan family house d'insu bayan yazeed yashige da motarsa suko me npp yajiyesu nakin Gert Amma sunyi sunyi sosojin dake Nan sun hanasu shiga anacikin hakan Sega motar Abba da abbe atare sunyi Perkin tareda fitowa suna tambayar Mike faruwa..gaisawa mutumin yayi dasu kana yayimusu D'an gajeren bayanin daya kawoshi..jinjina Kai Abba yayi tareda fad'ar badamuwa mushiga daga ciki semuyi magana acan..cikin motarsa yakoma yajata zuwa cikin gidan shima Abbi yaja tashi bayan sunyi Perkin moticinsune Abba yadawo wurin mutanen yace sushigo daga ciki.. autar alheri ✍️✍️ 75 & 76 __bayanshi sukabi yakaisu pert d'in hajiya mama aperlon,shi kana shima yazauna Abbi ma yashigo bayansu gaisa damutanen ne Abba yace""to malam munajinka Mike tafedakai? D'agowa namijin yayi yakalli abba yamun yanisa yace ""to hakane alhaji dafarkodai sunana malam lado se medakina shatu ni d'an Niger ne nemane yakawoni Nan inda nake aikin gadi agidan alhaji Yusuf mek'arfi.."to Masha Allah alhaji Yusuf mek'arfi Wanda nasani? Cewar Abba Yana kallan baba lado.."insha Allah kila shine baba lado yafad'a Yana cigabada fad'in wata mahimmiyar maganace ketafedani alhaji yafad'a tareda zaro wasu hotuna cikin aljihun rigarsa yanamikawa Abba yace kokasan yarinyar dakejikin Wannan hoton? Karb'a Abba yayi yakallah tareda zaro idonshi Yana mik'awa Abbi cikin mmki shima Abbi karb'a yayi yaduba cikin mmkin yake fad'ar""Aina kasamu Wannan hoton malam miye had'inka da Wannan yarinyar? Aina kasanta? Wayasaka nemanta? Duk atare Abbi keyiwa baba lado tambaya cikin tuhuma..shima Abba kallan baba lado yakeyi sosai dam yakasa tantance abunda zuciyarsa keraya masa.. Nisawa baba lado yayi kamun yace""tabbas Wannan yarinyar y'atace..""what? Abbi yace dak'arfi Yana nuna baba lado yace y'arkafa? Tayaya tazama y'arka?""kwantarda hankalinka alhaji wlh Wannan yarinyar y'atace subiyu kawai muka Haifa aduniya k'addara ce tarabamu da,ita Kuma munyi Neman duniya bamu sametaba Dan girman Allah alhaji kutemakemu muganta tunda tana taredaku yak'arasa zancen k'wallar datacika idonsa nasaukowa..""kutemakemu alhaji kamar yadda Allah yatemakeku karku rabani da y'ata narasa komai aduniya tinda narasata bacci yak'aura cewa idona bana iyacin abuncin kirki alhaji kullun addu,ana itace idan tana Raye Allah yanunamun Koda gawartace nasan binneta akayi kohankalina zekwanta..umma shatu tafad'a tana kuka me bantausayi..shiru Abba yayi domin yakasa cewa komai Yana kallansu kamun yace shikenan mlm karka damu idai yarkace yanzu zaka ganta yafad'a Yana zaro wayarsa yadan,nawa Ahmad Kira tareda karawa akunnenshi.. Bugu d'aya Ahmad yad'auka tareda sallamah abakinsa..amsawa Abba yayi kamun yace""kad'auko matarka kuzo yanzu inasan ganinku.."to Abba ai tana gidan lele itada su tetee yazeed yaje d'aukarsu barana gaya masa.."okay to kaima kazo barinakira yazeed d'in yafad'a tareda yanke Kiran yakira yazeed.. Acan pert d'in Nene kuwa sunacan sunbaje aperlo se famar cin kwad'on da Nene yayimusu sukeyi suna Santi domin ciki tasaka maganin dankarsuk'ici..yazeed kuwa nazaune gefe Yana Danna wayarsa kamar besan abunda kefaruwaba Amma duk abunda sukeyi Yana kallansu wayarsace yaji tayi k'ara Koda yaduba yaga Abba ne d'agawa yayi cikin girmamawa yace "hello Abba..""na,am my son idan kad'auko su safnah kakawominsu anan.."okay badamuwa Abba aima Muna gidan.."to alhmdllh ainakukene? Muna pert d'in Nene barana fayamusu..ah,ah Bari mu muzo Chan zefi Abba yafad'a tareda yanke wayar.. Mik'ewa yayi yanafad'ar kutashi muje pert d'in Nene yakalli Abbi yace kakira su hajara da Zara susamesu achan Yana Gama fad'ar hakan yayi gaba baba lado da umma shatu nabiyedashi abaya..Chan pert d'in Nene kuwa kallansu yazeed yayi yaga duk yadda sukayi d'ai2 bame ko kallabi akanta sefamar cin kwad'on suke Amma kallo d'aya zaka musu kagano safnah batada nutsuwa shiru yayi Yana tinanin yazeyi dasu karsu Abba susamesu hakan sekawai wani abun yazo Masa arai cikin sauri yayi na,amda shawarar dazuciyarshi tabashi gyara zamansa yayi kana yamotsa D'an k'aramin bakinsa kamar bayaso yace""tetee cikin wani Dan iskan salo..d'agowa sumayya tayi Jin yakirata suna hada Ido yakashe Mata Ido d'aya tareda yin murmushi yace""sefamar cin kazantar Nene kukeyi to gabak'i Nan Nene zatayi yanzu Abba yagayamin sekusan abunyi..Ido sumayya tazaro tana fad'ar dagaske my uktee... murmushi yak'arayi yanafad'ar sosaima..aikamun yak'arasa fad'a Sumayya tayi zumut tamik'e Kamar bame tsohon cikiba Ido yazaro cikin sauri yace""Kee miye hakan bi,ahankalimana ah,ah..Suma duk kallanta sukayi seda takai k'ofar shiga kitchen sa,Annan tatsaya tana fad'ar kodai kutashi kokutsaya Allah bak'i zasu shigo perlon Nan tana Gama fad'a tashigewarta suna duk mik'ewa sukayi saurat nafad'ar kedai tetee Allah yashiryeki wlh shine bazaki gaya manaba seda kikatashi watomu suzo susamemuko? tak'arasa zancen sunabin bayanta.. Suna shigewa su Abba nashigowa tareda su hajiya mama Zama sukayi Abba ya amsa gaisuwarda yazeed kemasu taredasu baba lado kana yace Ina Nene da yaran suke..."Nene tashiga gunsu sameer suko suna ciki.."to kirasu duka cewar Abbi.. mik'ewa yayi yashiga kitchen d'in duk basa ciki tak'ofar kitchen d'in yabi yashiga bedroom d'in nene suna ciki zamansu ita safnah harta kwanta.."kuzo Abba nanemanku sukaji muryar yazeed yafad'a tareda juyawa batareda yajira cewarsuba Suma duka tashi sukayi sukafito perlon.. Yazeed nazama suna shigowa saurat ce agaba sa,annan sumayya safnah na bayansu..tinda suka fara fitowa idon umma shatu ke Kan k'ofar tanaso taga yarinyar da,ake magana ko,itace safnah na kunno Kai umma shatu tace wlh itace mlm itace wlh tafad'a dak'arfi tareda mik'ewa tanufo safnah datinda taji saukar muryar mahaifiyarta tad'ago arazane Aiko dai tabbas itace agabanta bawataba cikin matsanancin farin ciki da kuka umma shatu tarugume safnah yayinda mlm ma yamik'e tsaye yayo kusansu tareda hadasu duka yarun guma Yana fad'ar alhmdllh alhamdulillah alhamdulillah Allah nagodema yafad'a Yana shafa Kan safnah datayi mutuwar tsaye tazama kamar mutin mutimi gatadai kana gani Amma daganinta kasan batacikin hankalinta