Downloaded from GNOVELS.COM.NG This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG For feedback and support Facebook : https://facebook.com/gnovels Twitter : https://twitter.com/gnovels Telegram : https://t.me/gnovels 'Kwary tabi'kwarya complete 2/11/21, 8:19 AM - ???: *'KWARYA TABI 'KWARYA* *NA* _BINTA UMAR ABBALE🍒_ *bintaumarabbale@gmail.com* *MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION📘🖊?* _'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_ _________________________ *Littafin na kudi ne....!* _#300.....0542382124...Binta Umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai ki same ni ta wannan numbers..08089965176 _07084653262 Zanyi miki bayanin yanda zaki turo katin.......... Ga masu bukatar VIP Group 600 ne_ _Mutanan Nijar zaku tura dala dari ta wannan numbers katin airtal ko orange VIP jakka d'aya 90899076_88137740_ *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 1&2 Lokacin dana shiga masarautar sai da nasha jinin jikina dan ganin yanda tarin bayin dake karkashin masarautar suka nutsu gabas yamma kudu Arewa dukkaninsu suna tsaye sunja layi mazansu da matansu da 'ya'yansu suna sanye da uniform wanda ke dauke da tambarin masarautar gaba da baya, kowanne kansa a sunkuye 'kwakkwaran motsi babu wanda yake iya yi.......Can wata rumfa na hango iyayen masarautar zaune kan kujeru na alfarma sun jeru su uku wanda yake tsakiyarsu shine nafi tunanin shine shugaban masarautar wato (Sarki Maimartaba) abinda yasa nake tunanin shine Sarkin sabida ganin yanda wasu mutane gudu biyu masu dauke da jajayen kaya suke tsaye a gefe da gefensa suna masa firfita da wani irin mafici mai baza gwanin birgewa........Shiru masarautar babu hayaniyar mutane busar algaita gami da sarewa ne kawai take tashi a gurin. Cikin nutsuwa wasu lafiyayyun motaci guda guda su shigo cikin masarautar, Maimartaba ya fara yun'kurin miqewa tsaye fuskarsa dauke da wani qayattacan mirmushi, Ganin zai miqe yasa fadawan dake gurfane a gabansa suka miqe da sauri suna baza manya manyan rigunan jikinsu......Waziri Galadima Ciroma suma suka miqe tsaye sabida ganin maimartabar ya miqe, dan ganin iyayen masarautar sun miqe ya sanya dukkanin wa'inda suke zaune suma suka miqe tsaye domin girmamawa.......masu busar sarewar suka rud'e tare da sanja salo....gabadayansu suka nufi inda motocin nan sukayi parking suna ta aikin busa algaita gami da sarewa, Wani bafadane yayi saurin bude motar ya fito da sauri ya bud'e daya hannun ya matsa gefe guda tare da dun'kule hannunsa alamun jinjina ga wanda ke cikin motar "Barkan ka da dawowa masarautar gado Aliyu Haidar namijin zaki Sarki mai jiran gado fari kake mai farar aniya Ali baka fito ba sai da ka shirya hakika masarauta da duk wanda ke karkashinta yana murna da dawowarka lafiya." Wannan kirarin daga bakin bafadan yake fitowa....shuru gurin yayi na minti biyar kafin ya zuro qafarsa d'aya kafar dake dauke da takalmin sarautar na tsirawa ido cikin socond guda na gane cewar mamalakin kafar mugun d'an izzah! ne a qalla ya kai minti biyar da zuro kafa daya ya gagara fito da dayar ko me yake a cikin motar oho! gabadaya idanun kowa a gurin yake mutane da dama sun 'kagauta suyi tozali dashi mussaman na qasa wa'inda basu sanshi ba sai dai labarin sa, cikinsu har da Sumayya wacce ta kasance d'aya daga cikin 'ya'yan bayin masarautar itama idonta kur! a gurin tana jira ya fito daga motar ta ganshi tun kafin ya fito ta gazgata abinda jama'ar masarautar ke fada a kansa wato shi d'in mugun d'an izzah! ne mugun d'an d'agawa ne! mugun d'an gadara ne! Mugun muskili ne wanda babu wanda yake gane al'kibularsa sai mutum d'aya itace mamanshi amma hatta da mahaifinsa maimartaba baya gane inda ya dosa. Cikin nutsuwa ya rankwafo ya fito daga cikin motar tare da zura bak'in gilashin dake hannunsa dan saboda gujewa had'a ido da jama'ar da sukayi masa caaa! da idanunsu ya tsani kallo a rayuwarsa shiyasa sam baya sakarwa mutane fuska mussaman mata dan ya fahimci kamar kallo a jininsu yake be sai ba ko shi suka raina suke k'ure shi da kallon 'kurrula. Wasu matasan samari ne wa'inda sukayi sa'anni dashi naga sun fito daga d'aya motar su biyu suna sanye da kayan sarauta a jikinsu amma shi uban gayyar suit ne a jikinsa Shatima da Moddibo sune suka tilasta masa d'aura alkyabba a jikinsa saboda da ita sukaje airport din suka kuma sheda masa cewar maimartaba ne yace lallai su bashi yasa ya shigo da ita cikin masarautar. Da sauri naga wasu bayi su hudu sun shimfid'a wani farin abu mai tsayi a dadai kafafunsa sai da abin ya dangane har inda iyayen masarautar suke Cikin nutsuwa yasa kafarsa akan abin ya fara tafiya. Tafiya yake abokansa kuma 'yan uwansa na gefe da gefensa, yayin da masu busa algaitu suka cigaba da aikinsu tare da rufa musu baya....Lokacin masu camera man vedio camera suka fara aikinsu suma 'yan Jarida ba'a barsu a baya ba aikin daukar hotonsa kawai sukeyi shi kuma yana d'agawa jama'ar dake gefe da gefan sa hannu ammafa babu walwala ko ta kwabo a fuskarsa wanda ya kamata ace ya saki fuskarsa ya tar'bi dubbanin mutanan dake murnar dawowarsa gida ko a jikinsa daga karshe ma daya ga yana damun kansa sauke hannunsa yayi sai kawai ya sunkuyar da kansa ya cigaba da tafiya babu um! babu umum!! Sukuwa jama'ar masarautar sai kirari suke masa gami dayi masa fatan alkairi a rayuwarsa amma gogan bai d'ago kansa ba ballantana yasan sunayi.........."Wani irin takaici ne ya rufe ni naja tsaki tare da kauda kaina daga kallonsa tabbas na gazagata maganganun da jama'a sukeyi a kansa na rashin kirkinsa yanzu ina laifi ga wanda ke murna da zuwanka gami dayi maka addua idan da mutunci yaci ace ya d'ago kansa ya nuna jin dadinsa amma saboda tsabar izzah! ya gagara kallon inuwar inda mutanan ke tsaitsaye. Silalewa nayi daga cikin iyayena na kama hanya domin tafiya can shashenmu na bayi, zuwa zanyi na huta dan bazan iya jurar tsayuwa ba rana sai duka na take gashi wanda akeyi dominsa baya gani, mahaifina kawai nake tausayawa dan ba wata cikakkiyar lafiya gareshi ba amma saboda tsabar bin dokar masarauta yasa ya lalla'ba ya fito ya tsaya a matsayinsa.............. *BINTA UMAR ABBALE* *Kuyi sharing👏🏻* 2/11/21, 8:19 AM - ???: *'KWARYA TABI 'KWARYA* *NA* _BINTA UMAR ABBALE🍒_ *bintaumarabbale@gmail.com* *MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION📘🖊?* _'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_ _________________________ *Littafin na kudi ne....!* _#300.....0542382124...Binta Umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai ki same ni ta wannan numbers..08089965176 _07084653262 Zanyi miki bayanin yanda zaki turo katin.......... Ga masu bukatar VIP Group 600 ne_ _Mutanan Nijar zaku tura dala dari ta wannan numbers katin airtal ko orange VIP jakka d'aya 90899076_88137740_ *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 3&4 Yarima Aliyu a nutse ya 'karasa rumfar da iyayen nasa suke zazzaune ya cire rufaffun takalmansa a nutse yaje ya gurfana a gabansu tare da 'kaskantar da kansa sosai yace"Allah shi taimake ka ina fatan na same ku lafiya."? Maimartaba ya d'ora hannunsa a saman kansa cikin farin ciki yace."Lafiya lau alhamdullilahi Aliyu ina fatan ka dawo gida cike da samun nasarorin da muke bukata." Ali! Yayi murmushi tare da sake sunkuyar da kanshi qasa, Waziri ne ya karaso gurin a nutse yasa hannunsa ya d'agoshi ya miqe tsaye! wani qayataccen murmushi yayi wanda yay masifar yi masa kyau tabbas da yasan dariya nayi masa kyau to da ya mayar da hankali gurin yi.......Rungume 'Kanin mahaifin nasa yay a daidai kunnansa ya furta "Baba Waziri ina fatan duk na same ku lafiya." Waziri cike da walwala da farin ciki yace."Lafiya lau ka same mu Aliyu haki'ka muna farin cikin dawowarka masarauta lafiya." Idanunsa dake lumshe ya bud'e! still da ragowar murmushin a fuskarsa yana kokarin yin magana suka hada ido da Galadima shida Ciroma suna tsaitsaye a inda suke fuskarsu babu wata cikakkiyar walwala. Gyara fuskarsa yayi dan saboda yasan halinsu da rainin hankali suna iya tsinkashi a gaban mutane a kullum burinsu suga sun 'bata masa rai tun yana yaro suke nuna masa qiyayya tamkar wani abokin gabarsu. Inda suke ya nufa ya d'an risina cikin nutsuwa yace."Ina fatan na same ku lafiya."? Galadima ya gyara yanayin sa yana kokarin danne 'bacin ran dake ransa yace."Lafiya lau Alhamdullilahi ina fatan ka dawo gida tare da nasara." "Alhamdulillahi." Shine a binda ya fada tare da yin kasa da kansa gami da goya hannuwansa a baya................Daf da zan shiga kofar mu d'aya daga cikin matsu tsaron 'kofa ya dakatar dani, tsayuwa nayi ina kallonsa har ya qaraso inda nake, Yace."Waye ya baki ikon barin gurin taro bayan ba'a tashi ba." Kai tsaye nace"Kaina ne yake ciwo sannan rana na takura min shiyasa na dawo gida. Shar'be'biyar bulalar hannunsa ya labta min a qafafuna yace."Kina a matsayin baiwa maqasqanciya kike wannan maganar, baki san abinda kikayi ya sa'bawa dokokin masarauta ba to bari kiji har iyayenki sai an hukunta sabida abinda kika janyo musu." Wani irin gumi! nake ina kallonsa bakina sai rawa yake yi ga wani irin zafi da kafafuna sukeyi min. Bulalar ya sake d'agawa zai shaud'a min nayi saurin riqe hannunsa hawaye suka 'kwace min nace"Bafa ni da lafiya na fad'a maka kaina ke ciwo sannan ga rana a gurin laifi ne dan na dawo gida na huta."! Finkice bulalar yayi daga hannuna ya daga da karfin gaske ya shaud'a min a bayana ban san sanda na k'wallara k'ara ba, wannan 'karar da Sumayya tayi har can gurin taron babu wanda beji ba. Maimartaba ya tashi fadawa da sauri yace suje su duba cikin gidan..........."Wuce mu koma gurin taro ki fuskanci hukunci ko su waye iyayenki a cikin gidan nan kin janyo musu fushin masarauta.'' Abinda yake fada min kenan tare da inginza ni wai lallai sai mun koma gurin taron, ni kuma tsabar taurin kaina sai turjiyewa na keyi hawaye na zuraro min. Fadawan da Sarki ya turo suka karaso gurin suna tambayar abinda ke faruwa, a take Sarkin kofa yayi musu bayani, Naga babban cikinsu ya zare min ido hade da buga min razananniyar tsawa! ya bani umarnin shigewa mu tafi. Turjewa nayi ina kallonsa da busassun idanuna a fusace! ya tattare babbar rigarsa ya d'auki ni ya sa'ba a kafad'arsa kai tsaye gurin taron ya nufa dani ina kuka da dukansa da zille zille haka ya dinga ratsa mutane dani bai dure ni a 'ko'ina ba sai gaban maimartaba. gurfana nayi nayi qasa da kaina hawaye na karakaina a fuskata.......Lawi da matarsa hankalinsu ya tashi dan ganin 'yarsu a gaban maimartaba da alama ta janyo musu fushin masarauta sai duk jikinsu yay sanyi cikin kaskantar da kai suka sunkuyar da kansu gabansu na faduwa, Gabad'aya gurin shuru yay kowa na jiran sarki yayi magana.....wanda har lokacin Yarima Ali! na tsaye goye da hannu kamar wani soja! Maimartaba ya kalli bafaden yana bukatar karin bayani. Da sauri ya sunkuyar da kansa kasa yace."Ranka ya dade wannan yarinyar can cikin gida muka sameta tare da d'aya daga cikin masu tsaron kofar bangaran bayi suna jayayya da juna kan umarnin daka bayar." Mai tsaron kofa yace."Allah ya taimake ka na ganta zata shiga gida sai na dakatar da ita tare da tambayarta wanda ya bata izinin baro gurin taro bayan ba'a tashi ba shine take fadin maganar da bata cancanta ta fito daga bakinta ba a matsayinta na makaskanciya bai kamata ta nuna gazarwata gurin jimirin tsayuwa a cikin rana domin tar'bar Yarima Ali ba, yarinyar tayi min bayani cewar ita ba zata iya tsayuwa a cikin rana ba." Gurin yay tsit kowa na mamakin furucin da 'yar gidan Lawi bawa! tayi shin da me take taqama dashi ko kuma dame tafi sauran bayin dake masarautar da har take fadar wannan maganar.......Yarima Ali kansa a kasa kamar mai kallon kasan gurin amma yarinyar kawai yake kallo takasan idanunsa bakin gilashin dake idonsa shi ya hana a gane ita din yake kallo, mamaki maigirma yake akan furucin yarinyar ba zata iya tsayuwar a rana ba saboda bata daukeshi da mahimanci a cikin masarautar ba, murtuke fuskarsa yayi ya kauda kansa daga gefan da take gurfane wani irin tsanar yarinyar yaji a cikin zuciyarsa.......Maimartaba yay gyara murya a nutse yace."Yarinya meye sunanki."? Murya na rawa tace"Ranka ya dade sunana Sumayya Lawi mahaifina shine ke kula da 'bangaran dokuna." Sarki yay shuru na minti biyu kafin yace."Sumayya me yasa kika karya dokar masarauta bayan kin san dacewa qa'ida ne idan na kira taro kowa ya hallara kuma masarauta bata bawa kowa damar tafiya ba sai na tashi shin kin san muhimmacin wannan ranar a gurina da masarautar gabad'aya."? Kanta a 'kasa ta girgiza kai da fad'in "A gafarce ni a ranka ya dad'e nima ba'a son raina ba wallahi kaina ne keyi min ciwo." Jin abinda tace yasa Yarima Ali harar gefan da take yaja tsaki 'kasa-'kasa d'auke kansa yay yana sake 'bata rai. Sarki! yace."Naji uzirin ki Sumayya mai yasa da zaki tafi baki nemi izini a gurin wakilai ba." Shuru tayi tare da kaskantar da kanta kasa....Maimartaba yace."Wannan rana nada mutukar mahimanci a gurina da masarautarmu rana ce wacce ya kamata mu sata a cikin kudin tarihin masarauta, tsayin shekaru goma sha biyar masarauta tayi ba tare da d'an cikinta ba wato Yarima Aliyu mai jiran gado.....Tun yana da shakaru goma sha biyu a duniya ya sauke al'kur'ani maigirma tare da sauran littafan addini sai na turashi can kasar amuruka domin neman ilimin zamani Aliyu ya za'bi karatun likitanci wanda ya tabbatar min dashi ne ra'ayinsa ni kuma na goya masa baya domin ya samu ingantaccan sani ta kowane 'bangare..Alhamdulillahi ya sama dukkanin abinda ake bukatar a samu muna sanya ran dawowarsa gida sai 'kasar ta b'ukaci daya zauna da ita domin ya taimaka musu da abinda Allah yayi masa, ina zaune a fada sa'ko ya isa gareni akan wannan magana, ba'a son raina na amince da zamansa a kasar ba sai dan ganin shi ya nuna yana bukatar ya zauna ya taimaka musu yasa na amince masa, anan yake tabbatar min da cewa shekara bakwai kacal zaiyi dasu ya ajiye aiki ya dawo 'kasar sa domin suci moriyarsa wannan dalilin ya sanya na amince da bukatarsa.....A Yau ne Allah yayi nufin dawo dashi gida gabad'aya kamar yanda yayi min al'kawari, wannan dalilin yasa na bada umarni kan cewa dukkanin wanda yake karkashin masarautar nan ya fito domin ya nuna farin cikinsa akan dawowarsa gida lafiya, sai gashi ke! da baki san shi ba kin kasa tsayuwa ki tantance shi ki kama hanya kin tafi koda yake kema kin kawo uzirinki ciwo ya wuce komai! saboda haka anyi miki afuwa abisa karya doka da kikayi amma kada ki sake kwatanta abinda kikayi a yanzu dai masarauta ta yafe miki laifin da kika kaita." Kaina a 'kasa nace"Godiya nake ranka ya dad'e ubangiji Allah ya qara maka lafiya da nisan kwana insha Allahu ba zan kara ba." Lawi da Tambaya iyayena sune suka karaso gurin suka gurfana gaban maimartaba suna godiya gami da sake neman afuwa." Maimartaba ya girgiza kansa a nutse yace."Babu damuwa kuna iya tashi." Da sauri muka miqe a tare muka koma muka tsaitsaya cikin 'yan uwanmu bayi....... *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 8:19 AM - ???: *'KWARYA TABI 'KWARYA* *NA* _BINTA UMAR ABBALE🍒_ *bintaumarabbale@gmail.com* *MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION📘🖊?* _'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_ _________________________ *Littafin na kudi ne....!* _#300.....0542382124...Binta Umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai ki same ni ta wannan numbers..08089965176 _07084653262 Zanyi miki bayanin yanda zaki turo katin.......... Ga masu bukatar VIP Group 600 ne_ _Mutanan Nijar zaku tura dala dari ta wannan numbers katin airtal ko orange VIP jakka d'aya 90899076_88137740_ *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa Dashan Allah✊?) 5&6 Bayan mun koma gurin tsayuwar mu mun nutsu sai maimartaba ya umarci yaron nasa daya fito ya nunawa jama'a farin cikinsa na dawowarsa masarauta lafiya....A lokacin idanun jamaa yayi caaa! a kansa kowa kokarinsa yayi tozali dashi, ni dai sunkuyar da kaina qasa nayi saboda jin yanda gabana yake faduwa haka kurrum naji bana bukatar kallonsa ba dan komai ba sai dan mugun halinsa na rashin ganin darajar mutane........Wani bafade ne yay gaggawar gyara masa abin magana ya saita masa daidai bakinsa, kamar wanda akayi wa dole yay gyara sai da yaja lokaci tukkuna cikin rashin walwala a fuskarsa da maganarsa yace."Alhamdullilah Allah kaine abin godiya. hakika nayi farin ciki mutuka daga dawo dani gida cikin koshin lafiya gami da tarin nasarori masu yawa." shiru yayi tare da sunkuyar da kansa qasa. Jin yayi shiru yasa nayi saurin dago kaina ina kallon gurin da yake, gani nayi kansa a sunkuye yana kallon 'kasan gurun tamkar me neman wani abu......Tsaki naja a cikin zuciyata nace"Wannan anyi d'an wulaqanci ya sani sarai jama'a shi suke sauraro amma ya fara magana yayi shiru, kaina na d'auke ina jin takaicin abinda yake......Gyaran murya ya kuma yi kafin ya cigaba da magana..."Sannan kuma nayi farin cikin samun iyayena da 'yan uwana da dukkanin wanda ke k'ark'ashin masarautar nan lafiya hakika naji dadi sosai da ganin yanda kuka fito 'ya'yanku da jikokin ku kuka nuna farin cikin ku dangane da dawowa ta gida Nagode sosai inayi muku fatan alkairi." yana k'are maganarsa ya janye bakinsa daga gurin abin maganar can kusa da Waziri ya koma ya tsaya har yanzu babu fara'a a fuskarsa. Hayaniya da kace kace ne ya cika gurin, Wani bafade yayi tsawa tare da umartar kowa yay shuru kafin minti biyu gurin yayi tsit! Maimartaba ya miqe a nutse ya karasa gurin da abin magana yake, kafin ya fara magana sai da ya d'aga hannuwan sa sama alamar gaisuwa ga tarin jama'ar dake gurin.....Gurin ya sake rikicewa da hayaniya kowa sai fadin albarkacin bakinsa yake akan maimartaba. Da kyar aka samu sukayi shuru suka bar maimartabar yayi jawabi gami da miqa godiyarsa ga Allah ya kuma miqa godiyarsa ga tarin manyan mutanan da suka samu hallatar gurin suma bayin dake karkashin masarautarsa sai da ya miqa godiyarsa a gurinsu sannan ya koma ya zauna gurin zamansa, Baba Waziri yazo yay nasa jawabin Galadima da Ciroma suma sukayi nasu daidai gwargwado sannan maimartaba ya rufe taron da addua, ya miqe da niyyar shiga cikin gida fadawa ne suka kewaye shi suna ta gyara kintsi dai."!! Gurin ya karad'e da bushebushe gami da tashin muryoyin maro'ka da hayaniyar jama'a, sai da Sarki da muqarrabansa suka shiga gida tukkuna aka samu lafiya, jama'ar gurin suka watse kowa ya nufi 'bangaran da yake a cikin gidan.........Nida iyayena Cikin yanayi na ciwo muka shiga gurin mu, da sauri muka zaunar dashi, Tambaya ta ri'ke kafadarsa ni kuma hankali a tashe naje na d'ebo masa ruwa jiki na kyarma nazo na tallafo kansa ina kokarin bashi ruwan, bakinsa ya bud'e ina sa masa ruwan yana dawowa, lokaci guda zuciyoyinmu suka karye nida mahaifiyata hawaye muka fara, cikin karfin hali gami da kokarin janyo maganar yace."Ku daina kuka bashi ne abinda nake bukata ba."! Zama nayi kusa dashi na rike hannunsa har yanzu hawaye bai da zubo min ba nace"Baba wai dan Allah me yake damunka kwana biyu ka'ki lafiya kullum cikin rashin kuzari da karfin jiki gashi kuma ka'ki ka bari a kira mai kula da lafiya yazo ya duba ka." A hankali yace."Sumayya ba wani ciwo mai tsanani bane yake damuna zazza'bi ne mai zafi sai hajijiya gami da rashin kuzari to ni dik a tunani na ko shawara ce shiyasa na mayar da hankalina gurin shan maganinta amma yanzu ina ganin dole kije ki kira d'aya daga cikin masu kula da lafiya yazo ya dubani dan ni kadai nasan abinda nakeji a cikin jikina. Tambaya hawaye ta share a sanyaye ta kalleni da fadin"Kiji can bangaran masu kula da lafiyar ki kirawo daya daga cikinsu yazo ya dubashi ni kaina jikina yay sanyi da wannan rashin lafiyar tasa a tsaitsaye fa ya kai sati hudu yanayi duk da yana shan maganin shawarar babu sauki kullum jikin rikicewa keyi." Miqewa nayi da sauri nace "Bari naje can gurinsu na samesu." takalma na zura da saurin gaske na kama hanyar sashen masu kula da lafiyar gabad'aya bana cikin hayyacina ina tsananin kaunar mahaifina shiyasa rashin lafiyarsa ta d'aga min hankali mutuka. "Sumayya." Sunana naji an kira da sauri na tsaya ina waigen bayana. babu walwala a fuskarsa ya karaso inda nake tsaye kai tsaye yace."Ina Lawi yake ya bar aikinsa kamata yayi ace kafin mu fita gurin taro ya zubawa dokuna abinci yanda zai ishesu yanzu yanzu na shiga gurin na tarar da gabad'aya babu abinci a gabansu idan fa maimartaba ya samu labarin abinda yake zai fuskanci hukunci." A marairace nace"Buba dan Allah kayi hakuri kada ka kai 'korafi wallahi babana bashi da lafiya tsayin sati hudu yake ciwo a tsaitsaye dukkanin abinda yake dauriya kawai yake dan Allah ka taimaka masa kana bawa dawakan abincin kafin yaji sauqi. "Ke! saurara da wannan maganar.'' Nayi saurin kallonsa kwalla na kokarin zobomin, Ya cigaba da cewa''Kowa da kika gani akawai aikinsa a masarautar nan nawa aikin ma yafi nasa wahala tinda ni kwana nake a tsaye ina zirga zirga banga dalilin da zai sanya na d'auki nauyin wani na d'orawa kaina ba, ke aikin me kike da ba zaki d'auki nauyin mahaifinki ba kafin ya samu lafiya. Hannu nasa na goge hawayen da suka zubo min nace" Shikkenan zanyi kokari ganin na dauki ragamar kula da dawakan kamar yanda babana yake yi amma ka san dai muna zaman karatu ranaku uku a sati ko kuma idan mun zauna tin safe sai yamma muke tashi. D'aga kafad'a yay yace."Ke zaki tsarawa kanki yanda al'amura zasu tafi ni dai na fad'a miki ku kula da aikin ku kada maimartaba yaji wata magana. Ajiyar zuciya na sauke mai zafi! nace"Shikkenan Buba nagode sosai insha Allahu zan iyakacin bakin kokarina." Gyda kansa yayi ya bar gurin, nima da sauri na wuce domin nufar inda nayi niyya. Na jima a tsaye a bakin kofar d'akin nasu ina sallama kafin naji an amsa da fadin"Ko wacece ta shigo.'' Jim nayi ina tunanin shiga dan gabad'ayansu maza ne a ciki ina ganin kamar hakan bai dace ba. Sallama na sakeyi, naji anyi min tsawa! da fad'in "Wai wacece take sallama ne ki shigo ki fadi uzirinki." Shahada nayi na tura kaina dakin....wasu na kwance kan katifunsu wasu kuma na zazzaune daga su sai gajerun wanduna. Daga bakin kofa na tsaya nace"Dan Allah d'aya yazo ya duba babana Lawi bashi da lafiya." Shuru sukayi min kowa ya cigaba da sabgarsa, raina ya 'baci! nace"Magana fa nakeyi muku kuna jina." 'Dantala ya zaburo min da hayaniya yace."Ke! babu wanda zai katse abinda yake a cikinmu yaje ya duba babanki idan kina so ayi miki abinda kike so ki shigo ciki muna bukatarki." Cike da mamaki nake kallonsu nace"aikin ku ne fa mai zai sanya kuce sai nayi muku wani abu sannan zakuyi to ni ba 'yar iska bace idan kun saba latsa 'yan matan dake masarautar to ni ba' irinsu bace kuma wallahi idan bakuyi wasa ba yanzu zanje fadar sarki na sheda masa abinda kuke aikatawa..........A fusace! naga ya miqe yayo kaina zai mareni na kauce da sauri ina kare fuskata....wanda yake da sauqin halin cikinsu ne ya miqe tare da zira rigarsa ya kalleni da fadin" Shige muje na duba jikin mahaifin naki." Da sauri na fita daga dakin gabana sai faduwa yake......Tafiya nake zugwi zugwi ina mamakin al'amarin, kawai naji ana ta'ba min mazaunai! Da sauri na juyo ina kallonsa, murmushi yayi ya sosa kansa ido jawur yace."A gaskiya Sumayya Allah yayi miki baiwa mai mutukar daukar hankali, kina da duk abinda d'a namiji ke bukata a jikin mace kirjinki a cike yake dam-dam uwa uba mazaunai masu masifar rikimin lissafi wallahi tunda kika shiga dakinmu sha'awata ta tashi dan Allah ki bani damar mallakar wannan jikin naki wanda yake kokarin fitar dani hayyacina. Kallonsa kawai nake wani 'katoton abu ya tokare min a ma'koshi nace"Yanzu Usman ashe kaima halinku d'aya dasu Dantala a zahiri inayi maka kallon salihi ashe kaima baka da d'abi'a mai kyau Usuman dan Allah meye amfanin lalata da kukeyi da 'ya'yan mutane idan fa masarauta ta samu labarin abinda kukeyi ba zakuji dad'i ba. A sanyaye ya sosa kansa cikin jin kunya yace."Sumayya dan Allah kiyi hakuri wallahi ni ban fiya haikewa 'yan matan masarautar nan ba su Dantala ne masuyi kema yanzu hankalina ne ya tashi sosai shiyasa na gaza hakuri na kai hannuna mazaunanki amma kiyi hakuri dan Allah kada naji maganar a bakin kowa. Cikin takaici na girgiza kaina tare da juyawa na cigaba da tafiya raina a masifar 'kuntacce. To koda Usuman ya duba babana nan ya gano cewa hawan jini ne ke damunsa hankalinmu ya tashi nida tambaya muka dinga kuka dan mun riga mun san ciwon hawan jini babban ciwo ne gani muke kamar mun kusa muyi bankwana dashi shiyasa gabadaya hankalinmu ya tashi....Usuman ganin duk muna hawaye yasa ya rarrashe mu tare da bamu shawarwarin yanda zamu kula dashi da lafiyarsa yace "Insha Allahu mutukar aka bi dokar da ake bukata masu dauke lalurar suka bi to zai samu lafiya, Ya miqe tare da fad'in " Zaije yanzu ya kawo masa magungunan da zasu taimaka masa...godiya mukayi masa muna zubar da hawayen tausayi...... *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 8:19 AM - ???: *'KWARYA TABI 'KWARYA* *NA* _BINTA UMAR ABBALE🍒_ *bintaumarabbale@gmail.com* *MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION📘🖊?* _'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_ _________________________ *Littafin na kudi ne....!* _#300.....0542382124...Binta Umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai ki same ni ta wannan numbers..08089965176 _07084653262 Zanyi miki bayanin yanda zaki turo katin.......... Ga masu bukatar VIP Group 600 ne_ _Mutanan Nijar zaku tura dala dari ta wannan numbers katin airtal ko orange VIP jakka d'aya 90899076_88137740_ *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 7&8 Tamkar mai tausayin taka k'asa haka yake cire qafa yana tafiya kanshi a 'kasa hannuwansa a goye a baya, Shatima da Moddibo suna gefe da gefansa sai hira sukeyi masa yana dai jinsu da kunne amma ya gagara cewa uffan sai dai idan sun fadi maganar da ta bashi dariya yayi murmushi had'e da girgiza kansa, Yarima Ali mugun miskili ne wanda magana ke masa wuya shiyasa mafi akasari mutane ke ganin kamar dan wulakanci ne 'Dabi'arsa ce ta rashin son magana da hayaniya gami da rashin fara'a 'yan uwansa da iyayensa sun san wannan halin nasa tun yana yaro dashi ya taso, tun kafin su qarasa bakin kofar masu tsaron gurin suka zube gwiwowinsu a kasa sunkuyar da kansu sukayi hade da d'unkule hannuwansu alamun gaisuwa. Shatima da Moddibo ne kawai suka d'aga musu hannu shi kuwa gefan da suke ma bai kallaba ballantana yasan sunayi.......Shatima ne yasa hannu ya bude narkekiyar kofar da zata sada su da falon Fulani wato mahaifiyarsa, A nutse yasa kafarsa cikin falon tare da sauke ajiyar zuciya, lumshe idonsa yayi yana jin wani irin sanyi na ziyartar zuciyarsa yau dai Allah ya dawo dashi gida gaban iyayensa hakika babu wanda ya kaishi farin cikin wannan rana......Bude lumsassun idanunsa yayi ya sauke su a kanta tana gishingide kan kilishi jakadiyarta na gefanta a zaune tana mata firfita da wani irin mafice, Mama fulani kyataccan murmushi ne a fuskarta ta zuba masa ido tana jin wani irin farin ciki a cikin zuciyarta. Da sassarfa ya k'arasa kusa da ita yayi zaman raquma a gabanta tare da sunkuyar da kansa yace."Mammah hakik'a yau ni dake ban san wanda yafi wani farin ciki ba nasan zuciyarki tana cike da farin cikin dawowata gida wannan dalilin ne ya sanya na kasa shiga sashena nace lallai sai nazo nayi tozali dake uwa tagari nayi farin ciki dana dawo gida na sameku cikin koshin lafiya keda maimartaba da duk wani makusancina." Ajiyar zuciya ta sauke ta gyara zamanta hannu ta dora a saman kansa a nutse tace"Allah yayi maka albarka babana nayi mutukar farin cikin dawowarka masarauta lafiya tabbas farin cikin da nake ciki a yau ba zai yafi gaban a kwatanta shi zuciyata tas take da ganinka cikin koshin lafiya babana ka kara girma kayi lafiya ka kara nutsuwa ka cika mutum ta kowane 'bangare babu shakka dole nagodewa ubangiji a bisa wannan karamaci da yayi mana ina rokon Allah ya raya min kai ya albarkaci rayuwarka da zuriar da zaka samu." Hannunta dake saman kansa ya r'iko yasa a bakinsa ya sumbuta lumshe idonsa yay yana murmushi yace."Mammah nagode sosai da adduarki akoda yaushe ina alfaharin kasantuwarki a matsayin mahaifiyata." Murmushi tayi tare da girgiza kanta ta mayar da hankalinta kansu Shatima dake zaune a gefe da gefansa, murmushi ta sakeyi tana kokarin magana suka fara gaisheta, hannunta ta d'ora a saman kansu tace"Ubangiji Allah yayi muku albarka ya had'e kanku kuyi zumunci dan Allah tabbas nasan kuma yau kuna cikin farin cikin dawowar d'an uwanku lafiya." Shatima yace.''Hakane Mammah hakika muna cikin farin ciki mara mislatuwa muna yiwa Allah godiya daya dawo mana dashi gida lafiya. Har yanzu da murmushi a fuskarta tace"Yana da kyau ku rakashi ko wane 'bangare na gidan nan ya gaisa da iyayensa kamar yanda yazo ya gaisa dani." Moddibo yace."Insha Allahu Mammah." Kallonsa tayi har yanzu yana durkushe a gabanta tace"Babana zakuje sauran sashen iyayenka ku gaisa kafin ka shiga gurinka ka huta nasa hadimai sun shirya maka komai da komai." Hannunta ya sumbata cike da bin umarni yace."Mammah abinda kikace shi za'ayi insha Allah."! Miqewa yayi a nutse ya kalli 'yan uwan nasa da fad'in " ku Tashi muje." Shatima da Moddibo suka miqe kai a kasa suka ce "Mammah a tashi lafiya." Hannu ta d'aga musu fuskarta yalwace da fara'a idonta a tsaye a kansu har sai da suka fita daga falon ta girgixa kanta gami da sunkuyar da kanta kasa addua take a cikin zuciyarta kan Allah ya cigaba da had'a kawunansu suyi zumunci tsakani da Allah. *Tushen Labari* Maimartaba Sarki Adamu Abdullahi dattijon mutum ne wanda ya iya mulki gami da jagoranci akan komai maimartaba Adamu Abdullah mutum ne mai tsananin tausayi da jin'kai, baya ta'ba yarda talaka ya kaskanta kuma bai yarda da cuta gami da zalinci ba, al'ummar garin suna mutukar jin dadin mulkinsa gami da yanda yake gudanar da hukunci akan wanda yayi zalinci, Sarki Adamu yana da 'Ya'ya amma dukkaninsu matane d'aya ne Namiji a cikinsu, sai dai 'yan uwansa suna da yawan 'ya'ya maza shi kadai Allah yayiwa albarkar 'ya'ya mata sai ya bashi guda d'aya namiji wanda yake mutukar alfahari dashi kasancewarsa mai tsananin biyayya a gareshi.....Mahaifin Waziri da galadima ya rasu dama a hannunsa suka taso tare da 'ya'yansa tare kuma duk suka gudanar da harkokin karatunsu.........Sulaimanu Dan uwan Sarki Adamu ne ciki daya suka fito shine ya kasance mafi kusa dashi a fada sarki Adamo baya zartar da kowane irin hukunci sai yayi shawara da d'an uwansa wato Waziri Sulaimanu, duk da wannan karamcin da maimartaba keyi masa hakan bai sa ya janye muguwar kiyayyar da yake masa ba da shida zuriarsa kullum burin Waziri Sulaimanu yaga bayan d'an uwansa dan ya tsani ya wayi gari ya ganshi kan karagar mulki.......Shi a yanzu baya sha'awar mulkin tunda shekaru sunja masa yafi sha'awar d'ansa Ciroma ya hau kan kujarar badan komai ba sai dan kada bayan babu ransu a duniya mulki ya cigaba da tabbata a hannun zuriar dan uwan nasa wato Sarki Adamu, shiyasa kullum cikin damuwa yake gami da tunanin ya za'ayi ya ruguza karagar mulkin d'an uwan nasa, Kullum cikin shirya manakisa suke shida d'ansa Ciroma maimartaba sarki Adamu Allah na kareshi daga sharrinsu, Waziri Salmanu ganin ya kwanta ciwo sai jikinsa yay sanyi yana ganin kwanansa ya kare bukatarsa bata biya a kan dan uwansa ba, tabbas jikinsa na bashi mutuwa zaiyi sai kawai ya kira d'ansa ya zaunar dashi suka yanke shawarar karshe a tsakaninsu.......Ciroma mutum ne mara tsoron Allah da tunanin makomarsa, Kai tsaye ya shiga biye biyen malaman tsubbu bai bari ba har sai da bukatarsa ta biya ganin ya durkusar da maimartaba, mugwayen aljannu sun shafe jinsa da ganinsa kana sun kumbura masa jiki yana kwance sai sai komai ayi masa.....Wannan al'amari yayi wa Waziri Sulaimanu dadi mutuka yana kwance rai a hannun Allah amma 'kara tsarawa d'an nasa sharri yake yi. Hankalin iyalan Mairataba ya tashi mutuka gaya jama'ar gari suka shiga tsananin tashin hankali da damuwar rashin lafiyar data samu shugaba nagari malamai suka dinga bada taimakonsu iyakacin bakin kokarinsu.......Waziri Sulaimanu ya tara su kaf a guri daya yace"Tunda al'amarin ya kasance a haka to shi a matsayinsa na mai zartar da hukunci da yawun d'an uwansa wato maimartaba Sarki Adamu ya wakilta AbdulJabbar wato Ciroma ya zauna kan karagar mulki kafin aga abinda Allah zai zartar.....Da yawa daga cikinsu babu wanda yay na'am da wannan hukuncin to amma saboda gudun tashin hankali da gutsiri tsoma yasa sukayi fatan alkairi ga hukuncin da ya yanke........ba'a wani ja dogon lokaci ba Ciroma ya soma zama a fada ya cigaba da gudanar da mulki cikin rashin iyawa gami da tsantsar mugunta da zalinci.........A take jama'ar gari suka gane inda ya dosa gabad'aya yafi bada muhimanci akan harkar zalinci ko sharia aka kawo gabansa baya iya yanke hukuncin da sharia ta tanadar shi a ganinsa duk abinda yake daidai ne, Jama'a suka dinga k'orafi gami da surutai har labari ya isa kunan gomnati, a lokacin ta shigo cikin al'amarin bata kuma ja wani dogon lokaci ba ta sauke Ciroma daga kan kujerar mulkin, sannan kafin gomnati ta d'ora wani a matsayin sabon sarki sai da ta duba cancanta tukkuna ta za'bi Abdul-aziz ya maye gurbin mahaifinsa tunda shi cuta ta kwantar dashi.......Komai na saurata gomnati ta damqawa Abdul-aziz jama'ar gari suka dinga farin cikin samun sa a matsayin shugaba.......Wannan al'amari yayi wa Waziri Sulaimanu da d'ansa ciwo dan Ciroma kulle kansa yayi a daki ya dinga bankar giya yana tam'bele shi kadai sai zage zage yake yana surutai...........Waziri Sulaimanu kuwa sai muce tsabar bacin rai ne yasa ya had'iyi zuciya ya mutu sai shiga akayi aka ga gawarsa.....Hankalin iyalansa yayi tsananin tashi suka dinga kuka suna tofin alatsine ga zuriar Adamu suna ganin kamar sune sukayi sanadiyar mutuwar mahaifinsu.......Tun daga mutuwar Waziri Sulaimanu gaba mai tsanani ta shiga tsakanin zuria guda biyu har yanzu kuma itace akeyi 'ya'ya da jikoki sai dai kowa na kokarin 'boye bakin cikinsa akan dan uwansa amma daidai da kwayar zarra babu mai kaunar d'an uwansa..........bayan rasuwar Waziri Sulaimanu da sati uku Ciroma yabi dare da rana yaje ya sanyawa Sarki Adamu fillo ya toshe masa hanci murus! ya kashe shi har lahira ya fito daga dakin ba tare da kowa ya ganshi ba.....Shima iyalinsa shiga sukayi suka ga gawarsa al'amarin da yayi masifar tashin hankalinsu, Mutuwar Sarki Adamu ta girgiza zukatan al'ummar gari dayawa yawansu suka dinga kokawa suna fad'ar kyawawan halayensa............ *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 8:19 AM - ???: *'KWARYA TABI 'KWARYA* *NA* _BINTA UMAR ABBALE🍒_ *bintaumarabbale@gmail.com* *MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION📘🖊?* _'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_ _________________________ *Littafin na kudi ne....!* _#300.....0542382124...Binta Umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai ki same ni ta wannan numbers..08089965176 _07084653262 Zanyi miki bayanin yanda zaki turo katin.......... Ga masu bukatar VIP Group 600 ne_ _Mutanan Nijar zaku tura dala dari ta wannan numbers katin airtal ko orange VIP jakka d'aya 90899076_88137740_ *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah) 11&12 Tun bayan fitar su Satima daga 'bangaransa yake zaune shi kadai a guri guda ya gaza ta'buka komai kallon kasan d'akin kawai yake yana mamakin abinda ke faruwa a masarautar a lokacin da ya tafi karatu yana da kuruciya shiyasa baya saurin gane wasu abubuwan amma yanzu shigarsa sauran 'bangarorin gidan domin gaisawa dasu ya fahimci cewar har yanzu bata sauya zani ba a tsakanin iyalan mutane uku da suke da muhimmacin a masarauta ba'a ga maciji kowanne da akwai mugun abu a zuciyarsa dangane da d'an uwansa, Lokacin da suka shiga bangaran mai babban daki gabad'aya sun hallara a falo ita da 'ya'yanta sun kewaye ta babu wanda yasan abinda suke qullawa sai Allah.......Ganin shigowarsu ne yasa suka daidata nutsuwarsu suna masa barka da zuwa dukkaninsu sai ya'ke sukeyi da kokarin nuna masa kulawa, shi ba yaro bane ballantana ya kasa gane yanayin fuskokinsu dan wasu daga cikinsu sai satar kallonsa suke ta'kasan ido, dalilin daya sa kenan ya kasa zama ya miqe da niyyar tafiya........Uwargida na fara'a kamar gaske tace"Magajin Sarki ka tsaya kaci abincin ma tun safe 'Yan uwanka suka baro gidajan mazajensu suka yini suna shirya maka abun tar'ba." Ba tare da ya kalleta ba yace."Nagode Gwaggo ina ganin za'a iya kai min abincin sashena idan na samu nutsuwa sai na zauna naci." Ta washe bakinta cike da jin dadi tace"To shikkenan yanzu zansa a kai maka kamar yanda ka bukata." A nutse ya juya domin yiwa 'yan uwan nasa godiya sai kawai yaga sunyi masa caaa! da ido da sauri ya sunkuyar da kansa yana mamakin kallon da suke masa tamkar basu taba ganinsa ba, babu cikakkiyar walwala a maganarsa yace." My Aunt's ina godiya da hidima." Da farin ciki a fuskokinsu suka shiga amsawa, rufaffun takalmasa yasa ya fita daga falon, a tsaye a samu su Shatima na jiransa ya fito, kai tsaye suka wuce side din Baba Waziri nan ya samu cikakkiyar karba da kulawa gurin matayensa kamar yanda yake tsammani cike da jin kaunarsu yay musu sallama, Bangaran Ciroma da Galadima kuwa bai samu wata cikakkiyar kulawa ba dan kafatanin su adawa suke dashi Shatima da Moddibo ne kawai suke d'an nuna masa kauna da kulawa suma d'in Allah ne kad'ai yasan abinda ke zuciyarsu.......Wannan dalilin ne yasa tunda ya zauna yake tunanin al'amarin a rayuwarsa ya tsani rabuwar kai da lalacewar zumunci! ya fahimci suna masa hassada sosai saboda mahaifinsa ne ke kan mulki dukkaninsu suna zargin kamar shine zai maye gurbin mahaifinsa bayan Allah ya dauki ransa wanda shi kuma basu san mulki da wani abinda ya shafeshi baya daga cikin tsarin rayuwarsa, a wannan zamanin jan ragamar al'umma na da wahala mutuka shiyasa gabadaya baya da ra'ayi maye gurbin mahaifinsa. Ya jima zaune a gefen katafaran gadonsa daya sha shimfid'u na alfarma irin na saurata kafin ya miqe a nutse ya nufi toilet din wanda shi kansa abin kallo ne duk abinda mutum ke bukata a kwai a cikin toilet d'in, tsaf yayi wanka ya fito daure da towel a k'ugunsa, a bakin k'ofa ya samu wani bawa hannunsa ringume da kayan sawa irin na sarauta. Gefan gado ya samu ya zauna ba tare da yace komai ba, bawan ya karaso tare da durkusawa a gabanshi yace."Ranka ya dade ni sunana Haruna ni zan dinga yi maka hidima da duk abinda kake bukata na shigo naji kana wanka sai na dau'ko maka tufafin da suka dace.'' A nutse ya d'ago kansa yana kallon kayan dake hannun bawan, manyan kaya ne irin na saurata har da nad'i da katuwar alkyabba sam ba zai iya sanya kayan nauyi a jikinsa ba. Girgiza masa kansa yayi a nutse yace."Mayar da wa'innan kayan ka dauko min masu sauki." Da saurin ya miqe da kayan a hannunsa ya bud'e shirgegiyar wardorobe din dake kafe a bangon dakin ya ajiye kayan tare da nemo masa irin kayan da yake bukata......Farin yadi filtex mai taushin gaske ya dauko mashi ya jiye kusa dashi kana ya sake komawa wardorbe din ya dauko wani dan madaidaicin akwati shima yazo ya ajiye masa a kusa dashi........Wata iriyar hula naga ya dauko mai tafe da takalminta yazo ya tsuguna tare da cire ledar data lullube hular da takalmin ya d'ora kan kayan ya miqe tsaye da sauri tare da matsawa gefe guda kansa a kasa yace."Ranka ya dad'e na dauko maka dukkanin abin bukata ka duba ka gani idan da akwai wani abinda kake bukata. Gefan da kayan suke a ajiye ya duba minti biyu yana kallon gurin kafin yace."Jeka nagode." Da sauri ya sunkuyar da kansa kasa gami da fadin"Godiya nake Magajin sarki." yana gama maganarsa ya bude kofar dakin ya fita da saurin gaske........A nutse ya miqe ya nufi gaban mirror din dake cike da kayan shafe shafe da turaruka na mussaman irin na masu sarauta, Cream kawai ya shafa a jikinsa ya shafawa jikinsa turare mai kamshi, kana ya bar gurin, tsaf ya shirya jikinsa cikin farin yadin wanda akayi masa d'inki mai yankakken hannu irin na zaman gida gaban rigar da bayanta anyi aiki da farin zare wanda yake nuni da tambarin masarautar, a nutse ya bude akwatin nan naga tarin agoguna da manya manyan zubonan azurfa kala kala sai sheqi sukeyi, agogo mai sarqa yasa a hannunshi na dama kana ya zura wasu zubonan azurfa a tsayunsa guda biyu na hagu da dama, zubonan suyi masa kyau sosai da sosai. ya mayar da a kwatin ya rufe ya dauki hular yana gyarata hula ce aka d'inkata da wani irin yadi mafi akasari ma masu saurata suke amfani da ita tsayin hular ne ya bashi dariya ya dinga duba hular yana tunanin ajiyeta ya bar kansa a haka sai dai yayi dubarar lankafe saman ta ya rage mata tsayi yasa a kansa kana ya zura takalman dake gabanshi masu kalar hular .....Gaban mirror ya tsaya yana sake duba kansa, murmushi ya dinga yi yana shafa siririn sajen fuskarsa lallai malam bahaushe yayi gaskiya da yake fad'in kowa ya bar gida to gida ya barshi, yaushe rabonsa da sanya manyan kaya a jikinsa, sai yaga shi kansa ya k'arayiwa kansa kyau da kwarjini wannan zungureriyar hular da yake wa dariya yaga tayi masa kyau sosai ta sake fito masa da kewayayyar fuskarsa mai dauke da k'ayataccen sajensa, ajiyar zuciya ya sauke a nutse ya bar gurin mirror kai tsaye hanyar fita daga dakin ya nufa...........Yana fitowa Haruna dake tsaye kamar gunki a kofar dakin yayi kasa da kansa tare da fadin"Barka da fitowa." Ba tare da yace masa komai ba ya wuce cikin falon.....Nan ya ganta a hakimce a kan kujera k'afarta d'aya kan 'daya tana sakar masa kyakkyawan murmushi...........Idonsa a tsaye a kanta ya samu guri ya zauna cikin d'aya daga cikin k'ayattatun kujerun dake kewaye da falon Wani irin zama yayi irin na masu mulki yasa mata idonsa yana kallo fuskarsa babu d'igon annuri. Gimbiya Lawisa cikin iyayi da iyawa ta ma'kale murya tare da fadin "Barka da fitowa magajin sarki inayi maka barka da dawowa masarauta lafiya." falon shuru yayi bayan gama maganarta tana jiran amsarsa taji shuru bece komai ba, dago kai tayi tana kallonsa taga yana ta kallon jikinta.......Yarima Ali na da muguwar d'abi'ar san mata dan ko acan amurukan ma shagalinsa ya sha da matan turawa da bakaken fata amma duk kulafucinsa bai ta'ba zina ba sai dai romancing nan yake biyawa kansa bukata, yana da bala'in san mata masu kyau da k'irar jiki, Gimbiya Lawisa nada kyau da lafiyayyan jiki shiyasa ya gaza dauke idonsa daga kanta sha'awarta ce ta d'arsu a zuciyarsa. Ganin tana kallonsa tana murmushi yasa yayi gyaran murya da kyar yace."Daga wane 'bangare kike.''? 'Yar dariya tayi tana kallonsa tace"Yanzu dan Allah baka gane ni ba ? nice fa Lawisa ta gurin Baba Ciroma 'kanwar Moddibo."' Sajensa ya shafa har yanzu babu fara'a a fuskarsa yace."Ya za'ayi na gane ki bayan rabona daku sama da shekara goma lokacin dana bar gida ina tsammanin baki kai shekaru bakwai a duniya ba." Tace"Eh hakane kam shekaruna takwas a lokacin daka tafi karatu amma kuma ni kaga ban mance da kai ba."! Shuru yay yana kallonta, Ta cigaba da cewa"Wannan dalilin ne yasa ma na shirya gagarimar walima domin taya ka murnar dawowa gida lafiya.'' Murmushi yayi yana kallonta yace."Nagode 'Kanwata inaso naga ana nuna kulawa akaina nayi farin ciki sosai da wannan karamcin yaushe ne kika tsayar da taron. Cikin farin ciki da jin dadi tace"Naji dadi sosai daka kar'bi magana ta da mahimanci nagode sosai sannan kuma ranar jumaa ne ranar dana tsayar domin taron walimar." Da ragowar murmushi a fuskarsa yace."To shikkenan Allah ya kaimu ranar lafiya." Falon yayi shuru Lawisa sai sa'ke-sa'ke take a cikin ranta tana tunanin ko kawai ta fad'a masa tana sonsa tunda taga nan da nan ya kar'bi maganar da ta kawo masa da muhimanci.....tana kokarin tayi magana......Aunty Safiyya d'aya daga cikin yayyunsa ta shigo falon bayanta wasu bayi ne mata guda biyu suna dauke da tire din abinci kai tsaye can gurin daining suka..........Aunty Safiyya ganin Lawisa a zaune tana murmushi yasa tayi saurin kallonta ta kalli 'kanin nata sai kawai taji farin cikin ganinsu a tare lallai babu shakka Lawisa zata taimaka musu gurin ganin bukatarsu ta biya a kansa.....Cike da farin ciki gami da nuna jin dad'i tace"A'a k'anina soyayya akeyi ne.'' Kansa ya sunkuyar qasa bece uffan ba. Ita kuwa Lawisa sai murmushi takeyi na jin dadi tana kallon aunty Saffiyan tana sunkuyar da kanta. Kusa dashi taje ta zauna kamar gaske ta dafa kafad'arsa da fadin'' A gaskiya nayi farin cikin ganin ku a tare dama babban burinmu a yanzu kayi aure ka sake zama babban mutum to alhamdullilahi tunda ma 'yar gida za'ayi towo na mai na ne abun yayi dad'i nasan kuma iyayenmu zasuyi farin ciki mutuka, kuma inaso na tabbatar maka da cewar kayi sa'ar matar aure domin dai Lawisa babu abinda ta nema ta rasa na bangaran kyawun hali ga uwa uba kyawun sura." Ya d'ago kanshi a nutse yana kallonta "Aunty Safiyya waye yace miki soyayya muke? fitowa ta kenan daga daki na sameta a zaune dan sai da ta gabatar min da kanta na gane cewar famliy nace, tazo tana sheda min walimar da ta shirya domin murnar dawowata gida wannan shine dalilin daya saka kika gan mu a tare." *BINTA UMAR ABBALE* Shearing 👏🏻👏🏻 2/11/21, 8:19 AM - ???: *'KWARYA TABI 'KWARYA* *NA* _BINTA UMAR ABBALE🍒_ *bintaumarabbale@gmail.com* *MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION📘🖊?* _'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_ _________________________ *Littafin na kudi ne....!* _#300.....0542382124...Binta Umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai ki same ni ta wannan numbers..08089965176 _07084653262 Zanyi miki bayanin yanda zaki turo katin.......... Ga masu bukatar VIP Group 600 ne_ _Mutanan Nijar zaku tura dala dari ta wannan numbers katin airtal ko orange VIP jakka d'aya 90899076_88137740_ *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 9&10 Sarki Abdul-aziz yayi gadon halin mahaifinsa marigayi Maimartaba sarki Adamu gurin kyawawan halaye sosai al'ummar gari ke jin dadin mulkinsa gabadaya 'yan uwansa sunyi masa mubaya ma'ana sun bashi hadin kai sosai amma banda Ciroma muguwar hassada yake masa da kasantuwarsa a kan karagar mulki Ciroma babu irin qulunboton da ba yayi akan ya ruguza mulkin sarki Abdul-aziz Allah bai bashi nasara ba daga karshe sai ya hakura da biye biyen bokayen ya dawo yana shirya mana'kisa ta karkashin qasa....Sarki Abdul-aziz na da mata biyu Gimbiya Huwaila itace uwar gida ana kiranta da mai babban da'ki haihuwar su bakwai tare amma duk mata ne.....Gimbiya Hawwa 'yar sarkin Agadaz itace matarsa ta biyu ana kiranta da Fulani sai da suka shekara shida da aure ta samu ciki maimartaba ya tsananta addua akan cikin yana addua akan Allah ya azurtashi da samun d'a namiji ya zama magajinsa...........Allah maji rokon bawansa sai ya amsa masa adduarsa a daidai lokacin da mutane ke tsammanin Fulani zata haifi mace sai Allah ya nuna musu ikonsa Aliyu ya diro duniya cikin koshin lafiya da kuzari.....Haihuwa wannan yaro tayi masifar tashin hankalin Ciroma ya rasa inda zai saka kansa yaji dadi, shi duk a tunaninsa Abdul-aziz ba zai ta'ba haihuwar da namiji ba saboda yana ganin duk 'ya'yansa mata ne kamar dai yanda mahaifinsa ya dinga haifar 'ya'ya mata kafin ya rasu.......Mai d'akinsa rasa gane kansa tayi a lokacin dan kulle kansa yake a daki yayi ta surkulle lallai sai yaga karshen jinjirin daka a haifa, wanda tunda ya dira a duniya mahaifiyarsa ta d,daura masa wata 'yar sar'ka a wuyansa mai dauke da ayatulkursiyu a jiki, wannan dalilin yasa duk tsaface tsafacen da yake yi baya tasiri. 'Bangaran Mai babban daki kuwa itama ita da yaranta rasa nutsuwa sukayi dan gabad'ayansu basu tsammanin Fulani zata haife cikin jikinta lafiya ba saboda irin fadi tashin da sukeyi a cewar 'ya'yan wai su ba zasu had'a uba da kowa ba shiyasa tun sanda mahaifin nasu ya auro Fulani Hawwa suka tashi a tsaye dasu da mahaifiyarsu suka dinga jifanta da asiri iri iri wanda ya janyo mata matsala dik lokacin data samu ciki daga zarar yayi kwari sai ya zube hankalinta ya tashi sosai ta dage da azkar gami da rokon Allah ya kareta dan tayi imani cewar al'janu ne ke ra'bar jikinta tunda wani lokacin idan ta kwanta bacci suna zuwa suyi ta tsorata ta.......tunda ta samu cikin Aliyu ta dage da adduar har Allah yasa yayi k'wari gashi cikin ikon Allah ta haifeshi lafiya dalilin daya sa kenan tana haihuwarsa ta daura masa wannan laya mai dauke da ayatulkursiyu saboda tasan tilas ita da yaron su fuskaci kalubale mai girma a masarauta...........Yarima Ali ya taso cikin kauna da so da kulawar iyayensa duk wanda ya kwana ya tashi a cikin gidan yana kaunarsa, Ita kanta mai babban daki ganin kamar maimartaba naso ya gane manufarta akan yaron yasa ta zauna da 'ya'yanta ta umarce su akan kada su sake su nunawa yaron 'kiyayyarsu a fili komai za'ayi ta karkashin kasa za'ayi masa, wannan dalilin yasa suke danne hassadarsu a kansa suke nuna masa kauna ammfa Allah ne kadai yasan abinda ke zuciyoyinsu..........'Bangaran 'yan uwan mahaifinsa kuwa babu wanda ke nuna masa kauna da kulawa sama da Waziri shike jansa a jikinsa sosai yana nuna masa so hakan yana yiwa maimartaba dadi a cikin ransa yana kuma yiwa dan uwan sa addua akan Allah shima ya azurtashi da 'ya'ya masu albarka, Waziri Abdul-raham matansa uku amma duk cikinsu babu wacce ta ta'ba haihuwa sai da ya auri matarsa ta uku da yake bazawarace tana da 'ya'ya a wani a gidan sannan aka gane cewa rashin haihuwa daga gurinsa ne shiyasa yake masifar kaunar 'ya'yan 'yan uwansa.......wannan dalilin yasa Ciroma da Galadima suke jin haushinsa dan ganin kamar yana fifita Yarima Ali akan 'ya'yansu Galadima shine mahaifin Shatima shi kuma Ciroma shine mahafin Moddibbo wanda yaci sunan mahaifinsa shine suke kiransa da suna Moddibo, Ciroma Abdul-Jabbar nada 'ya'ya goma dan duk yafi 'yan uwansa yawan 'ya'ya shiyasa har kullum yake fatan sarauta ta dawo hannunsa, mata shida maza hud'u, cikin 'ya'yanshi akwai mai izzah da taqama tamkar ubanta ne a sarki a cikin masarautar haka take rashin mutunci tare da cin mutuncin duk wanda tayi ra'ayi, Gimbiya Lawisa kyakkyawa ce ta karshe sai dai ko kusa ko alama bata da kyawun hali tana da d'abiar izigilanci da wulakanta mutane mutum komai girmansa bai wuce cin mutunci a gurinta ba........Gimbiya Lawisa tun kafin tayi wayo tayi hankali Allah ya d'ora mata masifar son Yarima Ali a cikin ranta duk da tana yarinya k'ank'anuwa ya tafi karatu hakan besa ta mance kammanin sa ba. shiyasa yanzu take ta murna da farin cikin dawowarsa masarauta sai shirye shiryen walima takeyi domin nuna masa farin cikin dawowarsa lafiya........Da kanta ta shirya tsaf cikin shiga ta alfarma tare da bayin dake take mata baya ta nufi 'bangaransa domin sheda masa abinda ta shirya masa na taya murna.......... *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 8:19 AM - ???: *'KWARYA TABI 'KWARYA* *NA* _BINTA UMAR ABBALE🍒_ *bintaumarabbale@gmail.com* *MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION📘🖊?* _'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_ _________________________ *Littafin na kudi ne....!* _#300.....0542382124...Binta Umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai ki same ni ta wannan numbers..08089965176 _07084653262 Zanyi miki bayanin yanda zaki turo katin.......... Ga masu bukatar VIP Group 600 ne_ _Mutanan Nijar zaku tura dala dari ta wannan numbers katin airtal ko orange VIP jakka d'aya 90899076_88137740_ *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah) 13&14 Aunty Safiyya a nutse take kallonsa kafin tace"Kai kuwa Magajin sarki meye laifin Lawisa dan Allah kada kaje ka dauko mana ta waje gwanda ka duba a cikin gida ina ganin kamar haka zaifi alkairi." Shuru yayi mata tare da sunkuyar da kansa. Tace"Idan ka auri 'yar uwarka a ganina sai kafi samun cikakkiyar kulawa kuma tabbas hakan zai faranta ran iyayenmu dan Allah ka duba maganata da kyau kaji ko."! har yanzu kansa na sunkuye a kasa ya'ki kallonta ballantana ya bata amsa. mirmushi tayi tare da mikewa da fadin"Miskili kenan to kai dan Allah da irin wannan halin naka wacece zata iya zama da kai idan ba 'yar uwarka ba? babu macan da zata juri wannan wulakancin naka." 'Dago kansa yay yana kallonta cikin rashin walwala yace."Aunt Safiyya mai yasa kuke yi min irin wannan kallon ne? wallahi ban san ya ake wulakanci ba a rayuwa ku lura da kyau da'bia tace rashin son doguwar magana shiyasa nayi shuru na kyale ki amma duk irin maganganun da kikeyi ina jinki." Murmushi tayi tana kallonsa tace"Eh ni zan fadawa kowa hakan d'abi'ar kace shiyasa ma ai nace bama so ka auri bare gwara ka auri ta gida domin sai tafi jurar zama da halayen ka." murmushi yay wanda ya tsaya iya lab'bansa yace."Aunt Safiyya ki bar wannan maganar dan Allah.'' Jin abinda yace yasa Lawisa saurin kallonsa gabanta na faduwa lallai wallahi tasa rai ganin aunty Safiyya ta shiga maganar yasa take jin tamkar ma ta aure shi ta gama. Aunty Safiyya ta kalleta tare da fad'in "Lawisa kina sonsa ko."? babu kunya tace" Eh aunty. " murmushi tayi tare da kama hanyar fita tana fadin"Ba zan tafi gida ba har sai na bari an tashi daga fada na fadawa maimartaba halin da ake ciki. Da sauri ya dago kansa yana kallon bayanta cike da mamakin jin abinda ta fad'a......Fuska a kirne ya kalleta da fad'in "Tashi ki fitar min a daki wato dama abinda ya shigo dake kenan? waye ya fad'a miki ina sha'awar auran zumunci dake."? Lawisa gabanta ya dinga faduwa tana so tayi magana amma ta kasa saboda tsabar kwarjin da yayi mata gashi ya tsareta da idanunsa masu girman da furgita mara gaskiya. A sanyaye ta miqe tana gyara alkyabbarta hanyar fita ta kama ranta sai tafarfasa yake yi lallai wai duk wannan kyawun nata da kyawun surar jikinta bata burgeshi ba hakika taji takaicin tsawar da yayi mata meye laifinta da zaice baya sha'awar auran zumunci da ita.......masu take mata baya ganin ta fito fusace yasa suka shiga hankalinsu da sauri suka rufa mata baya suna sunkuyar da kansu 'kasa............. **** Cikin saurin na fito daga gurin mu domin zuwa duba dawakan da babana ke hidimarsu tun safe dana zuba musu abinci ban sake zuwa duba su ba saboda yini mukayi wankin kayanmu nida mahaifiyata wannan dalilin ne yasa ban je gurin da wuri ba............Ina daf da shiga kofar dawakan na hangeta ita da masu take mata baya, sanin halinta naso a girmamata yasa na sunkuyar da kaina qasa har suka karaso gurin nace" Barka da yamma ranki shi dad'e." banza tayi min bata amsa ba sai hararata take ni kam ban san me yasa ta tsaneni ba tsakanina da ita harara ne da kallon banza. Ganin taki amsawa yasa da sauri nayi nufin shiga kofar......Naji ta daka min tsawa da fad'in "Ke! mahaukaciya dawo ki tsaya a inda kike ko nace ki tafi ne."? Cike da mamaki nake kallonta kafin nace" Ranki ya dad'e na gaishe ki kin'ki amsawa me kike so nayi miki a yanzu ina da uziri zan zubawa dawakai abinci." Kallona naga tanayi tana girgiza kanta, ni kaina sai da na gama maganar nazo ina nadama sabida nasan na tarowa kaina jaraba, ni haka nake bana barin magana a cikina idan mutum ya gaya min biyar sai na fada masa goma gashi bani da tsoro ko kad'an cikin dubbanin mutane aka ajiye ni zan iya kwatar kaina saboda ina da baki. Inda nake tazo ta tsaya tana yi min wani irin kallon raini! kafin na ankara naji yawun bakinta a fuskata, da sauri na dago kaina ina kallonta........Tana wani irin huci! tace"Yanzu Sumayya a matsayinki na makaskanciyar baiwa a gidan nan har kina da damar tsallake umarnina nace miki ga abinda nake bukata kice kina da uziri."? Hannu nasa na goge yawun data tofa min nace"Ranki ya dade ki gafarce iya bakin kokarina nayi miki na baki girmanki na risina na gaishe shin to dan Allah dan annabi me kike so nayi miki ." Mari! ta kwad'a min a kumatuna kafin na dawo daidai ta sake waska min wani a d'aya gefan! Ido jawur nake kallonta ina jin tamkar nima na fitar da hannu na rama! marin......hannu ta daga kawai tana nuna ni tsabar b'acin ran dana kuntunka mata ya hanata magana, a rayuwar Gimbiya Lawisa tun tasowarta a gidan sarautar babu wanda ya ta'ba yi mata gardama akan umarninta sai Sumayya......Juyawa nayi zan shiga kofar dawakai ta janyo faffad'an wuyan rigata aikuwa a take rigar ta yage da yake rigar ta yadi ce mai dogon hannu zanin kuma na shadda kamfala shine uniform din mu a cikin gidan mata zani maza wando amma dai duk ranar jumaa muna sanya tufafi masu kyau domin girmama ranar haka ma ranar sallar 'karama da babba sarki nayi mana d'inkuna na atamfofi muyi ado domin murna da zuwan ranar.........Hannu nasa da sauri na dafe wuyan rigar ganin yana kokarin sab'ulewa. Tsira mata ido nayi rai a 'bace! nace tsirara zakiyi min ne? kada fa ki manta kema macace idan kinyi min tsirara a idanun jama'a kamar kin tonawa kanki asiri ne." Wani marin ta sake bani tana huci! ni kuma mirmushin takaici nayi hannuna dafe da kuncina ina kallon ikon Allah........Jama'a ne suka taru a gurin sai bata hakuri suke harda masu durkusa mata, Buba ta kalla dake riqe da shar'be'biyar bulala tace"Bani bulalar nan." Da sauri ya mika mata yana fadin "Tuba take ranki ya d'ad'e."........Ganin ta d'aga bulalar zata shaud'a min yasa nayi saurin fizgewa na nannad'eta a hannuna sai kawai muka tsirawa juna ido nida ita jama'ar dake gurin da ita kanta mamakin karfin halina suke.........Ta girgiza kanta tana kallon Buba tace" Inaso ka samo igiya mai kauri ka daure mata hannuwa da kafafu yau nayi al'kawarin sai naga karshen taurin kanki."..............Kallonta kawai nake tsabar takaici da bakin ciki yasa nake jin kamar na zazzabga mata bulalar dake hannuna, ina kallon Buba ya tawo da murtukekiyar igiya gabana ya yanke ya fad'i ganin ya nufo inda nake....................yasa na juya baya ina neman mafaka babu dan duk ko ina mutane ne sun kewaye mu, tsugunawa nayi a kusurwa hawaye ya kwace min, Buba babu tausayi yazo ya shiga kici kicin daure min hannuwa da kafafuna sai tirje tirje nake ina haurinsa amma sai da ya samu nasarar daure ni tamau! gwiwowina a kasa kaina a sunkuye na soma jin saukar bulala a gadon bayana.......tsabar taurin kaina yasa na kasa motsi ina dai jin radad'in bulalar na ratsa min jiki amma saboda na nuna mata a banza takeyi yasa na daure.........Gimbiya Lawisa sai da jikinta yay sanyi ganin ko gezau na 'kiyi ballanatana na nuna mata ina jin zafin bulalar, tunani tayi ko itace ba ta iya bulalar ba rai a 'bace tace"Buba zo kayi mata ka tabbatar da cewa ta ratsa jikinta shegiya basamudiya yanda take da wannan gansameman jikin dama ai duka ba zai ratsa ta ba." Gefe ta koma tana haki! dan ba karamin galabaita tayi ba.'' Buba cike da bin umarni ya daga bulalar zai shaud'a mata, muryarsa ta katse masa hanzari.....Kafatanin jama'ar dake gurin suka juya suna kallonsa ganin ya nufo gurin ne yasa kowa yayi k'asa da kansa har ita Lawisan sunkuyar da kanta tayi......Cikin nutsuwa ya 'karaso gurin aka bud'a masa hanya ya shiga har inda nake durkushe! ta 'kasan idona nake kallonsa yana tsaye hannuwansa duk biyun a baya sai kalle kalle yake a gurin kafin naga ya kalleta babu fara'a a tare dashi yace."Yace."Meke faruwa ina zaune Haruna ke sheda min ga jama'a sun taru kuma kina gurin saboda haka inaso nasan abinda ke faruwa." *BINTA UMAR ABBALE* Shearing👏🏻 2/11/21, 8:19 AM - ???: *'KWARYA TABI 'KWARYA* *NA* _BINTA UMAR ABBALE🍒_ *bintaumarabbale@gmail.com* *MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION📘🖊?* _'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_ _________________________ *Littafin na kudi ne....!* _#300.....0542382124...Binta Umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai ki same ni ta wannan numbers..08089965176 _07084653262 Zanyi miki bayanin yanda zaki turo katin.......... Ga masu bukatar VIP Group 600 ne_ _Mutanan Nijar zaku tura dala dari ta wannan numbers katin airtal ko orange VIP jakka d'aya 90899076_88137740_ *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 17&18 Tana kishingid'e a killace a guri guda da cazbaha a hannunta tana lazimi yau ita kadai ce a zaune a falon babu hadimai a kusa da ita ta bukaci zama ita kad'ai ne domin ta kad'aita kanta da mahallicinta shine da dalilin da yasa ta sallami bayin dake kusa da ita. Tunda ya shigo take sakin murmushi idanunta a kansa har ya k'asara kan kilishin da take kishingide zaman raquma yay a gabanta tare da sunkuyar da kansa cikin tsantsar ladabi yace."Mamma barka da yamma." hannunta guda ta dora a saman kanshi tana shafawa gyaran murya tayi tana nuna masa cewar akwai abunda takeyi....Kansa ya dago yana kallonta sai ta nuna masa carbin dake hannunta tana murmushi had'e dayi masa nuni dacewar ya jira ta kammala. Murmushi yay a nutse yasa hannu kan tire din dake gabanta wanda ke cike da kayan marmari.. tufa(apple) ya d'auka yasa a bakinsa ya gutsira yana sake gyara zamansa a gurin. Kallonsa take tana murmushi mai ma'ana wanda kai kana ganin yanayin fuskarta zaka gane cewar tana cikin farin ciki kuma akwai soyayya da shaquwa mai yawa a tsakaninta da yaron nata. Magajin sarki sai da ya cinye tufa(apple) uku tukkuna ta kammala lazimin a nutse tace"Babana barka da yamma." Ya dago kansa da sauri yace."Mammah barka dai ina fatan kin wuni cikin koshin lafiya." Yafadi maganar a sanda yake kokarin riko hannuwanta. Tace."Lafiya lau na wuni ina fatan baka da matsala dan tun safe nake jiran shigowarka yau ba kayi shigowar safe ba ina fatan lafiya." Zamansa ya gyara har yanzu kuma hannuwansa na rike da nata yace."Wallahi Mammah yau bacci na yini ina yi sai gefin la'asar na tashi nayi wanka wannan shine dalilin da yasa ban shigo mun gaisa ba." Ajiyar zuciya ta sauke tace"To alhamdulillahi tunda lafiyarka lau dama akwai muhimiyyar maganar da nake so mu tattauna da kai." Ya sake gyara zamansa cikin kulawa yace."Ina sauraran maganar Mammah." Da farin ciki ta tare da ita tace"Ashe bayan dawowarka gida kun shirya tsakaninku kai da Lawisa 'yar gurin Kawun ka Ciroma d'azu da safe maimartaba yake sheda min yanda al'amura suka kasance hakika naji dadi sosai daka za'bi matar aure acikin dangi ina ganin hakan sai yafi mana kwanciyar hankali da kai baki daya." Shiru yayi kansa a kasa ya rasa abinda zaice. ashe sai da aunt Safiyya taje ta fad'i maganar wallahi shi ya dauka da wasa takeyi! tunda yake bai ta'ba sha'awar auran zumunci ba saboda gudun lalacewarsa yafi so ya fita waje yaje can ya auro saboda baya so ya auri 'yar dangi zumunci ya sake lalacewa dama a lalace yake shiyasa kwata-kwata baiyi na'am da maganar ba ashe sai da taje ta fadi maganar. Fulani ganin yayi shuru tace."Babana ko akwai matsala ne? naga kayi shuru kana tunani kayi min bayani dan ba naso ayi al'amarin nan rayuka su 'baci idan ba kai ke son al'amarin ba to tun kafin tafiya tayi nisa a warwareshi." Zazzafar ajiyar zuciya ya sauke ya kalleta yana kokarin 'boye damuwar dake fuskarsa yace."Mammah ba wani abu bane yasa kika nayi shuru ina tunanin abinda aunty Safiyya ta aikata bayan nayi mata bayani cewar babu wata alaqa ta soyayya a tsakanina da Lawisa kawai tazo ta ganta ne a ranar dana dawo tazo tana sheda min cewa ta shirya walima domin murnar dawowata gida lafiya to ita kuma aunt Safiyyan shine take tunanin soyayya ce a tsakanina da ita. Fulani shuru tayi tana mamakin al'amarin ta kalleshi a nutse tace"To yanzu wace shawara ka yanke dan gaskiya al'amarin yayiwa Maimartaba dadi bashi kadai ba har sauran 'yan uwansa sunyi farin ciki nima kuma naji dadin hakan idan kace ka janye maganar baza suji dadi ba. Murmushi yay wanda ya tsaya iya le'bansa yace."Mammah bana fatan ranar da zata zo na 'bata muku rai dake da maimartaba tunda dai maganar nan ta fita har iyaye sunji to ina ganin babu damuwa zan auri yarinyar amma a gaba dole na 'kara aure mutukar Allah ya had'ani da wacce nake so." Fulani murmushi tayi tana girgiza kanta cike da tsantsar farin ciki a maganarta tace"Ubana ina alfahari dakai mutuka ina jin dadin yanda kake kula dani da gudun 'bacin raina ina rokon Allah ya azurtaka da zuria masu albarka kamar yanda kake mana ladabi da biyayya kai ma ubangiji Allah yasa 'ya'yanka suyi maka. Cikin sakin fuska ya amsa da ameen Mammana.! dama nace ina bukatar masu hidima a sashena domin wani sa'in hidima nayi wa Haruna yawa." Cikin kulawa tace"Ayya ai wannan mai sauki ne ubana dama saboda nasan baka san hayaniya yasa na tura maka Haruna saboda nasan yana da nutsuwa amma insha Allahu zan sake turo maka mutum uku sun isa ko."? Yace."Yace mutum biyu ma sun isa sai su zauna su uku ina ganin hakan yafi" Tace."To shikkenan Ubana kada ka damu insha za'a turo masu hankali da nutsuwa. *** Washe garin ranar bayan mun fito daga gurin karatu ni da Lahira muna tafe muna magana, Haruna yasha gabanmu yace."Sumayya Lahira kuje can b'angaran Fulani ana bukatar'ku.'' Kallonsa nayi nace"Haruna ina fata dai lafiya ba wani laifin mukayi ba." Yace."Babu komai ku kwantar da hankalinku sannan ba ku kad'ai aka nema ba har da sauran 'yan uwa.'' Ajiyar zuciya na sauke nace"Haruna dan Allah zan duba jikin babana kuje kawai na biyo bayanku daga baya." Da sauri yace."Wai sumayya mai yasa kike gardama da umarnin masarauta akwai 'ya'ya da yawa da iyayensu suke halin rashin lafiya amma basa irin abinda kikeyi. Hannu na d'aga masa nace"Haruna abinda yasa kaji nace haka sabida nike bashi magani yanzu haka Tambaya mahafiyata suna d'akin dahuwa(dakin girka abinci) suna aiki girka abinci kuma nasan idan naje bai zama dole a sallame mu da wuri ba shiyasa nace zan fara dubashi na bashi magani tukkuna. Haruna yace."Ba za'a wani dad'e ba insha Allah kedai kawai ki shige muje." Girgiza kaina nayi na kalli Lahira dake rungume da jaka nace"Muje." Haruna gaba yayi da sauri muka rufa masa ba zuwa b'angaran Fulani. A jere muka samu 'yan uwanmu bayi maza da mata sunja layi a bakin k'ofa kai tsaye 'bangaran mata muka nufa nida Lahira muka tsaya shi kuma Haruna da sauri ya bude kofar falon ya shiga ciku.....Surutai ne suka shiga tashi a gurin bayan shigar haruna falon dukkanin mu muna mamakin tara mu da Mammah fulani tayi sabida mun san da cewar ita din macace mai mutunci da karamci bata fiye tara mu taci mana mutunci ba kamar sauran 'bangarorin dake gidan, dukkanin mu dai addua mukeyi akan Allah yasa alkairi ne. Haruna na fitowa muka bishi da kallo ya kalli 'bangaran maza da sauri yace."Ku shigo a nutse." Suka dinga shiga falon a nutse har suka qare, kusan mintina goma sha biyar da shigarsu suka fito kowa ya kama gabansa banda mutum biyu da suka ja gefe suka tsaya. Haruna ya kallemu da fadin"Ku shigo a nutse." Da sauri muka tu'be takalman mu muka fara shiga daya bayan daya. Zubewa mukayi a gabanta muna gaisheta.....Amsawa ta dinga yi cikin walwala tana kallonmu fuska a sake babu nuna 'kyama A nutse ta dinga tambayar sunayenmu muna fad'a mata, ta d'ora idanunta a kaina fuskarta a sake tace"Sumayya ina tsammanin zaki fi 'yan uwanki kuzari da kazar kazar saboda haka ke kad'ai zan dauka a cikin ku zaki kasance daya daga cikin hadiman Magajin Sarki zaki dinga kulawa dashi da duk abunda yake bukata keda sauran 'yan uwanki amma su din maza ne Haruna da Isa da Hamza ke kad'ai ce mace a cikinsu." Tunda take maganar gabana ke fad'uwa sam banyi farin ciki dajin wannan al'amarin ba ba dan komai ba sai dan sanin da nayi cewar bani da lokacin kaina na farko ina d'awaniyya da mahaifina na biyu ina kula da aikinsa dake cikin gidan ina nufin d'awainiya da dawakai, na uku kuma karatun dana k'wallafawa raina a kansa wanda ba kowane yake da ra'ayin yinsa a cikin masarautar ba, dama Maimartaba ya bude sashen karatu a gidan sabida mu, wanda yake da ra'ayi yaje ya dauki darasi na boko dana arabic wanda kuma baya da ra'ayi yayi zamansa to nida iyayena muna da ra'ayin karatu shiyasa suka goya min baya domun na samu ilimi yanzu haka mun kai izifi talatin a cikin al'kur'ani maigirma, sauran littafan addini kuwa nan ma mun sauke wasu 'bangaran boko ma ina fahinta sosai dan ina jin turanci amma ba sosai ba wannan dalilin ya sanya naji gabad'aya banji dadin a'lamarin ba Cikin kokarin danne damuwata na kaskantar da kaina cike da ladabi nace"Godiya nake ranki ya dade hakika naji dadi mutuka da kika za'be ni a matsayin wacce zata kula da sashen Yarima ina rokon ubangiji Allah ya bani ikon daukar amanar da kika bani." Cikin farin ciki Fulani tace."Babu damuwa Sumayya kuna iya tashi ku tafiya Haruna zai jagorance ku zuwa sashen nasa sai ku gabatar masa da kanku a matsayin wanda na turo ku. A nutse muka mike mukayi mata sallama cike da ladabi muka fita daga falon, Haruna dasu Isa suna tsaye suna magana na kallesu fuskata babu walwala nace"Ku muje ko."? Haruna yace."Ke aka za'ba."? Daga masa kaina nayi na kalli Lahira nace"Dan Allah kafin ki shiga gurin ku ki duba babana ki bashi magani idan kuma Tambaya ta dawo shikkenan." Lahira tace"Kada ki damu insha Allah zan dubashi sai kin shigo. Lokacin da muka isa b'angaran nasa a kishingid'e muka same shi cikin furanni yana sanye da 'kananun kaya gabansa kayan marmari ne cikin tire wayarsa yake dubawa fuskar nan a had'e! cikin zuciyata nace "Naga sanda zan ga dariyar guy nan kullum fuska babu rahama Allah dai ya kyauta." Gabansa muka zube gwiwoyinmu a k'asa had'a baki mukayi gurin fad'in "Barka da hutawa Magajin sarki muna fatan mun same ka lafiya."! K'asa mukayi da kanmu bayan mun gama maganar..... Shuru yayi mana kamar bai san damu a gurin ba, raina ya 'baci sosai aqallah mun kai minti goma a gurfane a gabansa kamar wasu masu neman gafara wannan wace irin rayuwa ce. Kallonsa nayi a lokacin da yake kokarin gyara zama karaf! muka had'a ido kwarjini yayi min wanda yasa na ma'kale maganar dake raina nayi kasa da kaina gabana na fad'uwa guy ya tara duk abubuwan da ake bukata yana da kyau sosai gashi dogo abinda yafi birgeni a tare dashi manyan idanunsa wanda suke a lumshe k'wayoyin idanunsa basu cika fari ba sun d'an sirka da ja banta'ba ganin kwayar idanunsa tayi haske ba. muryarsa ce ta katse min nazarin da nake..... *BINTA UMAR ABBALE* Shearing 👏🏻 2/11/21, 8:19 AM - ???: *'KWARYA TABI 'KWARYA* *NA* _BINTA UMAR ABBALE🍒_ *bintaumarabbale@gmail.com* *MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION📘🖊?* _'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_ _________________________ *Littafin na kudi ne....!* _#300.....0542382124...Binta Umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai ki same ni ta wannan numbers..08089965176 _07084653262 Zanyi miki bayanin yanda zaki turo katin.......... Ga masu bukatar VIP Group 600 ne_ _Mutanan Nijar zaku tura dala dari ta wannan numbers katin airtal ko orange VIP jakka d'aya 90899076_88137740_ *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA''ATU S YARI* (Kainuwa dasha Allah✊?) 15&16 Ganin yanda ya tsira mata idanunsa gami da sake tamke fuskarsa ya sanya jikinta yay sanyi tana jin tsoron ya tozarta a gaban wa'inda suke ganin kima da mutuncinta.........Cikin kokarin aro jarumta tace"Tunda nake a cikin gidan nan babu wanda ya ta'ba yi min musu akan umarnin da zan bashi sai wannan ba'kar yarinyar mai fuska irinta ba'kar akuya ta raina ni sosai sai kace ni din abokiyar adawarta ce, gabad'aya mutane suna gaisheni suna bani girma da mutuncina amma ita kokarin ratse ni take ta wuce ina ganin ko wane irin hukunci nasa ayi mata ya dace da ita sabida ta kasa mutunta ni." Wani irin kallo yake min tamkar yana kallon abu mai muni! koda yake ban sani ba ko shima ya hango munin nawa da mutane suke fad'arsa wannan dalilin yasa da sauri na sunkuyar da kaina kasa zuciyata tana wani irin zafi! ta k'asan idona nake kallonsa sai ya mutsa fuska yake yana kare min kallo. A dan sace na dago kaina muka had'a ido dashi! da sauri na kalli inda ya k'urawa ido a jikina.....Cikakken kirjina dake cike dana shanu naga yana satar kallon inda rigata ta yage, nasa hannuna da sauri na sake rufe gurin ina jin wani mugun haushinsa ni ban san meye a jikina ba da maza suke lalacewa gurin kallona, ni dai nasan bani da wani cikakken kyau ga shegen baqi sai kace me? ban sani ba ko nonowa na da suka rinjayi kirjina ne ke d'aukar hankalinsu ko kuma mazaunai na wanda suka cika bayana tamkar suyi magana ni kaina na san a fiska ban cika kyau ba amma na amince da cewar a jiki na cika cikakkiyar macan da kowane namiji yake bukata. Da sauri na dago kaina ina kallonsa jin kamar yana magana cikin 'bacin rai! Aikuwa fad'a sosai yakewa Gimbiya Lawisa gami da nuna mata muhimancin mutun komai lalacewar dan adam tunda Allah ya karramashi to kaima sai ka mutuntashi." Gimbiya Lawisa cikin takaici take kallonsa sam bata dauka zai goyi da bayan yarinyar ba, ranta a 'bace ta bar gurin yaranta suka bi bayanta da sauri.......A nutse yace."Kowa ya koma bakin akinsa." Minti uku gurin ya watse kowa ya nufi inda yake....Hannuwansa na goye a baya ya tsirawa kasa ido yana kallo, cikin zuciyata nace"Anya kuwa wannan guy yana da lafiya gaskiya da matsala a tare dashi duba da yanda yake nacin kallon 'kasa sai kace wani makaho. Rigata na dafe na yunk'ura da kyar na mike tsaye. nayi nufin shiga kofar dawakai naji maganarsa. "Koma ki tsuguna inaso nayi magana dake." Da sauri na tsuguna tare da sunkuyar da kaina kasa.......sai da yaja dogon lokaci sannan yace.''Me yasa bakya mutunta Lawisa ko mahaifinki nada rawani a masarauta shiyasa kike gani tamkar daidai kike da kowa." Maganar tayi min ciwo sosai amma sai na daure wa zuciyata dan saboda nasan bakin rijiya ba gurin wasan makaho bane....."Ranka ya dad'e wallahi ina mutunta ta ina gaisheta a duk sanda zamu hadu itace dai ta tsane ni ban san me yasa ba kuma ko yanzu kafin al'amarin nan ya faru sai da na gaisheta tukkuna, maganar rawani kuwa mahaifina ba kowa bane a cikin masarautar nan fyace bawa mai d'aukar d'awainiyar dawakan dake cikin masarauta, sunana Sumayya sunan mahafina Lawi." Shuru yayi yana kallonta yana tuno ranar daya dawo ranar da take cewa ba zata tsaya a rana ba ." Babu annuri yace."Okey kece ranar dana dawo kika nuna gazawarki akan tsayuwa a cikin rana ko."? sunkuyar da kaina nayi gabana na faduwa.....Ya 'bata fuska sosai yace."Ke da bakin ki kin fad'i cewar babanki bawa ne wanda nasan a cikin bauta aka haifi iyayensa, sannan aka haifeshi shi kuma ya haife ki to me zai sanya ke! kike nunawa masarauta gadara gami da rashin girmama dik wanda yake sama dake." Shuru nayi mishi dan banga rashin kyautawar da nayi ba, iyakacin bakin kokarina ina girmama duk wanda ya dace na girmama a masarautar to ban san kuma wane girma zan bata ba. Tsaki yaja yace."Tashi kije amma kada ki sake kwatanta abinda kikayi a wannan masarautar wanda keda muqami ko kuma ya gaji sarauta shine zai nuna iko akan komai amma banda ke da kike a matsayin baiwa 'kasa da sama to wane gadara da izzah zaki nunawa mutane? kinyi sau biyu kada kiyi na uku idan kika sake da kaina zan hukunta ki." Cike da mamaki nake kallonsa nace"Ranka ya dad'e a gafarce ni watakila maganar da zan fad'a ba za tayi maka dadi ba, sai nake ganin ita izzar da kake magana akanta ai ba abu ne mai kyau ba izzah! da buwaya gami da iko duk na Allah da Annabi ne, wani Sarki ko mai wani mulki dashi da muqarabbansa duk aro Allah ya basu kuma idan suka kauce hanya akan mulkin da Allah ya basu dole a lahira Ubangiji ya hukuntasu saboda haka ni banga ma'anar wannan maganar da kayi ba dan izzah! na d'aya daga cikin munanan ayyuka." Kawai naga ya tsira min ido yana kallona fuskarsa tamkar hadarin dake dab da zubar da ruwa! sunkuyar da kaina kasa nayi na dafe a kasan gurin da hannuna nace"A gafarce ni idan maganar da nayi ta 'bata maka rai." Mikewa nayi na shige kofar dawakan wanda ko ban juya ba nasan bina yake da kallo. Ya jima tsaye a gurin yana kallon kasa! mugun mamakin yarinyar yake da kalaman da tayi wato tana nuna masa ba zata bi umarninsa ba, tana nuna masa shi din jahili ne be san abinda yake ba tunda gashinan a cikin maganarta har tana kawo masa hadisai! tunda yake ba'a ta'ba katse masa hanzari ba idan yana magana sai yarinyar yana da kyau ya nuna mata muhimancinsa a cikin masarautar. Koda na gama abinda nake a ciki na fito samunsa nayi a tsaye a inda yake sai kace wani dogari yana tsaye hannu a goye a baya sai kallon kasan gurin yake yi, na girgixa kaina tare da kokarin ratse shi na wuce. Gyaran murya yay kafin yace."Tsaya nan gurin." Da sauri na tsaya nayi kasa da kaina, karasowa yay ya tsaya daf dani har ina jiyo wucin numfashinsa, gabana ya shiga faduwa fuskata na dago na kallesa, naga sai kallona yake da tamkakkiyar fuskarsa, tsoro ne ya shiga jikina nace"Dan Allah kayi hakuri ranka ya dade wallahi ban fada maka magana ba dan na bata maka rai nayi nufin tunasar da kai ne akan abinda ka manta. Cikin fushi yace."Kina nufin ni jahili ne kome."