tashiga shock Sakinsu baba lado yayi yakoma gefe tareda yin sujjadar goduyawa Allah daya bayyana musu muradinsu yayinda umma shatu keshafa safnah tako,Ina tana kuka tanafad'ar maryama maryama kinaraye Ashe kinaraye aduniya baki nememuba? Maryama kinbarmuda kewarki maryama Ashe zank'ara ganinki aduniya? Tafad'a tana sake rungume safnah tana fashewada sobon kukan farin ciki.. ""Nashiga aljannah da izzinin ubangiji 🤔 Kee minene hakan zakiwanizo ki k'wak'ume yarinya haka da tsohon ciki sokikeyi kimana asara to wlh baki,isaba hukumace zata shiga tsakaninada duk Wanda yacezetab'a lpyr cikinnan hajiya Nene datashigo yanzu tafad'a tana fincike umma shatu daga jikin safnah fareda cewa "Kee Wai kina haukane Zaki saka yarinya gaba damaita kina zabgar kuka awa umarmiyagu atoo ni wlh Banga kukaba sedai yaganeki yau kinsan wahalar sanasha kafun asamu cikinnan zakiwani zo kimin asara kukuma sallamammi Kuna kallanta kunwani zuba Mata Ido Kamar Sabin mayu wlh Allah wani abu yasami cikinnan duk se nadaureku ehee 😏 Kuna kallansu dawasu idanuwa sekace ana sulala Rama😡 Itadai umma shatu batace komaiba segefe datakoma tana kukanta..""mahaifiyarta cefa Nene cewar dady dake zaune tind'azu Yana kallan ikon Allah cewa hakan Kuma yayi dededa shigowar Ahmad perlon Wannan kalamin yadoki kunnenshi inda yashigo yanabin kowa da ido...""mahaifiyar Waye? Yatambaya Yana kallan iyayen nashi..Waya sanar musu aikin kawai komade Yayane wlh akan cikinnan sedai amutu yawwa Nene tafad'a tana bankawa dady harara.."big mom ce tasauke ajiyar zuciya tana fad'ar mahaifiyar doter ce.."that ? Ahmad yace tareda kallan umma shatu kana yasake kallan big mom yace mahaifiyar ta big mom tayaya yafad'a tareda tinkarar inda yaga safnah tsaye kamar mutinmutimi Yana zuwa yadafata yaga Bata motsaba yasake rikan sunanta nanma shiru rik'e shoulder d'inta tayi dak'arfi yagirgizata tareda Kiran sunanta dak'arfi sekawai tayi.. Autar alheri ✍️✍️ 77 & 78 ___tayi firgigit tana kallan mutanen dakewurin kamar wata wawuya Sam takasa fahimtar komai..sumadai Ido kowa yazubamata musamman mahaifanta kaddai ace bataganesuba..itako kallansu takeyi d'aya bayan d'aya seda idonta yasauka akan mahai fiyarta Aiko tayi wata irin zabura daga rik'on da Ahmad yayi Mata wadda hadda d'an cikinta seda yamotsa tana fad'ar ummana tareda fad'awa jikin umma shatu tana fashewa da matsanancin kuka..itama umma shatu k'wak'meta tayi tana shafata ta ko,Ina suna rusar kukansu Wanda seda suka tab'a zuciyar kowa awurin duk su hajiya mama seda sukayi kukan tausayin uwa da y'a Sumayya da saurat ma duka kukan sukeyi itama tana neman zubewa ak'asa ganin hakan yasa yazeed yayi saurin tarota jikinshi yarungumeta tsam Yana rarrashin abarshi.. Ahmad ma idanuwansa sunyi jajir suntara k'walla..tinani yake aranshi Ashe iyayenta naraye duk tsawon lokacin Nan Basu nemetaba Kuma gasu akusadasu gidansu abokinsu tomiyasa suka banzatarda y'arsu? Kwashe2 dai kawai zuciyarsa kemasa Wanda bashida Mai ansamaisu..hajiya Nene kuwa tini tabar masifa tazuba Ido itama Kamar yadda kowa yayi Allah sarki Sega hajiya Nene nasharb'ar kuka hadda shafe majinnu😂 Sund'au tsawon lokaci ahakan kamun umma shatu taciro safnah daga jikinta Jin abun cikinta na motsi kamar zefito tad'agota tati cikin fad'uwar gaba tana kallan safnah da itad'inma ita take kallo cikin tsoro dagudun Kar abunda zuciyarta ke zargi yazama gaskiya tace""innalililahi wa innailaihiraji un maryama wayayi Miki ciki? Ko wayancan azzaluman sunsami nasarar kamaki? Maryama waya b'atamiki rayuwa? Waye yayi Mana Wannan tozalcin? Tafad'a dak'arfi taname jijjiga safnah datayi shiru tana kallanta danata tarin tambayoyin..""Yi hak'uri bawai Allah bawanda yab'ata Mata rayuwa cikin jikinta na Sunnah ne Kinga mijintanan akusanki big mom tafad'a tana nuna Ahmad dakegensu Yana Jin abunda umma shatu kefad'a..wata k'ak'k'arfan ajiyar zuciya tasauke wadda duk wandake kusanta yajishi sa,annan tashafa fuskar safnah tace "alhamdulillah maryama Allah ya,albarkaci Wannan auren..da,ameen kowa ya,amsa safnah kuwa dakyar ta,iya Bud'a bakinta dayayi Mata nauyi tace""ummana Ina appina Ina Yaya Marwan Ina uggo? Tafad'a k'wallar idonta nak'ara zubowa..murmushi umma shatu tayi me bayyana tsantsar farin cikinta tace""ga appinki Nan maryama akusadake..aiko cikin sauri tajuya sukayi Ido hud'u da baba lado Yana Mata murmushi..itama murmushin tayi tana share k'walla tareda yunk'urawa domin tatashi Ahmad yayi saurin kamata Yana fad'ar kibi ahankali qalbina..shiko baba lado ganin tashin namata wuya hakan yasa yace ah,ah yizamanki maryama baranazoni yafad'a tareda mik'ewa yayowurinsu shikuwa Ahmad yajaye domin Basu damar ganawa Aiko Yana zuwa tafad'a jikinshi tana fad'ar""appina dama Kuna raye? Kuka barni ajeji nikadai? Kukak'i nemana nasha wahala sosai appi miyasa kukabarni duk tsawon Wannan lokacin? Miyasa bakuzo gareniba? Appi Ina yah Marwan na? Kosun kasheshine appi? Tafad'a tana sake fashewada kuka..."Maryama kiyi hak'uri kinji munyi nemanki aduk inda mukasan zamunemeki tin k'asarmu harmukazonan sabida nemankine Marwan kuma yanaraye Kuma haryanzu bamu fasa nemankiba koyanzu megadin gidanda kukaje shine yagaya Mana inda kike har muka sameki..""alhamdulillah appina to Ina yah Marwan?""Marwan Yana India karatu Amma zedawo cikin makonnan insha Allah yanacan zecikamiki burinki nazama soja ko Wannan karatun sabida ke yaje maryama..wani irin k'ayatatcen murmushi tayi tareda fad'ar alhmdllh Allah yasa hakan takasance..kowa ya,amsada ameen d'agowar da appi zeyi yaga sadeeq dake tsaye bakin k'ofar perlon tind'azu yashigo bawanda yaganshi Yana tsayeda kayanshi na soja..murmushi appi yayi yace to Kuma gashi Allah yakawoki gidan dazaki rikaganin sojanma yafad'a Yana jamata hanci...dady ne yayi dariya Yana fad'ar tofa 🤔 soja takesan gani? Aiko dai anyi asa,a kenan domin mijin natama sojane..dariya kowa yayi awurin yayinda appi yace Masha Allah abuko yayi kyau Allah yasanya alkhairi..duk akace ameen kana Abba yayi gyaran murya yace kowa yasamu wuri yazauna hakanko akayi seda yayi addu,a mitsayi kana yadubi baba lado yace""mlm lado Koda bamusan tayaya kuka rabuda safnah ba Amma barakaji yadda tazo hanunmu Nan yafara bawa appi lbr tin daga ranarda sukazoda ita gidan da duk abunda yafaru har zuwa yadda akayi aurensu haryanzu dasuke zancen yak'are.. sa,annan yadubi baba lado yace iname Neman afuwa agareka abisa aurarda y'arka danayi batareda saninkaba Kuma bawai dasan Rai nayihakanba nayine sabida lpyrta..tsit wurin yad'auka bakajin komai se sautin kukan umma shatu..cikin jimami appi yace""hak'ik'a banida bakinda zanmaka godiya banada wasu kalamai dasuka ragemun abakina dazanyi anfanidasu alhaji Dan Allah kadena bani hak'uri domin abunda kayi shine dai2 Kuma konine amatsayinka iya abunda zan,iyakenan Wannan sadaukarwace wadda bakowanne ze,iya yintaba awannan zamanin kaida katallafi rayuwar yarinyar kuma kazo kana bani wani hak'uri wlh kobabu komai namatsala atareda ita ka,aurarda ita farin ciki zanyi balle akwai Kuma Wannan auren rubutacce ne acikin rayuwarsu Koda ba,ad'aurashiba sesun had'uda junansu sabida Wannan rabon fatana anan shine Allah yasanya albarka acikin rayuwarsu suduka..kowa ya,amsada ameen. Abbi yace "mlm lado baka gaya Mana yadda akayi kuka kasance arayeba bayan safnah tagayamana cewa bakwa duniya ya akayi kukarasata har Wannan matsalar tasameta.. ""To Masha Allah hak'ik'a Wannan gaskiya ne domin ba maryama ba kowa agarinmu kallan matacci yake Mana domin matsalar data abkamana..dafarkodai ni sunana alhaji Yusuf ishaq ni haifaffen Niger ne inada Mata d'aya gatanan Aisha inada Yara biyu Marwan shine babba se Kuma Wannan maryama Wanda sunan mahaifitane nasaka Mata Amma dayawa family nakirantada safnah inazaune acikin garin marad'i tareda mahaifiyata dakuma iyalina ni attajirin me kud'i ne inada gidaje da company's nataso cikin family masu yawa Wanda hakan yasa duk wani wurin nawa family nane ma,aikatana yarana Kuma alhamdulillah kowannensu Yana karatunsa cikin nasara kamun Wannan iftila,in yafad'a Mana..watarana dabazan tab'a mantawaba nadawo daga office nasami wasu mutane su ukku k'ofar gidana dashiga ta alfarma ajikinsu bayan nazo mungaisa nakaisu perlona muka zauna inda ananne abun yasoma domin sunnuna buk'atar neman auren maryama Kuma cikin k'ank'anin lokaci bankawo komai arainaba nace musu bakomai zanyi shawara subani kwana biyu duk yadda nayanke zasuji sukayimun sallamah suka tafi fitarsu keda wuya nima nafito domin ba d'auko komai nawaba a mota seda nazo Dede inda zanfita sekawai naji ana magana k'asa 2 Dana kasa kunne sa,annanne naji abunda yagirgiza tinanina..abunda suke fad'a Wai Ashe ba,auren gaskiya sukesan Maryama ba idanuwanta sukeso suyi tsafi bayan nagama Jin zancensu Sena Koma cikin gida inata tinanin yadda Zan bulkuwa way'annan bayin Allah har suka dawo daga makaranta sukasameni ahakan wandako mahaifiyarsu tayita tambayana miyake faruwa Amma nakasa gaya Mata..ahakan mukakwanta bacci seda dare yaraba kawai nafarajin motsi cikin gidan Koda nafito nako hangosu way'annan mutanen nad'azu sune hadda Karin wasu dabansan kosuwayeba cikin tashin hankali nakoma d'akina nahad'a duk wasu takaddu nawa masu mahimmanci Dana company na dakomai nasa ajaka naje d'akin Maryama tanada ita Nagoya mata jakar tareda saka Mata hijabinta nabud'e Mata k'ofar baya nace tafita kumakarta tsaya ko,Ina taso kawomun gaddama alokacin ganin yadda natirza akan setayi tafiyar yasata fita inadawowa naji wani mugun sauti natashi cikin perlonmu ana fad'ar Bata gidan yafitarda ita kubita karkubari murasa Wannan damar suko kuk'onasu..cikin sabon tashin hankali nakoma d'akin Marwan natadashi kafin inyi wani yunk'uri tuni gidan yakamada wuta tako,Ina hakan mukazo muna Neman hanyar fita Babu tako,Ina bahanya dak'yar mukasamu mukabita kitchen muka fita Muna fita natinada kayan uggo wato mahaifiyata data bani ajiya kafin taje gidan k'anenta nakoma ciki dasauri ind'auko Marwan yahanani shiyakoma ashewai uggo tanacikin gidan tad'akintama wutar tafara tashi atakyaicedai se gawar uggo Marwan yafitoda ita daganan mukabi hanya cikin jeji bamusan inamuka dosaba seda garin Allah yawaye kana mukayiwa uggo sallah muka binneta nida Marwan dawasu bayin Allah makiyaya daganan mukaci gada tafiya seda makabaro Niger Sam kana mukaci karoda jakarda nagoyawa Maryama dakuma hijabinta dasu abubuwan da munsan natane nad'auki jakar nabud'a komai nanan yadda nasakashi sedai Babu wasu daga cikin hutunanmu Kuma babu Maryama babu dalilinta munyi kukan zuci munyi nafili Amma Babu maryama munyi Neman duniya bamugantaba har Allah yakawomunan nasamu aiki agidansu sulaimanu Kuma bamu fasa nemantaba Muna gayawa Allah kukanmu batareda kowayasan wayeniba..appi yak'arasa zancen Yana kashe k'wallar idonshi..kowa aperlon yayi tsit bana jimami masu kuka nayi masu tagumi nayi sun d'au tsawon lokaci ahakan kamun Abba yace hak'ik'a kuga abubuwa arayuwa inatafan Kuma shikenan Allah ya kyauta gaba.. ameen y Allah aka amsa kana safnah tace""bayan fitata appi alokacin banyi wani nisaba naji anfincikini na Fad'i Ina d'agowa naji an sokamun wani abun Ido neda nakara fad'uwa danatashi naji idanuwana namin zafi sekawai nagudu sukarika Bina dak'ar na boye masu Amma Basu Dena bibiyataba kumani bansan kosu wayeba ahakan nake lab'e bayan wani kango har gari yawaye nafito nadawo gida Nan nataradda gidan yak'one ancika k'ofar gidan kowa na fad'ar mun mutu dagani harku Ina kukan ganin sunsami nasarar kasheku dudda bansan kosuwayeba natinkari gidan domin mutane suga cewa ni ban mutuba Nan nahango wani Yana nunawa yaso gardawa ni Yana fad'ar nacan shiyasa nasake guduwa suka shiga Bina har suka Sami nasarar kamani bayan jakarda appi yabani tafad'i sukashigo daninan garin kwanana biyar ataredasu kullun da,abunda sukeyi akaina daganan nasamu ranar bakowa se masu fad'in wurin nagudu danazo fita wurinne Naga duk abunda nakallah seya nakkasa tahakanne ma masu gad'in duk suka mutu Dana kallesu ganin Wannan Bala,in daya sameni yasa nayanke wakaina zama cikin jeji tinda banada kowa karnashiga cikin mutane narika cutardasu kunji abunda yasa banne mekuba tak'arasa zancen tana sake fashewada kuka...tofa ahakan dai akayita jimamin daza,ayi