? Na girgixa kaina da sauri nace"A'a ba haka nake nufi ba." numfashi ya fesar mai zafin gaske yace."Kada na sake fad'in wata magana ki kawo min hadisai gami da fad'ar Allah yace annabi yace na fiki sanin munin abinda kike magana akai ni inayi miki magana ne akan girmama na sama dake a matsayin ki na baiwar dake karkashin masarauta yasa nace miki lallai ki girmama wanda yake saman ki amma tunda taurin kai zakiyi akan umarnina duk ranar da Lawisa ta sake daukar hukunci akanki zan bari tunda haka kike so. A sanyaye nace"Yanzu na fahimci maganarka insha Allah zan kiyaye zan kuma cigaba da girmama wanda ke sama dani. Ba tare da yace komai ba ya janye daga kusa dani ya koma gefe guda ya cigaba da kallona. ajiyar zuciya na sauke gabana na fad'uwa na kallesa, naga sai kallona yake ikon Allah mutumin wai kallon k'urrular me yake min ni ba kwalliya nayi ba ba komai ba amma ya dame ni da kallo......yagaggen wuyan rigana na riqe da sauri na bar gurin tafiyata na hard'ewa nasan idanunsa ne ya janyo min hakan. Har sai data 'bace daga gurin sannan ya dauke idanunsa daga hanyar da tabi, yarinyar bata da wani cikakken kyau a fuska amma kuma Allah yayi mata kyawun sura tamkar ita tayi kanta, dugowa mai garin jiki gami da cikakken kirji da fad'in qugu wuyanta a cike dam!dam da wani irin guru-guru ba'kar fatarta lafiyayya lukwi lukwi sai she'ki takeyi abin sha'awa, shi kam tunda yake ganin ba'ka'ken fata bai ta'ba cin karo da fatar data burgeshi ba irin nata.....mirmushi yay gami da shafa siririn sajensa, hakika yarinyar da a waje take to babu abinda zai hanashi romancing da ita dan yayi masifar sha'awarta matsalar kawai yarinyar bata kai matsayin da zai had'a jiki da ita ba, makaskanciyar baiwa ce wacce take ci da sha a k'ar'kashinsa, daba dan haka ba da duk yanda zaiyi sai ya yaudareta ya mori albarkatun jikinta......Fitowa yayi daga gurin cikin sanyin jiki gami da rashin kuzari yake tafiya, kai tsaye sashen mahaifiyarsa ya nufa yana tafiya jama'ar dake shige da fice a gurin na gaishe shi Haruna ne yake take masa baya har ya isa kofar sashen mahaifiyarsa Haruna ya bude masa kofar falon, yayi saurin matsawa gefe shi kuma a nutse ya shiga falon da sallama a bakinsa..... *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 8:19 AM - ???: *'KWARYA TABI 'KWARYA* *NA* _BINTA UMAR ABBALE🍒_ *bintaumarabbale@gmail.com* *MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION📘🖊?* _'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_ _________________________ *Littafin na kudi ne....!* _#300.....0542382124...Binta Umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai ki same ni ta wannan numbers..08089965176 _07084653262 Zanyi miki bayanin yanda zaki turo katin.......... Ga masu bukatar VIP Group 600 ne_ _Mutanan Nijar zaku tura dala dari ta wannan numbers katin airtal ko orange VIP jakka d'aya 90899076_88137740_ *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 19&20 "Haruna wa'innan fa."? ya fad'a yana nuna mu da bakinsa.Haruna ya sunkuyar da kansa kasa cikin taushin murya yace." Ranka ya dad'e Mama Fulani itace tace nazo dasu domin su gabatar maka da kansu a a matsayinsu na wa'inda zasu taimaka min da d'awainiyarka." Kansa ya sunkuyar 'kasa yana nazari kafin ya dago yana yi min wani irin kallo babu walwala a tare dashi yace."Mutum biyu nace kuma banda mace a ciki nafi bukatar maza sabida haka ke kina iya tafiya.'' Yana kallona ya 'kare maganar. Dad'i naji ya rufeni jin abinda yace yasa da sauri na k'askantar da kaina da fadin"Godiya nake ranka ya dade.'' na yun'kura na mike tsaye risinawa nayi da fadin"A tashi lafiya." Da sauri nayi nufin barin gurin naji yace."Dakata." Nayi saurin juyowa ina kallonsa addua nakeyi a zuciyata kada yace ya fasa. Gani nayi ya sunkuyar da kansa raina ya 'baci! nida su Haruna kasa'ke mukayi muna jiran muji abinda zece.........B'angaransa kuwa tunani yay kan cewar zamanta a sashen nasa zai iya taimaka masa ta wani bangaran shine dalilin daya sa ya dakatar da ita daga tafiya. Kallona yayi a ya mutse yace."Meye sunanki ma."? Babu walwala a tare dani nace"Sunana Sumayya Lawi." Ya shiga girgiza kansa minti biyu ya kalli Haruna da fad'in " ka shiga dasu ciki ka nuna musu abinda ya dace akwai d'akuna a falo kuyi amfani da d'aya kai da 'yan uwanka ita kuma sai ta dauki daya inaso ku dawo sashena da zama har abadah kune hadimai na koda nayi aure." Gabana ya dinga bugawa ina kallonsa kwalla na taruwa a idona nace"Ranka ya dad'e inada magana." Ya kalleni yana ya mutsa fuska. Saurin sunkuyar da kaina kasa nayi bakina na rawa nace"Ranka ya dade naji kana maganar mu dawo sashenka har abada ni ina da mara lafiya mahaifina bashi da lafiya kuma ni nake jinyarsa." Kaina a kasa nake maganar ina kokarin mayar da hawayen dake kokarin zubowa.....shuru gurin yayi na kusan minti biyar kafin ya dago kansa ya kalli su Haruna da fad'in"Ku tashi kuje." Da sauri suka mike suna mika godiyarsu a gurinsa Bayan barin su Haruna daga gurin na kai minti goma a tsaye be kula ni ba, sai duba wayarsa yake yi fuskarsa a murtuke. gabadaya naji gwiwowina sun sage na kalleshi inaso nayi magana ido muka hada dashi gwarjinsa ya hana ni cewa komai. "Kina nufin kina tsaye 'kerere a kaina zanyi magana dake."? Ciki ciki ya fadi maganar, zubewa nayi gwiwa a kasa nace" Ranka ya dade a gafarce ni wallahi hankalina ne gabad'aya yana kan mahaifina." Ajiyar zuciya yayi ya mike zaune had'e dayin wani irin zama na saurata hannunsa ya d'ora kan gwiwarsa, na kalli hannun yatsunsa guda uku na sanye da zubonan azirfa masu kyau sake sunkuyar da kaina nayi ina jiran jin ta bakinsa. kallona yayi a ya mutse yace."Mai yake damun mahaifin naki."? Da sauri nace" Daya daga cikin masu duba lafiya ya tabbatar mana da cewar hawan jini ke damunsa tsayin wata daya yana fama amma dai yanzu da sauki tunda an d'orashi akan magani. Shuru gurin yay bayan na gama maganata, ya dinga kallon 'kasan kafet din da yake zaune kamar ba zaice komai ba daga bisani ya d'ago kansa tare da fad'in "Inaso kiyi min jagora 'bangaran naku domin na duba mahaifin naki." Kallonsa nayi ina mamakin maganarsa, girarsa dake cike da gashi ya d'aga min domin so ya tabbarar min da maganarsa. Nace"Babu damuwa ranka ya dad'e idan ka shirya zuwa yanzu sai nayi maka jagora." Ina d'urkushe a gabansa ya mi'ke a nutse yasa takalminsa yace."Tashi muje." Da sauri na mike ina karkad'e jikina. Tsayawa nayi ina jira yayi gaba nabi bayansa ya nuna min hanya da hannunsa ba tare da yace komai ba na fahimci abinda yake nufi da sauri nayi gaba ya rufa min baya. Yanayin tafiya ta da tashi ba daya bane koda na waiwaya sai naga nayi masa nisa sosai d'an tsayawa nayi ina jiran zuwanshi.....Bangaran shi kuwa tafiya kawai yake amma hankalinsa tuntuni ya tashi sakamakon yanayin tafiyar da takeyi sassan jikinta na motsawa mazaunanta ba 'karamin tayar masa da hankali yayi ba hakan ya sake sanya masa rashin kuzari da karfin jiki ya dinga tafiya tamkar wanda 'kwai ya fashewa a ciki gabad'aya sha'awarshi ta tashi yana so ya samu yarinyar da zata d'ebe masa kewa. Sai da ya kusa zuwa dab dani sannan na juya na cigaba da tafiya.....Yarima Ali ajiyar zuciya ya sauke ya tsirawa faffad'an qugunta ido wanda yake juyawa cikin zanin kamfalar dake jikinta........ajiyar zuciya ya dinga saukewa yana kokarin danne abinda ke taso masa. Koda muka shiga gurin namu Tambaya dake bakin rijiya tana wanke kwanuka mikewa tayi da sauri ganina tare dashi yasa hankalinta ya tashi tana tsoro ko wani abu ne ya faru, ganin ta razana yasa nace"Ki kwantar da hankalinki babu abinda ya faru Yarima zai duba jikin babana ne." Zubewa tayi gabansa tana gaisheshi gami dayi masa godiya. Cikin sanyin murya ya amsa tare da bata umarnin mi'kewa. Na kalleshi a nutse nace"Ranka ya dade bisimillah ka shigo." Takalmansa ya cire a nutse ya rankwafa domin shiga dakin dake gajeriyar kofa ce shi kuma ya kasance mutum mai tsayi shine dalilin da yasa ya risina domun shiga dakin. Guri na shiga karkad'ewa wai ko zai zauna, sai naga yaja ya tsaya yana kallon babana dake kwance yana bacci.....Cikin rawar baki nace"Ka ganshi ko wallahi yana jin ji......! hannu ya daga min alamanun baya bukatar maganata, nayi shuru ina kallonsa sai kallon babana yake kafin ya kalleni yace"Ina maganin da kuke bashi."? Da sauri na dauko na mika masa, ya jima yana duba magungunan kafin ya miko min da fadin"Kada ku sake bashi maganin ku ajeshi zamuje yanzu nasa Haruna ya samo masa wasu insha Allah zasuyi masa." Da sauri nace"To mungode shima na hausan da muke bashi mu daina."? Kallona yayi da sauri yace."Bayan wannan maganin akwai wanda kuke bashi."? nace."Eh akwai na hausa wanda na kar'bo gurin masu maganin gargajiya." Tsaki! yaja da fad'in"Jeki dauko min maganin nagani." Na mike da sauri na fita tsakar gida na samu Tambaya ta gama wanke kwanuka tana tsaye jikin bango (garu)ta rungume hannuwanta a kirji. "Tambaya ina maganin da ki'ka jiqawa babana." Da sauri ta shiga wani daki dake tsakar gidan ta dauko maganin cikin bokitin roba madaidaici karba nayi da sauri na shiga dakin, na mika masa . "Ajiye ki bud'e nagani." Ajiyewa nayi a kasan guri nayi yanda yace. Ni dashi gabad'aya tsirawa maganin ido mukayi ganin yanda yake wata irin kumfa ga wari na tashi a cikinsa. Dauke kansa yay rai a b'ace yace."Rufe." Jiki a sanyaye na rufe ina kallonsa, Yace."Wannan maganin kwanansa nawa a jiqe."? a sanyaye nace"Zai kai sati biyu." Cike da taikaci yace." Waye ya fad'a miki ana had'a maganin hausa dana bature a tare? shuru nayi kaina a kasa.....Ya cigaba da cewa"Magani kun jiqa shi tsayin sati biyu yana kumfa wari na tashi a cikinsa amma kuna d'irka masa so kuke ku kasheshi."? Nayi saurin kallonsa ina girgiza kaina. Yace."To ko dan gaba ba'a hada maganin hausa dana bature a tare sannan kuma idan kun jiqa maganin hausa to kuyi amfani dashi a lokacin idan ya kwana daya biyu ku zubar dashi domin ya tashi a aiki amma magani tsayin sati biyu a jiqe kuna bashi dole ku kasa gane kansa. Nace"Kayi hakuri zamu gyara insha Allah.'' Shiru yayi ya sunkuyar kansa 'kasa, na dinga satar kallonsa ina mamakin wannan d'abia tashi bini bini kallon 'kasa sai kace makaho........"Anjima bayan isha'i ki shigo ki kar'bar masa wasu maganin insha Allahu zai samu lafiya." Murya na rawa nace"To mungode ranka ya dade." Ba tare da yace wani abuba ya rankwafa da niyyar fita daga dakin........Bayansa nabi naga suna sallama da tambaya, har soro na rakashi ina godiya uffan bece min ba har ya fita daga zauran namu.....na koma cikin gidan da sauri na shiga yiwa Tambaya bayani da yayi akan maganin gargajiyar da muka jiqa. *BINTA UMAR ABBALE* Kuyi sharing👏🏻 2/11/21, 8:19 AM - ???: *'KWARYA TABI 'KWARYA* *NA* _BINTA UMAR ABBALE🍒_ *bintaumarabbale@gmail.com* *MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION📘🖊?* _'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_ _________________________ *Littafin na kudi ne....!* _#300.....0542382124...Binta Umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai ki same ni ta wannan numbers..08089965176 _07084653262 Zanyi miki bayanin yanda zaki turo katin.......... Ga masu bukatar VIP Group 600 ne_ _Mutanan Nijar zaku tura dala dari ta wannan numbers katin airtal ko orange VIP jakka d'aya 90899076_88137740_ *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 21&22 Sai bayan dana idar da sallar isha'i tukkuna na shedawa Tambaya maganar komawa ta 'bangaransa da aiki. shuru tayi tana nazarin al'amarin tace"Sumayya dole ne mubi umarnin masarauta bamu da za'bi sai abinda suka ce damu saboda haka na umarce ki kije ki kula da Yarima bisa amana ki kyautata masa kamar yanda zaki kyautatawa iyayenki." Nace"Tambaya babu wanda nake ji sai babana ki duba kiga halin da yake ciki gashi kema bakya zama sosai kullum kuna gurin girkin abinci bana so a barshi shi kadai a gidan shiyasa wallahi tunda naji maganar hankalina ya tashi." "Sumayya duk abinda Allah yayi nufun zartarwa akan mahaifinki to ko muna nan ko bama nan bamu isa mu hana Allah ikonsa ba, saboda haka ki nutsu ki kwantar da hankalin ki cuta ba mutuwa bace insha Allah Allah zai tashi kafad'unsa." Shuru nayi ina sa'ke-sa'ke a cikin raina. Tace"Tunda kinyi sallah sai kici abinci ki tafi kada ki 'bata lokaci a samu matsala. A sanyaye naje na 'Dauko kula ta abincin na had'o da plate na zauna inda na tashi abincin na zuba a plate nayi bisimillah a nutse na fara ci, Tambaya miqewa tayi ta nufi inda mijinta yake kwance, a hankali ta shiga kiran sunansa, bude idonsa yayi ya kalleta a hankali ya mayar da idon ya rufe, tace"Malam kaji maganar da muke tattaunawa ko.'' ? idanunsa ya bude ya kalli gefan da nake zaune ina cin abinci. A sar'ke yace"Sumayya kibi umarnin masarauta ko bayan babu raina bance ki bijirewa masarauta ba domin baki da wani tushe sai ita iyayenmu da kakannimu duk a k'arkashin masarauta suka rayu a haka duk aka haife mu saboda haka nake umartar ki da cewar kiyi biyayya kamar yanda kika ga munayi a matsayin mu na iyayenki." Muryata na rawa nace"Baba dan Allah ka daina maganar mutuwa insha Allahu zaka tashi ka cigaba da sabgogin ka cuta ba mutuwa bace." Murmushi yay yace."Sumayya kenan to ina rokon ubangiji Allah ya tashi kafad'una na cigaba da rayuwa a tare daku.'" murya na rawa nace"ameen baba Allah ya baka lafiya." amsawa sukayi da "ameen" na mike na fita domin wanke hannuna. Lokacin dana shiga dakin Tambaya na kokarin mikar dashi zaune domin ta d'aura masa alwala taimaka mata nayi mukayi masa alwalar ta gyara shi sosai yanda zaiji dadin sallah ya tayar da iqama a nutse! kallona tayi tace"Kiyi maza ka tafi mana." Sai Naji zuciyata ta karye tunda na taso ban ta'ba zuwa ko'ina na kwana ba kullum ina tare da iyayena A sanyaye na juya ina goge hawaye da hannuna nace"Na tafi." Itama tambayan cikin alhini tace"Sai da safe." Jin kuka naso ya kufce min yasa nayi gaggawar fita daga dakin, takalmana dake bakin kofar dakin na zura na fita daga gidan. Haruna da su Isa na samu a falon suna aikace aikace, gaisawa mukayi na nemi kan kujera na zauna ina rarraba idona a katafaran falon nashi daya gaji da had'uwa, ko wace kusurwa hotonshi ne a manne wani da manyan kaya na sarauta wani kuma da 'kananun kaya cikin hotonan nasa babu wanda yayi dariya a ciki fuska a murtuke tamkar wanda akayiwa dole gurin daukar hoton, muryar Haruna ce ta katse min tunanin da nake, na kalleshi inaso ya sake maimaita min abinda yake fad'a, Yace."Sumayya ba zama zakiyi ba zaki hau sama ne ki bubbuga idan ya bude sai ki sheda masa isowarki idan da akwai abinda yake bukata kiyi masa sai kiyi mu dai mun gama aikin mu zamuje mu huta sai ya b'ukace mu.'' Na kalleshi da fadin"Ina ne d'akin nasa." Wata matattakalar bene ya nuna min da fadin''Kina kaiwa karshen benan za kiga wata kofa mai biyu nan ne d'akinsa sai ki danna wani abu a jikin kofar zai yi magana. Nayi shuru ina sa'ke-sa'ke mi'kewa nayi na kama hanyar benan, da k'yar nake hawa benan sabida santsin ties d'in ina hawa ina ri'ke sandar benan gabana na fad'uwa! ajiyar zuciya na ajiye bayan na gani a kofar dakin Sai da na daidaita nutsuwa ta tukkuna na danna abinda zai isar masa da isowata. shuru ba'ayi magana ba, nasa hannu akan abun na latsa da kar'fi! Naji muryarsa yana fad'in "Wanene." "Nice Sumayya.'' Murya a hard'e na fadi maganar. shuru har tsayin mintina goma bai bude ba jikina yayi sanyi kamar nayi tafiya ta sai dai na daure na cigaba da tsayuwa, motsin bude kofar naji nayi saurin ja gefe tare dayin kasa da kaina, koda ya bude kofar ban kalleshi ba nace" Barka da dare ranka ya dade." "Barka dai shigo ciki." Yafada tare da juyawa cikin dakin. Dago kaina nayi da sauri na mayar dashi qasa sakamakon ganinsa da nayi d'aure da towel gabana ya dinga bugawa kasa shiga dakin nai nayi tsaye a bakin kofar ina tararrabi." Zama yay gefan bed dinshi yana kallon bakin kofar, "Ke! ki shigo nace dake."! A tsawace ya fad'i maganar, shahada nayi na shiga yace." Kulle kofar." hannu nasa na tura kofar dakin ta rufe, tsayuwa nayi jikin kofar kaina a qasa nace"Ranka ya dade gani nazo." Shareni yayi ya cigaba da murza vasilin a jikinsa, duk da kaina a qasa yake sai da naga cinyoyinsa d'an towel din ya dinga turewa daga jikinsa yana shafa vasilin din, ganin kamar yana so yayi tsirara yasa na juya masa baya. "Ke! dodo ne ni da zaki juya min ba okey zan saki yanzu ki shafa min vasillin din tunda abin hakane." Ji nayi yawun bakina ya bushe, nace"Dan Allah kasa kayanka baligin mutum kamar ka bai kamata ana ganin tsaraicinsa ba. "Wa'azi za kiyi min kome."? Shuru nayi masa, yace." Malama Zo nan ki shafa min vasilin din a bayana." Kasa juyawa nayi ballantana naje nabi umarninsa. "Ko bakya ji ne." Hanci na shaqa kunyar duniya ta isheni nace"Dan Allah kayi hakuri ba zan iya ba." Tsaki naji yaja daga hakan be sake cewa komai ba ya cigaba da shafa mai a jikinsa. "To na gama sai ki juyo.'' A hankali na juya kaina a 'kasa ban yarda na kalleshi ba, yace" Zo ki kar'bi maganin nasa Haruna yaje gurin seda magani ya siyo zo in nuna miki yanda zaku dinga bashi. Zuwa nayi na durkusa gabansa a nutse ya fito da magungunan daga ciki leda ya shiga nuna min yanda qa'idarsu take, muryata na rawa nace"Allah ya saka da alkairi mungode." Yace."Ki koma yanzu ki bashi maganin kamar yanda nace amma ki tabbatar kafin ki bashi yaci abinci ya koshi." Ina kokarin miqewa tsaye nace"Insha Allahu yanda kace haka za'ayi." da ledar maganin a hannuna na kama hanyar fita daga dakin. Ka shingid'a yayi tare da bin bayanta da shu'umin kallo, sajensa ya shafa yana lumshe idonsa gabad'aya yarinyar ta rikitashi duk wani abu da yake daurewa yake yi amma yana bukatar wacce zata d'ebe masa kewa. Sai da na tabbatar da yaci ya k'oshi tukkuna na bashi maganin kamar yanda ya umarce ni, mahaifiyata na kalla dake kokarin gyara masa shimfida nace"koda da safe ban shigo da wuri ba ai kinga yanda na bashi maganin ko."? Tace"Eh na gani insha Allahu zan kwatanta." Miqewa nayi na sakeyi mata sallama a karo na biyu, tace"To Allah ya tashemu lafiya." da ''ameen na amsa cikin sauri na fita daga dakin. Yana kishingid'e kasan kafet din dake 'kasan bed dinshi na same shi da romot a hannunsa yana kallon wa'ko'kin turawan america, kauda kaina nayi daga kan tv dan ganin yanda turawa ke bad'ala sai rungume rungume suke suna tsotsar bakin junansu. A sar'ke nace"Ranka ya dade na dawo na bashi maganin kamar yanda kace idan da akwai abinda kake bukata kayi magana sai nayi maka." Uffan bece min ba hankalinsa na kan tv yana kallon raye rayen turawa. Na sunkuyar da kaina k'asa, hakika raina yana 'baci idan yana min wannan wulakacin a rayuwata na tsani nayi magana a watsar dani. Sai da ya mula tukkuna ya kalleni tare da fad'in "Ina bukatar kiyi min matsar jiki kwana biyu sabida rashin motsa jikina da banyi ba yana min ciwo insha Allah gobe zan fita da doki cikin gari na wasa jinina." Duk da na fahimci abinda yake nufi sai nace"Ban gane abinda kake nufi ba." Gyara zamansa yayi yana fuskantata yace"Ina bukatar tausa shine abinda nake nufi." Jarumta na aro nace"Amma ina ganin kamar hakan be dace ba idan tausa kake bukata maza 'yan uwanka su yafi cancanta suyi maka bani ba da nake a matsayin mace ba." Gani nayi ya sha kunu! kaina na sunkuyar gabana na faduwa..."Kina a matsayin mace sai akayi yaya."? shuru nayi bance komai ba, ya cigaba da cewa''Na fahimci kina da taurin kai babu abinda za'a umarce ki dashi kiyi kai tsaye sai kinyi musu, kada ki manta fa kina karkashin masarauta duk abinda aka umarce ki dashi naki to ne." Hanci na shaqa na sake risinar da kaina qasa nace"A gafarce ni ranka ya dad'e ba wai ina jayayya da umarninka bane A'a inaso na nuna maka illar abinda kake so na aikata bai kamata na ra'bi jikinka ba a matsayinka na baligi nima haka." D'akin ne yayi shuru bayan gama maganata, dago kaina nayi na kalleshi naga ya tsirawa tv ido fuskar nan kamar wanda aka aikowa da sak'on mutuwa. Tv din na d'an kalla a sace naga abinda ake aikatawa ya zarce tunani na, mace da namiji ne tsirara sun dage suna sex sai nishi sukeyi......gabana ya dinga bugawa da sauri na miqe na kama hanya zan fita. "Kada ki kuskura ki fita a d'akin nan." Ja nayi na tsaya ba tare dana juyowa ba gabana na faduwa still ina jiyo nishin 'yan iskan." *BINTA UMAR ABBALE* Shearing👏🏻👏🏻 Dan Allah idan ba siyan book din nan zakiyi ba kada ki kira waya ta, masu flashing kuyi wa Allah da Annabi ku bari bana jin dadin abinda kukeyi🤨 2/11/21, 8:19 AM - ???: *'KWARYA TABI 'KWARYA* *NA* _BINTA UMAR ABBALE🍒_ *bintaumarabbale@gmail.com* *MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION📘🖊?* _'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_ _________________________ *Littafin na kudi ne....!* _#300.....0542382124...Binta Umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai ki same ni ta wannan numbers..08089965176 _07084653262 Zanyi miki bayanin yanda zaki turo katin.......... Ga masu bukatar VIP Group 600 ne_ _Mutanan Nijar zaku tura dala dari ta wannan numbers katin airtal ko orange VIP jakka d'aya 90899076_88137740_ [12/29, 12:33 PM] 💜: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 23&24 "Ki dawo kiyi aikin dana saki." Maganarsa ce ta doki dodon kunnena, juyowa nayi fuskata a had'e nace"Allah ya kiyashe ni aikata haramci Ranka ya dade bana jin zan iya bin umarnin ka tunda ya sa'bawa addinin musulunci." Ina gama maganata na kama handle domin bude kofa na fita muryar mahaifina naji a kunnena lokacin da yake min gargadin akan bin umarnin masarauta, hawaye ne ya ciko a idona ina jin tsoro kada garin bin umarni wani mummunan abu ya faru a tsakani na dashi tunda Annabi S.a.w yace." Duk inda mace da namiji suka had'u to na ukun su shed'an ne babban tashin hankalin kuma shine ya kunna iskanci a d'akin shiyasa gabad'aya na kasa samun nustuwa.......Saukar hannunsa naji akan nawa dake jin kofar dakin, na dinga jin hucin numfashinsa na sauka a daidai wuyana, cikin faduwar gaba na juyo sai na ganshi dab dani saura kadan kirjinsa ya gogi nawa, saurin jingina nayi a jikin bango(garu) numfashina na fita da sauri da sauri, sunkuyar da kaina kasa nayi bakina na rawa magana nake so nayi amma tsabar fargaba da tashin hankali ya hanani cewa komai. "Ba zakiyi min ba ko." cikin wata 'yar iskar murya ya fadi maganar, cike da jarumta na kalleshi nace"Kaji tsoron Allah a duk inda kake nasan kasan kallon tsaraici haramun ne yanzu dan Allah meye amfanin kallon blue film da kake yi kuma menene na cewa lallai sai nayi maka tausa idan baka da wata manufa akaina." Shuru yayi bece min komai ba kuma be daina kallona ba, hannunsa dake dogare a jikin kofar na ture ina kokarin fita daga tsakaninsa ya mayar dani jikin bangon ya matse da kirjinsa, kafin nayi aune naji saukar hannunsa akan mazaunai na yana shafa su, karfi ne yazo min da wani tunkude shi ina haki! na nuna shi da hannu da fad'in "Kada ka sake yunkurin kai hannunka jikina ni ba 'yar iska bace irin wanda ka saba nema a turai, yanzu na gane munufar ka a kaina dama badan nayi maka aiki ka bukaci zamana a sashenka ba na gane sabida ka cimma wata munufa ne to ta Allah zai kare ni daga sharrin ka." Cikin tsanani 'bacin rai na kare maganar a fusace na bude kofa zan fita ya finciko ni kafin nayi wani yunkuri naji saukar mari a kumatuna, ido na tsirawa masa ina kallonsa yana huci yace."Ni kike kira d'an iska."? Muryata na rawa nace"Ni ban ce maka dan iska ba amma nace kaji tsoron Allah akan abinda kake aikatawa wanda kasan haramun ne." Wani kallon banza yayi min da fadin "Saboda kin samu nayi sha'awarki shine kika samu damar fad'a min dukkanin maganar da kike so ko an fada miki ni sa'anki ne da zaki tsaya a gabana kina kokarin zagina."' Risinar da kaina qasa nayi nace" Allah ya baka hakuri idan akwai maganar data bata maka rai a cikin maganganuna to ina neman afuwa." Da hannu ya nuna min kofa cikin tsawa yace."Fice min a daki banza mummuna kawai." Da sauri na bude 'kofar dakin na fita gabana sai dukan uku uku yake.......Tamkar wani zautacce ya juya jikinsa na kyarma bed ya kwanta ruf da ciki yana murk'ususu mararsa ta cika tayi fam sai ciwo take masa. Dakin da Haruna ya nuna min na shiga na rufo kofa na samu gefan gado na zauna har yanzu ban dawo nutsuwata ba, sosai nake mamakin al'amarin, a haka idan ka kalleshi zaka dauka mutumin kirki ne sabida a zahiri yana da fuskar salihai ashe ba anan take ba shi d'in mugun shaid'ani ne mane min mata wato yana da manufa a kanta shiyasa ya bukaci zamanta a gurinsa, to kuwa idan hakane dole tayi takatsantsan dashi da dabi'unsa. Da kyar bacci ya d'auketa saboda tsabar damuwa da tashin hankali. B'angaransa kuwa yanda yaga rana haka yaga dare ya dinga matagugu yana riqe ciki sai gefin asubahi ya samu sassauci abinda ke damunsa cikin tsanani damuwa yayi wanka da alwala ya shirya shiga massalaci haka ya sakko tamkar wanda yayi shekara akwance tare suka tafi masjid din dasu Haruna domun gabatar da sallar asubahi. Bayan na idar da sallah na jima hannuna a sama ina rokon Allah ya kareni daga sharrinsa na shafa adduar na mike a nutse na fita falon na jima a tsaye ina sak'e sa'ke kafin na nufi kofar kicin domin shirya abin kari...........Tsaf na shirya kayan karin kummalo na fito dasu ina jerawa kan daning....Shine a gaba su Haruna na bayanshi, 'kasa nayi da kaina tare da risinawa nace" Ranka ya dade Barka da asubah." Banza yayi mun ya wuce benansa, a sanyaye na dago kaina muka hada ido da Haruna ya'ke nayi nace"Haruna kun tashi lafiya."? Yace."Lafiya lau Sumayya ina fata kema kin tashi lafiya."? na amsa da lafiya lau alhmdullhi." Har zai bar gurin sai kuma ya tsaya yace."Sumayya baki karanci damuwa a fuskar Yarima ba."? Girgiza kaina nayi ba tare da na kalleshi ba nace"Banga komai ba ai ka san shi ba'a gane farin cikin sa da 'bacin ransa tunda kullum fuskarsa a murtuke take da rashin fara'a." Yace."Hakane to amma yana da kyau mu had'u gabadayanmu muje mu sameshi mu tambayeshi ko munyi masa laifi sai mu bashi hakuri." Shuru nayi ba tare da nace komai ba na cigaba da ayyukana. Yace."Kinyi shuru bakice komai ba." Nace"To hakan yayi muje." Haruna ya kalli Isa da Hamza yace."Shawarata tayi ko." ? duk sukace tayi muje mu sameshi mu tambayeshi ko munyi masa laifi sai mu bashi hakuri. Jirana sukayi na gama gyara daning sannan muka hau saman nashi. Yana kwance cikin bargo yace."Kowaye ya turo kofar, a bude take." Haruna ya bude kofar dakin muka shiga gabad'ayan mu kanmu a kasa muka ajiye gwiwowin mu a kasa gaishe shi muka farayi kafin mu fara neman afuwarsa duk da bamu san laifin da mukayi ba. Shuru dakin yayi bayan mun gama magana uffan bece mana ba yana kwance cikin bargo fuskarsa na kallon rufin dakin. Haruna yace"Ranka ya dade a gafarce mu."! Gyaran mirya yayi ya juyo yana fuskantar mu, sunkuyar da kaina kasa nayi ganin fuskarsa a hade gashi kwayoyin idanunsa sun sakeyin jawur! "Babu wani abu da kukayi bana jin dadi ne shiyasa kuka ganni haka da rashin kuzari." Haruna dasu Isa suka shiga damuwa dajin furucinsa ni kuwa ko gezau banyi ba tunda nasan karya yake kawai ya fadi hakane domin kare kansa, sannu suke masa tamkar bakinsu yayi tsayi, nima sai nabi ayarinsu na dinga yi masa hannu ina rokon Allah ya bashi lafiya. Gyaran murya yay a karo na biyu yace."Kuna iya tafiya." Haruna yace."Ranka ya dade sai zuwa anjima za kayi wanka ko kuma yanzu na hada maka ruwan wankan." ? girgiza kansa yay yace."Bari anjima ka shigo ka had'a min inaso nayi bacci yanzu." Yace."To godiya nake ranka ya dade a tashi lafiya." Mik'ewa sukayi da niyyar fita, nayi kasa da idanuna ba tare da na kalleshi ba nace"Ranka ya dad'e yana qarko na shirya danning ina nufin gurin cin abinci komai ya kammala idan baka bukatar zama a daning din sai kayi magana na kawo maka nan." Shuru yayi min, jikina ya bani kallona yake, aikuwa ina dago kai muka had'a ido, a maimakon ya ji kunya na kamashi yana kallona sai ma ya sake k'ureni da jajayen idanunsa dake bani tsoro. Yun'kurawa nayi zan tashi naji maganarsa a dashe "Ki kawo min nan." na risina da fadin"angama ranka ya dade." da sauri na juya domun fita daga dakin......kallo ya bita dashi yana jin yanda gabansa ke miqewa hannu yasa ya danne jijiyar tashi yana jan tsaki a fili yace."Sabida rashin adalci ki rasa a inda zaki nuna kwad'ayin ki sai a inda be dace ba mtwww! tsaki yaja mai k'arfi yana danneta ita kuma sai miqewa take. Ina sauka qasa na samu 'Yan uwanshi Shatima da Maddibo har'kasa na durkusa na gaishe su, suka amsa min a sake mussaman Shatima sai murmushi yake min, wuce su nayi da sauri na nufi kicin na dauko wani tire na silver mai fad'i dainng din na nufa na shirya kayan break fast din akai na dauka a nutse na nufi saman da tire din a hannuna Abin mamaki! samunsa nayi a zaune shida 'yan uwan nashi suna hira, a nutse na ajiye tire din a gabanshi, kai a sunkuye nace"Dan Allah ina neman alfarama." "Wace irin alfarma." yafada ba tare da ya kalleta ni ba." naji dadi sosai da bai shareni ba nace"Zanje in duba dawakai kasancewar aikin babana kenan to tunda ya kwanta rashin lafiya na dawo da dawaniyyar hannuna bayan nan inaso zan zauna a gurin karatu." Jim yayi na minti biyu yace."Kije." cikin jin dadi nace"Nagode ranka ya dade." yunkurawa nayi na mike tsaye da fadin"A tashi lafiya." babu wanda ya amsa min a cikinsu. da sauri na kama hanyar fita daga dakin. Shatima ya kalli Moddibo da fad'in "Wannan yarinyar tana da dirin jiki mai kyau amma kuma bata da wani kyau gata 'baka." Moddibo dariya yay yace."Kai ina ruwanka da muninta idan biyan bukata nake nema ni bana duba muni ina duba abinda zai gamsar dani." Dariya sukayi tare da tafawa a tsakaninsu, Haushin abinda suke yasa ya mike ya nufi toilet yana jin wani irin d'aci! a cikin ranshi, ashe dai bashi kadai ke ganin kyawun jikin yarinyar ba, har da sauran mutane yaji takaicin yanda Shatima ke kwarzanta kyawun dirin jikinta, brush yay ya fito da fuska a had'e. kan kafet din ya zauna gami da tankwashe kafafunsa, a nutse ya tsiyaya bak'in tea a cup ya shiga kur'ba a hankali a hankali yana sauraran hirarrakin dasu Shatima keyi mafi akasari hiran ta 'yan mata ne, cup din tea ya ajiye a nutse ya bude wata silver farfesun zallan naman rago da dankali ne a ciki yayi kyau sosai sai 'kamshi yake Yaji yana sha'awar shan farfesun ya hada da bread a nutse ya zuba a plate ya kallesu da fadin"Bisimillah." Moddibo ya girgiza kanshi da fad'in" Ni dai Alhamdullhi ban san Shatima ba." Shatima dake duba wayarsa yace."Nima a koshe nake wallahi." Ba tare da yace komai ba ya fara shan farfesun yana had'ashi da bread....Modibbo ajiyar zuciya ya sauke ganin yana shan farfesun wani farin ciki ya cika masa zuciyarsa, dauke kansa yay suka cigaba da magana da Shatima. Wani irin tari ne ya sarqe shi ya ajiye bread din hannunsa yana riqe kirjinsa tari yake sosai idanunsa sun cika da ruwa. Shatima ne yay saurin miqa masa ruwa ya kar'ba yana kokarin sawa a bakinsa ruwan na dawowa, sai kawai ya ajiye goran ruwan ya danne kirjinsa yana cigaba da tarin cikin galabaita ya mi'ke tsaye! sai suma suka miqe cikin tashin hankali suna rirri'keshi ya fadi a gurin, jini ne ya biyo bayan tarin da yake.......A gigice suka rufu a kansa suna k'okarin mikar dashi zaune. Fitowa ta kenan daga gurin Dawakai Haruna ya karaso inda nake hankali a tashe yace."Sumayya Yarima Ali bashi da lafiya bayan fitarki daga sashen Tari ya sarqeshi ya dinga aman jini." Kirjina na dafe cikin tashin hankali nace"Haruna wane irin aman jini kuma."? Yace."Aman jini dai da kika sani Sumayya yanzu haka sashen nasa a cike yake da 'yan uwa dan har maimartaba ma yana gurin ana bunkice akan abincin da yaci wallahi ke kadai nake tausayawa." Kallonsa na shiga yi a tsorace nace"Haruna ni kuma meye laifina da kake tausaya min." Yana kokarin magana Hamza ya karaso gurin yace."Ke! Sumayya kizo ana neman ki a sashen Yarima." Naji gabana ya fad'i! Magana nake so nayi amma bakina yayi min nauyi, dakyar na iya furta kalmar innalillahi wa'ina ilaihi raji'un." nabi bayansu domin zuwa jin kiran da ake min...... *BINTA UMAR ABBALE* *Kuyi sharing👏🏻* 2/11/21, 8:19 AM - ???: *'KWARYA TABI 'KWARYA* *NA* _BINTA UMAR ABBALE🍒_ *bintaumarabbale@gmail.com* *MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION📘🖊?* _'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_ _________________________ *Littafin na kudi ne....!* _#300.....0542382124...Binta Umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai ki same ni ta wannan numbers..08089965176 _07084653262 Zanyi miki bayanin yanda zaki turo katin.......... Ga masu bukatar VIP Group 600 ne_ _Mutanan Nijar zaku tura dala dari ta wannan numbers katin airtal ko orange VIP jakka d'aya 90899076_88137740_ *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 25&26 Cikin tararrabi gami da fargaba muka shiga falon, gimbiya Lawisa ce a zaune akan kujera muna shiga ta mike tsaye da sauri tana watsa min mugun kallo! sunkuyar da kaina qasa nayi nace"Ranki ya dade barka da safiya." Hannu ta daga min cikin tuhuma tace"Me kika zubawa Yarima acikin farfesu wanda ya janyo masa aman jini."? Gabana na faduwa nace"Ban zuba masa komai ba ranki ya dade." Marina tayi tana huci! tace"Zaki fad'a ko sai kin fuskanci hukunci mai tsauri."! Hannu na dafe da kuncina nace"Iya gaskiyata na fada wallahi ban sa masa komai ba." Za tayi magana Haruna ya katseta da fadin"Sumayya ki hau sama Maimartaba na bukatar ganinki." naji jinin jikina ya tsinke gabad'aya neman yawu nayi na rasa a bakina, salo salo na nufi saman ina adduar akan Allah ya fitar dani. Lokacin dana shiga dakin sai naji na sare da al'amarin dan ganin yanda dakin ke ciki da jama'a gabad'ayan su suna tsaye a kansa yana kwance a bed kansa a cinyar mahaifiyarsa bakinsa rufe da wani abu da ya nuna alamun an tare jini likita ne a tsaye a kansa. Sunkuyar da kaina kasa nayi na zube gwiwata a kasa nace"Barkan ku da wannan lokaci." Gabad'aya suka juyo suna kallona.......muryar Moddibo naji cikin tsawa yace."K'araso ciki munufaka." Na yun'kura da sauri na karasa gabansu na tsuguna! Moddibo zai sake magana maimartaba ya katse shi. Shuru dakin yayi kafin maimartaba ya fara magana kamar haka. "Sumayya wace irin guba kika sakawa Yarima a cikin abincinsa inaso ki fada min wanda ya saki zuba masa guba a cikin masarautar nan."! hawaye suka k'wace min nace" Na rantse da wanda raina ke hannunsa ban zuba masa komai ba, lafiya lau na gama abinci na bashi kafin na tafi gurin mu." " 'Karya kike munufuka akwai abinda kika zuba masa wato kina so ki kashe ki ko."? Moddibo ne ke wannan maganar kamar zai kai min duka Waziri ne yayi masa tsawa yayi shuru yana huci......Uwargida wato mai babban daki tace"Wato ba zaki fadi gaskiya ba kenan musu zakiyi akan binkicen da likita yayi akan farfesun da kika bashi yasha, to shikkenan tunda kina gardama ki dauki farfesun kisha mu gani." Ina kuka nace"Ranki ya dade wallahi kiyashi ban ta'ba kashewa ballantana mutum, ni kuwa me Yarima yayi min da zan kasheshi dan Allah ku duba maganata kuyi binkice sosai akan al'amarin wallahi ban sa masa guba a acikin abinci ba." Ciroma yace."Zaki rufe mana baki ko kuwa." Shuru nayi ina kallon qasan gurin nace"Ku gafarce ni na fada muku iya gaskiyata ne." Dakin shuru yayi kowa yana jira yaji ta bakin Sarki, wanda yay shuru yana nazari tabbas al'amarin na bukatar bunkice kamar yanda yarinyar ta fada. Itama Mamma tunanin da take kenan ba zai zama dole ace yarinyar ce ta zuba masa guba ba mybe akwai dai wata mak'arkashiyar shiyasa tayi shuru ba tace komai ba. Sarki gyaran murya yay yace."Sumayya kin san girman Allah da Annabin Allah." Da sauri nace"Eh ranka ya dad'e." Yace."To magana ta k'are tunda har kinyi rantsuwa da Allah da annabi baki zubawa Yarima guba ba ki tashi ki tafi." Da sauri na kaskantar da kaina kasa nace"Godiya nake ranka ya dad'e. Yunk'urawa nayi na miqe da fadi "Na barku lafiya." Babu wanda ya tanka min har na fita daga dakin. Maimartaba ya kallesu a nutse yace."Ina ganin zamu tsananta binkice akan wannan al'amarin dan alamu sun nuna cewa yarinyar nan bata da alhaki akan wannan al'amarin saboda haka zamu bar maganar tunda Allah ya kiyaye gubar ba tayi tasiri a tare dashi ba ammafa hakan ba zai sa mu kasa d'aukar mataki akan duk wanda muka samu da alhakin faruwan wannan al'amarin ba." Waziri yace."Hakane ranka ya dad'e tabbas yanayin yarinyar ya nuna gaskiyarta sai a 'kara saka matakan tsaro a sashen nasa saboda gujewa faruwar wani abu makamancin wannan." Galadima da Ciroma shuru sukayi dan al'amarin gabad'aya bai musu dad'i ba sun so ace gubar ta kashe yaron kowa ya huta....... . Ko kallonta banyi ba na nufi kofa da niyyar fita daga dakin. cikin tsawa tace"Ke! mai baqi kamar bakin tukunya tsaya anan gurin." kamar kada na tsaya sai dai na yanke shawarar tsayawa amma ban juyo ba. Kamshin turaranta ne ya tabbatar min da cewa tazo inda nake na dago kaina ina kallonta tana yi min kallon kaskanci tace." Da izinin wa kike shige da fice a sashen Yarima." Wani kallo nai mata nace"Da izinin mahaifiyarsa." Girgiza kanta tayi tace"Itace ta baki guba kisa masa a abinci ko kuma wa." wani irin kallo nai mata nace'' Uwa ta haifi d'anta ta kashe shi anya kina da hankali kuwa."? Rai a bace ta kalleni tace"Ni kike fadawa wannan maganar."? Nace"To ai ji nayi maganar taki tayi kama data mahaukata." Shuru tayi na minti biyu, kafin tace"Tunda kin zama mai kula dashi ta fannin abinci inaso nayi amfani dake domin cimma munufata."! Kallonta nayi babu walwala a tare dani nace"Wace irin manufa ce."? Murmushi tayi tace"Kije zan neme ki gobe zamu tattauna." Girgiza kaina nayi na wuce daga gurin ina mamakin maganar ta Gurinmu na koma a gurguje nayi wanka na sauya kaya kana na zauna domun karyawa hira muke da Tambaya amma koda wasa ban fada mata abinda ya faru ba, Tace"Sumayya babu abinda zamu cewa Yarima Ali kinga maganin nan da kika kawo jiya yana da kyau dan jiya gabad'aya babanki bai kwana da zazzabi ba kinga jikinsa ma gumi yake alamu na nuna lafiya ta samu." Nace"To Alhamdulilahi idan na koma sashen zanyi masa bayanin yanayin jikin nasa." Tace"Hakan yana da kyau ki 'karayi masa godiya." Nace "Insha Allah." A gurguje na kammala karin kummalo na dauki jakar litattafaina sallama nayi mata na nufi gurin karatu. 'Karfe d'aya da rabi mun fito daga karatu hira muke da Lahira ina tunanin fada mata abinda ya faru, Lantana ta k'araso gurin. "Sumayya kije b'angaran Mamma Fulani tana son ganinki." Gabana ya fadi ido na tsirawa Lantana ina so nayi magana amma bakina yayi nauyi ina kallo Lanatana ta bar gurin na garara cewa komai..........."Lahira dan Allah zoki rakani." A sanyaye nayi mata maganar. Tace"Muje Allah dai yasa ba laifi kikayi ba." Nace" Bana tsammanin hakan." Tafiya muke ni da ita kowa na sa'ke sa'ke a ransa. Lahira guri ta samu ta zauna a harabar gurin ni kuma na nufi kofar shiga falon masu gadin kofar ne suka bude min na shiga a nutse sallama nayi cikin nutsuwa na 'karasa inda suke zaune ita da yaron nata. Gwiwa a kasa kaina a sunkuye nace"Ranki ya dade barkanku da wannan lokaci." Amsa min tayi a nutse tana gyara zamanta shi kuwa ko kallona baiye ba kanshi yana dukufe yana kallon kasan kafet kamar yanda ya saba. "Sumayya." Sunana data kira yasa na dawo cikin hankalina. a nutse na amsa "Na'am ranki ya dad'e. " Inaso ki nutsu da kyau zamuyi magana dake." Ciki da tsantsar ladabi Nace"To ranki ya dade ina sauraranki." "Sumayya kiji tsoron Allah kiji tsoron mahallicin ki ki fad'a min gaskiyar lamari shin waye ya saki zubawa Magajin sarki guba a cikin abinci? inaso ki fad'a min gaskiya akan al'amarin nan daya faru babu abinda za'ayi miki idan kin fad'i wanda yasa ki aikata wannan mugun aikin gaskiyar magana nake jira ta fito daga bakin ki. Zuciyata ce ta karye hawaye na kokarin zubo min ina kokarin mayar dashi sai da ya zuba a raunane nace" Ranki ya dade wallahi tallahi Allah d'aya ne daga shi babu wani, babu wanda ya sani na zubawa Yarima guba a farfesu wallahi ban san yanda al'amarin nan ya faru ba." ina kuka na kare maganar. Shuru falon yay na minti biyu kafin tace"Yi shuru ki daina kuka nayi miki wata tambaya." Hannu nasa na goge hawaye nace"Ranki ya dade ina sauraranki." tace"Bayan kin kammala aikin ki babu wanda ya shigo gurin."? Shuru nayi ina tunanin maganar....... *BINTA UMAR ABBALE* *Kuyi sharing👏🏻* 2/11/21, 8:19 AM - ???: *'KWARYA TABI 'KWARYA* *NA* _BINTA UMAR ABBALE🍒_ *bintaumarabbale@gmail.com* *MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION📘🖊?* _'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_ _________________________ *Littafin na kudi ne....!* _#300.....0542382124...Binta Umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai ki same ni ta wannan numbers..08089965176 _07084653262 Zanyi miki bayanin yanda zaki turo katin.......... Ga masu bukatar VIP Group 600 ne_ _Mutanan Nijar zaku tura dala dari ta wannan numbers katin airtal ko orange VIP jakka d'aya 90899076_88137740_ *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 27&28 "Anya Shatima da Moddibo zasu iya cutar da d'an uwansu? tunanin da nakeyi kenan a cikin zuciyata. ni dai nasan babu wani 'bako daya shigo sashen bayansu sai ni dasu Haruna bana tsammanin Abokanshi kuma shaqiqan 'yan uwansa zasu iya sa masa abunda zai kashe shi a cikin abinci. shuru nayi kaina a kasa ina tararrabin fad'ar maganar dake bakina. "Sumayya ke nake saurare." Muryarta ce ta doki dodon kunnena. A nutse nace"Ranki ya dade babu wani bako daya shigo sashen sai 'yan uwanshi wato Shatima da Maddibo sune suka shigo bayan na jera abincin a daning na hau sama domin in sheda masa lokacin dana sakko na samesu su biyu a falon." na karasa maganar ina sake sunkuyar da kaina......Fulani na shirin magana ya katseta da fad'in "Me kike nufi da wannan maganar kina nufin Maddibo ko Shatima wani na iya samin guba a abinci."? Shuru nayi gabana na fad'uwa sabida yanayin yanda yay maganar ya nuna min 'bacin ransa." "Sumayya." naji ta kira sunana, amsawa nayi ina kallonta, tace"Tun ganina dake na farko naji kin kwanta min a raina sosai na yaba da nutsuwarki da hankalinki ina mutukar son mutum mai gaskiya da rikon Amana, inaso ki ri'ke amanar dana dam'ka miki hannu biyu kisa idonki sosai akan masu shige da fice a sashen babana, tunda ka kan 'yan uwanshi maza da mata da kuma sauran bayin dake cikin gidan nan inaso kisa idonki sosai akan shige da ficen su a sashen sannan ki dinga lura da abincinsa gami da abin shansa ruwa ko lemo ko makamancin haka Ina neman wannan alfarmar a gurin." Cikin sanyin jiki nace"Insha Allahu zan kula da amanar da kika bani nayi al'kawarin bin umarninki." Murmushi tayi a nutse tace"Tashi kije Allah yayi miki albarka." na amsa da ameen ina jin sanyi a cikin raina. yun'kurawa nayi a nutse nace"A tashi lafiya ranki ya dade." Hannu ta daga min alamun naje da sauri na bar gurin zuciyata tas tabbas addua bata faduwa 'kasa banza. A nutse ta kalleshi gami da fadin"Babana me ka fahimta a maganar yarinyar nan? ni ina ganin wannan al'amarin daya faru da akwai saka hannun 'yan uwanka ina nufin Shatima da Moddibo." Kallonta yayi mamaki tattare a fuskarsa, tace"Ko shakka bana yi akwai saka hannunsa a ciki amma inaso kasa ido sosai a kansu sannan ka kula da kanka ba komai xaka ci a gabansu ba akwai mummunar manufa a zuciyarsu." "Mamma bana tsammanin Shatima ko Moddibo wani zai iya cutar dani a cikinsu ni nafi tunanin wani abu yarinyar nan tayi amfani dashi gurin girkin wanda ya janyo hakan bana zargin kowa akan faruwar wannan al'amari. Murmushi me ciwo tayi tace" Nima bana zargin kowa amma dai tunda nace maka kayi takatsantsan dasu to kayi domin hausawa na cewa makashinka na gindin ka nasan baka manta irin zaman marinar da akeyi a cikin gidan nan ba, kowa ka ganshi ka kalle shi kawai mafi akasarinsu babu kyakkyawar manufa acikin zuciyarsu." Shuru yayi yana nazarin maganar mahaifiyar tasa. *** Lahira tace"Wai ya naga kin fito jikinki duk a sanyaye." Ajiyar zuciya na sauke nace"Lahira ina cikin tsaka mai wuya amma na roki Allah ya fitar dani cikin ruwan sanyi." Tace"me ya faru." A nutse na warware mata dukkanin abinda ke faruwa. Lahira a jiyar zuciya ta sauke tace"Gaskiya dole ki shiga tashin hankali amma mungode Allah da ya sanya Maimartaba da amaryarsa masu fahimta ne, daba dan hakaba nasan da tuni kina fuskantar hukunci." Nace"Hakane Lahira amma shi Yariman bai yarda da cewa 'yan uwansa zasu cutar dashi ba ban san abinda ke cikin zuciyarsa ba." Lahira shuru tayi tana tunani kafin tace"Dama ai bai za ma lallai ya yarda ba saboda ganin sun taso tare abu makamancin wannan bai ta'ba faruwa ba a tsakaninsu dole ya shiga ko kwanton cewa zasu iya cutar dashi." Nace"nima nayi kokwanto da farko daga bisani da nayi tunani sai na gane hakan zata iya faruwa tunda yanzu gabad'ayansu idanunsu ya rufe babu abinda suke so sai mulki na fahimci cewa suna masa hassada dan ganin kamar shi zai gaji mahaifinsa." Lahira tace"Dama abinda yake faruwa kenan yanzu duk wani abu da 'yan uwansa zasuyi masa a kan mulki ne saboda haka shawarar da zan baki itace ki zage damtse ki kula da amanar da kika d'auka kiyi iyakacin bakin kokarin ki gurin ganin kin kareshi daga sharrin masu sharri." A sanyaye nace"Insha Allahu zan lura zanyi iyakacin bakin kokarina." Da wannan maganar muka rabu da juna. Sosai nayi farin cikin ganin babana a zaune yana cin abinci da kuzari a tattare dashi, cikin farin ciki na ajiye jakata na zauna kusa dashi ina murmushi nace"Baba nayi farin cikin ganinka a zaune kana cin abinci da hannunka hakika hankalina na tashi a duk sanda zanga Tambaya na baka abinci a baki yau naji dadi sosai dana ganka ka samu lafiya kana ciyar da kanka abinci da hannunka." Murmushi yayi a nutse ya kalleni yace."Ai tun bayan fitarku ke da mahaifiyarki naji kwari a jikina da kaina nayi wanka nayi dukk sallolin da ke kaina Sumayya hakika bamu da abinda zamuyi wa Yarima sai dai addua gami da fatan gamawa da duniya lafiya naji dad'in taimakon da yayi min Allah yayi nufin zan samu lafiya ta dalilinsa hakan yasa na yanke shawara kancewa bayan sallar isha'i zaki rakani nayi masa godiya kan alkairin da yayi min." Ina murmushi nace"Gaskiya ne baba Yarima ya cancanci godiya daga gurinmu insha Allahu zanyi maka jagora zuwa gurinsa kamar yanda ka bukata." Yace."To masha Allah kema ki dauki abinci kici dan naga kamar da akwai yunwa a tare dake." Cike da walwala nace"Baba lokacin dana shigo ina dauke da yunwa mai tsanani amma ganinka a zaune kana cin abinci da kanka yasa naji cikina ya cika yanzu bana jin yunwa ko kadan." Yana dariya yace."Sumayya ban yarda ba dole kici abinci domin bana son ki zauna da yunwa. kwanukan dake gabansa na janyo Cike da tsokana nace"To bari na fara cinye wanda ka rage saboda na samu albarka idan ban koshi ba sai na karo wani." Hannunsa na dama ya d'ora a saman kaina fuskarsa dauke da yalwataccen murmushi yace."Allah yayi miki albarka Sumayya." Ina kokarin kai abinci bakina Na amsa da ameeen baba." Tsaf na gama cikin abincin na gyara gurin na gyara masa shimfid'arsa kana na shiga tattaro kayan wankin mu kwata kwata bana san zama da daud'a shiyasa kullum gurin mu zaka sameshi a tsaftace babu kazanta ko kad'an. Wanki na fito dashi tsakar gida na ajiye a guri guda kana na koma cikin dakin, na sameshi yana duba littafin addini nace"Baba bari naje na duba dawakai bana so hankalina ya dauke gurin wanki na manta ban basu abinci ba." Ya kalleni yana girgiza kansa nasan abinda yake ji a zuciyarsa game dani,sunkuyar da kaina kasa nayi yace."Ina alfahari da Allah ya bani ke a matsayin 'ya kin fiye min haihuwar maza goma Sumayya ina alfaharin samunki kuma ina mai tabbatar miki da cewa yanda kikayi mana biyayya kema da yardar Allah naki 'ya'yan zasuyi miki." Murmushi nayi cikin jin dadin adduar da yayi min nace"Insha Allah baba kada ka damu zan cigaba da kula da aikin ka har sai sanda ka samu kwarin jikin ka." Murmushi yayi ya zuba mata ido har ta fita daga dakin, ajiyar zuciya ya sauke yana addua akan Allah ya bashi tsawan rai a duniya yaga auranta da abinda zata haifa........... *BINTA UMAR ABBALE* *Kuyi sharing👏🏻* 2/11/21, 8:19 AM - ???: *'KWARYA TABI 'KWARYA* *NA* _BINTA UMAR ABBALE🍒_ *bintaumarabbale@gmail.com* *MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION📘🖊?* _'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_ _________________________ *Littafin na kudi ne....!* _#300.....0542382124...Binta Umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai ki same ni ta wannan numbers..08089965176 _07084653262 Zanyi miki bayanin yanda zaki turo katin.......... Ga masu bukatar VIP Group 600 ne_ _Mutanan Nijar zaku tura dala dari ta wannan numbers katin airtal ko orange VIP jakka d'aya 90899076_88137740_ *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 29&30 Tana zaune a kan kujera ya shigo ya sameta, zama yay a gabanta ya dafe kansa kana ganin fuskarsa kasan yana cikin damuwa....Kallon fuskarta nayi itama nan take na gane akwai abinda ke damunta, Uwargida Huwaila mai babban daki ina nufin uwargidan Maimartaba itace tare da Moddibo a zaune abin duniya ya ishe su, Kallonsa tayi cikin tsantsar bacin rai da takaici tace " Wai shin Moddibo ka tabbata duka maganin ka juye masa a abincin."? Ajiyar zuciya ya sauke a cizgune yace"Wallahi gabadaya na juye domin ki tabbatar da magana ta ma kinga muzubin maganin." Hannu ya zira a aljihu ya dauko wata madaidaiciyar kwalba.......Tace"Amma gaskiya abin ya bani mamaki wallahi, wannan maganin karfi ne dashi banyi tsammamin Yarima Ali zai shura a gurin ba." Yace."Ni kaina al'amarin ya bani mamaki wallahi a yanda nasan maganin nan da saurin kisa banta'ba tsammanin zaiyi rai ba." Ajiyar zuciya ta sauke tace"Shegen yaro karfin jini gareshi to tunda ya tsallake wannan zamu barshi ya huta idan an kwana biyu mu cigaba da bibiyarsa dan ba rabuwa Zamuyi dashi ba har sai munga baya motsi sannan zamu hakura." Muddibo tsaki mai karfi yaja yace."gaskiya naso ya ya she'ka barzahu amma babu komai kamar yanda kika fada cewa ba zamu rabu dashi ba har sai mun cimma munufarmu a kansa." Tace"Ka manta kawai idan an kwana biyu zan sake kiranka mutattauna yanda za'ayi." Yace."Shikkenan sai naji daga gareki." Sallama sukayi da juna kowanne zuciyarsa cike da mugun nufi akan Bawan Allah. Sai kusan biyar da Rabi na yamma na gama wanki lokacin Tambaya ta dad'e da dawowa ina jin tashin maganarsu a daki suna hira ita da babana na dinga jin wani irin farin ciki da nishadi a cikin zuciyata hakika ina matukar so na ga iyayena na walwala da farin ciki. A gurguje nayi wanka na fito na kimtsa jikina da sauri na kallesu nace"Ni zanje sashen Yarima domin na dafa masa abinda zaici da daddare." Cike da nuna kulawa sukayi min fatan alkairi Da sauri nake tafiya ina kallon rana wacce take 'kokarin fad'uwa hakan ya nuna min cewa yamma tayi sosai daf ake da kiran sallar magariba tunda safe ban kara komawa sashen ba sai yanzu, addua nake a cikin zuciyata akan kada Allah yasa ya tuhume ni da wata magana. Su Haruna na samu a harabar gurin muka gaisa a gurguje na wuce su daya daga cikin masu tsaron kofar ne ya bude min na shiga falon........Can na hangoshi kwance kan doguwar kujera yayi filo da hannuwansa babu wata sutturar arziki a jikinsa vest ce mai duhu sai short nickar a jikinsa, kaina a kasa na 'karasa inda yake, tsugunawa nayi kamar koda yaushe nace"Ranka ya dade barka da yamma." Shuru yayi bai tanka min ba. satar kallonsa nayi ta kasan idona naga ya k'urawa rufin dakin ido, ganin yanda kwayoyin idanunsa suka kad'a yasa naji wani iri a jikina. gaishe shi na sakeyi yayi min banza. Jikina ne yayi sanyi da halin ko'in kular da yake nuna min, a rayuwata na tsani nayi magana a shareni, muryata na rawa nace"Ranka ya dad'e zan shiga kicin yanzu inaso ka fada min abinda kake bukatar ci da daddare." "Me ya hana ki shigowa da wuri."? a dakile yayi maganar, nace" Wallahi na tsaya nayi wanki ne shiyasa ban samu damar shigowa da wuri ba." Shuru yayi yana sake gyara kwanciyarsa, ta kasan idona nake kallonsa naga yana bin ilahirin jikina da kallo. sunkuyar da kaina kasa nayi ina adduar rinjaye. "Kin iya tuwo."? Yafad'i maganar a kasalance. da sauri nace''Ranka ya dade kowane abinci kake bukata na zamani dana gargajiya na iya insha Allah baka da matsala." Ji nayi ya sauke wata ajiyar zuciya kamar wanda yaci kuka ya koshi! saurin d'ago kaina nayi ina kallonsa har yanzu ni yake kallo koda muka hada ido bai dauke kansa ba, yace."Kiyi min tuwo amma bana san wannan abar mai wari a cikin miya. " na gane daddawa yake nufi nace"To insha Allah ba zan san daddawa ba." Mikewa nayi da sauri na nufi kicin din....Wani irin kallo ya bita dashi yana lumshe idonsa, a duk sanda zai kalli wani sashe na jikin yarinyar sai yaji kamar ana 'kara rura masa wutar sha'awarta a cikin jikinsa. Kullum so yake ya yakice abin daga jikinsa abin yaci tura da yarinyar yake kwana da ita yake tashi, a zahiri da bad'ini yasan yarinyar ba kalarsa bace domin hausawa suna cewa *'Kwarya tabi 'kwarya* yana ganin ko iskanci zaiyi bai dace yayi da 'yar bayi ba wacce take ma'kaskanciya a 'kasan sa, dalilin daya sa kullum yake kokarin cire sha'awarta a cikin ransa abin nacin tura, sam rashin kyawunta da 'bakar fatar ta basa damunsa abubuwan dake da wahalar samu daya hango a jikinta yake kulafuci yana ganin zai huta sosai a jikin yarinyar, yaso ace tana daidai dashi ne to da babu abinda zai hanashi auranta kodan ya kawar da 'kulafuncinsa a kanta. Mi'kewa zaune yayi ya rufe fuskarsa da tafukan hannayensa ya kai mintina goma a haka kafin ya mike yabi bayanta kicin din Motsin tsayuwarsa naji a bakin kofa nayi saurin juyawa ina kallonsa, tsorata nayi sosai ganin yanda yake kallonsa da idanunsa da sukayi ja gashi sai lumshesu yake......Baki na rawa nace"Ranka ya dade kana bukatar wani abu ne."? Girgiza kansa yay alamun baya bukatar komai. Jikina a sanyaye na juya domin cigaba da aikina amma inaa! tsabar yanda idonsa ke tasiri a kaina yasa na kasa ta'buka komai. 'Kasa - 'kasa naji yace.'' Idan kin gama kizo ki gyara min toilet d'ina." Na kalleshi inaso nayi magana sai naga ya juya ya tafi. Tsayuwa nayi ina mamakin maganarsa na dauka ai gyaran gida dasu toilet duk nasu Haruna ne ni bani da hurumin hakan, to kodai yana da wata munufa ne? wani sashe na zuciya ta yake fada min haka.. shuru nayi ina nazari, to ko ma dai wace irin manufa yake da ita a kaina bana fatan ya samu galaba a kaina toilet zan shiga in gyara masa da tsarkakkiyar zuciya. saboda haka ina gama ayyukana na nufin dakin nasa domin aikata aikin daya umarceni. Zaune na sameshi a kan sofa idanunsa tsaye a kofar shigowa hada ido mukayi nayi gaggawar sauke kaina kasa, cikin tsarguwa na k'arasa kofar toilet din zanin jikina sai hard'eni yake tsabar yanda ya 'kureni da idanunsa, toilet din na bude na shiga ba tare da nace masa komai ba gaskiya na fara gajiya da wannnan masifaffan kallon da yake min.........Girman toilet din da yanda aka 'kawata shi ya dinga bani mamaki bandaki gurin zubar da najasa an narka masa dukiya kamar baza'a mutu ba, girgiza kaina nayi na tattare zanina cikin sauri na soma aikina so nake nayi saurin gamawa kada magariba tayi.....Undis dinsa na tattara nasa cikin abin wanki ina kokarin kunna washing machine din ya shigo toilet din, ban yarda na kalleshi ba nace"Ranka ya dad'e za kayi wani uzirin ne."? Inda nake tsaye ya durfafo gabana ya tsananta fad'uwa adduar rinjaye na shigayi a cikin zuciyata. Daf dani ya tsaya yana fesa min hucin numfashinsa, kasa kallonsa nayi sabida yanda naga ya koma wani iri gabadaya yanayin fuskarsa ya sauya kalar tausayi. babu zato naji ya riko hannuna ya d'ora saman short nickar din dake cikinsa, a zabure! na cire hannuna ina kallon gurin.....gabansa naga ya mike cikin wandon yana sake kokarin kamo hannuna yasa a gurun....bangajeshi nayi da karfin gaske! yayi taga-taga zai fad'i! cikin zafin nama na bude kofar toilet din na fita gabana na dukan uku uku anya kuwa zan iya cigaba da zama da wannan guy kuwa? gabadaya yanda na fahimce shi baya nufina da alkairi. Bayan fitar ta daga toilet din goshinsa yasa a jikin bango (garu) yana furzar da wani irin huci mai zafi daga bakinsa, ya rasa wace irin masifa ce wannan gabad'aya ya rasa gane kansa da abinda ke damunsa burinsa bukatarsa ta biya da yarinyar ita kuma taki ta bashi had'in kai yarinyar gabadaya ba tsaransa bace har ya ajiye girma da muqamin sa yana biyayyarta tana wula'kantashi yana ganin dole ya nuna mata kuskuranta akan irin abinda take masa, da kyar yay wanka ya daura alwala ya fito fuskar nan babu fara'a ya kintsa jikinsa, k'asa ya sauka, lokacin na kammala komai na shirya gurin cin abincin ina zaune abin duniya ya isheni......tunda naga yanayin fuskarsa nasha jinin jikina, koda ya karaso inda nake sake risinar da kaina nayi da fadin"Barka da fitowa." Wuce ni yayi ya nufi hanyar fita ba tare da yace komai ba. bayansa nabi da kallo ina ayyana abubuwa da yawa a kansa. Bayan fitarsa da minti goma nima na bar gurun. Sai bayan daya gabatar da sallar isha'i ya shigo kai tsaye gurin cin abinci ya nufa ya zauna daya daga cikin kujerun gurin, wayarsa ya d'auko ya shiga ma'adanar hotuna tarin pictures ne na matan turawa da bakake fata wanda ba zasu irgu ba, yawanci kuma duk tsirara suke pictures din yake kallo wai ko zai samu sasaaucin abinda ke damunsa. Cikin wannan halin na fito na sameshi, kai tsaye inda yake na nufa. Dan risinawa nayi murya k'asa nace''Ranka Ina iya zuba maka abincin." A watse ya kalleni yace."haka kawai zan zauna anan gurin babu dalili."? Da sauri nace"Afuwa ranka ya dade." Mikewa nayi cikin nutsuwa na bud'e fulas din dana sa tuwon a ciki na dauk'o leda biyu nasa akan plate na mayar da fulas din na rufe miyar na bud'e itama nasa ma a plate na bude daya fulas din dake dauke da jar miya waccan nasa mata naman rago itama nasa masa a plate kana na mayar na rufe ruwa da lemo na ajiye masa gabansa naja gefe na tsaya kaina a kasa nace"Ranka ya dad'e na had'a komai." Dago kansa yayi yana bin abincin da wani irin kallo yana ya mutse fuska yace."Ke! wannan wane irin tuwo ne ba'ki sai kace ke."!! Naji ciwo cimin fuska da yayi, cikin dauriya nace"Ranka ya dade tuwon dawa ne.'' Tsaki yaja mai karfi ya mike a fusace ya d'aga k'yallen da abincin ke kai ya watso min a jikina.! cikin rashin mutunci yace."Waye zaici wannan ba'kin abun ko an fad'a miki kowa ma jaki ne kamar ki! dallah malama matsa ki bawa mutane guri."! Cikin hayaniya yake maganar har yana dukan daning d'in da hannunsa.... *BINTA UMAR ABBALE* *Kuyi sharing please👏🏻* 2/11/21, 8:19 AM - ???: *'KWARYA TABI 'KWARYA* *NA* _BINTA UMAR ABBALE🍒_ *bintaumarabbale@gmail.com* *MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION📘🖊?* _'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_ _________________________ *Littafin na kudi ne....!* _#300.....0542382124...Binta Umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai ki same ni ta wannan numbers..08089965176 _07084653262 Zanyi miki bayanin yanda zaki turo katin.......... Ga masu bukatar VIP Group 600 ne_ _Mutanan Nijar zaku tura dala dari ta wannan numbers katin airtal ko orange VIP jakka d'aya 90899076_88137740_ *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 31&32 Cikin wani irin yanayi na 'kunar zucci nake kallonsa kafin na kalli jikina gabad'aya gaban rigata ya 'baci da miya har wajejen wuyana da gefan fuskarta ya samu rabonsa, idona naji yana kawo ruwa wannan irin wulakanci ne dacin mutumci mutumin nan yake min, danne damuwa ta nayi na kalleshi yana zaune sai huci! yake kamar wanda akayiwa gagarimun laifi nace"Ranka ya dad'e kai ne ka bukaci da ayi maka tuwo ni kuma sai nayi tunanin tuqa maka na dawa saboda nasan abun marmari ne zai fi maka dadi akan sauran dan me zaka wulakanta ni ka wulakanta abinci babu kyau abinda ka'aikata domin akwai mutane da yawa da suke neman abinda zasu kai bakinsu kai ka samu kana watsar wa." Cike da jarumta nake maganar. Wani irin kallo naga yanayi min na k'askanci kafin ya tattaro yawun bakinsa ya tofa min a fuska cikin izigalanci yace."Ki 'bace min daga gurin nan na daine ganin wannan ba'kar fuskarta ki a idona." Takaici kamar ya kasheni nasa hannu na goge yawun daya tofa min, baki na bude zanyi magana ya daga min hannu alamun baya bukatar yaji abinda zance, banyi shuru ba domin na riga na dauki aniya akansa, Nace''Kana yawan kushe hallitar Allah shin wai me bak'in mutum yayi wa mutane ne da suke 'kyamatarsa kada ka manta yadin da akayiwa d'akin Allah ado ba'ki ne,, da farin mutum da b'akin mutum duka Allah ne ya hallicesu kuma bai fifita wani akan wani ba duk daya suke a gurinsa wanda yafi kyautata masa shine mafi kusanci dashi, amma kun d'auki karan tsana kun d'orawa 'bakar hallita wannan yana nuni da cewar kuna nunawa Ubangiji cewar bai hallita ba." Mi'kewa tsaye yayi ya nuna min kofar fita da hannunsa. Girgiza kaina nayi na bar gurin zuciyata na wani irin tafarfasa gabad'aya halayyar sa bata da kyau girman kai gami da izzah muna nan ayyuka ne wanda Allah baya so yana da ilimin addini daidai gwargwado yasan abubuwan da yake aikatawa basu da kyau amma saboda shed'an ya riga ya gama yi masa fitsari akansa kullum daukar kansa yake wata tsiya alhalin kuma a gurin Allah ba komai bane. Koda na shiga gurin mu kai tsaye ruwa na zuba a bokiti na shiga band'aki domin wanke jikina nasan idan na shiga daki iyayena suka ga jikina a 'bace zasu tambayi dalili shiyasa nayi wannan dubarar, bayan nayi wanka zanin kamfalar na d'auro a kirjina na yafa dankwalin na fito, ina tsaka da d'aura alwala Tambaya ta fito daga daki, tace"haba ni tun dazu nake jin motsi ina daki nace bari dai na duba na gani ashe kece."tana kallon fuskata tafadi maganar, kokarin kawar da abinda ke damuna nayi nace"Ai ina shigowa bandaki na nufa nayi wanka ko jikina ya warware." Tace"Ai kam wannan uban wanki da kikayi ai dole jikin ki yayi miki tsami amma me yasa baki d'umama ruwan zafi ba? ina ganin da da ruwan zafi kikayi wankan sai kinfi jin dadi." Nace"Nima sai da na fara wankan sannan nayi tunanin hakan." Tambaya kicin ta wuce domin ajiye kwanonin abinci dake hannunta ni kuma bayan na daura alwala dakin na shiga na samu babana zaune a kan dadduma yana lazimi sannu nayi masa na shige cikin kuryar dakin domin na kimtsa jikina. Irin dai kayan nasa a jikina na fito da hijabin da nake sallah a wuyana, dadduma na hau na tayar da sallah..........Tambaya ta shigo dakin hannunta rike da silba mai murfi a kusa dani ta ajiye silbar tace"Idan kin idar ga abincin ki nan." kuryar dakin ta shiga domin gabatar da tata sallar, bayan na idar da sallar na jima hannuna a sama ina rokon Allah yasa naci jarabawar daya d'ora min na kuma tsananta addua ta akan ya kareni daga sharrin masu sharri. shafawa nayi a fuskarta na juya ina kokarin cire hijab din wuya na, sai naga babana na shafa fuskarsa da dukkanin hannuwansa hakan ya nuna min cewar adduata yake shafawa a fuskarsa. Ina murmushi nace"Baba barkan ka da dare." Shima da murmushin a fuskarsa yace."Barka dai yarinyar arziki." silbar abincina na janyo a nutse nace"Naso na dawo da wuri muci abinci a tare domin samun tabarraki." da yalwatacciyar fara'a a fuskarsa yace."Na riga naci abinci Sumayya amma kawo na sa miki albarka." Da sauri na miqa masa silbar abincin ina murmushi, bisimillah yay yasa hannunsa ya d'ibi dafadukan shinkafar dake cikin silbar a bakinsa yasa yana taunawa yace."To gashinan nasa albarka." Silbar na janye na gyara zamana ina murmushi nace"Godiya nake baba Allah ya kara maka lafiya." ya amsa da amin yana kallona da murmushi a fuskarsa. D'akin ne yay shuru na minti biyu kafin na kalleshi a nutse nace"Yanzu idan na kammala cin abincin zamuje can sashen Yariman ko."? Yace"Af kinga na manta wallahi gwara da kika tuna min maza gama cin abincin muje." "To nace" na mayar da hankalina gurin cin abincin...Tsaf na kammala na fita da kwanon ina shiga dakin na tarar dashi a tsaye kuryar dakin na leqa Tambaya na kan dadduma da carbi a hannunta nace"Zamuje sashen Yarima da Baba." Hannu ta daga min alamun sai mun dawo." Koda na juyo sai na tarar har ya rigani fita murmushi nayi nabi bayansa da sauri. Lokacin da muka isa sashen shuru dan su Haruna ma a harabar gurin muka samesu nan yake sheda min ai Yalla'bai din ne yace su fita su bashi guri zuwa anjima sa dawo." hakan ya nuna mun cewa har yanzu yana cikin 'bacin ran abinda ya faru tsakani na dashi.....Babana na kalla a tsanake nace"Baba zauna bari na hau sama na sheda masa zuwanka. Ya samu kujera ya zauna a nutse ni kuma na nufin saman domin sheda masa zuwansa.....Na jima ina nocking kafin naji yace."Waye."? A sanyaye nace."Nice." shuru na minti biyar naji alamun bud'e k'ofar matsawa gefe nayi kaina a kasa......Wani irin kallon banza ya watsa min da fad'in "Lafiya."? Kai a kasa nace" Babana nayiwa jagora zuwa gurinka yana so ku gaisa kana yay maka godiya kan alkairin da kayi masa sosai yaji dadin magungunan daka bashi yanzu haka yana 'kasa jiranka.'' Shuru bece komai ba na d'ago kaina a sace na kalleshi sai naga yana kallon 'kasan gurin, ajiyar zuciya na sauke cikin raina nace"Abin yazo kenan kallon k'asa kamar makaho." Mun kai minti biyar nida shi a tsaye a kafin naji yace." Ni Bana abun alkairi domin a gode min, ba ni na bawa babanki Lafiya ba Allah ne dan haka shi zaiyi wa godiya ba niba." Yana k'are maganarsa ya bugo min kof'a. Na jima a tsaye a gurin ina kallon kofar kafin na sauke ajiyar zuciya a sanyaye na sau'ko 'kasa na sameshi a zaune a inda yake. Cikin taushin murya na sheda masa abinda yace....bai nuna komai ba yace."To babu komai Sumayya dama mafi akasari masu taimako basa so a damesu da godiya tabbas hakane Allah ne ya bani lafiya amma kuma shine ya zama sanadi dan haka zan cigaba dayi masa addua har karshen rayuwata." A sanyaye nace"Hakane baba Allah ne abin godiya a garemu addua kuma ba zamu daina yi masa ba tunda shi ya zama sanadi.'' To Har muka isa gurin mu muna tattauna maganar a tsakanin mu........... *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 8:19 AM - ???: *'KWARYA TABI 'KWARYA* *NA* _BINTA UMAR ABBALE🍒_ *bintaumarabbale@gmail.com* *MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION📘🖊?* _'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_ _________________________ *Littafin na kudi ne....!* _#300.....0542382124...Binta Umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai ki same ni ta wannan numbers..08089965176 _07084653262 Zanyi miki bayanin yanda zaki turo katin.......... Ga masu bukatar VIP Group 600 ne_ _Mutanan Nijar zaku tura dala dari ta wannan numbers katin airtal ko orange VIP jakka d'aya 90899076_88137740_ *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 33&34 Kwana biyu kyara da hantara ne a Tsakanina dashi komai nayi masa ba nayi masa gwaninta, magana kuwa sai nayi sau biyar bai bani amsa d'aya ba, haka dai na cigaba da hakuri da halinsa ina kokarin ganin na sauke nauyinsa dake kaina, a tsakanin kwanaki biyu zuwa hud'u duk abinda zan girka masa naci ko sha baya ko kallon daning din ballanatana ya zauna yaci, yanda na ajiye haka zan zo na dauke, ganin kamar 'barnar tayi yawa yasa na yanke shawarar samun sa muyi magana idan baya bukata sai na daina wahalar da kaina da asarar abinci........ samun sa nayi gurin da yake hutawa na tsuguna gwiwa a 'kasa kamar koda yaushe nace" Ranka ya dade Barka da yamma." Kamar da dutse nake magana, kallonsa nayi ina jin wani kunci a cikin zuciyata, a gaskiya na fara gajiya da wannan wulakancin, hankalinsa na kan wayarsa yana latse latse a kai......'bacin ran dake taso min na danne Nace"Dama inaso muyi magana da kai ta fahimta ne." Ta 'kasan ido naga yayi min wani kallo, na cigaba da cewa"Naga kamar baka 'bukatar abincin da nake hidimar girka maka safe da rana da dare me zai hana a daina a sarar abinci idan baka bukata sai na bari akan a dinga zubarwa." Zamansa ya gyara yayi wani irin zama irin nasu na saurata hannunsa dake d'auke da zobunan azurfa ya d'ora saman gwiwarsa ya tsira min idanunsa. Kasa kallonsa nayi a yanayin dan ganin yanda ya 'kara wani kwarjini da cika ido gashi zaman da yayi yay masa kyau ha'kika ya dace a kirashi da *Sarki!* ba Yarima ba dan komai nashi cikin mulki da muskilanci yake yi. "Kece kika ajiye abincin gidan da kike wannan maganar."? Maganarsa ta bani mamaki sosai nace" A'a bani bace ba, ni a nufina 'barnar abincin da ake tayi yawa sabida na safe haka yake tarar dana rana sannan na dare ya tarar dana rana, wani zubin lalacewa yake sai dai na bawa dabbobi ko na zubar." "Ki cigaba da aikin ki bana bukatar ki huta." Yafad'a tare da tsira mun ido gami da san ya tabbatar min da maganarsa, "Inaso ka fad'a min dalilin ka na yanke wannan hukuncin ya za'ayi kai ba cin abinci kake ba amma kasa a girka a zubar wannan ai izgilanci ne." Gaura min mari yay yana huci yace."Koda yaushe kina yawan fad'ar wannan maganar akai na sabida kin raina ni ko."? yana nuna ni da hannunsa yake maganar, d'auke kaina nayi daka fuskarsa nayi kasa dashi hannuna dafe da kuncina....."Wallahi duk sanda na sake jin kin jefe ni da kalmar izgilanci sai na baki mamaki na lura dake kwata-kwata bakya shakka fad'a min kowace kalma kodan kinga na nuna ina sha'awarki ne kike tunanin wani abu.'" D'agowa nayi raina a 'bace Nace"Allah ya baka hakuri idan furucina ya 'bata maka rai ni inaso na tunasar da kai abinda ka sani ka manta ko kuma nace kake takewa saboda giyar mulki ranka ya dad'e kai mutum ne mai girman kai gami da Izigilanci a kan komai alhalin kai d'in ba komai bane a gurin Allah inaso na tunasar da kai cewa wannan d'abi'un da kake yi zasu nesan taka da rahamar Allah." Hawayen da nake maqalewa ne suka zubo. "Tashi ki bani guri."! Kalmar da ya fad'a kenan cikin 'bacin rai! Mikewa nayi na sunkuya cikin tausasawa nace" A gafarce ni idan maganar da nayi ta 'bata maka rai." Ba tare da yace min komai ba ya sunkuyar da Kansa k'asa. Gurin na bari da sauri na nufi sashen Mahaifiyarsa wato Fulani zuwa zanyi na sheda mata dukkanin abinda ke faruwa, domin kamar ita ta dauke ni aiki ta bani amana yana da kyau duk abinda ke faruwa tasa ni saboda kada wani mummunan abu makamancin wanda ya faru a baya ya faru a tuhume ni da wani abu, a tsakanin kwanaki biyar din da suka gabata bani da masaniyyar inda yake cin abinci na safe rana da dare idan ma a gurinta yake ci to yana da kyau na sani ko hankalina ya kwanta. Ina gurfane a gabanta na sheda mata dukkanin abinda ke faruwa......a da tana kishingid'e a lokacin da nake maganar sai naga tayi saurin mi'kewa zaune gabad'aya ta mayar da hankalinta kaina tace"Sumayya kika ce yau kwana biyar babana baya cin abincin da kika girka."? Nace"K'warai kuwa ranki ya d'ade ganin kwanakin suna yawa ne yasa na yanke shawarar zuwa na sheda miki." "A'ina babana yake cin abinci."? Tafad'a tana kallona, Nace" Ranki ya d'ad'e nima wallahi ban sani ba." Ajiyar zuciya ta sauke da sauri tace"Miko min wayata gata nan." Da sauri na dauka na mika mata. Number shi ta kira inaji yana gaisheta bata amsa ba tace"Maza kazo sashena ina nemanka." Kashe wayar tayi ta kalleni da fad'in "Sumayya kije ki cigaba da aikin ki kada ki fasa yi masa abinci a duk sanda kika kammala kika sheda masa idan bai ci ba kizo ki sheda min." Nace"To insha Allah ranki ya dade zanbi umarninki."Tace."Tashi kije Allah yayi miki albarka." Cikin farin ciki na amsa da "ameen Ranki ya dade ina godiya." Raina fari tas na bar sashen gurinmu na nufa domin nayi shirye shiryen shiga gurun karatu......Tsaf na fito cikin hijabi fari tas da jakar littafai a hannuna Babana na kwance a katifa bacci naso ya daukeshi nace"Baba kayi bacci ne."? Mi'kewa zaune yay yace." Yana dai so ya dauke ni dama ke nake jira ki shirya mu fita tare yau inaso na shiga gurin Dawakai na dubasu.'' Nace"Baba ka zauna ka sake samun 'kwari jikin ka dawakai na nan kalau babu abinda ya samesu." Yace."Sumayya zaman nan ya isheni wace lafiya kuma akeso na samu bayan wannan inaso na koma bakin aiki."Nace"To shikkenan baba nida naso ka k'ara watsakewa sosai kafin nan." Mi'kewa yay yana dariya yace."Sumayya zaman gida sai mata idan kinga namiji ya zauna a gida to dole ce kamar dai ni da rashin lafiya ya hanani gudanar da harkokina." Murmushi nayi nace "Hakane baba, to tunda Tambaya na gurin aikinsu sai mu sawa kofar 'kwad'o." Yace."Eh hakane yi maza ki d'auko kwad'on insha Allahu kafin ta dawo nima na dawo." 'Kwadon (key) na dauko muka fito tare muna hira na kulle gidan na bashi key din yasa a aljihun rigar jikinsa, muka fara tafiya.......Daf da zamu rabu kowa yay inda ya nufa Lantana ta tari gabanmu, a duk sanda zanga Lantana sai gabana ya fad'i saboda duk sa'kon da zata fad'a bana alkairi bane. "Sumayya kije can 'bangaran Maigirma Ciroma Gimbiya Lawisa ke san ganinki." Na kalleta da fad'in "Lantana kin dai ga shirin da nayi ko zan shiga gurin karatu ne sai dai idan na fito." "Kinga Sumayya bani zaki fad'awa hakaba ita wacce ta aiko ni ita zaki fad'awa ni dai na cika umarnina idan kin'ki zuwa zan tabbatar mata da cewa na sheda miki sa'konta." Zanyi magana babana ya katseni Ya kalli Lantana a nutse yace."Kije kice gatanan zuwa." Lantana ta bar gurin da sauri.......Cikin kulawa ya kalleni yace."Sumayya duk wani uziri naki to yabi bayan na masarauta, kiran da Gimbiya Lawisa tayi miki yafi uzirinki wanda zaki gabatar a yanzu, nasha fad'a miki cewar baki da wani gata da abinda zakiyi tun'kaho dashi sai wannan masarautar domin a cikinta aka haifi iyayena da kakanni na gabad'ayan mu tasowa mukayi muka ganmu a cikinta tsohuwar marasauta ce mai d'umbin tarihi, iyayenmu sunbi umarnin masarauta har suka koma ga Allah, Ina fatan ni dake da mahaifiyarki muma mu kamanta abinda magabatan mu sukayi dan haka kibi umarnin masarauta kije kiji kiran da akeyi miki. Ajiyar zuciya na sauke ina kallonsa a sanyaye nace"Baba naji kana maganar nabi umarni inaso nayi maka wata tambaya." Yace."Ina sauraranki."" Nace"Baba idan ya kasance wani umarnin ya sa'bawa dokokin Ubangiji ba shin har dashi zan bi."