daganan su baba lado sukace zasu koma tinda yanzu sunga inda safnah tace keko hajiya mama kicce sutafi da,ita suk'ara ganin juna zuwa kwana biyu sunkoji dad'in hakan Sosai inda baba lado yace se idan mijinta ya yadda.. Ahmad kuwa murmushi kawai yayi yace bakomai sutashi yakesu suka d'auke su shiga yazeed sukamaidasu gidansu sulaiman... Autar alheri ✍️ 79 & 80 __bak'aramin mmki sulaiman da mmanshi sukayiba Jin Wannan lbr musamman yadda bb lado yake attajirin me kud'i kuma yabige a aikin gadi sabida yab'adda Kama anan kuwa akagayawa baban sulaiman komaidayafaru yaji dadi sosai Kuma ya jinjina abun hakan yasa atake yace yadakatar dashi daga aikin dayake Masa shidama can besaniba ba yadda baba lado beyiba Amma yace Sam ai dama Wannan aikin bekamaceshiba..todai hakan su yazeed sukatafi sukabarsu badan ran Ahmad yasoba. Awannan ranar fad'ar farincikinda su baba lado sukeciki fata lokacine hakan suka raba dare suna firada Y'arsu da Yaya marwan ma domin tini umma shatu tagaya Masa Aiko shima kamaryataka Kan jinjiri Dan murna💃 Suko suna komawa gida kowa gida sukad'auki matansu akabar Ahmad nan domun cewa yayi bazekomaba se safnah tadawo haka yabud'e pert d'insu nada yayi zamanshi.. Yau kusan satin safnah ukku tareda iyayenta Kuma ya marwan yadawo inda sukeshirin komawa jiharsu Amma se Allah yasauki safnah lpy...su Ahmed kuwa gabaki d'aya hankalinshi nakan matarshi dudda sunyi busy cikin kwanakinnan domin shirye2 auren sulaiman da,akeyi da suhaima k'anwar sadeeq Wanda tin ranar mother's night d'insu yazeed suka kulla suke soyayyar su bawanda yasani sabida itabatare takedasuba shima begaya musuba seda akazo Neman aure kowayasani Aiko yasa zancen agunsu Wai yazo sace musu kanwane shine tab'oye musu abudai sulaiman yashashi to yanzu bikiyazo kusa inda sumayya keta kunburin za,ayibiki tana hakan baza,abari seta haihuba tofa 🤔 su teteee tayazaki Hana masoya morewa kice sekin haihu? Masha Allah komai akasakawa lokaci tabbas zezo yau akeyin kamun suhaima su sumayya tinsafe anagidan ammy itada fauza da saurat seda hamma safnah matazo Wanda sadeeq ne yaje yad'auko ta shirye2 akeyi sosai su k'irjin biki ansha gayu da tsululun ciki abundai ba,amagana misalin k'arfe 4 nayamma kowa yashirya tsaf Dan zuwa kamu mazazenma susha gayu sabida kunsafa bikina farar kaza akace balbela bagayyarta akeyiba😜 Sunacan tareda ango sulaiman inda sukacewa matan bazasusami zuwaba suhad'u acan kawai hakanko bakaramun dad'i yayiwa sumayya ba domin D'inkin jikinta yakamata sosai shiyasa taji dad'i tasan idan yazo zehanata zuwane koyasata canja kaya ahakan suka fito domin abokanan ango sunzo d'aukar mutane Koda suka fito motoci suncika Ammy tasanya safnah cikinta k'awayenta itako sumayya akace tashiga wata motardake gefe sabida itace kawai Bata cikaba seda tashiga sa,annan taga bamakowa aciki..nacikin motar kuwa tana shiga yasauke wata wahalalliyar ajiyar zuciya tareda fegar motar.. Acan gun bikin kuwa tini kowa ya,Isa wurin har amarya da angonta sun iso suma mazajen haka Amma sumayya batazoba gayase shagali akeyi anci ansha ancashe har biki yafarq tafiya Amma ba sumayya babu dalilinta yazeed ma yad'an damu daga bayaseyayi tinanin kohana Mata zuwa akayi Amma Kuma yakasa samun natsuwar zuciya..fauza kuwa da agabanta sumayya tashiga mota duk tak'osa batazoba sabida atab'a Hali Amma Inna cikin tsoron data faraji kardai kowani abun yasame sumayya talallaba kusan yazeed can inda abokanan ango kezaune Kuma kowanne matarsa na mak'ale dashi kasa tayida murya tace ""yah yazeed yah yazeed..sambejitaba seda tayina ukku kana yad'ago da kyawawan idanuwansa Yana kallanta bece komaiba..shiru tayi kamar bazatayi magaba sekuma tace""dama tetee ce batazoba haryanzu Kuma agabana tashiga mota Amma haryanzu Bata isoba..rasss gaban yazeed yayi wata muguwar fad'uwa Amma tadake yace""wacce motar tashiga? Yatambaya idonshi akanta..""Nima wlh bansaniba..okay kawai yace tareda Kiran wayar sumayya seyaji tana k'ara akusadashi...cikin sauri saurat tace laaa yah yazeed aiga wayarnan ahanuna Bata isoba Amma kakira number suhaima wayartace ahanun tetee.. okay kawai yace tareda mik'ewa yacewa fauza muje sukafice d'aga hold d'in yah Marwan maganin fitarsu yabi bayansu domin tin shigowar fauza idonshi kekanta Kuma daga baya Sega Kamar tana cikin damuwa Wannan dalilinne yasashi bin bayansu koma Koda yaje harsun tada mota sunbar wurin cikin sauri shima yashiga motar yamara musu baya. Tafe suke Yana Kiran nomber suhaima tana ringing Amma ba,adagawa cikin tashin hankali yakira wani abokinsu Yana d'agawa yace""hello man yadai..""musty zanturoma wani contact please yanzu inaso nagano inda yake yazeed yafad'a batareda ya,amsawa musty d'inba.."okay badamuwa turo..kashe wayar yayi tareda turawa musty contact d'in suhaima.. Acan gun sumayya kuwa ganin tafiyar da,keyi tayi nisa yasata fad'ar Wai inazamuje hakan kobakasan inda ake kamun bane? Asharad'a hotel nefa yanaga munzonan? Eh zan d'auki k'annena ne semuwuce tinda bakowa ke kad'ai ce Dan Allah kiyi hak'uri..shuru tayi tanatinanin inatasan Wannan muryar ganin Bata tinaba sekawai tace okay..seda sukazo wata unguwar da bamutane dayawa acikinta sekawai ya perka motar yafito. Shiga yayi cikin wani Dan madedecin gida Kamar minti 5 dashigarshi yafito yasake shiga motar yace "waisunrigada suntafi barakawai muje..okay kawai sumayya tace tacigaba da game d'inda takeyi awayar suhaima shiko jiyowa yakeyi time to time yadda yaga hankalinta yad'auku ga,abunda takeyi se kawai yafesa Mata wani abun afuska.."innalililahi wa innailaihiraji barak'arasaba tayi luuuu tafad'i kwace wayar suhaima dake hanunta tafad'i kararta akashe ko,ankira ba,ajin kukanta..safwan dayaga sumayya tazube sekawai wayi wani k'ayatatcen murmushi Yana fad'ar ""ketawace sumayya ninakine har abada sabida cin Amana shine yayanki yayimun shigar sauri hadda d'and'anamin zumarki yacuceni darigani saninki Amma bakomai yanzukam kinzama tawa ba,abunda zek'ara rabamu shima seyaji abunda naji yafad'a tareda k'arawa motarsa gudu.. Gunsu yazeed kuwa yadda musty yaturomai location d'in yagaya Masa Kuma bagasunan tafiya sukeyi haryanzu har fita cikin garin Kano..cikinn sauri yazeed yakatse wayar dasukeyi da musty yakira wani abokinsu daduyi karatu tare Dan jigawa state Amma shi polis ne yagamasa Dan Allah yasaka mada katai adede Hanya kaza zasu had'a call d'in su ukku sabida kowannensu yaji abunda musty kefad'ar inda wayar suhaima take..aiki cikin gaggawa jabeer yabayarda umurni wayaranshi yafito harshi suka tare hanyoyin damutin ze,iyabi gaya magariba takawo kai..yah Marwan ma cikin mmki yakebin motar yazeed duk inda yayi yanabiyedashi. Safwan kuwa driving dinsa yakeyi hankali kwance har yakawo nadakatar da yansanda ke tsaye bedamuba domin bekawo komai aransaba har yazo gunsu suka gaisa sa,annan sukace zasu duba mitarshi yace bakomai.. Suko su yazeed da jabeer suna waya musty yace Dede inda diddigin layin kenunawa Dede inda su jabeer ketsayene shiko jabeer yace lallai yanzu wata farar mota tazo wucewa gatanan sun tsayar za,aduba..cikin sauri yazeed yaduba fauza yace wacce""wacce kalar motace tetee tashiga?""farace Yaya..kamun yayi magana jabeer yace Wannan motar maybe ba,ita bace yazeed domin bakomai aciki Kuma Wanda yake driving motar beyi kamada melaifiba hasalima matarsa yad'auko zekaita hospital yace gasunan zasu wuce..""Nooo jabeer don't sey it goo please.. yafad'a cikin k'araji..cikin mmki jabeer yace okay don't worry yafad'a tareda saurin dakatarda safwan dahar yafara tada motar.. Yazeed kuwa wani mugun gudu yakeyi damotar nafitar hankali fauza kuwa kamar tasaki fitsari sabida tsoron yadda yake Jan motar kamar Kamar me yak'i jijiyoyin kanshi suntaso rud'a rud'a fuskarshi ba,alamun Wasa kokad'an..yah Marwan ma k'arawa tashi motar gudu yayi ganin yadda yazeed ke gudun Amma dudda hakan yakasa cimmasu sabida tukin badaya bane shinashi hankali kwancene shiko tukin kawai yakeyi Amma baya bisa natsuwarsa. Cikin k'ank'anin lokaci ya,iso jigawa state yanabin inda sukemai kwatance her yakai gun. Safwan kuwa tini yafara Shan jinin jikinshi domin yayi dakarya da gaskiya sun hanashi wucewa daya matsa musuma cewa sukayi baze wuceba se matar tasa tatashi daga baccin datakeyi idan tace itad'in matarsace sesubarshi yawuce Wannan abun bakaramun tadawa Marwan hankali yayiba.. yazeed na,iso damotar yab'alle marfin yafito ko Perkin bega Dede tawaba tatinkari Wannan farar motar dayagani perke agefe jabeer namasa magana Amma kojinsa bayayi ganin hakan yasashima yataso daga inda yake tatinkari motar..yazeed nazuwa yab'alle marfin motar aiki Sega sumayya kwance kamar matacciya cikin fargaba da tashin hankali yace""hayatina tareda kafe safwan da Ido dasukayi jajir kamar muta yace""mikayiwa mamata ta? Inazaka kaita? Miye hadinkada ita?""ah,ah dama am matarka ko matat..kafin ya,Ida fad'ar matarshi yaji saukar wani gigitacce Marin daseda hak'oranshi biyu suka cire kamun yazeed y Yafincikoshi k'asa yashiga dukanshi baji bagani kamar Allah ya aikoshi seda yanakassa Masa halitta Sam idonshi yarufe jiyakeyi idan bekasheshiba zuciyarshi bazata nutsuba ganin Yana Neman kasheshine yasa da jabeer da yaransa dakuma yah Marwan daya iso yanzu suka taru dakyar suka kwaci safwan hannun yazeed kana yaran jabeer suka tafi dashi bayan gagarumin gargad'in da yazeed din yayimusu akan kowa yazo beyadda tinda sunhashi yatafi dashi. Duk'awa yayi cikin motar yad'aukota da tsululun cikinta kana yasakata anashi motar se,asannan yakulada Marwan da fauza dake rakub'e gefe cikin sauri tashiga motar ganin kallanda yake mata shima zeshiga yah Marwan yayi saurin cewa barana tuk'a yah yazeed Dan Allah karkayi tuki cikin fishi..kallanshi kawai yayi bece komaiba seda jabeer yace "eh gaskiya ne yazeed baraya jaku senasaka shi akawo Masa tasa daga baya Amma ba Kano zaku komaba yanzuko? Naga dare yayi..bece komaiba seda yashiga baya inda yakwantarda sumayya kamun yace""no Kano zamu yafad'a tareda janyota jikinshi..shiko yah Marwan shiga yayi yayiwa motar key yanama jabeer godiya tareda bashi hannu yatada motar sukabar wurin.. Acan gida kuwa tini angama kamu har kowa yawatse ba,aga sumayya ba daga baya akace ba fauza ma da yazeed Kuma gashi dareyayi sosai ba,agansuba hankalinkowa yatashi inda aketa famar Kiran wayar yazeed baya d'auka ta suhaima ma dake hannun sumayya ba,ad'auka Tini aka gayawa su Abba inda hankalin kowa yake tashe..seda sukayi tafiya menisa yajanyo wayarshi kodaya duba miss call yafi 50 kowa kiranshi yakeyi zebi Kiran Abba kenan Kiran Ahmad nak'ara shigowa d'auka yayi cikin sauri Ahmad yace""biyayye kana Ina inasu sumayya? Miyake faruwane?""shiru yayi kamar bazeyi maganaba..ganin hakan yasa Ahmad fad'ar banasan iskanci yazeed kana,inane? Jin Ahmad yakira asalin sunanshi Kuma Yana magana cikin fad'a yagano kowa yasan basagidan kenan..cikin basarwa yace""duka inataredasu gamunan zuwa yanafad'ar hakan yayanke wayar... Autar alheri ✍️✍️ 81 & 82 __sororo Ahmad yayi dawaya ahannushi kamun yasauke ajiyar zuciya yanaduban iyayen nasu yace""Wai sunazuwa yace yanataredasu duka.."okay to alhmdllh indai hakane Allah yakowosu lpy cewar Abba..ameen y Allah Shiko yazeed yanasauke wayar yakalli sumayya dake bacci ajikinshi tareda shafa fuskarta se alokacin idonshi yahango mashi kayan jikinta wani mugun kishine yarufeshi yafara tinanin yanzuko hakan Wannan D'an,iskan yaganta yadda manyan breas d'inta sukayi rud'a rud'a acikin rigar jikinta har shatinsu kina iyagani cikin Jin haushinta yajanyo mayafin data saka domin yanada girma yarufe Mata jikinta dashi..shidai Yaya Marwan driving d'inshi kawai yakeyi yanayi Yana satar kallan fauza data makure Kamar marainiya ahakan suke tafe harsuka shigo garin Kano kaitsaye yacewa Marwan yawuce dasu gidanshi hakako akayi suna zuwa yayi perking suka fito shima fitowa yayi d'aukeda ita ajikinshi yashiga cikin gidan seda yakai k'ofar perlon sa,annan yajiyo dabeji fauza tabiyosuba yawatsa Mata harara yayi tareda fad'ar ubanme to kikeyi anan?""gida zani yah yazeed.."okay sekijeto yafad'a agatse tareda kallan Marwan yace dareyayi sosai zokakarb'i key kazo kakwanta..""ah,ah Yaya bakomai Zan,iya tafiya.."" okay to shikenan kaje da motar kawai dasafe seka