? Girgiza kansa yay yace."A'a Sumayya ban umarce ki akan sa'bawa Allah ba, duk abinda ya zama na sa'bawa mahallici ne to kiyi kokarin nesanta kanki dashi. Nace."Alhamdullihi baba bari nayi sauri naje domin naji kiran da ake min." Cikin kauna gami da tausayi irin na iyaye yace."To d'iyar kirki Allah yay miki albarka." Ameen nace cikin sauri na bar gurin....Lawi bai bar gurin ba har sai da ya daina hango 'yar tashi. Lantana ce tayi min jagora har Lambun da take hutawa, tare da hadimanta na sameta. takalmana na cire a nutse nasa gwiwowina a k'asan gurin nace"Barka da hutawa ranki ya dade." Shuru tayi min bata amsa ba. gurin ya dauki shuru na kusan minti uku kafin ta dago kanta cikin shan qamshi ta kalli hadimanta dake gefe da gefanta tace"Ku tashi kuje zanyi sirri da Sumayya." Jiki na rawa suka miqe suna godiya. Gurin ya sake daukar shuru na 'yan mintina kafin naga ta gyara zamanta cikin kasaita ta kalleni da fad'in "Zauna sosai muyi magana aini daga yau kin zama qawata aminiyata." Cike da mamaki nake kallonta ina mamakin furucinta. zamana na gyara sosai a gabanta nace"Ranki ya dade ina sauraranki. Ajiyar zuciya ta sauke kafin naji ta kira sunana. a nutse na amsa ina kallonta, Tace"Inaso na saki wani aiki ta 'bangaran Yarima Ali ina nufin magajin Sarki, tunda ya kasance kin zama mai kula dashi ta fannin abincinsa da abin shansa to zanyi amfani dake gurin ganin bukata ta biya a kansa. Nasan kin san da maganar auran dake tsakanina dashi ko."? Kallonta nayi ina mamakin maganarta aure a tsakaninta da Yarima gaskiya ban san da maganar ba. Girgiza kaina nayi nace"A'a ranki ya dade ban san da maganar ba." Tace"To yau na sanar dake cewa Iyayanmu zasu daure aurena dashi farkon watan gobe, a zahiri nike sonsa koda yana sona bai kai wanda nake masa ba, wannan dalilin yasa nake so nabi matakan da zasu janyo hankalinsa kaina, inaso kafin zuwan ranar daurin aurena dashi na mallake shi da zuciyarsa gabad'aya." Da sauri na kalleta, sai naga tayi murmushi tana d'aga min gira 'kasa nayi da kaina tare da cigaba da sauraranta. "A kwai wasu sinadarai da zan baki wanda zaki dinga zuba masa a cikin abincinsa da abin shan sa ya zama na dai duk wani abu da zai ci ko ya sha kina sa masa sinadaran dana baki.'' ajiyar zuciya na sauke tare dago kaina na kalleta bayan gama maganarta ta Nace....... *BINTA UMAR ABBALE* *Please kuyi sharing👏🏻* 2/11/21, 8:19 AM - ???: *'KWARYA TABI 'KWARYA* *NA* _BINTA UMAR ABBALE🍒_ *bintaumarabbale@gmail.com* *MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION📘🖊?* _'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_ _________________________ *Littafin na kudi ne....!* _#300.....0542382124...Binta Umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai ki same ni ta wannan numbers..08089965176 _07084653262 Zanyi miki bayanin yanda zaki turo katin.......... Ga masu bukatar VIP Group 600 ne_ _Mutanan Nijar zaku tura dala dari ta wannan numbers katin airtal ko orange VIP jakka d'aya 90899076_88137740_ *Sannu da kokari mai babban suna* *DR MUHAMMAD MK* Ina mutukar godiya da alkairin ka, na baka kyautar wannan pege d'in🥰 *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 35&36 "Ranki ya dad'e wane irin sinadarai ne kike magana akansu inso kiyi min bayani yanda zan fahimci inda maganar ki ta dosa." Duk da na gane abinda take nufi sai kawai na tsinci kaina dayi mata wannan maganar. Murmushi tayi tace"Haba Sumayya kamar ba mace ba zaki ce baki fahimci inda na dosa ba, to shikkenan tunda baki gane ba bari na fahimatar dake, Takanas! Mamana ta tura aka kar'bo mata Taimako daga gurun malamanta duk domin na samu nasarar mallakar zuciyarsa kin san hausawa nacewa ko kana da kyau ka qara da wanka to ballanatana ni da ban zauna daram a cikin zuciyarsa ba, kinga kuwa dole na tashi tsaye naga na r'ikeshi a tafin hannuna kafin zuwan ranar daurin auran namu." Wani irin kallo nake mata na mara hankali Nace"Ranki ya dade ki gafarce koda maganata zata 'bata miki rai ni ina ganin wannan sinadaran babu wani abu da zasuyi miki me zai hana ki nemi soyayyarsa ta hanyar Allah duk ga hanyoyi nan a saukake hanyoyin da zaki bi ki mallakeshi da zuciyar sa, a ganina idan kika ce ta wannan hanyar zaki mallake shi to zakiyi ta wahalar da kanki a banza da wof........."Ke! rufe min shegan bakin ki a nan gurin." A fusace ta katse min magana. Tsira mata ido nayi kallona take tana huci tace"Ba shawara na nema a gurinki ba umarni na baki zaki aikata abinda na saki ko ba zaki aikata ba. Har na bude baki zanyi magana sai kuma nayi shuru ina nazari, kai tsaye idan na'ki aminta da umarninta zata bi wata hanyar ne ta cimma k'udirinta, tabbas asiri zaiyi gaggawar tasiri a jikinsa tunda na lura bai wani damu da addini ba wannan tunanin da nayi yasa nayi saurin neman afuwarta nace"Insha Allahu zan zartar da umarnin zaki bani." Gyara kishingid'ar tayi tana saukar da numfashi, shuru gurin yay kimanin minti goma kafin naji tace"Kalleni nan." Na dago kaina na zuba mata ido. Wata leda viva ta miko min da fadin"Bud'e ki fito da kayan dake ciki." Da sauri nayi abinda tace, magunguna ne a 'kulle a wani 'bakin yanki mai ratsin ja da fari dauri uku tace."Ki duba a tsanake zanyi miki baya ni kada kije kiyiwa mutane baragada." Nace"Ina dubawa ranki ya dade." "Wannan wanda yake da ratsin baki da fari na abinci ne kina jina ko."? nace" Eh ina jinki." Ta cigaba da cewa"Duk wani abinda zaici ya kasance sai kin barbad'e shi da wannan maganin sannan ki bashi." Nace" na fahimta ranki ya dade." Ajiyar zuciya ta sauke tace"Shi kuma wannan mai ratsin ja da fari din na lemo ne kina jina ko."? Nace"Eh." ta cigaba da cewa"lemo ko wane iri ne kafin yasha ki bude ki barbad'a maganin a ciki." Nace"To ranki ya dad'e na fahimta insha Allah zanyi miki kokari nima inaso ki mallaki zuciyarsa." Dariya tasa tana kallona jin furucin da nayi....tsaki naja cikin zuciyata nace"Dubi shashashar banza." "Zaki iya tashi ki tafi inaso yau ki fara gudanar da aikin ki idan naga al'amura na tafiya kamar yanda nake so nayi miki alkawarin kyauta mai tsoka." 'ka'kalo murmishi nayi na yunkura domin mikewa nace"Godiya nake." Hannu ta daga alamun ta amsa. Takalma na zura hannuna ri'ke da ledar maganin nace"A tashi lafiya." Hanya ta nuna min alamar na tafi. da sauri na bar gurin zuciyata cike da takaici. Ina tafiya ina mamakin al'amarin gaskiya na raina wayon ta ashe duk 'kasaitarta ta banza ce tunda gashi ta kasa janyo hankalin namiji sai ta had'a da asiri! a zahiri gimbiya Lawisa nada kyau da kyawun jiki babu namijin da ba zaiyi sha'awar ta zama mallakinsa ba, gaskiya nayi mamaki da ba tayi wa Yarima Ali ba wato yanda na fahimce shi kyau ko yawancin wasu abubuwa basa burgeshi yafi duba nagartar mutum. ajiyar zuciya na sauke tsigar jikina na tashi dana tuna irin masifaffan kallon da yake min a duk lokacin da muka had'u....... cikin ramin bulo nasa ledar magungunan na dauki wani dutse na rufe gurin da sauri na bar gurin kai tsaye gurin karatu na nufa karatu sosai akayi an gabatar da wasu darrusan bana nan haka nayi hakuri na zauna na samu abinda na samu. 'Karfe d'aya da rabi mun fito kowa sai shiga gurinsu yake ni kuwa Lahira na bawa jakar littatafai na nace ta'aje min a gurinta, kai tsaye sashensa na nufa domin gabatar da aikina. Samun sa nayi a falo yana d'acin rai! dan tunda na kalli fuskarsa jikina yay sanyi, gaishe shi nayi ya watsar da gaisuwa cikin 'bacin rai yace."Wato maganar da nayi miki bata gamsar dake ba sai da kikaje kika had'a ni da mahaifiyata ko."? Da sauri na sunkuyar da kaina nace"Ban fad'awa mahaifiyarka maganar da wata manufa sai dan ganin yana da kyau ta san lamarin domin ta binkici a'ina kake cin abinci." "Ni yaro k'arami ne da zakiyi min wannan maganar."? girgiza kaina nayi, 'kwafa yay da fad'in " Tun ranar da kikayi min wannan 'bakin abun nake 'kyank'yamin ki da dukkanin abinda zai fito daga hannunki, kece wahalalliya kiyi ta girki kina zubarwa ba zanci ba kuma wallahi kika kuskura kika sake zuwa kika fad'a mahaifiyata wata magana sai nayi miki mugun abu.'' Na jima ina kallonsa kallon da banta'ba yi masa ba, gabad'aya mamakinsa ne ya rufe ni ashe abin arziki yana zama tsiya to wane mugun abu zaiyi mata........"Ki wace ki bani guri kullum kina cikin tufafi d'aya sai kace jaka." Na sake kallonsa zuciyata sai zafi take kamar na mayar masa da martani sai dai na daurewa zuciyata da sauri na bar gurin, kicin na nufa, koda na shiga kicin din kasa aikata komai nayi na tsaya jikin drowars ina sa'ke-sa'ke! yanzu dai koda nayi masa abincin baci zaiyi ba tunda ya fad'a min to ina ganin idan nayi abincin na ajiye tamkar nayi albazazzaranci ne. wata dubara ce ta fad'o min ina ganin itace mafita a gareni. Zama nayi kan wata kujera ta mussaman wacce aka tanade ta domin hutawa, sai da na dauki kimanin mintuna ar'ba'in kana na mi'ke na dauko tire din da nake jera masa abincin sabbi fulas na jera a kai na fita daga kicin din hannuna rike da tiren kai tsaye gurin cin abincin na nufa, na jera tsaf tamkar da abincin a ciki. Da sauri na baro gurin nesa dashi na tsuguna nace"Yallabai na kammala." ko kallona beyi ba ballanatana ya amsa min, miqewa nayi da fadin" A tashi lafiya'' da sauri na nufi kofar fita. Kallo ya bita dashi yana sauke wata zazzafar ajiyar zuciya, akan idonsa ta fita daga falon, ya tsirawa fuskar wayarsa ido ta nayi masa gizonta a idonsa......Ya'ki yay da zuciyarsa ya miqe ya nufi danning din domin ganin abinda ta girka, dan yayi wa mahaifiyarsa al'kawari akan ya daina cin abincin waje sai na yarinyar tunda da ita ta amince masa, A kwanakin da suka gabata yana aika Haruna restaurant yay masa take a way da safe kuma ruwan tea kawai yake sha da biscuits...... Zama yay kan kujerar daning din a nutse ya fara kici-kicin bud'e fulas din, yana budewa yaga wayam babu komai. da sauri yasa hannunsa kan d'ayan tunkafin ya bud'e ya nuna masa da babu komai a ciki.......Cike da takaici ya daga fulas din yana duba cikinsa tamkar me neman wani abu. Lallai ashe yarinyar bata da mutunci ashe bata girka komai ba amma tazo ta jera fulas a daning sai kace wacce tayi abin arzi'ki! sosai ya shiga mamaki abunda tayi, kafin kuma al'amarin ya shiga bashi dariya. Ya dinga dariya shi kad'ai ya mi'ke ya nufi 'kofa da niyyar fita Haruna zai kira yazo ya samo masa abinda zaici dan yunwa yake ji. Moddibo ne ya shigo falon a lokacin da yake daf da fita, tsayawa yay yana murmushi, shima Muddibon murmushi yay masa ya bashi hannu suka gaisa da juna. A nutse yace."Ina zuwa na ganka cikin manyan kaya ina Shatima yake.''? Muddibo yace." Shatima na gurin aiki ni kuma zanje gurin bikin birthday din wani friend d'ina shine na keso muje tare ko babu komai kaga gari na lura tunda ka dawo kullum kana gida baka san zuwa ko'ina.'' Sajensa ya shafa a nutse yace."Okey jira ni nayi wanka na kimtsa jikina dama yanzu yanzu nake tunanin kiran Haruna ya samo min abinda zanci babu damuwa yanzu idan mun fita sai mu tsaya a gurin cin abincin." Muddibo yace."Okey to babu damuwa muje ka kimtsa a nutse sai mu fita." Sai suka nufi saman a tare suna maganganun da suka shafe su...... *BINTA UMAR ABBALE* *Please kuyi sharing👏🏻* 2/11/21, 8:19 AM - ???: *'KWARYA TABI 'KWARYA* *NA* _BINTA UMAR ABBALE🍒_ *bintaumarabbale@gmail.com* *MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION📘🖊?* _'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_ _________________________ *Littafin na kudi ne....!* _#300.....0542382124...Binta Umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai ki same ni ta wannan numbers..08089965176 _07084653262 Zanyi miki bayanin yanda zaki turo katin.......... Ga masu bukatar VIP Group 600 ne_ _Mutanan Nijar zaku tura dala dari ta wannan numbers katin airtal ko orange VIP jakka d'aya 90899076_88137740_ *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 37&38 Shigar 'kananun kaya yayi a jikinsa kasancewar ana d'an busa sanyi yasa ya d'ora jacket wacce ta sauko har gwiwarsa hular sanyi yasa ya sunkufe kanshi, ya sakaye idanunsa da bakin galishi, Moddibo sai tsokanarsa yake yana kiransa da bakin bature wai idan ba wanda yayi masa farin sani ba babu wanda zai ce ya had'a jinsi da bakar fata, murmushi kawai yake bai tanka masa ba, suka sauko a tare suna hira Moddibo farin ciki fal a zuciyarsa yana addua Allah yasa bukatarsa ta biya a kansa. Su Haruna na ganin fitowarsu suka mike suna mika gaisuwa, ya tsaya yana magana dasu shi kuma Moddibo parking area ya nufa direba ya mike tsaye da sauri ya karaso gurin, Moddibo key ya kar'ba daga hannun Direban ya bashi umarnin tafiya....a nutse ya karaso gurin yana kallon Moddibon dake zaune a cikin motar yana sa mata key yace."Meye Amfanin direba za kayi draving da kanka. Moddibo na murmushi yace."Yau d'aya naji ina sha'awar tuqa mota da kaina shigo kawai mu tafi." Jim yay na minti biyu ya kama murfin motar zai bud'e, da sauri Yakubu direba ya bude masa ya shiga ya mayar da murfin ya rufe da fadin"A sauka lafiya ranka ya dade." Hannu kawai ya daga masa Moddibo yaja motar suka bar gurin. Hira suke sosai a tsakaninsu Yarima Ali ya saki jikinsa da Moddibo yana ganin dan uwansa ne dake kaunarsa ba zai ta'ba cutar dashi ba, yayin dashi kuma Muddibon ke Allah Allah su isa gurin birthday din ya cimma manufarsa a kansa, Yanayin Moddibo bai nuna cuta da zalinci ba sosai ya saki fuskarsa sai fara'a yake yana nunawa d'an uwan nashi kauna da kulawa, Magajin sarki ya sake sakin jikinsa dashi yana ganin ba zai ta'ba cutar dashi ba. Gurin birthday din ya cika da samari da 'yan mata 'ya'yan manya masu kudi duk wanda ya hallaci gurin birthday diin Nura promise to d'an gayu ne kuma ubanshi mai kudi ne kuma mai mu'kami ne Guri na mussaman aka tanadar musu suka zaune a killace Magajin sarki sai sake tamke fuskarsa yake ganin yanda idanun 'yan mata yayi caaa a kansa, gaskiya yayi dakacan zuwa gurin a rayuwarsa ya tsani kallo mussaman daga gurin mace...........Cikin k'ayatarwa Nura ya yanka cake kafin a shiga rabon kayan ciye ciye. A nutse ta k'araso gurin da suke zaune hannunta dauke da tire da yake cike da kayan ci da sha, ajiyewa tayi kan tevur din dake gabansu ta zauna kusa da Moddibo suka gaisa tana satar kallon Yarima Ali wanda shi kuma tun zamanta a gurin yayi kici kici da fuska. "Moddibo ganinku yayi wuya tun bayan kammala karatunmu kowa ya watse ko a waya bama gaisawa yanzu dai kafin taro ya watse inaso ka bani number wayarka. Muddibo yace." Wallahi kam Latifa al'amura ne sukayi yawa ina fatan kina lafiya ya mutan gida." Da murmushi a fuskarta ta amsa kafin tace"Wannan d'an uwanka ne naga kuna yanayin kama da juna." Muddibo murmushi yay ya kalli gefan da yake zaune yace."Kingdom kenan Magajin sarki kenan shi muke sa ran ya gaji sarautarmu." Latifa zare ido tayi tana kallonsa tace"Ashe masu 'kasar ne a gabana Yallabai barka da wannan lokacin." tafad'a tana kallonsa, Ba tare da ya kalleta ba ya amsa ya mayar da hankalinsa gurin Moddibo da fadin"Yana da kyau mu tafi kamar yanda na fad'a maka inaso na samu abinda zanci.. Moddibo yace."Okey me zai hana kaci abincin gashi nan Latifa ta ajiye mana ina ganin ba sai munje restaurant ba.'' tevur din ya kalla ya dauke kansa daga gurin, yana da kyankyami ba kowane abincin yake iya ci ba. Latifa ce ta shiga bud'e mishi ledar da aka rufe abincin tana fadin "bisimillah ranka ya dad'e." Ya sake kallon abincin a karo na biyu...Shinkafa ce akayi mata wata irin dahuwa sai kayi da gaske sannan zaka gane shinkafa ce taji kayan lambu da nama sai kamshi take daya plate din kuma gasheshshen nama ne da akayi mishi had'i da ganyayyaki sai manyan lemuka masu sanyi......A nutse yasa hannu kan cokalin ya d'ebo abincin yasa a bakinsa, yana taunawa yaji tes din abincin be masa ba daurewa yay yaci cokali uku ya ajiye tare da goge bakinsa da tissue. Moddibo yace.''Ya naga ka ajiye cokalin." Girgiza kansa yay yana ya mutsa fuska "Alhamdullhi wannan da naci ya isa." Moddibo na dariya yace."Ashe ba yunwa kake ji ba dama." Ta'be bakinsa yayi yace."Ina jin yunwa sosai dan rabona da wani abincin kirki tun jiya da daddare kawai tes din abincin ne beyi min ba." Muddibo murmushi yay a cikin zuciyarsa yace."Ai tunda dai kaci magana ta 'kare. A zahiri kuwa cewa yay ."Okey bari ni na gwada na gani ko zan iya ci." Shiru yay yana kallonsa. Moddibo a maimakon yaci na plate din dake gabansa sai ya janyo sabon plate ya bude ya fara ci a nutse....Lokacin Latifa ta jima da barin gurin..Moddibo abinci yake ci yana satar kallonsa ta kasan idonsa. Yana zaune yaji kansa na juyawa amai na taso masa, daurewa ya dinga yi yana danne aman sabida jama'ar dake gurin, Moddibo ya kalleshi hade da fadin"Ya dai dan uwa naga sai ya mutsa fuska kake.'' Hannu yasa cikin Aljihu ya dauko hankici ya tsane gumin goshinsa a kasalance yace."Wallahi kaga ina zaune kawai nake jin jiri ga wani amai na taso min. Cikin kulawa ya ajiye cokalin hannunsa da fadin"Subahanallahi kodai abincin da kaci ne ya janyo maka hakan." Cikin damuwa yace.Mybe shine amma nafi tunanin yunwar dana tara ce ta janyo hakan kai dai yi sauri ka gama mu tafi gida dan na soma ganin dishi dishi a cikin idanuwana. Moddibo ya mike tsaye da sauri da fadin"Ina zan ga nutsuwar cin abinci bari na kira Nura yazo ku gaisa mu wuce kawai.'' yana gama maganarsa ya kusa cikin mutane domin kiran abokin nasa. Tare suka dawo gurin da Nura, Magajin Sarki ya danne abinda ke damunsa suka gaisa da Nura yay masa fatan alkairi sosai kana ya mi'ke gaba yay ya barsu suna magana. Cikin mota Muddibo ya sameshi yay gaggawar bude motar ya shiga ya zauna kunnar motar yay hankalinsa a kansa yace.''Kodai mu tsaya a hospital ne dan naga kana jin jiki sosai." Girgiza kansa yay yace."Muje gida kawai a yanzu babu abinda nake so sai kwanciya daga baya sai a kira Family doctor ya duba ni." Moddibo yaja motar da fadin"To Allah ya sawwake. "Ameeen yace yana rintse idanunsa.......sosai Muddibo ke sharara gudu kan kwalta ya kalleshi da fadin" Muddibo tafi a hankali mana." Muddubo yace."Ina sauri ne mu isa gida ka kwanta ka huta gabadaya Hankalina ya tashi wallahi bana k'aunar ganinka cikin damuwa. Murmushi yay yana kallonsa yana sake jin kaunarsa a cikin ransa yace."Nagode sosai dan uwa amma kayi tu'ki a nutse zamu kai gida da yardar Allah" Muddibo murmushi yay yace."Insha Allah." Rage gudun motar yay motar ta cigaba da tafiya a nutse.....ajiyar zuciya ya sauke ya rintse idanunsa yana jin yanda wani irin mahaukacin amai yake taso masa kansa sai juyawa yake tsigar jikinsa na tashi, sake rintse idonsa yay yana kiran sunan Allah................"Innalilihi wa'ina ilaihi raji'un."!!! kalmar daya ji Muddibo ya furta kenan da sauri ya bud'e idonsa da yake gani dishi-dishi dasu, gani yay motar ta 'kwace daga hannun Muddibo sun nausa cikin bishiyu motar sai tangal-tangal takeyi tana dukan duwatsu da manya manya bishiyu. kafin yay wani yunkuri yaga Muddibo yay fittt! ya fice a motar murfin ya koma ya rufe gam! Kansa na juyawa yana kiran sunan Allah yasa hannu kan sitiyarin motar yana kokarin tsayar da ita ai kamar kara ingizata yake motar ta sake nausawa cikin gurin, sai kawai ya shiga kalmar shahada yana ganin kamar lokacin sa ne yayi. Muddibo mi'kewa yay da sauri ya shiga karkade jikinsa gabadaya bai damu da daddaujewar da yayi ba shi dai tunda Mota ta nausa da Ma'kiyansa cikin daji shikkenan ajiyar zuciya ya sauke yasan ko shakka ba yayi dole yau yayi kwanan barzahu......Wayarsa ya dauko cikin aljihu cikin tashin hankali ya shedawa Waziri abinda ke faruwa.... Gabad'aya masarautar hargitsewa tayi masu koke-koke nayi masu salati nayi, masoyan Yarima Ali irina mune muke cikin tsananin tashin hankali dan ni dana samu labarin al'amarin sai da na d'auki buta na zagaya band'aki(Ummu Siyama kince wai me yasa ba'a sa star din littafi tana kashi😂 to gashinan Sumayya ta zaga bayan gida cikinta ya karta lol) 'Bangaran iyayensa kuwa gabad'aya Maimartaba rikicewa yay ya dinga salati yana neman fad'uwa, Fulani har ta fishi dauriya da tawakkali dan labarin abinda ya faru yana riskarta "Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un! ta ambata dalilin da yansa kenan ta samu kwarin gwiwar tausar mijin nata. Gabadaya maimartaba jikinsa saki yay ya zauna kan kujera zufa na karyo masa, a yanda Muddibo ya sheda musu yanda accident din ya kasance basa tsammanin zasu sameshi da rai........Waziri Galadima da Ciroma tare da fadawa suka shiga mota domin riskar gurin da accident din ya afku. Fulani kuwa kad'aita kanta tayi da Ubangijinta tana kuka tana yi wa yaron nata adduar samun rahamar ubangiji dan gabad'ayansu sun fitar da rai a kansa suna ganin gawarsa kawai za'a kawo cikin gidan. Bangaran Uwargida kuwa tamkar ta zuba ruwa a kasa tasha saboda dadi dan bayan Muddibo ya shedawa Waziri faruwar al'amarin ita ya kira ya tabbatar mata da cewa aiki yay kyau Magajin sarki sai dai wani kuma dan yana da tabbacin wannan ya she'ka barzahu." Murna da farin ciki kamar ya kasheta. a take ta dinga kiran yaranta tana fada masu abinda ya faru, tace dukkaninsu suzo gidan suna kuka gami da nuna alhininsu amma Allah ne kadai yasan abinda ke zuciyoyinsu. aikuwa hakane ya kasance kowacce da kuka take shigowa gidan harda masu fadin" Magajin Sarki Allah ya jikanka muna murna ka dawo gida xamu zauna da kai ashe ba zaka dade tare damu ba zaka koma ga mahallincin ka, wayyo Allah mutuwa Kinyi mana yank'an kauna......Abinda wasu daga cikinsu ke fada kenan suna kuka da fyatar majina...... *BINTA UMAR ABBALE* *Please kuyi sharing👏🏻* 2/11/21, 8:19 AM - ???: *'KWARYA TABI 'KWARYA* *NA* _BINTA UMAR ABBALE🍒_ *bintaumarabbale@gmail.com* *MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION📘🖊?* _'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_ _________________________ *Littafin na kudi ne....!* _#300.....0542382124...Binta Umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai ki same ni ta wannan numbers..08089965176 _07084653262 Zanyi miki bayanin yanda zaki turo katin.......... Ga masu bukatar VIP Group 600 ne_ _Mutanan Nijar zaku tura dala dari ta wannan numbers katin airtal ko orange VIP jakka d'aya 90899076_88137740_ *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) *LAST FREE PEGE🥰* wannan pege din shine 'karshe 'yar uwa kina so ki karanta littafi ki nishad'antu ki fad'akantu amma kuma kike ganin kyashin biyan #300 akan abinda za'ayi tsayin wata biyu ko uku ana baki kina farin ciki kina dariya, dan Allah mu dai nayi wa junanmu ganin ido wallahi rubutun nan akwai wuya meye #300 ko #600 dan kin biya marubuciya kin karanta labarinta, idan kina bukatar ki biya kudinki sai ki duba bayanai na na sama, kada ki zauna sai an sato kin ganshi a gruops ki karanta akwai 'karanta a ciki da zubar da aji kina karanta littafin da akayi doka akai ke kanki ba zakiji dadin hakan ba #300 ko #600 ta biya miki bukata🥰 masoya na asali sai na ganku😇 39&40 Kiran sunan Allah kawai yake yana kici kici da sitiyarin motar duk a kokarinsa naganin ya tsayar da motar, inaa! motar tuni ta k'wace ita nausawa kawai take cikin sa'ko gami da kwazazzabai tana cin tuntu'be da duwarwatsu gami da manya manyan bishiyun da suke gurin, da sauri ya dauke hannunsa daga kan sitiyarin motar ya fara kici kicin bude motar lokacin wuta har ta soma tashi, motar tayi duhu da haya'ki! tari mai karfi ne ya sar'ke masa shi da sauri ya dafe kirjinsa yana salati.....Motar ce ta daki wata rusheshiyar bishiyar kuka a take ta wuntsila zata kifa cikin ikon Allah ya wuntsilo can gefe ya fad'i kansa ya bugu da wani k'aton dutsan wuta dake dashe a gurin.........Kirjinsa ya rike yana janyo numfashi gami da kiran sunan Allah numfashin sa ne ya dauke jikinsa ya saki ya fadi a gurin jini duk ya wanke masa fuska da rigar jikinsa. 'Karasowar su gurin yayi daidai da tashin wuta motar ta dinga ci da wuta wani irin haya'ki na tashi. a gigice Muddibo ya durfafi gurin yana ihu! gami da kiran sunansa "Magaji sarki?"!!! gurin sai da ya amsa sabida yanda yake wani irin ihu! yana fizgewa dole sai yaje gurin. Waziri hawaye ya shiga sharewa yana ta ambaton Allah a cikin zuciyarsa, Galadima da Ciroma kuwa Allah ne kadai yasan abinda ke zuciyoyinsu a zahiri dai idan ka kalli fuskarsu zaka ga alamun tashin hankali da damuwa amma mugun dadi da farin ciki sukaji a cikin ransu bukatarsu ta biya wanda suka tsana ya bar duniya. Jami'an tsaro ne suka iso gurin Tare da Shatima da labari ya sameshi yana gurin aiki kuka sosai yake yi daya iso gurin yaga yanda wuta taci ta cinye motar ko kyallin Dan uwan nasa ba'a gani Shatima shine ya kewa Magajin sarki kauna ta gaskiya shiyasa ya shiga mugun tashin hankali da ya samu labarin faruwar al'amarin..Durkushewa yayi a gurin ya rufe fuskarsa da tafukan hannayensa yana kuka hade da nemawa dan uwan nasa gafara. Jami'an tsaron ne Suka durfafi gurin suna haska fitilar su, Shatima mi'kewa yay yabi bayansu shima Muddibon sai ya mike da sauri yabi bayansu, Shatima wayarsa ya kunna yana goge hawaye yana dube dube a gurin. A tsanake jami'an tsaron suka binkita cikin motar dake tashin hayaki kad'an kad'an duk ko ina sun duba basu ga wani abu da ya dangace shi ba, misali koda wutar ta cinyeshi ai bazu rasa ganin koda agogonsa ba hakan zai tabbatar musu da zarginsu. Babban cikinsu ya kalli Muddibo dake haske haske a gurin yace."Bana tsammanin fa wutar ta tashi da Yarima a motar nan dan ba muga wani abu wanda zai tabbatar mana da zarginmu ba." Moddibo gabansa ya fad'i! da sauri yace."Ku dai kara dubawa yanda wutar nan ta tashi bana tsammanin zata bar wani abu daya dangance shi amma ku tsananta binkice a gurin sosai." Yana maganar yana laluben gurin gumi ne kawai ke tsiyaya a jikinsa, shima ya soma shan jinin jikinsa dan ko alama bai ga wani sashe na jikinsa a gurin ba da wuta ta 'kona shi to da tuni sunga sassan jikinsa a wani gurin. Binkice sosai sukayi a gurin ba suga komai ba Muddibo ya dinga share zufa yana mamakin al'amarin to ya akayi haka ta faru! ina Magajin sarki ya shiga da wuta bata 'kone shi ba. A sanyaye jami'an tsaro suka shedawa su Waziri abinda ke faruwa.....Waziri ya sauke ajiyar zuciya yana godewa Allah yace."Ko shakka ba nayi jikina na bani yaron nan yana raye dan da wuta ta cinyeshi to da anga sheda saboda haka gurin dai za a tsananta dubawa watakila ko ya gangara wani gurin ne. Galadima da Ciroma kasa magana sukayi murnarsu gabad'aya ta koma cikinsu sai muzurai suke gurin gabadaya zuciyoyinsu babu kyakkyawan abu... Shatima cikin gurin ya dinga kutsawa yana haska wayarsa yaji yaci tuntu'be da wani abu da sauri ya Haska gurin, ganinsa a kwance a gurin yasa ya razana wayar ta fadi da sauri ya dauka ya tsuguna a gurin yana tatta'ba jikinsa jinin dake fita daga saman kansa shine ya tsorata shi, hannu ya dora a kirjinsa nan yaji yana harbawa akwai alamun rai a jikinsa, da sauri ya cire rigar jikinsa ya shiga tsane masa jinin ganin kamar wahalar da kansa yake yasa da sauri ya mike ya fita daga gurin yana waiwayensa......Kicibus sukayi da jami'an tsaron suna sake dubawa ......a sarqe yace musu kuzo gashi can bakin gangare da alama akwai sauran rai a tare dashi." Hankali a tashe suka durfafi gurin suna godewa Allah Yanda aka fito da Magajin sarki daga gurin zaku dauka ya dad'e da mutuwa dan gabad'aya jikinsa ya sandare ya saki wani police ne ya d'aukoshi daukar jarirai suka fito dashi .......Muddibo tun daga nesa da ya hangosu jinin jikinsa ya tsinke jiki na kyarma ya iskesu yana haska fuskar sa da wayar hannunsa baki na rawa ya kalli Shatima yace."A ina aka ganshi anya ma kuwa da akwai rai a jikinsa."!? a kid'ime yake maganar kana ganinsa zaka gane a cikin rud'u yake. Shatima yace."Can karkashin wani k'aton dutse na ganshi a sume goshinsa na zubar da jini akwai alamar rai a tare dashi." Muddibo hular kansa ya cire cikin tsantsar tashin hankali ya shiga firfita da ita. Shatima ya shiga mamaki mai tsanani ganin yanda Muddibon ya rud'e sai fadi yake ."Wannan da alama ya jima da mutuwa Shatima duba fa ka gani yanda jikinsa ya sandare.....Dansandan dake dauke da Magajin sarkin a hannunsa yace."Akwai rai a jikinsa kawai taimakon gaggawa za'ayi masa." Muddibo shuru yay da bakinsa dan baya so ya sake wata maganar su zarge shi da wani abun. Kai tsaye babban asibiti suka nufa dashi, Waziri da Shatima ne kawai ke masa fatan samun lafiya Ciroma da Muddibo Galadima fatan mutuwa kawai suke masa.........Kai tsaye emagancy aka nufa dashi manya manya likitoci suka rufu a kansa domin ceto ransa.......Waziri ne ya umarci Shatima ya sanarwa da Maimartaba halin da ake ciki, koda Maimartaba ya samu labarin cewa yaronsa na raye sujjada yayi a gurin ya godewa Allah, a lokacin ya shirya tafiya asibitin domin duba yaron nasa, Fulani kuwa kawaici ta nuna ta zauna a gida tana addua gami da godewa Allah, Bangaran Uwargida kuwa da suka samu labarin abinda ke da akwai sai murnarsu ta koma ciki suka dinga 'kunci suna zage zage da kyar suka iya danne 'bacin ransu suka shiga mota suka nufi asibitin suna shirya wata mana'kisar. Ni kaina dana samu labarin cewar yana raye bai mutu ba sai da nayi sallah raka biyu na godewa Allah sannan kafin na tashi sai da nayi masa addua da fatan samun lafiya ingantacciya. Sai bayan kwana biyu Ya farfado yasan wanda yake kansa babu wanda ya fara kira sai Muddibo hawaye suka sakko masa a kumatu. Maimartaba yace maza aje a kira Muddibo yazo ya ganshi yana daina zargin ya mutu....Muddibo na shigowa dakin ya sauke ajiyar zuciya, tsirawa juna ido sukayi, kawai sai Muddibo ya fashe da kuka tare da riqe hannunsa yace."Sannu Yarima ashe tsautsayi da qaddara ne ya fitar damu naji dadi da Allah ya taikaita mana wahala ina kuma rokon Allah ya tsaremu da sharrin karfe.'' Kamar wani mutumin arziki yakare maganar. Rintse hannun Muddibon yayi a cikin nasa yana so yayi magana amma bakinsa yayi masa nauyi wani irin sarawa kansa yake ga wata irin ishirwa na damunsa da kyar ya iya furta maganar dake bakinsa. "Bani ruwa." Muddibo yayi saurin daukar goran ruwa dake kan drowar ya bude masa zai sa masa a baki ya kar'ba ya sha da kansa, kadan ya rage ya mika masa goran ruwan kana ya shiga bin dakin da kallo. iyayensa ya gani ya tsaitsaye sai yaji zuciyarsa ta karye, ya kamo hannun Waziri ya rike da kyau yace."Baba ku kwantar da hankalinku insha Allah zan samu lafiya." Waziri ya tsira masa ido babu abinda ke tayar masa da hankali sai kat'on bandejin dake nad'e a kansa gabadaya hallitar fuskarsa ta sauya ko'ina a kumbure dalilin daya sa ma kenan Maimartaba ya kasa tsayuwa a dakin ganin hallitun yaron nasa sun sauya yasa ya fita daga dakin hankali a tashe. Kwana biyar da faruwar al'amarin na samu su Haruna domin mu tattauna yana da kyau muje asibitin mu duba jikinsa dan gabad'aya tunda al'amarin ya faru na rasa gane kaina kullum da damuwa nake kwana ina ganin kamar idan na wayi gari za'a zo a fadi mutuwarsa. Haruna yace."Shawara tayi sai mu bari da daddare bayan munyi sallar isha'i sai muje muga yanayin jikin nasa." Nace"To shikkenan tare ma zamuje da babana shima yana so ya duba shi." Haruna yace." To babu damuwa. Ina k'okarin shiga 'kofar dawakai Jakadiyar Fulani ta dakatar dani, gaisawa mukayi da juna kafin ta isar da sak'on ta, nace"Fulani na nema na." Karyar da kaina nayi nace"Dan Allah ta tsaya na zubawa dawakai abinci sai mu tafi tare." Da yake tana da saukin kai tace" Muje na taya ki." Tare muka shiga gurin, Hira muke sama-sama nake tambayar ta yanayin jikin Yariman sabida nasan ita ba zata rasa sanin abinda ke zuwa ya dawo ba, tace"Jikinsa da sauki wallahi kullum ana ganin cigaba amma zamansa a asibitin nan akwai hadari dan kullum 'yan uwansa mata cikin zurga zurga suke wai sunje dubashi gabadaya babu tsoron Allah a ransu zasu iya cutar dashi saboda irin kiyayyar da suke masa. Cikin mamaki nake kallonta nace"Yan uwansa na jini su cutar dashi me yayi musu mai zafi wai shin ma nawa duniyar take." ? Jakadiya tayi murmushi mai ciwo tace"Yarinya ni nasan abinda baki sani ba a masarautar nan babu wanda ke kaunar dan uwansa dukkaninsu kisan mummu'ke sukewa junansu kowa na samun dama akan dan uwansa cutarsa zaiyi wannan al'amarin ma da ya faru da Yarima muna zargin dasa hannun ma'kiya kin san gabad'aya kowa ya daura masa kiyayya da kyashi da hassada saboda suna ganin kamar shine zai gaji kujerar mahaifinsa. Na jima ina mamakin maganar kafin na girgiza kaina nace"Jakadiya mutane idan suna wani abu wallahi har mamaki suke bani mutum fa bai ta'ba tsarawa kansa abinda yake so ba face wanda Allah ya tsara masa nasan ba'a kan komai suke wannan abunba akan mulki ne a ganina sai su bari suga abinda Allah zai zartar ba wai su dinga cutar dashi ba watakila ma bashi ne zai hau kujerar ba wani ne babu fa wanda ya san gaibu sai Allah." Muna kokarin fita daga gurin Jakadiya tace"Ke da kika san Allah kenan amma su ina mai tabbatar miki da cewar basu san Allah ba, dan da sun sanshi ba zasu dinga aikata munanan ayyuka ba." Ajiyar zuciya na sauke nace"Allah ya kyauta Allah kuma shiryemu baki d'aya." Ta amsa Ameeen ya Allah." Cikin nutsuwa na gaisheta tare dayi mata jaje akan abinda ya faru. Amsawa tayi kafin ta gyara zamanta tana kallona tare da kiran sunana. Na amsa ina kallonta, tace"Ina fata baki mance akinki ba ko."? Nace."Eh ranki ya dad'e." Tace."To Alhamdullhi ina so kije asibiti ki zauna da babana ki cigaba da kula dashi kamar yanda kike kula dashi a gida." Nace"Dama yau muka yanke shawarar zuwa duba shi nida su Haruna'' Tace"To babu damuwa suma suna iya zama asibitin ku hadu ku kula dashi har randa za'a sallamoshi ya dawo gida, alhmdullhi kullum jikin nasa 'kara sauki yake. Shuru nayi ina tunani maganarta tace"Nasan kina tunanin gurin kwanciya ko.''? nace"Eh ranki ya dade." Tace"Kada ki damu babban asibiti ne akwai dakunan da zaku kwanta ku sake babu damuwa ki tafi da 'yan kayan sawarki bana tsammanin ma zakuyi sati daya da zuwa ba'a bashi sallama ba tunda jikin nasa ya soma warwarewa." ajiyar zuciya na sauke da fadin"To babu damuwa ranki ya dade bari naje na shirya kayana." Ta amsa min da to shikkenan. Har na kai kofa ta dakatar dani juyowa nayi ina kallonta tace"Ki kula da kyau ba kowane irin abinci zaki bari yaci ba." ko ba tayi min bayani ba na gane inda ta dosa sannan kafin shigowata gurinta mun tattauna maganar da Jakadiyarta. Lokacin da zamu tafi asibitin iyayena fatan alkairi sukayi min, na sake jin kwarin gwiwa ganin yanda babana yake kuzari jinin jikinsa ya dawo yanzu bashi da matsalar komai yana fita yayi sabgoginsa hankalinsa a kwance to wannan dalilin yasa naji bana fargabar tafiya asibitin. Lokacin da muka shiga dakin yana zaune kan gado da tufa (apple) a hannunsa yana ci Gimbiya Lawisa na gefansa suna magana kan kujera kuma daya daga cikin yayyunsa ne wacce bata dade da zuwa ba, ta kawo masa abinci cikin kwando wai lallai sai yaci a gabanta sannan zata tafi. A nutse nabi su daya bayan daya na gaishe su sannam muka karasa gadon da yake zaune....Haruna ne ya fara magana "Ranka ya dade barka da dare ya jiki munayi maka fatan alkairi ubangiji Allah ya tsare gabanka da bayanka." A nutse ya amsa fuskarsa tana nuna alamun yaji dadi da zuwan mu Isa da Hamza suka gaishe shi dayi masa ya jiki nima a nutse na mika gaisuwata ya amsa cikin sakin fuska harda godiya." Fita mukayi daga dakin muka zauna a reception muna hira....Kimanin minti ashirin da zaman mu a gurin suka fito daga dakin. Aunty Sakina gaba tayi ita kuma Lawisa tsayawa tayi a kaina tana kallona tace"Ina fata kina gudanar da aikin dana saki."? Nace"Sosai kuwa ranki ya dad'e kullum ina yi har nake tunanin tambayarki ko kinga sauyi sai da na ganku a tare ke dashi kuna hira na tabbatar da cewa maganin yana aiki." Murmushi tayi tace"Har yanzu na kasa gane inda ya dosa akan soyayyata Ali mugun baud'addan mutum ne wanda ba'a gane gabansa da bayansa, amma tunda muna da zafafan malamai nasan zasuyi min maganinsa." Nace"Kwarai kuwa ranki ya dade." Tace'' Ki cigaba da gudanar da aikin ki bance ki d'aga kafa ba wai dan ganin bashi da lafiya karki saurara a cikin ko wane yanayi burina aikin da nake a kansa yayi tasiri." Nace"Kada ki damu ranki ya dade tafe nake da sinadaran da kika bani ko yanzu ya shirya cin abinci zanyi dubarar zuba masa. Murmushi tayi tare da fadin" Na fada miki idan aiki yay kyau zanyi miki kyauta ta mussaman saboda haka sai ki sake zage damtse." Ina murmushi nace "Nayi alkawari." Tana tafiyar takama ta bar Gurin, tsaki naja 'kasa-kasa nace''Dube ta dan Allah jahilar banza da wofi. Su Haruna na gani sun mike sun nufi dakin, ido na zubawa kofar ina sauraran fitowarsu basu dade a ciki ba suka fito Hamza ya kalleni da fad'in ''Ki shiga ki bashi abinci yana bukata.'' Mik'ewa nayi da sauri na nufi dakin Yana zaune a inda yake ganin shigowata yasa ya fara yunkurin sauka kasa. da sauri na janye kwandon abincin dake gaban gadon ya zuro kafafunsa a nutse ya mike tsaye bayansa nabi da kallo ganin ya nufi toilet yasa na sauke ajiyar zuciya. Ina tsaye a gurin ya fito muka hada ido, kaina na sunkuyar kasa ina jin faduwar gaba kada'n kad'an, idan na kalli fuskarsa sai naji zuciyata na karyewa nima yanzu na tabbatar da cewa yana da makiya gaba da baya dalilin daya sa kenan naji zan iya sadaukar da rayuwata a kansa tausayi yake bani. K'asan kafet ya zauna ba tare daya kalleni ba yace."Ki zuba min abinci nasha magani na kwanta bacci nakeji." Nace"to ranka ya dad'e." Kwandon abincin dake gabana na janyo na fara kokarin fito da fulas din dake ciki......Yace."Kada ki bude wannan dauko wancan na aunty Sakina shine nake bukata dan nayi mata al'kawarin cin abincinta." A nutse na mayar da fulas din hannuna na janye kwandon gefe na dauko wanda ya bukata. Cikin nutsuwa na fito da komai na kwandon na dauki plate mai dan zurfi na bude fulas din dake dauke da abincin. pride rice ce a ciki taji kayan lambu da nama amma kuma qamshin da take yasha bambam dana lafiyayyan abinci....Tsirawa cikin fulas din ido nayi ina duba abincin ciki. nan na hango taratsatsin magani a ciki dan wani gefan ma har ya rine da kalar maganin, kallonsa nayi gabana na fad'uwa yanzu ya za'ayi na fad'a masa abinda ke da akwai. Kallona yayi yana yamutsa fuska yace."Zaman me kike ne ke nake jira fa." murya na rawa nace"Ranka ya dade abincin ya lalace." Wani irin kallo ya watsa min da fadin"Kamar yaya ya lalace."? Nace"Eh duba ka gani wallahi ya lalace gashinan kamshin sa ya sanja." Tsaki yaja tare da fadin"Kinga bana son wata magana ki zuba min abinci naci koda tsutsa ke fita a cikinsa to tunda nayi alkawari sai na cika." shuru nayi ina sake sake a raina. "Wai ba zakiyi aikin dana saki ba." Cikin tsawa yay maganar.......Cikin jin tsoro nace"Wallahi abincin bashi da kyau ba zaka ci ba." Ya dinga kallonta yana mamakin maganarta, a fusace! yasa hannu zai Dauki fulas din abincin nayi gaggawar daukewa. bayana nasa fulas din ina kallonsa kwallah ta cika kwarmin idona. A murtuke yace."Ina wasa dake ko."? girgiza kaina nayi ina nufin aa. Yace."To zuba min abinci bani da lafiya bana son hayaniya." Hannu nasa na dauke kwallar data taru a idona nace"Sai dai na zuba maka wancan dan wannan da kake so kaci bashi da kyau." Yace."Wai cikin ki ko nawa ? ina ruwan ki idan naci lalataccan abinci cikina ne ba naki ba sannan nayi wa 'yar uwata al'kawari zanci abinda ta kawo min." Nace"Kayi hakuri ba zan iya baka kaci abinda zai cutar da kai ba dan kai amana ne a hannuna." Kallona yayi yana mamakin maganata, yace." Wai Saboda me bakya son naci abincin aunty Sakina ne."? bakina ne ya su'buce da fad'in "Saboda akwai guba a ciki." Gani nayi ya murtuke fuskarsa "me kike nufi? kina nufin anty Sakina zata cutar dani kome."? kai tsaye na daga kaina " Zata iya cutar da kai tun ba.......! kafin na karasa ya wanka min mari a kumatuna. cikin gigita nake kallonsa bakina na wani irin rawa so nake na fadi karshen maganar amma na kasa sakamakon marin daya waska min. kallon banzan da yake min yasa nayi gaggawar yin kasa da kaina. *BINTA UMAR ABBALE* *LAST FREE PEGE* Kada ki sake ayi wannan tafiyar babu ke 'Yar uwa kada ki saka ganin kyashi a kan abinda kike so ki kauda kanki ki biya #300 ki karanta littafin nan hankali kwance........Vip gruop#600 Normal gruop#300 idan kati zaki turo #400 ne. *PAID BOOK* NANA KHADIJA YARO DA KUDI GIMBIYA BALARABA BABBAN YARO MASHAHURI SADAUKI OMAR LADIDI KWADAGA TSANTSAR BUTULCI DA WATA A KASA NIDA YAYA SADAM YAR BANGAR SIYASA MADADI Kai tsaye zaki iya samun wa'innan littafan idan kin tuntu'bi wannan numbers *08089965176* *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 43&44 Yau dai nayi rantsuwar akan ba zan ta'ba jikinsa ba saboda na lura da gayya yake sani ina matsa masa sassan jikinsa da sunan tausa, na riga na gane ba manufarsa tausar ba burinsa kawai na dinga tatta'ba masa jiki yana sakin nishi da rungume fillo tun ina dau'ka abin nasa wasa har na tsargu da abunda yake a duk lokacin da nake masa tausar ya dinga juye juye a gadon yana matse fillo a kirjinsa idan yana ji da iskaci kuwa ya dinga danne min hannu kenan yana kwantowa jikina wannan dalilin yasa na gane ba tausar yake bu'kata ba. Kafin goma na dare tayi zurga-zurgar jama'a yayi sauk'i, kamar koda yaushe muka shiga dakin domin yi masa bankwana yana zaune ragal dashi tamkar ba wanda yake jinya ba har wata qiba yayi ya kara haske hakan baya rasa nasaba da irin kulawar da yake samu a gurina , ni na tabbatar da cewa daba dan na tsaya a kansa ba da tuni makiya sun kaishi k'asa amma baya ganin hakan kullum cikin yi min masifa yake yana hantara ta mussaman idan yazo cin abinci nasa ido ko kuma na nuna ga wanda nake so yaci shi kuma sai yace ba zai ci ba, wanda bana so yaci shi zai ci, haka zamuyi ta jayayya da juna har sai Dr ya shigo ya raba gardamar dake tsakaninmu, haka yake hakuri yaci za'bin da nake so. Su Haruna bayan sun masa sallama sun fita sai nima na kalleshi yana kokarin miqe kafa kan gadon nace"Nifa yau ba zan samu zaman tausar nan ba."? Ya kalleni da fadin "Dalili."? Kai tsaye nace" Saboda ba itace manufarka ba." Shuru yay yana kallon wayarsa, Nace"Sai da safe." kai tsaye kofar fita na durfafa ina addua a cikin raina. "Sumayya." Sunana naji ya kira tamkar a bakinsa aka rad'a sunan. tsayawa nayi ina kallonsa. gani nayi yana min sauk'akaken kallo cikin taushin murya yace."Zo muyi magana." Ganin alamar sassauci a tare dashi yasa na koma da baya Gefansa ya nuna min a hankali yace."Zauna." banyi musu ba na zauna ina kallonsa. hannuwana ya rike a nashi yana min wani irin kallo wanda yasa tsigar jikina tashi, risinar da idona nayi dan ba zan iya jurar hada ido dashi ba. "Kin same."? yafada a kasalance. Girgiza masa kai nayi nace" Sai ka fad'a." "Ina mutukar sha'awarki." Yafada yana bin ilahirin jikina da kallo. Gabana ne ya dinga faduwa ina kallonsa ina mamakin maganarsa yana sha'awa ta wace irin sha'awa yake min. Bakina na rawa nace"Ban gane maganar ka ba." Murmushi yay yasa hannu ya shafi gefan fuskarta da fad'in "Nasan dole zaki shiga mamaki da rud'ani in kikaji irin sha'awar da nake miki Sumayya komai na jikin ki yana burgeni yana k'yatar dani tun ranar dana d'ora ido a kanki na rasa gane kaina wallahi kinji rantsuwar musulmi kullum da sha'awarki nake kwana da ita nake tashi ki taimaka min ki bani kanki na mori albarkatun jikinki ni bance dole sai na shiga ramin ki ba wa'innan kawai nake so ki mallaka min." Yak'arashe maganar yana kokarin kai hannunsa kirjina........A zabure na bige hannusa na kalleshi ido cikin ido nace"Ina ce na fada maka ni ba 'yar iska bace ko."? Shuru yay yana kallona. Cikin k'unar zuciya nace"Wato abinda zaka sakamin dashi kenan na kwana na yini a bautarka amma kake nema ka lalata min rayuwata to bari kaji ni ba 'yar iska bace jikina kuma na mijina ne wanda yake kaunata saboda Allah ya kuma biya sadaki aka daura mana aure da juna, kayi hakuri idan maganar da nayi ta b'ata maka rai kuma insha Allah ba zan fad'awa kowa ba." cikin rawar murya nake maganar ina mamakin al'amarin. Kansa a kasa har na kare maganata ya kasa cewa uffan! haba ai dole yaji kunyar hada ido dani a ganina ban cancanci haka a gurinsa ba.......A sanyaye na zare hannuna dake cikin nashi na kama hanya na fita daga dakin, a daran kafin nayi bacci na jima ina mamakin al'amarin dama jikina na bani sha'awata yake shiyasa kullum yake k'ureni da ido amma ban ta'ba tsammanin zai iya yin gaba da gaba dani ya fad'amin yana sha'awata na mallaka masa kaina, wato ashe dama a turai abinda yake aikatawa kenan.? humm! gashi dai fuskar salihai gareshi ashe shima shaid'anin kansa ne, to kuwa tunda haka ta kasance tilas nayi takatsantsan dashi domin kada ya samu nasarar cutar da rayuwata. da wannan tunanin bacci ya daukeni mara dadi da mafarka marasa kyawu. Da safe tsaf muka sameshi kamar koda yaushe sai kamshin turare yake dakin ma haka, yana zaune a gefan gado suna magana da likita. Muna shigowa likita yace."Yawwa gatanan ma ta shigo idan kayi breakfast din sai kasa maganin insha Allah anjima zan shigo a kwance daurin dake kanka. "Okey." kawai yace ya dauke kansa, likita ya kalleni a nutse yace."Sumayya ga magungunan nan kan drowar ki bashi idan yayi break." Da sauri nace"Insha Allahu zan bashi. Dr fita yay daga dakin, su Haruna suka shiga gaishe shi ya amsa a dakile yana kokarin kwanciya, fita sukayi daga dakin A sanyaye nace"Yallabai barka da safiya ina fatan ka tashi lafiya." ? banza yayi min ya rufe idonsa, na dinga nazarin fuskarsa inaso nagano ainihin abinda yake damunsa, ba wani abu bane yake damunsa illah rashin samun had'in kanki dalilin da yasa kenan yake wannan fizge fizgen, zuciyata ce take min wannan maganar nace"Aikuwa idan hakane zai dad'e cikin kunci dan nayi rantsuwa da Allah babu wani namiji da zan mallakawa jikina sai mijina na sinna......."Ranka ya dade ka tashi kayi bre......."Fita a dakin nan."! Cikin tsawa ya fadi maganar har yana mikewa zaune." Dakewa nayi nace"Kayi hakuri dan Allah kayi break kasha magani kaji dai abinda dr yace ko."? da sauri ya sauko kwalayen maganin ya watso min a jikina. "Ki fita tun kafin na taso." Rai a 'bace! nace"Saboda ina kula lafiyarka kake min tsawa maganin nan fa kanka zaka shawa kake watsi dashi." Dirgowa yayi daga bed din ya durfafo ni yana huci! da sauri na bude kofar dakin na fita ina jin wani irin faduwar gaba, shin wai me yayi zafi ne? me mutumin yake so ya mayar dani! daga taimako sai sharri ya biyo baya. Jikin kofar na jingina ina mayar da numfashin fargaba gabadaya gwiwata tayi sanyi nayi masifar tsorata da al'amarin, sai da na samu nutsuwa tukkuna na samu guri na zauna tare da rafka ta gumi. Na kai minti talati a zaune kafin na yake shawarar sake shiga dakin...mikewa nayi a sanyaye da niyyar shiga dakin, Ya shigo gurin. sunkuyar da kaina nayi a nutse nace"Ranka ya dade barka da asubah." "Barka dai." kawai yace yasa hannu a jikin kofar ya bude ya shiga tare da mayar da kofar ya rufe. Shuru nayi ina tunanin waye a cikinsu sam bana gane su Shatima ne ko Muddibo kusan dai suna yanayin kama da junansu harshi Yarima tunda dukkaninsu farare ne masu tsayi. Komawa nayi na zauna ina jiransa ya fito daga dakin na shiga, ko minti uku banyi da zama ba ya fito yana duba agogon dake daure a hannunsa, ganin ya fito yasa na mike da sauri "Ranka ya dade ka sauka lafiya." Tsayawa yay yana min wani kallo kafin yace."Meye ma sunanki."? Nace"Sunana Sumayya Lawi." Yace."Okey na shiga na sameshi yana bacci idan ya tashi ki sheda masa zuwana akwai tufa (Apple) dana kawo masa inaso idan ya tashi a bacci ki bashi yaci kinji ko." Da sauri nace"Insha Allahu zan bashi." Hanyar fita ya kama ba tare da ya sake magana ba, dakin na shiga da sauri. yana kwance ruf da ciki ya matse fillo a kirjinsa, girgixa kaina nayi cikin zuciyata nace aikin kenan rungume fillo gaskiya yana da tsananin bukata daga ganinsa, yana da kyau ya gaggauta aure domin shine mafita a gareshi. A hankali na karasa shiga dakin,nasa hannu na dauki ledar tufar(apple) din kan kujera na zauna na shiga fito da ita guda shida ce manya manya ido na tsira mata ina nazari, gani nayi kaman huda a jikinta dan a yanda nasan apple bata da huje huje sumul take, a take na tsargu da ita nayi saurin mayar da ita ledarta na daure bakinta tamau! toilet na shiga na wanko hannuna na fito, maganin dake tarwatse a kasan dakin na kwashe tsaf na ajiyesu kan drowar dan tsayawa nayi ina kallonsa bacci yake sosai kuma daka gani yana jin dadinsa, ajiyar zuciya na sauke na dauki ledar apple din na bud'e dakin na fita. Can inda aka tanada domin zubar da shara na nufa, na samu wata sanda mai tsayi na tona sharar ledar apple din nasa a ciki na mayar da sharar na rufe, gurin na bari da sauri. Daf da zan shiga reception din na hango su Haruna gurin masu gadin asibitin suna hira cikin zuciyata nace"Wato dama nan suke zuwa su zauna girgiza kaina nayi na bar gurin Ina shiga Dr na fitowa daga wani daki, murmushi naga yayi min wanda ya ban mamaki yace."Sumayya ina fatan Yarima yasha maganin nasa."? shuru nayi ina tunanin abinda zance masa." "Yake kyakkyawa Ina magana kinyi mun shuru ki bani amsa mana." Maganarsa tasa na tsira masa ido ina mamaki! tunda nake babu wanda ta'ba kirana da kyakkyawa kowa muni na yake gani amma saboda cin mutunci na likita yake kirana da sunan mai kyau.........Dago kai nayi na kalleshi naga yana sakar min wani lafiyayyan murmushi, shan kunu nayi nace"Be sha maganin ba bacci mai nauyi ya dauke shi. "Ayya keda nace kiyi kokari ki bashi kafin ya kwanta alright bari na shiga yanzu na tashe shi yasa magananin." Dakin ya nufa da sauri nima na rifa masa baya. A zaune muka sameshi da waya a hannunsa, kallo guda yay mana ya watsar damu Dr na ya'ke ya karasa kusa dashi da fadin"Ranka ya dade garin ya yau ka kwanta ba kasha maganinka ba." A dan ya tsine yace."Bacci ne yaci karfina amma ina ganin babu damuwa yanzu idan naci abincin zansha." Dr kallona yake cikin tuhuma yace."Haba baby me yasa kike wasa da aikin ne? wannan fa shi muke sa rai ya zama Sarkinmu amma kina wasa da lafiyarsa." Nace"Dr ba laifina bane shine yace sai yay bacci ya tashi zaici wani abu." "Okey to tunda ya tashi yanzu dan Allah ki tsaya sosai ki tabbatar yaci ya koshi kin gane ko.''? da sauri nace" Eh na gane" Juyawa yay yana kallonsa yace."Yallabai ni zanje na duba marasa lafiya dan Allah ka daure kaci abinci sosai kasha magani." Yace."Okey kada ka damu." Dr fita yay daga dakin shi kuma ya mi'ke tsaye. had'a ido mukayi nayi gaggawar yin kasa da nawa. Yace."Wai baby sunan bai dace dake ba yarinya kinfi dacewa da *Gwamma* dubeta dan Allah da ba'ki kamar wani guri."! Cikin tsantsar takaici da bakin ciki na kalleshi ya watsa min harara mai zafi! hanyar toilet ya nufa yana jan tsaki! bin bayansa nayi da kallo zuciyata nayi min wani irin zafi..... *BINTA UMAR ABBALE* *Littafin na kudi ne* Koda zaki ganshi a gruops na sata ne idan kina so ki biya ga yanda abin yake Vip group #600 normal group #300 account 0542382124...Binta umar gtbank idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min magana ta whasap da wannan number *07084653262* 2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 41&42 Cikin wani irin yanayi wanda yake nuna tsantsan 'bacin ransa yace."Kina nufi auntyna zata sa min guba a abinci dan ta cutar dani, ashe har kin kai matsayin da zaki kalli tsabar idona ki fada min wannan maganar."!!! Hawaye ne ya wanke min fuska bakina na rawa nace"Kayi hakuri idan maganata ta bata maka rai ban yarda da nagartar abincin ba shiyasa nayi wannan maganar amma ni bana zargin auntynka da wani mugun abu, dukkanin abinda kaga nayi a kanka ina kokarin ganin na rike amanar da mahaifiyarka ta bani. A lalace yace."Wato ke har kin kai matsayin da za'a dauki amana ta a baki me kika sani a rayuwa." ? Ido cikin ido nace"Ni nasan abinda baka sani na ranka ya dade dan Allah ka bani goyon baya akan dukkanin abinda za kaga nayi a kanka wallahi ba zan cutar da kai ba." "Rufe min baki." Yafada yana watsa min harara, ya cigaba da cewa'' Daga yau sai yau kada wani dan uwana ya kawo min abu ki dora zargi a kansa bani da kamar su a duniya banyi imanin da cewa zasu cutar dani ba saboda haka babu abinda ya shafe ki da tsakanina dasu." Sunkuyar da kaina kasa nayi tsabar takaici ya hanani cewa komai...."Kina ji ko bakya ji."? Ba tare dana dago ba nace "To." "Zuba min abincin naci." Yafad'a yana tsatstsare ni da idonsa. 'Kin zuba masa nayi na sake 'boye fulas din a bayana gabana sai faduwa yake ina jin tsoron ya turmushe ni ya dauki abincin yaci.......Gani nayi ya dafe kansa yana girgizawa da sauri nayi yunkurin tashi da fulas din a hannuna ya wani finciko ni na fad'a kansa fulas din abincin yay nasa guri duk rabi ya zube a gurin. da sauri na mike daga jikinsa gabana na bugawa, ya dinga hararata murya na rawa " nace kaga ka zubar ko." Tsaki yaja mai karfi ya mi'ke gani nayi ya nufi inda d'aya kwandon abincin yake ya dauko guri ya samu ya zauna yana kokarin zuba abincin. Nufarsa nayi dan na zuba masa "Idan kika zo nan sai ranki ya 'baci ki fita ki bani guri bana bukatar ganin ki.'' A sanyaye na tsaya ina kallonsa yana kokarin bude fulas din. juyawa nayi na fita raina a bace na dauko tsintsiya da abin kwashe shara gyara gurun daya 'baci nayi na goge gurin tsaf, ina kokarin fita Dr ya shigo, a nutse na gaishe shi nasa kai na fita daga dakin zuciyata gabadaya babu dadi. Muna zaune a reception likita ya fito daga dakin cikinmu babu wanda yay gangancin shiga muna dai kallon yanda 'yan uwa da abokansu suke zuwa su shiga dakin domin dubashi.....goma da rabi jama'a sun tsagaita, Haruna ya kallemu da fadin" Yana da kyau muje mu dubashi idan akwai abinda yake bukata sai muyi masa muje mu kwanta." Gabad'ayan mu muka miqe muka nufi dakin....Yana kwance kan bed da waya a hannunsa muka gaishe bai tare daya kallemu ba ya amsa, Haruna yace."Ranka ya dade akwai abunda kake bukata muyi maka.''? Girgiza kansa yay yace."Bana bukatar komai kuje ku kwanta sai da safe." Godiya muka mike muka juya da niyyar fita. Nice ta karshen fita naji ya kira sunana. juyowa nayi ina kallonsa. "Zonan." yafada idonsa a kan wayarsa, a sanyaye na saki kofar ta rufe na koma na tsaya tare da sunkuyar da kaina, na kai minti goma a tsaye a kansa kafin yace."Ki matsa min kafafuna." Kallonsa nayi inaso nayi magana naga yasha kunu. Kasa motsi nayi gabana na faduwa ni kam na rasa wane irin mutum ne wannan abinda Allah ya haramta sai yace sai nayi masa. "Ko ba zakiyi bane."? Nace" Bai dace ba na ta'ba jikinka ba dan Allah kayi hakuri na kira maka Haruna yayi maka." Mikewa zaune yayi yana kallona yace."Kafafuna nace ki matsa min ba Al'aurata nace ki matsa ba." da sauri na kalleshi ina mamakin maganarsa, Al'aura lallai mutumin baida kunya. Ya cigaba da cewa! ni bazan ji wani feelings ba ballanatana kiyi tunanin wani abu zai faru a tsakaninmu dan kin matsa min kafafu babu abinda zai faru ki kwantar da hankalin ki." Wannan maganar da yayi tasa naji kwarin gwiwa a jikina dama ina tsoron faruwar wani al'amarin ne. Ajiyar zuciya ya sauke ya ajiye wayar kan drowar ya koma ya kwanta yana kallon rufin dakin. A d'arare na zaune a gefansa nasa hannuna a kafafunsa na soma dannawa, rintse idonsa naga yayi yana sauke ajiyar zuciya, dauke kaina nayi daga kan fuskarsa na cigaba da daddana masa kafafunsa ina neman tsari a cikin raina......Gani nayi yayi ruf da ciki ya dauki hannuna ya dora kan cinyarsa 'kasa-'kasa yace."Ki danna min nan." Hannuna ne ya shiga karkarwa nayi sauri na janye ina danna inda be sani ba! shuru dakin yay na kusan minti ashirin na gaji na cire hannuwana ina dan kallonsa shuru naji kafin naji saukar numfashinsa, a hankali na mike ina leka fuskarsa naga idanunsa a rufe ina tunanin bacci ya daukeshi, kamar na tasheshi ya gyara kwanciyarsa sai dai na rabu dashi sabida ina tsoran kada na tashe shi ya bijiro da wata fitinar, fita nayi daga dakin tare da ja masa kofa......... Kasancewar asibitin babbane yana dauke da ma'aikatan jiyya yasa Washe gari da safe da muka shiga gaishe shi muka sameshi yayi wanka ya shirya jikinsa cikin k'ananun kaya sai kamshin turare mai dadi yake. Gaisawa mukayi dashi kafin su Haruna su fita su barni dashi, a dakin, Jikina ne ya bani kallona yake na dago kaina babu walwala a tare dani nace"Ranka ya dade ana iya had'a maka breakfast yanzu." Kansa kawai ya daga min still idanunsa na kafe a kaina, tsaki naja a raina na tsani wannan d'abi'a tashi idan ya dinga kallon mutum kamar ba zai bari ba........"Ki had'a min tea kada kisa sugar da yawa.'' nace"To ina kokarin dauko kwandon dake dauke da kayan tea din. Sukayi sallama suka shigo dakin. Uwar gida Huwaila ce da yaranta guda biyu su uku kenan....cikin isa da taqama suka karasa shigowa dakin., sunkuyar da kaina kasa nayi Nace"Barkanku da zuwa." Babu wacce ta amsa min a cikinsu nace"Ina fatan kun tashi lafiya."Nan ma basu ce min komai ba, jikina a sanyaye na bude fulas din tea ina tsiyayawa a cup.gefe guda kuma ina jinsu suna gaisawa dashi suna tambayarsa jikinsa. Cikin kulawa yake amsa musu har yana tambayar antis dinsa yaransu, mikewa nayi a nutse na isa gurinsa na mika masa tea din na kallashi nace"Ina iya tafiya."? Daga min kansa yay ya cigaba da magana da 'yar uwarsa, da zan fita sai da nayi musu fatan fitowa lafiya cikinsu babu wacce ta amsa min. Harabar asibitin na fita na samu wani guri na zauna ina kallon masu shige da fice tunani nake inasu Haruna suka shiga kuma dan tun fitowa ta gurin banga gilmawarsu ba......Motocin dake dauke da tambarin masarauta ne suke shigo cikin asibitin, da sauri na mike na nufi inda motocin ke parking Maimartaba ne dashi da Amaryarsa Fulani suka fito daga mota guda, d'aya motar kuma su Waziri ne a ciki, sunkuyar da kaina kasa nayi cikin ladabi na gaishe su, cikin kulawa suka amsa min, gaba nayi da sauri domin na jagorance su dakin da yake........Jama'ar dake kai kawo a asibitin ganin Sarki dashi da muqarrabansa yasa suka dunga zubewa suna kwasar gaisuwa, kofar dakin na bude tunkafin su karaso, sai da suka gama shiga dakin tukkuna na mayar da kofar na rufe na samu guri na zauna ina sauke ajiyar numfashi Maimartaba da Amaryasa sunji dadin ganin yaronsu ya samu lafiya a tsakankanin kwanaki bakwai da faruwar al'amarin ya samu lafiya ya warware sosai kumburin da fuskarsa tayi ya sa'be sai tabbanin dake saman goshinsa likita ya tabbatar dacewa a yanzu babu abinda ya rage a tare dashi sai jiran cikowar naman goshinsa inda ya bugu da dutse kasancewar gurin yayi rami sosai yasa ba'a kwance masa bandejin ba, abinda ya rage kenan a jikinsa. Ba iyayensa ba kadai sukayi murna da farin ciki ba har damu masoyansa munji dadi sosai da result mai kyau ya fito, ganin yanda ya bugu a kansa ne yasa iyayansa hankalinsu ya tashi suna ta fargaba kada ya samu matsala a kwakwalwarsa sai gashi likita ya tabbatar musu da cewar lafiyarsa lau abinda ya rage a tare dashi shine jiran tofowar naman goshinsa da yayi rami shima kuma da yardar Allah baza a dauki dogon lokaci ba......Cike da farin ciki Maimartaba da amaryarsa suka bar asibitin wanda kafin tafiyarsu sai da ta sake jaddada min cewa na kula sosai da shige da ficen jama'a a dakinsa sannan na kula da abinda zai ci da abinda zai sha. Sake zage damtse nayi akansa sai ya zamana kullum tsakanina dashi sai munyi fad'a yayi ta yi min tsawa yana marina ina daurewa duk rintsi bana barinsa yaci ko yasha abinda bai gamsar dani ba....... *BINTA UMAR ABBALE* *Na kudi ne* Idan kina bukatar biya #300 ne 0542382124...Binta umar gtbank idan kati zaki turo #400 kiyi min mgn ta wsp da wannan number 07084653262 ga me bukatar ViP gruop #600 2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 45&46 Cikin tsabar takaici da b'acin rai ya fito daga toilet din ya same ni a tsaye. kasa kallonsa nayi saboda ina gudun na fad'a masa maganar da zata dunguzuma masa zuciya, a yanda nake jin raina a bace kowace irin magana ina iya fad'a masa dalilin da yasa kenan na sunkuyar da kaina kasa ina cigaba da sha'kar takaici da 'bakin ciki. "Munyi waya da Muddibo yanzu ya sheda min cewa yazo ina bacci ya kawo min apple so kizo ki bani ita kad'ai nake muradi a yanzu.'' Kallonsa nayi gabana na fad'uwa yana zaune a gefan gado yake wannan maganar gashi ya kafe ni da manyan idanunsa......kasa cewa komai nayi domin nasan sai mun haura dashi akan hakan dalilin da yasa kenan nayi shuru ina tunanin abunda zan fad'a masa. " Ko bakya ji ne.''!? yafada a d'an hasale! a jajurce nace "Lokacin dana duba apple d'in sai naga ta lalace shine na zubar da ita." Gani nayi ya kura min ido ransa a 'bace yace."Wato ke ba zaki daina yi min katsalandan acikin al'amurana ba ko? shin ina ruwan ki da abinda d'an uwana ya kawo min, yau ko tsutsa apple din ke fitarwa baki da hurumin da zaki zubar min har sai na tashi a bacci na gani to saboda haka kije ki d'auko a duk inda kikaje kika zubar ko kuma wallahi na 'bata miki ranki.'' "Ranka ya dad'e kada fa ka manta kai amana ne a gurina ya za'ayi na barka kaci abinda zai cutar da kai wallahi apple din bata da kyau shiyasa na zubar kuma meye amfanin na bar abinda zai tayar maka da hankali idan ka ganshi ka gafarce ni ranka ya dad'e." Mi'kewa naga yayi ya durfafoni fuskar nan a murtuke! da har na tsorata sai kuma wata zuciyarta tace''Ki dake ki daina yawan tsoronsa sai ya raina ki. tsayawa nayi ina kallonsa har ya karaso inda nake tsaye, kawai yasa kirjinsa yayi baya dani saura kiris na fadi k'asa bayana ya jingina da bango(garu) sai muka shiga kallon kallo dashi, kasa jimirin kallonsa nayi na lura akwai wani sirri a cikin kwayar idanunsa gabad'aya jikina ne yake naman mutuwa jin kirjinsa ya danne nawa. "Zaki d'auko min apple dina ko sai nayi miki Zigidir a d'akin nan wallahi bani da mutunci zan iya tu'be miki kaya na tozartaki." Gabana ya dinga bugawa na kalleshi inaso nayi magana, amma na rasa abinda zance jajayen idanunsa da ya zuba min sun kassara ga'bban kijina. Mun jima a haka yana danne da kirjina ina fitar da numfashi da kyar kafin wani karfi yazo min na tunkud'eshi da karfi hanyar futa na nufa da sauri ya ri'ko hannuna na riqe kofar dakin da karfin gaske! da karfi ya jani sai gani a jikinsa, fad'uwa mukayi tsakiyar dakin na ganni kwance a saman kirjinsa, a zafafe na mike tsaye na sake nufar hanyar fita, kafarsa yasa min na fadi a gurin... kafin nayi wani yunkuri ya danne ni kauda kaina na dinga yi jin hucin numfashinsa na dukan fuskata Cikin rawar murya nace"Ka d'aga ni kada wani ya shigo ya same mu a haka." Banza yay min ya cigaba da bin fuskata da kallo. rai a bace nace"Ranka ya dade ka tashi a kaina kada zuciyata ta tunzurani nayi maka abinda bai dace ba. A sar'ke naji yace''Duk abinda kike ganin zakiyi kiyi." Hanci na sha'ka! rai a mugun 'bace na dunga tureshi ina kici kici zame jikina, Sake matse ni yake yana danne ni! hawayen bakin ciki suka zubo min yawun bakina na tattaro na fesa masa a fuska. ina kuka nace"Allah ya isa mugu azzalimi." Babu walwala a tare dashi yace."Ni kika tofawa kazamin yawun ki? ni kike wa Allah ya isa."? Kauda kaina nayi ina jan tsaki tare da dukan kirjinsa. Fuskata naga yana bi da kallo duk inda nayi da ita sai ya bini da tashi fuskar, kokarin had'a bakina yake dana shi ina kaucewa amma sai da ya samu nasara yasa bakinsa a nawa duk turje turjen da nake ina gumtse bakina sai da ya samu nasara ya dinga tsotsar min le'buna yana cizona. Hawaye nake ina dirka masa duka a bayansa ko gezau beyi ba sai da yasha bakina iya son ranshi ya zare bakinsa, ido jawur yake kallona, kunya da tsanarsa suka sa na kasa hada ido dashi. Sauka yay daga kaina na mike zaune ina gyara rigata. "Wallahi Allah sai ya saka min abinda kayi min kuma daga yau na daina kula da kai zan samu wacce ta turo ni na sheda mata cewa farautata kake yi kaga daga nan shikkenan ma'kiyanka sai su samu nasara a kanka." Ina gama maganata na miqe da niyar barin gurin, hannuna ya riqe na kalleshi ina goge fuska, yace."Mutukar kika fadawa mahaifiyata ina farautarki to wallahi daga ke har iyayenki kun daina shan ruwa a masarautar nan sai kun fuskanci hukunci mai tsauri daga gurina, kawai ki bani jikinki na mora shine kikewa bakin ciki da ganin k'yashi waye zai gani waye zai san abunda ke faruwa a tsakanina dake 'yar kauye irinki na nuna ina sha'awarki ki tsaya kina min yanga okey kiyi gangancin fad'awa iyayena wannan maganar kiga irin hukuncin da zai biyo baya." Jikina ne yayi sanyi jin furucinsa sai na tuno da nasihar mahaifina kullum sai ya umarce ni akan bin umarnin masarauta Yarima Ali ya nuna min cewa shi d'an sharri ne zai iya shirya min wani sharrin reshe ya juye da mujiya ni da iyayena mu muzanta a masarauta wannan tunanin da nayi yasa gabadaya naji gwiwata tayi sanyi da hukuncin da nayi aniyar dauka a kansa. "Muje inda kika zubar min da apple ki dauko min kayata. maganarsa ce ta dawo dani tunanina, cikin rashin mafita nayi hanyar fita ya biyo bayana. Sai dana isa gurin da kamar minti biyar ya karaso kwata-kwata yanayin tafiya ta da tashi ba daya bane ni ina da zafin nama yanayin girman jikina bai hanani kazar-kazar ba dalilin da yasa kenan da nasa hannu a aiki nake saurin gamawa Karasowa yayi yana bin gurin da wani irin kallon k'yank'yami! sandar dana tona sharar dazu yanzu ma ita na dauka na fara yunkurin tona sharar domin dauka masa tsiyarsa......Hannu yasa ya kar'be sandar ya jefar da ita can nesa, babu fara'a a tare dashi yace." Hannu zaki sa ki dauko.'' Na dinga kallonsa ina jin takaicin abinda yake min. kasa sa hannuna nayi dan nima k'yank'yami ne dani sai kawai na sunkuyar da kaina zuciyata kamar ta tsage saboda bakin ciki......"Ke! kin barni a tsaye rana na dukana ga kud'aje na bin jikina, kisa hannu ki dauko min apple dina ko kuma naci mutuncin ki anan gurin. Cikin takaici nace"Ai da zan sa apple din ba hannuna nasa na tona sharar ba sanda nasa kuma ka jefar da ita." Babu ruwana da sanda kika sa yanzu hannu zaki sa ki dauki min." yafada yana kusantoni. ganin kada mu aikata abu irin na dazu yasa nayi shahadar sa hannuwana a cikin sharar ina tonawa, can na dauko ledar apple din har ta soma jikewa da ruwan k'azanta.....Mika masa nayi da fadin"Gashi.'' Ya kai minti biyu yana kallon ledar apple din ya tsine fuskarsa yayi kafin ya tsartar da yawu ya juya da sauri ya bar gurin.....kasa'ke nayi da ledar a hannuna ina tunanin abinda yake nufi da hakan da yayi. Hawayen takaici da bakin ciki ne suka shararo min! nasa hannuna ina gogewa wasu na sake zubowa. gaskiya duk inda ake neman mara mutumci guy nan ya kai, ashe dan ya tozartani ya wulakanta ni yasa yace lallai sai nasa hannuna a cikin shara! kuka nake sosai abubuwa sun taro sunyi min yawa gabad'aya ni yanzu tsoro ma yake bani wallahi tunda ya nuna yana sha'awata nake jin fargaba da tsoron abinda zai biyo baya a tsakanimu, yanzu ta wace hanya zan kare kaina daga sharrinsa, shuru nayi ina tunanin karbar shawarar da zuciyata ke bani, zan shiga d'aure masa fuska daidai da 'kwayar zarra ya daina ganin sassauci a tare dani, duk sanda kuma ya sake yunk'urin kai hannunsa jikina to zanyi iyakacin kok'arina na 'kwaci kaina, da wannan tunanin na bar gurin, ina sake karfafawa kaina hukuncin dana yanke. *** Tsakankanin kwana ki biyu aka kwance masa bandejin dake nannad'e a kansa alhamdullhi aiki yayi kyau dan goshin sa bai nuna wani mummunan tabo ba gurin da yayi rami ya ciko sosai sai abinda ba'a rasa ba, a ranar asibitin cika yay da 'yan uwansa suka kewaye shi kowa na nuna murna da farin cikinsa dangane da samun lafiyarsa, Lawisa na kusa dashi sai kula take dashi tana bashi abubuwan ci da suka kawo masa, gabadaya kasa nutsuwa nayi dan ina jin tsoro kada yaje yaci abinda zai cutar dashi, mikewa nayi a sanyaye na nufi d'akin, har nasa hannuna a jikin kofar sai kuma na cire tsoro nake ji na shiga dakin wani yaci min mutunci, a sanyaye na juya da niyyar komawa na zauna aka bud'e dakin da sauri na juya baya gabana na faduwa, Muddibo ne ya fito daga dakin fuskarsa babu walwala yace....... *BINTA UMAR ABBALE* *Na kudi ne* Koda zaki ganshi a groups na sata ne idan kina bukatar ki biya kudin karatu ga yanda abin yake....Vip gruop#600 normal gruop#300 account 0542382124..Binta umar gtbank...idan katin zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta whasap da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 49&50 Cikin nutsuwa na 'karasa na sameta inda take zaune, zama nayi kaina a kasa nace"Barka da wannan lokaci ranki ya dade jakadiya tace kina nema na." A nutse ta gyara zamanta tana kallona cikin kulawa da kwantaccan murmushi a fuskarta tace"Barka kadai Sumayya ina fatan kun dawo gida lafiya." A nutse nace'Lafiya lau ranki ya dade." zamanta ta sake gyara tana kallonta tace." a gaskiya naji dad'in n ganin babana lafiya lau yayi ki'ba ya k'ara kwarjini idan ba'idona ne ke min gizo ba sai nake ganin kamar har haske ya k'ara, gaskiya Sumayya kin iya kiwo kin kula min da babana yanda nake so." Cikin farin ciki da jin dadin kalamanta kalleta nace"Godiya nake ranki ya dade.'' Tace"Ai ke zanyi wa godiya Sumayya dalilin da yasa ma kenan na kira ki domin na nuna miki jin dad'ina akan abinda kikayi min sannan na baki kyautar dana tanadar miki." Murmushi nayi cikin nuna farin cikina da yabawar dana samu daga gurinta nace"Ranki ya dade sabida Allah nake kula da Yarima badan kyauta ko yawancin wani abu ba duk abinda nake masa saboda Allah nakeyi bayan nan kuma ai ya cancanta a kula dashi a hidimta masa. Tana murmushi tace"Duk da haka dai Sumayya baki ji bahaushe yana cewa "yaba kyauta tukwici ba." Yar dariya nayi ina kara sunkuyar da kaina kasa....Tace"To kingani dole in nuna miki farin cikina a zahiri sannan nayi miki ihsani dan kiji dadi." Nace"To godiya nake "Ranki ya dade." Wata madaidaiciyar akwati dake gefanta ta janyo tace"Ki dauki akwatin nan Sumayya duk abinda ke ciki naki ne na baki kiyi ado dashi a ranakun juma'a da sauran muhiman ranaku." cike da murna da farin ciki na dubi akwatin sai kyalli take tana daukar ido nace"Kai masha Allah ranki ya dade hakika naji dadin wannan kyauta da kikayi min ina rokan Allah ya kare ki daga sharrin masu sharri ranki ya dade Allah yaja zamanin ki ya kara miki lafiya da nisan kwana." Da murmushi a fuskarta ta amsa da ameeen kafin ta d'ora da fadin" Kina iya zuwa ki aje akwatin a gurin ku kije sashen babana ki duba idan yayyunsa sun bar sashen ki fito da dukkanin abinda suka kai masa mutukar naci ne kada ki bar komai ki fito dashi a fitar dashi can waje a zubar." Da sauri nace"Insha Allah yanzu zan cika umarninki ranki ya dade." Mikewa nayi da akwatin a hannuna nayi mata sallama.....sauri sauri nake tafiya da akwatin a hannuna har na isa sashen mu, ko zama banyi ba na aje akwatin Tambaya tace"Wannan akwatin fa ? kin shigo kina gaggawa ina fata dai lafiya." Ina kokarin fita nace"Lafiya lau zanje sashen Yarima na dawo sai nazo mu bude akwatin dana ajiye." Ban jirayi amsar ta ba na fita da saurin gaske, gabadaya hankalina ya tashi da jin cewa tun dazu yayyunsa na sashensa, sai na dunga zargin mybe ma sun samu nasara a kansa watakila na shiga na tarar da gawar sa ko kuma na tarar dashi cikin mawuyacin hali, idanuwa na ne suka taru da ruwan hawaye nace"Insha Allah babu abunda ya sameshi." ........koda na shiga falon su Haruna na samu suna aikace aikace! ajiyar zuciya na sauke ina rarraba idanuna a falon, can na hango tarin warmas da kuloli a shirye akan kilishin da yake zama dan hutawa, ba tare da shawarar kowa ba na nufi gurin, ban yarda na zauna masa a kilishi ba gefe na tsuguna na soma binkicen abincin......Motsin saukowar sa yasa nayi gaggawar kallon benan gabana ya yanke ya fadi ganin yanda yasha kunu yana min kallon tuhuma, da sauri na mike daga gurun can gefe na matsa kaina a sunkuye nace barka da fitowa. ko kallona beyi ba ya zauna a gurin, su Haruna suka karaso suka gaisheshi suka fita, kallona yayi a watse yace."Me kika tsuguna zakiyi min akan abinci ko zaki zuba min guba ne." Idona na zuba masa ina mamakin maganarsa....Yace."kin tsareni da ido ko nayi 'karya ne."? girgiza kaina nayi ina danne 'bacin raina nace." "Zan duba ne domin na tabbatar da ingancin su." Ya 'kalle ni yana girgixa kai yace."Wato ke ba zaki daina saka kanki a kan abinda be shafeki ba ko." Kaina a kasa nace"A gafarce ni ranka ya dade." tsaki yaja da fad'in" Ki bud'e ko wanne abinci ki zuba min cokali daya a plate yanda nayiwa kowacce al'kawarin cin abincinta to ba zan sa'ba ba." Cikin bin umarninsa na tsuguna a nutse na fara budewa kular farko fatan doya ne wanda yaji kifi da da curry sai kamshi yake yi ido na tsira a cikin fatan sai naga kamar curry yay yawa da alama an zuba magani a ciki dan ban yarda dashi ba, kular na matsar gefe......tsawa! ya buga min da fadin"Meye haka zaki bude kuma ki matsar ko ba cewa nayi ki zuba min ba." Yanda ya tsattsare ni da ido yasa da sauri na de'bo fatan cikin cokali nasa a plate din.....Daya kular na bude.......Miyar hanta ce da taji kayan lambu itama sai kamshi take amma kuma ba tayi kyau a ido ba tayi b'aki kamar ba'a sa kayan miya a ciki ba. Girgiza kaina nayi nace"Ranka ya dade kada ka hada abinci kala kala kaci cikin ka ya b'aci ina ganin kaci guda daya ya isa." "Ina ruwanki ? cikin ki ko nawa."? abinda ya fada kenan yana tsatstsare ni da ido, cike da takaici na bude kular shinkafar na zuba a plata kana na zuba miyar hantar a gefe. Kula ta uku na bude farfesun dankalin turawa ne da kifi a ciki sai daya kular dake dauke da supargetti (Taliya) plate na dauka na zuba a nutse na jere su a gabansa." kallonsa nayi ya wani hard'e kafafu nace"Na gama had'awa." Warmars din ya duba da fadin"Kin bude wannan ne."