maidamun.."to ngd sosai seda safe.."Allah yabamu alkhairi yazeed yafad'a tareda shigewarshi yabanko k'ofar..ganin hakan yasa takwasa aguje tayi gidan saurat tana zuwa tashiga buga k'ofar Amma shisu tayi bugun duniya Basu bud'eba abunda batasaniba shine sunacan gida sunajiransu bawanda yadawo cikinsu..ganin itakad'aice awurin Kuma tafarajin tsoro yasata komawa dasauri tafad'a cikin perlon nasu azziki bakowa a perlon domin bedroom d'inshi yawuce da,ita..cikin sauri tafad'a wani bedroom d'in dakenan perlon tagark'ame kartasha rabon jibga😂😂 Shiko Yana zuwa yakwantarda ita kana yashiga wanka seda yafito yashirya cikin kayan baccin shi sa,annan itama yacire Mata tareda maida mata nabacci yasakata ajikinshi Yana shafa kwattacce sumar kanta kamun bacci shima yafara fisgasshi yaji wayarshi na k'ara seda yaja dan tsaki kamun yad'auka bareda yace komaiba domin beduba mekiranba..cikin fad'a yaji muryar Abbi Yana fad'ar Wai bazaka Fad'i indakuke bane inda wata matsalar kafad'a kabar mutane najiranka tin d'azu Kuma in,ankira wayarka baka d'agawa Wannan wanne irin Sha,shancin banzane..Abbi munfa dawo tind'azu..""kamarya? Kundawo Kuna,inane? Kuma Ina kukaje? Abbi yatambeshi ahasale.."muna gida Abbi har ita fauza gani nayi dare yayi sosai shiyasa wanine yasace tetee Amma ba,abunda yafaru ankamashi Kuma mundawo ba,abunda yasameta insha Allah yafad'a cikin tsantsar ladabi wa mahaifin nashi..nisawa Abbi yayi kamun yace tofa wata sabuwa to allah yakyauta gaba kawai yace tareda yanke wayar Yana cewasu Abba to kowa aiseyaje yakwanta domin shiyana gidanshi mune yabari zaune Kamar wasu wawaye tareda gaya musu abunda yazeed d'in yafad'a gameda d'auke sumayya.."to indai suna lpy ai ba,abun fad'a bane alhamdulillah zamuce Allah ya kyauta gaba kowa yaje yakwanta cewar abba..hakan kowa tashi yanufi pert d'inshi azzikin abun Nene batasaniba duk abunda akeyi anhana agaya Mata kawaide hajiya mama takira ammy tagaya Mata angansu.. Sumayya kuwa ba,ita tafarkaba seda akafara Kiran sallar asuba kanata bud'e rinannun idanuwanta dasukayi Mata nauyi sosai tajita ajikin mutin atake k'wak'wal warta tatariyo Mata abunda yafaru da,ita amota cikin masifa tasa hannu dak'arfi tature yazeed tana fad'ar Waye Kai Mike nufi dasatoni gidan ubanwaye Nan wlh Sena kasheke nizaka tozalta karabanida mujina Dan kana mat..kafun tak'arasa yayi saurin sakata ajikinshi tana fisge2 yakai bakinshi kunneta Yana fad'ar ninefa my life kiyi shiru kinutsu karkijiwa babyn mu ciwo kinjiko..seda taji muryar yazeed sa,annan hankalinta yakwanta sanan ma tafahimci k'amshin jikin Waye takeji..sund'au lokaci ahakan kamun tace""Wai waninefa daga yaje gidansu yad'auki k'annenshi muwuce bikin haka kawai bayan yace suntafi yafesamun wani abun afuska tukunnah ma ya,akayi nazonan? Murmushi yazeed yayi tareda jan hancinta yace nine nasakashi sabida karkije aikinga shigarda kikayi..kukan shagwab'a tafara tana dukanshi shiko yayi sauri tashi yashige bathroom sabida ankusa tada sallah Yana murmushi dama yafad'a Mata hakanne domin kartasaka abun aranta gatada juna biyu Kuma tsoho alwala kawai yad'oro yafice warshi masallaci itama tashi tayi Dakyar tayi sallar..seda garin yawaye kana su sadeeq suka dawo gida hadda Ahmad domin yahana safnah komawa..abakin get d'in da gidajensu suka rarrabune suka had'uda dashi domin se alokacin yadawo daga sallamar asuba harrana tafito Kuma damacan hakan sukeyi anan ne yagargad'i su safnah karsu gaya Mata abunda yafaru danya b'oye Mata tosukace suka shigewarsu sa,annan suko suka zauna harabar gidan yabasu lbrn abunda yafaru sunyi mmki sosai tareda jajanta abun kana sukayi mishi gargad'in idan irin hakan tafaru yadena zuwa shikadai surink'a fad'awa junansu yayi na,am da hakan Kuma yabasu hak'uri abisa Wannan kuskuren dayayi masu kana kowa yashige gidanshi.. Fanni ango sulaiman kuwa tin adaren ya farke suhaima yayi ihu yayi gurnani haryagaji domun bakaramun gyara ammy tayiwa yartaba seda yasamu cikakkiyar gamsuwa sa,Annan yaga aika,aikar dayayi Amma dai dasauki sosai Dan beji Mata ciwoba yadaikam gurjeta San ranshi cikin farin ciki da Jin dad'i tagyara matarshi... Haka rayuwa taci gabada tafiya inda kowannensu ke kulada matarsa cikinso dakulawa yayinda suka koma jigawa gun b'arawon tetee safwan yasha bakar azaba ahanunsu inda Dakar yafad'i burinshi akan sumayya tareda Basu hakuri yana neman afuwar yazeed Kuma yayi nadama sosai hakan yasaka suka sakeshi tareda yimai gargad'in kome yasamu sumayya shizasu Kama kana suka dawo gida yanzu cikinsu Sumayya yashigo watan haihuwa inda Nene tace sesun maidasu gida Amma sunk'i hakan tagaji damitarta tabarsu.. Yazeed ne kwance aperlo dagashi se boxes abun duniya yayi mishi yawa domin jiyakeyi Kamar yaci Babu sabida fitina marabada yakwantada sumayya tin cikinta na wata shida datayi wata Rashin lpy sedai kawai suyi Dan romance din juna yarage zafi yauko jiyakeyi Kamar abar zata tsinke Masa. Itako fitowa tayi daga bedroom d'inta domun rigima takeji dashi tazobo uban hijabi zatashiga gun safnah taganshi kwance idonta yasauka asetin boxes d'inshi taga yadda abarshi ke Harbin iska har waje ana,iyagani gata tayi tsaye k'ik'am Kamar rodi sematsar Mara yakeyi Yana cizan lips d'inshi nakasa..ajiyar zuciya sumayya tasauke domin Wannan halittar bakaramun tsoro take bataba idan taganta Amma kuma yayan nata nabata tausayi sosai domin tasan halin kayanta sabida yayi k'ok'ari matuk'a hijabin jikinta tacire dama bawasu kayan kirkine ajikintaba tashiga takowa wurinshi cikin sand'a..shiko yanacan duniyar tinanin yadda zekusanceta dawannan cikin yazesamawa kansa mafita sekawai yaji saukar hannuta aburarshi wata muguwar ajiyar zuciya yasauke tareda bud'e rinannun idanuwansa dasuka cika tabda jaraba Yana watsamatasu cikin alamar rok'o nakitemakeni..murmushi kawai tayi tareda jinjinamai kanta sekawai takai bakinta akan nashi tashiga tsotsa Aiko cikin sauri tashiga maida Mata martani kissing din junansu sukayi kamar hauka sabun kamun duk Wanda yaga yadda yazeed keyiwa sumayya yasan cewa tabbas amatse yakeda mace cikin fitar hayyaci yadamk'i manyan breas d'inta yashiga