? Nace."Ka gama cin wa'innan." bece min komai ba ya gyara zamansa, barin gurun nayi ina jin faduwar gaba tsintar kaina nayi dayi masa adduar kariya daga Allah. Bisimillah yayi ya fara da plate din fatan doya, ya cinye wanda na zuba masa ya janyo na gabanshi shinkafa ba ta dameshi ba shiyasa ko cokali daya beci ba miyar k'awai ya d"an sha ya ture plate din, na ukun ya janyo yana jin k'arnin kifin dake tashi a miyar zuciyarsa ta tashi, da sauri ya ture plate din, yana kallon gefan da nake, saurin sunkuyar da kaina nayi dan bana son ya gane kallonsa nake....."Zo ki janye kayan nan na gama." Da sauri na mike naje na kwashe plates din dake gabansa. "Bude min warmars din." Ba tare da nace komai ba na tsuguna na shiga bud'e masa snacks ne duk a ciki suna ta kamshi...."Zuba min a plate." Ya umarce ni, zuba masa nayi na mika masa kusa dashi, gyara zama a nutse yasa hannu ya dauki cake guda daya yasa a bakinsa, yana taunawa yaji radad'i a bakinsa furzar dashi yay a gurin, da sauri nida shi muka bi gurin da kallo, babu komai a cikin cake d'in , na kalleshi da sauri sai naga alamun jini a bakinsa, cikin fad'uwar gaba nace"Ranka ya dad'e meye a bakin ka." ? Hannu yasa da sauri ya shafo jinin yana dubawa! kuka nasa ina kallonsa ina hawaye nace"Kaga abinda nake gudar maka ko.? ni dama nasan sai kaci baragurbin abu.....mikewa yay da sauri ya hau samansa, ina kuka ina dudduba cake din babu alamun komai a cikinsa shar dashi sai kamshi yake, na mike tsaye hankalina duk ya tashi! addua nake yi Allah yasa cake din be shiga cikinsa, dan daka gani guba mai karfi akasa a ciki. Shawara na yanke a kan nabi bayansa domin ganin halin da yake ciki......Kofar dakin a bude na sameta ba tare da tunanin komai ba na shiga, kakarinsa naji a toilet a guje na shiga toilet din, na ganshi ya rike kirji yana ta kakari babu abinda ke fita, k'asan gurin na kalla naga jini d'is-d'is yana diga. Hawayen nadama suka wanke min fuska Yanzu da wane ido zan kalli mahaifiyarsa data gama yabo na, me zan fad'a mata? bayan ta bani umarnin fitar da kayan abincin daga sashensa gashi na barshi yaci abinda ya cutar dashi, bani da bakin magana! dana sani da nadama suka baibaye ni, dana sani na bar shi ya dake ni ya mare ni nabi umarnin mahaifiyarsa na hana shi cin abincin......Sheshshakar kukanta ne ya ishe shi ido jawur ya dago yana kallonta sai yaga ta d'ora hannuwanta duk biyu a kanta tana zubar da hawaye. Tausayi ta bashi! ya dafa bango(Garu) ya mike tsaye. da sauri na kalleshi nace"Sannu ina fatan babu inda ke maka ciwo ? bai kalle ni ba yazo zai wuce hanya na bashi ya fita nabi bayansa, samunsa nayi kasan kafet yana maida numfashi. Gabansa na tsuguna ina kallonsa idanuwansa sunyi jaja wuyar, a sanyaye na sake yi masa sannu ina tambayarsa abinda ke damunsa.''' Kallona yay yace."Babu abinda ke damuna ki daina damunki kanki." Nace" To Alhamdullhi dama haka nake so naji dan Allah ranka ya dade ka dinga yarda da maganata dik abinda kaga inayi a kanka da umarnin mahaifiyarka nake yi ina fatan yanzu zaka gane gaskiyar maganata." Hannu ya daga min da fad'in "Kije kawai bana san dogon surutu." A sanyaye na mike na kama hanyar fita daga dakin banji dadin gwasale ni da yayi ba.. Bayan fitar ta daga dakin mamaki sosai ya shiga yi akan abinda ya faru! to me hakan ke nufi? ashe dai duk tsayayyar da yarinyar nan takeyi da gaskiyarta 'Yan uwansa na jini zasu kasheshi!? wai shin ma snacks din da yaci na wacece a cikinsu.? bashi da mai bashi amsa, ajiyar zuciya ya sauke ya jingina bayanshi jikin gado har yanzu yana jin zafi a mak'ogwaron sa, yana jin kamar an tsatstsaga masa da reza, pridge ya bud'e ya d'auko ruwa mai sanyi wai ko ya samu sa'ida yana sa ruwan a bakinsa yaji radadi da zugi a mak'ogwaronsa da kyar ya iya had'iye ruwan ya ajiye goran ruwan a kusa dashi yana mamakin al'amarin. Cikin sauri na fitar da kayan abincin na lodasu a cikin wani buhu mai zurfi dan har kulolin na hada ina ganin suma barinsu had'ari ne d'aure bakin buhun nayi na umarci Hamza da ya dauka ya fita buhun, oma nasa sosai na wanke hannuna kana na koma ciki. Samunsa nayi tsakiyar falon yana safa da marwa, nace"Kana bukatar wani abune." ? "Kije ki kira min Haruna." yafada yayin da yake kokarin zama kan kujera da sauri nace to na juya na fita. Tare muka shigo da Haruna yace."Ranka ya dade gani." Da kyar naga yayi maganar." Ungo jeka pharmacy (gurin seda magani) ka kar'bo min wannan maganin." Haruna ya 'karasa kusa dashi da sauri ya kar'bi takardar hannunsa da kudi. Fita yay da sauri! nima na juya da niyyar fita......"Ke! juyawa nayi ina kallonsa, "Kada ki kuskura naji maganar nan a bakin kowa mahaifiyata ma ban amince ki fad'awa ba kinji ko."? Da mamaki a tare dani nace" Ranka ya dade mai yasa baka so mahaifiyarka tasan abinda ke faruwa? wannan al'amarin fa bai kamata a 'boye ba, ya kamata ta sani domin ayiwa tufkar hanci da wuri." "Ke baza a ta'ba fada miki magana kice to ba sai kin kawo hojjojin ki ko."? A sanyaye nace" Ranka ya dade ba haka bane duk abinda kaga na'ki aminta dashi kai tsaye to na duba naga ba mai kyau bane dan Allah ka bari a shedawa mahaifiyarka a'lamarin nan." "Ke ki kula fa ni babu me shiga tsakanina da 'yan uwana kinji na fad'a miki ban yarda wani abu na cutarwa naci ba saboda haka na fada miki ki iya bakinki ban amince ki fadawa kowa wannan maganar ba. Na dinga kallonsa ina jin wani irin takaici a cikin raina 'kiri-'kiri yana ganin gaskiya yana takewa sau biyu yana tsallake rijiya da baya amma wai fadi yake bai yarda yan uwansa zasu cutar dashi ba, girgixa kai nayi nace" To shikkenan tunda baka so kowa ya sani insha Allahu babu wanda zan fad'awa." Kauda kansa yay daga kaina ya tsirawa kasan gurin ido." Nace"Ina iya tafiya."? hannu ya daga mun alamar na tafi, na juya da sauri na bude kofa na fice raina a 'bace! na isa sashen mu... Na kudi ne..! Koda zaki ganshi a gruopa na sata ne idan kina bukatar biyan kudi ga yanda abin yake.....Vip gruop#600 normal gruop#300...account... 0542382124...Binta umar gtbank....idan kati zaki turu #400 ne kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 47&48 "Ke ranar dana zo na kawo Apple din nan kin bashi yaci ko kuwa."? Cike da tuhuma yake min maganar sannan ya wani tsatstareni da idanunsa, cikin zuciyata nace"Ni dai na shiga uku kowa so yake yay amfani dani gurin cimma munufarsa, cikin ladabi nace" Ranka ya dade na bashi sai dai ban sani ba ko yaci ko kuma beci ba dan umartata yayi dana fita daga dakin. Ajiyar zuciya naga ya sauke a fusace! ya bar gurin, zama nayi a sanyaye ina bin hanyar da yabi kallo nace "Insha Allahu Allah ba zai baku nasarar cutarsa ba." shuru nayi ina mamakin abinda sukeyi gabad'aya sunbi sun tayar da hankalinsu akan sa kowa so yake yaga bayansa sabida suna ba'kin cikin kada ya gaji mulki a hannun mahaifinsa, a gaskiya idan haka sha'anin sarauta yake da bita da k'ulli gami da ma'karkashiya to babu shakka akwai matsala da damuwa acikin al'amarin sha'anin sarautar dai ya zama sai gyaran Allah dan gabad'aya kowa babu Allah a cikin zuciyarsa. Sai bayan la'asar Jama'a suka tsaigata, koda muka shiga dakin ragal muka sameshi a zaune yana ta abinda ya saba, latse latse a waya, a jiyar zuciya na sauke naji dadi sosai ganinsa lafiya lau, Haruna da 'yan uwansa suka shiga tsaftace dakin, ni kuma na kama hanya na fita daga dakin ganin ko kallon inda nake beyi ba. Alwala nayi nai sallah na fito na sake zama ina saka wasikar jaki, muryar babana naji yana sallama da sauri na daga kaina sai na gansu shida Tambaya, wani irin farin ciki ne ya ziyarci zuciyata dama kwana biyu dauriya kawai nake da tunaninsu nake kwana nake tashi, da sauri na mike naje na taresu ina dariya nace"Baba sannunku da zuwa naji dadin zuwanku." Tambaya tace"Muna ta sa ranar zuwa Allah bai nufa ba sai yau." Cikin kulawa babana yace."Ai izini na nema gurin Fulani amaryar Maimartaba shine tasa aka kawo mu." Nace."Aikuwa naji dadi sosai da zuwanku kuzo muje nayi muku jagora." Hannunsa na rike muka nufi dakin..............Yana zaune a inda yake da alama ma baiyi sallah ba cikin zuciyata nace"Saboda rashin kula da addininsa komai aka nufe shi dashi na sharri yana iya kamashi, a zahiri kuwa cewa nayi "Ranka ya dad'e fatan ka wuni lafiya ga Iyayena sunzo domin su dubaka." Dago kansa yayi yana kallonsu, su kuma sun sunkuyar da kansu kasa cikin ladabi da tausasa harshe suke gaisheshi, sai naga shima ya sassauta muryarsa ya amsa cikin kulawa yana nuna musu gurin zama da hannunsa. Yanda ya tar'bi iyayena da sakakkiyar fuska yasa naji dadi a raina, nace"Baba ku zauna ga guri nan." Zama sukayi kan kujera suna murmushi yanda na lura suma sunji dadin tar'bar da suka samu. Shuru dakin yay na minti biyu nida iyayena tunani muke shi kuma hankalinsa gabadaya yana kan wayarsa, da alama yana duba abu mai muhimanci a wayar......Muryar babana naji yace."Kar'bi wannan Sumayya ki bashi kayan dubiya ne babu yawa, ranka ya d'ade gashinan babu yawa.'' Da sauri na kar'bi ledar da yake mi'ka min, na isa inda yake na bashi A nutse yace."Ajiye kan drowar nagode sosai." Ajiyewa nayi da sauri na matsa daga gurin.....d'akin ne ya sake dau'kar shuru na tsayin minti goma kafin babana yace."Ranka ya dade zamu tafi Ubangiji Allah ya kare ya kiyaye gaba munayi maka fatan alkairi har karshen rayuwarka. Wayar dake hannunsa ya ajiye kan drowar cikin kulawa ya amsa da fadin"Ameen suma ameen nagode kwarai ku sauka lafiya." Babana da Tambaya suka kama hanyar futa suna jin dadi a cikin zuciyarsu bayansu nabi nima raina tas naji dadi sosai da bai wulakanta min iyayena ba. Har bakin mota na rakasu suka shiga direba yaja suka tafi cike da kauna da kewarsu na koma cikin asibitin... dakin na koma still yana zaune a inda yake ya d'auki wayar yana dubawa, agogo na duba naga biyar shaura, jikina na bani baiyi sallah ba cikin rawar baki nace"Ranka ya dade biyar saura lokacin sallah ya wuce." Kallona yayi cikin mamaki yace."Waye yace miki banyi sallah ba? lallai yarinyar nan kin raina ni da yawa ni kike tunawa lokacin sallah."? Da sauri nace"Aa ba nufina na 'bata maka rai ba ranka ya dad'e nasan sharrin abar dake hannunka waya tana hana ibadah akan lokaci shiyasa nayi maka wannan maganar." Tsaki! mai karfi yaja ya d'auke kansa daga kaina, juyawa nayi zan fita daga dakin yace."Ke! zo ki d'auke tsiyarku bana bukata." Da sauri na Juyo ina kallonsa dan ban fahimci maganarsa ba, ledar kayan dubiyar da babana ya kawo masa ya jefo min ta sauka daidai kafafuna. "D'auka ki fita dashi d'aga d'akin nan."! yafada yana min wani irin kallo. A hankali na sunkuya ina kallon kayan dubiyar manya manyan mangwaro ne masu kyau da nuna duk wanda ya gansu sai yayi sha'awa saboda kyawunsu, cikin ledar na mayar da mangwaron k'walla na taruwa a idona na mi'ke tsaye da ledar a hannuna, cikin rawar murya nace" Me yasa lokacin da'aka baka ka kar'ba harda godiya wannan abin da kayi d'abiar munafukan mutane ne." Uffan bece min ba dan idan da sabo ya saba da tsayayyata bana jin tsoron fad'a masa gaskiya komai d'acinta sai dai ya gaji da marina ko dukuna........."Allah ya shiryeka shirin addinin musulnci." Abinda na fad'a kenan a k'untace na kama hanya zan fita daga dakin naji yace."Da yake Ubanki ne ya kawo min kayan dubiyar ai baki tsaya kin duba kin binkicika ba kai tsaye kika ajiye min sabida kina ganin shi ba zai iya cutar dani ba ko."? Kallonsa nayi raina bak'ik'irin nace"Babana ba zai cutar da kai ba kuma baza'a hada baki dashi a cuceka ba, inaso na tabbatar maka da cewa akan gaskiya mahaifina na iya rasa rayuwarsa mutum ne shi mai tsoron Allah da gudun duniya idan ma kana zarginsa akan wani abu to ka daina domin kuwa kana daukar hakkinsa. "Dallah malama fita ki bani guri kin tsaya kaina kina tsara magana ni bana shedar mahaifinki dan ban yarda dashi ba ke bari kiji ke kanki ban yarda dake ba ballanatana Ubanki duk wannan tsayayyar da kike a kaina kallon ki kawai nake." Cikin sigar k'unsa ba'kin ciki nace"Na lura tunda na hanaka kaina kake zagina kana cin mutuncina to bari kaji wallahi mai kusantar wannan jikin nawa sai salihin namiji nagartacce mai addini maganar rashin yarda daka keyi ka yarda dani ko kada ka yarda dani bai dameni ba domin Allah nake kula da kai kuma nasan yafi kowa sanin zuciyata insha Allahu burinka ba zai cika a kaina ba."! ina kare maganar na bude kofar dakin a zafafe! na fita tare da buga masa kofar da karfin gaske. Ya jima maganganun yarinyar na yi masa amsa kuwwa a kunne tunda yake ba'a ta'ba mayar masa da raddi masu zafi irin na yarinyar ba, tana samun dama a kansa sosai tana farfada masa ba'ka'ken maganganu iya son ranta yasan kuma ba komai ne ya janyo haka ba illah zulamarsa daya nuna a fili amma yana da kyau rana guda ya nuna mata cewa bakin rijiya ba gurin wasan makaho bane. Tunda mukayi haka dashi naji gabadaya zaman asibitin ya fita daga raina addua na dinga yi akan Allah yasa a sallameshi domin mu koma gida na gaji da zama a asibitin na kuma gaji da irin wulakanci da iskancin da yake min, sati biyu da nayi a asibitin nayi asarar karatuna nasan an wuce ni sosai dole idan na koma na nemi wata ta koya min hakan ya sake sakani cikin damuwa kullum fuskata a had'e babu walwala, Dr Rabo shine yake nema ya shige min hanci kusan kullum da daddare sai yayi kirana ofis dinsa idan naje kawai nsai kura min ido yayi ta kallona idan na tambayi ba'asi sai yay murmushi yace."Kawai ya kirani ne domin mu gaisa ya kuma kalleni yaji dadi. cike da takaici nake tambayarsa meye amfanin kallon nawa, kai tsaye sai yace." Shi kadai yasan amfanin hakan, rai a 'bace nake fita daga ofis din.......Ana ya gobe za'a sallameshi dana shiga dakin na sameshi kan kujera daga shi sai gajeran wando farar fatar jikinsa sai daukar ido take kirjinsa cike yake da gashi hakanan saman kafafunsa gashine a kwance bakikirin, ban iya kallonsa a hakaba ba na kautar da kaina da fad'in "Ranka ya dad'e Haruna yace." Kana nema na."? Banza yay dani bai kalli inda nake tsaye ba ballantana ya amsa min. daure zuciyata nayi na sake yi masa magana, ya kalleni a watse yace."Meye tsakaninki da wannan likitan mai ciki kamar rumbu." Dr Rabo gajere ne mai tumbi shiyasa ya kirasa da wannan sunan. Murmushi nayi dan na sake 'kuntata masa nace"Ranka ya dade kana yawan kushe hallitar Allah kaima fa kana da mukusa a jikinka kasan d'an adam tara yake be cika goma ba." Rai a 'bace! yace."Ba wannan na tambayeki ba na tambayaki abinda yake tsakanin ki da Dr Rabo." Ajiyar zuciya na sauke nace"Sirri ne a tsakani na dashi bana bukatar kowa ya sanshi. Naga ya zuba min da'kwa-da'kwan idanunsa yana hararata yace."Wane sirri zaki 'boye bayan abu gashinan a zahiri na sani jama'a sun sani duk daran duniya kina shiga ofis dinsa yana lalata dake shine zaki ce sirri."!! Gabana ya dinga fad'uwa! wannan wane irin d'an sharri ne? 'kazafi zaiyi mana kenan, tsabar firgici da tashin hankali na gagara cewa komai....Yace."Ko nayi k'arya ne."! Hawaye ne suka zubo min na kalleshi muryata na rawa nace" Allah ya sakamin k'azafin da kayi min insha Allahu sai mun tsaya gaban ubangiji akan wannan magana da ka fad'a.'" Hanyar fita na nufa ina kuka wiwi!! jikinsa ne yay sanyi ganin irin uban kukan data fita tanayi! tsaki yaja ya mik'e ko banza ya samu sassauci a cikin zuciyarsa yarinyar ta jima tana 'kuntata masa yau ya rage kuncin dake damunsa, tuntuni ya gane Dr Rabo sonta yake shiyasa gabadaya ya gaza nutsuwa yana fargaba kada yaje wani abu ya shiga a tsakaninsu mugun kishin Dr yake ya'ki nunawa ne saboda wata manufa tashi, da yarinyar ta amince ta zama mai d'eba masa kewa to da tuni ya 'yanta ta ita da iyayenta su tashi daga sunan bayi su koma mutane masu 'yanci, yana jin tsoron Dr Rabo ya yaudareta ta bashi kanta shiyasa gabadaya shima yaji zaman asibitin ya isheshi. 'Daki na shiga na zauna na dinga rizgar kukan dana dade ina tarawa, a duniya ba'a ta'ba yi min abinda ya sani cikin kunci da bakin ciki ba irin k'azafin da guy nan yayi min wato tunda na'ki yarda dashi da bukatarsa shine ya yanke shawarar 'bullowa ta wannan hanyar na tsani zina da masu aikatata sai gashi yau banji ba ban gani ba anyi min 'kazafi da ita, kuka sosai nake ina rirrike kaina. Muryar Haruna naji a kaina a firgice na dago ina kallonsa hannu nasa na goge hawayen fuskata nace"Haruna yaushe ka shigo ko motsin bude kofa banji ba. A sanyaye yace."Ya za'ayi dama kiji motsin bude kofa kina irin wannan kukan." Cikin ya'ke nace"Haruna waye yace da kai kuka nake wani abu ne ya shige min ido shine ruwan hawaye yake futa. Murmushi yay yace."Ni ba yaro bane ballantana ki yaudareni da wannan maganar akan idona kika fito daga dakin da Yarima Ali yake kina kuka dan Allah yau dai kiyi min bayanin abinda ke tsakaninki dashi dan sau tari ina yawan ganinki kina fitowa daga dakin cikin bacin rai." Kasa cewa komai nayi ina mamaki maganarsa ashe Haruna yana hankalce da abinda ke faruwa tsakanina da Yarima! a gaskiya nayi mamaki, dan kada ya zargi wani abu mai muni a tsakanina dashi yasa na yanke shawarar fad'a masa haka." Wallahi Haruna na gaji da zaman asibitin nan na gaji da wulakancin da muke fuskanta daga gurinsa nifa sai nake ganin kamar ni kadai ya tsana kullum cikin zagin iyayena yake yana buga min tsawa duk abinda zanyi masa bana gwaninta, wannan dalilin yasa kullum kake ganina ina fitowa daga dakin raina a bace." Haruna yace."Hakuri zakiyi da yanda kika tsinci rayuwarki a ciki sumayya ki cigaba dayin aikin ki koda kuwa zai ce ki kwanta a kasa ya bi ta kanki baki da za'bi dole kibi umarninsa kasancewarki baiwar dake karkashinsa dole ki d'auki hakurin dukkanin abinda zaki gani, shawarar da zan baki shine ki tsananta addua akan Allah ya baki miji a kurkusa idan kinyi aure shikkenan kin huta da wannan aikin. amma mutukar ba kiyi aure ba to babu shakka zaki cigaba dayi masa hidima har karshen rayuwarki." Maganganun Haruna sun kashe min jiki sosai na soma hango 'kamshin gaskiya a cikin maganarsa babu shakka idan nayi aure na huta da fargaba da tashin hankali ko banza nasan zan samu sassauci a wani 'bangare. A sanyaye nace"Haruna nagode sosai na kuma ji dadi da wannan shawarar taka insha Allahu zan duba wanda ya dace dani na aura." Murmushi yayi yace."To babu damuwa Sumayya nima ina cikin layin masu so dan a gaskiya kina burgeni mutuka Sumayya kina da nutsuwa da kamun kai babu namijin da ba zaiyi sha'awar ki zama uwar 'ya'yansa ba." Kallonsa nake ina mamakin furucinsa, yay murmushi yana shafa sumarsa yace."Ni zan tafi domin na barki kiyi tunani sai anjima." hanyar fita ya kama nabi shi da kallon mamaki har ya fita daga dakin...... *BINTA UMAR ABBALE* *Na kudi ne..!* Koda zaki ganshi a gruops na sata ne idan kina bukatar biyan kudin karatu ga yanda abin yake.....Vip gruop#600 normal group #300 account... 0542382124...Binta umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084563262* 2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 53&54 Wai shin da wane ma'auni zan auna irin wulakancin da guy nan yake min? me nayi masa kullum yake wulakanta ni yake cin zarafina yana tozartani! a ganina ban cancanci haka daga gurinsa ba, ina ruwansa da alaqata da Haruna da har zai dauki zafi! ya kiramu fasikai wannan kalma daya kiran mu da ita tafi damuna akan watsa min fruit salad din da yayi. Hannu nasa na share hawayen daya kasa daina zuba, na mike jikina a sanyaye na shiga gyara gurin ina jin wani irin zafi a zuciyata tsaf na gyara gurin na nufi kofa da niyar fita, kicibus mukayi da Haruna kallona ya shiga yi yana nazari, nayi saurin sunkuyar da kaina ina kokarin magana yace."Sumayya me ya 'bata miki jikinki."? Ji nayi zuciyata ta karye hawaye suka zubo min, murya na rawa nace"Haruna muje kada ya sauko ya same mu a tsaye." A sanyaye ya bude min kofa na fita ya biyo bayana, sai da mukayi nisa sosai na sheda masa abinda ya faru Haruna shuru yay yana girgiza kansa yace."Sumayya ni dai banga abinda mukayi wanda ya kaucewa sharia ba amma zan kiyaye shige miki idan kina gurin kada wata maganar ta sake biyo baya. Nace"Nima haka na gani amma wannan shawarar daka yanke itace tafi amfani idan kana so muyi hira ka bari idan na gama abinda nakeyi na fito sai muyi hirar." Yace."Babu damuwa anjima zan sanar da mahaifina maganar auramu sai ya samu baba Lawi su tattauna." Murmushi nayi nace"To shikkenan hakan yayi.' Haruna har sashenmu ya rakani na sanjo kaya na fito ya rakani sashen Ciroma domin amsa kiran da Gimbiya Lawisa keyi min. Samun ta nayi a hakimce bayin ta sun kewaye ta sai fadanci sukeyi durkusawa nayi ina gaisheta, a wulakance ta amsa, ta dubesu tare da basu umarnin tashi. da sauri suka bar gurin. Minti biyar a tsakani naji muryarta." Sai yanzu ki kaga damar zuwa."? cikin nutsuwa nace"Afuwa ranki ya dade aiki nake a lokacin da kika aika kirana ki gafarce ni." Shuru tayi tana watsa min kallon banza tace"Sumayya anya kuwa kina aikata aikin da nake sanya ki kuwa nifa bana ganin canjin komai a gurin Yarima kullum iskanci yake min ya'ki ya dinga nuna min so da kulawa. Nace"Haba ranki ya dade ba zan ci amanarki ba ina aikata aikin ki akan tsari kin san komai sai a hankali insha Allah zaki shawo kansa zai soki ya kaunaceki tamkar ransa. Murmushi tayi tace"Sumayya shiyasa nake sonki domin kina kwantar min da hankalina amma al'amarin Yarima Ali ya soma bani tsoro wallahi.'" Murmushi nayi nace"Ranki ya dade ki yawaita addua kina rokon Allah ya janyo miki hankalinsa kanki gefe guda kuma kina 'yan daburu irin namu na mata. Gyara zamanta tayi tace"Sumayya duk dabaru na sun kare wallahi kullum na kai masa ziyara da fada muke rabuwa gabadaya ma ni gani nake kamar tunaninsa na wani guri bana gabansa. Shuru nayi ina nazarin abinda zance mata naji tace"Ko kina ganin na bashi kaina ne."? na kalleta da sauri inayi mata kallon mara hankali .....Tace"To Sumayya duk wasu dabaru nayi ya'ki karkato da hankalinsa kaina. Nace"Ranki ya dade idan kika bashi kanki ya sanki a matsayin mace ai kin cutar da kanki ko kunyi aure ba zakiyi daraja ba kuma wulakancin da zaiyi miki sai yafi nada, kada kiyi wannan gangancin ki cigaba da dayin 'yan dabaru insha Allah za'a dace." Ajiyar zuciya mai zafi ta sauke tace"Shikkenan Sumayya zan cigaba da bin shawararki." Nace"Yawwa ranki ya dade......Akushin dake gabanta tace"Ki dauka wannan ki kai masa farfesun kifi ne nayi masa ki tabbatar yasha farfesun dan na zuba sinadarai a ciki kuma ina saka ran zanci galaba." Nace"Angama ranki ya dade yanzu kuwa zanje na aikata aikin ki." Akushin na dauka na rike hannu biyu nai mata sallama na bar gurun......Lantana dake la'be tana ganin fitowar Sumayya a hankali tabi bayanta Ina isa inda nake zubar da kayan asirin na waiwaya ko'ina sai dana na tabbatar da babu kowa a gurin na watsar da farfesun da sauri na rufe akushin na bar gurin ina jin takaicin abinda ke faruwa. Ko zaman minti goma banyi ba sakon kiran Lawisa ya iskeni, Cike da mamaki nake kallon 'Yar aiken, inaso nayi magana Babana ya katseni da fadin na tashi naje....jikina ya bani akwai wani abu mikewa nayi nasa takalmana nabi bayan 'Yar aiken. Tsaye muka sameta tana kaiwa da kawowa a gurin, fuskarta kawai ta isa ta nuna min akwai matsala "Ranki ya dade gan......Kafin na karasa ta wanka min mari! tana huci tace" Sumayya ashe dama munafurta kikeyi ? ashe duk abinda nake baki zuwa kike kina zubarwa.'' Gabana ya yanke ya fadi baki na rawa nace"Ranki ya dade waye ya fada miki haka? wallahi karya ne ina bin umarninki.'' Wani marin ta sake kawo min nayi saurin kaucewa ina binsu Lantana da kallo sai 'kus-'kus sukeyi tabbas a cikinsu wata ta kawo gulmar. "Bazan yarda da rantsuwarki ba Sumayya sai kin tabbatar min da gaskiyar magana daga bakin ki kana kuma ki nuna min inda kike zubar min da kaya.'' Shuru nayi zufa na keto min. " Ke nake saurare 'yar iska munafuka kawai." Naji ciwon zagin da tayi min amma sabida nasan nice bani da gaskiya yasa na cije nace"Ranki ya dade dik wacce ta kawo miki gulma gaskiya ne duk wani kayan asiri da zaki bani nasawa Yarima abinci da ruwan sha zubarwa nake a wani kebantacen guri idan baki manta ba ko dazu sai dana sake tunasar dake cewa asiri ba zai janyo miki kauna da so ba nace miki ki dage da addua sannan kuma ki canza salo, wannan dalilin yasa nake zubarwa saboda ba zan jefa kaina a halaka ba." Huci! ta dinga yi tana kallona tace"Shin kin san irin mak'udan kudin da ake fitarwa kafin a 'karbo maganin nan kuwa."? shuru nayi mata tace"Lallai Sumayya baki da mutunci kuma wallahi sai na dauki tsatstsauran mataki a kanki ki shige muje ki nuna min inda kike watsar min da kaya." Nace"Ranki ya dade ki gafarce ni banyi hakan dan na bata miki rai ba ina guje miki fushin Alla....Hannu tasa ta gwabe min baki! rufe min baki munafuka kawai wallahi sai naci mutuncinki a gidan nan." shuru nayi ina kallonta tasa takalmanta tayi gaba suka rufa mata baya, sai da sukayi nisa kana nabi bayansu.. a gurin na same su Lantana tana nuna mata ramin da nake zubawa. juyowa tayi tana kallona na sunkuyar da kaina kasa, rai a bace ta juya suka rufa mata baya.....wata rumfar bukka na samesu sai zurga zurga take tana magana dasu. Ina karasowa gurin tace nasa gwiwata a kasa, nayi yanda tace kallonsu tayi tace su biyo layi kowacce ta mare ni hagu da dama. Mikewa nayi ina kallonta nace"Ranki ya dade ke nayi wa laifi dan haka ke zaki hukunta ni basu ba.'' "Sumayya so nake ki 'kask'anta yanda kika sa raina baci kema naki sai ya 'baci."! " Ranki ya dade ki gafarce ni ba zan zauna wanda muke matsayi daya dasu su mare ni ba gaskiyar magana kenan." Tana huci! tace"Ni kikewa gardama ko."? kasa nai da kaina babu yanda xa'ayi na zauna su Lantana su mareni duk abinda za tayi sai da tayi. "Lantana je ki kirawo min Buba kice yazo da bulalarsa." Lantana da sauri ta tafi....hannu ta goya a baya ta shiga zagaye gurin cikin zuciyata nace wahalalliyar banza da wofi kawai. Buba da Haruna na tare suna hira Lantana ta isa gurin ta shedawa buba kiran da ake masa, Buba yace kije ganinan zuwa... Haruna jikinsa ne yay sanyi yace"Buba dan Allah kada ka doki Sumayya akan gaskiyarta."Buba yace."Idan tana tsaye a gurin dole nabi umarninta idan ta bar gurun zan kyaleta amma dai duk da haka zan dinga dubarar dukan kasa a madadin ita nake duka." Yana kare maganarsa yay saurin barin gurin, Haruna jikinsa dik yayi sanyi kwata kwata baya so a ta'ba lafiyar Masoyiyarsa. yana kokarin mikewa Buba ya karaso gurin hannunsa nannade da murtukekiyar bulala mai baki biyu, ko sauraransa beyi ba yay gaba. Haruna da sauri ya nufi sashen Yarima domin ya sheda masa abinda ke faruwa. Sai da gabana ya fadi ganin katuwar bulalar dake hannun Buba, gumi ya dinga tsiyaya a jikina dana sani na yarda su Lantana sun mareni da tuni an wuce gurin. "Ranki ya dade gani." Buba ya fada yana me kaskantar da kansa.... jajayen idanunta ta watsa masa tace"Buba so nake ka zane jikin Sumayya har sai rigarta ta yage wallahi idan ka sassauta mata sai ka fuskanci hukunci daga gurina." Murmishi yayi irin na mugunta yace."Angama ranki ya dade." Bulalar ya daga da karfi gaske ya labta min a gadon bayana, kara na saki na rintse idona ina jin radadin zafi a inda ya doke ni....Gimbiya Lawisa murmushi tayi suma su Lantana suka soma dariya, ido jawur nake kallonsu....Buba na dariyar shakiyanci ya sake daga bulalar zai labta min "Kai kar ka daketa." da sauri na bude idona! yana tsaye a gurin haruna na gefansa gani nayi kowa ya shiga hankalinsa har ita Lawisan ta sunkuyar da kanta. Hannu nasa na sharce gumin goshina ina godewa Allah da zuwansa gurin........'"Kai buba me tayi maka kake mata irin wannan dukan."? yana watsa masa harara yake maganar. Buba yace"Ranka ya dade umarnim gimbiya lawisa ne amma ni Sumayya ba tayi min komai ba." Yace."To duk ku bar gurin nan." Buba dasu Lantana suka bar gurin...yunkurawa nayi zan tafi yace."Ke! ku sameni a gurina domin naji ta bakin kowa dan na fahimci akwai rashin jituwa a tsakaninku.'' gurin ya bari haruna yabi bayansa. Kawai sai na tsinci kaina da watsa mata kallon banza a fusace na bar gurin....Gimbiya lawisa a sanyaye ta nufi sashen Yarima saboda tana tsoron abinda zai biyo baya tana tsoron ya tozarta irin na kwanakin baya *Na kudi ne...* Allah ya isa kika karanta baki biya ba idan kina so ki biya ga yanda abin yake......Vip group #600 normal #300 account.. 0542382124...Binta umar gtbank....idan kati zaki turo kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa Dashan Allah✊?) 51&52 Shara na samu Tambaya nayo shigowata yasa ta dakata ta tsaya tana kallona. kasa cewa nayi da ita komai nayi saurin shigewa daki, Tambaya kasa nutsuwa tayi ta ajiye tsintsiyar hannunta a sanyaye tabi bayanta, samuna tayi a zaune na zabga tagumi, shigowarta tasa nayi gaggawar cire tagumin ina kallonta xama tayi gefena a nutse tace"Sumayya lafiya na ganki kin shigo jikin ki a sanyaye ina fatan ba wata matsala bace."? shuru nayi ina kallon kasan gurin, shawarwari nake da zuciyata yana da kyau na sanar da mahaifiyata abubuwan da suke faruwa saboda ina jin tsoron wani mummunan abu ya faru nasan nida iyayena zamu shiga uku, ni sam ban san me yasa baya so mahaifiyarsa tasan abinda yake faruwa ba, kuma idan akace za'a cigaba da tafiya a haka to babu shakka ni dashi rayuwarmu na cikin matsala domun 'yan uwansa basa kaunarsa zasuyi amfani da yardar da yake musu su cutar dashi babban burinsu suga baya motsi a duniya inda shi kuma ya kasa ganewa kullum gani yake ba zasu ta'ba cutar dashi ba.....A sanyaye na warware mata abunda ke faruwa babu abinda na rage mata, yanda na lura itama jikinta yayi sanyi amma domin ta kwantar min da hankali yasa ta dafa kafad'ata tace"Sumayya ki nutsu kinji ko ki daina sa wasiwahsi a cikin zuciyarki insha Allah ba zasuyi tasiri a kansa ba duk sharrin da suke shiryawa zai koma kansu, kamar yanda yace baya bukatar mahaifiyarsa tasan abinda ke faruwa to kiyi shuru kada ki sheda mata, shawarar da zan baki shine ki tsananta gurin kula da shige da ficen masu shiga sashensa, sannan ki kula da duk wani abu naci da zasu kawo masa insha Allah duk sharrinsu sai ya koma kansu, ki kwantar da hankalin ki babu abinda zai faru sai ikon Allah." Ajiyar zuciya na sauke ina kallonta hakika naji sanyi a zuciyata sakamakon kwantar min da hankali da tayi nace"Insha Allahu zan kula kuma ba zan fada Mamma Fulani maganar ba, zan cigaba da kula dashi ina addua kema a matsayinki na mahaifiyata ina rokon ki ki taya ni addua Allah ya kareni daga fad'awa cikin mugun hali." Tambaya tace"Kada ki damu Sumayya kullum cikin yi miki addua muke insha Allahu kuma adduarmu ba zata fad'i kasa ba. Nace"Nagode sosai ina fatan kin bude akwatin kin duba kyautukan dake ciki. Da murmushi a fuskarta tace"Ban bude ba kada ki manta da zaki fita cewa kikayi sai kin dawo sai mu bude." Mikewa nayi ina yar dariya nace"Da kin sani kin bude kin rigani gani ai kina da iko akan duk abinda ya dangance ni." Tambaya mirmushi tayi ba tace komai ba tabi ta da kallon kauna da tausayi. Cikin nutsuwa na bude akwati nasa hannu ina fito da kayan ciki. Manya manyan lifayu ne guda uku sunyi kyau sosai sun kuma birgeni mutuka sai na dinga hango kaina a ciki nasan zasuyi min kyau kasancewa ta doguwa....sauran kayan na cigaba da dubawa, d'inkakkun atampa guda biyu supar da ingila anyi musu dinkin mutanan Nijar rigunan har gwiwa anyi musu ado da bakin leshi mai tsada... mayafai da takalma biyu sai turare biyu sai set din mayukan shafawa, Tambaya bakinta kasa rufuwa yayi ta kasa daina duba kayan sai farin ciki take tana godiya, ina mirmushi na dauki 'yar karamar akwatin da zoben gold din ke ciki na bude a nutse na fito da zoben ina duba shi sai kyalkyali yake yanda nake jin nauyinsa a hannuna nasan zaiyi kudi sosai Tambaya tace"Kai amma wannnan zoben yana da kyau sosai duba sai kyalli yake." Nace"Tambaya gold ne Mamma ta bani wai nasa a hannuna nayi ado dashi." Tambaya ta kar'bi zoben tana dubawa, kawai sai hawaye ya shiga zobowa a fuskarta, da sauri na kalleta ina mamakin kukan da take. Girgixa kanta tayi tace"Sumayya dole nayi kuka nayi mamaki! yanzu kece zaki saka zoben gold a hannunki tinda nake a masarautar nan ban ta'ba ganin baiwar da tayi ado da gold ba sai *murjani* amma cikin ikon Allah ke anyi miki kyautar zoben gold mai dauke da tambarin masarauta babu shakka Sumayya kin kafa tarihi a cikin bayi. Mirmushi nayi na girgiza kaina ina kara duba zoben ni kaina ina mamakin al'amarin dan sai da ta fada ma sannan na duba zoben sosai naga tambarin masarautar jiki, ajiyar zuciya nayi na zura zoben a ya tsana na tsakiya, sosai yay min kyau na mika mata hannuna, rikewa tayi ta goge fuskarta da fad'in "Yanda kika sa shi bana fatan duk rintsi ki cireshi inaso ya dawwama a hannunki har ranar mutuwarki." Hannu nasa na goge mata fuska da fad'in "Ki daina hawaye rabona ne ya rantse har Mamma tayi min wannan kyautar abinda kawai nake bukata a gurin ki shine addua ki cigaba dayi min akan Allah ya cigaba da bani ikon rik'e amanarta. Hannuna dake fuskata ta rike ta sumbata cikin kauna tace" Sumayya insha Allahu kina tare da nasara a rayuwarki ke kadai muka haifa ke muke gani muji dadi in Allah ya yarda adduarmu sai tayi tasiri a kanki." Murmushi nayi cikin jin dadi mayar da kayan cikin akwati hannu tasa tana taya ni. Babana ma da shigo yaga abin arzikin dana samu yay ta murna yana farin ciki, yace idan anyi sallar isha'i sai na jagorance su suje suyi godiya, haka kuwa akayi muna idar da sallar muka tafi..... Tare muka sameta da yaron nata yana kishingide a gefanta ita kuma tana zaune tana fuskantarsa da alama magana mai muhimanci sukeyi.....a nutse muka gaisa dasu, na kalleta da murmushi a tare dani nace"Ranki shi dade mahaifana sunyi farin ciki sosai da kyautar bajintar da kikayi min dalilin daya sa ma suke ce lallai sai na kawo su sunyi miki godiya bisa alkairin da kikayi min. A nutse ta juya tana kallonsu fuskarta a sake tace"Haba Tambaya ai yarinyarku ta cancanci abinda yafi haka menena na zuwa godiya, ni wallahi Sumayya ta gama min komai data tsaya take kula da Babana babu abinda ba zan iya yi mata ba, saboda haka kada ku damu kanku akan duk wata kyauta da zanyiwa 'yarku domin ta cancani abinda yafi haka. Cike da farin ciki sukayi kasa da kansu suna sake jaddada godiyarsu babana yace."Ranki ya dade kasa hakuri nayi nace lallai ta kawo mu mu mika godiyarmu a gurinki babu abinda zamu ce miki sai dai fatan gamawa da duniya lafiya, muna rokon ubangiji Allah ya tsare gabanki da bayanki Yarima Ali Allah ya kareshi daga sharrin abin'ki.'' Mamma Fulani cikin kulawa take amsawa, kafin ta bamu umarnin tafiya, kallon gefan da yake nayi, tun lokacin da muka shiga ya sunkuyar da kansa gashi har mun 'kare abinda ya kaimu mun mike bai dago kansa ba, hakika wannan 'bakin halin nasa na 'bata min rai! Babana ya durkusa kusa dashi da fadin"Ranka ya dade a tashi lafiya." Dukkaninmu bamuyi zaton zai amsa ba ballantana ya dago kansa, dalilin daya sa ma kenan lokacin daya dago nayi saurin sunkuyar da kaina ina mamaki! "A sauka lafiya nagode." Abinda yace kenan ya mayar da kansa kasa, Sai da mahaifana sukayi gaba sosai kana nabi bayansu, gaskiya naji dadi sosai dana ganshi rad'au dashi! sai na saki raina ina addua akan Allah ya kiyaye gaba. **** Bayan sati biyu al'amura na tafiya sannu a hankali, yanzu ya daina ta'ba min jiki sai dai kullum cikin yi min masifa yake abu kadan idan na kuskure sai yayi min wulakancin da zanji tamkar na dora hannuwana a ka, haka dai nake ta daurewa ina kulawa dashi tare da saka idona akan dukkanin abinda zai cutarshi.....Moddibo yay tafiya shiyasa na dan samu nutsuwa, sai dai Gimbiya Lawisa dake yawan aikowa kirana idan naje zata bani lemo ko farfesu da girke girke tace lallai na bashi yaci jiki na rawa nake kar'ba kafin na fita sai na tabbatar mata da cewar zan cika aikinta, ina fitowa nake samun inda babu idanun mutane na haka rami na zuba a ciki.....haka mukeyi da ita kullum kuwa cikin kallon shashasha nake mata cikin zuciyata ina fadin dama ta daina wahalar da kanta domin na lura koda da asiri a kansa ba zai tank'waru! kamar yanda take so ba, kanyi dariya da mamaki a duk lokacin da zata kawo masa ziyara kullum basa abin arziki ko sun fara hira cikin mutunci ta koma fad'a ya ci mata mutuci tas amma saboda bata da zuciya bata sati zata sake zuwa nayi ta mamakin al'amarin tunda ni dai tunda nake dashi ban ta'ba gani yaje gurinta domin suyi hira ba, a zahirin gaskiya Son da take masa bai kai wanda yake mata ba kamar dai yanda take fad'a kullum shine har yanzu ba ta gane inda ya dosa ba, dariya na kanyi a duk lokacin da tayi wannan maganar a zahiri yana nuna mata bata gabansa amma sai kace dabba ta kasa ganewa. Ina tsaka da aiki ta aiko kirana, nace aje ace mata gani nan zuwa." da sauri na gama had'a fruit salad samun sa nayi a kishingid'e a gurin da yake hutawa, aikin da ya saba yake yi latsa waya, tire din hannuna na ajiye kusa dashi a nutse nace"Ranka ya dade ga fruit salad din na had'a." Wannan karon be k'yale ni ba, naga ya ajiye wayar tare da mi'kewa zaune, gani nayi ya zuba min ido yanayi min kallon da ya jima beyi min irinsa ba, sai jikina yay sanyi na tabbata akwai matsala tunda ya tsareni da ido. "Meye tsakanin ki da Haruna ne? naga yana yawan bin ki kicin idan kina aiki.'' Shuru nayi ina nazarin abinda zance masa. "Bakya ji ne."? a dakile yay maganar yana sake tsareni da ido. Ajiyar zuciya na sauke na dago a nutse nace" Akwai kyakykyawar fahintar juna a tsakanina da Haruna bayan wannan babu wani abunda yake tsakanina dashi. Cikin tsawa yace."Ke kada ki rainawa mutane hankali mana! wace irin fahimtar juna ce wannan? ace kullum yana binki a dik inda kike kada ku sake ku aikata min fasiqanci a guri wallahi tallahi kika sake na kama ku sai na d'auki babban mataki a kanku." Na dinga kallonsa zuciya na tafarfasa tsabar bacin rai naji yawun bakina ya bushe guy nan bai ta'ba 'bata min rai irin yau ba amma bari nayi maganinsa. Babu sukuni nace"Haruna kamaman namiji ne hakanan Sumayya kamammiyar macece, Haruna da Sumayya suna san junansu shiyasa suke nesa da junansu saboda suna so suyi aure mai tsabta, ranka ya d'ade shi fasiqi ya futa daban! ana gane fasiqi a fuska da ayyukansa ba duka mutane suka taru suka zama d'ay......Wawan! duka ya kaiwa bakina nayi saurin kaucewa ina kallonsa, idanunsa naga sunyi jawur! gabana ya dinga bugawa! "Me kike nufi da wannan maganar da kike."? Cikin dauriya nace" Bana nufin komai ranka ya dad'e inaso na nuna maka cewar maganar da kayi a kan mu bata dace ba zargi haram....."Rufe min baki munufaka."!! katseni yay da wannan magana. shuru nayi ina kallonsa, ya jima yana kallon k'asan kilishin da yake zaune, ya dago ido jawur yace."Tashi ki fice min a guri bana bukatar kallon wannan bakar fuskar taki." "Ranka ya dad'e kayi hak..! hannu ya daga min alamun baya so na karasa, shiru nayi na yunkura na mike.." Dauke tsiyarki banza 'kazama kawai."! banji ciwon zagin da yayi min ba saboda na riga na saba, tire din dake gabansa nake kallo a sanyaye nace"Kaine fa kace na had'a maka fruit sal.....Kafin na rufe bakina ya dago tire din ya watso min shi a jiki....gabadaya gaban rigarta da zanina ya 'baci 'kasan gurin da gefan kilishin ya lalace... wayoyinsa ya kwasa yana watsa min kallon banza ya bar gurin....ban dauke idona daga kansa ba har sai da na daina ganinshi....hawayen takaici ne suka shiga zubo min a fuska durkushewa nayi a gurin na dinga kukan da yake nema ya tarwatsa min zuciyata. *Na kudi ne..* Koda zaki ganshi a gruops na sata ne idan kina so ki biya kudin ki ga yanda abin yake....Vip gruop#600 normal #300...0542382124..binta umar gtbank idan kati zaki turo #400 sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number. *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *GAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 55&56 Samun sa nayi a tsaye a tsakiyar falon yana zagaye koda na shiga gefe guda na samu na tsuguna kaina na sunkuyar k'asa ina addua kada Allah yasa ya tozartani a gabanta dan na fahimci take takensa. bece min komai ba ya zauna kan kujera tare da d'ora kafa daya kan daya zaman yayi kama dana kasaita da nuna isa, ta kasan idona nake kallonsa yana ta girgiza kafa yana latsa waya, haka ta shigo ta same mu, kujera ta nema ta zauna, falon yayi shuru na tsayin minti goma a sace na kallesu shi yana can aikin latsa waya ita kuma alamun tsoro da fargaba na hango a cikin idonta. kaina na mayar kasa ina jin faduwar gaba, ni da ita duk abu daya ne yake damun mu. "Lawisa me Sumayya tayi miki da zaki sa Buba ya doke ta ."? A sanyaye tace" Laifi tayi min wanda ya fusata ni shine na yanke mata wannan hukuncin.'' "Ba kwana ki nayi miki magana akan hakan ba."? Yafada yana tsareta da ido, cikin dauriya tace" Naso nayi mata hukunci da kaina tayi min gardama shiyasa na kira buba ya koya mata hankali tunda dai ita bata da mutunci. Saurin kallonta nayi muka hada ido ta watso min harara, kaina na sunkuyar ina jiran naji abinda zaice. "Me tayi miki abinda nake son ji kenan."? yafada hankalinsa akan wayarsa.....ajiyar zuciya ta sauke tace" Yau tsayin wata kenan ina aikota ta kawo maka sa'ko ashe zuwa take ta zubar a wani guri daya daga cikin bayina suka sheda min koda na tambayeta ba tayi gardama ba ta tabbatar min da gaskiya ne al'amarin ya 'bata min rai sosai shiyasa na yanke mata wannan hukuncin." Kallona ya shigayi yana gyada kansa yace."Wato ke ba zaki daina saka kanki a cikin abinda be shafe ki ba ko? shuru nayi yace."Me kike nufi akan abinda kike aikatawa ke kowa baki yarda dashi ba 'yan uwana zarginsu kike yi ke yafi kamata nayi zargi tunda kece bare amma na amince nake tarayya dake ban nuna miki komai ba to ki tashi ki fita ki bani guri bana bukatar sake ganinki a gurina dan na gaji da abinda kike min." kallonsa nake inaso nayi magana ya daga min hannu fuska a murtuke yace "bana bukatar sake ganinki a sashena 'yan uwana nawa ne idan kashe ni sukayi babu abinda ya shafe ki saboda haka tashi fice min daga falo."! Cikin tsawa da kyara ya kare maganar. Ji nayi gwiwa ta tayi sanyi ruwan hawaye ya taru a kwarmin idona ni kam wannan wulakanci ina zan kai shi, a sanyaye na mike na nufi kofa zuciyata na wani irin zafi......ina fita hawaye ya wanke min fuska, haruna ya tare ni guri muka samu muka zauna sai da nacu kukana na koshi tukkuna na fada masa yanda mukayi. Yace." Ki daina kuka kada ki janyowa kanki ciwon kai ni wallahi naji dadi ma da haka ta faru saboda haka yanzu abinda za'ayi shine kije can sashen Fulani ina nufin mahaifiyarsa sai ki sheda mata abinda ke faruwa kin san hausawa nacewa ta inda aka hau tanan ake sauka. Hanci na shaqa na goge fuskata tare da mikewa tsaye nace" dama dole naje na sanar mata dan saboda kada wani abu ya faru daga baya ta zarge ni da wani abu. Mikewa yay yace."Muje na raka ki ki fada mata." Tare muka tafi muna sake tattaunar maganar. Ta jima kafin ta dago kanta ganin b'acin rai a fuskarta yasa na sunkuyar da kaina kasa, tace"Sumayya duk naji maganarki raina kuma ya 'baci da irin wulakancin da babana yake miki yanzu ina laifin mai kula da kai abinda babana yayi miki ya bata min rai sosai kiyi hakuri Sumayya kada kiyi fushi kinji ko zaki cigaba da hidima dashi wallahi da ke kadai naji na aminta, ita kanta yarinyar da zai aura bata kwanta min a rai ba dan dai babu yanda zanyi ne tunda iyaye sun shiga cikin lamarin, zan sameshi zanyi masa fada sosai dole ya mutun taki ko dabbah ai tasan mai kyautata mata bare mutum saboda haka kije yanzu zan kirashi a waya zan zauna dashi zamuyi magana kuma zan nuna masa kuransa. Daurewa nayi ina kokarin danne damuwata nace"Insha Allahu zanbi umarninki zan cigaba da dawainiya da Yarima kamar yanda kike so." Albarka ta dinga sa min kafin ta bani umarnin tafiya sallama nayi mata na fito Haruna na tsaye yana jira na ina fitowa na fada masa duk yanda mukayi jikinsa ne naga yayi sanyi yace."Shikkenan Sumayya sai ki sake kiyayewa sannan ki daina yawan saka idonki akan 'yan uwansa tunda baya so ki rabu dashi idan da rabon yasha wuya ne shikkenan." Shuru nayi kawai ina sauraransa bana jin zan iya zuba ido wani ya cutar dashi amana na daukarwa mahaifiyarsa zanyi iyakacin bakin k'okarina sai dai idan abin yafi karfina A waya ta kira shi ta rufeshi da fad'a ta inda ta shiga bata nan take fita ba sosai ta nuna masa bacin ranta akan abinda yake yi mamaki ne ya rufeshi ashe yarinyar nan zuwa tayi ta had'ashi da mahaifiyarsa ransa idan yay dubu ya 'baci! tunda yake da mahaifiyarsa wani abu na sa'bani bai ta'ba shiga tsakaninsu ba sai ta dalilin yarinyar.....Girgiza kansa yayi ya shiga bata hakuri tace"Haba babana ai dole raina ya 'baci akan abinda kakeyi yarinyar nan kullum na dawainiya da kai amma kullum cikin cizguna mata kakeyi su 'yan uwan naka da kake fifitasu a kanta ba kaunarka sukeyi ba har yanzu ka kasa ganewa cewar kullum farautarka suke to mutukar kana kaunar farin cikina ka mutunta Sumayya bana san cin zarafin da kake mata ka sanja hali." Ajiyar zuciya ya sauke yace."Mamma naji na d'auki laifina insha Allah zan gyara na daina bana san kina fushi da 'bacin rai akan abinda bai kai ya kawo ba." "Babana idan ka naso na daina bacin rai sai ka daina abubuwan da kake na rashin kyautawa tukkuna." Hannuwanta ya ri'ke yace."Insha Allahu na daina yarinyar ta dawo ta cigaba da aikinta shikkenan ko."? Ajiyar zuciya ta sauke tace"Shikkenan magana ai ta wuce na bata hakuri sosai anjima da daddare zata shigo ta baka abinci kaima sai ka nemi afuwarta dan Allah yana san haka. Da mamaki a fuskarsa yake kallonta har abadah baya tsammanin zai iya bawa yarinyar hakuri akan wani laifi da yayi mata kawai dai ya amsa mata ne domin ta kwantar da hankalinta ta kuma daina 'bacin rai akan al'amarin. To koda na koma gurin mu ban yarda na fadawa iyayena abinda ya faru ba kawai nace musu nayi mata wani aiki ne...Tambaya tace"Muna nan muna tattaunawa akan maganarki da Haruna dan gidan Labaran bayan fitarki yazo gurin babanki suka tattauna ashe dama soyayya ce a tsakaninku mu bamu sani ba." Kunyace ta rufe ni nayi yar dariya ina kokarin shiga daki nace "Tambaya kenan." Babana dake zaune kan darduma yana murmushin farin ciki yace."Sumayya a gaskiya nayi farin ciki da wannan al'amari sosai na yaba da tarbiyar Haruna yana da nutsuwa da kintsi nayi imanin zai rike min ke da mutunci wannan dalilin yasa na amince da maganar amma na cewa mahaifin nasa sai na zauna dake kin sake tabbatar min da bakin ki. Shuru nayi ina wasa da hannuwana, yace."Sumayya babu kunya a tsakanina dake ni mahaifin ki ki fada min shin kina son Haruna ko aa." Murmushi nayi nace"Eh baba ina sonsa ina rokon Allah yasa shi din alkairi ne a tare dani." cike da farin ciki ya amsa da ameeen Sumayya ubangiji Allah ya tabbatar mana da alkairi Allah yasa damu za'ayi." Mikewa nayi ina jin kunya da nauyi na shiga daki, kayana na tube nayi shirin wanka.......Bayan nayi wanka naci abinci gurin karatu na nufa karfe biyar da rabi mun taso Lahira na bawa jakata nace ta kai min gurin mu kai tsaye sashen Yarima na nufa A falo na same shi yana kallace-kallace a tv gaishe shi nayi ya'ki amsawa mikewa nayi na nufi kicin na shiga aikina............Tsaf na shirya mai abinci na jera komai kan tire mai fadi ina kokarin dauka ya fad'o kicin din. Gabana ne ya fadi da sauri na risina ina gaishe shi, sama-sama ya amsa yace."Yawwa kin gama abincin ko."? kaina na daga masa gabana na bugawa. Wata yar takarda ya ciro daga aljihunsa ya kwance cikin bada umarnin yace."Bude abincin.'' a sanyaye na bude fulas din, maganan ya zazzage a cikin miya yace ."Sa cokali ki juya sosai." da sauri nayi yanda yace."maza dauki muje." da sauri na rufe fulas din na dauki tire din hanya ya nuna min da hannunsa, na fito falon ina diri-diri!! cikin tsawa! yace."Wuce muje sama ki kai masa abincin yana can mutukar naji maganar nan ta fito sai na kashe ki." Da sauri na shiga hawa benan har ina had'awa da biyu, shawarwari nake da zuciyata shawarar karshe na yanke da zuciyata, da gangan na gurde kafata na fadi a gurin sosai na bugu da karfen benan tire din abincin da abubuwan dake kai suka watse a gurin fallatsin miya har jikin rigarsa. Cikin zafi nama ya mi'kar dani tsaye! wuyana ya matse yana tsuma yace."Kina sane kika zubar da abincin nan ko."? idanuwana sun gwalalo waje sabida wahalar sha'ka na girgiza kaina, alamun A'a, hannu ya fitar ya tsinka min mari wanda sai da hancina ya fashe na dinga jin dummm! a kunnena! dishi dishi nake kallonsa yana wani irin huci!! ya sake fitar da hannu zai mare ni, Yarima ya bude ya kofar dakinsa Ganinta sha'ke a hannun Muddibo yasa da sauri ya k'arasa gurin kokarin cire hannunsa yake daga wuyana yana sake matse ni.....cikin b'acin rai yace."Muddibo wai me tayi maka ne ka matse mata wuya haka."? Yana huci yace."Ka duba jikina da kyau ka gani yarinyar bata san ta ratse a wani a gurin na wuce ba ta hada kafada da kafada dani har sai da ta samu nasarar 'bata min jiki da miya." Kallon jikinsa yayi yaga duk jar miya a jikin rigarsa hakuri ya shiga bashi yana kokarin cire hannunsa dake d'amke da wuyana, da kyar Muddibo ya cika ni na zube a gurin ina tari makogwarona ya bushe sosai sai zare ido nakeyi ina kallonsu suka sauka k'asa a tare, sunkuyar da kaina nayi ina kiran sunan Allah a cikin zuciyata. *Na kudi ne* Kika karanta baki biya ba Allah ya isa! idan kina so ki biya ga yanda abin yake...Vip group #600 normal gruop#300 account....0542382124...Binta umar gtbank.....idan kati zaki turo #400 sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 57&58 Sai da na samu nutsuwa tukkuna na mike jikina a mace na sauka 'kasa sunkuyar da kaina nayi ban yarda na kalli inda suke ba na wuce kicin tamkar kazar 'kwai ya fashewa a ciki. gabadaya jikina ya mutu ina tunanin da Muddibo ya samu nasara kashe ni yayi niyyar yi, tsintsiya da abin kwasar shara na dauko ina fitowa muka hada ido dashi, ganin fuskarsa nayi tamkar hadarin dake daf da zubar da ruwan sama da sauri na janye idona cikin zuciyata nace''duk wani abu da nake akanka inayi ne domin mahaifiyarka daba dan daraja da mutuncinta ba wallahi da bazan zauna ina wahalar da kaina ba......gurin na gyara tsaf nayi mopping dinshi ina kokarin sauka kasan sai gashi, ratsewa nayi na bashi hanya yazo daidai dani yana hararata da fadin"Na dauka nima kafad'a da kafad'ar zakiyi dani." Sunkuyar da kaina kasa nayi ina Allah-Allah ya wuce dan bana bukatar tashin hankali "Kizo ina san ganinki." Da sauri na dago kaina naga ya wuce ni yana kokarin bude dakinsa, sai da ya shiga tukkuna na ajiye mopper hannuna bayansa nabi ina adduar rinjaye. Samun sa nayi kan sofa yayi zaman kasaita na tsuguna dan nesa dashi babu walwala a fuskata nace"Gani." sai daya mula tukkuna yace."Ashe haushi kika ji dan na kore ki daga sashena shine kikaje kika hadani da mahaifiyata ko."? Babu fara'a a tare dani nace"Banji haushi ba wallahi sai ma farin ciki da nayi naje na fad'awa mahaifiyarka ne domin yana da kyau ta san cewar ka kore ni tunda itace ta turo ni nayi maka hidima ni ban fada mata domin na shiga tsakaninku ba." Tsaki yaja yana min kallon kaskanci yace.''Ke dai kika sani munafuka kawai tunda kin nace sai kinyi min aiki sai kizo na saki aikin kuma wallahi kikayi min gardama ranki sai ya 'baci.'' "Ranka ya dade ko wane irin aiki ka sanya ni zanyi maka mutukar bai sha'ba sharia ba." Shuru yayi min yana duban k'asa nasan idan ya tsirawa kasa ido yana daukar lokaci yasa nima na dauke kaina ina jiran ya gama. sai da ya dauki mintina goma tukkuna yace."Shiga toilet ki hada kananun kayana ki wanke." ba tare da nace komai ba na mike na nufi toilet din.....Bin bayanta yayi da kallo har sai da ta shige ya dauke idonsa shi dai ya rasa yanda zaiyi da rayuwarsa sha'awarta kullum karuwa take yayi yayi ya cireta daga ranshi abin ya fassakara ya rasa wace irin masifa ce Allah ya dora masa. Duk kananun kayansa dake toilet din sai da na wanke tas na shanya inda aka tanada toilet din na gyara yayi tsaf tsaf dashi na fito na same shi zaune a inda yake ya kurawa tv ido.....nishin dake tashi a cikin tv yasa nai saurin kallon gurin mace da namiji ne suke sex sai nishi suke namijin yana kan macan ta daga kafafunta sama shi kuma sai bugunta yake tana nishi hade da sambatu. Da sauri na dauke kaina ina fadin"Subahanallahi! kallonsa nayi naga idanuwansa sunyi jajawur! ya k'ura min ido yasa lips dinsa na kasa a baki yana tsotsa, tsorata nayi da yanayin sa nayi gaggawar kama hanya domin fita daga dakin wata zuciyar tace "Ki tsaya ki tunasar dashi abinda yake aikatawa bai dace ba. Juyowa nayi still idonsa na tsaye a kaina, nace" Ranka ya dade kaji tsoron Allah kaji tsoron ranar haduwarka dashi, wallahi wannan abinda kakeyi sam bai dace da kai ba, yanzu meye amfanin ganin tsaraici Allah ya la'anci mutanan dake ganin tsaraicin wani wannan dan abun daka raina yana iya janyo maka fushin Ubangiji ranka ya dade a daidai wannan lokaci ya kamata ace kana massalaci kana salati kafin a kira sallar amma ka zauna kana kallon shed'anu kafurai wa'inda Allah ya la'ance su fisibilillahi meye fa'idar abinda kake aikatawa." Har na kare maganata idanuwansa na tsaye a kaina. ganin bece min komai ba yasa na girgiza kaina na kama hanya zan fita. A sanyaye naji ya kira ni "Sumayya." juyowa nayi a karo na biyu ina kallonsa, nadama nagani a fuskarsa, yace."Zo nan muyi magana." Zuwa nayi na durkusa gefansa ina addua Allah yasa ya dauki nasiha ta. "Zoki zauna nan muyi magana." kusa dashi ya nuna min wai naje na zauna, gaskiya ba zanje ba dan ina tsoron abinda zai biyo baya. "Ranka ya dade ba sai nazo kusa da kai ba zan fahimci abinda xaka fada kunnuwana naji duk abinda zakace." romot ya dauka ya kashe tv kana ya juyo yana kallona, ni kallon da yake min shine yake d'aga min hankali dan a tsorace nake a dakin. Sai da ya gama kallona tukkuna yace."Naji nasihar ki nima kuma nasan abinda nake yi bashi da kyau na rasa yanda zanyi ne Sumayya a duk lokacin da kika gifta ta gabana sai naji sha'awarki a yanzu bani da muradin ko wace mace sai ke na roke ki ki bani kanki na rana guda na biya bukatata." Ji nayi gumi na tsatstsafowa daga jikina kallonsa kurrum nake ina mamakin maganarsa, kallon da yake min shine ya tabbatar min da gaskiyar maganarsa duk ya koma kalar tausayi sai marairaice fuska yake yana kankantar da idanuwansa.......sunkuyar da kaina kasa nayi ina tunanin abinda zance masa, motsinsa naji a kusa dani da sauri na dago kaina ido muka hada yana gurfane a gabana ya wani zuba min idanuwansa kamar zai cinye ni. Cikin wani irin yanayi na fargaba da tashin hankali nace"Ranka ya dad'e nasha fada maka baza ka samu abunda kake so ba, ni bana daya daga cikin irin matan dake sarayar da kima da mutucinsu inaso jikina da komai nawa ya zama mallakin mijina na sinna dan girman Allah da darajar Annabi kada ka sake yi min irin wannan maganar wallahi tallahi bazan ta'ba amincewa bukatarka ba kayi hakuri da maganata ranka ya dade kayi na farko kayi na biyu idan ka kuskura kayi na uku zan samu mahaifiyarka na fada mata abinda ke faruwa ka rabu dani da wannan maganar." Ido jawur nakare maganata inaso na tabbatar masa da cewa daf nake dana tona masa asiri. a maimakon ya saduda sai ya sake kusanto ni ya matseni jikin kujera yana min wani shu'umin kallo gabadaya ya fita daga cikin hayyacinsa dan da alama ma bai ji barazana ta ba. tureshi nayi ina kokarin mikewa ya rike hannuwana tsam na dinga kokarin kwacewa karfin ba daya bane hawayen fargaba ne suka soma zubo min. Kirjina ya ban'kare min ya tsirawa nonuwana ido ajiyar zuciya ya sauke ya d'ora fuskarsa a kan kirjina yana wani irin abu, wani irin abu naji ya tokare min a wuya, hannuwa nayi yun'kurin kwacewa ya rike sosai ya cigaba da goga fuskarsa a kirjina sai nishi yake fitarwa. Ya kai minti biyar yana iskancin da yake so kafin ya dago kansa, yawun bakina na tofa masa a fuska ina masa kallon banza nace"Yanzu me kaji da akayi hakan wato kai kai baka jin nasiha ko? kasan gaskiya kasan abinda kake aikatawa haramun ne shine ka ban'kare min kirji kana iskancin da kake so Allah ya isa." Ajiyar zuciya ya sauke yace."Sumayya idan baki rufe bakin ki ba wallahi zanyi miki abinda yafi haka! har ni kike tofawa yawu saboda kawai ina bukatarki to idan baki fadawa mahaifiyata ba bakya kaunar Allah da annabi." "Kaga yallabai sakar min hannu tunda kayi abinda kake so." a zafafe nayi maganar.....hannuwana ya sake d'amkewa yace."Wannan tsiwar taki ita zata janyo miki komai nifa ba cewa nayi sai na shiga ramin ki ba ki bani wannan kawai ya isa ya gamsar dani." Yana maganar yana kallon kirjina. Shuru nayi zuciyata sai tunzurani take...."Sumayya ki taimaika min dan Allah ki bari na samu satisfaction dake ba zan rabaki da budurcin ki ba." Hawayen da nake makalewa suka zubo a kumatuna ni yau na rasa wane irin mutum Allah ya had'ani dashi wannan wane irin naci ne? hawayen fuskata ya shiga lashewa yana tsotsar kumatuna, na dinga jin tsigar jikina na tashi bakina yake so ya kama na kautar da fuskarta, hannu yasa ya juyo da ita, muka dinga kallon juna, ''Kin amince ko."? cikin mayaudariyar mirya yayi maganar." Girgiza kaina nayi nace"Ban amince ba." mirya na rawa yace."To yanzu ya kike so ayi ni dai ba zan bari ki fita ba sai bukatata ta biya." shuru nayi ina shawarwari da zuciyata nace"Ranka ya dad'e sha'awata kake ba sona kake ba ko."? Eh ina sha'awarki Sumayya ki bani jikinki na biya bukatata." na dinga kallonsa ina mamakin maganarsa..."Na amince zan baka jikina ka biya bukatarka amma ta hanyar aure." da sauri ya kalleni, kaina na daga masa nace"Ka aure ni na amince idan bukatarka ta biya a kaina ka sake ni ina ganin haka shine mafita. Ina sane nayi masa wannan maganar saboda nasan abin ba zai yuwu ba. "Ke a ganinki ni na dace da zama mijinki.''? cikin izgilanci yay maganar. Nace" Be dace ba amma ai kaji abinda nace ko nace idan bukatarka ta biya sai ka sake ni nidai ba zan baka kaina ba sai da aure. Tsaki yaja da fadin''Ke bana san ki 'bata min rai ki sanja wata shawarar wannan ba tayi ba ni ba sa'an auranki bane kin gane ko.''? nace"To shikkenan sai ka danne sha'awarka a kaina tunda ka ki'yin yanda nace." Bina yay da kallo yace."ba zan aureki ba saboda baki dace dani ba ta kowane fanni kawai ki gindaya kudin da kike bukata sai na biya mutukar zaki mallaka min albarkatun jikinki. Cikin zafin zuciya na ture shi na mike tsaye "Bana bukatar komai a gurinka na yanke shawara idan ba tayi maka ba sai kayi hakuri ." Kafata ya janyo da karfi na fada kansa matse ni yay a jikinsa daidai kunnena yace."Bafa fin karfina kikayi ba wallahi yanzu zanyi miki rashin mutunci ." Imani na cire na dasa masa hakora na a wuyansa, da sauri ya sake ni yana yamutsa fuska, da sauri na dauki dankwalina na daura na fita daga dakin, duk rintsi na daina shiga dakinsa sai dai duk abinda zaiyi min yayi. Sai da muka dauki tsayin sati biyu bama magana da juna kullum idan na shiga sashen aikin gabana nake nayi tafiyata shima nasa bangaran fushi yake dani sosai dan har na gama aikina baya kallon inda nake kullum fuskarsa a murtuke, sai dai duk sanda Gimbiya Lawisa ta kawo masa ziyara ina shan dariya dan kafin su rabu sai sunyi fada yafi a 'kirga sam bata da zuciya sai tayi ta bashi hakuri alhalin duk rabin laifin nasa ne amma sai ta dauka ta dorawa kanta cikin zuciyata nace aiki ya same ki. Hidima ce ta tashi a gidan sarautar sai shirye shirye ake ana gyara gurin da za gudanar da gagarimar Walimar da maimartaba ya shirya domin murna bud'e katafaran asibitin daya ginawa yaron nashi, hankalin Uwargida da 'yayanta ya tashi suka dinga sintiri a gidan suna 'kulle-'kullen yanda zasu tarwatsa taron jama'ar da maimartaba ya gayyato domin su tayashi farin ciki......Muddibo ya zama tamkar mahaukaci sai shige da fice yake gurin malamai burinsa kawai bukatarsa ta biya Gama aikina kenan na fito da niyyar tafiya aunty Safiyya ta shigo, har 'kasa na durkusa na gaisheta, ta amsa a lokacin da take kokarin zama kan kujera, mikewa nai tsaye tace"Yarima na sama."? da sauri nace"E ranki ya dad'e." Tace."Je kice masa nazo yazo mu gaisa." Da sauri na amsa da to. Aunty Safiyya na ganin 'bacewar Sumayya da sauri ta mi'ke ta isa bakin benan ta shiga barbad'a wani abu tana yi tana kiran sunansa, sai da tayi sau bakwai tukkuna ta koma ta zauna. Bubbuga kofar dakin nayi gabana na fad'uwa! ciki ciki naji maganarsa, nace"Ranka ya dade aunty Safiyya ce tazo tana falo tana jiranka." "Gani nan." abinda ya fada kenan. nayi saurin barin gurin, samun ta nayi tana duba wayarta nace"Ranki ya dade gashi nan zuwa." Tace."Okey kawo min ruwa." da sauri na nufi kicin domin cika umarninta. Hannuna ri'ke da tire me dauke da goran ruwa da kwalin lemo na fito daga kicin din daidai lokacin da yake kokarin saukowa hawa biyu ya taka amma sauran be iya ba takawa ba kansa ya dinga juyawa yana ganin dishi dishi kafin nayi aune kawai na hango shi yana gangarowa! salati na kurma tire din hannuna ya fadi a guje na nufe shi ina kiran sunansa, duk tsayin benan da yawan steps haka ya dinga gangarowa yana buge kansa, zuwa nayi domin tareshi kafin nayi wani yunk'uri ya tunkud'e ni na fad'i a gurin tare muka dinga gangarowa har sai da muka dire kasa, na mike zumbur! ina nishi da salati! aunt Safiyya ta karaso gurin sai salati take tare muka isa inda yake kwance tamkar wanda ya mutu haka yay numfashinsa sai fita yake da sauri, wasu hawayen fargaba da tashin hankali ne suka shiga zubo min....."Ke! maza jeki dauko ruwa suma yayi." miryar ta ta dawo dani da sauri na bar gurin.....Tun daga nesa na hange ta tana danna kirjinsa tare da kara kunnanta a kirjinsa.. murya na rawa nace"Aunty ga ruwan! kar'ba tayi ta bude ta shiga shafa masa a fuska, shuru be farfado ba, jikina na rawa nace"Ranki ya dade ko naje na fadawa Mamma." Girgixa kanta tayi tace"Zo ki cigaba da shafa masa ruwan bari naje na sanar da maimartaba." Da sauri na zauna inda ta tashi na cigaba da shafa masa ruwan a fuskarsa kuka kawai nake ina tofa masa addua, kansa na tallafo na rungume a kirjina goran ruwan na ajiya na cigaba da tofa masa duk adduar da tazo bakina gabadaya na kasa tsayar da hawayen dake zuba. Zazzafar ajiyar Zuciya ya sauke naji yayi motsi, da sauri na kalli fuskarsa naga ya bude idonsa Allah na godewa kana na kira sunansa, "Ranka ya dade sannu me yake damunka." jikinsa ya cire anawa ya tsira min ido minti biyu kafin yace."Me ya faru jikina ciwo yake min.'' naji wani irin rauni gami da tsabar tausayinsa. " Gangarowa kayi daga sama." nafada ina goge hawayen dake zubo min.'' juyawa naga yayi yana kallon tsayin benan.'" Ya juyo nai saurin kauda kaina...."Ina aunty Safiyyan." ? "Taje kiran Maimartaba." mikewa yay yace."Zoki hada min ruwan zafi na gasa jikina kamar anyi min dukan tsiya haka nake ji.'' Na mike da sauri na rike hannunsa, kallona yayi nace."Kada ka sake hawa benan ka zauna a falo." "Sabida me."? ya fada cikin sigar tuhuma! cikin fargabar masifar sa nace ni dai nace kada ka hau." Kasa yayi da kansa yana nazari kafin ya cire hannunsa yaje ya zauna a kan kujera, da sauri na nufi kicin......kanwa na jika a madaidaicin bokiti na fito benan na nufa da addua a bakina na shiga bin Steps d'in one by one ina yayyafa ruwan kanwar ina addua a bakina, sai da ruwan kanwar ya bushe na same shi a zaune a inda yake nace"Kana iya hawa." mikewa yayi ba tare da yace komai ba ya nufi saman nace"Ranka ya dade ka hau kana karanta ayatulkursiyu." bece min komai ba ya fara hawa steps din. ajiyar zuciya na sauke bayan hawansa Allah nagodewa kana nabi bayansa domin hada masa ruwan wankan daya b'ukata.. *Na kudi ne..!* Kika karanta baki biya ba Allah ya isa, idan kina so ki biya kudinki ga yanda abin yake...Vip gruop#600 normal #300 account... 0542382124....Binta umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 59&60 Tsaye na sameshi a bakin toilet din kallona yake har na karaso kusa dashi ina kokarin shige shi na shiga toilet din ya tare hanya, kallonsa nayi gabana na fad'uwa yace."Ki fada min gaskiyar abinda ya faru dani." Nace"Ranka ya dade abinda na sani shi na fada maka gangarowa kayi daka sama." Okey to meye amfanin abinda kika yayyafa a jikin steps. " yafada yana tsare ni da ido, duk sai naji gwiwata tayi sanyi ina jin tsoron kada ya zargeni da wani abun nace''Ruwan kanwa ne na yayyafa." "Kina nufin me kenan."? haushi ya bani nace" Dan Allah ka bar maganar tunda dai Allah ya kare shikkenan." Shuru yayi yana kallona sauri nayi na shiga toilet din bayana ya biyo koda na ganshi a tsaye yana kallona sai na sake tamke fuska na hada masa komai na wankan da sauri na fita. Wanka yake yana tunanin al'amarin jikinsa ya soma sanyi ya kuma soma gazgata abubuwan dake faruwa 'yan uwanshi na kokarin suga bayanshi ya rasa me yasa suka damu dashi da duk abunda ya Shafeshi sarauta suke so shi kuma baya so sune suke wahalar da kansu a banza. Na jima zaune a falon ina jiran dawowar aunty Safiyyar shuru har kusan mintina talatin bata dawo ba cikin zuciyata nace dama karya take babu wanda zata kira, ajiyar zuciya na sauke ina mamakin al'amarin babu shakka wani mugun abun ta shigo dashi gashi nan yaso yayi tasiri a tare dashi mikewa nayi da fadin''Insha Allahu haka zaku gaji ku bari, gurin mu na nufa ina cike da mamakin al'amarin. Aunty Safiyya tare da mahaifiyarta suna zaune suna sake tattauna maganar , tace"Nasan da wuya ya tashi dan lokacin dana fito daga sashen numfashinsa ya dauke jikinsa ya saki." Uwargida tace"Koda Allah yasa zai tashi to fatanmu ya tashi da nakasa so nake wani sashe na jikinsa ya lalace kafa ko hannu." Aunt Safiyya ajiyar zuciya ta sauke tace''Bari na koma sashen nasa domin ganin abinda ke faruwa. Lokacin da ta shiga falon shuru taje ta tsaya a inda ya fadi tana mamakin ina yake, motsin saukowarsa taji tayi saurin daga kanta ganinsa tayi yana saukowa cikin kwalliya kamshin turaransa har inda take. Gabanta ya dinga faduwa tana kallonsa yana saukowa sai murmushi yake mata, gwiwa a sanyaye tace"Kanina.'' yace."Na'am aunt Safiyya zauna mana kin tsaya." kujera ta nema ta zauna tana kallonsa ya zauna a kujerar dake fuskantarta, gaisheta yayi ta amsa jikinta sanyi kalau tace" Amma nayi mamakin ganin ka a haka dazu fa yanke jiki kayi ka fado daga sama, na fita a gigice domin naiman taimako abin mamaki kuma yanzu na ganka radau. Yace."Nima a jikina naji abinda ya faru sai bayan na dawo daidai nake tambayar hadimata take sheda min abinda ya faru." Girgiza kanta ta shigayi kafin tace"Allah ya kiyaye gaba." "Ameeen yace yana nazarinta ya soma hango rashin gaskiya a tattare da ita....gyaran murya yayi tayi saurin kallonsa yace." Aunt Safiyya na rasa abinda nayi wa mutane suke son suga bayana." Taji gabanta ya fadi jin abinda yace tace"Yarima ai dole mutane su nuna ganin kyashin su a kanka kai dai ka dage da addua.'' Murmushi yayi yace."Addua kullum cikin yinta nakeyi kuma a matsayinku na 'yan uwana ku tayani." tace"Kada ka damu dan uwana." Shuru falon yayi yace."Kin same aunt." girgiza kanta tayi yace."Na soma zargin wannan hadimar tawa domin dazu na ganta tana yayyafa wani abu akan stpes." yana maganar yana kallon reaction dinta ta dinga kallonsa bakinta na rawa tace"To me take yayyafa wa ? kaji shegiya ko ta hada baki da wani a cikin gidan nan dan cutar da kai."? Yace."Nima abinda nake zargi kenan." mikewa tayi zumbur ta nufin benan ta hau duddubawa! nan ta gane *kanwa* yarinyar ta zuba dan duk ga alamunta nan, lallai yarinyar nan bata da mutunci ta karya musu aiki, a sanyaye ta juyo suka hada ido dashi nan ya sake tabbatar da zarginsa gaskiya al'amarin ya bashi mamaki mutuka. Zama tayi tana xage zage da fadin"Lallai sai ta tura an kira mata yarinyar ta turketa domin ta fada mata wanda ya turo ta ta zuba masa magani. Yace."Aunt Safiyya ki barta kawai ni zan koya mata hankali daga yau ta bar aiki a sashena, tace."Eh dama hukuncin da zaka yanke mata kenan ni da kaina zan duba wacca ta cancanta ta kula da kai anjima zamu tare Yace."To shikkenan godiya nake." Hira sukayi sama sama tayi masa sallama ta tafi, tana fita ya shiga mamakinta gabadaya yanayin data nuna ya tabbatar masa da rashin gaskiyarta, yana sane ya juya maganar kan Sumayya ya nuna ita yake zargi domin kawai yaga yanda zata nuna. Shatima ne yay sallama ya shigo ya samu guri ya zauna yana kallonsa yace."Na ganka kamar kana da damuwa ina fatan ba aunty Safiyya bace dan naga fitar ta rai a bace. Shuru yayi na minti uku kafin yace."Shatima al'amarin gidan nan yana bani mamaki mutuka ashe har yanzu ba zamu daina cin dunduniyar junanmu ba! ashe ba zamu kaunaci junanmu ba shin wai me muka mai da mulki ne? kowa babu alkairi a zuciyarsa kullum kudirinsa ya za'ayi ya cutar da jininsa ni aunty Safiyya ta shigowa guri da surkulle bansan me take nufi dani ba." Shatima yace."Kayi min bayani yanda zan fahimta wane irin surkulle aunty Safiyyan ta shigo maka dashi."? ajiyar zuciya ya sauke yace."Ina kwance a daki yarinyar nan Sumayya ta shiga take sheda min zuwanta lafiya lau na fito a dakina ina fara saukowa na fita daga hayyacina a yanzu zancan da nake maka jikina ciwo yake min. Shatima mirmushin takaici yayi yace."Yarima kenan wato kai ka dauka zaka zauna lafiya a masarauta ko? to bari kaji na fada maka abinda ka tafi ka bari yana nan sai ma abinda ya k'aru Uwargida da 'ya'yanta suna nan suna shirya mugun abu Baba Ciroma da iyalinsa suma suna nan akan bakansu.....Baba Galadima shine mahaifina shima bazan rufe maka ba baya kaunarka dan saboda suna ganin kai zaka gaji sarauta dukkaninsu sunfi so saurauta ta dawo hannunsu saboda haka sai ka kula da kyau ni dai bana cikin tsarinsu dan mulki sam be dame ni ba shiyasa idan naga Muddibo na hauka yake bani mamaki Wallahi ni nafi bukatar kasuwanci na yafi min komai. Yarima ajiyar zuciya ya sauke yace." Shatima su suka damu da mulki kasan Allah mulki baya gabana nafi bukatar na tsaya akan aikina na taimakon marasa lafiya nayi mamaki sosai da jin wannan magana, Muddibo duk yanda muke dashi ashe adawa yake dani." Shatima yace."Ban fada maka wannan magana ba dan ka 'kullace su inaso dai ka kula sosai ka daina sakewa da duk mutanan dana lissafo maka wallahi basa kaunarka Waziri da iyalinsa ne kawai ke kaunar cigabanka." Yarima Ali shiru yayi yana mamakin al'amarin Shatima yace."Shiyasa fa sam banyi na'am da auranka da Lawisa ba nasan zasu Iya Shiryo wata ma'karkashiyar ta 'bangaranta." Da sauri yace."Ni dama sam yarinyar ba tayi min ba wallahi tunda abun ya zama haka zan samu maimartaba akan maganar. Shatima ya girgiza masa kai da fadin"Kada ka yanke wannan hukuncin tunda dai an riga an tsayar da magana sai kayi hakuri kasan ko kaje ka cewa maimartaba ka janye ba zai yarda ba sai anyi." Shuru yayi yana tunanin maganar. Washe gari da sassafe na tashi nayi mana Wanki nayi wanka na fito ina tsaka da shiryawa Tambaya ta shigo dakin ta same ni, tunda na ganta a sanyaye nasha jinin jikina tace"Sumayya jikina yayi sanyi jin Uwargida ta aiko kiran ki. Gabana ya fadi jin abinda tace nace''Yaushe ta aiko." Tace"Yanzu yanzu. cikin tararrabi da faduwar gaba nace"Ki kwantar da hankali babu wani abu tunda dai nasan banyi mata komai ba ko naje ba zata tuhume ni ba." Tace" To Allah yasa kiyi sauri kisa kayan ki kije. dankwalina na daura nace bari naje daga can zan wuce sashen Yarima tace."To Allah yasa muji Alkairi. Koda na shiga falon sai da nasha jinin jikina ganinsu duk sun kewayeta fuskokinsu babu fara'a zubewa nayi ina gaishesu babu wacce ta amsa a cikinsu na sunkuyar da kaina cike da ladabi nace"Ranki ya dade gani." Zama ta gyara tana kallona tace"Wama sunanki." da sauri nace"Sunana Sumayya Lawi." Tace"Ubanki wace irin bauta yake a cikin gidan nan."? nace"Yana bautawa Dawakai ne." Ta ya mutsa fuska tana wasa min kallon banza tace"Kece kika wargaza mana aikinmu na jiya ko."? mirya na rawa nace"Ranki ya dad'e wane irin aiki."? Wani bahagon mari aunty Safiyya ta kwada min tana huci! tace"Kada ki raina mana hankali dan ubanki tambaya ma kike."? Ido jawur nace"Tuba nake ranki ya dade." Uwargida tace"Kalle ni da kyau."! na dago kaina ina kallonta, tace."Kinyi na farko kuma kinyi na karshe wallahi tallahi duk sanda mukaje muka gudanar da aikinmu kika karya sai na saubata miki rayuwarki sai kin rasa ruwan kur'ba a masarautar nan ki tsaya a matsayin ki na baiwa babu ruwanki da Yarima duk wani abu da zamuje sashen mu gudanar ido ne naki." Nace"Ranki ya dade ku gafarce ni wallahi ban san wane aiki na lalata muku ba." Gabadaya zuba min ido sukayi, aunty Safiyya tace"Wato ba zaki daina wannan maganar ba ko. " shuru nayi tace"kinji abinda aka ce ko baki ji ba."? da sauri nace"Naji ranki ya dade....tace"Na tura hadima daga nan bangaran zata dinga saka mana ido akanki babu ruwanki akan dukkanin abinda zata gudanar aiki muka sata kiyi aikin ki tayi nata." nace insha Allah zan kiyaye." Aunty Bishira tace"Sumayya idan kika sake 'bata mana aiki a karo na biyu sai kin zubar sa hawaye wallahi tallahi mummunan mataki zamu dauka a kanki." Nace."Ranki ya dade zan kiyaye insha Allah." "Tashi kije." uwargida ce tayi maganar, sunkuyawa nayi da fadin"Na barku lafiya." babu wacce ta kulani da sauri na fito gabana na bugawa, kai tsaye sashensa na nufa ina shiga na tarar da sabuwar hadimar da suka turo tana goge goge, harararta nayi na wuce, samansa na hau na tsaya bakin kofa ina bugawa "Waye"? da sauri nace" Nice." "Kije babu abunda nake bukata an riga an gabatar min da komai." abinda yace min kenan ba tare da ya bude kofar ba, tsaye nayi ina mamakin maganarsa, an riga an gabatar masa da komai hakan na nuna min cewar dasa hannunsa gurin zuwan sabuwar Hadimar, na kai minti biyar a tsaye ina sa'kawa da kwancewa kafin na sauka kasa na sameta tana ta aiki.....hararar ta na sakeyi ina jin wani irin mugun haushinta, hanya na kama zan fita tace"Ke Sumayya wai me nayi miki ne tunda kika shigo kike hararata." Juyowa nayi kamar zanyi magana sai kuma na fasa tsaki mai karfi naja na fice na barta taba bina da kallo Koda na koma sashen mu kasa nutsuwa nayi na dinga tunane tunane marasa kyau ina idar da sallar magariba na koma sashen, babu kowa a falon shuru sai kamshi yake tsayawa nayi zuciyata sai sa'ke-sa'ke take min kai tsaya benan na nufa, hannu nasa na buga shuru beyi magana ba na sake bugawa gabana na faduwa gani nake Suwaiba na cikin dakin, can naji muryarsa a shaqe yana fadin"Waye."? da sauri nace"Nice ranka ya dade ka bude na gyara maka dakin." Still muryarsa a hard'e yace."Kije bana bukata." Gabana ne ya dinga faduwa kawai naji kwalla tana neman zubo min kasa barin gurin nayi sai kasa kunnena nake a jikin kofar dakin wai ko zanji wani abu shuru banji wata a alama ba na juya jiki a mace na sauka kasa, kicin na nufa nan na ganta a tsaye tana shirya abinci a tire ajiyar zuciya na sauke naji dadin ganinta a kicin din dan zuciyata babu irin sa'ke-sa'ke da ba tayi min ba. Gani nayi tana 'boye wani abu a cikin zaninta sai na nuna kamar banganta ba na bude firji kayan marmari na shiga fitowa dasu, ina kallonta ta goge hannunta da tissue ta dauki tire din ta fita dashi. Jingina nayi jikin firjin ina tunanin yanda zanyi na hanashi cin abincin nan nasan wani mugun abun ta zuba a abincin ganina yasa ta tsorata, ajiyar zuciya na sauke na cigaba da aikina, fruit salad na had'a masa nasa 'kankara a ciki yay sanyi daidai misali kana na shirya a kan tire........Inda yake zaman cin abinci na same shi a zaune yau 'yan wulakanci ne a kusa dan da gashi sai treequtar ko vest bai sanya ba, tire din ne ya kusa fad'uwa daga hannuna, tunda nake banta'ba ganin zahirin namiji ba sai yau sunkuyar da kaina kasa nayi dan ba zan iya kallon kirjinsa ba, tire din na ajiye kusa dashi da fadin"Ranka ya dade ga fruit salad din." "Dauke kayan ki bana so" Da sauri na kalleshi. gira ya daga min nace"Naga duk dare kana sawa na hada maka ne." cikin tsawa yace."Bana bukatar naki.'' Gabadaya naji gwiwata tayi sanyi da irin wulakancin da yake min a sanyaye nace"Dan Allah kada kaci komai na Suwaiba wallahi tasa maka maganin cutarwa kada ka mance abinda ya faru da kai kwanakin baya." Wani irin kallon banza yake min....raina ya 'baci mikewa nayi nace"Kai na gaji wallahi! zanje na samu mahaifiyarka na fad'a mata ka'ki bani had'in kai bazan iya ba."! hanya na kama zan fita. "Sumayya ranki sai ya 'baci mutukar kika je kika fadawa mahaifiyata wata magana." Nace"To shikkenan idan baka so na fada mata kar kaci komai na Suwaiba." "Sai naci dama nagaji da duniyar gwara na mutu sai kowa ya huta." Nace"Dan Allah kada kayi haka ka tausayawa mahaifiyarka da mahaifinka da masu kaunarka a masarautar nan.'' "Kinga ki daina wannan maganar babu wani mai kaunata a cikin masarautar nan sai iyayena idan kuma akwai sai ki fad'a." Murya na rawa nace"Wallahi kana da masoya." jajayen idanunsa ya zuba min yace."Suna ina."