kissing d'insu Yana matsarsu tareda lailayasu Kamar Allah ya aikoshi..itadai sumayya se shafa kwattacce sumar kanshi kawai takeyi tana k'ara bank'aro Masa nonon.. yad'auki tsawon lokaci Yana hakan itako ganin duk yarasama mizeyi domin gabaki d'aya hanyar samun nutsuwa kawai yake nema.. Hannuta d'aya tatura cikin boxes d'inshi tafara shafa mararshi zuwa cinyoyinshi..cikin sauri yak'arasa tura hannun akan joystick d'inshi yanafad'ar ashhhhhhh babyyyy murzamun please yafad'a tareda mayarda nono bakinshi.. murmushi tayi ganin duk yadda yayan nata yarud'e kamarba miskilin nanba dako magana aikice agunshi domin gani takeyi ko rik'a hannun ya yazeed seyayi Mata wuya lokacinda basuyi aureba Amma yanzu gatarikeda Abu mafi mahimmanci ajikinshi kumawai shi dakanshi yakai hanunta wurin sekawai ta cabkota tareda yimata wata sahihiyar murza me shiga jiki wadda tasa yazeed kantsarewa Yana fad'ar oshhhhhhh ashhhhh dadiiiiiii teteeee jikinshi ko,Ina na karkarwa cikin jindadin tafara yimasa abunda yakeso tacigabada murza Masa ita tana lailayawa tareda shafa ko,Ina na jikinshi..shiko se Nishi yakeyi Yana K'ara yamutsa nonuwanta sund'au tsawon lokaci ahakan kamun sumayya tamik'e ahankali ta,idasa cire kayan jikinta shima tazare boxes d'inshi. Taka kujerar dayake Kai tayi kamar bame cikiba taraba kafafuwanta biyu tad'auko burar dakanta tadanna acikinta seda tasaki K'arar azaba domin Bata shiga duka Kuma ga tsohon ciki..shi kanshi yazeed dayaga abunda zatayi seda yazaro Ido Amma jarabar dake cinshi tahanashi fahimtar komai be Ida rud'ewa ba sedayaji tafara sukuwa akanshi kamar wadda bakomai ajikinta ruwan ni,imarta kuwa b'ulb'ulowa kawai sukeyi akan hajiya babba gasuda d'imi sosai abunga mai tsohon ciki..habawa ai yazeed besan lokacinda yafara aikin nashiba wato ihu muddin zasuyi sex da sumayya to seyayi ihun balle yau dayakeji kamar betab'a Jin dad'in maceba irinshi wani rarraba Ido yakeyi Yana d'ago k'ugunshi tareda rik'e nata kugun Yana Kara dannawa anashi Yana surfa ihunn gabaki d'aya yagigice ya gigitata yahaukace Yana Neman haukatarda ita itama ihu yakeyi da,iya k'arfinshi yau Babu zancen kukan kissa wani abunne yazubo daga cikin sumayya irin ruwannan masu mugun santsi da d'imi suka saukarwa yazeed.. wayyyo dadiiiiiiiiiii zeekashe wlh wayyyo Allah na ashhhhhhh babyyyy wayyyo buraaaataaaa awshhhhh ohhhhhhhh wayyyo Allah sumyyyyynaaaaa ashhhhhhh babyyyy burata zata tsinnnnnnkeeeeeee wlhhhhhhhhh washhhhhhh auchhhhhhh shiiiiiiiiii ashhhhh dadiiiiiii teteeee wayyyo dadiiiiiii ashhhhhhhh ohhhhhh wayyyo Allah wayyyo wayyyo sumayya kidena hanamun kogin dad'i please ashhhhhhh babyyyy wayyyo buraaaataaaa awshhhhh ohhhhhhhh wayyyo sumyyyyynaaaaa don't stop please ohhhhh yessssss baby so sweet ashhhhhh ohhhhh yessssss ashhhhhhh kamun jikinshi ko,Ina yad'auki Raya ana zazzagarshi Kamar wani zararre yazabura dak'arfi da,ita acikin jikinshi yajuya yashiga cinta cikin zafi da kuzari Yana surfa ihunshi yajima ahakan kamun yatsandara wani ihun da maybe ko maigadinsu yaji Yana fad'a wayyyyyoooooooooooooooooooooooooo ashhhhhhhhhhhhhhh sumyyyyyyyyyyyyyy zannnkawooooooooooooo ashhhhhhhhhhhhhhh yafad'a dak'arfi tareda faramata farin Madara seda yajuye tsab hankalinshi yadawo jikinshi kana yadagata Yana murmushi itama murmushin tayi na k'arfin hali tana kallanshi aranta tana fad'ar ji yadda yake tsandara ihu dawata maganar ce akayi zeyi Kamar bejiba..shiko mik'ewa tsaye yayi tareda mika hanun zed'auketa tace ah,ah yaje yadawo tukunnah yad'auketa hakako yajuya Yana murmushi yashiga bedroom d'inshi tareda fad'awa bathroom dayayi wanka abunda besaniba sumayya tafad'a mishi hakane kawai danya tafi domin wata muguwar mird'a mararta keyi Wanda Bata tabajin irinshiba cikin azaba tasauko k'asa tana karanto duk addu,ar datazo bakinta wani abun taji yadanno Mata dak'arfi daga gun kashinta har gabanta kamar zetsagata biyu cikin dauriya taruntse idanuwanta dak'arfi tareda Kiran sunan Allah domin idan azaba tayi yawa bazancen kuka aiko setaji abun yak'ara dannuwa tareda fitowa sulubbb sekawai taji kamar ancire Mata k'aya tatsaya tana maida numfashi kusan sakan 20 kamun perlon yad'auke rad'au da kukan jariri 😜 cikin iyawar ubangiji yasauke sumayya lpy arazane tawaigo Dan itasam batayi tinanin aihuwana tayiba itadai gatadai batamasan kominene ba zatace..yin kukan jaririn yayidede da Gama saka kayanda yazeed yayi yaji kukan jinjiri yad'auke agidanshi Sam bekawo komai aransaba yadunfari perlon.. Autar alheri ✍️✍️ 83 & 84 __yana kunno Kai yayi turus ganin sumayya agurfane ga baby agefenta na kuka..Ido yazaro tareda fad'ar sumayya aihuwa kikayi anan kodai gizau idona kemun yafad'a cikin matsanancin farin ciki tareda k'arasowa inda take Aiko dai haihuwace wlh y Allah yafad'a tareda rungumota jikinshi bedamuda yadda jikinta yakeb'aceba yasakata jikinshi Yana fad'ar alhmdllh bini,itami rabbi Alhamdulillah sumayya Wannan yaronane ya Allah yak'ara fad'a duk yarod'e...cikin dauriya sumayya tadubeshi tace""yayana babyn mu nakukafa..se alokacin ma hankalinshi yakoma Kan baby cikin sauri yasaketa tareda tallabo kyakkyawan jinjirin mekamada sadeeq sak kamar d'ansa ga cibiyarsa na lilo ko uwar tafiyar batazoba..Masha Allah watafarakallah bi ahasanil,khaliqeen lallai jini baya k'arya yarannan kamarsu d'aya da biyayye Kamar antsaga Kara yafad'a cikin Jin Dad'i Yana k'arewa yaron kallo..""yazanyi Masa my life? Kinga bansan yazancire Wannan abun ba..Nima bansaniba kawai akatse..Ido yazaro Yana fad'ar akatseme lallaima yarinyar nan to badaniba Kinga barana gayawa sadeeq muji yaza,ayi..to kawai sumayya tace shiko ya,ajiye yaron yafita dagudu ko takan takalminshi bebiba. Yana zuwa pert d'in sadeeq ba sallamah bakomai yashiga perlon Yana fad'ar biyayye biyayye kana,inane biyayye..sadeeq dakecan duniyar maji dad'i har yafara lulawa Kamar daga sama yarink'a jiyo muryar yazeed nakiranshi cikin sauri yamik'e yanacewa saurat inazuwa baby wandonshi yajanyo zesaka yasakejin wani Kiran besan sanda yafigi bedsheet ba yalauyo ak'uginsa yafitoba. Yazeed na ganinshi yak'arasa wurinshi dasauri Yana fad'ar Wai