? ganin yana min kallon tuhuma yasa na sunkuyar da kaina yace."Sumayya nafi bukatar na mutu na bar musu duniyar tunda na tsare musu guri." A sanyaye yayi maganar sai naji zuciyata ta karye na kalleshi idona cike da ruwan hawaye......'Kasa ya tsirawa ido yana kallo kai da kagani kasan yana cikin damuwa mai tsanani fatar saman goshinsa duk tattare saboda tashin hankali....a sanyaye naje na tsuguna gabansa. *Na kudi ne* Kika karanta baki biya ba Allah ya isa! idan kina so ki biya kudin littafin ga yanda abin yake....Vip #600 normal #300 accont...0542382124...Binta umar gtbank.....idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 61&62 A hankali na kira sunanshi. Ya dago kanshi yana kallona kasa hada ido nayi dashi na sunkuyar da kaina a nutse nace"Dan Allah ka daina fadar wannan maganar Ubangiji baya so ya jarrabi bawansa ya dinga fadar maganar da bata dace ba, ka dauka abubuwan dake faruwa da kai jarrabawa ce daga rabbil izzati insha Allah sai dai suyi su gama amma baza zasuyi tasiri ba." Idonsa a kafe a kaina har na k'are maganata, jin bece komai ba yasa na kalleshi, ganin kallon da yake min yayi yawa yasa nace"Ranka ya dade ka gafarce ni idan maganata ta 'bata maka rai." Girgixa kansa yay yana jin sassauci a zuciyarsa a sanyaye yace."Nagode." nayi saurin kallonsa gira ya daga min da alamun sassauci a fuskarsa, wani irin farin ciki ya lullu'be ni naji dadi sosai da ya fara fahintata, nace"Me zan girka maka." "Komai." nace"Kafada dai." a yamutse yace."Bana jin ma zan iya cin komai a yanzu." a marairace nace"Ka daure dai kada ka kwana da yunwa." Kallona naga yanayi, nai mirmushi tare da sunkuyar da kaina kasa, yace."Cikina ciwo yake ba zanci komai ba." nace"To kasha fruit salad din." kai kurrum ya daga min. cike da farin cikin samun nasara na kwashe kayan abincin Suwaiba na fita dasu. Can inda nake zubarwa na nufa..."Ke Sumayya wallahi tallahi kika zubar da abincin nan sai kin fuskanci hukunci mai tsanani." kallon banza nayi mata nace "ashe kin san kin zuba guba a ciki." ta tsira min ido bakinta na rawa. nace"Wallahi kika sake kika kai maganar gurin uwargida sai na tona muku asiri gurin Maimartaba ke dai kin san makomarki gwara ma kizo mu hada kai mu taimaki Yarima duk sanda suka baki guba kisa masa a abinci ki zubar tun a hanya." Suwaiba gumi ya shigo yanko mata tace"Ta yaya zan aikata hakan Sumayya kin san duk sanda suka gane bana aikata aikin da suka sani sai na fuskanci hukunci." kafadarta na dafa nace"Kada ki bari su gane kullum ki dinga nuna musu cewar kina iyakacin bakin kokarin ki idan ma sun gane ni nayi alkwarin kare ki daga zarginsu." A sanyaye tace"Shikkenan dama nima cikin fargaba nake gudanar da aikin saboda ina tsoro wani abun ya samu Yarima wallahi tausayi yake bani." Nace"Ai abin tausayi ne duk sun tsane shi gabad'ayansu bayansa suke so su gani insha Allahu sai Allah ya kareshi daga sharrinsu. Har yanzu yana zaune a inda yake kuma da alama be sha fruit salad din ba. kawai ya tsirawa guri guda ido a sanyaye nace"Ranka ya dade kasha fruit salad din." dago kansa yayi tsorata nayi ganin yanda kwayoyin idanunsa suka sauya, k'asa nayi da kaina ni kam na rasa gane abinda ke sanyawa idanuwan sa nayin ja. "Sumayya ina bukatar ki rarrashe ni a yanzu bana bukatar komai sai rarrashi zuciyata a k'untacce take ina da damuwa babu abinda zan iya ci ko sha ki taimaka min."!!! Kallonsa nayi dan na kasa fahintar inda maganarsa ta dosa yana bukatar wanda zai rarrashe shi wane irin rarrashi kuma. " Ranka ya dade bangane maganarka ba." murmushi yayi ya lumshe idonsa ya bude su a kaina "Ba zaki gane rarrashin da nake bukata ba."? kai na daga masa jikina na mutuwa da yanayin kallon da yake min........girgiza kansa yayi ya cigaba da kallon kasa. Yanke shawarar tafiya nayi saboda na gane abinda yake nufi..." Ranka ya dade ka tashi lafiya." abinda na fada kenan na mike tsaye. "Kada ki tafi baki rarrashe ni ba zuciyata na dab da tarwatsewa ki taimaka min kinji." kallonsa na dinga yi ina mamakin maganarsa. "Ranka ya dade wane irin rarrashi zanyi maka kaje kayi alwala kayi nafila ka roki ubangiji zai yaye maka damuwarka nima nayi alkawari idan na koma gurinmu zanyi nafila nayi maka addua Allah ya kare ka." Shuru yay yana kallona girgiza kaina nayi na cigaba da tafiya ina mamakin fitinarsa.....ina daf da fita ya tari gabana, gabana ya yanke ya fadi yau naga jaraba, sunkuyar da kaina nayi ina adduar rinjaye, hannuna ya rike ya rintse da nashi. Rai a 'bace na kalleshi! kalar tausayi ya koma yana marairaicewa yace."Ki taimaka min kada ki tafi." naji kamar na kwada masa mari saboda takaici sarai nagane abinda yake nufi "Ranka ya dade wai kai wane irin mutum ne dan darajar Allah da Annabi ka daina zuwar min da bukatarka tunda kasan ba samu za kayi ba." Le'buna na naga yana kallo tsaki naja nace"Sakar min hannu na fita tunda baka san mutunci ba."! "Ni kike fadawa wannan maganar."! rai a bace yayi maganar..." Ranka ya dade ka gafarce ni kai ka janyo.'' "Naji ni na janyo kuma nayi turr da zuciyata data kasa hakura dake banza k'azama kawai.'' " Duk abinda zakace naji na dauka ni dai bani hanya na wuce."' "Sumayya ba zaki fita ba sai bukatata ta biya tunda na fahimci baki da tausayi to zan gwada miki karfi.'' Gabana na faduwa nace" Me kake nufi." ? "Ban sani ba." ya fada yana hararata, hannuna na fizge na tunkude shi zan fita. A fusace ya juyo dani mari na yayi hagu da dama! na dinga kallonsa hawaye na zubo min..."Ki shige muje daki." "Wallahi babu inda zani sai dai duk abinda zakayi min kayi." ina kuka nake maganar. Matse ni yayi jikin bango yana kiss din fuskata, tureshi nayi ina haki!! yace.'"Ba zaki daina ture ni ba ko."!! takure jikina nayi ina kuka ina mamakin rashin adalcinsa wai duk irin abinda nake masa da abinda zai saka min kenan Hannuna ya rike ya dinga jana wai lallai sai na bishi, turjewa nayi na tsuguna a gurin, tsugunawa yay ya dago fuskata na fizge ya sake kamo fuskar harshe yasa yana lashe hawayen dake zubowa. A sanyaye yace."Wai meye abin kuka wannan abunfa taimakon kai da kai ne zakiji dadi nima zanji kuma babu wanda yaji ya gani dan Allah ki daina kuka kinji ko." Fuskata na fizge nace"Kana cewa taimakon kai da kai ne waye yace maka ina bukatar wani abu!? sannan kana cewa babu wanda yaji ya gani to Ubangiji fa kasan duk abinda zamuyi yana ganinmu saboda haka kama daina wannan maganar idan kana son ka biya bukatarka dani ka aure ni." "Baki da hankali ko."? a zafafe nace" Gaka nan babban mara hankali mai manta alkairi." kallona yake yana mamakin irin zafafan maganganun da nake masa. "Ba zan aure ki ba saboda ke ba tsarana bace sha'awata kuma sai na kawar" yana gama maganarsa ya turmushe ni a gurin, kayan jikina ya yayyaga ya 'balle breziyar jikina, a gigice ya shiga wasa da kirjina....dukansa na shigayi ina haurinsa, tunda yasa Brest dina a baki yake sha nayi nayi na 'kwace ya'ki ya rike tam sai tsotsa yake yana lugudar d'ayan, wani irin hali na shiga na tashin hankali da tsananin sha'awa amma ban bari sha'awar tayi tasiri a tare dani ba, tureshi na cigaba dayi ina 'kokarin kwatar kaina. Sosai na shiga tashin hankali ganin yana nema yaci galaba a kaina yasa na dinga yi masa wani mahaukacin duka ina tuttureshi kamar maye yana sake nanewa a jikina sai nishi yake........gefan wuyansa na dasa hakora na dinga ciza ina ihu!!! a gigice ya sakar min nono na tunkude shi na mike tsaye ina ihu! tare da neman suttura.....mikewa yayi zai kamo ni na fitar da hannu na tsinka masa mari!!! cikin reshin kuka nace"Ka sake kusanto ni sai na kashe ka mugu azzalami sai Allah ya saka mun." Tunda na tsinka masa mari naga yayi sanyi ya zuba min ido mamaki sosai na hango a cikin kwayoyin idanunsa, yagaggun kayana na dauka nasa ina kuka na kama hanyar fita daga falon....... naji dadi dana samu bakin kofa babu kowa da sauri na nufi gurinmu ina share hawayen bakin ciki da takaici. Lokacin dana shiga gurinmu naji dadi dana samu iyayena sunyi bacci da sauri na shige kuryar daki, zama nayi hawaye na tsere a kumatuna, wai wace irin masifa ce take bina anya kuwa zan cigaba da kula da guy nan kuwa!? hannu nasa na goge fuskata gaskiya bana tsammamin zan koma aikin sashen yaje ya 'karata da mugun halinsa idan sun kashe shi shine ya janyo ni dai ba zan sake zuwa bare bukatarsa ta biya a kaina......Motsin shigowa dakin naji nai saurin mikewa tsaye can inda kayana suke na nufa na shiga fito dasu..."Sumayya yau dad'ewar me kikayi ne."? Muryar Tambaya naji a kaina tana tambayata......sai dana saisaita kaina nace"Bani kadai na dade a sashen ba har dasu Haruna mun tsaya munyi masa aiki ne kin san gobe ne Walimar da za'a gudanar domun taya shi murna bude babban asibitin sa." Ajiyar zuciya ta sauke tace"Da kyar bacci ya dauke mu nida mahaifinki muna ta zullumi ko kina can gurun Uwargida ta tsareki da wani laifi." murmushi nayi ina boye damuwata nace" Tambaya kenan ai tuntuni na gama da gurin uwar gida duk wannan zaman a sashen Yarima nayi." Tace"To alhmdullhi ina fatan dai babu wata matsala." nace"Babu matsala ki koma kiyi kwanciyarki." Tace"To shikkenan ." Tana fita daga dakin na sauke ajiyar zuciya, riga da zani na dauko nasa a jikina na karkade shimfidata kwanciya nayi tare da tsirawa rufin dakin ido, tunani nake akan abinda ya faru dani....da gaske yake daya samu galaba a kaina sai ya cutar dani gaskiya banta'ba ganin butulu irinshi ba dole ne na nemawa kaina mafita gaskiyar magana kenan dan ba zan bari ya cutar da rayuwata ba, da wannan tunane tunanen bacci mai nauyi ya dauke ni... *Na kudi ne!* Kika karanta baki biya ba Allah ya isa! idan kina so ki biya ga yanda abin yake...Vip #600 normal #300 account.. 0542382124...Binta umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 65&66 Muddibo zama yayi a kan kujera ya dafe goshinsa abin duniya ya taru yayi masa yawa shima ji yake tamkar ya fashe da kuka saboda tsabar bakin ciki da takaici. "Muddibo wane mataki zamu dauka akan wannan al'amarin dake faruwa wallahi ni har na gaji da abu daya kullum yaron nan gaba yake yi yana barinmu a baya yanzu yanzu Muzanbil yazo yake sheda min cewa gashi can a gurin taro sai mubaya ake masa jama'a sai addua suke masa gami da fatan nasara a rayuwarsa wannan al'amari yayi masifar daga min hankali ta inda har na rasa tunanin da zanyi." Muddibo fuskarsa ya bude yana binsu da kallo ido jawur yace."Wallahi nima gabadaya kaina ya kulle na rasa wane mataki zan dauka akan Yarima duk wani tarko idan muka d'ana masa sai ya tsallake na rasa daga inda matsalar take." Aunty Safiyya tace"Matsala fa daga gurin wannan mutsiyaciyar yarinyar take itace ke saka ido a kan komai duk aikinmu itace take wargazawa daba dan hakaba da tuni hakan mu ya cimma ruwa a kansa, Muddibo yace."Nima na soma zarginta akan hakan to lallai kuwa zata janyowa kanta dan wallahi zan iya kasheta mutukar bukatata zata biya. Uwargida tace"Dan Allah ku bar wannan maganar tukkuna ni yanzu so nake dani daku mu zauna muyi tunani akan wannan asibitin da aka bude masa inaso muyi tunanin wane mataki zamu dauka a kan hakan. Muddibo shuru yayi yana girgiza kafarsa yace"Hajiya bani da imani akan bukatata wallahi zan iya kashe rayuka ina ganin tunda asiri da sharri ya kasa tasiri akansa kawai zan sa a cinnawa asibitin wuta kowa ma ya huta kuma bazan gudanar da aikina yanzu ba sai jama'a sun soma zurga zurga a cikin asibitin tukkuna zan sa a sa wuta in yaso kowa ya guje shi dan naji masifar haushi da yanda jama'ar gari ke nuna masa kauna wannan shine mataki da zamu dauka. Uwargida murmushi tayi tace"Muddibo shiyasa nake kaunarka nake kuma sanya ka a cikin al'amurana saboda kasan abinda ya dace hakika wannan shawarar taka itace abar dubawa naji dadi sosai daka samo mana mafita idan ta kama har shi wutar cinye sai mu huta kaga mun yar da kwallon mangwaro mun huta da kuda. "A'a kada ayi haka sai zunubin namu yayi yawa ina ruwan jama'ar gari kuma Yarima Ali shi muke so muga bayansa saboda haka idan abin ya kasance da haka shi zamu sawa wuta ba jama'ar gari ba." Aunty Bishira ce take wannan maganar bayan taci kukanta ta koshi. "Ke kinga Bishira ki daina wannan maganar ashe akawai sauran imani a tare dake, babu ruwanmu mu kan mai uwa dawabi zamuyi ko ba haka bane."? aunty Safiyya ta 'kare maganarta tana kallon Muddibo." Yace." Kwarai kuwa ni na rasa wace irin zuciya ce da Aunty Bishira jama'ar garin ba sune suke 'kara masa karfin gwiwa ba na tabbata idan asibitin ya tashi da wuta mutane suka 'kone suka mutu to kowa zai kiyaye kai kansa asibitin gudan faruwar matsala kinga bukatarmu tabiya mun ruguza shi." Uwargida tace"Muddibo rabu da Bishira dan Allah mu cigaba da abinda yake gabanmu." Gabadaya suka zuba masa ido yana cigaba da tsara musu yanda al'amarin zai kasance. Ni dai ina ganin Maimartaba ya shiga gida nima na bar gurin dan gabadaya hayaniyar dake tashi a gurin nema take tasa min ciwon kai, daf da gate din sashen Sumayya naji an kira sunana ina juyowa muka hada ido da Dr Rabo ashe yazo taron, murmushi nayi na tsaya ina kallonsa har ya karaso inda nake tsaye, da murmushi a fuskarsa yace."Baby Sumayya kinyi wuyar gani." ina yar dariya nace"Dr Rabo barka da hantsi ya gida ya iyali.''? Yace."Alhamdullhi ina fatan kina lafiya ko da yake ai ga alamu nan sun nuna kina cikin koshin lafiya Sumayya ashe haka kike da kyau.'' hararasa nayi ina dan bata fuska nace"Ka saba fada min wannan maganar dan ka bata min rai dan Allah ka daina bana so." Murmushi yayi ya shafa sajensa yana kallona yace."Kin san Allah ba karya nake ba kina da kyau sosai sai dai ba kowane zai fahimci hakan ba sai wanda yasan meye kyau, mafi akasari maza sun dauka fari shine kyau basu san ba haka bane dan wallahi da wata farar macan gwara babu zaki ga wata fari ne kawai amma sam bata da k'ira da cika irin wanda namiji ke bukata ke kam Sumayya kin cika mace ta kowane fanni na jima banga macen da ta tara irin abubuwan da kike dashi ba. Cikin kankanin lokaci na murtuke fuskata ashe Dr Rabo kare min kallo yake har yana kwarzanta kirar jikina, dauke kaina nayi sabida takaici na rasa ma abinda zance masa, ina jinsa yana surutu na juyo domin na fada masa cewa zan tafi dan banga amfanin tsayuwata ba dashi ba na tsani namijin da zai dinga nuna zulama a kaina.....Magana zanyi Yarima shida Shatima da wasu fadawa biyu suka karyo daga wata hanya, sunkuyar da kaina kasa nayi gabana na wani irin faduwa. Yarima tun daga nesa yake so ya tabbatar da abinda yake gani a kofar gate dinshi, Yarinyar nan ce Sumayya da Dr Rabo suke zance a gurinsa saboda sun raina masa hankali! mugun kishi ne ya rufe shi, nan take yayi kici kici da fuskarsa, Shatima nayi masa magana yana amsawa ciki ciki takaici ne fala cikin zuciyarsa. "Dr Rabo ni zan shiga gida kaina ne ke ciwo dan Allah ka gaishe min da yaranka idan ka koma gida." Yana yar dariya yace."Ba zaki tsaya yarima ya karaso ba naga sai wani sauri kikeyi kada dai kice min har yanzu tsoransa kike." Kallonsa nayi ina mamakin maganarsa nace"Dr Rabo Allah ne kadai abin tsoro ba wani mahalu'ki ba." Maganata tayi daidai da karasowarsa gurin kuma nasan yaji......da sauri nayi gaba ba tare da nayi kuskuran kallonsa ba nace"Dr ka sauka lafiya." Gabadaya harshi bina sukayi da kallo suna mamakin abinda na aikata wanda ya dace ace na tsaya na kwashi gaisuwa gurin Yarima amma na kad'a kaina na wuce! na bar gurin, ba Yarima kadai ba har Shatima sai da yaji haushin abinda nayi......Yarima Ali kuwa kasa tsayawa yayi yay cikakkakiyar sallama da Dr Rabo hannu kawai ya daga masa ya shige ciki Dr Rabo anan ya sake gazgata zarginsa akan cewa shima son yarinyar yake. Koda suka shiga cikin gidan kasa samun nutsuwa yayi gabadaya hankalinsa ya tashi ganin yarinyar sannan babban abinda ke duguzuma masa zuciya ganin Dr Rabo ya tsayar da ita suna hira a bakin kofarsa sai yake ganin kamar da gayya sukayi masa haka yaji gabadaya ya tsani Dr Rabo duk da ya kasance abokinsa amma a yanzu bashi da babban makiyi kamarsa. Shatima ya dafa kafadarsa a nutse yace."Na lura abinda yarinyar nan tayi maka a gaban Dr Rabo ya bata maka rai ni kaina raina ya baci wallahi kayi hakuri yanzu zansa a kirata ta nemi afuwarka." Girgiza kansa yayi yace."Rabu da ita kawai kada ka kirata zata shigo da kanta idan ta shigo ni zan mata hukunci daidai da abinda tayi min." Shatima yace."Okey yanzu me ka fuskanta a tsakaninta da Dr Rabo."? kai tsaye yace."Sonta yake." Shatima yayi dariya yace."Lallai idan bakayi da gaske ba zaiyi maka shigar sauri." Cike da mamaki yace."Ban fahimci maganarka ba." Shatima da murmushi a fuskarsa yace."Kana son yarinyar nan alamu sun nuna min hakan wannan dalilin yasa na fadi wannan maganar. Baki a sake yake kallonsa yana mamakin yanda akayi yayi saurin gane shi. Shatima yace."Yanayin yanda aka kasa 'boye bacin ranka da kishinka yasa na gane tsananin son da kakewa yarinyar naji dadin hakan sosai kuma yarinyar ta dace da kai domin duk ta had'a abubuwan da ake bukata ina maka fatan alkairi." Rai a 'bace yace."Shatima kai yanzu ta ina ka hango dacewa ta da yarinyar nan ka dube ta da kyau kuwa ka gani na rasa wacce zan aura sai ita." Shatima yace."Gaskiya ka bani mamaki Ali yanzu dan Allah wace dacewa kake nema bayan wannan ? meye aibun yarinyar nan Sumayya ta cika mace kuma ta kai ta zama matar Sarki governor ko shugaban kasa, tana da kyau daidai misali kana tana da kyawawan halaye to me kuma ake nema a gurin 'ya mace."? Girgiza kansa ya shiga yi yace."Shatima mu bar wannan maganar dan Allah yarinyar nan bata dace dani ba saboda bata da ilimin da zatayi goyayya dani ta kowane fanni." Shatima yace."Mutukar tana da ilimin addini to baka da matsala dan wani ilimin boko ba wani abun damuwa bane ilimin addini shine abin dubawa saboda haka ina me baka shawara akan kayi wani abu akai idan kuma ka tsaya wasa nima zan shiga kawai dan dab'iun yarinyar da kyawun halayenta na burgeni ina so na aureta mace mai hankali da nutsuwa kodan na samu 'yaya masu tarbiya. Yarima Ali shuru yayi yana kallon Shatima da ya dage yana ta gwarzanta kyawu da kyawawan d'abi'un yarinyar..........Yace."To shikkenan naji maganarka zan zauna nayi nazari akai." Shatima yace."Yawwa ko kaifa wallahi sosai nayi maka sha'awar auran yarinyar saboda kun dace da juna." Bayan fitar Shatima tunani ya shiga yi akan maganarsu, shima yasan yarinyar nada kyawawan halaye wanda ko wane namiji zai sha'awar auranta, to amma ai idan ya zauna yayi duba na tsanaki zai fahimci cewar yarinyar bata dace da ta zama matarsa ba saboda ita din ma'kas'kanciya ce a gurinsa a kasan sa take babu yanda za'ayi ya auri baiwarsa a matsayinsa na Yarima dan Sarki babu macan data dace dashi sai Yar sarki ko yar wani mai mulki ko Lawisa ma zai aureta ne badan yana sonta ba kawai dai abinda yasa ya kwantar da hankalinsa da auranta saboda ya hango akwai mamora a jikinta shine dalilin da yasa bai damu ba, amma abin kunya ne abokananshi su san matsayin matarsa Sumayya sam ba tsaran auransa bace, amma zai duba ya gani yana ganin ko ya aureta ba zaiyi yarda ya haihu da itaba zata zame masa matar biyan bukatarsa. wannan shawarar ya yankewa kansa. Bayan kwana biyu al'amura sunyi sauki kullum da safe idan na fita daga gurinmu gurin karatu nake tafiya acan nake yini nayi ta karatun al'kur'ani da sauran littafai sai yamma likis nake dawowa, Tambaya da babana duk basu san da cewar na daina zuwa sashen Yarima ba tinda kullum ba'a gida nake yini ba shiyasa basu gane komai ba..........Koda Haruna ya same ni da maganar kasa 'boye masa nayi saboda na riga nasan irin kaunar da yake min, Haruna ya dinga mamaki al'amarin yace."Sumayya a gaskiya nima ban goyi da bayan ki cigaba da zuwa ba, kiyi zamanki idan Fulani ta kira ki kan maganar sai ki san abinda zaki ce mata." nace"To shikkenan da wannan muka rufe maganar Yarima muka shiga hirar soyayyarmu. Yarima Ali tun bayan damuwa da rashin zuwanta har abun ya soma damunsa kullum idan zaici abinci sai yayi takaici da bacin rai dan Suwaiba sam bata iya girki ba wani sa'in inda ta ajiye abincin haka take zuwa ta tarar da abunta beci ba, wani lokacin kuma idan yaci loma daya yaji babu dadi kiranta yake yayi tai mata masifa irin wacce yake min akanta yake huce fushinsa, Suwaiba ta dinga data sanin zuwanta sashen dan komai tayi masa bata gwaninta. Umartar Gimbiya Lawisa yayi data dinga kawo masa abinci dan baya tsammanin zai iya tunkarar mahaifiyarsa da maganar daina zuwa yarinyar yasan dole ta binciki dalili shiyasa ya kasa tunkararta sai ya Umarci gimbiya Lawisa da ta dinga kawo masa daga sashen su, Lawisa abin nema ya samu kullum xata zauna ta tsara masa girke girke safe da rana da dare ta barbade da maganin mallaka ta kawo masa sashensa, ta zauna yana ci suna hira babban burinta maganinta yayi tasiri a kansa, aikuwa ha'kan ta ya cimma ruwa dan yanzu sun daina fad'a yana nuna mata kulawa farin ciki tamkar ya kasheta...... Bayan wata biyu al'amura suna ta tafiya cikin nutsuwa yanzu na manta na daina fargabar abinda zai biyo baya tunda naga har an dauki tsayin wannan lokaci fulani bata kirani da wata magana ba sai hankalina ya kwanta sosai na cigaba da karatuna maganar auranmu da Haruna kuwa an tsayar da lokaci wata shida mai zuwa Mahaifina da Mahaifin Haruna har gaban Sarki sukaje suka sheda masa abinda ke faruwa, Sarki ya nuna farin cikinsa kana kuma yasa mana albarka.......Tsakanina da Haruna soyayya mai karfi ta sake 'kulluwa Bangaran Lahira kuwa abun nata sai a hankali dan daukar gaba tayi dani ta daina yi min magana, na tambayeta dalili taki fada min sai nima kawai na tattarata na watsar da ita na cigaba da sabgogina hankalina a kwance.. Bangaran Magajin Sarki kuwa sai godiyar Allah Cikin nasara da yardar Ubangiji ya fara aiki a asibitinsa yayin da jama'ar gari ke zirga zirga cikin asibitin domin nemawa kansu da 'ya'yansu lafiya kamar yanda ya fada a ranar Walima haka Asibitin na dauke da 'kwarrarun ma'aikata wa'inda suka san aikinsu wannan dalilin ya sanya hatta da manyan mutane masu kudi suke zuwa a dubasu a asibitin, alhamdulillhi bukatarsa ta biya ta kowane b'angare sai abu guda dake damunsa shine yanda zai tunkari Hadimarsa ya fada mata cewar ya yanke hukuncin auranta kamar yanda ta bukata ya amince zai aureta ita da Lawisa a rana daya, kullum da tunanin yanda zai tunkare ta da maganar yake kwana yake tashi gabadaya kunyar hada ido yake da ita sabida abin da yayi mata, amma yana ganin tilas yaje ya samu mahaifiyarsa ya shirya mata wata maganar akan rashin zuwan yarinyar gurinsa. Karfe takwas da rabi na dare ya samu mahaifiyar tasa a kishingide akan dadduma ta idar da sallah tana jan carbi, a nutse ya zauna a gabanta tare da mika gaisuwarsa, ta amsa da fuska a sake tace"Babana aiki ya 'boye ka bana ganin ka a kan lokaci." Murmushi yayi yace."Wallahi kuwa Mamma wannan dalilin yasa ma na yanke shawara cewa kullum kafin na fita zan dinga shigowa mu gaisa sabida wani lokacin bana shigowa gida da wuri sai can dare. Tace"Aikuwa dai hakan shine daidai ina fatan komai yana tafiya cikin nutsuwa da kwanciyar hankali." Yace."Alhmdullhi mamma komai na tafiya daidai jama'a da yawa najin dadin alkairin da kukayi musu kullum cikin yi muku addua sukeyi." Murmushin jin dadi tayi tace"Alhamdullhi dama babban burinmu shine mu faranta ran mabukata kaima Allah ya saka maka da alkairi ya baka ladan abinda kake yi.". "Ameeen Mamma na." Dakin ne yayi shuru na minti biyu kafin ya dago kansa a nutse yace."Mamma wannan yarinyar dake yi min hidima kwana biyu ta dauke kafarta ta daina zuwa ni ban san dalili ba rashin samun zama yasa ban shigo na sheda miki ba sai yanzu dana shigo gidan da wuri nace bari nazo na sheda miki halin da ake ciki ko zaki aika a kira ta gani gata gaki sai ta fad'i abinda akai mata ta daina zuwa tayi aikinta ." Fulani mikewa tayi zaune tana kallonsa da mamaki a fuskarta tace"Babana har tsayin wane lokaci sumayya ta dauka bata tare da kai."? *Na kudi ne* Idan kika karanta baki biya ba Allah ya isa! idan kina so ki biya ga yanda abin yake...VIP gruop#600 normal group #300 account... 0542382124....Binta umar gtbank....idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 63&64 'Bangaran Yarima Ali kuwa al'amarin ne ya dinga bashi mamaki! kamarshi yarinyar nan ta fitar da hannu ta tsinka masa mari! wannan al'amari ya girgiza mutuka kaf a tarihin rayuwarsa ba'a ta'ba cin mutuncinsa kamar na yau ba amma babu komai yasan duk abinda ya faru shine ya janyowa kansa kamar yanda yarinyar ta fada kafin ta fita, yana ganin dole ya hakura da ita komai k'ulafucinsa kuwa tunda raini da wulakanci ya soma shiga tsakaninsu, lallai dole ya kafa tarihi da yarinyar dan tunda yake babu 'ya macan da ta ta'ba yi masa abinda ta aikata masa, mari!! abin ya bashi mugun mamaki ta yanda har ya rasa wane irin hukunci zai yanke akanta ........Yana ganin ko kawai yabi shawarar ta ta farko wato ya aureta tunda taki bashi hadin kai idan ya biya bukatarsa sai ya saketa dan shi abin kunya ne a gurinsa ace itace matarsa sam bata kai matsayin da zaiyi zaman aure da ita ba, amma dole zai zauna yayi nazari da tunani akan al'amarin yanzu babban burinsa ya wulakantata kamar yanda ta wulakanta shi ta mare shi ba tare da taji tsoron abinda zai biyo baya ba, da kyar ya iya barin falon duk jikinsa yayi sanyi nadama da kunyar hada ido da yarinyar duk ya dameshi. Washe gari da zazzabi na tashi na dinga daurewa domin bana so iyayena su fahimci abinda ke damuna. Muna gama karyawa na nemi guri na kwanta ina lumshe idona babu abinda ke damuna sai al'amarin daya faru jiya har yanzu na kasa yanke hukunci. "Sumayya ya kika koma kika kwanta kuma ki tashi kiyi wanka ki shirya jikin ki yau ai kaya zamu sa masu kyau tunda Walima za'a gudanar. Tambaya ce take wannan maganar a lokacin da take tsaye a kaina. bude idona nayi ina kallonta, tace" Ki tashi ga ruwa can na dora nasan yanzu yayi zafi sai kiyi wankan'' nace"Sai fa sha daya na rana za'a zauna zaman Walimar." Tace''To idan kinyi wankan ai kin huta." Mikewa zaune nayi ina gyara daurin dankwalina. Tace"Kuma naga baki je sashen Yarima ba Allah yasa dai lafiya."Nace."Lafiya lau sai an dan jima zanje." Fita tayi daga dakin tana fadin"To ai sai kiyi maza kizo kiyi wankan kafin lokacin Walimar yayi kinje kin gama abinda zakiyi. Mi'kewa nayi ina kokarin cire rigata gefe guda kuma ina mamakin yanda tambaya ta damu da dole sai nayi wanka na shirya nida zan samu yanda nake so wallahi ba zan fita ba balantana na ganshi gabad'aya ya fice min daga raina tausayinsa ma na daina ji sabida irin rashin kyautawar da yayi min jiya. Daya daga cikin tamfofin da Fulani keyi min kyautarsu na dauko wata super mai ruwan ganye nasa a jikina, nayi mamaki sosai da dinkin ya zauna a jikina tamkar an auna ni. Murmushi nayi a sanda na kalli mudubi naga yanda nayi kyau Atamfar ta haska ni Zama nayi domin na gyara fuskata babana ne ya shigo fuskarsa cike da walwala da farin ciki yace."Yawwa Sumayya ki shirya sosai ga 'yan uwanki can kowacce tayi ado inaso ki zama tauraruwa a cikinsu.' cikin tsokana yake maganar Dariya nasa nace"Baba kenan ashe kana so nayi kyau nafi kowa ko."? da mirmushi a fuskarsa yace."Eh mana ai kowa nasa ya sani." murmushi nayi nace"To kaima sai ka shirya mu fita tare." Yace."Ke dai ki fara fita nida mahaifiyarki zamu biyo bayanki." Nace"To shikkenan baba yanda kace haka za'ayi......Kwalli na zirara a idona na shafa hoda sama-sama! sai nasa man le'be kadan a fuskata kana na hada kayan kwalliyar naje na ajiye. Ina kokarin nade lifaya a jikina Tambaya ta shigo dakin....gani nayi ta tsaya tana murmushi, na saki fuskata ina dariya nace nayi kyau ne."? Kanta ta daga tace"Sosai kuwa idan zaki futa kiyi addua saboda bakin mutane." Dariyar maganar ta bani nace"To shikkenan zanyi insha Allah. Tsakar gida na fito da mudubi a hannuna ina dubawa, gaskiya nayi kyau ni kaina nasan hakan, ajiye mudubin nayi kan taga nace"To Tambaya ni na fita sai kun fito." Tana daga daki tace"to shikkenan." Koda na fito ban zarce gurin Walimar ba sai dana na biyawa Lahira na sameta a tsaye da mudubi a hannunta tana gyara daurin dankwalinta, wani irin kallo naga tabi ni dashi a take yanayin fuskarta ya sauya naso na fahimci wani abu...."Lallai Sumayya kece kikayi kyau haka."? abinda tafada kenan tana kallon sutturar jikina. Yar dariya nayi ina duba jikina nace"Haba Lahira wane irin kyau banda zagi dai." Ta'be baki tayi ta cigaba da gyara daurin dankwalinta sosai abinda tayi ya bani mamaki na hango hassada da ganin kyashi a idonta. Lami mahaifiyarta ce ta fito daga daki sai naga itama ta saki baki tana kallona, cikin sanyin jiki na tsuguna har kasa na gaisheta, bata amsa ba sai kumbura fuska takeyi tace"Ke Sumayya waye ya baki wannan kayan ni dai in banda ke banta'ba ganin wata baiwa tasa irin wannan sutturar ba.'' Wasa na shiga yi da hannuwana nace"Wallahi Mamma Fulani ce tayi min kyautarsu kin san ni nake kula da Yarima ta fanni abincinsa jin dadin yanda nake bashi kulawa yasa tayi min kyautar sutturu harda zoben gold." Lahira da mahaifiyarta suka saki baki suna kallona kafin su mayar da hankalinsu kan zoben dake hannuna! Lami tsaki taja tayi gaba ba tare da tace komai ba, kallo na bita dashi ina mamakin abinda ya janyo haka. Lahira kuwa gani nayi idonta yayi jawur kamar wacce tayi kuka duk sai naji banji dadin hakan ba, daurewa nayi nace."Lahira idan kin gama kizo muje mu samu gurun zama kada guri ya cika da jamaa mu tsaya a tsaye kinsan ni bana jurar tsayuwa. Fitowa tayi daga dakinsu tana yafa mayafi ba tare data kalleni ba tace"Muje.'' bayanta nabi ina dana sanin biyo mata dan dana san zata nuna min hassada to da sai dai ta same ni a can..........."Sumayya da gaske ne auranku da Haruna."? Katsaham naji ta jefo min wannan tambayar....ajiyar zuciya na sauke nace"Eh mana ko haruna nada wata illar ne." Ta'be baki tayi tace"Babu." dauke kaina nayi ina jin haushin abunda take yanzu na gano Lahira da zuciya biyu take zaune dani tunda gashi nan tana nuna min bakin ciki. Koda muka isa gurin taron samunsa mukayi a ciki da kyar muka samu gurin zama muka zazzauna muka cigaba da jiran fitowar Sarki da tawagarsa shi kansa wanda ake gabatar da Walimar dominsa bai fito ba. amma kuma manya bakin sun fara zuwa an tanadar musu gurin zamansu na mussaman. Mun kai kusan mintina arbain da zama kafin Maimartaba ya fito da tawagarsa, gurin ne ya hautsine da bushe bushe gami da hayaniyar jama'a kullum idan Sarki zai fito jama'a nunawa suke kamar basu ta'ba ganinshi ba, da kyar aka samu gurin yayi lafiya, Sarki ya zauna a mazauninsa 'yan uwansa suka zauna kusa dashi, can gefe guda kuma Yarima Ali ne dashi dasu Shatima sun sashi a tsakiya sunsha kwalliya da kayan sarauta amma nashi na mussaman ne dan ba karamin kyau yayi ba yana sanye da farar shadda sai ya dora bakar alkyabba a jikinsa, gaskiya wanda ya nad'a masa nad'in dake kanshi gwani ne dan ya fito dashi sosai kuma nad'in yayi masa kyau mutuka! kamar koda yaushe fuskarsa a had'e babu fara'a jefi jefi yake kallon jama'a gabadaya ya kasa sakewa a gurin sabida rashin san mutane Malam Ahamad Sulaiman shine ya gabatar da karatun al'akurani mai girma gurin yayi tsit har malam ya gama karatun kana ya bude taron da addua. Maimartaba yayi jawabin godiya ga jama'ar da suka samu damar hallartar taron sannan yayi addua tare da fatan kowa ya koma gidansa lafiya. Bayan ya koma gurin zamansa, Waziri ya fito yayi nasa jawabi Bayanshi Galadima Yayi Ciroma yazo yayi nasa dukkaninsu sun danne bakin cikin dake cikinsu suna ta fara'a gami da nuna farin cikinsu. Koda Yarima Ali ya taso domin yin nasa jawabin gurin ne ya hargitse da hayaniya, sai da masu kula suka tsawatar tukkuna aka samu lafiya, dago kansa yay an samu ya dan saki fuskarsa ya daga hannuwansa sama alamun gaisuwa ga tarin jama'ar dake gurin, gurin ya sake rikicewa kowa na fadar albarkacin bakinsa, zuciyoyin Ma'kiya kamar su buga saboda ganin yanda Jama'a ke nuna kaunarsu akan Ma'kiyinsu.......Shima nasa 'bangaran yaji dadi sosai da yanda jama'a ke nuna masa kauna dalilin da yasa kenan ya sassauta fuskarsa ya dinga d'aga hannuwansa sama yana sakin murmushin farin ciki...Dauke kaina nayi daga kallon fuskarsa dan ni duk mubayar da jama'a ke masa ba burgeni suke ba, da sun san waye shi da duk basu yi masa ihu gami da fadin sai yayi ba, gabadaya ma ni ji nayi zaman gurin ya isheni kallonsa ko jin muryarsa na tayar min da bacin rai. Tsaki naja lokacin dana ji miryarsa yana fadin"Alhamdullhi Allah kaine abin godiya daka nuna min wannan rana mai albarka wannan rana r ba zan ta'ba mancewa da itaba a cikin kundin tarihin rayuwata saboda rana ce mai muhimanci a gareni daku baki daya nagodewa Allah na kuma godewa mahaifina wanda ya zama silar samuwa ta a wannan duniya, mahaifina ya taka muhimiyyar rawa a tare dani ya tsaya min akan dukkanin al'amurana na yau da gobe tun ina yaro yake dawainiya dani har na kai wannan matakin dana ke kai a yanzu.....Naje america nayi karatu mai zurfi dan na taimaki kaina da al'ummar musulmi alhamdullhi yau wata na hudu da dawowa gida duk wani hutu dana ke bukatar nayi na samu insha Allahu ranar monday litinin kenan zan fara aiki a sabon asibitina mai musa *Zinariya Hospital* asibitina ya kasance kyauta ga duk masu wa'innan lalurorin da zan lissafo.".. ...........Jin wannan magana tasa yasa jama'a da yawa suka mayar da hankalinsu kansa suna sauraransa. Yarima Ali ya cigaba da cewa." Idan akwai masu fama da matsalar hawan jini Sugar ciwon qoda ciwon hanta cancer duk suna iya zuwa asibitina a sati mai zuwa domin su fara kar'bar magani, sannan akwai 'bangaran mata masu cika da masu haihuwa akwai bangaran yara masu fama cutar sikila asma nimonia da sauran cutukan dake dake addabar yara a kananu idan d'anka ko 'yarka na fama da daya daga cikin wa'innan cutukan dana lissafo to sai ka maxa ka garzaya dashi asibiti a sati mai zuwa insha Allahu za'a dora shi kan maganin daya dace, akwai likitoci na mussaman da muka tanada domin duba marasa lafiya amma duk da haka muna bukatar karin wasu kananun ma'akaita saboda haka dik wanda ke bukatar mu daukeshi aiki sai yazo mana da takardunsa a cikin satin da zamu shiga insha Allahu idan mun duba cancanta da nagartarsa zamu daukeshi aiki domin ya taimaki kansa kuma ya taimaki al'umma da ilimin da Allah yayi masa, wannan shine takaitaccan jawabin da zanyi!.'" Yarima Ali na gama jawabinsa guri ya hautsine jamaa suka dinga murna da farin ciki jin abin alkairin da suka samu. da kyar aka samu gurin yayi shuru, Maimartaba tsabar farin ciki kasa cewa komai yayi sai mirmushi yake yi, Waziri na taya shi, Bangaran su Ciroma kuwa tamkar zuciyarsu zata fito waje saboda haushi da takaici...Muddibo kuwa tashi yayi ya bar gurin can bangaran Uwargida Huwaila ya nufa, nan ya samesu sunyi jugum! abin duniya ya ishe su Aunt Safiyya da Aunty Bushira sai kuka sukeyi suna fad'in su basu yarda da wannan kyautar da Sarki yayi wa Yarima Ali ba kyautar Asibiti gari guda su suna zaune ko tsinke bai basu ba dan haka wallahi ba zasu tafi ba sai ya shigo gidan suma yayi musu kyautar filaye ko gidaje.,.... *Na kudi ne..!* Kika karanta baki biya ba Allah ya isa! idan kina bukatar ki biya ga yanda abin yake...Vip group #600 normal gruop#300 account... 0542382124...Binta umar gtbank...idan kati zaki turo #400 sai kiyi min mgn ta whasap da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 69&70 Gabad'aya tsarguwa nayi da yanayin kallon da mutane suke min bina suke da kallon zargi da tuhuma sun had'a rukuni rukuni suna surutai a kaina kowa dai da abinda yake fad'a dangane da faruwar al'amarin, can gefe na hango iyayena cikin yanayi na tsantsar damuwa da tashin hankali Tambaya sai hawaye take sharewa babana ne mai karfin halin danne abinda ke zuciyarsa amma kallo guda za kayi masa ka gane cewar yana cikin tashin hankali......Zuciyata ce ta sake karyewa zafafan hawaye suka zubo min da sauri nasa hannu na goge nayi kasa da kaina gami da cigaba da bin bayan jakada zuciyata cike da wasiwahsin abinda zanje na tarar a fadar sarki, duk nasan ina da gaskiya amma zuciyata ta kasa tsayawa guri d'aya sai sa'ke-sa'ke takeyi min dangane da abinda ya faru. Ganin Maimartaba a tsaye yana kai komo yasa naji gwiwata ta sage, a sanyaye na zube a kasan gurin murya na rawa nace"Ranka ya dad'e barka da wannan lokaci ina rokon Allah ya ja zamanin ka ya kara maka lafiya da nisan kwana." Zama yayi kan kujerarsa ya tsira min ido, sunkuyar da kaina nayi ina wasa da yatsun hannuna. Maimartaba kallon yarinyar yake yi yana mamakin abinda ta aikata masa a masarauta dole ne ya binkiceta domin sanin wanda ya sata zubawa d'ansa guba mai karfi a cikin abinci." A nutse yace."Yarinya ya sunanki."? Kaina a kasa nace"Sunana Sumayya Lawi. kallona yake yana girgiza kansa, Yace."Yanzu na samu labarin abinda ya faru a bangaranku ina so ki fada min gaskiyar magana." Hawaye ne suka zubo min da sauri nasa hannuna na goge wasu suka sake zubowa. gyaran mirya yayi yace."Ba kuka nace kiyi ba kiyi min bayani akan irin gubar da kika zubawa d'an uwanki musulmi." Muryata na rawa nace"Ranka ya dade na rantse da wanda raina yake a hannunsa ban sawa kowa guba ba." Shuru yayi na minti biyu kafin yace."To kinyi rantsuwa da Allah Sumayya kin san Allah ba abun wasa bane idan baki sa musu guba a abinci ba ya akayi bayan sunci abincin da kika basu suka fita daga hayyacinsu." A sanyaye nace"Naje sashen Yarima domin nayi ayyukan dana saba sai na tarar da Suwaiba tana soya doya da 'kwai Yarima ya shigo kicin din ya sallameta yace ba zai zauna ya ci komai ba saboda ya makara a gurin aiki, ganin kada ayi asarar doyar yasa na juye a cikin kula na kawowa su Haruna daga nan na wuce gurin karatu ina zaune a cikin 'yan uwana malam ya shigo ya fito dani yana tuhumata akan wannan dalilin daya faru Ranka ya dade wannan shine iyakacin abinda na sani." Shuru fadar tayi Maimartaba yana nazari akan maganar da nayi, yace."Me ya hanaki cin doyar bayan kema kina bukata." Jin abinda yace ya sanya gabana faduwa, cikin mika lamura na ga Allah nace"Lokacin ina sauri na shiga karatu shiya banyi tunanin tsayawa naci ba." Girgiza kansa yayi kafin ya kalli Jakada dake tsaye a bakin kofa yace."Kaje da yarinyar can cikin gida ka rufeta a dakin duhu gabad'aya hujjojin da ta kawo basu gamsar dani ba ina ganin idan taji matsa zata fada min yanda al'amarun suka faru." Kuka na fashe dashi nace"Ranka ya dade wallahi tallahi iya gaskiyata na fada maka ban san komai ba akan faruwar wannan al'amari ranka ya dade ka yarda da rantsuwata." Babu yabo babu fallasa yace."Kwantar da hankali binkice zanyi akan al'amarin idan na gano gaskiya zansa a fito dake." Gwiwa a sanyaye nace"Godiya nake ranka ya dade ina rokon Allah ya bayyana mai gaskiya akan faruwar wannan al'amari." Ameeen yace ya bawa Jakada umarnin tafiya dani dakin duhu. "Ya sunanki."? Suwaiba dake gurfane tana shar" ba gumi tace"Sunana Suwaiba Munzali." Maimartaba yace."Ke kika soya doya a bangaran Yarima ko."? da sauri tace"Eh nice ranka ya dade." Yace."Waye ya baki guba kisawa Yarima a cikin abincinsa." Suwaiba hannu tasa ta sharce gumin goshinta cikin inda inda tace "Ranka ya dade babu kowa." Yace."Sumayya ta tabbatar min da cewa kece kika soya doyar ta shigo ta sameki kina aiki kafin Yarima ya sallame ki bana son kiyi min gardama akan abinda na tambayeki inaso ki fada min gaskiyar abinda ya faru.'' Suwaiba kuka ne ya 'kwace mata jiki na kyarma tace"Wallahi babu kowa ranka ya dade ni dai nasan na soya doya da kwai amma bansan abinda ya biyo baya ba." Shuru yayi yana kallonta babu shakka yaran naso suyi masa wasa da hankali a cikinsu dole a samu mai gaskiya da mara gaskiya dan haka itama Suwaibar tunda ta'ki fada masa gaskiyar magana sai kawai ya umarci Jakada da ya kaita dakin duhu inda yasa aka kai Sumayya. Mun jima muna kallon junanmu cikin yanayi na tashin hankali da damuwa nace"Suwaiba ashe baki ji maganata ba sai da kika janyo mana shiga masifa yanzu meye ribarki a duniya idan aka hada baki dake aka kashe rai me zaki ce da Ubangiji a ranar lahira." "Ke kinga Sumayya kada ki d'ora min sharri dan sabida kinga ta kwa'be dake a ciki shine zaki ce naji tsoron Allah to idan banji tsoransa ba tsoranki zanji mtssw! dan Allah kada ki sakeyi min wannan maganar dan ni ban zubawa kowa guba a abinci ba kije ki tuhumi kanki." Tsabar haushi da takaici kasa cewa komai nayi ina kallonta sai surutai take tana fuffukar karya nace"Shikkenan tunda kin k'aryata kanki akan abinda kika aikata insha Allahu a yau sai Allah ya tona muku a siri keda wa'inda suka saki." "Sai dai Allah ya tona miki asiri banza kawai! kece baki da tabbas amma ni na tabbata ba zan kwana a gurin nan ba za'a fito dani banza kawai." Shuru nayi mata ina jinta tana zagina gami da fadin na zuba ido na gani sai an fita da ita daga gurin an bar ni a ciki. Gefe guda na samu na karkade kurar dake gurin na zauna ina bin dakin da kallo, tabbas ya amsa sunansa dakin duhu babban daki ne wanda yake da taga d'aya itama yar mitsitsiya kuma acan sama take, ta wannan tagar haske yake dan shigowa, idan mutun na dakin baya gane yanayin gari safiya ko dare sai dai kawai kaji kiran sallah yanzu ma hakane ya kasance ina zaune a gefe Suwaiba na zurga zurga a dakin mukaji kiran sallar magariba na mike tsaye na isa bakin kofar fita, kofar na dinga jijjigawa rufe take gam ko motsi takiyi, juyowa nayi cikin rauni da sarewa da al'amarin muka had'a ido da Ita gani nayi tana share hawaye nace"A'a ya kike kuka keda kikace baki da damuwa." Tsaki taja ta koma jikin bango ta jingina, girgiza kaina nayi naje na zauna a inda na tashi, addua na cigaba dayi a cikin zuciyata Motsin bude kofar mukaji da sauri na mike tsaye Suwaiba kuwa har ta kai bakin kofar tana zazzare ido. Wani babban bawa ne ya bude kofar duk muka zuba masa ido muna kallonsa, gefe ya matsa yana me yin kasa da kansa, Muddibo ne ya shigo dakin, gabana ya yanke ya fadi ganin yana watsa min wani irin kallo, sunkuyar da kaina nayi, ya kalli Suwaiba da fadin"Biyo bayana." Da sauri na dago kaina naga Suwaiba da sauri tabi bayansa nima sai na rufa mata baya, tana fita nayi yunkurin bin bayanta mari ya kwada min ya tankad'ani ciki faduwa nayi kaina ya bugu da wani babban dutse dake girke a gurin, dishi dishi na dinga gani kafin na fadi a gurin, Muddibo umartar bawan yayi da yayi maza ya kulle dakin.......... Magajin sarki ya shiga tsananin rudani a lokacin da aka kai masa manya hadiman sa a sume a take ya shiga basu taimakon gaggawa da irin baiwar da Allah yayi masa, cikin ikon Allah Haruna da Hamza suka farfado Isa kuwa ta Allah ta kasance a kansa ya mutu, Haruna da Hamza suka dinga kuka suna kallon gawar dan uwansu, Magajin sarki duk dauriyarsa sai da ya zubar da hawaye hakika mutuwar Isa ta ta'ba shi, ma'aikata ya umarta dasu had'a gawar Isa su daureta. Lokacin da Maimartaba ya samu labarin mutuwar daya daga cikin mutum ukun da tsautsayin ya ritsa dasu, hankalinsa ya tashi ainu! ya dinga mamakin al'amarin yana tunanin da tuni fa d'ansa ne zai mutu idan da Allah ya nufe shi dacin doyar, lallai babu shakka dole ya tsautsara binkice akan wa'inda keda hannu gurin faruwar wannan al'amari. Magajin Sarki bai bari ya fito daga asibitin ba sai da ya tsananta binkicensa akan sanin wace irin guba akayi amafani da ita domin a cutar dashi, ragowar doyar dasu Haruna suka rage ita yasa aka dauko masa yayi ta binkice a kanta har sai da ya gano yanda al'amarin yake, anyi amfani da gubar ne a cikin man da'aka soya doyar ya dinga girgiza kansa tabbas wanda ya aikata wannan aikin bashi da imani kuma baya k'aunarsa da gasken gaske, dole ne shima ya tsananta binkicensa akan faruwar al'amarin......hannuwansa ya wanke tas ya dauki rigarsa ta likitoci yasa yasa farin gilashinsa, kana ya kwashi wayoyinsa da duk abinda yake bukata ya fita daga ofis din nasa, Direban sa ne ya bude kasa kofar mota ya shiga ya zauna, da sauri ya zagaya gurin zamansa ya kunna motar suka fita daga asibitin........a rikice ya tarar da gidan sarautar mutane sunyi cirko cirko kowa yana alhini akan abinda ya faru, umartar direban yayi daya yatsar da motar, ya zuge glass wani bawa ya kira da sauri yaje ya runkufa yana gaisheshi ba tare daya amsa ba yace."Kowa ya koma gurinsa tsayuwar bata da amfani wanda ya mutu ya riga ya mutu addua zakuyi masa." Da sauri bawan yace."Ranka ya dade a gafarce mu bari nayi sauri na isar musu da sakon ka." Gilashin motar ya rufe ya bawa direba umarin tafiya. Ciroma na zaune a dakinsa yana jijjiga kafarsa ya kalli Muddibo rai a bace yace."Gabadaya al'amarin beyi min dadi ba naso ace Shi wanda akayi aikin dominsa shine ya mutu ba bawan sa ba, amma babu komai insha Allahu hak'an mu sai ya cimma ruwa a kansa." Muddibo cikin rashin jin dadi yace."Nima wallahi gabadaya al'amarin beyi min dadi ba amma ina ganin dole ne mu d'auki shawarar mu ta biyu akansa amma ba zamu gabatar da komai ba yanzu sai 'kura ta lafa tukkuna." Ciroma shuru yayi yana kumbura fuska, hannu ya mika ya dauki tufa yasa a bakinsa yana taunawa yana girgiza kansa yaso ace Yarima ne ya sheqa barzahu da yafi jin dadin hakan amma babu damuwa shima ba zai tsallake tarkonsu ba. Kai tsaye bangaran mahaifiyarsa ya nufa, koda ya shiga samun iyayen nasa yayi sunyi jugum! kana ganinsu kasan suna cikin alhini da damuwa, zama yayi kansa a kasa ya gaishe su, suka amsa suna binsa da kallon tausayi da jin kai irin na iyaye da tuni ma'kiya sun samu galaba a kansa, A nutse yace." Ranka ya dade ya mukaji da wannan mummunan al'amari daya faru.'' maimartaba ya sauke ajiyar zuciya yace."Sai godiyar Allah kuma muna nan muna addua akan Allah ya bayyana mana wa'inda suke da hannu a cikin wannan al'amarin shi kuma wannan yaro daya riga mu gidan gaskiya muna rokon Allah ya jikansa da gafara."" A nutse ya amsa da ameen kafin yace.'' Ranka ya dad'e kafin na fito daga asibiti nayi binkice sosai akan abincin da ya janyo faruwar al'amarin sosai nayi binkice na gane matsalar daga cikin man da akayi amfani dashi ne ina tunanin ya samu matsala ma'ana yayi expire shine dalilin daya janyo yayi musu lahani a ciki Cike da mamaki suke kallonsa, Fulani tace"Yanzu kana nufin man suya shi ka dai zai iya janyo a rasa rai suma fa sauran Allah ne yayi da sauran kwanansu a gaba da da tsautsayi da tuni sai da labarinsu gaskiya ban yarda da maganarka ba." Maimartaba yace."Anya kuwa Yarima kayi binkice yanda ya kamata nima ina ganin man suya shi kadai ba zai janyo hakan ba Murmushi yayi yana kokarin danne damuwarsa yace."Ranka ya dade ku yarda da maganata gaskiya ce dan kafin na yanke hukunci sai da nayi binkice sosai akan abinda ya janyo faruwar al'amarin nan man suya zai iya kisa mutukar ya tashi daga aiki ma'ana lokacin sa ya wuce ranka ta dade ka tuna kayan abincin dake bangare na a store suke a rufe shi kansa man a gwangwani yake a rufe kuma ya dauki lokaci mai tsayi a ajiye yarinyar nan da tayi aikin abincin bata da ilmin da zata duba ta ga lalacewar abu ta dauka tayi amfani dashi bayan ya gur'bata wannan dalilin yasa na yanke shawara kan cewa gobe idan Allah ya kaimu duk zan sa a fito da kayan abincin dake cikin store d'ina a fita dasu can wani guri a zubar sabida gudun afkuwar wata matsalar." Maimartaba shuru yayi duk jikinsa yayi sanyi tabbas hakan na iya kasancewa "Babana nifa ban yarda da wannan maganar taka ba, har yaushe ka dawo garin da kayan abincin ka zasu lalace kuma me yasa lokacin da wannan yarinyar Sumayya take maka girki ba'a samu matsala makamanciyar wannan ba, nidai ina zargin wannan yarinya Suwaiba da Safiyya ta kawo maka." Girgiza kansa yayi yana kokarin kawar da damuwarsa yace."Mamma dan Allah ki daina zargin kowa akan faruwar wannan al'amari na fad'a miki ga dalili ki yarda a haka ke dai kawai ki cigaba dayi min addua akan Allah ya kare ni daga kowane abin qi." Jikinta ne yayi sanyi tace"To shikkenan babana Allah ya kare ka da kariyarsa." Maimartaba yace."Da har nasa an rufe yaran guda biyu to tunda gaskiyar lamari ta bayyana idan ka fita sai kasa a bud'e su." Yace."To godiya suke ranka ya dad'e." Sarki jijjiga kansa yayi yana kallon yaron nasa tare dayi masa addua a cikin zuciyarsa, mikewa yayi a nutse yace."Ni zan shiga gurina na huta a tashi lafiya." Fulani tace"To babu damuwa yanzu zan aiko maka da abinci nasan dai kana bukatarsa." Ajiyar zuciya ya sauke yace."Mamma tsabar fargaba da tension ya sanya cikina ya cushe amma babu damuwa ki aiko zanci insha Allah.'' maimartaba yace."Ka daure kaci abinci kada ka zauna da yunwa komai yayi tsanani maganinsa Allah.'' Yace."Insha Allah." Sallama yayi musu suka bishi da kyakkyawar addua. *Na kudi ne..*! Kada ki karanta min littafi sai kin biya, keda ki ka fita da book din keda Allah....idan kina so ki biya ga yanda abin yake...vip group #600 normal #300 accont..0542382124...Binta umar gtbank....Idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (kainuwa dashan Allah✊?) 67&68 kame-kame ya fara yana so ya tuna tsayin kwanakin da yarinyar ta dauka bata zuwa aiki, ganin yana kwane-kwane yasa ta 'bata fuskarta a kaurare tace"Babana baka da gaskiya duk yanda akayi kaine ka kore ta da 'bakin halinka." Da sauri yace."Haba mamma kada kiyi min wannan shedar mana wallahi ni banyi mata komai ba kawai wayar gari nayi naga bata zuwa aiki shiyasa ai nace ki aika a kirata a gabana idan nayi mata wani abu sai ta fada." Fulani jikinta ne yayi sanyi tace"Yanzu duk tsayin wannan lokacin a'ina kake samun abinci ni dai baka ta'ba zuwa ka nemi abinci a gurina ba." Ajiyar zuciya ya sauke yace."Mamma ki kwantar da hankalinki na gane abinda kike gudu insha Allah babu abinda zasuyi ya same ni." Tace"Insha Allah ka dai fada min inda kake samun abinci." takarashe maganar idonta a tsaye a kansa "Mamma Lawisa ce take kawo min daga 'bangaransu." Fulani shuru tayi tana kallonsa tana girgiza kanta shikkenan tasan sun wanke sun bashi yasha sai dai kawai ta dage da addua a kansa ba tun yau ba tasan wacece Hajiya Karima macece mai biye biyen malamai duk ta d'ora 'ya'yanta a turba mara kyau shiyasa gabadaya bata kaunar auransa da Lawisa saboda tasan zasuyi tayi wa yaron ta surkulle......."Mamma akwai matsala ne naga kinyi shuru kina girgiza kai." Ajiyar zuciya ta sauke tace"Bani da abinda zance sai dai addua akan lamarin Lawisa ita zaka aura dan ta baka abinci kaci ba laifi bane amma kafin kaci duk abinda zata kawo maka naci ko nasha ka dinga addua tukkuna." A sanyaye yace."Insha Allah zan kiyaye." Wayarta dake kusa da ita dauka ta kira Jakadiyarta, taba umarnin kiran Sumayya. Ina zaune tsakar gidanmu ina bitar karatun al'kur'ani Jakadiya ta shigo, ganinta ya sanya min faduwar gaba, al'kur'anin na rufe a nutse muka gaisa da juna tace"Fulani ce tace kizo tana neman ki." Kafin nayi magana Tambaya tace Allah yasa dai lafiya." jakadiya tace."Lafiya lau babu wani abu insha Allah." Ganin yanda Tambaya ta razana yasa nayi saurin daidaita kaina nace"To shikkenan kice mata ganin zuwa." Jakadiya ta amsa da to ta tafi. mikewa nayi ina yar dariya na kalleta nace"Wai mai yasa duk sanda aka aiko kirana daga cikin gida kika tsorata." Cike da kulawa tace"Dole na tsorara Sumayya bana son wani abu ya same ki na sharri na fahimci mutane nayi mana hassada saboda kawai kina kula da Yarima Lami da sauransu duk sun daina amsa gaisuwata ko haduwa mukayi a gurin rabon abinci basa kulani wani lokacin ina ji suna gulmar mu shiyasa nake jin tsoro kada a shirya miki wani sharrin." Murmushi nayi nace"Kada ki damu insha Allahu babu abinda zai faru sai al'kairi maganar su Lami kuma ki ajiye ta a gefe kiyi abinda ke gabanki Hassada sukeyi idan sun gaji zasu bari." Tace."To shikkenan Sumayya amma ki 'kara kula kinji ko." Nace"Insha Allah zan kiyaye." Takalmana nasa nayi mata sallama na tafi. Cikin nutsuwa nayi sallama na shiga falon, 'kamshin turaransa ya tabbatar min da cewa yana gurin, kaina na sunkuyar kasa na cigaba da tafiya a nutse har na karasa inda suke na zube a gabanta cikin ladabi nace"Barka da dare ranki ya dad'e." Cikin kulawa kamar koda yaushe ta amsa da "barka dai Sumayya ina fatan kuna lafiya.? " Lafiya lau ranki ya dade Jakadiya ta sanar dani kina nema na.'' a nutse na fadi maganar ina kara yin kasa da kaina ban yarda na kalli gefan da yake zaune ba ta gefan idona nake ganin irin kallon da yake min cikin zuciyata nace "Kallo sai kace sabon makaho." Falon ne yayi shuru na minti biyu kafin naji muryarta a nutse ta kira sunana. Amsawa nayi ba tare dana dago ba, Tace."Inaso ki fada min dalilin da yasa kika daina zuwa aikin sashen Yarima ashe kin watsar da amanar dana baki ban sani ba." A sanyaye nace"Ranki ya dade ki gafarce ni ba daina zuwa aiki nayi ba wallahi kwana biyu ne nake ta rashin lafiya shine dalilin da yasa na daina zuwa." A yanda ta fadi maganar tana rawar murya yasa ta gane karya take, Tace"Haba Sumayya mai cuta ai ya fita daban ki dube ki fa a dan tsayin kwanakin da nayi banganki ba kin 'kara girma ban yarda baki da lafiya ba kina 'boye min wani abune ki fad'i min gaskiyar magana shin me babana yayi miki kika daina zuwa ki kula dashi." Shuru nayi dan gabadaya ta daureni da jijiyoyin jikina, tace"Kina jin tsoron ki fada min kada yayi miki wani abu ko."? Da sauri nace"ba haka bane Mamma ki yarda da maganata ta farko bani da lafiya ne amma ni Yarima beyi min komai ba kuma insha Allahu gobe zan cigaba da zuwa aikina." Murmushi tayi tana girgiza kanta tace"Shikkenan tunda kin 'boye kin kasa fada min gaskiya ni zan baki hakuri akan laifin da yayi miki dan Allah ki daure ki cigaba da kula dashi har lokacin da Allah zai kawo lokacin auransa insha Allah kin kusa hutawa tunda an tsayar da rana wata uku masu zuwa idan matarsa nada ra'ayin zamanki domin ki cigaba da yi musu hidima to sai ki cigaba da zama idan kuma bata da ra'ayi sai ta kawo sabbi su cigaba da gabatar da aikin da kika bari ina fata kin fahimce ni kuma kin huce fushin ki." Murmushi nayi nace"Ranki ya dade ki daina hadani da Allah akan wannan al'amarin, wallahi kinfi karfin komai a gurina shiyasa duk sanda wani abu ya taso naga kina bani hakuri nake mamaki! kada ki damu insha Allah nayi miki al'kawarin cigaba da kula da amanarki har zuwa lokacin da kika fada ina rokon Allah ya bani ikon rike amanarki. Murmushi jin dadi tayi tace"Sumayya dole nayi miki godiya domin kin cancanta ayi miki komai kina da hankali da nutsuwa gaki da iya lafazi kyawawan halayenki sune suka sanya naji kin kwanta min a raina har na yarda dake a matsayin mai kula da gudan jinina dan haka dan nayi miki godiya ba abin damuwa bane." Murmushi nayi ina jin kaunar matar a cikin raina, hakika da Yarima ya gaji halinta da karamcinta da baiyi wasu abubuwan ba na rashin kyautawa cikin nuna farin ciki da yabawar da tayi min nace."Ranki ya dade nagode sosai da samun yabo daga gurunki." Kaina ta dafa a nutse tace"Allah yayi miki albarka." na amsa da ameen ina mirmushi. tace"Kina iya tafiya gobe idan Allah ya kaimu sai ki cigaba da aikin ki." Risinar da kaina nayi nace"To shikkenan ranki ya dade a tashi lafiya." A nutse ta amsa tana murmushi, gefan da yake zaune na kalla nace"Ranka ya dade a tashi lafiya." Ciki ciki ya amsa min. na mi'ke a nutse na fita daga falon Koda na koma gurinmu samun Iyayena nayi a zaune a tsakar gida suna magana shigowa ta yasa sukayi shuru dukkaninsu suka bini da kallo, murmushi nayi na zauna kusa da babana a nutse nace"Baba ina fatan baka ci abincin ba." Cike da kulawa yace."Ai ban jima da shigowa ba mahaifiyarki ke sheda min inda kike." Ganin yanayin damuwa a tare dasu yasa nace"Eh hakane dan Allah ku kwantar da hankalin ku ba wani abun bane aiki tasa ni shiyasa kuka ga na dad'e." Ajiyar zuciya ya sauke yace."To Alhamdulillah maza jeki dauko mana abincin muci." Da sauri na mike na nufi kicin domin dauko abincin...Tambaya daki ta shiga ta shiga gyara mana gurin kwanciya, nida mahaifina abinci muke ci a nutse muna hira cikin fahimtar juna shakuwar dake tsakanina da babana ba takai wacce take tsakanina da Tambaya ba, babana mutum ne mai sauki hali yana da barkwanci kullum cikin wasa da dariya yake kuma dukkanin abinda za'ayi masa na 'ba tanci ba zaka ta'ba ganin bacin ransa ba mutum ne wanda duniya da dukkanin abinda ke cikinta be dameshi ba. Washe gari da wurwuri na tashi domin ina so naje nayi duk aikin da zanyi na gama a kan lokaci na samu damar zama gurin karatu, tare muka fita da babana ya nufi b'angaran dawakai ni kuma kai tsaye sashen Yarima na nufa, duk wannan sammakon dana buga samunsa nayi a shirye cikin k'ananun kaya da cup a hannunsa ya shirya tsaf da alama daf yake da fita gurin aiki. jikina ne yayi sanyi na kalli agogon bango nan naga karfe bakwai da rabi, shaf na manta ya fara fita aiki dana sani ina idar da sallar asubahi na shigo nayi ayyukana na huta. Babu walwala a tare dani nace"Ranka ya dade barka da safiya ina fata ka tashi lafiya."? Cup din tea din ya ajiye kan tevur din dake gabansa babu yabo babu fallasa yace."Barka kadai." Kicin na nufa ba tare da na sake magana ba. Suwaiba na samu tana soya doya da kwai gaisawa mukayi na tsaya ina tunanin abunyi....kamshin turaransa ne ya tabbatar mana da shigowarsa kicin, Kasa nayi da kaina dan har yanzu ina ganin bakinsa, a nutse yace."Ke Ki ajiye wannan aikin da kikeyi me shi ta dawo kije kawai na sallame ki kada ki kara zuwa kiyi min hidima." Suwaiba ta ajiye abin hannunta a nutse tace"Godiya nake ranka ya dad'e." Hanya ya nuna mata da hannunsa alamar ta futa, kai a kasa ta fita daga kicin din. Shiru na minti biyu kafin naji gyaran muryarsa, dago kaina nayi babu walwala a tare dani, yace."Me yasa baki zo akan kari ba? ko kin manta na fara fita aiki.'' Nace"Wallahi na manta amma ka gafarce ni naga Suwaiba ta gama hada komai bari kawai na fito maka dashi.....girgiza kansa yayi alamun baya bukata. Juya yayi zai fita yace."Idan na dawo daga asibiti ina da muhimmiyar magana dake." Bayansa nabi da kallo ina mamakin wace magana zamuyi, har ya fice daga kicin din ban dauke kaina daga hanyar daya bi ba, na jima sosai a kicin din ina tunani akan maganarsa, ajiyar Zuciya na sauke ina addua akan Allah yasa al'kairi ne ke tafe dashi, kicin din na gyara tsaf na juye soyayyar doyar da Suwaiba ta soya a cikin kula na dauka na fita da ita, can gurin su Haruna na nufa na dire musu kular a gabansu, Haruna yana murmushi yace."Ranki ya dade me muka samu ne."? Cikin kulawa nace"Soyayyar doya ce na kawo muku Suwaiba ta soyawa Yarima tayi mishi yawa shine na yanke shawarar kawo muku." Cike da farin ciki ya kalli su Isa da fadin "Ku taso ga abin arziki Sumayya ta kawo mana." Gurin suka iso suna min godiya na dinga mamakin godiyar da sukeyi min. nace"Haruna ni zan tafi gurin karatu sai yamma zan shigo." Yace."To babu damuwa Sumayya." gurin na bari da sauri naje na dauko jakar litattafaina na wuce gurin karatu.....ko zaman minti ashirin banyi ba hayaniya ta tashi wani malami ya shigo ajinmu da fadin"Ke Sumayya fito." gabana ya fadi jin ya kira sunana! fitowa nayi daga cikin 'yan uwana ya tasa ni a gaba tun kafin mu karasa gurin na hango Haruna da Isa ri'ke da kirji sai kakarin amai suke, a gigice na k'arasa inda suke ina tambayar abinda ke faruwa Usuman ne yace."Ki rufe mana baki anan gurin ba kece silar faruwar komai ba." Murya na rawa nace"Usuman ban fahimce ka ba dan Allah kayi min bayani." Tsaki yaja kafin yace."Tun bayan da sukaci doya da 'kwai din da kika basu cikinsu ya hautsine sai amai suke suna zawo ko ba kiga yanda kudaje ke bin gurin ba.'' Da sauri na shiga binsu da kallo naga yanda kudaje ke binsu suna tashi sai kakari suke suna yunkuri idanunsu yayi jajawur! kuka na fashe dashi nace"Wallahi tallahi bani bace." Buba ya kawo min mari a fusace yace idan baki rufe bakin ki ba yanzu zaki sha duka anan gurin." Gum! nayi ina zazzare ido hade da kallonsu Haruna dake durkushe a gurun.......Jakadan maimartana ne ya iso gurin shida wasu fadawa suka saka su Haruna a mota suka nufi asibiti, hankalina ya tashi sosai na juya domin shiga gurinmu, Jakada yace."Kece Sumayya ko."? da sauri na daga kaina. Yace."Muje Maimartaba nasan ganinki." gabad'aya gwiwata tayi sanyi jin abinda yace bani da yanda zanyi dole nabi bayansa zuwa fadar Maimartaba nasan dai zai tuhume ni ne akan abinda ya faru dasu Haruna........ *Na kudi ne!* Allah ya isa idan kika karanta! idan kina so ki biya ga yanda abin yake vip group #600 normal group #300 account.. 0542382124...Binta umar gtbank idan kati zaku turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number. *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 73&74 Da 'kyar na iya cin abinci na mik'e domin wanko hannuna dakin na dawo na same su suna magana shigowata yasa suka tsira min ido, a nutse nace"Zanje sashen Yarima koda abinda yake bukata nayi masa, cike da tausayi da kulawa sukace "To sai kin dawo." Fitowa nayi daga dakin nasa takalma na fita. Koda na shiga falon shuru babu kowa da alama yana sama ko kuma be shigo ba, juyawa nayi da niyyar shiga kicin naji motsinsa, a hankali na juyo ina kallonsa yana sakkowa, kaina na sunkuyar har ya sauko ya zauna kan kujera gaishe shi nayi hade da fadin"Ko kana da bukatar wani abu.'' Kai ya girgiza kafin yace.''Bana bukatar komai kije ki huta." Tsira masa ido nayi......ganin inaso nayi magana yasa yay saurin katse ni da fadin"Sarkin zargi da rashin yarda nace kije ki huta naci abinci a gurin Mamma. Sarkin zargi da rashin yarda maganar nayi ta nanatawa a cikin raina wato duk abinda nake nunawa a kansa bai dameshi ba tunga gashinan yayi min wata fassarar tunda nake kula dashi dayi masa hidima bai ta'ba yi min godiya ba ko kuma ya nuna min jin dadinsa kullum cikin fada min bakar magana yake, kaina na girgiza ba tare dana sake magana ba na juya da niyar fita daga dakin. "Sumayya." a kasalance naji ya kira sunana, juyowa nayi muka hada ido dashi, yace."Idan hankali ya kwanta inaso muyi magana dake." ajiyar zuciya na sauke ina kallonsa ido da ido nace"Ko wace irin magana ce take bakin ka zaka iya fada min a yanzu ina sauraronka." Girgiza kansa yayi yana lumshe ido yace.''Sai kin samu nutsuwa tukkuna dan na fahimci yanzu bakya cikin hayyacinki." Kaina na girgiza tare da fadin"Babu damuwa Allah yasa naji alkairi." Murmushi yay had'e da shafa sajensa yace ."Alkairi ne insha Allah.'' Ganin yana munafikin murmushi yasa na tsargu babu shakka har yanzu akwai mugun abu a cikin zuciyarsa, sallama nayi masa na kama hanya na fita ina mamakin al'amarin Cikin kwanaki bakwai da rasuwar Isa al'amura sun d'anyi sauk'i masarautar ta samu nutsuwa kowa ya fawwalawa Allah ya cigaba da harkokinsa 'bangaran basawan masarautar kuwa kullum cikin shirya kitumurmura da ma'kar'kashiya sukeyi har yanzu sunqi saduda burinsa bai wuce ace sunga bayan Yarima Ali ba inda shi kuma nashi bangaran kullum zuciyarsa fes take a kansu baya ta'ba yarda da cewa sharrinsu da makircinsu zaiyi tasiri a kansa tunda ya riga ya kad'aita Allah yayi ya'kini da cewar babu abunda zai sameshi sai abinda Ya hukunta, ko a fuska bai ta'ba nunawa kowa ba duk bayan kwana biyu sai ya shiga kowane sashe na gidan sun gaisa inda su kuma suke nuna masa kauna a fili a bad'ini kuwa su kadai suka san irin 'kiyayyar da suke masa Magajin Sarki ya turke Suwaiba ita dashi ya tsoratar da ita mutuka Suwaiba na kuka gami da nadamar abinda tayi ta sheda masa yanda al'amarin ya faru, wato Muddibo ne ya tursasata kan lallai sai tabi umarninsa tayi amfani da wani igur'bataccan ruwa mai wari daya kawo mata cikin wata jarka yace lallai tayi dahuwar abinci da ruwan kuma ta tabbatar Abinda ta dafa Yarima yaci, babu yanda ta iya haka ta dinga mu'ku-mu'ku da ruwan guban har dai ta yanke shawarar dafa doya dashi, bayan ta tsame doyar ne tana tsaka da soyawa a ranar da al'amarin zai faru ya shigo kicin din ya sallameta daga aiki ita kuma Sumayya ta dauka ta kaiwa su Haruna suka ciki. Magajin Sarki beyi mamaki ba dan yaji ta ambaci sunan Muddibo dama tuntuni yake zargin akwai sa hannunsa a cikin faruwar al'marin, nasiha mai ratsa jiki yayi mata ya tsoratar da ita sannan ya nuna mata illar abinda ta aikata wato ta amince an hada baki da ita anyi kisan kai. Suwaiba kuka kawai take tana neman gafararsa, yace."Bani zaki nema gafara ba Allahn daya hallice ki shi zaki nema gafara ki tuba ki nemi gafararsa sai ya yafe miki." Tace."Insha Allah na tuba nabi Allah da manzon Allah ba zan sake yarda wani ya tursasani ga aikata sa'bon Allah ba.'' Magajin sarki yaji dadi sosai da tuban ta, sallamarta yayi ta tafi tana addua akan Allah yasa kada ya fad'awa mahaifinsa harda saka hannunta a cikin faruwar al'amarin, bangaran Yarima kuwa baya tsammanin zai fad'awa kowa maganar domin fitar da ita yana nufin abubuwa da yawa barin ta shine yafi kwanciyar hankali. ****** Yau asabar duk ranakun weakened baya fita da wuri yana gida yana hutawa wani sa'in har na gama abinda nake na fita yana sama yana bacci abunsa abin mamaki yau dana shiga samun sa nayi a falo a zaune yana kallon kwallon kafa. gaishe shi nayi babu yabo babu fallasa ya amsa, kicin na nufa ya kira sunana Tsayawa nayi ina kallonsa, kusa dashi ya nuna min. "Zo ki zauna yau ranar taki ce zamu tattauna maganar dana jima ina fada miki." Gabana ne ya fadi ni sam na manta da wata magana, cike da rashin tsoro nace"Yallabai wace irin magana zamu tattauna wacce har sai nazo na zauna kusa da kai." remot din hannunsa ya ajiye yace."Magana ce ta mussaman wacce take bukatar sirri." Ajiyar zuciya na sauke nace"Ni da kaine kadai a dakin nan ina ganin ba sai na zauna kusa da kai ba babu wanda zaiji ko ya gani kawai ka fadi maganarka ." 'Kure ni yayi da ido yana kallona, nima nawa idon nasa masa dan gabadaya yanzu na daina jin tsoransa, "Kinga ni ba wani abu zanyi miki ba naga kina min kallon rashin yarda maganar da zanyi miki nafi bukatar na ganki a kusa dani shine dalilin daya sa nace kizo ki zauna?" Shuru nayi ina naxarin maganarsa a sanyaye yace."Ki yarda dani da maganata ba zanyi miki komai ba." kallonsa nayi naga yana marairaicewa, ajiyar zuciya na sauke naje na zauna kusa dashi. Ya kai minti biyar yana kallon k'asan gurin kafin ya dago kansa ya kalleni, kauda kaina nayi gefe, hannuwana ya ri'ke nayi saurin kallonsa! a sanyaye yace."Sorry.'' ajiyar zuciya na sauke nace"Ka sakar min hannuwa ka kuma fadi maganar dake bakinka." Murmushi yayi yace."Yarinyar nan watarana idan kina bani umarni har mamaki kike bani gaskiya kina da karfin hali kina kuma burgeni wani lokacin kuma kina 'kuntata min" Zum'bura bakina nayi na kauda kaina gefe hannuwana na cire daga nasa. Hannu yasa ya juyo da fuskata naga yana min wani irin kallo wanda ya sani faduwar gaba, da sauri nace"Wai baka zaka fadi maganarka ba." Ba zato naji saukar hannunsa a le'bena yana shafawa.'' doke hannun nayi ido jawur nace"Ai dama nasan sai ka gwada halin ka." mikewa nayi da sauri yay gaggawar mayar dani na zauna Fuska a hade yace."Ni kike dokewa hannu.'' hanci na hura ina ji tamkar na doki bakinsa dan haushi fitinannan mutum ne shi mai 'ketare iyakokin ubangiji. Ajiyar zuciyarsa naji na kalleshi naga ya shiga hankalinsa sosai, kasa nayi da kaina ina jiran naji ta bakinsa "Kin san abinda yasa nace kizo kusa dani muttauna." ? girgiza kaina nayi nace"Sai ka fada." Yace."Na dauki d'amarar auranki kamar yanda kika kwad'aita min zan aureki insha Allahu ina bukatar amincerki." Kai tsaye nace"Yallabai ai ka makara me yasa tun lokacin da nayi maka maganar baka amsa ba a yanzu iyaye sun riga sun shiga cikin lamarina da Haruna an tsayar da maganar auranmu wata hudu masu zuwa maganar auranmu ma maimartaba ya san da ita Wani irin shan kunu yayi yana kallona yace."Karya kikeyi kizo min da wannan maganar baku isa ba keda Harunan naki aure ni zan aureki shi yaje can ya nemi daidai dashi.'" Cike da mamaki nake kallonsa nace"Haruna nice daidai dashi kamar yanda yake daidai dani kaine zakaje ka nemi daidai da kai tunda ka fada cewa ni ba tsaran auranka bace.'' Shuru yayi gumi na yanko masa. nace"Idan ka gama maganarka ni zanje nayi aikina." Ido jajawur ya dago yana kallona yace."Na fada miki fa baku isa ba wallahi sai an warware maganar auranki da Haruna ko kuma naga bayansa." Gabana ya fad'i jin abinda yace nace."Ranka ya dad'e kana musulmi kake fad'ar wannan maganar zaka ga bayan Haruna me zakayi masa to."? Ido yasa yana kallona nace"Ashe kaima zuciyarka irin ta 'yan uwanka ce gashinan kana mummunan lafazi akan wanda be maka komai ba." Ajiyar zuciya ya sauke ya kama hannuwana duk biyun ya rike a raunane yace."Kada kiyi min wata fassara ta daban raina ne ya 'baci na fad'i wannan maganar Please Sumayya muyi maganar da zata amfane mu ni dake a yanda nake jin ki a zuciyata bana tsammanin zan iya bari Haruna ya aure ki." Nace"Ranka ya dad'e Haruna shike sona tsakani da Allah kai kuma sha'awata kake zaka aureni domin ka kawar da sha'awarka shikkenan idan bukatarka ta biya sai ka sake ni, Haruna kuma zai aureni saboda yana sona tsakani da Allah badan wani abu na jikina ba kai kanka ka zauna kayi nazari da tunani akan al'amarin nan Yallabai kasowa kanka abinda zakasowa d'an uwanka yanzu babu wata sauran magana a tsakanina da kai tunda maganar aurena da Haruna ta shiga tsakani." "Kin san dai Haruna bai isa ya had'a neman aure dani ba ko."? kallonsa nayi inaso nayi magana ya katseni a harzuqe yace.''Kije ki kira min Harunan naji ta bakinsa." Cikin fad'uwar gaba nace"Bangane kaji ta bakinsa ba." Hannu ya d'aga min fuska a had'e yace."Kada ki sake harzuqani kije ki kira min shi nace." Jikina ne yayi sanyi nace"Dan Allah ka bar wannan maganar ka fuskancin abinda ke gabanka ka auri daidai da kai nima na auri daidai dani." "Sumayya." ya kira sunana kallonsa nayi, yace."Ba zan hakura dake ba ki rubuta wannan ki ajiye idan kin auri Haruna kin barni sai na hana ku jin dadin rayuwa gwara ku magance matsalarku keda shi Nafi karfin na nemi abu wanda yake kark'ashina ya had'a takara dani dole Haruna ya janye maganar auranki." Nace"Ranka ya dad'e lafazan ka na nuna min cewar babu kyakkyawan nufi a cikin zuciyarka kada ka cutar da Haruna dan beyi maka laifin komai ba kuma ka daina gwada iko da mulki a kaina Allah ba'a nuna masa gadara idan Allah ya kaddara ni d'in ba matarka bace ya zakayi."? Jajayen idanunsa ya zuba min yace."Bakya shakka kallon tsabar idona ki fada min magana ko." ? sunkuyar da kaina kasa nayi nace"Gaskiya d'aci gareta shiyasa kake gani kamar naci maka fuska." Kwafa yayi yace."Dallah tashi ki bani guri kafin na da'uke fuskarki da mari."!! ganin yanda yake zabura yana huci! yasa nayi gaggawar tashi ina mamakin al'amarin.......kicin na nufa ba tare da naje aiken da yayi min ba. Mikewa yay ya bude kofa ya fita, suna ganinsa suka taso daga inda suke zubewa sukayi a gabansa suna tambayarsa, babu walwala a tare dashi ya kalli Haruna da fadin"Ka shigo ina neman ka." Haruna yace."To ranka ya dade." Juyawa yayi ya koma ciki Haruna yabi bayansa. Yana tsaye a tsakankanin kujeru Haruna ya same shi, Cike da ladabi yace."Ranka ya dade ina fata banyi laifi ba. wani irin kallo yayi masa kai kana ganin kallon kasan na kishi ne......Yace."Meye tsakaninka da yarinyar nan Sumayya."? Haruna yasha jinin jikinsa a sanyaye yace."Ranka ya dade itace matar da zan aura.''' ''Yaushe aka tsayar da ranar auran naku bani da labari."? Haruna ya sake kaskantar da kansa yace."Ranka ya dade ayi min afuwa wallahi na sha'afa shiyasa ban fada maka halin da ake ciki ba." Ajiyar zuciya ya sauke ya zauna kan kujera yana kallonsa da wata iriyar murya yace."Inaso ka janye maganar auranka da Sumayya."! Haruna gabansa ya buga da sauri ya dago kanshi yana kallonsa bakinsa sai rawa yake ''Ranka ya dade ban.......! Hannu ya daga masa ya hanashi karasa maganarsa, Haruna 'kasa yayi da kansa Gumi na tsiyayo masa. "Kasan a 'karkashina kake ba zai yuwu ina neman abu kana nema ba dole ka janye maganar auranka da yarinyar nan." Wannan maganar da yayi yasa Haruna ya gane inda ya dosa. Shuru yayi ya kasa magana yayin da gumi ya jikashi jagab ta yaya zai janye maganar auransa da Sumayya bayan ansa rana iyaye da abokanan arziki duk sun san halin da ake ciki, ta yaya zai iya cire tsananin so da kaunar da yake wa Sumayya a cikin ransa? babu shakka wannan babban al'amari ne a gare shi. "Haruna kana jina ko."? da sauri yace." Eh Yallabai naji maganar ka nasan kai ba sa'ana bane ta kowane fanni! insha Allahu zanbi umarninka." "Okey nagode sosai inaso ka shedawa iyayenka umarnina." Jiki a mace yace."Idan Allah ya yarda zan sheda musu." "okey kana iya tafiya." Yafada yana nuna masa hanya da hannu. Yana juyowa muka had'a ido dashi, sai naga yayi wani irin murmushi kai kana ganinsa kasan na saduda ne tabbas bahaushe yayi gaskiya da yace ( bakin rijiya ba gurin wasan makaho bane) ina shi ina had'a neman aure da Magajin sarki mai jiran gado tilas yanaji yana gani ya hakura da Sumayya ya bar masa, girgiza kansa yayi yana kallona nan na hango yanda idanunsa ya tara ruwan hawaye da sauri ya bude kofa ya fita. Nima hawayen dake kokarin zubo min na mayar ina danne wani k'aton abu a mak'ogwarona, kallonsa nayi yana hard'e a kan kujera nace."Wallahi idan ka raba wannan soyayyar da k'arfin mulkin ka idan ka raba wannan k'aunar da karfin ikon ka to na tabbata Allah ba zai barka ba, kuma mutukar ka samu nasarar raba tsakanina da masoyina na gaskiya ka rubuta ka ajiye ko ka aureni ba zaka samu biyan bukatarka ba, saboda haka ka zauna kayi tunani da kyau akan maganata." Hanya na kama zan fita, da sauri na ganshi ya tari gabana zuba masa ido nayi ina kallonsa, Yace." Ni kuma nayi al'kawarin auranki ko kina so ko bakya so auranki bani na nema ba ke kika nema bayan kin kwad'aita min kuma daga baya kizo min da wata maganar banza! to na d'aura d'amarar auranki domin na kawar da sha'awata a kanki." Cikin 'kunar zuciya na kalleshi magana nake so nayi tsabar bacin rai da takaici ya hana ni cewa komai ratse shi nayi zan wuce ya sake tare min hanya yana min wani irin kallo. girgiza kaina nayi nace "Bani hanya na wuce." Sake babbake hanyar yayi ya dogare hannusa a jikin bango....karfi nasa na doke hannun na ture shi! taga-taga yayi zai fadi baki ya bude yana kallona! tsaki mai karfi naja na bude kofa na fita. Murmushi yay yana mamakin k'arfin yarinyar har ta iya tureshi yana tsaye bai dauki mataki ba, kan kujera ya zauna yana tunanin ta yanda al'amarin zai yuwu..... *Na kudi ne* Kada ki karanta min littafi sai kin biya ke kuma da kika futar da littafin keda Allah, idan kina so ki biya ga yanda abin yake....Vip group #600 normal group #300 account.... 0542382124.....Binta umar gtbank....idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min magana ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 71&72 Cikin kasala da mutuwar jiki yake tafiya tsirarun mutanan da suka rage a gurin suka dinga mika gaisuwarsu zuwa gareshi baya iya amsawa hannu kawai yake daga musu ya wuce.....Ya kusa isa kofar shi ya tuna da maganarsu da Maimartaba idan yake cewa idan ya fita ya bada umarnin fito da yaran, kai tsaye can ya nufa ya tarar da masu tsaron kofar suna shawagi a gurin, suna ganinsa suka zube gwiwa a kasa suke gaishe shi tare da sunkuyar da kansu kasa, a kasalance yace."Ku bude yaran nan su fito." Yana kare maganar ya juya da niyar barin gurin........."Yallabai babu lafiya." Da sauri ya juyo yana kallon mai maganar cikin rawar murya yace." 'Daya daga cikin yaran ce ta suma." Gabansa ne ya fadi jin abinda bawan ya fada, da sauri ya dawo da baya, bawan ya matsa masa hanya ya shiga dakin, wayarsa ya kunna yana haskawa, ganinta a shema tamkar matacciya gabansa ya tsananta fad'uwa! da sauri ya tsuguna kusa da ita tare da umartar daya daga cikinsu ya kawo masa ruwa. Ido ya tsirawa fuskarta yana mamakin tsayin lokacin data dauka a sume, hannunsa ya d'ora a kirjinta shuru babu alamun numfashi, ya sauke ajiyar zuciya tare dayin zaman durshan a gurin, kanta ya tallafo ya dora a cinyarsa, yana danna kirjinta a hankali a hankali, Bawan ne ya shigo da ruwa a hannunsa, ya kar'ba tare da umartarsa ya futa, bayan futar bawan sai ya shiga shafa mata ruwan a fuskarta da wuyanta yanayi yana kallon fuskarta, ya kai minti goma sha biyar yana aikin shafa mata ruwa a fuska bata motsa ba, jikinsa ya dinga kyarma yana addua Allah yasa itama ba mutuwa tayi ba.......Ruwan ya ajiye a hankali ya gyarata a jikinsa rigarta ya cire yayi saurin kauda kansa yana sauke wani irin numfashi, ya kai minti biyar yana kallo gefe guda kafin ya dan juyo a hankali yasa hannunsa a ruwan ya d'ebo ya yayyafa mata a jikinta ya cigaba da shafawa a kirjinta, hannunsa na mutsika nonowanta yana ya'ki da zuciyarsa kada ta rinjayeshi, yafi bukatar ta farfad'o tayi rayuwa a duniya. Ido jawur ya cigaba da shafa mata ruwa a sassan jikinta yana sakin wani irin nishi mai wahalar gaske. Ganin gashin idanunta na motsi yasa ya sauke ajiyar zuciya, alhmdullhi ya fad'a sai ya saurin de'bo ruwan da yawa ya yayyafa a fuskarta, a firgice ta bude idonta tana kalle-kalle a dakin, wayarsa ya dauka yana haskata, ta dinga kallonsa shima yana kallonta, jikinta tabi da kallo taga babu riga ballanatana breziya duk ya cire mata ga sanyin ruwa tana ji da tashin tsigar jiki, hannuwanta tasa ta rufe kirjinta zafafan hawaye suka shiga zubowa a fuskarta bakinta na rawa take so tayi magana amma ta kasa fargaba da tashin hankali sun dabaibayeta A kasalance yace."Kina iya saka kayan ki ko na sanya miki.'' Kallon banza na watsa masa ina masa kallon macuci azzalami wato duk guje-guje na sai da yasan yanda yayi yazo ya cutar dani Hannu nasa na goge hawayen fuskarta, Yace."Kisa kayanki mu fita daga cikin duhu da sauro." Banzar harara na watsa matsa tare da dauke kaina "Kada ki 'kara hararata ballantana kiyi min tsaki sai ranki ya 'baci.''' A zafafe nace" Sai me idan raina ya 'baci! ashe da sauran 'bacin rai bayan wannan da nake ciki, wato ka samu labarin a inda nake shine ka biyo dare kazo ka biya bukatarka a kaina ko."!? Kallona yay da yanayi na 'bacin rai a tare dashi yace."Idan ina so nayi wani abu dake ba sai na biyo dare na fakaici idanun mutane ba, ko can baya ni ne banga dama ba banyi ra'ayin yin abinda nake so dake ba dan haka ki daina wannan maganar sam ba wannan dalilin ne ya shigo dani ba'' A fusace! nace"To ai sai ka fada min dalilin daya shigo da kai! gashi nan ka tu'be min riga kaima ka cire botiran rigarka wane irin iskanci ne yasa zaka tu'be min rigata bayan bana cikin hayyacina." "Sumayya bana neman wata magana mai tsayi na fada miki ba wannan dalilin ne ya shigo dani dakin nan ba ki yarda ko kada ki yarda be dame ni ba ki tashi kisa kayanki mu fita daga cikin duhu." Tsaki! mai karfi naja nace"Babu abinda zan......Bakina ya murd'e min ya tsira min jajayen idanunsa, nan na hango tsantsar damuwa da tashin hankali a cikinsu. Mutsika min le'buna yake cike da muguna hawaye suka dinga karakaina a kuncina, sai da ya gaji dan kansa ya sakar min baki. Kaina na sunkuyar kasa hawayen azaba na zubo min . Rigata ya dauko zai saka min da sauri na daga hannu zan mareshi! ri'ke min hannu yayi ya murd'e da kyau! yace." Marina zakiyi irin na kwanakin baya." Shuru nayi ina kallonsa, yace."Ki kiyaye aikata hakan idan kuma kin'ki watarana kina ji kina gani zan 'balla miki hannu babu abinda ya dameni." Yana gama maganarsa ya jefa min rigata a jiki da fadin "Dallah dauka kisa ki tashi." Babu yanda na iya haka na dauki rigar nasa hannuna daya murde sai zafi yake min. Mikewa tsaye yayi yana mayar da botiran rigarsa, yace."Ina d'aya yarinyar take?" Shuru nayi masa, ya buga min wata irin tsawa da fadin"Ba magana nake ba." Nace"Muddubo yazo ya fita da ita." Shuru yay yana kallona na dauke kaina tare da nufar kofar fita, sawun tafiyarsa naji a bayana da sauri na 'kara gabana ina addua a cikin zuciyata Jugum-jugum! na samu iyayenta Tambaya taci kuka ta koshi kanta sai ciwo yake mata, ina shigowa suka mike tsaye suna godewa Allah! Tambaya rungumeni tayi tana kuka hade da dudduba jikina, nace"Tambaya dan Allah ki daina kuka wuya bata kisa kuma Allah zai bayyana gaskiya dukkaninku ku kwantar da hankalinku Babana ya rike hannuna a sanyaye yace.''Sumayya dole hankalinmu ya tashi ana tuhumarki da aikata mummunan abu ba zamu ta'ba samun nutsuwa ba sai gaskiya ta bayyana babu shakka duk wanda ya aikata wannan abu bashi da imani tunda gashi yayi nasarar kashe mai rai." Cikin faduwar gaba nace"Waye ya mutu a cikinsu.'' A sanyaye yace."Isa ya rigamu gidan gaskiya yanzu haka gawarsa na ajiye sai da safe za'ayi jana'izarsa." Zubewa nayi a gurin ina fadin "Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un!! Tambaya tasa hannu ta rungumo ni ina kuka muka shiga daki tana rarrashina. Yanda naga dare haka naga rana, tsabar fargaba da tashin hankali ya hanani rintsawa, 'bangaran Magajin Sarki ma hakan take a zaune ya kwana yana tunanin yanda zai 'bullowa al'amarin babu shakka akwai saka hannun Muddibo a cikin faruwar wannan al'amarin ya rufewa iyayensa maganar ne saboda gudun tashin hankali dan mutukar Maimartaba ya tabbatar da cewa Muddibo ne ya aikata wannan mugun abun to zai dauki mataki akansa kamar yanda yake yankewa duk mai laifi hukunci, 'Bangaran Ciroma da iyalansa kuwa zasu sake 'kullatarsa dashi da iyalansa gaba gami da 'kiyayyar juna zata sake nunkuwa akan tada shiyasa kawai yace matsalar ta faru ne daga man da'akayi suyar doyar dashi, amma dole ya zauna da yarinyar da tayi aikin ya tsorarta da ita domin ya tabbatar da zarginsa. Kasa tsayawa nayi na karya kummalo na nufi sashensa, nan na samu Haruna da Hamza a harabar gurin sunyi jugum-jugum! ganinsu ya sanya hawaye suka 'kwace min koda na karasa inda suke kasa magana nayi kallonsu kawai nake ina share hawaye. Haruna yace." Ba kuka zakiyi ba Sumayya addua ya kamata kiyi." Nasa hannu na goge fuskata "Haruna ya mukaji da hakurin rashin Isa."! Sunkuyar da kansa yayi murya na rawa yace." Hakuri da godiya Isa ya rasu yayi shahada muna rokon Allah ya gafarta masa." A sanyaye na amsa da "ameeen ya rabbi dan Allah kuyi hakuri da faruwar wannan al'amari Haruna kunsan ba zan ta'ba cutar daku ba, wallahi dana san akwai guba acikin doyar nan ba zan kawo ku muku ba kai kanka kasan yanda mutanan gidan nan ke dauki ba dadi akan Yarima burinsu suga bayansa Allah bai nufeshi da cin doyar ba sai ku gashi sunyi nasara sun kashe wanda beji ba be gani ba amma babu komai zasuje su tarar da Ubangijinsu." Hamza yace.Hakane maganarki Sumayya mu bamu ga laifinki ba wallahi saboda tuntuni mun riga mun san halinki ba zaki cutar damu ba sabida haka ki kwantar da hankalinki duk wanda kikaga ya mutu to dama can kwanansa ya kare Allah yasa ta wannan sanadin Isa zai rasa rayuwarsa muna rokon Allah ya kar'bi shahadarsa.'' Jiki a sanyaye na amsa da ameen ya rabbi ni zan shiga gurin Yarima." Suka ce to sai kin fito." Yana tsaka da saukowa daga benan shi na shiga, sai na tsaya har ya karasa saukowa, kauda 'bacin raina nayi na gaishe shi. a dakile ya amsa min. nace"Me zakace dangane da abinda ya faru jiya."? Harara ya watsa mun yace." 'Yar jarida ce ke da zaki titsiye ni da tambaya."? A dake nace"Dole na titsiye ka da tambaya saboda duk abinda 'yan uwanka keyi maka baka ta'ba yarda gashi sanadiyar cin doyar da aka zuba maka guba a ciki wani yaci ya mutu ina fatan yanzu ka gazgata maganata." "Kinga Sumayya ba wannan ne a gabana ba wanda ya mutu dama can kwanansa ya 'kare mai yasa su sauran da suka ci doyar basu mutu ba, bana son zargi akan abinda mutum baida tabbas a kai nayi binkice na gane ba guba ce ta janyo faruwar al'amarin ba man da yarinyar tayi suyar doyar dashi shine ya gur'bata saboda haka kada na sake jin kinyi wata magana akan wannan al'amarin idan na sake jin kin sako wani nawa a ciki sai ranki ya 'baci! Kallon shashasha nayi masa nace"Ai dama ba zaka ta'ba yarda ba sai ranar da suka kai ka 'kasa sannan zaka yarda da abinda ake fada maka! kai me 'yan uwa kullum baka so ace ga abunda sukayi maka su kuma kullum cikin shirya maka mugun abu suke ka'ki ka gane ka dauki son duniya ka d'ora musu idan sun kashe ka iyayenka su sukayi asara su kuwa ranar zasuyi kwanan farin ciki bukatarsu ta biya a kanka." Har na 'kare maganata idanunsa na tsaye a kaina, yace.''Idan sun kashe ni ina ruwanki."? shuru nayi ina kallonsa ya cigaba da cewa 'yan uwana ne ba naki ba ko Wu'ka suka dauko suna yankar namar jikina idone naki kullum ina fad'a miki cewa ki fitar da kanki akan abinda be shafeki ba kin'ki kije kiyi tayi yanda suke farautata kema ba zasu barki ba." Yana gama maganarsa yazo ya wuce ta gabana fita yayi daga falon, da sauri nabi bayansa na sameshi tsaye shida hadimansa suna magana nan na gane gurin jana'izar Isa zasu tafi! a sanyaye na nufi gurinmu ina share hawaye shikkenan Isa ya mutu mutumin kirki sarkin fara'a da barkwanci Isa bashi da abokin fada kullum zaka sameshi da carbi a hannunsa, duk wanda yasan Isa dole ne ya fad'i halinsa nagari. Koda na koma gurinmu shuru na same shi Tambaya bata nan shima babana baya nan jikina ya bani dukkaninsu sun nufi gurin jana'izar Isa, juyawa nayi nima da niyyar naje can inda ake jana'izar sai kuma nayi wani tunani gurin nasan akwai dandazon mutane ina iya zuwa wata hatsaniyar ta tashi, can kuryar daki na shiga na kwanta a shimfidata rufin dakin na tsirawa ido ina tunanin rayuwa hakika da ina da inda yafi nan da tuni na gudu dan masifar ta isa haka! tunani nake akan maganarmu dashi ta dazu na yarda da maganarsa da yake cewa nima ba zasu barni ba saboda yanda nake saka ido sosai akansa da dukkanin abinda suke aikatawa, ni kaina na rasa me yasa nake damuwa dashi da lafiyarsa sam! bana kaunar abinda zai cutar dashi ko ya ta'ba lafiyarsa inda shi kuma kullum yake nuna min na tsaya a matsayina babu ruwana da 'yan uwansa babu shakka da zan iya dauke idona daga kansa da abinda suke masa to dana zauna lafiya, amma ba zan iya ba saboda ina tsananin tausayawa mahaifiyarsa da mahaifinsa da suka qallafa ransu a kansa, hawaye masu dumi ne suka zubo a kumatuna nasa hannu na goge wasu na sake zubowa hakika ina cikin tsaka mai wuya ina rokon Allah ya kawo mana mafita dani dashi da dukkanin wanda yake da damuwa a cikin zuciyarsa.............Haka na yini a kwance lokacin sallah ne kawai yake tayar dani, Tambaya bata shigo gidan ba sai dab da magariba ta shigo kai tsaye kicin ta nufa ta ajiye kayan abincin hannunta, tsakar gidan na fito muka hadu tace"Ashe kina ciki dama."? kaina na daga nace "Tun dazu dana shigo na tarar bakwa nan bacci ya dauke ni." Tace."Ayya ai bayan futar ki can gurun Iyayen Isa naje akayi jana'iza dani la'asar nayi kuma na nufi gurin aikin abinci shiyasa ban shigo da wuri ba." Nace"Sannu da aiki nima nayi niyyar zuwa sai na fasa saboda gudun abinda ka iya zuwa ya dawo.'' Tace."Ai gwara da baki je ba dan ni kaina zaman hakuri nayi a gurin Lami da sauran mutane sun had'u sai gulma sukeyi suna zaginki dauke kaina kurrum nayi na rabu dasu sukayi su gama." Girgiza kaina nayi cikin 'kunar zuciya nace"Tambaya kada ki damu Allah yana tare da masu gaskiya kedai ki tsananta addua a gurin Allah ya bayyana gaskiyar lamari." Tace!"Addua kullum cikin yin ta nake Insha Allahu Allah sai ya kare ki daga sharrin masu shari.'' Ameen nace na dauki buta domin daura alwalar sallar magariba.... *Na kudi ne* Kada ki karanta min littafi baki biya ba keda kika futar da book din keda Allah idan kina so ki biya ga yanda abin yake....Vip gruop#600 normal gruop#300 account.. 0542382124...Binta umar gtbank idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 77 Sosai ya rike 'kuguna ya matseni a jikinsa yana sauke wani irin numfashi yun'kurin k'wace jikina nayi ya sake matseni a raunane yace."Ba zan sake ki ba sai kin yafe min." Hawaye suka sake xubo min nace"Me kayi min kake neman yafiya a gurina ni ai baiwa ce zan iya kwanciya kabi ta kaina kaga dan ka 'kona ni ai ba wani abu bane." Saukar hannushi naji a kirjina yana shafawa, "am sorry my love." a hard'e ya fadi maganar, yanda yake shafa fatar gurin yasa tsigar jikina duk ta tashi, gabadaya naji gwiwata tayi sanyi, a raunane nace"Sake ni na yafe maka." K'in saki na yayi ya cigaba da shafar gurin 'kunar yana sauke min hucin numfashinsa a wuyana, jikina yay la'asar ikon Ubangiji Allah ya had'ani da nataccen mutum........"Ki bari na duba miki." Da sauri nace."Nifa ban 'kone ba ka sake ni na tafi na yafe maka." Da sauri ya juyo dani kafad'una ya rike ya kurawa fuskata ido kafin naga ya sauke idonsa inda k'unun ya zubawa ido ." ina kallonsa yasa bakinsa yana hura gurin, nayi saurin ture kansa gabana na bugawa, a buge ya dago yana kallona da jajayen idanunsa, dauke kaina nayi daga kallon fuskarsa dan gabadaya ni yanzu al'amarin sa tsoro yake bani. Hannu yasa ya juyo da fuskata yana wani marairaice fuska yasa harshe yana lashe bushashshen hawayen daya bushe a fuskata......mirya na rawa nace"Dan darajar Allah ka bari babu kyau fa abinda da kakeyi ka sakeni na tafi wallahi na yafe maka." Zazzafar ajiyar zuciya ya sauke naga ya daidaita nutsuwarsa hannuna ya rike ya fara tafiya. Turjewa nayi cikin faduwar gaba nace"Ina zaka kaini." ? "Zan duba miki 'kunar ne." Girgixa kaina nayi nace"Ka barta kawai in Allah ya yarda ba zata tashi ba.'' Ido ya tsira a gurin kafin ya sauke ajiyar zuciya ya kalleni, dauke kaina nayi saboda bana son kallon kwayoyin idanunsa, "Sumayya.'' kallonsa nayi saboda yanda naji ya ambaci sunan nawa ya cigaba da cewa" Maimartaba ya umarce ni akan lallai na janye maganar aurena dake." Ajiyar zuciya na sauke lokaci guda naji wani irin farin ciki ya mamaye zuciyata. Girgiza kansa yayi yace.''Nasan jin wannan maganar yasa ki farin ciki ko.''' shuru nayi ina kallonsa! girgiza kansa yayi yana wani murmushi yace."Ni yaro ne mai biyayya gami da bin umarnin iyayena saboda haka zanyi kokari ganin nabi umarnin mahaifina ammafa ki sani duk hanyar da nasan zanbi na hanaku rayuwar jin dadi dake da masoyin naki na sani mafita a nan shine ki mallaka min abinda nake 'kulafuci idan na samu ko sau daya ne to zan barki ki zauna lafiya da mijinki.'' Yanda yake maganar ya nuna min da cewa tabbas zai iya aikata komai akaina da Haruna, jikina ne yayi sanyi na dinga jin tsoron sharrinsa kasa magana kawai nayi na zuba masa jajayen idanuna. "Baki ce komai ba." Yafada yana sake nani'kar Jikina.'' ''Yallabai bani da abinda zance maka saboda na fahimci kayi nisa kuma baka tsoron Allah akan biyan bukatarka babu komai duk abinda zakayi mana kaje kayi Allah yana kallonka.'' "Okey! wannan maganar taki ta nuna min cewa ba zaki bani abinda nake bukata ba." Kai tsaye nace"Wai shin sau nawa zan fada maka wannan maganar ne? na fada maka cewa ba zan ta'ba amincewa da kai akan sa'bon Allah ba ranka ya dad'e ba zan baka kaina ba koda kuwa zaka sa min bakin bindiga a mak'ogwaro na wallahi akan na baka kaina sai dai ka kashe ni."!!! Ya dinga kallona fuskarsa tana rikicewa da wani 'bacin rai gabad'aya kammaninsa sun sauya! nima idanuna nasa masa ina tabbatar masa da gaskiyar maganata........Motsin bude kofa ne yasa gabad'aya muka kalli bakin kofar, gimbiya Lawisa ce ta shigo cikin shiga ta alfarma da alama kwalliyar ta mussaman ce, ganinmu daf da juna yasa nan take yanayin fuskarta ya sanja da zallan 'bacin rai. Matsawa nayi daga jikinsa na sunkuyar da kaina gabana na wani irin fad'uwa, Gimbiya Lawisa ta karaso kusa damu shashshekar kukanta naji tana magana........ da sauri na dago kaina ina kallonta ina kuma mamakin abinda take fada, tana wani irin kuka ta cigaba da cewa"Yanzu meye a jikin wannan mummunar yarinyar da har kake rungumeta a jikinka ashe dama ba aikin abinci kawai take maka ba tana biya maka bukatarka idan ta tas........Wani gigitacan mari ya kwada mata ido jajawur yace."Kada ki sake jifan mu da wata mummanar kalma kawai saboda kin shigo kin tarar damu daf da juna sai ki fassara da wata manufa ta daban! wallahi idan kikayi wasa akan wannan dalilin sai na janye maganar auranki dama ba sonki nake ba takura min akeyi.' Lawisa gumi ya dinga yanko mata kai amma Yarima baida kirki a gaban baiwa ya kwada mata mari yana fadin ba sonta yake ba.sunkuyar da kanta tayi takaicin duniya ya isheta wai shin ya za tayi ta janyo hankalinsa a kanta, tsaki yaja mai karfi ya wuce ya bar mu a tsaye a gurin.. Ganin ya futa yasa nima nayi yunkurin barin gurin, da sauri ta tari gabana na kalleta ta kalleni cikin tashin hankali tace''Sumayya ki fada min abinda ke tsakaninki da Magajin sarki." Cikin jarumta nace"Ke me kika gani a tsakaninmu."? a fusace tace"Wace irin magana kikeyi wannan ki bani amsar tambayata." nace"To babu wani abu dake tsakanina dashi." "Babu abunda ke tsakaninki dashi na ganku dab da juna." Cikin k'osawa nace"Duba kirjina ki gani'' ta dinga wulkita idanunta tana dubawa. nace"Me kika gani."? ''Naga kamar kin kone." Kai tsaye nace"Shi ya 'kona ni da kunun gyada mai zafi haka kawai banyi masa komai ba, idan kina so ki tabbatar ga sheda nan." na nuna mata kayan dake watse a gurun, a sanyaye ta kalleni tace"To me yasa na ganku dab da juna?" kaina na dafe cikin damuwa nace"Nadama yayi da abinda yayi min shine yake min tofi a gurin 'kunar." Ajiyar zuciya ta sauke tace"Allah ya taimake ki kin fada min gaskiya kuma naga sheda a zahiri wallahi da baki fada min gaskiya ba da sai na dauki mataki mai tsauri a kanki''' cikin takaici nace ranki ya dade na baki shawara."? tace"Ina jinki." nace "Ki rage son Yarima domin idan kika bari ya gane zaki sha wahala tunda gashi a gabana yana fadar shi takurashi akayi akan ya aureki.'" Bina tayi da kallo ta kasa cewa komai, ganin haka yasa na sunkuya na kwashe kayan dake watse a gurin, kicin na kai na fito na sameta a tsaye a inda take, goge gurin daya 'baci nayi tas na mayar da Mopar na fito na sameta a tsaye sai kace gunki sai tunani take tsaki naja a zuciyata na kama hanyar futa ina fadin shashasha mara tunani. Ban shiga gurin mu ba sai da na samu Haruna na fad'a masa labari mai dadi. Haruna ya dinga murna yana godewa Allah, a gurin yayi sujjadar godiya ga Ubangiji ya mike yana mana kyakkyawar addua. Jigum-jigum! na samu iyayena a tsakar gida, gwiwata tayi sanyi d'an farin cikin dana shiga dashi ya dauke, guri na samu na zauna ina tambayarsu.. A sanyaye Tambaya tace"Maimartaba ya aiko mahaifinki yaje koda yaje fada sai yace masa maganar auranki da Haruna tana nan dan haka suje su cigaba da shiri shi bai bada goyan baya Yarima ya aureki ba. Sumayya lokacin da naji wannan maganar sai da na kusa kuka gaskiya naso ki auri magajin sarki." Murmushi nayi nace"Tambaya ki daina damuwa dan Allah tunda kikaga Allah yayi haka to shine alkairi." babana yace."Nima abinda nake ta so ta gane kenan amma taki fahimta sai damuwa take." Nace"Hakane baba duk yanda Allah ya tsara haka zamuyi hakuri mu kar'ba nima naso na auri Yarima saboda ganin yanda kuka nuna farin cikin ku amma tunda kukaga Allah ya zartar da wannan hukunci to shine alkairi ni daku sai mu barwa Allah ikonsa'' na fadi hakane domin na kwantar musu da hankali amma ko daya bana fatan auran Yarima saboda nasan da aniyar da zai aureni nafi sha'awar auran Haruna saboda nasan shine daidai dani kuma yana min kaunar da Yarima ba yayi min irinta. ***** Bayan sati biyu al'amura suka cigaba da gudana yanda ya kamata, maganar aurena da Yarima ta rushe tsakanina kuma da Haruna a kullum 'kauna da sha'kuwa na kara 'karuwa a tsakaninmu yanzu mun kwantar da hankalin mu mun daina fargabar abinda zai faru tunda Maimartaba ya shiga cikin al'amarin mun san dole duk wanda yake adawa da auranmu ya hakura, ta 'bangaran Yarima kuwa kullum babu yabo babu fallasa a tsakaninmu ya zuba mana ido dan tun ranar daya 'kona ni wata magana mai tsayi bata sake shiga tsakaninmu ba, kullum ina shiga nayi aikace aikace na baya ce min kanzil sai magana ta kama sannan zai kulani naji dadi sosai daya janye jikinsa dani ina adduar Allah yasa ya hak'ura ya rabu dani nayi rayuwata hankali kwance..................Cikin shiri ya sauko ya same ni ina goge-goge yace."Sumayya bana tsammanin zan zauna nayi breakfast." kallonsa nayi yana gyara necktie d'in wuyansa nace"Ranka ya dad'e yana da kyau dai ka zauna ka karya kafin ka futa idan ka zauna a ofis baka da lokaci saboda jama'a." Girgiza kansa yayi yana gyara gilishin idonsa yace." Ba zan iya tsayawa ba amma ki bawa Haruna ko Hamza kayan breakfast din ya kawo min ofis." Nace"To shikkenan ranka ya dade Allah ya bada sa'a." Amsawa yayi tare da kama hanyar fita, har ya kai bakin kofa ya tsaya na kalleshi saboda nasan da abinda ya tsayar dashi, yace."Na bar bedroom dina a bude ki gyara min har toilet." nace"To insha Allahu zan gyara." Fita yayi ni kuma da sauri na hau saman domin gyara masa dakin kamar yanda ya 'bukata. Koda ya shigo falon yaji shuru kai tsaye kicin ya nufa nan yaga komai a shirye akan tire ajiyar zuciya ya sauke, yaji dadi sosai da samun komai a kammale, hannu yasa ya dauko wani abu a cikin aljihunsa, ya kwance abun dake cikin wata bak'ar takarda, bud'e fulas din yay nan yaga miyar taushe wacce taji gyada da watadaccan nama, sai kamshi take, gabadaya ya zazzage abinda yake cikin takardar a cikin miyar yasa spoon ya juya sosai maganin ya 'bace a cikin miyar, rufewa yayi da sauri ya fita daga kicin din yana addua Allah yasa bukatarsu ta biya. Tsaf na gyara masa dakin nasa turaran wuta mai kamshi kana na sauko kasa, kicin din na nufa a gurguje na had'a komai a cikin wani kwando na mussaman Hannuna rike da kwandon dake dauke da abincin na fito na samu Haruna shi kadai a zaune , ina mirmushi nace"Sahibi kana zaune kai kadai ina Hamza ya tafi ya barka cikin kadaici." kallon kauna yayi min yace."Hamza yaje gurun iyayensa domun su gaisa nima abinda ya hanani tafiya ina jira ki fito nayi tozali dake. Murmushi nayi cikin kauna nace"Haruna kenan to gani na fito ina fata kaji dadi daka ganni." Yace."Naji dadi sosai Sumayya jiya kwana nayi ina mummunan mafarki sai nake ganin kamar na kusa rabuwa dake Sumayya mafarkin jiya ya bani tsoro wallahi." Ji nayi gwiwata tayi sanyi nace"Haruna dan Allah ka daina irin wannan maganar bana so insha Allahu babu abunda zai rabamu nasan har yanzu kana fargaba akan lamarina da Yarima to ka kwantar da hankalinka tunda Maimartaba yace dole ya hakura ai magana ta kare." Murmushi yayi yace."To shikkenan Sumayya insha Allahu na daina damuwa sannan kuma ina rokon Allah ya cika mana burinmu." Cikin jin dadi na amsa da ameen ya rabbi." Nace"Magajin sarki yau ya futa da sauri da alama akwai abinda yasa ya kasa tsayawa ya karya kummalo shine yace idan na kammala komai kai ko Hamza wani ya kai masa ofis." Yace."To babu damuwa ai tunda Hamza baya nan bari na kar'ba kawai na kai masa." 'Dan 'bata fuska nayi nace" bana so kasha wuya naso Hamza yana nan da shine zai kai masa. Dariya yayi ya mike tsaye yace." Sumayya kenan kamar yanda bakya so na wahala nima haka wallahi dani mai iko ne da duk wannan wahalar bakiyi ba." murmushi na dinga saki ina kallonsa, ya kar'bi kwandon abincin daga hannuna, tare muka jera har gurin da motoci suke, nayi wa daya daga cikin direbobin bayani a take ya mi'ke had'e da bud'ewa Haruna mota ya shiga, shima ya zauna a mazauninsa, hannu na daga masa da murmushi a fuskata nace"Sai ka dawo." shima da kyakykyawan murmushi a fuskarsa yake daga min hannu, na dinga mamakin yanda fuskarsa ke fitar da annuri murmushin da yake min yayi yawa dan har direba yaja motar bai dauke idonsa daga kaina ba, a sanyaye na nufi gurinmu gabana na faduwa kadan kadan... Koda ya isa ofis ruwan coffee kawai yasha yaji ya gamsar dashi, kawai sai ya cigaba da aikin dake gabansa, yayin da marasa lafiya keta shige da fice a asibitin...............Haruna a nutse ya fito daga motar bayan direba yayi parking a gurin da aka tanada, kai tsaye cikin asibitin ya nufa, da yake yasan ofis din nasa kai tsaye kofar ya nufa, masu gadin kofar suka dakatar dashi. sai da daya ya shiga ya sheda masa tukkuna ya fito ya bashi umarnin shiga. Kanshi a kasa yana rubuce rubuce jikin wata takarda ya amsa sallamar Haruna, haruna yaja gefe ya tsaya hannunsa rike da kwandon abincin, sai bayan kusan minti goma ya dago kansa, Haruna da sauri ya mika gaisuwarsa, babu yabo babu fallasa ya amsa, Haruna yace.''Ranka ya dade Sumayya ta aikoni da kayan karin kummalon ka." Yayi shuru yana kallon takardar dake gabansa, dagowa yay a nutse yace."Haruna kaje da abincin nan ba zan iya cin komai ba yanzu idan kuma kana bukata kaje ka samu wasu su taya ka ci'' A sanyaye yace."To godiya muke ranka ya dad'e Allah ya taimaka maka a cikin dukkunanin al'amuranka." Ya amsa da amin ya Allah. hanya ya nuna masa da hannu da fadin"Kana iya tafiya." Haruna da sauri ya bude kofa ya fita bayan yayi masa fatan tashi lafiya. Haruna yana fita direba ya samu yace ya fito su samu wani guri suci abincin dan wanda aka kawowa baya bukata, Direba da sauri ya kulle mota suka samu wani 'ke'bantaccan guri a cikin asibitin suka zauna a nutse suka fito da kayan abincin.........Funkaso ne shar dashi yana ta kamshi, suka bud'e fulas din miya yawun bakinsu duk ya tsinke, cikin plate suka zuba funkason da yawa suka lafta miya da uban nama, suka shiga ci suna hira, bayan sun gama ci da minti biyar gabad'ayansu suka fice daga hayyacinsu suka dinga mur'kususu a gurin suna matagugu! da ri'ke cikinsu!! salati suka shigayi idanuwansu suka kafe suna kallon sararin samaniyya, babu shakka gubar da'aka zuba cikin abincin mai karfi ce dan anan take Haruna ya fadi a gurin rai yayi halinsa, minti goma a tsakani direban shima ya fad'i yana kiran sunan Allah.... *Na kudi ne* Kada ki karanta min littafi baki biya ba, keda kika futa da littafin keda Allah! idan kina so ki biya ga yanda abin yake....Vip group #600 normal group #300....account... 0542382124..Binta umar gtbabk...idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKAWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 75&76 Koda na fito samun Haruna nayi shi kadai a zaune ya zabga uban tagumi! kai tsaye inda yake na nufa a sanyaye na zauna a gefansa kallonsa nayi a nutse na kira sunansa Ya dago yana kallona da jajayen idanunsa, tausayi ya bani saboda nasan irin kaunar da yake min, nace"Haruna kada ka tayar da hankalinka akan wannan maganar Yarima bai isa ya raba tsakaninmu ba.'" Cike da mamaki yake kallona kafin yace."Sumayya kin san bani da kwanjin da zanyi gogayya da Yarima a gurun neman auranki dole na hakura dake na bar masa." Nace"Haba Haruna kada ka bani kunya mana me yasa zaka karaya da wuri ashe dama duk so da kaunar da kake min suna ya tara ba zaka iya tsayawa a fafata da kai ba." Girgiza kansa yayi yace."Sumayya kenan ba zaki gane abinda nake nufi ba, ki sani ni bawa ne wanda yake karkashin masarauta dole ne nabi umarni koda kuwa hakan na barazana da rayuwata tilas na janye maganar auranki kamar yanda ya bukata cewa na sanar da mahaifina halin da ake ciki to dole na fada masa ya samu mahaifinki ya sheda masa halin da ake ciki." A sanyaye nace"Amma ban ta'ba tsammanin haka daga gurunka ba wallahi na raina kaunar da kake min daga magana guda har ka karaya ka janye na yarda kaima ba sona kake ba sha'awata kake.'' rai a bace na mike zan bar gurin da sauri yace."Sumayya duk me ya janyo wannan maganar dan Allah ki tsaya ki saurare ni wallahi karfina akafi akan soyayyarki amma ina me tabbatar miki da cewa da wani ne ba Yarima ba to da sai inda karfina ya 'kare.'' Saboda yanda nake jin zafi a zuciyata yasa ko tsayawa banyi ba bare na saurari maganarsa, gurinmu na shiga raina a 'bace." Kai tsaye k'uryar daki na shiga na kwanta hawaye ba zuba a kuncina Yarima zai gwada iko da mulki ya aureni domin ya biya bukatarsa daga baya ya sake ni anya kuwa zan iya amincewa da wannan al'amarin. "Sumayya." Muryar Tambaya naji tana kirana, da sauri na goge fuskata na amsa da "Na'am." Tace."Yawwa ashe kin shigo kinga ni ina zaune zaman jiran shigowarki bacci ya dauke ni babanki ma bai shigo ba ko."? Nace"Eh bai shigo ba ai lokacin dana shigo kina bacci shiyasa." Tace"Eh yanzu ma motsinki naji na farka akwai kwad'on zogale a kicin na ajiye miki." Nace"To kafin na kwanta zan dauka naci.'' Shuru tayi ba sake magana ba da alama bacci ne a kanta, sai da aka jima tukkuna na mike a hankali na fita na dauko kwadon zogalen a tsakar gidan na zauna nasa kwanon zogalen a gabana na garara ci gabad'aya hankalina ya dauke gurin tunani naji muryar Babana a kaina....da sauri na dago kaina ina kokarin kawar da damuwa ta nace"Baba ka shigo." a sanyaye yace."Eh tun dazu nake tsaye a kanki ina magana baki ji ba." Shuru nayi ba wai dan bani da abin fada ba." Yace.''Ki dauko kwanon abincin ki shigo ciki akwai maganar da zamuyi.'' naji gabana ya fadi jin abinda yace binsa nayi da kallo har ya shiga dakin.......Mikewa nayi ba tare dana dauki kwanon zogalen ba nabi bayansa dakin. Zaune na same shi a kan shimfid'arsa kallon guda nayi masa na gane yana cikin damuwa, a sanyaye na zauna ina fuskantarsa Kallona yayi a nutse yace."Sumayya wani babban al'amari ne yake so ya faru dake damu baki daya." Nayi shuru ina sauraransa nasan dai mahaifin haruna ya sameshi da maganar data dame ni. Ya cigaba da cewa"Yanzu kafin na shigo mahaifin Haruna yaron nan da aka tsayar da maganar auranku yazo min da wata magana wacce ta sani farin ciki ta kuma sani fargaba." shuru yay yana kallona na lura kamar yana jin nauyin fada min maganar nace"Baba na riga nasan maganar dakake so ka fad'a min." kallona yayi yana so yayi magana Tambaya ta mike zaune da alamun bacci a tare da ita tace"Allah yasa dai lafiya naji sai magana kuke 'kasa-'kasa ga alhini a tare daku.'' A sanyaye yace."Tambaya yanzun nan mahaifin Haruna yake sheda min cewar yaronsa ya janye maganar auransa da Sumayya saboda ba zai iya had'a takara da magajin Sarki ba." Tambaya cike da tsoro tace."Malam kayi min bayani yanda zan fahimta bangane ba zai iya had'a takara da magajin sarki ba, me ya sako Yarima cikin al'amarin auran Haruna da Sumayya." Murmushi yayi yace."Tambaya Magajin Sarki da kansa ya umarci Haruna ya janye maganar auransa da Sumayya saboda yana so ya aureta." Tambaya gud'a ta ragwad'a cike da farin ciki da annushuwa tace"Malam da gaske kake wannan magana ko mafarki nake yi." Murmushi yayi yace."Ba mafarki kikeyi ba gaskiya ne wannan maganar." Tambaya kamo ni tayi ta rungume a jikinta ta dinga rangwad'a min gud'a akaina tana zabga min addua." har sai da babana ya dakatar da ita sannan ta sake ni kana ganinta kasan tana cikin walwala da farin ciki. Ni kam kallonsu kawai nake ina mamakin murnar da sukeyi tabbas da sun san da munufar da Yarima zai aureni da basuyi murna ba, ganin yanda suke ta farin ciki yasa na danne damuwata kawai na dinga binsu da kallo.....Babana sunkuyar da kansa yayi yana girgiza kansa, Tambaya tace."Malam ya kuma naga ka shiga halin damuwa." Ajiyar zuciya ya sauke yace."Tambaya ina tunanin abinda zai biyo baya idan Allah ya kaddara al'amarin babu shakka mutane zasu nuna mana bakin ciki ina tsoran kada wani ya cutar damu ta dalilin wannan al'amarin." A sanyaye tace."Malam ka kwantar da hankalinka babu abinda zai same mu da izinin ubangiji duk wanda ya nufe mu da sharri sai ya koma kansa da yardar Allah kuma wannan aure sai anyi shi tunda maganar ta fito daga bakin Yarima ai magana ta kare sai da muyi kyakkyawar addua."" Ajiyar zuciya ya sauke ya kalleni a nutse yace."Sumayya kinyi shuru baki ce komai ba ina fata kinyi na'am da wannan al'amari." A sanyaye nace" A gaskiya Baba ni wannan al'amari sam be kwanta min a rai ba wannan dalilin ne yasa kukaji nayi shuru da bakina." Tambaya hannuna ta rike a sanyaye tace"Haba Sumayya kiyi wa kanki kyakkyawan addua mana ki roki Allah yasa haka shine alkairi a rayuwarki mu dai mun amince da wannan sauyin da Allah yayi miki a matsayinmu na iyayenki muna miki fatan alkairi kuma muna umartarki da ki kar'bi al'amarin da zuciya daya insha Allahu Allah zai sa albarka a ciki." ajiyar zuciya na sauke a sanyaye nace Allah yasa albarka a cikin al'amarin." Gabadaya suka amsa da "ameeen ya Allah." Washe gari da safe sukuku! na tashi inata tunanin yanda al'amura zasu kasance a gaba iyayena sun kar'bi al'amarin hannu biyu sai murna da farin ciki suke wannan dalilin yasa gabadaya gwiwata tayi sanyi kawai na zubawa sarautar Allah ido ina tunanin yanda al'amura zasu kasance............Sallama mukaji daga waje, da sauri babana yasa takalminsa ya fita, minti biyar ya dawo yana murmushi yace."Tambaya al'amarin nan fa da gaske ne dan yanzu Magajin sarki ya aiko naje na sameshi a gurinsa. Cikin murna tace"To shikkenan Ubangiji Allah yasa muji alkairi." Yana kokarin fita ya amsa da ameeen ya Allah." Cikin hijabi na fito daga daki kafadata rataye da jakar litattafai na, nace"Tambaya ni zan shiga gurun karatu'' Tace."To yau ba zakije sashen Yariman ba." Ajiyar zuciya na sauke a hankali nace"Zanje idan na taso." Girgiza kanta tayi tace"To Allah ya bada sa'a sai kin dawo." amsawa nayi da ameen nasa takalmana na fita. "Ranka ya dad'e babu wani abu da zaka nema a gurina na kasa mallaka maka mutukar ina da iko ni ne mahaifin Sumayya kuma na baka ita ina rokon Allah ya sanya alkairi a cikin auranku''' Magajin sarki fad'ad'a fuskarsa yayi da murmushi cikin jin dadi yace." Nagode sosai da wannan kyauta da kayi min insha Allahu zan samu Maimartaba na sheda masa maganar da duk yanda mukayi nagode kwarai da gaske kana iya tashi ka tafi.''' Lawi godiya yayi sosai kafin yay masa sallama ya fito fuskarsa cike da annushuwa! kai tsaye bangaran dawakai ya nufa yana tafiya yana addua akan Allah yasa alkairi a cikin al'amarin. Sai misalin sha biyu da rabi muka tashi daga gurin karatu ji nayi kamar naje gida na kwanta na huta saboda gajiya da tunani duk sun sa karatun ma bana ganewa, har na nufi gurinmu sai kuma na sanja shawara 'bangaransa na nufa domin gabatar da aikina idan yaso idan na gama sai na huta gabadaya.......koda na shiga gurin samun su Haruna nayi a zaune suna hira kallo guda nayi masa naga ramar da yayi girgiza kaina nayi muka gaisa sama-sama na shigesu. Yana zaune a falo yana kallo nayi sallama, ya amsa tare da 'kure ni da ido, babu yabo babu fallasa na gaishe shi, ya amsa min fuskarsa a sake kamar bashi ba, kicin na nufa, ya dakatar dani. Cikin 'kosawa na tsaya ina kallonsa yace."Me ya hanaki kizo ki had'a min breakfast. " ? "Kayi hakuri naje gurin karatu ne kasancewar yau lahadi duk rana irin ta yau muna zaunawa da wuri mu tashi da wuri wannan dalilin yasa banzo akan lokaci ba.'' Yace." Me zai hana kizo gurina duk ranakun asabar da lahadin na dunga karantar dake." cike da mamaki nake kallonsa. Yace."Ko kina ganin ba zan iya ba."! girgiza kaina nayi nace" ba haka nake nufi ba kawai abar maganar yanzu ka fadi abinda kake bukatar kaci."! "Bana bukatar naci wani abu.'' Na dinga kallonsa ina mamakin maganarsa ganin yana min shu'umi kallo yasa na 'bata rai juyawa nayi zan bar gurin yace." Kin san d'azu muyi magana da mahaifinki ko."? Wani irin kallo na watsa masa, 'bata fuska yayi yace."Abun naki kuma nema yake ya wuce gona da iri ni kikewa wannan kallon. Tsaki nayi niyyar ja sai na fasa, nace"To kunyi magana da babana sai akayi me."? Cikin nuna isa yace."Ya tabbatar min da cewa ya mallaka min ke ko kina da ja ne."? girgiza kaina nayi nace"Bani da ja sai abinda Allah ya kaddara a kaina amma ka sani idan ka samu nasarar aurena to zaka sha mamakin abinda zai biyo baya." Kai tsaye yace."In dai ta bangaranki ne ban damu ba saboda duk girma da karfin da kike dashi baki fi karfina ba." Girgiza kaina nayi na wuce kicin zuciyata nayi min zafi! babu shakka guy nan da gaske yake aurena zaiyi ya lalata min rayuwa, koda na shiga kicin din kasa kata'bus nayi na nemi guri na zauna tare da zabga uban tagumi! iyayena na farin ciki zan auri dan sarki! ni kuma ina 'bakin ciki domin nasan da aniyar da zai aureni babu shakka ina jin tsoran ranar da zai sako musu ni a matsayin bazawara shin wane irin hali zasu shiga idan haka ta kasance wannan shine babban abinda ya dame ni, to a takaice dai sai da na shafe kusan rabin awa a zaune a kicin din ina sa'kawa da kwancewa kafin na mike da sanyayyan jiki na fara aikace aikace na. Magajin sarki sai da dare ya samu zama da mahaifinsa cikin nutsuwa ya sheda masa abinda yake tafe dashi, maimartaba ya dinga kallonsa yana mamakin maganar dake tafe dashi. Magajin sarki jikinsa ne yayi sanyi dan ganin yanda Maimartabar ya nuna a lokacin da yaji maganar dake tafe dashi, yace."Ranka ya dad'e naga kamar maganar da nake tafe da ita bata gamsar da kai ba." Maimartaba yace."Kwarai kuwa maganar bata gamsar dani ba Magajin sarki ka duba wata yarinyar wannan da kake magana akanta ka hakura tsayin wata uku iyayen yaran suka same ni da maganar auran 'ya'yansu nasa albarka a ciki sannan daga baya kai kuma kazo da wata magana, bana so na amince maka jama'a suga rashin adalcina yarinyar nan Sumayya ba ita kadai bace mace a masarautar nan ka duba da kyau ka samo wata sai na shige maka gaba amma wannan dai tunda wani ya rigaka sai ka hakura." Wani irin gumi ne ya shiga tsatstsafo masa bai ta'ba tsammanin zai samu matsala daga gurin mahaifin nasa ba, yace."Ranka ya dad'e yanda na yarda na amince da yarinyar nan ko Lawisa ban yarda da ita ba, yarinyar nan sumayya tana tsaye a kaina sosai take bani kulawa ta kowane fanni wannan dalilin ne yasa naji ina sha'awar auranta." Maimartaba ya sauke ajiyar zuciya yace."Nima nasan da haka domin mahaifiyarka na fada min irin kokarin da yarinyar take a kanka babu shakka zanso ka aureta domin ta cigaba da kula da kai sai dai kash!! ba zan iya shige maka gaba akan al'amarin ba saboda dalilina dana fada maka idan nine mahaifinka to na umarceka daka janye maganar auranta ka nemi wata." Magajin sarki kasa motsi yayi a gurin ya dinga jin zazzabi mai zafi na nema ya rufe shi, Mamma dake gefe guda a zaune tace"Magajin sarki kabi umarnin mahaifinka ka janye maganar auran yarinyar nan kamar yanda ya bukata idan so kake ka had'a mata biyu sai ka duba wata koda a cikin bayin ne insha Allahu zamu shige maka gaba." Murya na rawa yace."Mamma ke kin san mahimancin yarinyar nan a tare dani ke kika hadani da ita ina ganin duk wacce zan nema ba zata kama kafarta ba yarinyar nada gaskiya da rikon amana mamma kiyi wani abu akan wannan al'amarin." Girgiza kanta tayi tace"Magajin sarki zan fi kowa so ka auri yarinyar nan saboda ni nasan wacece ita amma a yanzu ni bani da wata magana tunda mahaifinka ya yanke hukunci shikkenan magana ta kar'e sai dai mu roki Allah yasa haka shi yafi alkairi." shuru yayi tare da sunkuyar da kansa kasa Washe gari da wurwuri na shiga saboda nasan da wuri yake tafiya aiki yasa na shiga sashen da wuri, shuru lokacin dana shiga kai tsaye kicin na wuce na fara aikina, kunun gyada na dama masa na soya masa kosai a gurguje na shirya komai a tire na dauka na fito kenan na hangoshi yana saukowa yanda naga fuskarsa a murtuke yasa nasha jinin jikina! kai tsaye hanyar futa ya nufa, baki na na rawa nace ranka ya dade "Barka da asuba zaka fita baka karya ba kayi hakuri dan Allah bangama akan lokaci b.......kafin na 'karasa ya juyo a fusace! ya doki! tire din hannuna! a take fulas din kunun ya tintsira murfin ya cire ya kwaro min a kirjina mazubin 'kosan kuwa tuni ya fad'i a kasan gurin k'osan ya watse a gurun, rad'ad'in zafi ya gigita ni da sauri na jefar da tire din a kasa ina kiran innalillahi! gami da yarfe ruwan kunun dake rigata ......Fulas din kunun ne ya gangara kusa da kafarsa ya sameshi da yake Takalmin dake kafarsa mai yatsa ne! da sauri ya janye 'kafarsa yana dubawa Ido jawur nake kallonsa tsabar takaici da bakin ciki yasa hawaye ya kwace min, kallonsa kawai nakeyi bakina na rawa , bangaransa kuwa bai tsammaci hakan da yayi mata zata samu tsautsayi ba yayi mata ne dan ya huce fushinsa sai gashi kuma ya 'kona mata kirji da ruwan kunu!!! a sanyaye ya dinga bin kirjinta da kallo fatar duk tayi ja! ta soma tashi, sai yaji gabad'aya ya saduda dan ya lura ta k'one sosai! Inda nake ya nufo yana karasowa na daga hannu da niyyar marin sa, rike hannuna yayi yana kallona!!! a marairace yace."Sorry banyi tsammanin zaki 'kone ba." Fuzge hannuna nayi da sauri na tureshi na kama hanya zan bar gurin, kawai naji ya ru'ko 'kuguna tsam! ya d'ora ha'barsa a kafad'ata, bakinsa yasa daidai kunnena a sanyaye yace."Kiyi hakuri." Gabadaya ji nayi jikina yay sanyi na dinga zubar da hawayen bakin ciki babu shakka Yarima ya zame min karfan 'kafa ya shiga rayuwata yana yanda yake so da ita............. *Na kudi ne* Kada ki karanta min littafi sai kin biya keda kika fita da littafin keda Allah idan kina so ki biya ga yanda abin yake Vip gruop#600 normal gruop#300 account... 0542382124...Binta umar gtbank....idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta whsap da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 78 Tun bayan tafiyar Haruna na tsinci kaina da fad'uwar gaba, guri na nema na zauna ina kiran innalillahi wa'ina ilahi raji'un domin na tabbata itace zata saukar min da nutsuwa, na dauki kimanin minti ashirin a zaune a guri daya kafin na dan samu sassauci a sanyaye na mike na nufi bandaki bokitin wanka na dauko naja ruwa a rijiya na cika bokitin da ruwa wanka zanyi ko naji sassauci dauka na shiga bandakin dashi............Ina fitowa na samu Tambaya ta shigo tana zaune a tsakar gida tana hutawa, nace"amma yau kun gama aikin da wuri." tace."Eh yau aikin yayi sauri nima nayi mamakin haka ai yau mutumin ki akayi." A sanyaye nace "Wake da shinkafa." Kanta ta d'aga min. na kalleta sosai sai naga kamar tana da damuwa! nace"Tambaya kamar akwai abinda ke damunki." Tace"Wallahi tun safe gabana yake faduwa." Shuru nayi ina kallonta tace."Allah yasa dai alkairi ne amma faduwar gabar ya tsananta!! ajiyar zuciya na sauke nace"Nima haka tun dazu gabana ke faduwa sai dai ki yawaita kiran innalillahi insha Allahu babu wani abu da zai faru." Tace."Insha Allahu. daki na shiga ina addua a cikin zuciyata, na shirya jikina, dadduma na hau na tayar da sallar azuhur, bayan na idar fitowa nayi na sameta a kwance a rumfa bacci na nema ya dauketa, nace"Tambaya ai gwara ki tashi kiyi wanka kada kiyi bacci lokacin sallah yayi." Tace."Ai naji ba'ayi kiran sallah ba shiyasa na d'an kwanta na matse." nace"Yanzu za'a kira daya da rabi." Kiran sallar ne ya katseni nace"Kinji ko.'' mikewa tayi tana hamma, nace "ai zafi akeyi kawai kiyi da ruwan rijiya nima dashi nayi." tace."aikam dai waye zai sawa kansa ruwan zafi yanzu. Mikewa tayi nayi sauri fita na zuba mata ruwan wankan kicin na shiga na d'ebo abinci a plate na zauna a tsakar gidan, loma uku kacal nayi naji gabad'aya abincin ya fita daga kaina, duk sona da wake da shinkafa naji bana sha'awa, guri guda na zubawa ido......"Sumayya." muryar babana naji a kaina. da sauri na dago ina kallonsa yace."Me yake damunki kika zabga tagumi." Da sauri nace"babu komai baba." zama yayi kusa dani yace."Sumayya akwai abinda ke damunki tun dazu nake tsaye ina miki magana kina can tunani kinsa abinci a gaba kin kasa ci." Hawaye ne suka 'kwace min. Lawi jikinsa yayi sanyi ganin yanda take kuka. A sanyaye yace."Ki fada min damuwarki."? hanci na shaqa nace."Baba wallahi tun dazu gabana ke fad'uwa sai nake ji a jikina kamar wani abu zai faru dani." Lawi jikinsa yayi sanyi yace."Sumayya dukkan tsanani yana tare da sauki babu abunda zai faru sai alkairi ki kwantar da hankalinki ki daina damuwa a duk lokacin da gabanki ya fadi ki dinga addua kinji ko." Hawaye nagoge yay murmushi cikin sigar so ya kwantar min da hankali yace."Bari na zauna na taya ki cin abincin." murmushi nayi nace."Aikuwa naji dadi baba ka zauna muci tare ina so na samu albarka." hannunsa yaje ya wanko yazo ya zauna kusa dani a nutse yace."To saka hannu muci. ina murmushi nasa hannuna a nutse muka fara cin abincin Tambaya ta fito daga bandaki ta same mu mirmushi tayi ta shiga daki domin kimtsa jikinta, koda muka cinye abincin cewa yayi na bari ya dawo daga masallaci sai mu 'kara wani nace "to." ruwa na zuba masa a buta ya daura alwala ya fita. To wajejan biyar saura na yamma na isa sashen Yarima na dinga wulkita idona a harabar gurun ina neman Haruna banganshi ba, Sai Hamza na gani a zaune a rumfar masu gadi suna hira, kai tsaye rumfar na nufa a nutse muka gaisa dasu. Nace."Hamza ina Haruna ne."? yace."Sumayya tun safe rabona da Haruna amma Mika'il yanzu yake fad'a min wai sunje kaiwa Yarima abinci ofis." Na kalli Mika'il cikin faduwar gaba nace"Kana nufin har yanzu basu dawo ba."? Yace."Eh wallahi basu dawo ba watakila ko Yallabai din ne yace su zauna su jirashi." ajiyar zuciya na sauke nace"Eh haka zata iya kasancewa ai yanzu zaka gansu tunda biyar ta kusa." Suka ce hakane, nace"bari na shiga ciki." suka ce "To sai kin fito." wuce wa nayi ina sauke ajiyar zuciya da godewa Allah. To har na gama dukkanin ayyukana a shashen babu alamun dawowarsu na shiga mamaki mai tsanani dan idan ba wani gagarimun abune ya faru ba to Yarima baya kaiwa karfe shida a asibiti biyar yake dawowa ko biyar da rabi yau gashi har shida ta wuce ana dab da kiran sallar isha'i bai dawowa, gabad'ayanmu ma'aikatansa mukayi jugum-jugum muna Jimami, Mika'il yace."Bari kawai naje asibitin naga abinda ke faruwa ni dai nafi tunanin aiki ne ya rikeshi." Nace."Idan aiki ya ri'ke Yarima su kuma su Haruna me zai ri'kesu."? Hamza yace."Nima dai abinda na gani kenan." Mika'il yace."Bari dai naje insha Allahu babu matsala." Muna kallo Mika'il ya shiga mota ya tafi gabad'ayan mu muka zauna zaman jiran tsammani. 'Daya daga cikin ma'aikatan dake tsabtace asibitin ne yake shawagi a sa'ko da loko na asibitin da tsintsiya da mazubin shara a a hannunsa duk inda yaga leda ko takarda sai ya dauke, tun daga nesa ya hangesu a kwance k'udaje sai binsu suke, gabansa na fad'uwa ya isa gurin, ganinsu a sheme ido a kafe yasa ya tsorata a guje ya yar da mazubin sharar ya ruga cikin asibitin........Yana haki! ya shiga reception din, jama'a suka bishi da kallo, kai tsaye ofis din Yarima ya nufa, masu gadin gurin suka mike tsaye, tare shi suke yana yun'kurin shiga daya daga cikinsu ne ya buga masa tsawa da fad'in "Kai kada ka karya mana doka mana ka nutsu kafad'a mana abinda ke faruwa." Yana haki! yace."Babu lafiya a cikin asibiti nan can wajejan shuke-shuke naga gawarwakin mutane biyu."" Gabadaya jama'ar dake gurin suka tsorata jin abinda ya fada, gurin ya kaure da hayaniyar da tayi sanadiyar fitowarsa, kafin ma ya tambayi ba'asi suka fara sheda masa abinda ke faruwa. kafin kice kwabo gumi ya jiqashi, hanyar futa ya kama wasu daga ciki suka rufa masa baya masu tsoro kuwa tuni suka silale daga asibitin. Magajin sarki hankalinsa yayi masifar tashi ganin su Haruna a sheme idanunsu a tsaye suna kallon guri guda, kallo daya yayi musu ya fahimce cewa sun dade da rasuwa, jikinsa ya dinga kyarma ya dinga nanata kalmar innalillahi wa'ina ilahi raji'un! hankici ya dauko ya goge gumin goshinsa ya dago kansa yana kallon jama'ar da sukayi dafifi a kansa, tsaye ya mi'ke ya umarci mutum biyu daga cikinsu akan suje su sanyo safa a hannuwansu domin su harhad'a kwanakun abincin................Jami'an tsaro da 'yan jarida ne suka k'araso gurin, kallonsu yake yana mamakin wanda yaje ya fad'a musu, suna zuwa gurin suka fara aikinsu sai bayan da suka gama daukar gawarwakin a hoto suka dawo da hankalinsu kansa, yana tsaye kamar mutum mutumi k'wayoyin idanunsa sun kad'a sunyi jajawur....."Yallabai ya akayi wannan al'amarin ya faru a cikin asibitin ka wanda muke mutukar alfahari da samuwarsa a wannan jaha tamu." ? Tambayar da suka jefo masa kenan dukkaninsu sun rufeshi had'e da kara wayoyinsu a gurin bakinsa. Girgiza kansa kawai yake yana kallon Kasan gurin yayinda masu daukar hoto suke ta aikin daukarshi a duk motsin da zaiyi.....ya kai kimanin minti biyar yana kallon kasan gurin kafin ya dago kansa a nutse yace."Ni akayi nufin a kashe sai tsautsayi ya ritsa da wa'innan bayin Allahn kamar yanda ya kwanakin baya d'aya daga cikin bayina ya rasu a sakamakon cin abincin daya kasance abincin cina." "Ranka ya dad'e " A gaskiya wannan al'amarin yana bukatar kayiwa mutane cikakken bayani shin ya akayi suna hadiman ka suke cin abincin daya kasance naka abun tambaya anan shine a ina za suga abincinka suci? ranka ya dad'e muna so kayi mana cikakken bayani." Murmushi yayi wanda kana ganinsa kasan na nadama ne yace."Ni nake basu da hannuna." gabad'aya mutanan gurin suka zuba masa ido suna mamakin maganarsa, 'Yan jaridar kuwa caaa! sukayi a kansa, Girgiza kansa kawai yayi ya kalli ma'aikatansa ya basu umarnin su d'aure gawarwakin su had'a guri guda susa a mota sukai masarauta..........Daya daga cikin jami'an tsaron yace.''Yallabai akwai bukatar muje da kai station mu tattauna da kai." Ba tare da damuwa ba yace "babu damuwa........ Gaba yayi suka rufa masa baya yayinda jan jarida suka bi bayansu a guje suna daukar hotonansu har suka shiga mota, da hannu ya kira d'aya daga cikin ma'aikatansa yace." Lallai a ajiye masa ragowar abincin da mamatan suka ci zaiyi binkice a kansa." Jiki a sanyaye ya amsa ya matsa daga jikin motar, suna daf da fita Mika'il ya shigo da mota, ganin dandazon jamaa harda 'yan jarida da motar 'yan sanda yasa Mika'il gabansa ya tsananta faduwa, da sauri yayi parking ya fito yana tambayar abinda ke faruwa, wanda ya fara ganin abun ne yayi masa bayani, Mika'il a gigice! ya nufi inda yaga mutane na fitowa, tun daga nesa ya hango abunda ke faruwa, yana karasawa ya zube gaban gawarwarkin da'aka gama dauresu, ihu! yake kurmawa yana dukan kansa Wani bawan Allah ya dafa kafad'unsa yana rarrashinsa yace."Ba ihu za kayi ba innalilihi wa'ina ilaihi raji'un zaka dinga fad'a." Mika'il ya dinga fad'in Kalmar innalilihi wa'ina ilahi raji'una da karfin gaske! Cikin tsantsar tashin hankali Shatima ya shiga masarautar kai tsaye sashen Fulani ya nufa ganinta cikin nutsuwa yasa ya fahimci bata san abinda ke faruwa ba, gaisawa sukayi tana nazarinsa tace"Shatima ina fata dai lafiya dan ba haka na saba ganinka a hargitse ba." ajiyar zuciya ya sauke yace."Mamma lafiya inaso naga Maimartaba ne." Tace."Yau ba anan yake ba yana gurin uwargida." sallama yayi mata ya nufi gurin uwargidan Tun kafin ya k'arasa ya hangosu a tsaye koda ya karasa gurun samun fuskokinsu yayi cikin yanayi na alhini da damuwa Mussaman shi maimartaban ya hango tsantsar tashin hankali a cikin kwayoyin idanunsa.........Cikin yanayi na damuwa yace."Allah ya baka yawan rai al'amarin nan fa da yake ta faruwa wallahi ko shakka ba nayi dasa hannun masarauta a ciki wa'inda baka ta'ba tsammanin zasu aikata wannan mummunan aikin ba zakayi mamaki idan binkice ya nuna maka su......Ciroma da Galadima jikinsu yayi sanyi suka maida hankalinsu kansa da fadin"Kai a iya bunciken ka wa kake tunanin zai aikatawa Yarima wannan mummunan aikin kada fa ka manta dukkaninmu cibiyarmu d'aya ya za'ayi wasu daga cikinmu su zama bara gurbi." Shatima yace."Ni dai na fad'i abinda nake hasashe nasan kuma tabbas idan an tsananta binkice akan al'amarin a samu wa'inda suke da hannu a cikin al'amarin." Ciroma cikin dakiya da nuna shi mai gaskiya ne yace."Shatima kayi gaskiya da wannan maganar insha Allahu zamu tsananta binkice domin gano wa'inda suke kokarin su kawo mana rud'ani a cikin wannan masarautar mai albarka." Waziri ya sauke ajiyar Zuciya cikin sanyi yace."Yana da kyau muje mu zauna mu jirayi dawowar Yariman amma a gaskiya wannan al'amarin yayi tsanani duk wanda yake shirya wannan abu to babu shakka rayuwar Aliyu yake nema saboda haka yana da kyau dukkaninmu mu zauna domin mu kawo karshen wannan matsala." Maimartaba ya sauke zazzafar ajiyar zuciya a nutse yace."Ku muje fada mu zauna mu tattauna domin mu samu mafita." Gabad'aya suka nufi fada kowa na sa'ke-sa'ke a zuciyarsa. "Wayyo Allah na shiga uku na lalace Wayyo! Allahna."!!! Muryar Laure mahaifiyar Haruna mukaji ta shigo tana kurma ihu! had'e da fad'in ta shiga uku ta lalace.!!! da sauri mukayo waje muna rarraba ido! Laure ta shigo a jigace! tayi kozai kozai da ita sai ihu! take tana fadin ta shiga uku! gabadaya rikicewa nayi na nufe ta ina kokarin rik'eta kawai naji saukar mari a kumatuna, kafin ta cukume ni tana fad'in " Sumayya kece kika kashe min d'ana ni dake zanyi kuka ba da kowa ba Haruna yaron arziki ya mutu ya barni a duniya na shiga uku na lalace."!!!!! tana gunjin kuka takarashe maganar, kallonta na dinga yi bakina na rawa nace" ki fad'a min abinda ke fa...ruwa." wuya na ta ri'ke tamau! ta matseni a bango (garu) tace" Ni zaki mayar shashasha ko ? kina nufin bakin san abinda ke faruwa."? Hawaye ne suka kwace min nace"Wallahi tallahi bansan abinda ke faruwa ba dan Allah kiyi min bayani amma kada kice min Masoyina ya mutu." Wani gigitaccan marin ta dauke ni dashi jikinta na rawa tace"Haruna ba masoyinki bane makiyin ki ne tunda har kika iya bashi guba yaci ya mutu to Haruna bashi da babbar abin 'ki kamar ke." Kallonta nakeyi inaso nayi magana bakina yayi nauyi jiri ne ya shiga d'iba na ina jin sautin muryarta a kunnena silalewa nayi na fad'i a gurin, sama-sama naji salatin Tambaya a kaina..............Idona na bude a hankali ina kalle kalle Tambaya na gani a gurfane a gabana tana kuka tare da shafa min ruwa a fuskata, a furgice na mike zaune ta rike ni "Sumayya kwanta ki huta kada ki tashi." Girgiza kaina nayi cikin nauyin baki nace."Ina Laure take."? Tace."Me zakiyi mata."? kai tsaye nace."Inaso ta tabbatar min da gaskiyar mafarkina." Hawaye ta share tace"Sumayya ki shiga hankalinki ki samu nutsuwa ki kad'aita Allah ki sani Allah shike rayawa kuma shi ke kashewa babu mahalukin da ya isa yayi wannan al'amarin idan ba Ubangiji ba kawai kiyi wa Haruna kyakkyawar addua da samun rahamar Allah." Wasu zafafan hawaye ne suka 'kwace min nace"Da gaske ne ashe."? kanta ta daga min....Rungumeta nayi tare da fashe da kuka "Wayyo Allah na shiga ukun...bakina ta rufe min kafin karasa, naji tana nanata kalmar innalillahi da sauri nima na kar'ba na dinga yi da karfi ina wani irin kuka mai tsuma zuciya, Yarima bukatarsa ta biya ya kashe Haruna yaji dadi dama yace." yana da hanyoyin da zai iya ruguza mana farin cikin mu tabbas dana san da gaske yake zai kashe min masoyi to dana bashi abinda yake bukata! da karfi nace"Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un wannan masarauta akwai azzalimai a cikinta."!!! Da sauri ta rufe min baki ta dago ni tana kallona tace"Sumayya wace irin magana ce wannan? ashe kina so ki janyo mana masifa."? Ina kuka nace"Shine ya kashe shi wallahi shine dama yace sai yaga karshen soyayyarmu bukatarsa ta biya ya kashe shi ya huta." *Na kudi ne...!* Kada ki karanta min littafi idan baki biya ba ke kuma da kika futa da book din keda Allah! idan kina bukatar biyan kudin ga yanda abin yake...Vip gruop#600 normal gruop#300 account... 0542382124..Binta umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA* *SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 79 Wani irin kallon mamaki Tambaya keyi min, ina gunjin kuka nace"Da gaske ne shine ya kashe shi dama yace yana da hanyoyi da yawa da zai iya raba tsakanina dashi domin ya samu nasarar aurena."! Tambaya kafad'una ta ri'ke tana jijjigani tace."Sumayya ki shiga nutsuwarki dan Allah ki daina sambatu sai surutai kikeyi marasa kan gado da ma'ana shin waye wannan da kike magana akansa."?. Hanci na sha'ka na kalleta har yanzu na kasa tsayar da ruwan hawayen dake zuba nace"Tambaya Yarima yayi al'kawarin sai ya aureni ko ta halin 'ka'ka bayan mahaifinsa ya gargadeshi akan ya janye maganar aurena sai ya 'kudiri mummunar aniya a kanmu nida Haruna ya tabbatar min da cewa duk rintsi sai ya san yanda yayi ya aureni domin biyan bukatarsa." Kallona ta dinga yi tana girgiza kanta gabadaya yanayin ta ya nuna alamun tsoro da tashin hankali......Ganin kawai ta kura min ido tana kallo yasa nayi yun'kurin mikewa, tayi saurin rike hannuna na zauna jiki a sanyaye tace"Sumayya da gaske kike Yarima ne silar mutuwar Haruna." Murya a dashe nace."Tabbas ko shakka ba nayi shine ya kashe s......! saurin rufe min baki tayi kafin na karasa maganar dukkaninmu muka kalli bakin kofa saboda sawun tafiyar mutane da mukaji......Murya na rawa tace"Sumayya ki bar wannan maganar a cikin ki duk rintsi kada ki fito da i ta, idan kin fad'a Yarima yayi silar mutuwar Haruna babu shakka zamu shiga tashin hankali a masarautar n........Katse maganarta tayi dalilin shigowar babana da wasu 'yan sanda guda biyu mace da namiji. cikin tashin hankali muka Mi'ke tsaye. "Malam wannan ce Sumayyan ko."? A sanyaye Lawi ya daga kansa. ya kalli 'yar uwarsa da fad'in ''Merry je kiyi aikin ki." Gani nayi ta nufo inda nake da ankwa a hannunta, bakina ya dinga motsi jikina ya dinga karkarwa a lokacin gabadaya kwakwalwata toshewa tayi na dinga tunanin adduar da zanyi, Tambaya kuwa kuka ta fashe ta durkushe a gurin tana rirrik'e kafar ma'aikaciyyar a lokacin da take kokarin daure min hannu. Kallonta tayi cikin yanayin hausarta tace."Kiyi hakuri ba zamuyi mata komai ba mutukar bata wahalar damu ba." Tambaya ta kalli namijin tana kuka tace"Dan darajar Allah da annabi kada ku tafi da ita wallahi bata da laifi akan faruwar wannan al'amari." Yace."baba dole ne ayi binkice akan 'yarki domin itace ta girka abincin dake dauke da guba a ciki idan ba tayi mana gardama ba to zata samu sassauci idan kuwa ta tsaya gardama za tasha wuya a gurinmu." Tambaya kallona tayi tana marairaicewa! naji wani irin tausayinsu ya rufe ni, babana tsabar tashin hankali duk kammaninsa sun sauya ya kasa magana kawai ya jingina jikin bango (garu) sai kallonmu yake. Cikin kokarin danne tashin hankalina nace"Tambaya ki daina kuka dan Allah kiyi min addua insha Allahu mai gaskiya baya ta'bewa Allah zai kub'tar dani daga dukkanin wata musiba." Mi'kewa tsaye tayi tana kokarin magana suka tasa 'keya ta, Lawi da saurin gaske ya shiga daki yana share hawaye ita kuwa Tambaya bayanmu ta biyo tana kuka had'e da ri'ke min hannun riga sai hakuri take bawa jami'an tsaron.........Dandazon mutanan dake gurin yasa nayi saurin sunkuyar da kaina kasa na dinga tafiya kaina a sunkuye ina kiran sunan Allah a zuciyata, motarsu suka saka ni, na dukufar da kaina k'asa band'ago kaina ba har sai dana muka fita daga gidan. Suna zaune suna tattanawa dangane da faruwar al'amarin sa'kon mai girma governor ya iso, mai girma governor yayi umarni da cewa lallai a rufe asibitin *ZINARIYA HOSPITAL* sai gwamnati ta gama binkice akan mutuwar da mutane keyi a cikin asibitin." Maimartaba beji ciwo akan umarnin governor ba koda bai bada umarin rufe asibitin ba dama ya yanke shawarar rufe shi..........Galadima da Ciroma cike da tsantsar farin ciki suka bar fada, suka had'u a gurin guda suna ta 'bab'baka dariya bukatarsu ta fara biya gwamnati ta shigo cikin al'amarin zasu san yanda zasuyi su had'a kai da gwamnatin domin su ruguza asibitin. Ta jima kanta a kasa tana kaiwa Allah kukanta kafin ta d'ago kanta tana zubar da hawaye ta daga hannuwanta sama ta dinga addua tana 'kas'kantar da kanta a gurin mahallicinta, Mamma Fulani ta dade hannunta a sama tana neman sasaauci gurin Ubangiji kafin ta shafa a fuskarta a nutse ta juyo tana kallon mijin nata dake zaune akan kujera, tace"Ranka ya dad'e Har yanzu bai dawo ba kenan."? Maimartaba ya sauke ajiyar zuciya cikin sanyin murya yace."Bai shigo ba har yanzu gabad'ayan mu mun gaji da zaman fada kowa ya shige gurinsa.'' Kanta ta d'aga ta kalli agogon dake kafe a falon tara na dare, a sanyaye tace."Inasha Allahu, Allah zai dawo mana dashi lafiya." Maimartaba ya amsa da ameeen tare da mikewa tsaye! sallama yayi mata ya nufi gurin Uwargida Huwaila.......Tana zaune a bakin gado kunnanta makale da waya sai 'ba'bbaka dariya takeyi da alama tana cikin nishad'i, Tace."Ai al'amura gabad'aya sun dagule wannan karon mun samu nasara akansa dan har yanzu yana hannun 'yan sanda kuma gwamnati ta shigo cikin al'amarin asibitin da yake tutiya dashi gwamnati ta rufe shi, wannan dalilin yasa duk na kira wayarku na sheda muku cewa yau kuyi bacci harda munshari dan bukatarmu daf take da ta biya." Daga daya b'angaran aunty Safiyya ta dinga k'yakyata dariyar farin ciki tace"A gaskiya naji dadin wannan abu Wai!! ya muka ga idon mutsiyaci a cell a gwara yasha duka dan ya bamu wuya." Uwar gida tace"Ai be zama lallai su doke shi ba yanzu abinda nake so daku shine gobe da sassafe ku shigo cikin nuna alhini da damuwarku bana so ko kad'an a gane akwai sa hannunmu a cikin al'amarin." Aunt Safiyya tace."Kada ki damu Mama zamu shigo da wuri kuma ba zamu nuna farin cikin mu ba zamu nuna tsantsar damuwar mu dangane da faruwar al'amarin." Uwar gida tace"To shikkenan sai kun......shigowar Maimartaba dakin yasa ta kasa karasa maganar kashe wayar tayi ta ajiye kusa da ita tana masa barka da shigowa. Guri ya samu ya zauna a nutse yace."Dawa kike waya da daddare haka."? Tace."Wallahi Safiyya ce ta kira ni yanzu take sheda min cewa na nema mata alfarma a gurinka wai tana so ta 'kara jari akan wanda take juyawa gashi tana jin kunyar Tambayarka kudi." Murmushi yayi yace."Da alama basu san abinda yake faruwa ba a masarauta ba." Da sauri tace."Me yake faruwa ranka ya dad'e."? yanda ta nuna damuwarta sai ka rantse da Allah bata san komai ba. Maimartaba cikin nutsuwa ya sheda mata dukkanin abinda yake faruwa, fashewa tayi da kuka ta ri'ke kanta tana fad'in "Innalillahi wa'ina ilaihi raji'una! wannan yaro yana ganin tashin hankali wai shin me Aliyu yayi wa mutane ne suke nema suga bayansa." Maimartaba tace."Wallahi ni kaina na rasa abinda yasa mutane suke nuna masa 'kiyayya al'amarin yana bani mamaki mutuka! ada ina zargin daga waje al'amarin ya fito sai da na zauna nayi tunani sosai na gane cewa a kwai saka hannun wasu daga cikin masaurata.". Tana kuka da fyatar majina tace"Allah ya taimake ka shin kai wa kake zargi da aikata wannan aikin dukkaninku cibiyarku d'aya ashe akwai wanda zai iya neman ran d'an uwansa." Maimartaba yayi murmushi mai ciwo yace."Hulaiwa baki san mulki ba har yanzu mutane na iya aikata komai akan mulki na lura da tun sanda na fara kiransa da Magajin sarki fuskokin wasu daga cikin makusanta na ya nuna b'acin rai ni ban kira Aliyu da Magajina ba wai dan ya gaji kujerata Ali sunan surikina ne wato mahaifin Fulani ke kin sani itama ta sani wannan dalilin yasa nake kiransa da wannan suna na Magajin sarki."! Uwar gida girgiza kanta ta shagayi kafin ta sauke ajiyar zuciya tace"Babu shakka mutum daya ne zai iya aikata wannan rashin imanin ba kowa bane sai Waziri shine makusancin ka wanda kafi aminta dashi shine kuma zai cutar da kai da zuriar ka Waziri bai ta'ba haihuwa ba tsayin shekarunsa wannan dalilin zai sa ya aikata mugun abu akan 'ya'yan 'yan uwansa sabida yana ba'kin cikin shi Allah be bashi haihuwa ba...... Cikin wani irin yanayi Maimartaba yake kallonta yana mamakin maganarta akan d'an uwansa mafi kusanci dashi wato Waziri." Ganin ya nuna alamun alhini yasa tace"Nasan dole za kayi mamakin maganata ranka ya dade kada kayi mamaki halin dan adam wallahi ko shakka ba nayi Waziri zai iya kashe Yarima saboda wannan dalilin dana fad'a maka.". Maimartaba girgiza kansa yayi cikin yanayi na damuwa yace."Huwaila kada ki sake wannan maganar zargi bashi da kyau Waziri yana da kyawun zuciya na yarda ba zai cutar dani da zuria ta ba idan da wa'inda ya kamata a d'ora zargi a kansu to Ciroma da Galadima ne domin sune suka fito da hassadar su a kaina kada fa ki manta gwagwarmayar da nasha dasu a lokacin da Allah ya bani mulki nasha wahalarsu kafin su rabu dani nayi mulki cikin nutsuwa, Waziri kuwa tunda muke dashi bai ta'ba nuna min hassadar sa ba yana kaunata yana kuma kaunar zuria ta wannan al'amarin da ya faru yafi kowa damuwa bana zargin akwai saka hannun Waziri dangane da faruwar al'marin." Huwaila shuru tayi bata sake tofawa ba, ta dauka mijin nata zai dauki maganarta babban burinta ta raba zumuncin dake tsakaninsa da dan uwansa Waziri saboda ta fahimci cewa Wazirin kamar shi yake hana Maimartaba ya kula da 'ya'yansa tunda ta lura da irin kaunar da yake wa Magajin sarki gabadaya taji ta tsane shi dan ita duk wanda zai kaunaci Fulani da d'anta to bata kaunarsa. Magajin Sarki tare da Acp Mahmud a station, cikin nutsuwa suka gaisa da juna Acp yace.''Ranka ya dade ya kuma ji da faruwar wannan al'amari."? Ajiyar zuciya ya sauke yace.'' Sai godiyar Allah.'' Acp yace."Ranka ya dad'e wannan al'amari daya faru yayi mutukar girgiza mu mun shiga alhini da damuwa dangane da faruwar al'amarin dalili kuwa shine wannan asibitin naka asibiti ne mai mutukar muhimmanci a gurin al'ummar dake cikin wannan jaha mai albarka duka-duka asibitin bai kai rabin shekara da kafuwa ba amma ya kawo mana cigaban da bamu ta'ba tsammani ba, sai dai mace-macen da ake samu a asibitin yasa dukkaninmu jikin mu yayi sanyi dayawa daga cikin mutanan dake kwad'ayin zuwa asibitin domin a duba lafiyarsu tabbas nasan zasu tsorata su janye jikinsu domin tsira da ransu, ranka ya dad'e muna so kayi mana cikakken bayani akan dalilin daya sa ake samun wannan matsala a cikin asibitin ka." Acp ya 'kare maganarsa yana kallonsa. Dago kanshi yayi da niyyar magana, dan jaridar dake tsaye ya matsa kusa dashi yana gyara masa abin magana, shi kuma Acp ya gyara biron hannunsa....Yana fara maganar ya fara rubutawa a jikin takardar dake gabanshi............A nuste yace."Acp Mahmud wannan al'amarin da yake ta faruwa sai nace maka family issue ina nufin abinda ya shafi cikin gidanmu . wannan al'amarin tunda na diro duniya yake faruwa dani bazan 'boye maka ba kuma bazan 'boyewa media ba al'amarin nan daga cikin gidanmu na sarauta yake fitowa, Acp a rayuwa ta banta'ba nufin wani da sharri ba amma ni kullum cikin 'kokarin so a ga bayana ake abin na damuna mutuka gaya." Acp ya girgiza kanshi a nutse yace."Ranka ya dad'e Allah ya kare ka daga sharrin abinqi.'' Ya amsa da ameen yana goge gumin dake goshinsa.....Acp yay rubutu jikin takardar ya d'ago a nutse yace."Ranka ya dad'e afuwa shin ya akayi kasan abincin ka na dauke da guba mai karfi ka bawa hadimanka suka ci muna so muji yanda akayi haka ta faru." Murmushi yayi ya girgiza kansa yace."Acp kasan Allah ban san abincin nan na dauke da mugun abu ba, yanda al'amarin ya faru shine........Na sauko cikin shiri domin zuwa gurin aiki na samu Amintacciyar hadimata tana aikace-aikace muka gaisa da juna nan take sheda min cewa ta kammala breakfast lokacin na duba time naga idan na tsaya break zan 'bata lokaci dalili kuwa shine akwai marasa lafiyan da zan duba sai nace ta bari kawai bana bukata, ta biyo ni da magana akan na daure naci abinci saboda yanayin aikina....still na sake duba agogon hannuna na kalleta naga ta nuna yanayi na damuwa, nace ba zan tsaya ba amma ta had'a abincin ta bayar a kawo min ofis. da wannan na fita na barta a sashen nawa. ina zuwa ofis na samu coffee nasha na cigaba da gudanar da aikina misalin sha biyu shaura na rana sai ga Hadimi na Haruna marigayi ya shigo ofis d'ina da kayan abinci a hannunsa, muka gaisa yake sheda min abunda yake tafe dashi, time na duba naga idan naci abinci a lokacin zan samu matsala kai tsaye nace ya koma dashi bana bukata idan kuma yana so to ya samu wani ya taya shi ci." daga wannan magana sai na sallameshi na cigaba da aikina. to daf da zan tashi d'aya daga cikin masu kula da hospital din yaga gawarwarkin wad'annan bayin Allah a can gurin shukoki a guje yazo yana sheda mana abinda ke faruwa, Acp wannan shine cikakken bayanin da zan iya yi maka dangane da faruwar wannan al'amari. Acp Mahmud girigza kanshi yay yayi rubuce rubuce a jikin takardar kafin ya d'ago kansa yana kallonsa Yace.'' Ranka ya d'ade tilas mu aika yanzu yanzu azo da wannan yarinyar domin alamu na nuna mana cewa akwai sa hannunta a cikin faruwar wannan al'amari." Kallonsa yayi yana girgiza kansa yace."Acp ba wai zanyi maka katsalandan a cikin aikin ba amma kasan Allah yarinyar nan ta gari ce, ni zan bada shaida a kanta ba zata ta'ba yarda a had'a baki da ita a kashe ni ba, ni nasan ta ciki da waje nasan wacece ita Sumayya ba zata iya kashe kishayi ba ballanatana mutum mai rai." Acp yayi murmushi yana kallonsa a nutse yace."Ranka ya dade kai da kanka kace itace ta girka abincin nan to amma me yasa kake 'kokarin kare ta."? Girgiza kansa yayi yay shuru yana kallon kasan gurun....Acp yace."Kayi hakuri ba zamu yi mata komai ba kawai zamu tsoratar da ita ta fad'a mana gaskiyar lamari." Ajiyar zuciya ya sauke yace."Okey to babu damuwa." Acp ya dauki waya ya kira daya daga cikin ma'aikata, ya shigo sanye da kayan aiki qamewa yayi yana miqa gaisuwarsa, Acp yace."Kuje da Merry gidan Sarki zaku dauko wannan yarinyar Sumayya zamuyi binkice akanta." qamewa yayi da fadin"Okey sir.'' da sauri ya juya ya fita........... *Na kudi ne!* Kada ki karanta min littafi sai kin biya, keda kika futa da littafin keda Allah! idan kina so ki biya ga yanda abin yake....Vip group #600 normal group #300 account... 0542382124....Binta umar gtbank....idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:27 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 82 "Dan Allah kar kaqara." nafada ina sake janye jikina. Lumshe idonsa yayi ya bude a take na sunkuyar da kaina gabana na wani irin faduwa ganin yanda lokaci guda idanunsa suka jirkice." "Idan bakya so na ta'ba ki to tashi muje mu kwanta." Hannuwana nasa na rufe kirjina hawaye na zubo min nace"Nifa ba zan yarda na kwanta daki d'aya da kai ba tunda dai kai ba muharrami na bane." Tsira min ido yayi babu yabo babu fallasa yace."Nace dake babu abinda zan miki kin tsaya taurin kai ko tom zaki janyo na kwanta a kanki yanzu." Kallonsa nayi ina girgiza kaina hawaye na sake zubo min, ni dai ban san da wane nataccan mutum Allah ya had'ani ba." ''Ki daina zubar min hawaye bakya gajiya da kuka Sumayya kina dani bai kamata ki dinga zubar da hawaye ba." Cikin zuciyata nace "Zubar da hawaye dole ne tunda Allah yasa ka sauka kasar nan nake kuka har yanzu na kasa samun sassauci." A zahiri kuwa shuru nayi ina kallonsa tare da kare kirjina da hannuwana, murmushi yay ya kawo hannu zai ta'ba ni zabura nayi da sauri na matsa ina girgixa masa kaina. Dariya yasa yana kallona, na dinga watsa masa harara hawaye na zubo min, matsowa ya sakeyi sai kawai na mike da sauri zan bar gurin. 'kuguna ya ri'ko kawai ya janyo ni na zauna a cinyarsa, kansa ya d'ora a kafadata, naji ya sauke zazzafar ajiyar zuciya, hucin numfashinsa ne yake nema ya kassara ni! kafad'ata na gotar ya sake mayar da kansa yana shanshana wuya na, kafin nayi wani yun'kuri naji yana sumbatar wuyana sai goga fuskarsa yake a gurin, cikin tashin hankali nace"Dan Allah ka bari na yarda zan bika dakin." Shuru yayi yana cigaba da abinda yake, gabad'aya jikina ya mutu kasala duk ta baibayeni tuntuni hawaye ya daina fita tsoro da fargaba duk sun dabaibaye ni. Hannuwansa yake kokarin 'dorawa a kirjina na rike katamau! muryana na rawa nace"Ka bari."!!! Girgiza kansa yayi a kasalance yace."Ki bari na ragewa kaina damuwa." cikin takaici nace"Ranka ya dade wani lokacin kaine kake janyowa ina maka abinda be dace ba yanzu dan Allah meye amfanin wannan iskancin da kake min."! a kufule nake maganar. girgiza kansa yayi saitin kunnena yace."Ni ba d'an iska bane.'' fuzgewa nayi na mike ina kallonsa dik ya koma wata kala nace"To idan ba d'an iska bane menene kawai ka matseni a jikinka kana wani abu." Hannu ya miko min da fadin "Zo my love ina cikin mayen sonki." Naji kamar na kwad'a masa mari! girgiza kaina nayi nace"Ba sona kake ba dan inda kana sona ba zakayi kokarin yin wani abu dani ba har sai na zama mallakinka." Hannu ya miko zai rike nawa na kauce! ina watsa masa harara, mikewa yayi tsaye, abinda nagani yasa ni saurin kautar da kaina, gabansa ya mi'ke sosai har ya nuna ta gaban rigarsa, gabana na faduwa nayi yun'kurin barin gurin, hannuna ya rike ya juyo da fuskata yana kallona, na dinga kauda kaina dan bana so naga abinda yake firgitani! "Sumayya." sunana ya kira can cikin ma'koshi!! kasa amsawa nayi gabana sai faduwa yake yace."Kinga abinda kika janyo min ko."? k'in kallonsa nayi kawai naji ya dauki hannuna ya d'ora a gurin, ihu! mai karfi na kurma! na tunkud'eshi ya fadi saman kujera! fita nayi daga tsakanin kujerun na dinga nuna shi da hannu ina girgiza kaina, ganin ya yun'kura zai mike yasa a guje na bude kofar kicin na shiga na kulle ina haki! da kiran sunan Allah! Yarima a jigace! ya haura sama ya zube kan bed yana jan numfashi, hannu ya dora saman joystick d'inshi tana nan a mike tana harbawa, a raunane yace."Kaico! kaicon ki da kai kanki inda bai dace ba! kaicon ki da sha'awar abinda ke karkashin ki!!! jijjigata yayi yaji kamar ya murd'eta ya huta da takaici! mikewa yayi zaune yasa hannu ya dafe goshinsa zufa ce kawai take keto masa, idanu yasa kan agogon dake kan bedside Uku shaura na dare, mikewa yayi yana rangaji ya shiga toilet ruwan sanyi ya dinga kuzawa kansa yana kiran sunan Allah a zuciyarsa. Jingina nayi jikin kofar na dinga wani irin kuka abubuwa biyu sun dame ni Mutuwar Haruna ta tsaya min a rai! sai kuma masifar wannan taqadirin da Allah ya jarrabeni dashi hakika da ina da inda zanje bayan masarautar nan to dana gudu na huta da masifar wannan bawan Allah. Zamewa nayi na zauna kasan ties had'a kaina nayi da gwiwa ina takure jikina sosai nake addua a zuciyata akan Allah ya kawo min mafita. Tsakanin Magajin sarki da Sumayya babu wanda ya rintsa yanda suka ga rana haka suka dare! Asubah nayi na bude kicin din na fito, lokacin yana kokarin saukowa ko kallonsa banyi ba na karasa bakin kofa, hannu nasa naji ta a rufe gefe na matsa sakamakon karasowarsa gurin Daf dani ya tsaya yana sanye da jallabiya ash color sai kamshin turare yake, na dauka zai min magana sai naga shima ya dauke kansa, kofar ya bude ya fita, da sauri nabi bayansa.........Hadimansa na ganin fitowarsa suka karaso gurin ganina yasa sukayi sak!! yace."Sumayya ta kwana a sashena dalili jiya ni da ita bamu shigo da wuri ba sai bayan sha biyu na dare wannan dalilin yasa na hanata tafiya sashensu." yafadi hakane domin kada su zargi wani abu. Sunkuyar da kansu sukayi suna masa barka da fitowa, gaba yayi ba tare daya amsa musu ba da sauri suka rufa masa baya domin shiga massalaci. Ina kokarin shiga gurin mu babana ya fito daure da alwala, ganina yasa ya zube a gurin yana godewa Allah! mikewa yayi ya rike hannuna cikin murna yace."Sumayya ina fata ba suyi miki komai ba."