kana inane tetee tahaihu wlh yaro sak Kamar Kaine bansan yaza,ayiba please muje kagani..ajiyar zuciya sadeeq yasauke domin yatsorata da kiranada yazeed kemai cikin Jin Dad'i yarungumeshi Yana fad'ar Masha Allah alhamdulillah gaskiya naji Dad'i sosai biyayye narigaku samun baby mekamadani..murmushi duka sukayi kana sadeeq yace barana kira doctor sameerah zefi yafad'a Yana k'ok'arin komawa d'akin yad'auko wayarsa se alokacin yazeed yakulada yanda sadeeq d'in yake..cikin tsokana yace au ashe yaro yahana abbansa jindad'i tinyanzu dazuwansa tab biyayye wlh anyi jarababbe a,nan..jiyowa sadeeq yayi shima cikin Wasa yace ai wlh duk fitinata baikaba namamajo kawai kumani ba,abunda yarona zehanani sedaima yak'ara bani damaryi ehee..dukkansu dariya sukayi kana sadeeq yashiga yagayawa saurat tareda d'auko wayarsa yafito zekira doctor sameerah cikin sauri saurat tamik'e tace""no my sweet karka kirata bara muje hospital d'in kawai inazuwa.."to ai ba,acire mahaifaba..""eh zancire yisauri siyomin kayan aiki kawai..Ido yazaro yace tayaya keba mlmr asibitiba..""Dan Allah my sweet karmu B'ata lokaci ni malamar asibitice Kuma fanni haihuwa kawaide banfara aiki bane.. rungumeta kawai sadeeq yayi cikin Jin Dad'i yasaka kasanshi yafito kotakan yazeed bebiba yaje yasiyo kayan aiki shigo yazeed nanan zaune domin saurat tahanashi shiga. Sadeeq kuwa bejimada tafiyaba yadawo yabawa saurat kayan aiki cikin k'ank'anin lokaci tagyara mejego da baby tareda perlon fyass Kamar ba,ahaihu awurinba se kanshi d'akin keyi. Haka saurat tad'auko baby takawo musu tashiryashi tsab cikin tsadaddun kayan jarirai masu kyau da laushi..suka karb'a sadeeq yafara koromai addu,a baji bagani yakare yabawa yazeed shima yayi se,alokacin yazeed yace""Kai bamufa Kira biyayye ba..au hakane wlh Sam nasha,afa barana kirashi..korufe baki sadeeq beyiba shima Ahmad yafito dagudu safnah tahaihu besan yazeyida baby ba Aiko sukashiga murna datsalle abun gwanin Sha,awa kamar wasu Yara..cikin sauri saurat tanufi inda safnah itama tayimata duk abunda yadace kana tafito musuda baby girl Masha Allah zokuga farin ciki agun way'annan zaratan samarin INGARMAN MAZAJE abun ba,amagana.cikin tsantsar farin ciki sadeeq yace ikon Allah yafi gaban Wasa wato Wannan yarinyar itako kamar Kai biyayye yafad'a Yana kallan yazeed murmushi yayi yace""wlh Nima Naga hakan bamuda banbanci nida ita..dariya sukayi dukkansu sunayiwa Ahmad gwalo waiba yaranda yabiyoshi..shima cikin dariyar yace Aiza,ahaifamun nawa very soon duk seyafiku kyau..sukasake shekewa da dariya. Sannan suka Kira iyayensu suka gaya musu kamun kace Mee zancen haihuwarsu yagame dangi baki d'aya fad'ar farin ciki da Wannan ahlin keciki ayanzu b'ata lokacine su fauza da saurat ga Kuma suhaima sune kangaba iyayen Yara Nene kuwa har rawa tataka tana kuka tana tikar rawa tsabagen farin ciki tace lallai se,ankawo matasu gunta zasu zauna basuna kadaiba har Arba,in hakako akayi akakwasosu duka aka,ajiyewa Nene ammy da su anty lele anty khadi ko basada hutu sune sushiganan afitacan Inna shatu ma anyi2 tazo Tak'i Yaya Marwan ne kawai yazo inda fauza tad'auko Mai Yara yagani yasanya musu albarka shima Anan dai akacigabada hidimar jarirai da iyayensu inda aka Hana su yazeed ganin matansu Koda daga nesane b'oyo sosai Nene kamasu Kuma Alhamdulillah suna samun kulawa sosai gun iyayensu mazajensu kuwa sunyi sintiri har sungaji anhanasu doli suka hak'ura ahakan kwanaki keshud'ewa inda takasance yaune safiyar suna Kuma za,ahad'a bikinne Dana walimar k'arin girmanda akayiwa su yazeed Masha Allah gidafa yacikada jama,a tako,Ina nanesa Dana kusa angwayen k'arni sunsha kyau ba,amagana domin anko sukayi su 5 inda sulaiman ne yayi musu d'inki sunan shiyasa yayiwa har Yaya Marwan..agun suna Yara sukaci suna kamar hakan yaron Sumayya akasa mishi Ahmad baby safnah Kuma akasaka saurat abun bakaramun dad'i yayiwa kowaba a family dumin gani sukeyi and'auko haryar k'ara samun zuminci..sekuma wani abunda yabawa kowa mmki awurin anagama suna akaji ana daurin auren fauza da Yaya marwan abunda yabasu matsanancin mmki domin bawanda yasan lokacin dahakan tafaru..abunda basu saniba shine tin lokacin da Abba yadawo daga gun aiki yasamu fauza da Yaya marwan nafira pert d'in Nene ya bincika yagano kowaye daga lokacin ya,ajiye aranshi ze,aura masa ita Wannan abun kuwa bakaramun dad'i yayiwa baba lado ba dama shikanshi Marwan d'in. Cikin Wannan dadd'an abun farin ciki dayasamesu akaci gabada asha,anin biki inda biki yazama ukku taro yayi taro anci ansha abun sewanda yagani Kuma anwatse lpy.. Bayan K'are suna dakwana biyu Abba yakirasu yace sushirya ranarda za,aimayarda masu haihuwa d'akinsu aranar za,akai hadda fauza..Aiko abun yayiwa hajiya mama Dad'i sosai inda big mom da Amma suka duk'ufa gyaran amaren Kuma sunkasa sun tsare akan mazajen shiyasa ko keyarsu basa gani..seda sukayi wata d'aya kana su baba lado sukashirya zuwa Niger Abba ko yace aje hadda safnah da fauza da Ahmad hakako akayi domin har su yazeed seda sukaje sun,Isa lpy inda suka samu danginsu dasuki matukar mmkin ganin suna Raye anyi murna anyi farin ciki abun ba,acewa komai seda sukayi tsati biyu acan kana su safnah suka dawo Amma baba lado yacedamashi badan yadawoba acan sukayi zamansu cikin daginshi inda yakomama kasuwancin Kamar da harma ace fiyeda da tinda komai na kadararsa na,Nan. Satinsu biyu dadawowa daga Niger akamardasu safnah d'akinsu fauzama tatare sabon gidanda abban sulaiman yabawa Yaya marwan..aranardai Kam bakanta domin anga zallar soyayya k'auna wadda akajima ba,ayiba su yazeed da Ahmad Kai harmada Yaya marwan asha ihu ansha gurnani da binge 2 dominfa jisukeyi kamar alokacin suka farasanin mace..Masha Allah hakan rayuwa taci gabada tafiya har Allah yanuna musu saurat tasauka tasamu baby boy Wannan ma bakaramun farin ciki sukayiba domin dai yaro koyanzu yazeed yabiyo Kuma sunyi farin c Downloaded from GNOVELS.COM.NG This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG For feedback and support Facebook : https://facebook.com/gnovels Twitter : https://twitter.com/gnovels Telegram : https://t.me/gnovels