? Nace"Ba suyi min komai ba baba amma dai basu gama binkicensu ba." A sanyaye yace."Ni da mahaifiyar ki bamu rintsa ba saboda fargaba kwana mukayi muna addua akan Allah ubangiji ya kubutar dake." Hawaye na share ina jin tausayinsu na ratsa ni nace."Baba insha Allahu Gaskiya tana tare da mai gaskiya in Allah ya yarda Allah zai wanke ni." ya amsa da ameeen da fadin" Ki shiga ciki mahaifiyarki ta ganki ko hankalinta ya kwanta." Da sauri nace"To baba." Lawi sai da yaga shigewarta cikin gidan sannan ya nufi massalaci domin gabatar da sallar asubahi. Tambaya rungume ni tayi ta dinga kuka da kyar na rarrasheta tayi shuru ta dinga duba jikina wai ko sun dake ni. nace"Tambaya ki kwantar da hankalin ki babu abunda akeyi min sai tambayoyi." A jiyar zuciya ta sauke tace."Sumayya jiya na shiga tashin hankali da damuwa sakamakon zuwan 'yan sanda da tafiyarki na dinga addua ina rokon Allah akan kada ya basu dama su cutar dake ina jin tsoron kada wani mara imanin ya keta miki alfarmarki." Girgiza kaina nayi nace"Tambaya Allah ya kare ni kuma zai cigaba da bani kariya albarkacin adduarku insha Allahu wani mummunan abu ba zai faru dani ba." Zazzafar ajiyar zuciya ta sauke ta cigaba da kallona kai kana ganinta zaka san tana cikin tashin hankali mai tsanani, sai da na tabbatar hankalinta ya kwanta tukkuna naje na dauro alwala, na dawo kuryar dakin na shiga nasa hijabi kana na tsaya kan dadduma a nutse na tayar da sallah. Ganinsa a massalacin yasa jikin Ciroma da mu'karrabansa yayi sanyi ikon Allah yaushe ya dawo gidan? kai amma ba suji dadin ganinsa ba. Maimartaba da Waziri kuwa babu wanda ya kaisu farin cikin ganinsa ko bayan da'aka idar da sallar Liman ya dade yana addua akan abubuwan dake faruwa a masarautar Liman yayi zafafan adduoi akan Allah ya tuni asirin masu aikata mugun 'kulli a masaraura, Ciroma da galadima jikinsu ne yayi sanyi ganin yanda Liman ya dage yana addua jama'a na amsawa da ameeen ya Allah! duk sai suka tsargi kansu da kansu suna ganin kamar asirinsu na daf da tonowa.......Muddibo kuwa dama ana idarwa ba tare da kowa ya ankara ba ya silale daga massalacin, can sashen Uwargida ya nufa ya sheda mata abinda ke faruwa, Uwargida Huwaila ranta yayi mugun b'aci! jin cewa ai Yarima ya dawo gida su duk a tunaninsu hukuma zata ri'keshi akan abinda ya faru sai kuma suka ga sa'banin haka, jiki a sanyaye ta koma ta zauna kan kujera tana tunanin mafita. Tare suka fito da Shatima daga massalaci, kai tsaye sashen fulani suka nufa suna tafiya suna tattauna al'amarin, karo suka ci da Muddibo ya fito daga sashen uwargida ganinsu a tare yasa gabansa faduwa amma da yake 'kwaro ne nan da nan ya dake! ya karasa inda suke a nutse ya basu hannu suka gaisa, yace."Yanzu nan nake tunanin zuwa sashen ka ashe ka dawo gida."? Yarima yace."Eh Allah ya takaita na dawo jiya misalin sha biyu na dare." Cikin alhini yace."To Ubangiji Allah ya kiyaye a gaba amma yana da kyau kasa ido sosai a sashen ka abubuwan dake faruwa da kai sunyi yawa." Yace."Insha Allah yau din nan zan zauna dasu saboda jiya bayan dawowata na samu abun hannun wani daga cikinsu hakan ya sake tabbatar min da cewa akwai sa hannunsu a cikin al'amarin." Muddibo cikin faduwar gaba yace."Ka samu sheda kenan."? Yace."Kwarai kuwa." Muddibo girgiza kansa yayi yace."To babu damuwa Muje mu gaisa da Mamma sai mu zauna dasu din." tare suka shiga falon, tana zaune kan dadduma da carbi a hannunta, ganin gudan jininta lafiya lau yasa taji wani sanyi ya sauka a zuciyarta, lallai addua bata faduwa kasa banza, a nutse suka zauna gabanta suna gaisheta, ta dinga amasawa tana shafa kansu, tace''Ina rokon Allah yayi muku albarka ya kareku daga dukkanin sharrin abinqi dukkanin mai nufin ku da sharri ina rokon Allah ya mayar dashi kansa, babana hakika naji dadin ganinka cikin nutsuwa ina rokon Allah ya kiyaye gaba su kuma wad'annan bayin Allah da suka rigamu gidan gaskiya ina rokon Allah ya jikansu ya gafarta musu." Suka amsa da ameeen suma ameeen." Koda suka fito daga sashen mamma kai tsaye Sashen Waziri suka nufa, iyalin Waziri ganinsa lafiya lau yasa su farin ciki suka dinga yi masa adduar kariya daga dukkanin abinqi! lafiya lau suka fito daga sashen suka nufi na Galadima, babu yabo babu fallasa suka gaisa da juna har suka fito babu wanda yayi masa jajen abinda ya faru ballantana ya samu kyakkyawar addua, sosai al'amarin ya bashi mamaki! Shatima ma yaji takaicin abinda iyayensa sukayi 'karara suke nuna hassadarsu abin da iyayensa da sauran 'yan uwansa keyi sam bayayi masa dadi, hakuri ya shiga bashi, Magajin sarki ya dakatar dashi da fad'in "Kada ya sake bashi hakuri akan abinda akayi masa shi bai dauki abin da zafi ba yana ganin duk abinda sukayi a kansa daidai ne! Shatima ganin ransa ya baci yasa ya bar maganar, Suna daf da shiga sashin Ciroma Mudibbo yace." Su shiga kawai zai dauko wayoyinsa a gurinsa, ba tare da sunce wani abuba sukayi gaba, shi kuma kamar gaske ya nufi gurinsa, tsayawa yayi na minti biyar, ya leko kansa ganin sun 'bace daga gurin yasa da sauri ya fito, kai tsaye 'bangaran bayi ya nufa. Babu yabo babu fallasa suka gaisa da iyalin Ciroma dukkaninsu suka cika falon kowa na fadin albarkacin bakinsa akan abunda ke faruwa, shi dai jinsu kawai yake dan ya kasa cewa komai saboda hayaniyar da tayi yawa a falon sai zagin Sumayya suke suna cewa ita za'a daure tunda itace ta girka abincin dole a tsaurara binkice akanta ta fadi wanda ya bata gubar.....Gimbiya Lawisa ta zage sai cin mutuncin Sumayya takeyi, 'yan uwanta suna taya ta, ga mahaifiyarta a zaune ta kasa tsawatar musu, takaici yasa ya mike Shatima ya mike sukayi musu sallama suka fito, rai a 'bace ya kalli Shatima yace." Gabad'aya naji na tsani Lawisa wallahi bata da tarbiya ko kadan." Yace."Kasan hausawa nacewa Tarbiya daga gida take farawa Hajiya Karima sam bata da tsawatarwa shiyasa 'ya'yanta suka lalace." Yace."Allah ya kyauta hakikanin gaskiya ina fargabar auran Lawisa ta haifi min lalatattun 'ya'ya." Yace."Haba ai ba 'anan take ba kaifa tsayayyan namiji ne kai zaka tsaya akan iyalinka sosai na tabbata zaka iya sanja mata hali idan kukayi aure." Girgiza kansa yayi yace."Hakika idan ta sake tazo min da mummunar d'abia to zata sha wuya a gurina dan na tsani mace mara nutsuwa wallahi." Shatima yace."Gaskiya mace mara kintsi bata da dad'in sha'ani kamar yanda na fad'a maka da farko hakane idan kukayi aure zaka iya canzata mutukar tana kaunar zama dakai dole tabi dokokinka." shuru yayi be sake magana ba har suka isa sashen nasa, kafin su shiga ciki ya kira Mika'il yace dashi gabad'ayansu suzo yana san ganinsu.......Suna zama Muddibo ya shigo hannunsa rike da wayoyinsa kusa da Shatima ya zauna yana duba 'karamar wayarsa Shatima kallonsa kawai yake sam be yarda dashi ba, tuntuni yake zarginsa kawai dai yayi shuru ne yana kallonsa kuma yana rokon Allah ya tona masa asiri.......Su shida suka shigo suka samu guri guda suka jeru gabad'aya sunkunyar da kansu sukayi kasa suna jiran suji kiran da ake musu. *Na kudi ne!* Kada ki karanta min littafi sai kin biya keda kika futa da book din keda Allah idan kina so ki biya ga yanda abin yake Vip group #600 normal group #300...account... 0542382124....Binta umar gtbabk....idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:27 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (kainuwa dashan Allah✊?) 81 "Idan ba shine yayi sanadiyar mutuwar Haruna ba to waye? ni daina nasan lafiya lau na gama abinci na shirya komai akan tire kafin na fito daga kicin din na sameshi yana kokarin fita! gabana ne ya fad'i! lokacin dana tuna kafin ya fita ya bani umarnin akan na gyara masa daki, tabbas a wannan lokacin wani zai iya shigowa ya aiwatar da kudirinsa" Anya kuwa ni nafi zarginsa akan shine keda hannu akan faruwar al'amarin watakila bayan haruna ya kai masa abincin ya zuba guba a ciki ya bashi." To in banda abinki Sumayya idan Yarima ya kashe Haruna akan wata manufa shi kuma direba mai yayi masa da zai had'a dashi ya kashe."? jikina ne yayi sanyi jin irin k'alabulanta ta da zuciyata takeyi akan zargin da nakeyi akan Yariman. Gabad'aya jikina ne yayi sanyi na dinga tunanin waye yake da hannu a cikin wannan abu, ance zargi zunubi ne koda ya kasance gaskiya ne to amma irin munanan kalaman da ya dinga yi akan haruna yasa nake zarginsa da kashe shi domin bukatarsa ta biya a kaina. Na jima ina sa'kawa da kawancewa kafin naji motsin saukowarsa, kauda kaina nayi da barin kallonsa har ya karaso kusa dani ya zauna yana sanye da farar jallabiya mai karamin hannu da alama wanka yayi kafin ya sauko. Ganin yanda ya naniqa dani yasa na janye jikina gami da sunkuyar da kaina kasa. "Sumayya." Naji ya kira sunana! shuru nayi ban amsa ba. Ya sake kiran sunana da fadin"Ina so ki kalle ni sosai zamuyi magana." Kallonsa nayi, naga babu wasa a fuskarsa yace." Ni Ban kashe Haruna ba sai dai ajalinsa ya sauka ta dalilin cin abincin da ya kasance nawa, Allah yayi nufin Haruna da Atiku ne zasu mutu ta wannan hanyar saboda haka kada na sake jin kinyi furuci akan cewa ni na kashe su. Bude baki nayi zanyi magana yasa hannu ya rufe min baki yana girgiza kai yace."Nasan abinda zaki ce! kina so ki kalubalance ni akan maganata ko."? shuru nayi ina kallonsa, ya cigaba da cewa." saboda kawai nayi wad'annan furucin nawa na baya kike so ki gazgata zargin ki a kaina wallahi Allah kenan ban kashe wad'annan bayin Allah ba." Jin yanda yake rantsuwa da Allah! yasa jikina ya mutu, a sanyaye nace"To idan ba kai bane wanene ? ni dai nasan tsaf na kammala komai kafin naje na gyara maka dakinka kamar yanda ka umarce ni. Girgiza kansa yayi yace." Wata'kila lokacin da kika tafi gyara min daki aka samu wani ya shigo yayi abinda zaiyi ya fita ba tare da kin sani ba, kin dai san yanda ni dake muke fama da masu farautata a kullum dama suke nema akaina su cutar dani , ki tsaya kiyi tunani sosai akan maganata, Sumayya duk 'kiyayyar da nakewa Haruna ba zan kashe shi a kan son duniya ba, naji ciwo sosai da abinda kikayi a station har kina fitar da hannu kina mari na! sannan har kina kiran mu azzalimai shin kin san irin masifar da zaki jefa kanki a sakamakon wannan haukan da kikeyi to bari kiji na tausayi miki ne saboda nasan kina cikin rud'ani inda naso a station d'in zan sa ayi miki rashin mutumci! bayan nan kuma na ku kulle ki har karshen rayuwarki!! ina da dama a hannuna wacce zan iya yi miki dukkanin abinda nake so amma na kyale ki kike cin kashi a kaina! ki sani idan ni na kashe Haruna wallahi ba zan 'boye ba, zan fada kuma na kwana lafiya babu wanda ya isa yace don me! ina da wannan ikon saboda dukkaninsu a k'arkashina suke, sai dai duk ikon da nake dashi na duniya ne idan naje Lahira nan zan ga sakamakona! Sumayya ki sani Haruna da Isa da Atiku sunyi mutuwar shahada wanda yayi sanadin mutuwarsu duk sun rataya a wuyansa Ubangiji ya wankesu tas saboda haka inaso ki nutsu sosai ki daina zargina akan wannan abu, idan Allah ya kaimu gobe Acp yazo ki nutsu kiyi masa cikakken baya ni amma kika sake wani mummunan furuci a kaina to zai cigaba da daukar ki a matsayin mahaukaciya." Tun kafin ya gama maganarsa nake zubar da hawaye, ya kama dukkanin hannayena ya rike yana rarrashina, cikin sanyin murya nace"Yanzu to ta yaya za'a iya gane wanda yake aikata wannan mugun abu, idan ya kasance d'an sarauta ne shikkenan jininsu Haruna ya tafi a banza tunda kace shi mai mulki yana iya yin komai ba tare da an d'auki mataki a kansa ba." Girgiza kansa yayi yace."Baki fahimce ba sumayya ina yi miki misali ne a kaina nace miki idan ni na kashe su Haruna ba zan 'boye ba zan fad'a nine saboda nasan da wuya a d'auki mataki a kaina saboda wani dalili misali bana fatan hakan ya faru dani ace na taka wani da mota ya mutu to zan aikata abinda musulunci ya tanada zan biya diyyar rai kana kuma nayi azimi sittin kamar yanda Allah yace. idan kuma ina sane na kashe rai to zan mi'ka kaina ga hukuma nima a yanke min hukunci daidai dani idan anyi min haka to anyi min gata tunda nasan idan naje lahira dole Allah ya tuhume ni.......Sannan idan ya kasance cewa binkice ya nuna wa'inda suke dasa hannu suna da alaqa da masarauta to dole duk yanda zanyi naga nayi kokarin ganin hukuma ta dauki tsautsauran mataki a kansu tunda dai al'amarin yi sukeyi ba d'aya ba biyu ba suna ta kashe rai duk a kokarinsu nasan suga bayana gashi har yanzu Allah bai basu iko ba suna ta daukar zunubi suna dorawa kansu saboda son duniya! ba zasu daina ba har sai sun ga bana numfashi kinga kuwa dole a dauki mataki akansu idan ba hakaba to zasuyi ta kashe wanda beji ba bai gani ba." Tunda yake maganar nayi shuru ina sauraransa gabadaya jikina ya mutu da kalamansa ban ta'ba tsammanin yana da kaifin tunani da hange nesa ba sai yanzu, ni da kallon sakarai nake masa wanda ya mayar da duniya gidan jin dadi ashe yana da tunani mai kyau kuma ko yaya yana tsoron Ubangijinsa ko ga yanayin kalamansa sai dai dama ance dan adam tara yake bai cika goma ba, dole duk tsoron Allahn mutum ka same shi da wani abu na rashin kyautawa Shuru nayi ina sake risinar da kaina kasa gabadaya kunyarsa ce ta lullub'eni gaskiya nima naga tsaurin idona dana falla masa mari gaban mutane! wani lokacin har mamaki nake idan nayi masa abu ya kyaleni bai d'auki matakin komai ba, matsayin sa ya wuce ace na hada hanya dashi, amma sabida rashin girman kansa yana zama kafad'a da kafad'a dani........"Sumayya kin manta furucinsa a kanki Yarima Ali dole ya kaskantar miki da kai saboda yana so ya mori albarkatun jikinki har kike kiransa mara girman kai akwai manufa a zuciyarsa." Zuciya tace take tunasar dani abinda na manta.....Jikina na janye daga kusa dashi gabana na faduwa nace"Ka bud'e min kofa na tafi." Girgiza kansa yayi yana kallona kasa kasa yace."Kin san karfe nawa yanzu."? kaina na daga da sauri ina duba agogo, saboda rashin wadataccan haske a falon yasa banga lokacin ba Yace." 'Daya na dare ta wuce yanzu ba zan barki ki futa ba kawai ki bari sai gobe." kallonsa nayi ya d'age min girar shi! na mayar da kaina kasa ina wasa da hannuwana gaskiya nima ba zan iya fita a daran nan ba ina jin tsoron kada wani yaga fitowa ta sai dai da asuba. shawarar dana yanke kenan da zuciyata. "Tashi muje mu kwanta." Yafad'i maganar yana kokarin kamo hannuna. Da sauri na janye ina masa wani irin kallo nace"Kaje ka kwanta ni ka kyaleni anan." Girgiza kansa yayi yace."Babu amfani na tafi na barki a falo ke kadai ki tashi mu hau sama." Na dinga kallonsa ina mamakin furucinsa sai kace matarsa ta aure kai tsaye yake fad'ar maganar, tsoronsa ne ya kama ni, murya ta na rawa nace"Ni dai bana san doguwar magana dan Allah kaje ka kwanciyarka ka barni anan." Mikewa yayi ba tare da yace min komai ba ya nufi kicin, kallo na bishi dashi, minti biyar ya fito daga kicin din yana kallona yace."dana na shiga kicin ne wai ko zan iya wani abu na kasa ko zaki dafa min coffee ne kema akwai bukatar kici abinci dan na lura da yunwa a tattare dake, girgiza kaina nayi ina kokarin mikewa nace"Ni bana bukatar komai amma dai bari na kawo maka coffee din." Zama yayi kan kujera tare da fadin" Nagode." Kicin din na nufa, cikin minti goma na had'a masa abinda ya bukata ina kokarin fitowa ya shigo, kallonsa nayi ya tsaya a bakin kofa yace."Kin gama."? kaina na daga, ya karasa shigowa yasa hannu ya kar'bi tire din hannuna, bayansa nabi naji k'afata ta hard'e da wani abu, da sauri na tsaguna domin na cire abinda ya hard'e ni! wata 'yar igiyace na dago ina dubawa! "Menene wannan."? yafada yana kallon hannuna, a sanyaye nace." Igiyar hannu ce wacce su Haruna suke d'aurawa duk wanda yake a matsayin bawa a masarautar nan yana da ita d'aure a hannunsa." kar'ba yayi yana dubawa, ya kalleni a nutse yace."Muje falo." a sanyaye nabi bayansa ina mamakin abinda ya kawo igiyar kicin din. Ajiye igiyar yayi saman centar table din gabansa a nutse ya dauki cup din dake dauke da coffee din yasa a bakinsa, da sauri ya cire jin zafi na nema ya kona masa baki, ajiye cup din yayi ya dauki igiyar yana dubawa, a nutse nasa spoon a cikin coffe din ina d'an motsa masa saboda na lura zafinsa ne ya hana shi sha......"Sumayya me ya kawo wannan igiyar kicin."? naji ya jefo min tambayar, a sanyaye nace."Nima tun dazu tunanin da nake kenan."? Yace."Kodai akwai sanya hannun wasu daga cikin hadimai na idan ba haka ba me zai kawo abun hannunsu kicin me ya kaisu? me suka shiga suyi? Nace"Gaskiya kam ga alama nan ni wallahi yanzu gabad'aya al'amarin tsoro yake bani." Girgiza kansa yayi yace."Dole ya baki tsoro sumayya mutum mugun ice ne babu shakka wasu daga cikin hadimai na dake waje suna da masaniya akan abinda ke faruwa akwai bukatar na zauna dasu domin wannan igiyar ita zata tona asirin wanda ya shigo tunda kince kowa yana daure da ita a hannunsa." "Eh gaskiya ne duk wanda yake a matsayin bawa to in dai namiji ne yana daure da ita mahaifina ma yana da ita a daure a hannunsa na dama, saboda haka nima na bada goyon bayan akan ka tarasu kowanne ya nuna maka hannunsa sai ka tabbatar da yana daure da igiyar sai ka sallameshi." Igiyar ya ajiye tare da daukar coffee d'in yace.''Kada ki damu in Allah ya yarda ba za'a ja dogon lokaci ba Allah zai bayyana mana komai." A sanyaye nace"To Allah ya yarda." Falon ya dauki shuru na tsayin mintina tsakanina dashi babu wanda ya sake magana, shi yana k'urbar coffee dinsa ni kuma ina can tunanin wanda ya shigo bayan na bar falon.....Tas ya shanye ya ajiye cup din a nutse ya kalle ni yace."My lov." Gabana ne ya fad'i na kalleshi yana kallona, yace."Kin bani tea nasha ke zaki kwana da yunwa anya kuwa nayi wa kaina adalci." shuru nayi ina mamakin shu'umancin sa wai my lov muna cikin wannan tashin hankalin yake wani shirme, hannuna ya rike cikin wata kwantacciyar murya yace."Dan Allah tashi muje sama wallahi ba zan miki komai ba, ina so na kwanta na huta ne kuma bana so na barki a falo ke kadai." Cikin faduwar gaba nace"Nifa ko na kwanta ba zan iya bacci ba saboda abinda ya dame ni shi ya dame ni, bana tsammanin zan iya yafewa wanda ya kashe min masoyi." 'Bata rai yayi yace."Na gama kiran ki masoyiyata kina kiran wanda ya mutu masoyinki ashe na zama shashasha kenan kin maida soyayyata karkashin kafarki kina takawa tare dayi min abinda kike so kada ki manta fa ina sane da marin da kikayi min a station idan kinyi wasa yanzu zan fanshe abina." Kuka nasa ina masifar tsoron fitinar sa na riga nasan halinsa da naci! nace"Dan Allah kayi hakuri ka rabu dani naji da abinda ya dame ni, ka dame ni da surutai ni ban san ma sanda na mareka ba idan kuma baka bari ba ka rama marin ka shikkenan ka rabu dani da wani love." Girgiza kansa yayi yana dan murmushi yace."Waye ni! ai da zan rama da tun a can na rama na kyale ki saboda soyayyar da nake miki." Harararsa nayi ina share hawaye nace"Sau nawa kana marina a station d'in ai ka rama kawai dai yanzu kana neman wata fitinar ne ni dai na baka hakuri ka rabu dani dan Allah na samu nutsuwar zuciya nayi tunanin rayuwar da zan fuskanta bayan babu Haruna." Ina sane nayi wannan maganar domin na bashi haushi. Aikuwa yaji haushi dan wani irin kallon banza yake min kafin yace."Kada ki sake maganar matacce idan kika sake zan miki abinda bakya so kin gane ko." ? Nace"To nima kada ka sake kira na da wannan suna saboda sunan bai cancanta ya fito daga bakin ka ba tunda kasan nasan ba soyayyar gaskiya kake min ba, Haruna shi yaf........Saukar hannunsa naji a kirjina! a zabure! na buge hannunsa gabana na faduwa na matsa daga kusa dashi, matsowa ya sake yi jikina, na fashe da kuka da fad'in.................! *Na kudi ne* Kada ki karanta min littafi idan baki biya ba, keda kika futar da book din keda Allah! idan kina so ki biya ga yanda abin yake.....Vip gruop#600 normal group #300 account... 0542382124....Binta umar gtbank....idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *0708465326* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:27 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 83 Cikin nutsuwa ya d'aga kansa yana kallonsu, "Ina Hamza yake."? yafad'a yana binsu da wani irin kallo. da sauri Mika'il yace." Yana can b'angaransu Haruna." "Me yake yi a can."? Mika'il yace.''Yana taimakawa ne gurun had'a gawar." shuru yayi yana kallon k'asan kafet. Muddibo yace."Kai Mika'il maza jeka ce yazo yanzu yanzu." A nutse yace."Barshi kawai tunda akwai abinda yake yi, idan ya gama Mika'il kace ina nemansa." Mika'il yace."Insha Allahu zan sheda masa." Falon ya sake daukar shuru, Shatima ne ya mike fuska a daure ya karasa inda suke, daya bayan daya yake kallonsu kafin yace."Nasan kun san abunda yake faruwa ko."? gabadaya suka ce "Eh ranka ya dade mun sani muna rokon Allah ya kawo karshen Al'amarin." Ya amsa da ameeen kafin ya cigaba da cewa"Jiya misalin karfe bakwai zuwa takwas na safe waye ya shigo gurin nan wanda har ya samu nasarar zuba gubar data kashe wad'annan bayin Allah."? Dukkaninsu suka shiga cikin wani irin yanayi na tashin hankali suka shiga tunanin waye ya shigo a daidai wannan lokacin." Shatima yace."Kunyi shuru idan fa baku fadi gaskiya ba dukkaninku d'aureku za'ayi muddun rai gwara ku fada mana gaskiya idan da akwai hadin bakin ku a cikin abinda yake faruwa." Mika'il yace."Wallahi ranka ya dade ni dai banga wanda ya shigo gurin nan ba, iyakan mu ne kawai a gurin sai Sumayya da take shige da fice a gurin." Magajin sarki mikewa yayi ya iso gurin, igiyar hannunsa ya fito da ita da fadin""Wannan ta wacece jiya na tsince ta a kicin." dukkaninsu suka tsirawa igiyar ido, kafin su fara duba hannuwansu! Shatima yace."Dukkaninku ku nuna min hannuwanku." suka fito da hannunsu kamar yanda aka bukata, abin mamaki kowanne da tasa a daure! al'amarin ya dauresu musu kai mutuka, Muddibo ya karaso gurin yasa hannu a kafadar Yarima da fadin"ammafa abun ya bani mamaki mutuka kodai Hamza nada hannu acikin al'amarin nan shiyasa ya tsaya a wani gurin."? Ya kalli Mika'il da fadin "Maza jeka idan sun gama kace ina nemansa, Mika'il ya kama hanya ya fita da sauri Kujera ya samu ya zauna zufa na keto masa, Shatima ya zauna kusa dashi yana tausarsa, Muddibo kuwa kujararsa ya koma ya zauna yana cigaba da latsa wayarsa, Mika'il da Hamza suka shigo, da sauri ya mike tsaye, Hamza a tsorace yake kallonsa yace." Ranka ya dade a gafarce ni na tsaya ne gurin had'a gawar su Haruna." Yace."Babu damuwa, nuna min igiyar hannunaka irin wannan." Hamza da sauri ya mika masa igiyar hannunsa! Ya dinga bin hannun da kallo yana mamakin ashe zarginsa suke yi gashi kuma bashi ne ba tunda gashi yana daure da igiyarsa a hannu! Shatima yace." Wannan igiyar ta nuna mana cewa babu sa hannun d'ayanku a cikin wannan al'amari saboda haka zaku iya tafiya." Dukkaninsu sukayi godiya kafin su fita daya bayan d'aya. Muddibo murmushi samun nasara yayi ya mike da fadin"Ni zan dan fita amma ba zan dade ba zan dawo." fatan alkairi sukayi masa, hanya ya kama ya fita cikin nishadi! Shatima yace."Kasan Allah ban yarda da Muddibo ba." Kallonsa yayi yace."Shatima me yasa kake da zargi ne?" Shatima murmushi yayi yace."Ba zargi bane halinsa na sani Muddibo baya kaunarka ko kadan duk wannan abin da yake yanayi ne kawai amma zuciyarsa babu alkairi." Ajiyar zuciya ya sauke yace."To idan yana nufi na da sharri Allah ya mayar dashi kansa, babban burina shine nasan wannan igiyar ta waye a cikin bayin dake cikin masarautar nan idan aka gane me wannan igiyar ina ganin 'karshen komai yazo dole ya fadi gaskiya. Shatima yace."Binkice za'a tsaurara insha Allahu za'a gane mai ita." Yana kokarin magana, sallamarta ta katseshi, gabadaya idanu suka zubo min, a sanyaye na karasa tare da dan risinawa, gaishe su nayi, Shatima ne kawai ya amsa amma shi bina kawai yake da kallo, nace"Ranka ya dade me zan hada maka na break." "Duk abinda kikayi ra'ayi." Ba tare da nace komai ba nabi hanyar kicin, akan idonsa ta shige ya sauke ajiyar zuciya yana girgiza kansa, Shatima yace."Sosai yarinyar nan take bani tausayi wallahi tana kokari akanka mutuka." Yace."Nima nasan da haka Shatima yarinyar nan jajirtacciya ce mara tsoro naji dadi mutuka da Allah ya had'ani da ita wallahi daba dan tsayuwarta akaina ba da tuni na zama tarihi! duk wannan abubuwan dake faruwa suna faruwa ne a bisa kaddara shiyasa gabadaya naki bayar da goyan baya a station a d'aureta saboda nasan itama ba tasan yanda al'amarin ya faru ba, tunda tsaf ta kammala komai a lokacin na umarceta data gyara min daki, wannan damar aka samu aka shigo akayi abinda za'ayi aka fita tabbas Sumayya da tasan akwai abin cutarwa a cikin abinda ta dafa ba zata yarda 'kwaro yaci ba ballantana mutum mai rai." Shatima yace."Gaskiya nima na yarda ita duk rintsi ba zata taba yarda a hada baki da ita a cutar da wani ba, naji dadi sosai daka kareta a station din.'' ajiyar Zuciya ya sauke yace.''Yana da kyau muje mu samu jana'izar wad'annan bayin Allah." Shatima yace."Hakan nada kyau." Mikewa sukayi a tare suka fita, kai tsaye inda za'a sallaci gawarwakin suka nufa. Koda na gama had'a masa abin karyawar kasa barin sashen nayi sabida ina jin tsoro na fita wani ya shigo, guri na nema na zauna ina sa'ke-sa'ke! shikkenan Haruna tashi ta'kare a duniya ya bar wannan duniyar mai cike da rud'ani, hawaye ne suka zubo min nasa hannu na goge ina girgiza kaina, hakika naso nayi rayuwar aure da Haruna saboda shine yake min sahihin so wanda babu algus a cikinsa, tabbas zanfi samun cikakkiyar nutsuwar da nake bukata mutukar na aureshi, ashe duk hasashe nakeyi rayuwar Haruna takaitacciya ce a duniya ya tafi ya barni da kaunarsa a cikin raina...........Hannuwana na daga sama na soma yi masa addua samun rahamar ubangiji ina kuka nace"Ya Allah ka tona asirin wanda yayi sanadiyar mutuwar bayin ka, ya Allah dukkanin wanda yake da hannu a cikin wannan al'amarin Allah ka nuna masa iyakarsa, Allah ka jikan Haruna da dukkanin musulmin da suka gabata bayansa........Adduar na shafa a fuskata, nayi saurin kallon bakin kofa, shine a tsaye yana kallona, ashe ya shigo lokacin hankalina ya dauke gurin addua, Mi'kewa tsaye nayi, ina kallonsa Acp ne ya shigo bakinsa dauke da sallama, sunkuyar da kaina kasa nayi na d'an matsa gefe guda, A nutse suka karaso cikin falon suka samu kujera suka zauna, "Barka da zuwa." nafada ina kallon Acp. kallon mamaki yake min, kafin ya amsa da "barka ka dai." dauke kaina nayi daga gurinsa nace. "Ranka ya dade na kammala komai." A nutse yace." Ki zauna Acp yana so yayi magana dake." a nutse na zauna kasan gurin......Acp ya jima yana kallona kafin yace."Ya sunanki! Nace"Sumayya Lawi." Rubuwata yayi a jikin wata 'yar takarda, Yace."Sumayya jiya da zaki shigo sashen nan suwa kika samu ina nufin mutane nawa kika gani."? Shuru nayi ina nazari. Nace."Haruna ne da Hamza sai masu gadi da direbobi." Yace."Kin tabbata dukkaninsu kin gansu da idonki."? Nace"Eh na gansu." rubuce rubuce yayi jikin takardar, Ya cigaba da cewa! "bayan kin shiga falon baki samu kowa a gurin ba."? Nace" Eh gaskiya banga kowa ba dan har na gama aikina na fito wani be shigo ba." Acp ya kalleshi cikin nutsuwa yace."Ranka ya dade jiya bayan fitar ka shin ka rufe kofar falo ko kuma a bude ka barta."? Jim! yayi kafin yace."Acp wallahi ba zan iya tunawa ba saboda a gaggauce na fita so na manta na rufe ko kuma ban rufe ba." Acp yace."Okey daka fito wa ka samu a harabar gurin."? Yace."Ba zan iya tunawa ba tunda na fada maka a gaggauce na fito kuma ban tsaya amsawa gaisuwarsu ba kai tsaye mota na shiga direba ya jani ya fita dani." Acp ya kalleni a nutse yace."Sumayya bayan kin hau sama domin gyare-gyare shin ko yaya bakiji motsin da zai nuna miki an shigo ba." Murmushin takaici nayi nace."Banji motsin komai ba Yallabai ka duba nisan benan da kuma falon koda an shigo ba zanji motsin komai ba saboda akwai tazara mai tsayi." Yace."Hakane shin da kika sauko ba kiga wata alama ba."? "Eh gaskiya banga wata alama ba dan yanda na bar komai haka na same shi, sai dai jiya da daddare mun tsinci igiyar hannu a kicin d'in." Yace."Eh Yallabai ya nuna min kuma kafin na shigo sai da nayi binkice a kanta." Da sauri nace"Ina fata an samu me ita."? girgiza kansa tayi yace."Ba'a samu me ita ba tunda duk wa'inda muke zargi suna da ita." Jikina ne yayi sanyi na dinga kallon igiyar hannunsa ina tunani a kanta, Acp ya sauke ajiyar zuciya yana kallonsa yace."Ranka ya dade duk wani binkice da ya kamata ace munyi min gabatar dashi kuma mun rubuta komai insha Allahu zamu cigaba da binkice muna bibiyar lamarin a nutse da izinin Allah sai mun gano masu shirya wannan mugun abu, amma muna bukatar hadin kanka dake Sumayya keda kike kula da abincinsa da abinsha a duk lokacin da kika ga wani abu ko yaya ne to ki kira waya ki sanar damu halin da ake ciki insha Allahu mun shigo cikin al'amarin sai munga karshensa........Ranka ya dade shawara anan shine yana da kyau gabad'aya ka sauya hadiman ka tun daga kan masu gadi har i zuwa kan direbobi ga sanja sabbi tanan zamu gano bakin zare, sannan a cikin ma'aikatanmu zamu kawo mutum biyu domin su sa ido sosai akanka da dukkanin abinda ya shafeka ina ganin idan akayi haka za'a samu sassauci ta wani b'angaran." Ajiyar zuciya ya sauke yana kallon Acp din yace."Acp dukkanin abinda ka fad'a haka za'ayi insha Allahu zan duba shawararka yau da daddare zan zauna da mahaifiyata domin mu tattauna batun nagode sosai da kokarin ku akan wannan al'amarin ina rokon Allah ya saka muku da Alkairi." Acp ya bashi hannu yana kokarin mikewa yace."Haba abokina ai babu komai ka daina godiya dan Allah kafi karfin ayi maka komai kuma kada ka manta binkice da kare rayukan al'umma a kanmu yake kaga kuwa dole ne mu tsaya maka a cikin al'amuranka har sai munga komai ya daidaita." Murmushi yayi ya mika masa hannu sukayi musabaha, hannunsu a hade suka fita daga falon. Bayan fitar su na jima a zaune a falon ina nazari mikewa nayi da sauri na kama hanyar fita, sai nayi karo dashi, fuskarsa kawai na kalla naji jikina ya mutu, kana ganinsa da yanayinsa zaka gane yana cikin tsananin damuwa kawai dan dai yana da kokari ne, tausayinsa ne ya rufe na koma falon ina kallo ya zauna kasan kafet, a sanyaye nace"Na kawo maka kayan karin."?Girgiza kansa yayi yace."Sumayya bana tsammanin zan iya cin wani abu yanzu cikina ya cunkushe da damuwa." A sanyaye nace"Ka barwa Allah komai da sannu zai kawo maka sauki kada kayi wa kanka horon yunwa." Girgiza kansa yayi bece min komai ba ya cigaba da kallon guri guda. Nace"Na kawo maka ko."? kansa ya daga alamun "Eh." da sauri na dauko tire din dana shirya kalacin......a gabansa na ajiye, yace."Hada min tea." da sauri na had'a masa, hannu yasa ya dauka yana kur'ba yana kallona, soyayyan dankali da kwai na zuba mishi a plate nace"Ka dinga hadawa da dankalin." Shuru yayi min ya cigaba da kurbar tea din ba tare da ya dauki dankalin ba......a sanyaye na mike da fadin."Ni zan tafi." Ban jira ya amsa ba na kama hanyar fita...."Sumayya." sunana ya kira na juyo ina kallonsa. "Kizo ki karya kema." girgiza kaina nayi nace"Nace"Na karya a gurinmu." Bata rai yayi yace."Wannan uban dankalin da kika zuba waye zai ci miki." ? kai tsaye nace"Kaine zaka cinye abinka." Girgiza kansa yayi yace."Idan kina so naci to zo ki zauna ki taya ni ci bana so ki tafi ki barni cikin kad'aici.'' Kallan mamaki nayi masa, ya dage min gira yana lumshe idonsa gabadaya ji nayi gwiwata tayi sanyi a duk lokacin da zaiyi min irin wannan kallon nakan shiga cikin wani irin yanayi. "My love." a firgice! na kalleshi, yayi murmushi da fadin"Meye na furgita dan na kira ki da wannan suna. Nace"Dan Allah ka daina kirana da suna nan." "Saboda me."? nace" Kawai dai bai dace ba." Yar dariya yayi yace."Sumayya kenan to zan daina amma ba yanzu ba." Nace"To nagode." Juyawa nayi zan bar gurin, Yace."Kada ki fita." Dafe goshina nayi cikin yanayi na damuwa na juyo ina kallonsa. Yace.'"Na dame ki ko."? shuru nayi, "Ki dawo ki cinye dankalin ki." Saboda ya barni na tafi yasa na koma na zauna, kusa dashi. Plate din dankalin ya turo min yace."Oya had'a tea mai kauri ki hada da dankalin ba zan barki ki fita ba sai na tabbatar da cewa cikin ki ya cika......ba tare da nayi masa musu ba na tsiyaya tea din daidai misali, ido ya tsira min da cup din tea a hannunsa ya bar kur'ba kawai yana kallona. Nace"Wannan kallon da kake min yayi yawa za kasa na k'ware dan Allah ka dauke idonka." Ba tare da yace uffan ba ya dauke kansa cigaba yayi da kur'bar tea dinsa, a nutse nake kur'bar tea din ina had'awa da dankalin, ina kallonsa yana kallona ta gefan ido cikin zuciyata nace"Wannan idan maye ne ya kama mutum sai ya kasheshi na rasa abinda yake kallo a jikina. cikin damuwa na ajiye cup din tea d'in! kawai naga ya ajiye nasa ya dauki nawa, daidai saitin bakina yasa a bakinsa ya sumbuta kafin ya fara kur'ba! ya wani tsatstsare ni da ido, jikina ne yayi sanyi na dinga jin shigar bakon yanayi sunkuyar da kaina kasa nayi kwata-kwata bana san kallonsa saboda yanayin yanda yake sarrafa idonsa a kaina yasa naji bani da kuzari....Cup din tea din ya ajiye a gabana yana nuna min inda bakinsa yake wai na dauka nasha!! kawai na tsinci kaina da bin umarninsa, ina kokarin daidaita bakina a inda yasa nasa Lawisa ta shigo falon, cikin shigar alfarma 'kamshin turaranta duk ya game gurin, 'Kwarewa nayi nayi saurin ajiye cup din ina kallonta a yayin da take kokarin karasowa gurin da muke, sunkuyar da kaina nayi naganin yanda taci kunu! mikewa nayi da sauri, yace."Sumayya koma ki k'arasa.''! girgiza kaina nayi nace."Ranka ya dade na'koshi.'' ido ya tsira min yana so ya tabbatar da maganarsa, Gurin na bari ina fargabar kallon da Lawisa takeyi min.. Kallonta yayi sama da kasa babu laifi tayi kuma za'a huta da ita Lawisa nada kyawun jiki gata fara tas jikinta dam sai dai bata da tsayi sosai, kusa dashi ya nuna mata wai ta zauna, zama tayi tana wani cin magani tace...... *Na kudi ne!* Kada ki karanta min littafi sai kin biya, keda kika futa da littafin keda Allah idan kina so ki biya ga yanda abin yake....Vip gruop#600...normal#300 account... 0543282124....Binta umar gtnank....idan kati zaki turo#400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:27 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 84 "Wai dan Allah me yake tsakanin ka da wannan yarinyar ne? a gaskiya kusancin da nake gani a tsakaninku yana d'aga min hankali wallahi! nasan dai kafi karfin kace kana sonta tunda a karkshinka take to me zai sanya ta dinga zama kusa da kai tana cin abinci da kai."? Cikin yanayi na bacin rai ta karashe maganar, Shuru yayi yana kallon guri guda bai ce mata uffan ba, Lawisa ta sake sha'ka! murya na rawa tace" Da kaifa nake magana kana jina kayi shuru shin kasan irin son da nake maka kuwa."? A nutse ya dago kansa yana kallonta, yace." Babu abinda yake tsakanina da ita sai mutunci kada ki manta wannan yarinya itace amintaciyyar baiwa ta yanda na amince da ita ko ke ban amince dake ba saboda haka ki daina damuwa idan kin ganta a kusa dani idan da yiwuwar na aureta zan aureta babu ruwana da 'kas'kancinta." Lawisa wasu zafafan hawaye suka shigo zubo mata a kumatu tace"Yanzu kai dan Allah sai ka auri yarinyar nan shin me ka gani a tare da ita wanda ya burgeka dan Allah kada kayi min haka kada ka had'ani kishi da wannan ma'kaskanciyar idan aure kake so ka auri 'yar mulki irina amma ni nafi karfin nayi kishi da wannan yarinyar." Gyara zamansa yayi yana kallonta fuskarsa a 'bace! yace." Ni baki isa ki tsara min ga yanda zanyi ba, Sumayya baiwa tace kuma ta cancanci na aureta na 'yantata daga baiwa ta dawo mai 'yanci! Sumayya ta nayi min abinda ke bakiyi min ba, sannan naji kina fadin cewa mai na gani a tartare da ita nagarta da kyawawan halaye nagani har yasa nayi sha'awar auranta nasan kin san hakan ba haramun bane ko? zan aureku ku biyu a rana daya daga yau kisa a ranki mijinki mijin mace hudu ne bayan na aureku zan iya kara biyu sannan inyi kwarkwara idan ina da ra'ayi saboda haka kada ki kara zama a kusa dani kice zaki tsara min yanda zan tafi da rayuwata." Lawisa hawaye kawai take sharewa tana kallonsa tsabar bakin ciki da takaici ya hanata cewa komai, da shashshekar kukanta ya dameshi mikewa yayi ya haye sama ya barta zaune a gurin tana kuka na rashin madafa. "Lallai wannan yaro bashi da kirki wato ta inda ya 'bullo kenan? ya rasa yarinyar da zai aura sai baiwa makaskanciya wacce take karkashinki da ita zai hada ki kishi lallai kuwa zanje na samu mahaifiyarsa akan maganar." Hajiya Karima mahaifiyar Lawisa ce ke wannan bambamin. Lawisa na kuka tace."Wallahi Hajiya ni kaina nayi mamakin al'amarin kuma abin ya tsoratar dani mutuka dan banyi tsammanin zai iya auranta ba saboda nasan kin san yanda yarinyar take da muni gata 'baka wai har cewa yake zai aureta saboda kyawawan halayenta sannan harda cewa tafi ni a gurinsa sau dubu." Hajiya karima na girgiza kafa tace"Ki daina kuka kina damunki insha Allah idan 'kura ta lafa zan samu mahaifiyarsa da maganar dole ya za'ba ke ko baiwa dan kinfi karfin kiyi kishi da baiwar gidanku." Kai tsaye dana fita daga bangaran Yarima gurinsu Haruna na nufa, nan na samu gurun da jama'a sun kewaye mahafiyarsa suna tausarta, ganin yanda idanun jamaa yayi caaa a kaina yasa nayi niyyar juyawa, wata mata dake bakin kofa tace"Aa sumayya ya zaki koma kuma ki shiga mana." Simi-simi na shige gabana na faduwa na zauna a gabanta ina gaisheta, da kyar ta amsa min tana harara jamaar dake kusa da ita suna taya ta, shuru nayi na minti uku kafin nace"Ubangiji Allah ya jikan Haruna da dukkanin musulmin daya rigamu gidan gaskiya." Tsiraru ne suka amsa adduata, na cigaba da cewa"Lami akwai wata igiya da take daure a hannun Haruna dan Allah ita nake so ki bani domin za'ayi binkice akai." Hannu ta daga min tace."Sumayya wane binkice kuma bayan bukatarki ta biya kin kasheshi domin ki samu nasarar auran Yarima to bari kiji duk halin da kike ciki keda iyayenki mun sani Yarima ya bukaci ya aureki a lokacin da baikon Haruna akanki koda Maimartaba ya samu labari yace ba za'ayi haka ba dole ki auri Haruna Shi Yarima ya hakura, da kuka ga haka sai kuka shirya kashe Haruna saboda biyan bukatarku ko ba haka bane."? Ina kuka nace"Hakane maganarki amma inaso ki sani wallahi bamu muka kashe Haruna ba kwanansa ne ya 'kare kuma ni ko kusa ko alama bana kaunar na auri Yarima saboda wani dalili nawa, wallahi nafi bukatar na auri Haruna domin shi nake so muna san junanmu aka shiga tsakaninmu dan Allah kada ki sake wannan maganar Bamu kashe Haruna ba." Tsaki taja tace"Ni dan Allah ki tashi ki bani guri bani da wata magana dake a yanzu." Hannunta na rike ina kuka nace"dan Allah kiyi hakuri ki dauko min igiyar nan wallahi binkice za'ayi a kanta." Wacce take kusa da ita tace"Ke munafuka tashi ki futa ko kuma yanzu muyi miki duka wallahi wane irin binkice za'ayi bayan mun san gaskiyar lamari zaki zo ki nayi mana kukan munafurci." Ta kusa da ita tace"Lami ki daina kuka haka dan Allah ku dauko mata igiyar akwai alamun gaskiya a maganar yarinyar nan watakila zarginta kawai muke saboda haka ki dauko mata igiyar." Shuru lami tayi tana nazari kafin tace."Uwani wallahi ba zance miki ga inda igiyar nan take ba lokacin dai da'aka shigo da gawarsa na ganta a daure a hannunsa, sai dai ku duba gurin da'a kayi masa wanka ko zaku ganta." Uwani tace"to bari na duba." Mikewa nayi da sauri nabi bayanta, sako da loko na gurin muka duba tsaf ba muga igiyar ba jikina yayi sanyi muka fito daga gurin, Uwani tace"Muje Shara mu duba mugani ko anshare.......Muka zazzage sharar a gurin duka muka tona babu igiya, Uwani tace"Kinga ni babu alamun igiyar nan a gurin, amma bari a kira wa'inda sukayi masa wankan." Uwani da sauri ta fita ni kuma na jingina a jikin bango(garu) ina tunanin al'amarin, tare suka shigo su uku ita ta hud'u, had'a ido mukayi da Hamza na hango firgici a tare dashi, Uwani tace"Hamza kune kuka wanke gawar Haruna to binkice ne yazo ana bukatar igiyar hannunsa mahaifiyarsa ta tabbatar da cewa lokacin da'aka shigo da gawar akwai igiyar a hannunsa." Labaran yace."Tabbas kuwa ni ne na kwance igiyar daga hannunsa, na ajiye a gurin." Salisu yace."Kwarai kuwa nima na ganta da idona wallahi." Hamza cikin dauriya yace."Nima naso naga lokacin da kake kwance ta sai dai yanayin tashin hankalin da nake ciki yasa shaf na manta ban dauketa ba." Nace"To gashi dik mun duba guraran da kuka zauna ba muganta ba." Cikin firgici Hamza yace." Ku muje mu sake dubawa." Dukkaninmu muka bi bayansa, ya dinga lalube a gurin baiga komai ba, yana sharce gumi ya dago muka hada ido sai yayi saurin dauke kansa yace."Amma al'amarin nan akwai ban mamaki gashi duk an duba ba'a ganta ba." shuru babu wanda yayi magana yace."Ku muje mu duba shara." Uwani tace"Wace shara kuma bayan duka mun duba." A sanyaye ya tsaya yana kallonmu, ajiyar zuciya na sauke ina wani tunani, anya kuwa babu sa hannun Hamza a gurin kashe abokinsa? nace"Uwani tunda ba'a ganta ba ni zan tafi Allah ubangiji ya tona asirin munafukai." Uwani ta amsa da ameeen ya Allah." gurin na bari na barsu suna sake tattauna maganar. A ranar yini nayi cikin zullumi da tunanin yanayin furgicin da naga Hamza ya shiga na dinga tunanin anya kuwa be san wani abu daya shafi 'batan igiyar Hannun Haruna ba? tsabar damuwa da tunani ya janyo min ciwon kai mai tsanani idanuna sukayi jawur tamkar wacce taci kuka ta koshi nan kuwa tsabar fargaba da damuwa ce, Tambaya ganina haka yasa ta shiga damuwa ta dinga rarrashina da bani kulawa, ganin yanda duk ta tashi hankalinta yasa na sassautawa kaina tunani kawai na mika al'amarin ga Allah na cigaba da addua akan Allah yayi gaggawar tona asirin wa'ina suke shirya wannan mugun abun. *Bayan sati hudu* Al'amura sunyi sauk'i masarautar ta samu nutsuwa kowa ya kwantar da hankalinsa ya koma harkokinsa harshi Magajin sarkin ya koma aiki dama tunda gwamnati tayi dogon binkice ta gane daga inda badak'alar ke fitowa yasa ta bada umarnin bude asibitin tare da kira ga Jamaa cewa su cigaba da shige da fice a asibitin babu abinda zai sake faruwa da yardar Allah." Wannan kira da gwamnati tayi ga al'umma yasa kowa ya kwantar da hankalinsa, Asibitin *Zinariya* ya ci gaba da gudanar da aiki kan tsari da sanin ya kamata.........Al'amarin yayi masifar 'bata rayukan wa'inda suke adawa da samuwar asibitin dukkaninsu sai suka yanke shawarar karshe akan asibitin amma ba zasu aikata aikinsu ba sai ankwana biyu tukkuna sai kowa ya sakin jikinsa sai su kuma su gudanar da abinda suka shirya, 'Bangaran Yarima ya samu sabbin hadimai kamar yanda Acp ya bukata, kuma kamar yanda yayi alkawarin kawo jami'an tsaro guda biyu ya cika al'kawarinsa ya kawo jami'ai gudu uku tare da amincewar gwamnati, sosai gurin yayi lafiya kowa yana gudanar da aikinsa yanda ya kamata, jami'an tsaron sunsa ido sosai da sosai dan ba kowa suke bari ya shiga sashen kai tsaye ba sai sunyi binkice a kansa tukkuna suke bari ya shiga, mutukar kuwa Yarima baya nan to basa barin kowa ya shiga har sai ya dawo nima ina gama ayyukana nake fitowa. 'Karfe hudu da rabi na ranar talata na fito daga gurin karatu kai tsaye sashen Yarima na nufa domin gudanar da aikina, tun daga nesa na hangoshi a tsaye a bakin kofar shida jami'an tsaron, fuskarsa kadai na kalla na hango tsantsar bacin rai a tare dashi, Koda na k'arasa gurin nan na fahimci akan abinda yake faruwa, wato yana so ya shiga sashen Su kuma sun hana shi sunce yayi hakuri mai gurin ya dawo daga aiki! Muddibo ya dinga huci yana sakar maganar da duk tazo bakinsa, Daya daga cikinsu yace."Ranka ya dade ba wannan muke nufi ba ai mun san kai ba zaka ta'ba cutar dashi ba muna so ka fahimci yanda tsarin namu yake Shugabanmu dashi kansa mai gurin yace kada mu bar kowa yana shiga sai da izininsa saboda haka kayi hakuri idan ya dawo ya bamu umarni sai mu barka ka shiga." Muddibo ya dinga wani irin huci! yana zaginsu, gami da fad'in "Idan mai gurin ya dawo zai nuna musu muhimancinsa a gurinsa." a hankali nace"Ranka ya dade barka da yamma." ko kallona beyi ba ya bar gurin, Da sauri daya daga cikinsu ya bude min kofa da fadin"Maza shiga kiyi aikin ki ki rabu dashi." Da sauri na shige ina mamakin al'amarin, to me ya kawo Muddibo sashen Yarima bayan yasan baya nan? idan an bude masa ya shiga me zaiyi a ciki, ina ayyukana ina tunanin al'amarin, sai bayan magariba na gama aikina na fito lokacin sun fito daga gurin sallah bude min kofa sukayi na fita tare dayi musu bankwana, Ganin gari yayi duhu yasa na kara sauri domin isa gurinmu kawai naji an tare ni!! gabana ya fadi ina dago kai muka hada ido dashi! ido jawur yake kallona cikin dauriya nace"Ranka ya dade kana bukatar wani abu ne."? Wawan mari! ya kwada min na fadi a gurin! tsaye na mike ina kallonsa hannuna dafe da kumatuna! wuya na ya shaqe na dinga kakari!! sai da ya galabaitar dani tukkuna ya sake ni! na sake faduwa a gurin! Ya tsuguna gabana yana kallona ina kallonsa makogwarona ya bushe kamas! Yace."Zan saki aiki a sashen Yarima wallahi tallahi idan kika kuskura kika ki aikatawa sai nabi dare da rana na kashe ki."!!!! Gabana ya dinga faduwa! ya cigaba da cewa'' Kin saba lalata mana aiki to wannan ce damarki ta karshe mutukar banga biyan bukatata ba to ki tabbata zakiyi kwanan barzahu! sai na kasheki.''!!! nace"Ranka ya dade babu mai kashewa sai Allah haka kuma babu me rayawa sai Allah! mutukar kaga na mutu to kwana nane ya k'are." Hancina ya kaiwa duka! a take ya fashe! jini ya shiga shatata! ido jawur nake kallonsa, sai huci! yake! nace"Ranka ya dade wane irin aiki zanyi maka."? Murmushin mugunta yayi yace."Wato kinga uwar bari ko."? shuru nayi ina kallonsa hancina na cigaba da zubar da jini! Hannu yasa a aljihu ya d'auko wani abu a d'aure a takarda! " Wannan maganin nake so kisa masa a lemo." Kar'ba nayi ina kallonsa, yace."Kin gane ko."? kaina na daga masa! ya yunkura zai mike tsaye na kwance maganin na watsa masa a fuskarsa! da sauri na mike tsaye! zan gudu, ya tad'o kafata na fad'i a gurin! cikin fitar hayyaci na 'kwallara 'kara! wanda yayi daidai jin saukar wani irin bugu a kaina! idanu na na rintse na zube a gurin ina kiran sunan Allah! Muddibo na jin sawun mutane da sautin maga na yasa da saurin gaske ya bar gurin.............. *Na kudi ne* Kada ki karanta min littafi sai kin biya keda kika futa da littafin keda Allah! idan kina so ki biya ga yanda abin yake Vip gruop#600 normal gruop#300 account... 0542382124...Binta umar gtbank idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:27 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 85 Hayaniyar mutane na dinga ji sama-sama a kaina na mika hannu cikin mawuyacin hali nace"Ku taimake ni ku kira min iyayena mutuwa zanyi." Rumfa sukayi a kaina suna so su tantance abinda ke faruwa, cikin bushewar makogwaro na sake cewa"Uwani ku taimaka min ku kira min iyayena mutuwa zanyi." Uwani tasa salati tana fadin"Ai wannan Sumayya 'yar gidan Lawi ce." Da yake da karfi tayi maganar babu wanda beji ba, Tambaya turmutsawa tayi cikin mutane ta iske inda d'iyarta ke kwance cikin jini! dan dutsen da Muddibo ya buga mata yayi nasarar fasa mata kai. Jiki na kyarma ta zube a gabanta hawaye na shatata a fuskatarta hannu tasa ta tattaro ta jikinta ta rungumeta tana kuka had'a kiran innalilihi wa'ina ilaihi raji'un.! Mika'il ne ya karaso gurin da toch a hannunsa yana haskawa dawowarsu kenan yaje ya dauko Yarima daga asibiti ya samu labarin abinda ke faruwa shine yazo ya ganewa idonsa, aikuwa ganin Sumayya cikin mawuyacin hali yasa a guje yaje ya shedawa Yallabai din halin da ake ciki. Tare suka zo gurin da jama'i guda d'aya lokacin Sumayya ta suma dan bata san wanda yake kanta ba, Tambaya kuka kawai take tana jijjigata gami da kiran sunan Allah tana langwa'bewa! Jama'ar dake kewaye dasu suna ganinsa suka bashi hanya, ganinta cikin jini ya daga masa hankali, tsugunawa yayi yana kallon fuskarta, Tambaya ta fashe da kuka da fadin"Ranka ya dade ka taimaka mana kada mu rasa ta." Maganarta ce ta dawo dashi nutsuwarsa ya kalli Lawi dake gefe a tsugune ya had'a uban tagumi! yace."Me ya faru da ita."? Lawi yace."Wallahi ranka ya dade dukkaninmu bamu san abinda ya faru ba kawai dai munji ihunta ne koda muka zo gurin sai muka ganta kwance cikin jini." Juyawa yayi ya kalli jama'ar da sukayi dafifi a gurin, yace."Kowa ya tafi.' da sauri suka watse! ya kalli Tambaya jiki a mace yace."Zamuje da ita asibiti domin taimaka mata." Tana kuka tace"Allah ya saka maka da alkairi." Hannu yasa yana kokarin daukarta, Lawi yace."ranka ya dade da kanka." Kansa kawai ya girgiza masa shi yanzu meye ba zaiyi wa yarinyar nan ba watakila ma gurin bashi kariya ta had'u da tsautsayi koma dai menene idan ta farfad'o tilas tayi masa bayani. Mikewa yayi da ita a hannunsa, Mika'il da security dinsa sukayi gaba da sauri, Tambaya da Lawi suka rufa musu baya. Bayan mota ya kwantar da ita, ya dan gyara ta domin ya samu gurin zama ya kallesu sun bashi tausayi mutuka ciki kokarin kwantar musu da hankali yace."Insha Allah da kafafunta zata dawo ku daina damuwa kuyi mata addua." Lawi ya sauke ajiyar zuciya da fadin"Ubangiji Allah ya tashi kafad'arta." ameen yace tare da bawa Mika'il umarnin tafiya, sai da motar ta 'bace wa ganinsu sannan suka nufi sashen su cikin halin damuwa gami da rokon Allah sassauci! Tun mota yake bata taimakon gaggawa dan bakinsa da nata ya had'a ya dinga hura mata iskar bakinsa gabadaya jikinsa ya baci da jinin dake fita ta goshinta, hannusa guda yasa ya danne inda jinin ke zuba ya cigaba da bata taimako irin nasu, cikin ikon Allah kuwa suna daf da shiga asibitin ta farfad'o Allah ya godewa ya rike hannunta tsam a cikin nasa. Cikin kwarewa da sanin makamar aiki ya tsayar da jinin dake zuba daga goshinta, duk wani taimako da yasan tana bukata sai da yayi mata ya samu nutsuwar zuciyarsa, zama yayi gefanta tare da rike hannunta guda, fuskarta ya tsirawa ido tana ta bacci dan sai da yayi mata allura kafin ya fara aikinsa. Ajiyar zuciya ya sauke ya tsirawa ties ido babban burinsa yarinyar ta samu nutsuwa ta sheda masa abinda ya faru da ita, tabbas yana zargin wasu daga cikin ma'kiyansa ne suka soma farautar ta, shi kam ya rasa yanda zaiyi da rayuwarsa da makiya. Agogon hannunsa ya duba karfe daya da rabi na dare, ashe ya jima a zaune yana tunani, hannunsa dake cikin nata yayi nufin cirewa ta rik'e! sai yayi saurin kallo ta yana kiran sunanta Jin muryarsa ta doki kunnena yasa nayi gaggawar bude idona! idanuwanmu ne suka had'u, kawai hawaye ya kwace min na rintse hannunsa dake cikin nawa ina kallonsa hawaye na ambaliya a fuskata, Jikina ya matso sosai jikinsa har rawa yake yace."Sumayya sannu kinji ko ki fada min inda ke miki ciwo." Hannuna na dora saman goshina naji shi a nannad'e! cikin sanyi jiki ya dauke hannuna dake gurin yace."Zai daina ciwo insha Allah! kiyi hakuri kinji ko." Kaina na daga ina kallonsa tausayinsa na ratsa zuciyata. Yace."Ko zaki tashi zaune."? kaina na girgiza alamu A'a. Dakin yayi shuru na minti biyar kafin yace." Zaki iya yi min bayanin abinda ya same ki."? Kai na d'aga alamun "E" ya sake matsowa kusa dani murya a kasa yace." Ina sauraranki. Muryata na rawa nace"Muddibo ne." da sauri ya kalleni nasan mamaki yake jin na ambaci sunan Muddibo. Yace."Muddibo ne sumayya me yayi miki." ? nasa hannu nagoge hawayen dake zuba, nace"Aiki ya sani nace ba zanyi ba shine ya kwada min mari hakan be isheshi ba ya dauki dutsen wuta ya buga min akaina kashe ni yayi niyyar yayi kamar yanda ya fada zuwan mutane gurin yasa ya gudu. Gani nayi ya sunkuyar da kansa fuskarsa kamar ta nuna alamun rashin yarda Nace"Dama nasan ba zaka yarda ba." ya kalleni babu walwala a fuskarsa yace."Sumayya dole nayi kokwanto akan hakan shin wane irin aiki ne ya sakiyi masa kikai masa gardama."'? "Magani ya bani yace." Lallai na zuba maka a lemo." Kallona yayi yana mamakin maganata! nace"Ni kuma na kwance maganin na watsa masa a fuskarsa." Cike da mamaki yake kallona kafin yace." Sumayya me yasa kike da tsaurin ido ne? saboda kawai Muddibo ya baki magani kisa min a lemo sai ki watsa masa a fuska sa'anki ne ko kuwa ? Muddibo zai iya daukar mummunan mataki akanki." Raina a bace nace"Akan na kashe wani gwara ni a kasheni dama aini baiwa ce kowa yana iya amfani dani ta kowace hanya amma nayi rantsuwa ba zan taba bari amanar Allah ta cini ba."! Girgiza kai yake yana kallona yace."Kwarai ina yaba miki! bisa namijin kokarin da kike gurin ganin kin kare raina da lafiyata, amma me yasa baki bi umarnin muddibo ba, me yasa baki kar'bi maganin ba idan yaso ke kuma sai ki san yanda kikayi kika zubar dashi a wani gurin, na tabbata tsaurin idon da kikayi masa ne yasa yayi miki wannan mumman dukan, Sumayya inaso ki san da cewa ni kad'ai ne zaki iya yiwa zafin kai! na rabu dake amma baki isa kiyiwa wanda yake sama dake tsaurin ido ya kyaleki ba." Shuru nayi ina nazarin maganarsa, eh kamar yanda yace dana sani na yaudareshi na karbi maganin daga bisani sai na zubar kawai. wani lokacin ne idan zuciyata ta dauki zafi ni kaina bana iya tank'warata." "Kin tabbata cewa Muddibo ne ya aikata miki wannan mummunan abun."? Kaina na daga ina goge hawaye, Yace." Lallai za'a ramawa kura aniyarta dan ba zan k'yale Muddibo ba sai naci mutuncinsa wallahi tallahi sai yayi daya sanin ta'ba lafiyarki, ni akan wannan zan dauki mataki a kansa daga baya kuma sai ya shedawa Police Maganin me ya baki kisa min a lemo." Dad'i naji a cikin zuciyata jin cewa zai dauki mataki akansa, nace"Daka dauki mataki akan yunkurin kashe ka da yake ina ganin shi yafi amfani tunda ni ba'a bakin komai nake ba a cikin masarauta kamar yanda ka gama fada yanzu." Girgiza kansa yayi ya rintse hannuna da nashi yace."Sumayya a cikin masarauta ba'a bakin komai kike ba kamar yanda na fada miki yanzu amma sanadiyar faruwar wannan al'amari masarauta zata san kina da muhimanci a tare da ita." Lumshe idona nayi kawai na tsinci kaina da d'amke hannunsa dake cikin nawa, gabad'aya muka had'e yatsun hannunmu guri guda tamkar masu d'aukarwar junanmu al'kawari. ' Dakin ne yayi shuru na tsayin lokaci kafin naji ya kira sunana, idona na bude ina kallonsa, yace."Kiyi bacci kada kisa damuwar komai a cikin ranki kinji ko." Lumshe ido nayi a hankali nace"Dan Allah kayi hakuri kabar maganar kada kayiwa Muddibo wani abu ni dama babban burina ka gane gaskiya ka amince da dukkanin gaskiyata." Ido ya zuba min kafin ya shiga girgiza kansa yace."Sumayya ba zan ta'ba yafewa kaina ba mutukar na bar jininki ya zuba a banza ni d'an halak ne kuma nasan abinda ya dace ." Shuru nayi ina tunanin abinda zai faru a gaba bana so garin d'aukar fansa wata masifar ta faru a tsakaninsu nafiso kawai ya bar maganar kada yace zai dauki mataki kan abinda akayi min. Hannuna ya saki ya mike kallo na bishi dashi, ya nufi toilet, ajiyar zuciya na sauke a hankali na rintse idona ina addua cikin zuciyata. Motsin fitowarsa tasa na bude idona ina kallonsa naga ya shimfida dadduma, da alama sallah zaiyi idanuwa na mayar na rufe ina tunanin iyayena yanzu ko wane irin hali suke ciki? nasan dai duk inda suke suna cikin tashin hankali da damuwa mai tsanani! hawaye suka zubo min a kumatu hannu nasa da sauri na goge ina kokarin danne kukan dake kokarin kufce min. b'angaran Magajin Sarki kuwa nafila yayi raka biyu ya daga hannu sama ya roki Allah sosai akan abubuwan dake faruwa da rayuwarsa da makusantan sa yanzu abun ya wuce kansa har yazo kan masu kula dashi, tunda an kasa samun galaba a kansa to bari a sabauta hadiman sa, gaskiya magana dole ya dauki mataki akan al'amarin dan yana ji yana gani jinin yarinyar dake tsaye a kan rayuwarsa ya tafi a banza ba dole ya nunawa Muddibo kuskuransa, ya jima hannu a sama yana rokon Allah kafin ya shafa adduar a fuskarsa ya mike a nutse ya nufo gadon da nake kwance. Cikin bacci na jishi a jikina, nayi saurin bude idona ina kallonsa yana kokarin kwanciya kokarin mikewa nayi yayi saurin rike hannuna! Girgiza min kai yayi a hankali yace."Ki kwanta mana." Murya na rawa nace"To ka tashi daga kusa dani.'' a hankali yace."Dan gurin dana kwanta bai isa ya tsare miki gurinki ba kiyi hakuri ki kwanta babu abinda zai faru sai alkairi." A sanyaye na dinga kallonsa ina mamakin karfin halinsa Tamkar wata matar auransa haka yake Mu'amula dani. "Gaskiya ni bazan kwanta gado daya dakai ba saboda haka bari kawai na sauka kasa.'' Yunkurin sauka nake ya rike kafaduna! cikin kulawa yace." Saboda na kula da motsin ki yasa zan kwanta kusa dake amma tunda bakya so shikkenan bari na sauka." kallo na bishi dashi lokacin daya sauka daga gadon ya koma kan doguwar kujera ya kwanta, tausayi ya bani ganin yanda yayi sanyi yana min magana cikin kwantar da murya na amince da cewa abinda ya faru ya girgizashi mutuka yanzu kuma na gane cewa ina da muhimanci a rayuwarsa tunda gashinan a zahiri ya nuna tashin hankalinsa..........Na jima ina tunane tunane kafin bacci ya d'aukeni! bacci mai cike da munanan mafarkai marasa dadi da ma'ana. Kiran sunana da ake yasa na bude idona da sauri ina kallonsa yana tsaye a kaina, hannu na dora saman kaina ina jin wani irin ciwo a gurin, a nutse yasa hannu ya cire hannuna, "Sannu." kaina na d'aga ya cigaba da cewa"Kinga gurin yayi fushi ko."!? kaina na girgiza a hankali na fara kokarin mikewa ya kama hannuna, kallonsa nayi ya girgiza min kai da fadin"Kada kice komai taimaka miki zanyi kiyi alwala ko." Shuru nai masa, ya fara kokarin dora hannuna a kafadarsa, yana so ya rike kuguna. da sauri nace"Dan Allah ka barni zan iya komai da kaina. Bai saurare ni ba, ya ratsa hannusa a k'uguna, ya sani a jikinsa sosai muka nufi toilet, kallona yayi yace."Babu inda ke miki ciwo ko."? ganin yanda ya damu yasa nace"Eh babu kaina ne ke ciwo." Cikin rarrashi yace."Bari kiyi sallah sai muje gida kiyi break kisha magani insha Allahu zaki samu sauki." Kaina na dauke jin wani irin abu dangane dashi, ya miko min brush da fad'in" Maza ki wanke bakin ki idan kuma ba zaki iya ba nayi miki ko."? saurin kar'ba nayi na nufi inda famfo yake, a nutse na wanke bakina cikin dubara nai alwalar, ya karaso gurin hannuna ya rike muka fita daga toilet din. Farin hijabi irin na ma'aikatansa ya samin a wuyana ya gyara min dadduma na tayar da sallah. Zama yayi kan kujera da wayarsa number Acp ya kira, suka gaisa cikin mutumci yayi masa bayanin dukkanin abinda ke faruwa, Acp yace."Tabbas biri yayi kama da mutum ranka ya dade a binkicenmu na baya sai da naso na fuskanci wani habu daga gurinsa to alhamdulillahi dama barinmu mu kama wanda yake da hannu acikin al'amarin sabida haka ka kwantar da hankalinka insha Allahu yau din nan zamu dam'keshi dole ne yayi mana bayanin yanda al'amuran suke faruwa." Yace."Okey to babu damuwa amma bana so ku shiga masarautar da niyyar kamashi kuje gurin aikinsa ku tozartashi acan sannan ku daureshi ku tafi dashi, bayan kun dam'keshi ka kira ni a waya inaso dik wani bayani da zaiyi ya kasance ina gurin." Acp yace."Babu damuwa insha Allah zan kira ka idan komai ya kammala." Sallama sukayi ya kashe wayar, ido muka had'a! naga fuskarsa ta rikice da zallar 'bacin rai! a gaskiya ban ta'ba tsammanin ina da kima a gurinsa ba. A marairaice nace"Don Allah ka bar maganar nan wallahi idan nice na yafe." Wani irin kallo yayi min kafin yace."Kada ki sake wannan maganar idan kina so mu zauna lafiya dake kiyi shuru da bakin ki Muddibo kashe ki yayi niyyar yayi kina tsammanin idan kin bar duniya zanyi rayuwa mai dadi? dole ne nabi kadin jinin daya zubar miki." Kallonsa na dinga yi ina mamakin maganarsa nace"Mutuwa dole ce a gurin ko wane musulmi koda Muddibo ya kasheni nayi shahada kuma na rataya a wuyansa sabida haka dan Allah ka daina wannan maganar. Ya jima yana kallona kafin yace."Ke! Sumayya bari nayi miki maganar k'arshe daga yau na 'yan taki kin zama mai 'yanci kuma insha Allahu a cikin satin nan za'a daura min aure dake! inaso ki zauna a k'arkashina cikin tsaro! dan na fahimci cewa ma'kiya zasu huce fushin su a kanki to zan aureki ki zauna a karkashina mu cigaba da rayuwa cikin inuwa daya. Cikin tsabar kad'uwa da firgici nake kallonsa, ya daga min hannu tare da fadin"Bana bukatar naji komai daga bakin ki na gama yanke hukunci." Mikewa yayi tare da fad'in "Tashi muje gida." Na mike jikina a mace! gaba yayi nabi bayansa ina mamaki abinda yake shirin faruwa da rayuwata, Yarima zai aure ni sabida ya ceci rayuwata! ko kuma dai zai aureni ne saboda ya biya bukatarsa a kaina kamar yanda ya kud'urta a can baya, wannan tunane tunane ne ya dameni a fakaice na dinga kallonsa ina so na karanci abinda ke cikin zuciyarsa. *Na kudi ne..* Kada ki karanta mun littafi idan baki biya ba, idan kina bukatar ki biya ga yanda abin yake....Vip gruop#600 normal gruop#300 account.. 0542382124.....Binta umar gtbank....idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta whsap da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:27 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 86 Duk yanda naso na karancin abinda ke cikin zuciyarsa kasawa nayi dan gabad'aya tunda muka shiga mota ya sanja fuskarsa ta rikid'e sosai tamkar wanda bai ta'ba dariya ba, na dinga satar kallonsa ina mamakin sauyawarsa, har muka shiga masarautar wata magana ta fatar baki bata had'ani dashi ba......"Mika'il Ka wuce damu can sashen Mahaifiyata." Da sauri na kalleshi, hankalinsa nakan direba yana bashi umarnin inda zai ajiyemu, Mika'i da sauri ya juya mota ya hau hanyar da zata sadamu da sashen mahaifiyar tashi......Alhamdullilahi naji yace kafin yasa hannu ya bude kofar motar, yana fitowa nima na fito kaf ma'aikatan dake gurin suka bar abinda sukeyi suka zo suna mika gaisuwarsu gurinsa, nayi mamaki sosai da ganin ya tsaya yana amsa musu, gaba yayi da sauri nabi bayansa, jama'ar gurin suka bi bayanmu da kallo domin dayawa daga cikinsu sun dauka ba zata dawo da rai da kafafunta ba saboda yanda aka fita da ita jina-jina da jini. Tana zaune kan kilishi da carbi a hannunta muka shiga falo tare da sallama a bakin mu. zamanta ta gyara ta amsa sallamar tare da tsira mana ido fuskarta kadai ta isa ta nuna mana cewar taji dadin ganinmu, cikin sanyi jiki nake tafiya kaina a kasa, dan shi har ya karasa kusa da ita ya zauna suna gaisawa, gurfana nayi a gabanta kawai naji ta janyoni ta rungume kam a jikinta sai saukar hawayenta naji a bayana, kawai naji nima zuciyata ta karye hawaye ya dinga kokarin kwace min. Cikin rarrashi yace."Mamma dan Allah ki daina kuka ai gatanan da ranta bata mutu ba kamar yanda Muddobu yayi niyyar kasheta." buka Da sauri ta kalleshi tana mamakin furucinsa. kansa ya daga mata yana so ya tabbatar mata da gaskiyar maganarsa, A sanyaye ta dago ni tana kallon fuskata, cikin alhini ta dora hannunta saman raunin dake goshi na murya na rawa tace"Sannu kinji ko."? kaina na daga mata cikin kokarin danne damuwata nace"Mamma ki kwantar da hankalin ki insha Allahu babu wani abu da zai sake faruwa dani dukkanin mai nufin mu da sharri zai koma kansa." Ajiyar zuciya ta sauke tace"Sumayya jiya da kyar na iya bacci saboda wannan tashin hankalin daya faru, shin wai su waye sukayi kokarin halakar dake ne."? Shuru nayi tare da sunkuyar da kaina kasa Ta daga kai tana kallonsa domin karin bayani, yace."Mamma kamar yanda na fada miki da farko hakane Muddobo shi kadai ya nemi ya halakar da ita kawai saboda taki bin umarninsa. Cike da mamaki mai tsanani tace"Ni kuwa wannan al'amarin ya bani mamaki mutuka sumayya me muddibo yake so kiyi masa kika gaza har ya kai matakin daukar dutsen wuta ya buga miki. Murya na rawa na shiga fada mata dukkanin abinda ya faru......Mamma kuka take sosai tana girgiza kanta, gabad'ayan mu hankalinmu ya tashi muka dinga rarrashinta, da kyar tayi shuru ta rike hannuna kam! "Sumayya ke 'yar halak ce kuma kin cancanci komai a gurina hakika kina d'aya daga cikin mutane da ba zan ta'ba mantawa dasu ba a tarihin rayuwata, kina da gaskiya da amana kin rike amanar dana baki duk rintsi kina kokarin kare lafiyar gudan jinina ni kuwa me zanyi miki a duniya wanda zai birgeki." ta karasa maganar tana rintse hannuna da nata.....mirmushi nayi a sanyaye nace"Ranki ya dade wallahi banyi wannan aikin domin ki biyani ba, duk abinda nakeyi akan Yarima inayi ne saboda Allah da manzon sa, Mamma wallahi bana bukatar komai a gurinki..........Mirmushi tayi tana kallona tace"Sumayya babu macan data dace da Babana sai ke ina rokon alfarma a gurinki dan Allah ki aureshi domin ki cigaba da kula dashi." Kaina na sunkuyar gabana na faduwa naji yace."Mamma ki kwantar da hankalinki dama nima hukuncin dana yanke kenan zan aureta saboda kyawun halinta da kuma tsayayyarta akaina sannan kuma zan aureta ne domin ganin ta k'ubuta daga gurin masu farautar ta, tunda duk iya kokari sunyi domun suga bayana Allah be nufa ba wannan dalilin yasa suka dawo kanta tunda itace garkuwata to idan suka kasheta suna ganin bukatarsu zata biya a kaina." ajiyar zuciya ya sauke kafin ya cigaba da cewa" Mamma na riga na yanke hukunci akan Muddibo sai dai duk abinda zai faru ya faru na shedawa Acp dukkanin abinda ke faruwa kuma ya tabbatar min da cewa zasuje su kamashi a gurin aikinsa, dole sai tabbatar mana da gaskiyar lamari." Fulani shuru tayi tana nisawa kafin tace"Babana ba zan hanaka ka dauki mataki akan wannan lamari ba, idan ya kasance da saka hannu Muddibo cikin faruwar wannan al'amari to duk matakin da hukuma zata dauka a kansa daidai ne saboda haka yanzu zan sa aje fada a sanar da mahaifinka cewa yazo shida 'yan uwan nasa a zauna ayi magana." girgiza kansa yayi yace."Hakan yayi yana da kyau kowa ya sheda cewa Muddibo shine wake d'aya a cikinmu ke Sumayya ki nutsu sosai duk wani abu da kika san ya faru to kiyi bayani yanda kowa zai fahimta, kaina na daga gabana na wani irin faduwa. Fulani wayarta ta dauka ta kira jakadiyarta tace maza taje fada ta sanar da Maimartaba tana da magana dashi da 'yan uwansa su Waziri.'' Jakadiya da sauri ta amsa ta mike ta fita. Ya kalli mahaifiyar tasa a nutse yace."Mamma inaso Yarinyar nan ta zauna a gurinki bana bukatar ta sake koma sashen su har abada ta bar gurin sai dai taje da niyyar gaishe da iyayenta. Murmushi tayi tace"Babana babu damuwa Sumayya zata zauna a gurina har zuwa lokacin da za'a daura muku aure.''' Yace."To nagode kwarai da gaske Mammana." Falon ne yayi shuru kowa na sa'ke-sa'ke a zuciyarsa, ni dai gabad'aya hankalina a tashe yake ina tsoron abinda zai faru idan jama'a suka sheda cewa Muddibo shine yake farautar d'an uwansa shin idan kowa ya yarda da maganata iyayensa zasu yarda kuwa? wace irin fahinta zasuyi min......shigowarsu falon yasa hankalina ya dawo daidai lokaci guda na shiga nutsuwata kaina a kasa, na gaishesu, Maimartaba ya dinga kallona yana girgiza kansa, a nutse ya kalli yaron nasa da fadin"Ina fatan yarinyar nan bata hadu da wata matsala ba."? Yace."Ranka ya dade Allah ya kiyaye bata samu rauni mai muni ba amma hakika wanda ya aikata mata wannan mugun abu ranta yaso ya d'auka.'' Waziri yace."Subahannallahi! wai shin ke Sumayya ya akayi al'amarin nan ya faru dake muna so kiyi mana bayanin komai." Mamma tace"Eh shine ai yasa na tura nace kuzo dukkaninku dan mu tuntuni tayi mana bayani kuma mun gamsu mun yarda da cewar yarinyar nan ba zata 'kir'kiri karya domin ta d'orawa wani sharri ba, a gaskiya idan kukaji wanda ya aikata mata wannan mugun abu sai kunyi mamaki amma inaso kafin ta fara bayani maimartaba ya bada umarnin kiran iyalan 'yan uwansa." Maimartaba yace."Fulani maganarki tayi ma'ana yana da kyau Huwaila na gurin nan yana da kyau Hajiya Karima na gurin nan yana kuma da kyau ace Hajia Kubra da Falmata na gurin nan domin kowa yaji bayanin da wannan yarinya za tayi." Gabad'ayansu suka amince da maganarta, da sauri ta kira Jakadiyarta tace maza taje ko wane sashe tace maimartaba nada bukatar ganinsu domin tattauna muhimiyyar magana." Jakadiya da sauri ta tafi cika umarni. Shuru falon yayi bayan kowa ya hallara, Maimartaba ya kalleni a nutse yace."Sumayya dukkaninmu ke muke saurare muna bukatar muji komai daga gurinki." Ajiyar zuciya na sauke a hankali na dago kaina sai naga dukkaninsu sun zuba min ido yanayinsu ya nuna min cewa ni suke saurare. Kaina na sunkuyar cikin nutsuwa na fara magana.......................'Karya kike munafuka."!! Hajiya Karima ce ta katseni tana wani irin huci! ta mike tsaye tana nuna ni da hannu 'Karya kike algumguma! kice Muddibo shine wake d'aya 'bata gari! a masarauta me Magajin sarki yayi wa Muddibo da zai kasheshi."!?? Maimartaba ya buga mata tsawa! Mijinta Ciroma shine ya zaunar da ita gumi! sai karyo masa yake, Hajiya Karima ta koma ta zauna tana muzurai idanunta sunyi jajawur saboda tsananin tashin hankali. Sai da kowa ya samu nutsuwa tukkuna maimartaba ya umarceni dana cigaba da maganata, Na cigaba da cewa"Ranka ya dad'e na rantse da wanda raina yake a hannunsa wannan maganar dana fad'a ba karya bace Muddibo shine ya tareni cikin dare bayan fitowa ta daga sashen Yarima, ya umarceni dana kar'bi magani lallai yana so na zubawa Yarima a lemo ya kuma tabbatar min da cewa mutukar na sake lalata musu aikinsu akan Yarima to sai ya kasheni, koda na kar'bi maganin a hannunsa sai na kwance na watsa masa shi a fuskarsa, na tabbatar masa da cewa ni ba za'a hada baki dani akashe mai rai ba! kafin nayi wani yunkuri ya dauki wani dutsen wuta dake gurin ya tad'e kafafuna na fadi a gurin kawai ya dinga buga min a kaina ina karewa , sawun mutane yasa ya jefar da dutsen ya bar gurin......to tun daga sannan ban san inda kaina yake ba." Maimartaba yayi shuru yana girgiza kansa gabadaya yanayin fuskarsa ta sauya da zallan 'bacin rai! Ya kalleni a nutse yace."Sumayya koda ba kiyi rantsuwa da Allah da mazon sa ba, na tabbatar da cewa ba zaki zauna ki shirya wannan maganar ba, Tabbas ni na amince da maganarki Muddibo zai iya aikata wannan abu saboda wata manufa tashi." Ya kalli su Waziri da duk fuskokinsu suka nuna alamun alhini da tashin hankali mussaman Ciroma da duk ya muzanta a gurin sai gumi yake idanunsa sun kada sunyi jajawur saboda tashin hankali! Maimartaba yace."Inaso gabad'ayan ku ku amince da maganar yarinyar kada wanda ya saka kokwanto a cikinta yarinyar nan Sumayya ni na amince da cewa ba za tayi wa muddibo k'arya ba sannan kuma inaso dukkaninnku ku kauda kanku akan irin hukuncin da zan yanke a kansa mutukar hukuma ta tabbatar mana da gaskiyar magana a kansa." Hajiya Karima ta fashe da kuka mai tsanani! tace"Ranka ya dad'e ka tsaya ka nisa tukkuna kayi binkice akan wannan al'amari wallahi na tabbatar Muddibo ba zai aikata wannan mummunan akin ba a duniya me magajin sarki yayi masa da zai kashe shi, ranka ya dad'e ka duba maganata." Maimartaba yace."Karima ki kwantar da hankalinki kamar yanda Magajin sarki ya sheda mana cewa yanzu haka Muddibo na hannun hukuma to ba zamu yanke hukunci ba sai mun tabbatar da gaskiya kan maganar saboda haka ki daina kuka kina tashin hankalinki dole Masarauta ta nuna fushinta akan abinda ya aikata. Da bakin zaninta ta fyace hanci ta kalli Magajin sarki murya na rawa tace"Ali dan Allah kayi hakuri da wannan al'amari kada fa ka manta Muddibo dan uwanka ne tare kuka taso kuna kaunar junanku idan binkice ya tabbatar da gaskiya a kansa to ka yafe masa abinda ya aikata maka. Yace."Hajiya kiyi hakuri wallahi idan ni Muddobo ya bugawa dutse ya fitar min da jini zan k'yaleshi saboda dangatakar dake tsakanina dashi, amma ki sani ba zan iya hakurin ganin ya zubarwa da wannan baiwar Allah jini na kyaleshi ba haki'kanin gaskiya sai nabi kadin jininta." Falon yayi shuru kowa yana mamakin maganarsa, ya kalli mahaifinsa a nutse yace."Ranka ya dade wannan yarinya sumayya nayi alkawarin aureta a cikin satin nan nake so a daura min aure da ita inaso gabadayan ku kusa min albarka a cikin aurena da ita." Maimartaba da Waziri fuskarsu ta fad'ad'a da farin ciki suka dinga fatan alkairi a ciki, Ciroma da Galadima kadarah kadahan sukayi magana akai, ita kuwa Hajiya Karima tashin hankali biyu ne ya had'e mata Yarima zai auri baiwa kafin ya auri 'yarta sannan yasa an d'aure mata gudan jininta Muddibo! rai a mugun 'bace! ta mike ta fita, dukkaninsu suka bita da kallo suna girgiza kai......Hajiya Huwaila da yake tana da wayo da siyasa kwata kwata bata nuna wani alamun da zai nuna cewa bakinsu daya da Muddibo ba, cikin nuna farin ciki takeyin fatan alkairi kafin ta tafi........Ciroma kuwa ya jima yana jajanta al'amarin kafin ya mayar da komai ba komai ba a zahiri kenan a bad'ini kuwa shi kad'ai yasan abinda ya kudirta, ya kalli Magajin sarki da fad'in "Inayi maka fatan alkairi a rayuwarka ina kuma baka hakuri a bisa wannan abu da ya faru da kai da dan uwanka sannan kuma inaso na jaddada muku cewa duk wani mataki da hukuma zata dauka akan Muddibo bana bakin ciki da hakan mutukar binkice ya tabbatar mana da gaskiya to ina mutukar farin ciki da umarnin da maimartaba zai yanke a kansa." Maimartaba ya dafa kad'arsa cikin taushin murya yace."Inaso ka kwantar da hankalinka akan wannan abu insha Allahu hukuncin da zamu d'auka akan Muddibo zai zama izina ga masu mugun hali irin nashi. Muddibo na ofis d'insa sakatarensa ya shiga ya sheda masa cewa yana da baki, kai tsaye yace ya shigo dasu, koda yayi tozali da Acp da sauran jami'ai sai yaji tsoro amma da yake 'kwaro ne sai ya dake! ya nuna musu gurin zama da fadin"Bisimillahi ku zauna." Acp ya girgiza kansa da fadin"Ba zama ne ya kawo mu ba, munzo domin mu tafi dakai." Cike da mamaki yake kallonsa kafin yayi murmushin gadara yace."Akan wane dalili zaku tafi dani Acp me na aikata.'' Acp ya murtuke fuskarsa yace."Muddibo ka aikata mummunan ayyuka ciki kuwa har da yun'kuri kisa." Muddibo gabansa na bugawa yace."Acp wannan wace irin banzar magana ce? mikewa yayi tsaye cikin hayaniya ce "ku fitar min daga ofis." Acp ya gyara tsayuwarsa da murmushi a fuskarsa yace."Wannan hargagin da kake da yanayin yanda fuskarka ta nuna ya tabbatar mana da cewa kaine ka aikata abinda muke zarginka dashi." Muddibo zufa! na keto masa yace."Wai shin Acp wane irin sharri kuke so ku laqaba min ne? wa na kashe da kuke zargina da aikata ta'addanci irin wannan."? Acp ya kalleshi sosai yace."Kayi yunkurin kashe baiwar gidanku wato sumayya saboda ta'ki kar'bar umarninka."! Muddubo zabura! yayi yana nunashi da yatsa baki na rawa yace."Acp ka kiyaye harshenka ka daina jifana da wannan munanan kalaman." Acp ya kalli na kusa dashi cikin bada umarni yace."Ka daure masa hannu muje station idan yaji mazga! zaiyi mana bayani." Da sauri suka nufeshi, muddibo ya dinga zare ido jikinsa na kyarma gumi! na keto masa, yau shi za'a daurewa hannu!!! yana dan mulki dan sarauta kafin ya ankara yaga sun kamo hannunsa duk biyun ya dinga fizgewa suka rike da kyau suka daura masa ankwa. Acp yazo ya cire hular dake saman kansa ya ajiye, botiran rigarsa ya cire yace."Ku fita dashi." Muddobo turjewa ya shiga yi bakinsa na rawa yace."Acp ni zaka ciwa mutunci a gurin aikina.''? Acp yace."Kaga Muddibo bani da wata magana da kai muje station kawai dukkanin bayanai suna can. Muddibo yace."Babu inda zanje wallahi." yafada yana turjewa, Acp wani bahagon mari! ya kwada masa! hancinsa ya fashe ya fara d'igar jini! a harzuke! yace."Muddobo bana san gardama muje station kawai." Muddibo idanunsa sukayi jajawur ya dinga kallon acp din yana mamakin marin daya kwada masa! Acp cikin wata irin tsawa! yace."ba za ka tafi ashe sai na kwance blet kenan."? cikin tsantsar takaici da tashin hankali ya soma tafiya, jami'an suka rirrike kafad'unsa, a haka suka fito daga ofis d'in, cikin tashin hankali jama'ar dake zaune a reception din suka mike tsaye suna kallonsu har suka fita, wasu daga cikinsu har bakin mota suka rakosu, sai da suka ga motar police din ta fita daga ma'aikatar sannan suka koma ciki suna mamakin abinda yake faruwa.......... *Na kudi ne* Kada ki karanta min littafi sai kin biya kudi...keda kika futa da littafin keda Allah! idan kina so ki biya ga yanda abin yake....vip gruop#600 normal gruop#300 account... 0542382124...binta umar gtbank...idan kati zaki turo..#400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number. *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:27 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 87 Acp suna isa station yasa aka rufe Muddibo a cell ofis d'insa ya shiga ya zauna a kan kujera yana godewa Allah. Hakika samun nasarar dam'ke Muddibo babbar nasara ce a tare dasu, wayarsa ya dauka cikin nutsuwa ya nemi number Magajin sarki ya kirashi ya sheda masa cewa Muddibo na hannu a halin da ake ciki, a nasa 'bangaran ajiyar zuciya ya sauke yace."Alhmdullhi Acp gani nan zuwa insha Allah." Sallama sukayi ya kashe wayar yana kallon mahaifiyarsa, yace."Mamma ni zanje station domin ina bukatar naji komai a daga bakinsa, Tace."To babu damuwa babana Allah ya tsare.'' yunkurin mikewa yay ya kalleni da fadin"Idan kinci abincin rana kisha magani kinji ko." kaina na daga, cikin sauri ya fice daga falon, ajiyar zuciya na sauke ina kallon 'kasan gurin, gabadaya hankalina yana kan iyayena su kawai nake da bukatar gani...."Sumayya kina bukatar hutu saboda haka bari na kira jakadiya tayi miki jagora daki ki kwanta ki samu nutsuwa." Jin abinda tace yasa naji kamar na fad'a mata abinda ke damuna, shuru nayi ina jin nauyin fad'a mata, wayarta ta dauka ta kira Jakadiya, ta shigo da sauri tare da gurfana a gabanta, tace"Jakadiya kuje da Sumayya wancan dakin dake kusa da gurin cin abinci ki gyara dakin sosai idan da akwai abinda ake bukata sai kiyi min magana." Jakadiya tace"To ranki ya dade.'' Ta kalleni cikin kauna tace"Sumayya tashi kuje kinji ko kiyi wanka ki gasa jikin ki kafin ki kwanta ki huta." Yun'kurawa nayi domin tashi nace"Ranki ya dade godiya nake Allah ya kara girma." mirmushi kawai tayi min ta cigaba da kallona har muka shiga dakin. Komai Jakadiya ta nuna min yanda zanyi amfani dashi a toilet din, ta fito ta barni ina wanka cikin sanyin jiki, har yanzu fargabar abinda zai faru a gaba nakeyi yanda naga mahaifiyar Muddibo na kuka yasa gabadaya jikina ya mutu. Koda na fito daga toilet din samun kan gadon nayi da kayan sawa sabbi a d'inke cikin wata leda, atampopi da lesuka masu kyau da tsada sabbi kar dan kallo daya nayi musu na tabbatar da cewa ba wanda ya ta'ba amfani dasu, hannuna ne ya sauka kan wata leda, nayi saurin zazzageta sai naga wanduna dasu breziya na dudduba kayan sosai ina mamakin al'amarin! Jikina na shirya tsaf, na sauke ledojin kayan kasa, juyawa nayi ina kallon makeken gadon da yaji shimfid'u na alfarma, ko a mafarki banta'ba tunanin zan kwanta a irinsa ba, nasa hannu ina shafa lallausan zanin gadon da yake yad'e da bargo da wasu irin pillows masu ban sha'awa! lumshe idona nayi a hankali na kwanta rigingine a gadon ina tunanin halin rayuwa. 'Bangaran Magajin sarki kuwa yana fita mota ya shiga direba yaja kai tsaye station suka nufa amma kafin su isa sai da ya kira Shatima a waya yace."Idan bashi da aiki ya sameshi a bomfai wato headquarter 'yan sanda gabad'aya, Shatima cikin mamaki yace."Ina fata dai lafiya." ajiyar zuciya ya sauke yace."Kai dai kawai kazo idan baka da aiki za kayi mamakin abinda ke faruwa." Shatima yace."Okey to shikkenan bani da aiki da yawa a ofis insha Allah nan da minti ashirin zaka ganni." Yace."Okey to babu damuwa." Sallama sukayi da juna ya kashe wayarsa ya cigaba da kallon hanya. Acp da magajin sarki suna ofis suna tattauna maganar Shatima ya iso kai tsaye Acp yace a bude masa kofa ya shigo, cikin nutsuwa ya shiga ya samesu a zaune kafin ya zauna sai da ya basu hannu suka gaisa tukkuna ya nemi kujera ya zauna yana kallonsu. Acp waya ya dauka domin bada umarnin shigowa da Muddibo......Magajin sarki ya kalli Shatima cikin yanayin alhini da damuwa yace."Shatima ka jima kana kawo min 'korafi akan Muddibo ina gwasale ka, ashe kana da gaskiya kawai kana bari ne saboda a zauna lafiya, Shatima a yau Allah buwayi ya tonawa Muddibo asiri kowa ya gane cewa shine ke aikata 'barna mai muni a cikin masarautar mu.'' Shatima hularsa ya cire yasa hankici saman goshinsa ya goge gumi, girgiza kansa yayi yace."Dama ni nasan dole watarana asirinsa ya tonu Wallahi dukkanin wani abu da zanzo na fada maka akan Muddibo gaskiya ne ba wai dan na had'aka dashi bane, aa inaso ka kiyaye dashi, to sai dai kuma a duk sanda zanzo nace maka Kada ka yarda da Muddibo ta kowace siga kai kuma baka daukar maganar da muhimanci dan a wasu lokotan idan nayi maka maganarsa ka gwasale ni raina yakan 'baci ina daurewa ne kawai, amma yanzu alhamdullahi nagode Allah daya ganar da kai gaskiya, shi kuma Muddibo naji dadi sosai da Allah ya toni asirinsa, Acp kuyi binkice sosai a kansa na tabbatar da cewa yasan komai akan mace-macen da aka dingayi a masarauta." Acp yace."Kada ka damu Shatima zamuyi binkice sosai akan wannan al'amari." Dukkaninsu kofa suka tsirawa ido, jami'ai biyu suka shigo dashi ofis din, ganinsu a zaune yasa yaji wani iri a tare dashi 'boye razanarsa yayi ya tsaya hannu daure da ankwa......Acp ya zagayo hannunsa rike da key ya kwance masa hannun, kana ya nuna masa gurin zama, jami'an dake tsaye gaisuwa suka mika a gaggauce suka fita daga ofis d'in." Magajin sarki da Shatima kallonsa kawai sukeyi suna mamakin sauyawarsa lokaci guda ya zabge yayi rama tsabar fargaba da rashin gaskiya, gashi dan tijara Acp yasa an cire masa tufafi daga shi sai Singlet da gajeran wando. Acp ya koma gurin zamansa tare da tsira masa ido yace."Muddibo dani da 'yan uwanka guda biyu muna so ka gaya mana gaskiyar abunda yake faruwa, kada kayi mana gardama da jayayya zakasha wuya hukuma na bukatar kayi mata cikakken bayani akan yunkurin kashe Sumayya da kayi sannan kuma hukuma naso kayi mata cikakken bayani akan wane nau'in magani ne kace Sumayya ta zubawa Yarima a lemo kuma ka tabbatar mata da cewa idan ta sa'ba umarninka sai ka kasheta."!!!!!!! Muddibo kallon acp yake bakinsa sai rawa yake yi yace."Wato Acp ba zaka daina yi min qazafi ba ko? yanzu ku dan Allah kun yarda da cewa zan iya kisa."!!! dukkaninsu suka kalleshi suna girgiza kai. Ya cigaba da cewa"Shatima Yarima ni dan uwanku na jini amma kun bada goyon bayan aci zarafi na ashe ba zuwa kukayi ku tafi dani ba yanayin fuskokin ku ya nuna min da cewa kun yarda da wannan 'kazafin da akayi min."! Magajin sarki ya girgiza kansa ko ka dan bai tausaya masa ba sai ma mugun haushinsa da ya tokare masa a kirji, yace."Muddibo ni dan uwanka ne amma kuma kullum cikin bibiyar rayuwata kake, a zahiri kana nuna min kauna a bad'ini kuma kai kadai kasan irin 'kiyayyar da kake min, wai shin dan Allah mai nayi maka ne."? Cikin rawar mirya yace." Ya za'ayi na'ki ka Ali ka tuna fa tare muka taso in banda ka tafi america karatu babu abinda ke rabamu komai tare muke gabatarwa shak'uwar dake tsakanina da kai har tafi wacce ke tsakaninka da Shatima to kan wane dalili zan kashe ka me kayi min da zan dinga bibiyar ka." Shatima yace."Dalilai suna dayawa Muddibo ni nasan waye kai tinda Ali tafiya yay ya barni tare da kai tsayin shekaru masu yawa, na sanka nasan kuma kan abinda yasa kake kokarin halakar da d'an uwanka, Muddibo ba zan za'bi Ali na barka ba dukkaninku d'aya kuke a gurina duk kuma wanda yayi kuskure sai nayi masa magana, a tun lokacin da naga kana da damun kanka akan sarauta da yanda kake zagin mai girma Maimartaba yasa gabadaya al'amarin ka ya fita daga raina saboda nasan mutukar akan mulki ne to babu abinda ba zaka aikataba kamar yanda ka fad'a cewa insha Allahu daka kan Maimartaba mulki sai ya dawo hannun zuriar ku, yasa na shiga kokwanto akanka saboda irin mugwaye kalaman da kakeyi akan zuriar sarki Abdul-aziz a wancan lokacin kayi furucin kisa ba d'aya ba biyu ba duk akan mulki Muddibo me yayi zafi? mecece duniyar kuma menene mulki da zaka d'aga hankalinka akai! har ka dinga d'aukar nauyin daya fi karfinka na tabbata kana da hannu a cikin wannan mace-macen da akeyi a masarauta! shiyasa gabadaya banyi mamaki ba dana ganka anan na tabbatar da cewa hakkin mutunan daka dauka ne yasa asirinka ya tonu." Muddibo cikin wani irin yanayi na nadama yace."Shatima kaine da kanka kake fadar wannan maganganun akaina? hakan ya nuna min cewa kana da bukatar hukuma ta cigaba da binkice na akan abinda ban aikata ba! ashe zumunci yace haka? Magajin sarki kada ka yarda da wannan tatsuniyar Shatima dama tuntuni yake adawa da sha'kuwar da take tsakanina dai kai 'karya yake min ni ban kasance azzalimi ba ballantana na zalince ka, Ali kayi wa maganar kyak.............Acp ya buga tevur! din gabansa cikin tsawa! yace."Ka rufe mana baki a gurin nan bama bukatar wannan soki burotson naka sahihiyar magana muke bukatar kayi mana idan kuma ka tsaya gardama da 'karyata masu gaskiya yanzu zansa aje ya zane maka jikinka idan kaji a jikinka za kayi bayani."!!! Muddobo bakinsa ne ya mutu murus! dan har yanzu bai manta da marin da yasha ba.....Acp ya mike daga gurin zamansa zagayowa yayi yaja kujera ya zauna yana fuskantarsa, fuska a murtuke yace."Kai nake saurare.'' Cikin inda-inda yace."Acp na fad'a maka wannan al'amarin 'kazaf........Kafin ya 'karasa ya bashi wani wawan mari! da bayan hannu! Muddibo jinsa da ganinsa ne suka dauke na hucin gadi! ya bude idanunsa da sukayi jajawur! dishi-dishi yake ganinsu, murya na rawa Yace."Ali Shatima kuna kallon cin zarafin da ake min kuna kallo ko.''? ko gezau babu wanda yayi..........Da 'karfi! Acp yayi magana, sai aka bud'e kofar ofis ne, jami'an d'azu ne suka shigo da sauri suka qame alamu gaisuwa, Yace."Soloman kuje dashi ku bashi kashi! idan yaji ajikinsa zai mana bayani." Da sauri suka nufeshi, Muddibo ya dinga daga hannunsa da fad'in "Kada ku ta'ba ni na fad'a muku ni nafi karfinku kuma wannan abinda kuke zargina dashi qazafi ne."!!!!!! Soloman ne ya buga masa kan bindiga a kansa cikin tsawa! yace." Mi'ke tsaye! Muddibo ya mike da sauri yana kallon 'yan uwansa dake zaune suna kallonsa, hannu yasa ya sharce gumin goshinsa, Soloman da dan uwansa suka tasa 'keyarsa......Bayan fitarsa da minti biyu Acp ya kallesu tare da fad'in" Nasan dukkanin ku ranku zaiyi rashin dadi a bisa abinda yake faruwa da d'an uwanku, wallahi kuyi hakuri banso mukayi haka dashi ba naso muyi komai cikin mutunci! amma taurin kansa ya janyo masa kask'anci na tabbata yanzu idan su Soloman suka dan bubbugeshi yaji wuya zaiyi mana bayani." Magajin sarki ya sauke ajiyar zuciya mai zafi yace."Acp ko kusa ko alama bana tausayawa Muddibo wallahi duk irin hukuncin daya kamata a dauka a kansa bai dame ni ba.'' Shatima yace."Nima sam be bani tausayi ba wallahi saboda nasan dashi ne ya samu dama akanmu abinda zaiyi sai yafi haka Acp ya bude baki kenan zaiyi magana, sukaji wani irin ihu!! Muddibo yaji bugu!! sai zunduma ihu! yake! Acp mikewa yayi ya fita ya barsu suna tattauna maganar.......kafin Acp ya isa gurin Middobo har ya suma! yace maza maza a yayyafa masa ruwa ya farfado, da sauri suka yayyafa masa ruwan sanyi a fuska. A firgice ya bude ido ya gansu a tsaye a kansa kowanne da k'atuwar gora! hannunsa fuskokinsu tamkar towon dawar daya kwana biyu! Had'a ido sukayi da Acp a take fitsari ya kufce masa bakinsa cike da jini yake kokarin magana, Acp ya tsuguna a gabansa yana kallonsa, yace."Yanzu zaka iya yi mana bayani ko a 'kara dukan"!! Muddibo shuru yayi kansa na kallon kasa sai zare ido yake, Acp ya kalli su Soloman dake tsaye suna jiran umarni yace."Ku cigaba da aikinku ina ganin dukan be isheshi ba.! Muddibo ya razana a firgice! ya daga hannuwa sama jikinsa na rawa yace.'' Kada ku dake ni zanyi bayani." Acp ya kalleshi tare da fadin "ka tabbata."? kansa ya daga hawayen nadama na zubo masa Mikewa yayi ya kallesu cikin bada umarni yace." Ku kawo shi ofis." yana gama maganarsa ya fice. A rirrike aka shiga dashi ofis din dan gabad'aya jikinsa ya saki bashi da karfi da kuzari ko kwabo tsabar duka da tashin hankali yasa duk kammaninsa suka sauya......Ali da Shatima suka dinga kallonsa ganin yanda duk kammaninsa ya sauya. Acp zama yayi a kujerar dake fuskantarsa, sai da ya tabbatar da cewa ya dan samu nutsuwa tukkuna yace."Muddibo kai muke saurare." Ofis din ya dauki shuru na 'yan mintina kafin Muddibo ya fara magana cikin rawar murya yake musu bayanin abinda ya dinga faruwa a masarautar shine mussababi dan dukkanin mace-macen da akayi shine sanadi duk yana aikata hakane dan bukatarsa ta biya akan d'an uwan nasa. Magajin sarki idanunsa sukayi jajawur! ya zubawa Muddibo ido yana mamakin al'amarin! shi kuwa Shatima sam bai damu ba saboda dama shi can yasan shine silar faruwar dukkaanin abinda yake faruwa. Acp kansa na kasa yana rubutu a kan wata doguwar takarda, ya kai minti goma yana rubuce rubuce a takardar kafin ya dago kansa, yace."Muddibo da kuma ka musanta zargin da ake maka ko zaka iya fada mana dalili."? Cikin nadama yace."Dole na musanta domin na kare kaina amma yanzu dana fahimci cewa asirina ya tonu ai gashi nan nayi maka bayani yanda ya kamata." Acp murmushi yayi ya cigaba da rubutunsa, bayan ya gama rubutun sai yayi magana da karfi tare da kiran Soloman, da sauri suka shigo. yace."Ku mayar dashi.'' da sauri suka nufeshi, suka mikar dashi tsaye, rirrikeshi sukayi zasu fita ya juyo yana kallon 'yan uwansa hawaye ne suka gangaro masa shikkenan kuma yasan tasa ta k'are a duniya yazo a banza zai koma a wofi! Acp ya nannad'e takardar hannunsa cikin nutsuwa yace."Ranka ya dad'e mu nan mun gama aikinmu insha Allahu ranar litinin mai zuwa zamu tura shi kuto domin al'kali ya yanke masa hukunci muna rokon Allah ya kiyaye gaba Allah ya tsare gabanka da bayanka dukkanin wani mai nufin ka da sharri muna rokon ubangiji Allah ya mayar dashi a kansa." Magajin sarki ya sauke ajiyar zuciya tare da bashi a hannu cikin mutunci yace." Acp nagode kwarai da gaske kaima ina rokon Allah ya daukaka akan aikinka Allah kuma ya kareka da dukkanin abin'ki." Acp na murmushi ya amsa da ameeen." Ya mikawa Shatima hannu sukayi sallama da juna, har bakin mota ya kai su bai kuma bar gurin ba sai da ya tabbatar da cewa motocinsu sun fita daga station din cikin k'oshin lafiya........ *Na kudi ne..!* Kada ki karanta min littafi idan baki biya baa, keda kika futa da book din keda Allah, idan kina so ki biya ga yanda abin yake....Vip group #600 normal gruop#300....account... 0542382124...Binta umar gtbank... idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min magana ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:28 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 88 Yini nayi a kwance ina baccin gajiya sai daf da la'asar daya shigo Mamma ke sheda masa cewa tun bayan fitarsa nake bacci ban tashi ba kai tsaye dakin ya shiga, ya sameta kudindine a cikin bargo tana bacci ya jima a tsaye a kanta yana kallonta tausayinta na ratsa masa jiki, a hankali ya zauna gefan gadon yasa hannu ya janye bargon data rufa dashi, tafin kafarta ya shiga shafawa yana kiran sunanta a hankali, cikin bacci naji tsigar jikina na tashi yayin da kafata ta dama keyi min kaikayi janye kafar nayi ina sake jan bargon, ya janyo ni da sauri yana kirana, da sauri na bude idona, nan na ganshi dab dani a zaune! da sauri na mike zaune ina gyara bargon jikina cikin dubara na gyara zanina daya tattare daga ciki.........Kallona yayi cikin sassauci yace."My lov ashe tunda na fita bacci kike baki tashi ba bare kici abinci kisha magani." Kaina na daga masa ba tare da nace masa komai ba, yace."Okey to yanzu ya kike jin yanayin jikin naki."? A hankali nace "Da sauki kaina ne kawai yake min ciwo.'' yace." Shima zai daina insha Allahu, kije maza kiyi brush sai kizo kici abinci ko."? A hankali na mi'ke ya rike hannuna da fad'in"Ko na taimaka miki ne? girgiza kaina nayi tare da kwace hannuna nayi gaba da sauri, to har na fito daga toilet din yana zaune a dakin, kai tsaye hijabi na duba cikin kayan dazu nasa a jikina na tsaya a kan dadduma domin gabatar da sallah, mikewa yayi ya fita daga dakin, ganin uku da rabi tayi yasa kawai na gabatar da sallahr la'asar na jima kan daddumar ina addua kafin na shafa a fuskata na mike a nutse da hijabin a jikina na fita daga dakin Babu kowa a katon falon sai jakadiya tana 'yan gyare-gyare gaisawa mukayi tace"Ranki ya dade ai yau kinsha bacci sosai da sosai." cikin mamaki nake kallonta jin irin sunan data kira ni dashi, mirmushi tayi tace"Ga abinci can a shirye idan kina bukata sai na kawo miki inda kike." Girgiza kaina kawai nayi ina kallonta nace"Ina Mamma."? da sauri tace"Ta shiga ciki domin tayi sallah." Shuru nayi ina kallon kasan gurin lallai zama da mad'aukin kanwa guy nan ya koya min sara bini bini sai kawai na kurawa kasa ido sai kace me neman wani abu nazari da tunani ne idan Sukayi wa mutum yawa yake sanyawa ma kayi abu baka san kanayi ba shi dai al'amarin ya zame masa jiki magana daya biyu zai yi k'asa da kansa ya jima yana nisawa. Muryarta naji ta doki kunnena."Ranki ya dade a tashi lafiya." da sauri nace"Jakadiya ki daina kirana da wannan suna yayi nauyi da yawa." Murmushi tayi tace."Beyi nauyi ba ranki ya dade ya dace dake domin kin cancanta lokaci kadan zaki zama matar Yarima mai jiran gado kinga kuwa ai sunan daya dace a kira ki dashi kenan." Shiru kawai nayi ina binta da kallo, tayi murmushi a nutse ta juya naga ta shige wani daki dake can k'urya nafi tunanin dakinta ne dan ganin yanda take shige da fice a dakin. Falon na shiga bi da kallo ko ina tsaf tsaf dashi sai kamshi yake iri-iri gabadaya ma na kasa bambamce kamshin da falon yake komai ya tsaru kayan al'ada iri iri a falon ban ta'ba tsammanin akwai ranar da zata zo na zauna a kan kujerar falon ba sai gashi cikin ikon Allah yau nice a hakimce a kan kujera cikin shigar suttura irin ta sarauta har da alkawarin aure a tsakanina da dan sarki! a gaskiya babu abinda yafi gaskiya da rikon amana dadi a duniya gaskiyata da rikon amanata sun janyo min alkairi na zama abin kallo abin mutuntawa da ganin daraja na tashi daga baiwa na dawo mai 'yanci! hummm! rayuwa kenan idan Allah ya kaddara aurena da Yarima a matsayina na baiwa yar gidan Lawi mai hidima da dawakai watarana ina iya haifar sarki! kadan daga cikin ikon Allah kenan! ajiyar zuciya na sauke mai zafin gaske nasa hannu ina share hawaye dake zubowa a kumatuna.......shigowarsa yasa nayi gaggawar sunkuyar da kaina kasa ina dubarar goge fuskata, kusa dani ya zauna yana nani'kata kujerar kuma mai cin mutun daya ce dik ya takure ni. Kasa dago kaina nayi na kalleshi saboda damuwa, idan da sabo yaci ace na saba da halayyarsa. Hannu yasa ya dago fuskata ya tsira min ido lokaci guda ya karancin yanayin da take ciki.....cikin tausasawa yace." Me akayi miku kike kuka? Kallonsa nayi ina kokarin bagarar da maganarsa nace"Wane irin kuka kuma yanayin bacci ne kawai a idona." "Kada ki raina min hankali mana na shigo na sameki kina goge hawaye amma ki karyata maganata bana so kiyi zaman takura idan nan beyi miki ba zaki iya komawa sashena ki zauna mutukar hankalin ki zai kwanta." Cike da mamaki nake kallonsa kafin nace"Na koma sashen ka na zauna akan wane dalili? wai kan dan Allah me yasa watarana baka tunani ne."? 'Bata rai yayi yace."Ni ne mara tunani."? girgiza kaina nayi nace"Allah ya baka hakuri ban fad'a maka maganar dan kaji haushi ba abinda ya dace nake so na nusasheka yanzu kawai ba'a daura mana aure ba sai na tare a sashenka me kake tunanin zai faru."? Shuru yayi yana kallona, na dauke kaina tare da matsawa daga jikinsa, sake matsowa yayi ya matseni a jikin kujera, murya na rawa nace"Dan darajar Allah kayi hakuri ka matsa kada Mamma ta fito ta same mu a haka." Ya matsa tare da fadin"Tunda kince Allah na matsa shikkenan ko .''? shuru nayi masa, yace."Kinci abincin dai."? kai na girgiza alamun aa. Yace."To tashi muje muci ko." Mikewa nayi ya mike tare da kokarin rike kuguna da sauri na kauce na bashi guri, mirmushi yayi kawai yayi gaba nabi bayansa ina mamakin shu'umancinsa. Muna zama gurin cin abincin ta fito daga dakinta jikinta nannad'e da lifaya da carbi madaidaici a hannunta, gani nayi ta saki fuskarta cikin wasa da dariya tace"Ango da amarya ne za suci abinci a tare." da sauri na sunkuyar da kaina kunya duk ta dabaibayeni.......tana kokarin zama gurin zamanta yace."Mamma na shigo na sameta ita kadai a zaune a falo tana share hawaye shine nake tambayarta dalili tace babu komai ni kuma na k'aryata tabbas nasan akwai abinda ke damunta take kuka. Cikin kulawa tace"Sumayya menene."? kasa cewa komai nayi gabadaya kunyarta nake ji, tace"Ki gama cin abincin kizo ki sheda min abinda ke damunki ni ba surukar ki bace mahaifiyarki ce." Nace"Mamma babu komai wallahi kin san na yini ina bacci shine dalilin da yasa fuskata ta sauya. Da sauri yace."Karya kike yi." shuru nayi tare da sunkuyar da kaina dan gabadaya bana san jayayya dashi. Tace."Ki gama cin abincin Jakadiya ta rakaki gurun iyayenki ku gaisa." wani irin sanyi ne naji ya ratsa zuciyata, yace."Mamma ni zan rakata." Tace"To hakan ma yafi ma'ana sai ku gaisa sosai ka k'ara sheda musu abinda keda akwai duk da nasan maimartaba ya shedawa mahaifinta abinda yake faruwa a tsakaninku." Yace."Babu damuwa insha Allahu zanyi musu bayani sosai wanda zai gamsar dasu nasan kuma zasuyi farin cikin da faruwar al'amarin." Cikin farin ciki nake cin abincin na saki jikina sosai muna hira dashi, Mamma dake can falo tana jinmu idan ya kama tasa baki a hirar tamu tasa bakinta ayi da ita, cikin fahintar juna muka kammala cin abincin yace."To maza dauko maganinki a daki." da sauri na mike naje na dauko maganin, kar'ba yayi ya fito dasu ya dinga bani daya bayan daya, sai da ya tabbatar nasha kowanne sannan ya umarce ni dana mayar da ledar maganin daki, ina ajiyewa na fito na sameshi a tsaye suna magana da mahaifiyarsa magana ce dai akan abinda ya faru yana fada mata cewa Muddibon ya fadi gaskiyar lamari yayi rocoding din komai so yake Maimartaba ya shigo da daddare sai ya kunna musu su saurara." Kaina a kasa nazo na wuce bakin kofa na nufa, ya biyo bayana, Mamma naji na fadin"Sumayya ki gaishe min da iyayen naki." Da sauri na juyo cikin ladabi nace"Insha Allahu zasuji." Nice na fara fita kafinsa, gabad'aya naga ana bani girma yanda ake gaisheshi cikin mutunci da daraja nima hake ake gaisheni, na dinga takure jikina cikin hijabi ina mamakin ikon Allah! Har muka isa gurinmu a takure nake saboda ganin yanda jamaa ke bin mu da kallo gami da girmamani! Hayaniyar mata na dinga ji a cikin gidan namu. kallonsa nayi shima ya kalleni, nace"Ko zaka tsaya na shiga na sheda masu zuwanka."? yace."Duk yanda kika ce haka za'ayi ranki ya dade.'' Cike da mamaki nake kallonsa jin irin sunan daya kira ni dashi. Yace."Meye kike kallona."? girgiza kaina nayi da mirmushi a fuskata na wuce cikin gidan, Tawagar mata na gani gurfane gaban Tambaya sai fadanci suke mata saboda abun al'karin daya sameta.....ina shiga Uwani ta mi'ke da sauri ta rangwad'a bud'a! da fad'in "Ga amaryar nan ma tazo." Gabad'ayansu suka mike tsaye Tambaya sai mirmushi take tana kallona! nima da murmushin a fuskata na shiga gaisawa dasu, suka dinga amsawa suna yi min fatan alkairi." Nace"Ku nutsu tare muke da Yarima yana waje a tsaye hayaniyar ku tasa ya tsaya." Gabad'ayansu suka shiga nutsuwarsu kowacce tasa takalminta domin tafiya.....Tambaya tace"Sumayya maza jeki shigo dashi, kin barshi a tsaye." nace"To." Tawagar matan dake gidan suka biyo bayana, ganinsa a tsaye yasa suka zube kowacce gwiwa a kasa take gaisheshi, na dinga mamakin yanda yake amsa musu a sake yace."Gabad'ayansu su tashi su tafi. da sauri suka mike suka wuce, sai da gurin ya samu nutsuwa tukkuna na kalleshi a sanyaye nace"Ka shigo amma Babana baya nan sai Tambaya kad'ai zanje na kira shi yanzu." Girgiza kansa yayi yace."Ki bari kawai idan na gaisa da mamanki sai munje can gurin aikin baban mu gaisa." nace"Ka bari dai na kira maka shi." Dan 'bata fuska yayi yace."Haka zaki tafi babu sucurity kina so makiya su ritsa ki ko."? 'Babu abinda zai same ni sai ikon Allah." girgiza kansa yayi yace."Ban yarda ba tare zamuje kome zai faru ya same mu a tare.'' wani irin kallo nake masa shima yana yi min nasa da yake mutukar kassara ni. a sanyaye nace"To muje ku gaisa da Tambayan." da hannu ya nuna min hanya ma'ana nayi gaba, bayana ya biyo muka shiga. Sosai nayi mamakin yanda ya zube gaban mahaifiyata yana gaisheta ita kanta Tambaya sai da abun ya bata mamaki ta dinga jin kunya da nauyi tana kauda kanta da barin kallonsa, addua kawai take mana tare da fatan alkairi a rayuwar auran da zamuyi, ya dinga amsawa cikin kulawa yana sake yi mata karin bayani akan al'amarin, ni dai shuru kawai nayi ina kallonsa ina mamakin sauyawarsa a kaina, lokaci guda na dinga jin wani irin masifaffan sonsa na ratsa ni yanda yake mutunta iyayena yafi komai dadi a gurina. Lawi yana tsaka da hidima da dawakai muka shiga gurin, da sauri ya cire hular malafar dake kansa sabida girmamawa, yana kokarin zubewa a kasa kawai yaga Yariman ya zube masa, jiki a sanye yace."Ranka ya dade tashi dan Allah bancanci wannan gaisuwar ba." Mirmushi yayi ya kalleshi da kulawa yace."Ka cancanci irinta tunda har ka haifa min matar rufin asiri." Lawi yaji hawaye na nema ya kufce masa! hannuwansa ya had'e guri guda yace "Godiya nake ranka ya dade." Cikin kulawa yace."Baba babu kalmar godiya a tsakanina daku dan haka ku daina akan Sumayya babu irin abinda ba zanyi ba, wannan yarinya jigoce a rayuwata nagode kwarai da irin tarbiyar da kuka bata" Lawi cikin farin ciki da alfahari ya d'ora hannunsa a saman kaina "Ubangiji Allah yayi miki albarka yarinyar arziki hakika haihuwarki babbar nasara ce a tare damu." hannuna na dora a kan nasa nace"Baba nima ina alfahari daku da kasantuwar ku a matsayin iyayena ko wane mataki na kai rayuwata kune sanadi kun kula dani kun tarbiyantar dani kun d'ora ni akan tur'ba mai kyau kun d'ora ni a kan hanya madaidaiciya babu abinda yake tsakanina daku a yanzu sai kyakkyawar addua ina rokon Allah yaja da ranku ya kuma kara muku lafiya mai amfani." Ya amsa da ameeen suma ameeen Yarinyar arziki Allah yasa albarka a rayuwarki da rayuwar auranki." ya kalli Yarima dake tsaye yana kallonmu yace."Ranka ya dade naji dadi kuma nayi alfahari dacewar zaka auri jinina a gaskiya nayi farin ciki kuma nayi addua sosai ina rokon ubangiji Allah ya sanya muku alkairi a zamantakewar auranku Allah ya kade fitina yasa anyi kenan ya kareku ga dukkanin sharrin abin'ki." Yarima cikin jin dadi ya dinga amsawa da ameeen ya Allah baba muna godiya sosai da sosai............Zuciyata tayi wasai! na dinga jin nutsuwa na ratsa jikina hakika yanzu na amince da cewa Yarima na sona tsakani da Allah yanda yake karrama iyayena yake mutuntasu yasa naji duk duniya bani da masoyi kamarsa ina mutukar kaunar iyayena shiyasa duk wanda ke mutuntasu nake ganin darajarsa Yanzu Yarima Ali ya samu kyakkyawan matsayi a cikin zuciyata Allah ne kad'ai yasan irin kaunar da nake masa. A dakin taro kowa ya hallara iyaye da 'ya'ya da jikokin masarautar kowa yana gurin, Magajin sarki ya fito da wayarsa a nitse ya kunna rocoding din muryar Muddibo ta fito rad'au!! vollom ya karo yanda kowa zaiji da kyau!! kowa ya shiru yana sauraran Muddibo yana jawabi akan abubuwan da ya dinga shiryawa a masarautar........Famliy din Ciroma suka cika gurin da kuka Hajiya Karima kasa tsayawa tayi ta gama saurara tana kuka na tashin hankali ta bar gurin, da daya bayan daya 'ya'yanta suka bi bayanta, Ciroma yana zaune a gurin bai tashi ba har sai da recoding din ya 'kare! Magajin sarki ya kashe wayarsa ya ajiye kusa dashi, a nitse ya sheda musu cewa"Ranar litinin za'a shiga kuto dashi domin al'kali ya yanke masa hukuncin daya dace dashi dan haka dik wanda yaga yana da ra'ayin zuwa sai ya shirya yaje." babu wanda ya nuna sha'awar zuwa a cikinsu Iyalin Uwar gida Huwaila irinsu aunty Safiyya suka dinga zare ido a gurin gaskiya sunji dadi sosai da Muddibo ya rufa musu asiri suma sunyi nasu sai dai kuma bai ka nasa muni ba!! Maimartaba yace kowa ya tafi gurinsa tunda gaskiya tayi halinta sai a jira hukuncin da al'kali zai yanke a kansa, jiki a sanyaye kowa ya fita daga gurin taron..........Ciroma na daf da shiga sashen sa ya yanke jiki ya fad'i!! Hadiman dake aikace aikace a gurin suka rufu a kansa suna ihu!!!! kafin kice kwabo tawagar 'ya'yansa dake cikin gidan sun fito, mazan ne suka daukeshi suka shiga dashi ciki dakinsa suka shiga dashi su kwantar dashi a gado sun kewaye shi suna yi masa firfita! Ciroma bakinsa ya murgud'e sai zubar da yawu yake! magana yake so yayi amma ya kasa, Hankalin iyalinsa ya tashi, Wali shine me bin Muddibo da sauri yace."Bari naje na kira Magajin sarki yazo ya dubashi." Hajiya Karima cikin tsawa! Tace."Wali ka sake ka kira Magajin sarki ya shigo sashen nan sai na d'aga maka nono wallahi sai na tsine maka albarka."!!! Khalisat tace."To Yanzu hajiya muna ji muna gani zamu barshi ya mutu i duba da ki ga yanda yake haki! jininsa ne ya hau da karfi." Cikin karaji!! Lawisa tace"Khalisat ba za'a kira Yarima ba ai bashi kad'ai ne likita a duniya ba! saboda haka kawai kai Wali ku daukeshi kusa a mota mu nufi babban asibiti a dubashi." Wali yace." me zai hana a kira Dr Sa'adu ya dubashi a gida."? Hajiya karima tace"Aa shawarar Lawisa zamu dauka ku daukeshi kusa a mota muje babban asibiti." Manniru yayi saurin fita domin bada umarnin fito da mota... *Na kudi ne!* Kada ki karanta min littafi sai kin biya! keda kika futa da book din keda Allah! idan kina so ki biya ga yanda abin yake.....Vip group #600 normal group #300....account... 0542382124....Binta umar gtbank....idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:28 PM - ???: *SADAUKAWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 89 Sai bayan fitarsu daga gidan tukkuna Maimartaba ya samu labarin abinda ke faruwa ransa ya 'baci sosai da abinda iyalin d'an uwansa suka zartar ba tare da saninsa ba, ace akwai babban likita a gida amma su daukeshi su kaishi wani asibiti domin su nunawa duniya halin da suke ciki, sosai ya dinga jajanta al'amarin a cikin zuciyarsa, Waziri ganin yanda ya damu da a'lamarin yasa ya dinga tausar sa da kalamai masu sanyi Sarki ya dan samu sassauci a zuciyarsa sakamakon rarrashinsa da 'yan uwansa ke masa amma dai duk da haka zuciyarsa na can tunanin halin da Ciroma yake ciki dalilin da yasa kenan gari na waye wa suka shirya zuwa asibitin domin duba jikin nasa. Yanda suka tarar dashi cikin halin ciwo ya firgitasu dan gabadaya komai na jikin Ciroma ya daina aiki yana kwance sai dai ayi masa komai, Likitan dake tsaye a kansa ya sheda musu ciwar jininsa ne ya hau sosai sanadiyar tashin hankalin daya shiga amma insha Allah zai cigaba da kwanciya a asibiti su kuma zasu cigaba da kula dashi har ya samu lafiya." Maimartaba girgiza kansa kawai yayi yana mamakin kudirar ubangiji Tabbas ya yarda da cewa d'an adam ba'a bakin komai yake ba duba dai lafiya lau suka yini da Ciroma amma lokaci guda Allah ya sauya masa hallita, babu shakka idan suka rasa dan uwansu ta sanadiyar bacin ran Muddibo ba zasu yafe masa ba........Umartar Wali yayi akan ya kira Magajin sarki a waya ya sheda masa cewa ya turo motar asibitinsa tazo ta dauki Ciroman yana ganin kamar haka yafi mutunci. Hajiya Karima ita da zuriar ta babu yanda suka iya suna ji suna gani Magajin sarki ya turo da mota a kasa Mara lafiyan a ciki a ka tafi dashi asibitin, Tsabar bacin rai yasa hajiya Karima buge zaninta ta koma gida tare da fadin"Ba zata zauna zaman jinya ba mutukar ba sanja wa mijinta asibiti ba. Maimartaba yace kowa ya kyaleta! dama asibitin basa bukatar 'yan jinya akwai ma'aikatan da suka san aikinsu sai kawai ya basu umarnin tafiya gida bayan ya kwantar musu da hankali akan rashin lafiyar mahaifin nasu............Koda suka koma cikin tsananin damuwa suka samu mahaifiyar tasu sai zubar da hawaye take, Lawisa da khalisat suka zauna suna taya ta kukan. abun duniya ya taru yayi musu yawa Muddibo ya jefa su a cikin tsaka mai wuya ga rayuwar mahaifinsu na tangal tangal.....Hajiya karima hawayenta ta share ta kalli 'ya'yanta cikin rawar murya tace"Yanzu haka zaku zauna ku zuba min ido ina kuka kuna kuka ba zamu zauna mu nemawa kanmu mafita ba." Wali yace."Hajiya wace irin mafita kike so mu nemawa kanmu? duk fa abinda kika ga ya faru to da sanin Allah saboda haka dan ki kada kice zaki dauki fansa saboda nasan halinki da ri'ko! Muddibo shine ya janyowa kansa masifa muma gashinan ya jefa mu a cikinta a yau da kwanan mahaifinmu ya kare da tuni sai dai labari." A harkuqe! tace"Dallah malami rufe min baki mai matacciyar zuciya! ayiwa dan uwanka sharri amma ka dinga cewa shine ya janyowa kansa wato kana nufin kaima ka yarda da sharrin da'aka liqa masa." Cike da mamaki! yake kallonta kafin yace."Hajiya dan Allah ki nutsu ki shiga hankali ki daina wannan abinda kikeyi mutane zasu dauka kin samu ta'bin hankali! wannan fa al'amarin da gaske ne Muddibo ne ya aikata ba sharri akeyi masa Kin saurari muryarsa a lokacin da yake shedawa hukuma gaskiyar lamari amma saboda san zuciya kina cewa sharri a kayi masa." Lawisa na kuka tace"A gaskiya Yaya Wali ka bani mamaki wallahi wato kai ba zaka iya rufa asirin dan uwanka ba ko kenan yanzu ranar litinin din ba zakaje kuto ka bada sheda a kansa ba." Dafe kansa yayi cikin tsantsar damuwa yace."Wace irin sheda zan bayar a kansa bayan da bakinsa ya fadi gaskiyar magana, dole zanje kuto domin jin irin hukuncin da sharia zata yanke a kansa." Munniru yace."Ni wallahi na rasa ma abinda keyi min dadi a rayuwata nayi nadama nayi dana sani dana fito a cikin wannan masarauta gabad'aya bamu da power a masarautar nan komai mune a baya ai dole 'bacin rai yasa hawan jini ya kama babanmu. Hajiya Karima ta share hawaye cikin takaici tace"Ai Munniru ba kuga komai ba a yanda babanku yake bani labarin yanda mahaifinsa yasha wuya a cikin masarautar nan sai kunyi mamaki mutuka! zuri'ar Abdullahi Adamu ta riga ta kwace sarauta ta kafa kanta ta hana kowa ya kar'ba daga hannunta ni wallahi har yanzu banga laifin Muddibo ba dan yayi yunk'urin kwatar hakkinsa, bari na fad'a muku abinda baku sani ba zuri'ar Abdullahi Adamu sune suka kashe kakanku da bakin ciki sai wayar gari akayi da gawarsa ya mutu da bakin ciki! Munniru ya buga bango(garu) da hannunsa yana huci! yace."Tur! da zuria'r Abdullahi Adamu wallahi sun kasance azzalimai masu san kansu da yawa meye amfanin mu a masarautar nan da mu zauna muna ganin bacin rai a gwara mu tattara kayanmu mu fita daga cikinta.. Wali yace."Baka da hankali ko Munniru idan mun bar masarauta kana inda zakaje."? shuru yayi yana huci! Wali ya cigaba da cewa"Ka nutsu ka zauna kayi tunani malam komai kaga na faruwa to da yardar Allah idan Yayi nufin mulki ya cigaba da tabbata a hannun zuri'ar Abdullahi Adamu to babu yanda zamuyi idan kuma yayi niyyar k'wace mulkinsa ya kwace ya dawo dashi hannunmu kuma abunda nake so kuyi la'akari dashi anan shine Waziri da Galadima me yasa basa tayar da hankalinsu akan mu! kada ku manta suma fa suna da hakki amma sunyi shiru sun zubawa sarautar Allah ido ba wai dan basa sha'awar mulkin ba dukkaninsu suna so suna sha'awa sai dai babu yanda za suyi da abinda Allah ya hukunta saboda haka dan Allah kuma inaso ku hakura ku barwa Allah ikonsa kuma insha Allah idan baba ya samu sauki zan zauna na fahimtar dashi cewa shi mulki na Allah ne sai wanda ya za'ba yake bawa ba'a yiwa Allah dole akan ikonsa kowane irin hukunci ya zartar daidai ne." Jikinsu ne yayi sanyi da nasihar da d'an uwan nasu, da alama dai duk cikinsu shine mai kyakkyawar zuciya tunda gashi nan ya zaunar dasu yana nuna musu abinda ya dace Ubangiji Allah yasa zasu dauki nasiharsa su hakura su barwa Allah ikon sa. Bayan kwana biyu jikin Ciroma yayi sauki dan Magajin sarki ya tsaya a kansa sosai da sosai ya bashi dukkanin kulawar da ake bukata, alhamdullhi yanzu an samu yana iya sarrafa hannuwansa sai dai har yanzu idan yana magana ba'a fahimta sosai saboda yanda bakinsa ya karkace yana zubar da yawu....Ganin yanda hankali Maimartaba ya tashi akan hakan yasa ya zauna sosai ya kwantar masa da hankali yace."Insha Allah zai samu sauki ya dawo normal kamar yanda yake, jin haka yasa Maimartaba da 'yan uwansa hankalinsh ya kwanta, Suma su Lawisa suka kwantar da hankalinsu dan ganin yanda jikin mahaifin nasu yayi sauki sai dai har yayi kwana hudu a asibiti Hajiya Karima ba taje ba tana nan har yanzu da mugun nufi a cikin zuciyarta, cikin masarautar babu wanda bai je ya duba Ciroma ba amma ita da take a matsayin matarsa uwar 'ya'yansa ba taje ba tana zaune a gida tana sa'ka mugun abu a cikin zuciyarta. *RANAR LITININ* Kuto ta cika ma'kil da jama'a ana ta gabatar da shari'a yanda addinin musulunci ya tanada mai girma mai shari'a malam Umaru Musa ya d'auki takardar dake gabansa a nutse yake duba takardar yana girgiza kai! farin gilashin dake idonsa ya zare a nutse yace." Insha Allahu zamu kamanta adalci kuma zamu yankewa mai laifi hukuncin da addinin musulunci ya tanada muna rokon Allah yasa hakan ya zama izina ga masu hali irin na *Al'amin AbdulJabbar wanda akafi sani da Muddibo* Hukuncin da addinin musulunci ya tanadarwa dukkanin wani musulmin daya aikata kisa yana sane to shima akashe shi! Alhamdullahi wanda ake zargi da aikata laifin kashe masu rai guda uku ya amsa laifinsa ba tare daya wahalar da sharia ba saboda haka kuto tana bukatar ta saurari muryar wannan yaro a lokacin da yake wa hukuma bayanin yanda akayi yake aikata wannan 'barna kuto da jama'ar dake cikinta na bukatar su saurari jawabin da yayi domin kowa ya tabbatar da hukuncin da zamu yanke a kansa daidai yake da addinin musulunci." Da sauri wani dan sanda dake tsaye a gefe ya dauko wayarsa a take ya kunna rocoding din da Acp yayi wa Muddibo a lokacin da yake jawabi a ofis dinsa......tun kafin rocoding din ya kare gurin ya kaure da haniya kowa na fadar albarkacin bakinsa, Muddibo dake tsaye gurin tsayuwar masu laifi ya sunkuyar da kansa zufa sai keto masa take hakika bai ta'ba nadamar rayuwa ba sai yau, jama'a sai zaginsa suke suna ala wadai dashi.......Wali da Muniru sai girgiza kai sukeyi suma tamkar su fashe da kuka su kad'ai ne suka iya halartar kuto Hajiya Karima dasu Lawisa suna gida suna kuka saboda jikinsu ya riga yayi sanyi da jin irin kotu'n da'aka kai Muddibon kotun musulunci ce tsantsa kowa yasan Malam Umaru Musa tsayayyan al'kali ne wanda yake yanke hukunci akan doron gaskiya Kudi ko mulki na mutum basu isa susa shi ya kauce hanya ba komai muqamin mutum mutukar yayi laifi baya d'aga 'kafa sai zartar da hukuncin da addinin musulunci ya tanada Maigirma mai shari'a ya bada umarnin akan cewa kotu ta samu nutsuwa, nan take kowa ya nutsu gurin yayi tsit! A nutse ya cigaba da cewa''Saboda haka kuto zata yankewa Al'amin Abduljabbar hukuncin kisa kamar yanda ya kashe shima za'a kashe shi!! ta hanyar rataya."!! yana gama maganarsa ya buga tevur din gabansa da wani d'an katako! hukunci ya tabbata da izinin Allah! mikewa yayi gabad'aya jama'a suka mi'ke suna kiran sunan Allah. "Allahu Akbar! Allahu Akbar! Allahu! akbar!! 'Yan sanda kusan hudu suka kewaye Muddibo a rirrike a ka fito dashi yana kuka yana d'agawa su Wali hannu aka fita dashi y'an jarida da jamaa suka bi bayansu.......Wali da Munniru rungume juna sukayi suna kuka Wali yace." Munniru kaga irin rayuwar da nake gudu ko ka duba ka gani yanda Muddibo zaiyi mutuwar wulakanci jama'a sai tsine masa suke saboda mugun abunda suka aikata, dan Allah Munniru komai rintsi ka rike gaskiya kada kabi san zuciyarka irin na Muddibo." Munniru hawaye kawai yake sharewa yana girgiza kansa tabbas duniya abar tsoro ce shikkenan yanzu sunyi bankwana da dan uwansu. *Allah kasa mufi karfin zuk'atan mu amin.* Hajiya Karima faduwa tayi ta suma lokacin da ta samu labarin hukuncin da ya sauka akan d'anta koda ta farfado ma sambatun surutai ta dinga yi tamkar wata mara hankali sai alwashi take ci akan wallahi ba zata yarda ba sai ta dauki fansa! Wali ya rungumeta a jikinsa yana mata addua yana share hawaye.........A ranar Maimartaba kasa zaman fada yayi saboda tashin hankali yaje ya kwanta a sashen Fulani yana tunanin rayuwa......Magajin Sarki da Shatima yini sukayi cikin alhini da damuwa amma daga baya da suka zauna sukayi tunani sai suka ga hukuncin da mai shari'a ya zartar akan Muddibo shine daidai hausawa na cewa da kunyar lahira gwara ta duniya watakila hakan na iya janyowa Allah ya gafarta masa zunubansa, saboda haka sai dukkaninsu suka kwantar da hankalinsu su tsananta addua akan Allah yasa haka shine yafi alkairi a rayuwar d'an uwan nasu.... *Na kudi ne* Kada ki karanta min littafi ba tare da kin biya ba! keda kika futa da littafin keda Allah! idan kina bukatar biya ga yanda abin yake......Vip gruop#600 normal gruop#300 account number... 0542382124....Binta umar gtbank....idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:28 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 90 Masarauta da jama'ar dake cikinta sun jima cikin alhini da damuwar abinda ya faru. mussaman 'bangarar Uwargida Huwaila ita da zuri'arta babu wanda ya kaisu shiga tashin hankali dan ganin irin hukuncin da ya sauka akan Muddibo duk sai suka tsorata kowacce ta shiga nutsuwarta dan saboda sun san koda sune suka aikata abu makamanci na Muddibo baza su tsira ba, sosai uwargida da iyalinta suke godiya ga Allah da bai nufi Muddibo ya kiran sunan d'aya daga cikinsu ba! wannan dalilin yasa kowacce ta nemi guri ta zauna a dakinta yanzu ba sosai ma suke zuwa masarautar ba saboda gudun kada asirinsu ya tonu..........Alhamdulillahi jikin Ciroma yayi sauki sosai dan yana iya komai da hannayensa sannan yana tafiya da kafafunsa sai dai rashin kuzari da bai dashi amma ya samu lafiya sosai Magajin sarki ya tabbatar musu da cewa zai warware idan an kwana biyu, Satin sa uku a asibiti ya dawo gida, duk irin kulawar da Magajin sarki keyi akan Ciroma baya burge Hajiya Karima kullum cikin zaginsa take tana kwashe masa albarka da fad'in "Yanda yayi sanadin mutuwar d'anta itama sai tayi sanadin mutuwarsa........duk sanda tayi wannan furucin sai Wali yayi mata nasiha harzuqa takeyi ta rufeshi da fad'a haka yake fita ya barta ransa a 'bace! bangaran Lawisa kuma ta dan samu sassauci kuma ta rage jin haushinsa tunda yayi sanadiyar samun lafiyar mahaifinta amma da itama ta k'ullaceshi a zuciyarta saboda yayi sanadin mutuwar dan uwanta! gabadaya idonsu ya rufe sam basa hango laifin Muddobo su dai suna nan akan bakansu na cewa sharri akayi masa, duk sanda zasuyi wannan furucin Wali hauka yake d'ora musu ya bar musu gurin dan takaici!! Ya lura Lawisa halinsu d'aya da mahaifiyarsu amma Munniru da Khalisat idan yayi musu magana suna ji kuma sun daina zagin Zuri'ar Maimartaba suna zaune lafiya da kowa a masarautar..............To Sati na uku a b'angaran Fulani gabad'aya na sanja fatar jikinta ta washe na 'kara qiba! su kansu sutturun da nake amfani dasu a jikina abin kallo da sha'awa ne duk wasu kayan kyale kyale da 'kawa na sarauta Mamma tasa an kawo min ina amfani dasu, kullum cikin ado da kwalliya nake na fito na zauna kusa da ita muyi ta hira Fulani wayayyiyar macace ta saki jikinta dani yanda na lura gabadaya bata suruktaka dani dan watarana ma idan nayi ado da irin kayan sarautar itace ke gyara min sai taga yayi daidai sannan hankalinta zai kwanta, a tsayin satikan da nayi a gurinta na koyi abubuwa da yawa na sarauta dana yau da gobe, sannan kuma sa'i da lokaci na kanje na gaisa da iyayena cikin walwala da farin ciki..............Cikin nutsuwa na fito daga daki na sameta a inda ta saba zama domin hutawa, kusa da ita na zaune a nutse nace"Mamma barka da hutawa." da murmushi a fuskarta tace"Barka kadai Sumayya yau kin wuni kina bacci baki fito da wuri." Murmushi nayi ina wasa da hannayena nace"Wallahi kuwa ni kaina nayi mamakin baccin da nayi sai da nayi tunanin ko maganin murar dana sha ne ya kashe min jiki." Tace"Eh kwarai kuwa hakan zata iya kasancewa." Shuru nayi kaina a kasa kusan kullum idan inaso naje na duba mahaifana nakan ji kunyar fada mata, kwata-kwata bana so taga rashin kunyata. Murmushi tayi tace"Sumayya kina so kije ku gaisa da iyayenki ko."? murmushi nayi tare dayin kasa da kaina. zamanta ta gyara tana murmushi tace"Ai duk sanda kike so kije gaishe da iyayenki ina ganewa na rasa me yasa kike jin kunyata Sumayya." 'Yar dariya nayi nace"Mamma kece Allah yayi miki kwarjini shiyasa nake kasa fada miki.' Yar dariya tayi tace."Kwarjini har na kai ki sumayya."? da sauri na kalleta, ta daga min kanta tare da fadin"Gaskiya da rikon amanarki suna burgeki sumayya inaso ki sake dam'ke gaskiya hannu biyu duk rintsi kada ki kauce hanya ki tsaya akan gaskiyarki." Nace"Insha Allahu zan kula da maganarki.' Tace."Babu damuwa kina iya zuwa ku gaisa amma kada ki tafi ke kadai kuje tare da mutum biyu." nace"To shikkenan." Ina kokarin mikewa ta shigo falon, kallo daya nayi mata naji gabana ya fadi, hajiya Karima ce! Mamma tace"Sannu da zuwa hajiya yau kece a gurina." Cikin ya'ke tace"Fulani kenan ai kin san komai da dalili.'' guri ta nema ta zauna! na dan risina a nutse nace"Barka da yamma ranki ya dade." Wani banzan kallo tayi min kafin ta ta'be baki ciki-ciki ta amsa min. A sanyaye nace"Mamma sai na dawo." da sauri tace"To sumayya ki gaishe min dasu da kyau." Nace"Insha Allahu zasuji." Hajiya Karima bin ta tayi da ido tana girgiza kanta, sauke ajiyar zuciya tayi bayan fitarta tace"Fulani gurinki nazo." Mamma ta gyara zamanta sosai tana fuskantarta tace"Ai dama tunda na ganki nasan da akwai magana Hajiya Allah yasa alkairi ne yake tafe dake." Hajiya Karima gyara yanayin fuskarta tayi tace"Magana ce akan Lawisa naga tunda ake maganar auran nan banji ana saka sunanta ba idan Ali ya fasa auranta ina bukatar karin bayani. Cike da mamaki take kallonta kafin tace"Hajiya Karima wannan wace irin magana ce haka? a gaskiya banji dadi ba in banda abinki ya za'ayi Babana ya fasa auran 'Yar uwarsa." Murmushin takaici tayi tace."Haba Fulani ai dole nayi zargin hakan saboda ganin gabadaya an daina zance Lawisa sai na wannan baiwar akeyi ai dole dukkaninmu muyi tunanin ko baiwa tafi 'yar sarauta." Mamma ta girgiza kanta tana kallonta tace"Hajiya Karima dan Allah ki dinga gyara maganarki ya za'ayi kina babba ki dinga sakin maganganun da basu dace ba, wannan yarinyar Sumayya tuntuni ta 'yantu ta shigo cikinmu dan Allah ki daina irin wannan maganganun basu da dadi. Tace"Sumayya ta 'yantu amma kuma bata gaji sarauta ba ko.''? Fulani ta kalleta takaici kamar ya kasheta, Hajiya Karima ta cigaba da cewa" Wannan yarinya Sumayya sam bata dace da Ali ba saboda gabanta da bayanta bayi ne mak'as'kanta, wallahi ni rasa wace jaraba Ali ya hango a jikinta ." "Nagarta da kyawun hali babana ya hango a tare da ita shiyasa yayi sha'awar auranta, Kin san mazan da suke da wayo a yanzu sun daina duba so ko nasaba a aure nagarta da tarbiya suke dubawa kafin su auri mace wanda yanzu samun irin masu nagartar yarinyar nan zaiyi wahala sosai." Tsaki taja tace"Duk da haka dai Masarauta nada al'ada a tarihin masarautar nan banta'ba jin wanda ya auri baiwarsa ba sai Ali ina ganin kamar zai barwa zuri'arsa abin magana." Fulani tayi dariya tana kallonta tace"Babu wani abin magana da zai barwa iyalinsa, baiwa itama mutum ce kamar sauran mutane kuma idan Allah ya kaddara auran Babana da wannan yarinya rabo ya shiga tsakaninsu sai kiga ta haifi Sarki duk da take baiwa ma'kaskanciya babu ruwan ubangiji. Da sauri hajiya Karima tace"Bana fatan nayi tsawan ran da zanga wannan rana dan lalacewa ace d'an baiwa shine zaiyi mulki tunda nake banta'ba ganin wannan kwamacalar ba." Fulani ranta ya 'baci sosai ta rasa me yasa matar take da izgilanci rayuwar duniya a sannu ake bin ta na sama yana iya dawowa kasa na kasa ya hau sama, mutukar sarki ya auri baiwa ya 'yantata to idan ta haihu d'anta yana da gadon sarauta tunda dan sarki ne gabad'aya basu san mecece sarauta ba babu shakka koda mulki aka basu to ba zasu iya aikata komai ba sai shashanci! Ajiyar zuciya ta sauke tace"Hajiya Karima magana ta 'kare kije ki kwantar da hankali insha Allahu Babana zai auri Lawisa kamar yanda ya dauki alkawari tun farko." Ta mike tana gyara lullu'binta tace"To yanzu naji kinyi magana mai kyau ni zan koma gurina." Fulani ta bita da kallo har ta fita daga falon, girgiza kanta tayi tana mamakin halin matar kwata kwata bata da dad'in sha'ani gashi duk maganar da tazo bakinta fad'a take bata taunawa. Yau Yarima bai dawo gida da wuri ba hankalinmu duka ya tashi, Mamma ta kalleni a nutse tace"Ko zaki kira shi da wayarki ina ganin idan ya fad'a mana halin da yake ciki sai hankalinmu yafi kwanciya.'' Cikin nauyi nace"To shikkenan bari na dauko wayar a daki." a nutse na mike........Zama nayi gefan gado da wayar a hannuna number shi na kira sai da ta kusa katsewa tukkuna ya dauka, ajiyar zuciya na sauke a nutse nace"Ranka ya dade barka da dare." "Barka dai." ya amsa a takaice, nace"Muna nan hankalin mu duk ya tashi baka dawo da wuri ba ina fata lafiya." Zazzafar ajiyar zuciya ya sauke yace."Sumayya ina da marasa lafiya ne mata biyu ne zasu haihu haihuwar tazo da tangard'a yanzu shirye-shiryen shiga dasu dakin teatar ake." A sanyaye nace"Allah sarki wallahi har naji tausayinsu Ubangiji Allah ya sauke su lafiya." Ya amsa da "ameen ya rabbi ki bani Mammana mu gaisa." da sauri na mike da wayar a hannu na sameta zaune a inda take. A sanyaye nace"Mamma gashi na sameshi a wayar." da sauri ta kar'ba tasa a kunnanta tana kiran sunansa. Yace."Mamma Allah yayi miki albarka yasa ki gama da duniya lafiya." ta amsa da "ameen babana yana jika wani iri Allah yasa kana lafiya." a sanyaye yace."Lafiya ba lau ba mamma yau na shiga rud'ani mutuka! da sauri tace"Subahanallahi me ya faru da kai."? ajiyar zuciya ya sauke yace."Wallahi Mamma wasu mata biyu ne zasu haihuwa sai wuya suke sha haihuwar ta'ki zuwa daga 'karshe ma sai al'amarin ya rikice suka dinga jijjiga duk sun fita daga hayyacinsu Mamma ashe haka kuke shan wuya gurin haihuwa."? Cikin damuwa tace"Allah sarki! to Ubangiji Allah ya sauke su lafiya babana dan Allah duk wani taimako daka san suna bukata kayi musu Allah zai baka lada." Yace."Insha Allahu zanyi iyakacin bakin kokarina akansu dan yanzu na bada umarnin shiga dasu dakin teatar ina ganin haka shine maslaha domin kuwa idan mun tsaya mun jinkirta to ana iya rasa rayukan su.'' A sanyaye tace"Babana Allah yasa ku shiga a sa'a Allah ya tashi kafad'unsu ya sauke su lafiya." Ya amsa da "ameeen ya Allah insha Allahu komai dare zan shigo gida idan naga aiki yayi kyau." Tace"To shikkenan ubana Allah ya bada nasara." sallama sukayi jikinsu duk a sanyaye. Haka muka cigaba da zama a falon muna jajanta al'amarin dan ni kaina da ban ta'ba haihuwa ba ban kuma san yaya zafinta yake ba na tausayawa musu saboda wahalar da suke sha, har misalin goma da rabi na dare bai shigo ba, alamun bacci na gani a idonta a nutse nace"Mamma kije ki kwanta ki huta naga kamar kina jin bacci insha Allahu zai dawo lafiya." Tace"Wallahi kuwa bacci ne a idona Sumayya nafi so dai na zauna ya dawo naji lafiyar matan nan sun tsaya min a raina wallahi." Nace"Nima haka Mamma addua zamuyi Allah ya rabasu lafiya insha Allah idan ya shigo komai dare zan tasheki amma yana da kyau kije ki kwanta tunda bacci kikeji kada yasa miki wani ciwon.'' Na fadi hakane domin na kwantar mata da hankali amma bana tsammanin idan ya shigo na tashe ta a bacci da safe sa gaisa......Yunkuri mikewa tayi na mike nima tare da gyara mata nad'in lifayar jikina, hannunta na rike muka shiga bedroom d'inta, gefan gado ta zauna nace"Bari na hada miki ruwan wanka.'' hannunta ta rike da fadin"Sumayya bana jin zanyi wankan nan dazu da yamma nayi kayan bacci zaki dauko min." da sauri nace"To tare da nufar wardrobe dinta, riga da wando masu taushi na dauko mata da hularsu da takalminsu na ajiye kusa da ita ta kalleni tace"Allah yayi miki albarka." kaina a kasa nace"ameeen Mamma." tace"Kina shan wannan maganin dana baki ko."? cikin jin kunya nace"Eh." tace"Idan sun 'kare koda kin tare a d'akinki ki fad'a min nasa a kawo miki wasu na fad'a miki ni ba surukarki bace kada kiji kunyata." Ina wasa da hannuwana nace"To shikkenan Mamma." tace"Kije ki kwanta kema da safe ma gaisa dashi Allah ya dawo mana dashi lafiya." Na amsa da ameeen tare da fadin"Sai da safe." Tace"Allah ya tashe mu lafiya." Koda na shiga dakina na jima a zaune ina tunanin rayuwa kafin nayi wanka na kimtsa jikina cikin kayan bacci riga mai hannun shima da wandonta iya gwiwa kayan masu tsantsine shiyasa suka kwanta a jikina, hula nasa a kaina har naja bargo sai kuma na cire sauke kafafuna nayi kasa a nutse na janyo drowar dake gefan gadon, magungunan na shiga fitowa dasu, tunda ta bani su tace na dinga sha kullum banta'ba shaba duk da nasan amfaninsu a tartare dani........Ajiyar zuciya na sauke a nutse na bud'e zumar itace tafi daukar hankalina bakin jarkar nasa a bakina nasha sosai na cire ina dan ya mutse fuskata gabadaya babu zaqi irin na zuma sai kadan bakina ya game da baurin magani, tsigar jikina ta dinga tashi, d'aya bayan d'aya na dinga daukar magungunan inasha ina rintse ido sai dana sha kowanne sannan na had'a maganin nasa a drowar na rufe, brush naje nayi na dawo na kwanta tare da rufe idanawana, waya ta na bari a kunne nasan mybe idan ya shigo ya kira ni sai na ajiyeta a kusa dani kawai......bacci ne yake nema ya dauke ni ina korarsa har dai ya samu nasarar sace ni 'na bingire bacci mai nauyi ya daukeni na dinga wani irin mafarkai marasa dadi........Can cikin baccina naji nauyi a kaina, a razane na bude ido ina kiran sunan Allah, da yake ban kashe hasken dakin ba yasa na gane wanene, da sauri nasa hannuwa na tureshi jikina sai 'bari yake! shima jikinsa na kyarma ya sake qamqame ni yana fitar da wani irin numfashi, a jigace nace"Wai meye haka ne."? muryarsa na dan rawa yace."Sumayya bana cikin nutsuwa ta ina cikin damuwa." jikina ya mutu nace"Ina fata ka samu nasara a gurin aikin ka."? matseni yayi sosai a jikinsa Yace."Na samu dukkaninsu anyi musu aiki lafiya lau amma d'aya yaron data haifa ya mutu." jikina yayi sanyi nace"Allah sarki Allah ya bata lafiya Ubangiji Allah ya bata wani." da sauri ya tashi daga kaina yana kallona, na mike zaune tare da kare jikina da bargo ido na zura masa naga duk ya rame! yace."Baki da hankali kike mata irin wannan fatan taci wuya irin wannan sai ta sake haihuwa." Cike da mamakin maganarsa nace"To meye a ciki ai ba'a kanta a kafara ba kuma ko wace haihuwa da irinta mybe gaba ba zata sha wuya ba." Girgiza kansa yayi yace."Wannan ba tsari bane ace kullum rayuwar ki na cikin wahala tara 'ya'ya ba alfanu bane mutukar mace nashan wuya a gurin haihuwa sai ta 'kayyad'e ta." Na dinga kallonsa ina mamakin maganarsa "Tara 'ya'ya shine bai da alfanu."? 'kwarai kuwa mutukar gurin daukar cikinsu da haihuwarsu na barazana da rayuwarki to gwara ki hakura.'' cikin takaici nace" Mace koda haihuwa ko babu haihuwa sai ta mutu! kuma inaso kasani duk macan data mutu gurin haihuwa tayi shahada saboda haka ka daina wannan maganar dik wata wahala mai shigewa ce iyayenmu da kakannin mu a haka duk suka tara 'ya'yansu dan haka dan Allah ka daina wannan maganar sam bata dace ba su 'ya'ya rahama ne sannan kuma a ranar lahira Annabi Muhammad (SAW) zaiyi alfahiri da jama'arsa......... *Na kudi ne.* Kada ki karanta min littafi sai kin biya ni! Keda da kika futa da littafin keda Allah! idan kina so ki biya ga yanda abin yake....Vip gruop#600 normal gruop#300....account... 0542382124....Binta umar gtbank....idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:28 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 91 Har yanzu fuskarsa babu sassauci yace."Nasan da haka ba sai kinyi min wa'azi ba a tsarina ni bana son tarin 'ya'ya da yawa bayan haka kuma ita haihuwar wahala gareta mutanan da dana yanzu ba daya bane nada sunfi kwari da karko na yanzu kuwa haihuwa daya biyu sun lalace shiyasa bana son ki haihu da yawa." Murmushin takaici nayi nace"Ni kam wannan magana ta isheni wallahi duk yanda nake so na fahimtar dake yanda al'amarin yake ba zaka fahinta ba saboda haka mu bar maganar iya adadin 'ya'yan da zan haifa a duniya Allah ne kadai yasan yawan su." Shuru yayi yana kallona, babu alamun nadama a fuskarsa na dinga mamakin halinsa bashi da rufi ko kadan duk abinda yake zuciyarsa fada yake yi kansa tsaye in banda abinsa waye yake gudun rahama ai 'ya'ya rahama ne amma shi tun kafin ma yayi auran ya yankewa kansa hukunci Allah dai yasa kada zama da turawa yasa ya dauki munanan dabi'unsa dan gashi alamu nan." Kaina na sunkuyar ganin yana kure ni da kallo nace"Ka tafi gurinka dan Allah ko da akwai abinda kake bukata." Ajiyar zuciya ya sauke yace."Ina bukatar abubuwa guda uku amma nasan da wuya na samu duka. Kallonsa nayi ya daga min kai da fadin"farko dai ina bukatar naji ki a jikina na biyu ina bukatar abinci na uku kuma nayi wanka." 'Bata fuska nayi nace"Tashi muje falo na baka abincin." girgiza kansa yayi yace."Kije ki kawo min nan ni babu wani falo da zanje." na jima ina kallonsa kafin nayi yun'kurin mikewa sai na tuna da kayan dake jikina da sauri na koma na zauna gabana na faduwa. Bargon dake jikina yake kokarin janyewa na rike da kyau ina girgiza masa kaina nace"Dan Allah dauko min hijabina gashi can akan kujera. Cike da mamaki yace."Lallai kin raina ni zaki aika."? girgiza kaina nayi yace."Dallah tashi ni ki kawo min abinci me zaki boye min bayan komai nawa ne." Idona ne ya kawo ruwa nace"Ni dai dan Allah ka miko min hijabin wallahi kayan masu fitar da tsaraici ne." kallona ya shigayi yana girgiza kai yace."Tsaraici.''? kaina na sunkuyar ina sake rufe jikina da bargon, mikewa tsaye yayi kawai yasa hannu da karfi ya fizge bargon daga jikina, tsigar jikina ta mike da sauri na takure jikina guri guda ina watsa masa harara! Wani irin kallo yake bina dashi tun ba kirjina ba nasa hannu ina karewa, ajiyar zuciya ya sauke a hard'e yace."Tashi." 'kin tashi nayi na takure jikina hawayen bakin ciki na nema ya kufce min......"Kin san Allah idan baki tashi ba zan aikata miki abinda bakya so yanzu." jin abinda yace yasa da sauri na kalleshi, gani nayi idanunsa ya sauya, gabana na faduwa na mike, ya bini da wani irin kallo da hannu ya nuna min k'ofar fita, ina takure jikina na kama hanyar fita a jikina naji kallona yake shiyasa da saurin gaske na bude kofa na fita.......a gurguje nake hada masa abincin kawai naji motsinsa a bayana, da sauri na juyo kirjina da nasa ya had'u hannuwansa duka ya d'ora akan mazaunaina! ya wani matseni a kirjinsa yana matsa min mazaunai! kirjinsa na doka da karfi! tsaki naja da sauri na janye jikina, bina yake da kallo kamar maye, nayi gaggawar daukar tire din dana shirya masa abincin na barshi a tsaye a gurin. Ina ajiye tire din na dauki dogon hijabina nasa na zauna kan kujera gabadaya raina ya 'baci da irin abinda yake min. Koda ya shigo dakin be kalli inda nake ba, yaje ya zauna gaban abincin a nutse ya zuba abinsa ya fara ci, sai da ya kammala tsaf ya tashi ya nufi toilet........jin shuru bai fito ba yasa na shiga tunanin abinda yake a ciki, motsinsa naji nayi saurin kallon kofar toilet din daga shi sai gajeran wando da vest jikinsa ya nuna alamun ruwa wanka yayi, kallonsa nake har ya isa kan gadona ya kwanta hankalinsa kwance ya rufe jikinsa da bargona.......Nace"Bangane ba." shuru yayi min.......nace"kasan bai dace ba ko dan Allah ka tashi ka tafi gurina hakan bai dace ba." "Sumayya bazan tafi ba yau anan nayi niyyar kwanciya idan kuma kina da karfi kizo ki fitar dani." nace"Wacece ni ranka ya dade Allah ya baka hakuri." mikewa nayi na kama hanyar fita gwara na bar masa dakin akan mu kwana tare nasan halinsa zai iya haike min. Kawai na ganshi a gabana ido jawur na kalleshi! bai tanka min ba ya murza key a jikin kofar ya zare keyi din ya barni a tsaye! Hawayen takaici suka zubo min, a gaskiya lamarinsa akwai wuyar sha'ani! juyawa nayi naga ya koma ya kwanta tare da lullube jikinsa da bargo. Jiki a sanyaye naje na kwanta kan sofa ina kudindine jikina da hijabina, miryarsa naji ciki ciki yace."Ki zo ki kwanta ba zanyi miki wani abuba." Share shi nayi ina jin wani irin haushinsa a raina, magana yake min nayi masa banza daya gaji sai yayi shuru can kuma na dinga jin saukar numfashinsa a hankali nan na gane bacci ya daukeshi, a hankali na gyara kwanciyata ina addua a cikin zuciyata. Da asubah kusan a tare muka tashi dan ina jin motsin shigarsa toilet na bude ido, zaune na mike ina salati can naji kira ya shigo wayarsa, a nutse na mike na iske inda wayar take, lokacin kiran ya katse wani ya shigo, ina kokarin daukar wayar ya fito daga toilet din jikinsa sanye da kayansa na jiya daya cire da alwala a tare dashi, a nutse na mika masa wayar na nufi toilet domin daura alwala, koda na fito samunsa nayi zaune a gefan gado ya rufe fuskarsa da tafukan hannayensa, gabana ya fadi! da sauri na karasa kusa dashi tare da fadin"Lafiya."? Fuskarsa ya bude yana kallona da jajeyen idanunsa yace."Sumayya daya daga cikin matan da nayi wa operation ce ta mutu misalin uku da rabi na dare. Kafafuna suka shiga kyarma zama nayi kusa dashi ina kiran innalilihi wa'ina ilahi raji'un."!!!! dakin yayi shuru na minti uku kafin ya sauke zazzafar ajiyar zuciya ya kalleni, hawaye na share nace"Ubangiji Allah ya jikanta Allah yasa aljanna makomarta." Ya amsa da "ameeen ya rabbi Jiya fa lafiya lau aka fito da jaririn kafin na fito daga hospital din sai da na tabbatar da komai yayi normal sannan! ashe bayan tafiya da minti arba'in jini ya tsinke mata kafin ayi wani yunkiri ta mutu ta bar jaririnta." murya na rawa ya karasa maganar......Nace"ikon Allah kenan! kaga ita waccar matar yaron ne ya mutu ita tana raye! wannan kuma gashi ta mutu ta bar yaron Allah babu yanda baya tsara lamarinsa, dama haka rayuwar duniya take Allah Ubangiji yasa mu cika da imani." Babu kuzari a tare dashi ya amsa da ameeen ya rabbi! mikewa yayi da fadin"Bari naje masjid." A sanyaye na bishi da kallo har ya fita daga dakin. Ina kokarin nad'e daddumar da nayi sallah ya shigo dakin, kallo na bishi dashi ina mamakin abinda ya shigo dashi, na dauka ai ba zai dawo ba, yanayin fuskarsa ya nuna cewar lallai akwai magana a tare dashi. Zama yayi kan gado da fadin"Zo Sumayya." a nutse naje na zauna gefansa, ya jima yana kallona kafin yace." Bana so ni dake muyi aure a bebai yana da kyau tun kafin zaman aure ya had'amu ki san abinda nake so da wanda bana so a tsarina mace d'aya ta isheni sai dai nasan hakan ba zai yuwu ba sannan bani da ra'ayin tara 'ya'ya koda matan aurena zasu kasance hud'u to na riga na tsara rayuwata bance kowace mace dole sai ta haihu dani ba! yara biyu zuwa uku sun isheni rayuwar duniya Sumayya ina da tausayi mutuka wanda shine dalilin daya sa kwata-kwata naji haihuwa bata burgeni saboda irin wahalar da mata kesha kafin suyi bana so duk haihuwa ya kasance sai kinsha wuya kin galabaita saboda haka na zaunar dake na fada miki tsarina itama Lawisa zan zauna da ita a yau na fad'a mata ra'ayina ina fata zakiyi wa maganata kyakkyawar fahimta. Cikin wani irin yanayi na alhini da damuwa nake kallonsa, tsabar mamakin maganarsa ma ya hanani cewa komai baya son haihuwa ya riga ya tsarawa kansa rayuwa wannan wane irin bayahudan mutum Allah ya had'ani dashi, dauke kaina nayi kawai ina girgiza kaina! Ya juyo da fuskata muna fuskantar juna yace."Banji kice wani abuba." Murmushin takaici nayi nace"Ai ni maganar taka ce tayi min nauyi shiyasa kawai nayi shiru ina auna maganar." Yace."Wane irin kina auna maganar okey to ina sauraranki naji a wane ma'auni kika ajiyeta." yakarasa maganar tare da tsare ni da ido. Kallonsa nayi babu wasa a tare dani nace"Ni dai nasan musulma ce gaba da baya kuma nasan addini daidai gwargwado to a matsayina na musulma wacce ta kadaita Allah shi kad'ai ban isa na tsarawa kaina rayuwar da nake so ba koda zan haifi 'ya'ya dubu a duniya to ba zan ta'ba butulcewa Allah ba.''' "Bangane inda maganar ki ta dosa ba." fuska a murtuke yayi maganar, Nace"Ina nufin ban yarda da wannan tsarin naka ba ban sani ba ko ita Lawisan.......Mik'ewa tsaye yayi a zafafe! ya nuna ni da hannu yace."Ke ki shiga nutsuwarki fa ko dan kinga ina bibbiyar lamarinki kada ki manta da manufar da zan aureki kawai hallacin ki a kaina yasa na janye mummunan kudirina akanki! yanzu nazo ina fad'a miki ra'ayi kina wata magana kin san dai ke baki isa ki ruguza min tsari ba ko."? Kallonsa nayi naga sai wani huci! yake nace"Allah ya huci! zuciyarka ni bana munafurci shiyasa tun kafin tafiya tayi nisa na fad'a maka nawa tsarin saboda haka kaine zaka zauna ka nemawa kanka mafita." Ya jima yana kallona kafin yaja tsaki mai karfi ya kama hanyar fita daga dakin, kallo na bishi dashi ya bude kofar dakin a fusace! ya fita. Ajiyar zuciya na sauke na tallafe ha'bata gabana na faduwa da wannan gagarimar matsalar da take kokarin kunno mana Magajin sarki baya son haihuwa saboda wasu banzayen hojjojinsa marasa tushe da maka wanda ni kuma nake ganin duk abinda za'ayi sai dai ayi amma ba zan bi hanyar da yake kokarin d'ora ni a kai ba wallahi bazan 'kayyadewa kaina haihuwa ba sai na haifi iya adadin 'ya'yan da Allah ya hukunta." A nutse na fito falo cikin kwalliya kamar koda yaushe kuma ko alama ban bar wani 'bacin rai a fuskata ba wanda zai sa ta fahimci wani abu, muka gaisa cikin mutunci da kulawa kafin ma fara karyawa kamar yanda muka saba............Falon ya shigo tsaf dashi cikin shirin fita, kamshin turaransa duk ya cika mana hanci, amma fuskarsa kawai ta isa ta nuna maka cewa yana cikin 'bacin rai! dauke kaina nayi har ya karaso inda muke ya zauna gaban mahaifiyarsa yana gaisheta. Ta amsa cikin kulawa da fadin"Babana jiya ai gajiya mukayi da jiranka muka kwanta ina fata dai anyi aiki cikin nasara." ? Ajiyar zuciya ya sauke yace."Mamma sai hakuri wallahi jiya ban shigo ba sai can dare koda na shigo kai tsaye sashena na nufa saboda nasan kunyi bacci." kallonsa nayi ina mamakin 'karyar dayayi, ya cigaba da cewa."Alhamdulillahi lafiya lau muka gudanar da aikin mu sai dai bayan dawowata gida d'aya ta amsa kiran ubangiji ta mutu ta bar yaron ita kuma dayar yaron ne ya rasu amma yanzu haka tana cikin koshin lafiya." Girgiza kanta ta shiga yi cikin alhini da damuwa tace"Ya Allah kaji k'an musulmi Ai tayi shahada babana duk matar data mutu gurin haihuwa Allah yace."Aljanna ce makomarta sai dai muyi fatan samun baiwa irin tata." Kallonta yayi yana girgiza kansa yace."Hakane Mamma Allah kasa mu cika da imani." Ta amsa da ''ameeen ya rabbi."' Kallonsa nayi a nutse nace"Barka da asubah." "Barka dai." ya amsa a takaice! Kokarin mi'kewa yake tace"A'a ba zaka tsaya kayo break fast ba."? girgiza kansa yayi yana duba agogon hannunsa yace."Mamma gabad'aya bani da kuzari wallahi cikina ya cushe bana sha'awar komai a yanzu mybe idan naje ofis na samu Coffee nasha ya isa." Tace"Babana bana so kana zama da yunwa kada fa ka manta kune kuke hanamu zama da yunwa to me yasa kuma kake karya doka."? 'Yar dariya yayi yace."Mamma kada ki damu insha Allah idan naje ofis zan samu wani abu naci yanzu babu lokaci dana zauna nayi break din.". Tace."A ina zaka samu abu kaci kawai dai ka fad'a ne! bari kawai Sumayya ta had'a maka snaks ka tafi dashi." yace."To Mamma." Tace."Sumayya ki duba dakina akwai snakas cikin firji sai kisa masa a leda yanda zai isheshi." nace."To ranki ya dade." A nutse na mike na nufi dakin nata...........Suna hira na fito na same su, na mika masa ledar kar'ba yayi ba tare daya kalleni ba, na koma inda nake ina kallonsa da mamakin abinda yake min.....sallama naji sunayi da sauri nace"Ranka ya dade Allah ya tsare ya kiyaye gabanka da bayanka." a dakile ya amsa min." hakan besa ta gane akwai matsala a tsakanina dashi ba tunda sau tari haka yake amsa min magana a ciki shiyasa bata fahimci komai ba, nima nayi saurin korar 'bacin raina na fuskanceta sosai muka cigaba da hira cikin mutunci da mutunta juna. Haka muka kasance da juna tsakanina dashi babu yabo babu fallasa dan duk wannan shige min da yake ya daina watarana ma idan ya dawo daga asibiti baya nema na nice nake fitowa nayi masa barka da zuwa! ko kadan ban damu da wulakancin da yake min ba saboda na riga nasan ni nake da gaskiya a duk inda zamuje shiyasa fushinsa sam be daga min hankali ba...............Yau saura kwana biyu daurin aure gabadaya masarautar ta hargitse sai abubuwa akeyi irin na al'ada Mamma ta mayar da hankalinta sosai gurin gyarani da ingantattun magungunan matan da take sawa a kawo mata, kullum sai bani wani turere na tsuguna akai haya'kin na ratsa a jikina, ni da kaina na tabbatar ingancin turaran dan ba headquarter na kawai ke kamshi ba gabadaya jikina ne ke kamshi duk inda na gifta kamshi na mussaman ne ke tashi............Jakadiya ce ta zauna tayi min 'kananun kitso irin na bare bari da yake ina da tsayin gashi yasa tufkar kitson ta kwanta gefe da gefen fuskata, ana ya gobe daurin aure da sassafe ta shigo dakina da kayan lalle(kunshi) haka na zauna tasa min salatif a kafafuna da hannayena kana tasa lalle akai tasa leda ta d'aure! ta gyara gurin, zama tayi kusa dani tana d'ebe min kewa, sai da mukayi zaman awa hudu da rabi tukkuna ta cire min lallan, na dinga bin kafafuna da kallo ina murmushin farin ciki tunda nake banta'ba adon lallai irin wannan ba Lallai jakadiya tana da zane sosai yanda ta fitar da zanan kunshi ragadau ya dinga burge ni gashi yayi wani irin jajawur, hannuwana na kalla nace"Jakadiya kinga kamar na hannun ya fi fitowa." tace"Eh ai da yake shi aka fara cirewa shiyasa yasha iska ne." murmushi nayi ina kallonta ta shiga turare min kafafuna da wani turere data zuba a cikin wani dan madaidaicin kaskon wuta. 'Bangaran Lawisa ma shiri suke sosai ita da mahaifiyarta Hajiya Karima ta tashi a tsaye tasa Lawisa sai bankar magunguna take lallai sai tafi Sumayya ni'ima a gurin miji! duk wani gyara da ake bukatar amare suyi a lokacin auransu kowacce tayi nata daidai gwargwado yayinda shi kuma angon nasu yayi musu bajintar kayan lefe kowacce akwati goma sha biyu cike da kayan amfani sannan kuma yasa an gyarawa kowacce sashen da zata zauna a gidan, dan bashi da ra'ayi had'asu a guri guda, duk abinda kowacce zata bukata tana dashi a sashenta. *RANAR DAURIN AURE* Masarautar ta cika da jama'a manyan mutane attajirai masu mulki malamai da sauran jama'ar gari kowa ya samu halatar daurin auran *Yarima Ali Abdul-aziz* inda wakilai suka sheda daurin auran kowacce akan sadaki dubu dari - dari bayan kammaluwar daurin auren sai masarautar ta hargitse da bushe-bushe gami da wassanin al'ada Ango yayi shirin hawa kilasa domin nuna murnarsa da Allah ya nuna masa zuwan wannan rana mai albarka.......Har dare ana abu d'aya a masarautar wassani iri-iri aka dinga gudanarwa, Sai da Ango ya shiga gida tukkuna kowa ya watse wa'inda suke masarautar suka nufi gurinsa wa'inda kuma suka shigo domin taya murya suka dinga fita jama'a kamar ranar idi! babu shakka jama'ar gari sunyiwa masarauta kara sun nunawa Sarki Abdul-Aziz Abdullahi kauna shima yaji dadi sosai dan kafin taro ya watse sai da ya mika godiyarsa zuwa gare su.. *Na kudi ne...* Kada ki karanta min littafi idan baki biya ba! keda kika fita da littafin keda Allah! idan kina so ki biya kudin littafin ga yanda abin yake...Vip gruop#600 normal gruop#300....account... 0542382124....Binta umar gtbank.....idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannam number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:28 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 92 Tare suka shiga sashensa da Shatima, suka kimtsa jikinsu cikin kayan sarauta komai iri daya sukayi sosai sukayi kyau kana ganinsu kaga angwaye, da yake tare da Shatima aka daura auran shima amaryarsa 'Yar sarkin kazaure ce sun jima suna soyayya sai kawai iyaye suka zauna suka tattauna al'amarin lokaci guda akayi komai aka gama sai bayan da'aka daurawa Yarima aure da mata biyu tukkuna shi aka daura masa aure da tashi amaryar mai suna Mansura......koda suka fito kai tsaye sashen Waziri suka nufa sukaje suka gaisa dashi da iyalinsa sukayi musu bangajiya Waziri ya jima yana musu addua da fatan alkairi kafin su fito su nufi sashen Galadima shima iyalinsa duk suna nan sai hidima sukeyi, suka gaisa a tsanake Galadima yaji dadin ganinsu ya dinga farin ciki yana yi musu fatan alkairi, koda suka fito sai suka nufi sashen Ciroma yana zaune a kan kujera Hajiya Karima na kusa dashi sannan 'ya'yansa gabadaya sun kewaye shi suna magana, shigowarsu tasa dukkaninsu suka kalli bakin kofa......Ganinsu su biyu cikin kayan sarauta yasa wani bakin ciki ya lullu'besu da tuni harda Muddibo acikinsu Sunyi sanadiyar mutuwarsa sun kwantar da hankalinsu suna rayuwar jin dadi. Hajiya Karima ce ke wannan maganar cikin ranta, Ciroma kuwa b'acin ransa ya danne ya dinga murmushi yana amsa gaiswarsu tare dayi musu fatan alkairi Hajiya Karima kuwa lokacin da suke gaisheta kawar da kanta tayi sai da Wali yayi mata magana tukkuna ta amsa a ciki. gabadayansu basu ji dadin abinda mahaifiyarsu tayi ba har yanzu ta kasa 'boye 'bacin ranta gaban kowa nunawa take, suna fita Lawisa ta mike tabi bayansu, da sauri tace."Dan Allah ku tsaya." Magajin sarki da Shatima suka tsaya suna kallonta kamar wata mutuniyar arziki ta nufe su, Ya dinga kallonta yana mamakin kyawun da tayi tai ado sosai tayi kyau tamkar wata balarabiya lumshe idonsa yayi yana tunanin irin ni'imar da zai samu a tare da ita, ta tsaya kusa dashi kamshin turaranta ya bugi hancinsa bude idonsa yayi sosai yana kallonta, tace"Dan Allah kuyi hakuri da abinda hajiya tayi muku wallahi dukkaninmu bamu ji dadi ba." Shatima yace." Haba babu komai wallahi kada ku damu Hajiya uwa ce komai tana iya yi mana mu hakura." Murmushi tayi tace"Nagode sosai.'' Shatima ya kalleshi sai yaga ya k'urawa k'asan gurin ido, yace.''Bari nayi gaba na bar amarya da ango su tattauna." da sauri ya dago kansa yana harararsa, Dariya yayi ya bar gurin, kokarin tafiya yake ta rike hannunsa, ya juyo yana kallonta cikin wani irin yanayi yace." Kina bukatar wani abune."? murmushi tayi tace.'"Babu abinda nake bukata sai angona hakika yau ina cikin murna da farin ciki da Allah ya tabbatar mana da alkawarin mu.'' shuru yayi yana kallonta a sanyaye tace" naga kana kallona ko dai kwalliyata ba tayi kyau ba."? tafada tana duba jikinta Girgixa kansa yayi yace."Kinyi kyau sosai dalilin daya sa ma kenan na kasa dauke idona a kanki ." wani farin ciki ya ziyarce ta hannunsa ta damqe da fadin"Lallai tunda kana son ado zan diga yi maka mai kayatarwa." shima murmushin yayi yace.''Nagode amaryata anjima zan kira ki kizo ki taya ni hira." dadi ya sake rufeta lallai malamin da yake musu aiki gwani ne yau ita da Yarima ne suke hirar soyayya babu fada, fari tayi da ido tace"To shikkenan angona." hannunsa ya cire daga cikin nata ya bar gurin, kallon so da kauna tabi shi dashi har sai daya 'bace daga gurin sannan ta koma ciki cike da murna da farin ciki, kasa boye farin cikinta tayi ta shedawa mahaifiyarta sauyin da'aka samu Hajiya Karima ta dinga murna tana kara kuranta aikin malaminta. Samun Shatima yayi a tsaye a wani guri yana jiransa saboda haka yana karasowa suka nufi sashen Uwar gida Huwaila da jakadiyarta suna magana shigowarsu yasa ta washe baki kamar mutuniyar kirki ta dinga tsokanarsu su kuwa sai sunkuyar da kai suke suna murmushi jakadiya ta gaishesu da sauri ta fita daga falon, suka zauna a nutse suna gaisheta, ta amsa cikin sakin fuska tace"Tun dazu 'Yan uwanku suke zaman jiran shigowarku ku gaisa suyi muku Allah ya sanya alkairi ganin dare yayi sosai yasa nace ko wacce ta tafi dakinta daga baya sai su dawo ku gaisa sosai! ta fadi hakane domin ta karesu gabad'ayansu ana gama daurin aure kowacce ta shiga motarta ta tafi a cewarsu ba zasu tsaya zuciyarsu ta buga a banza da wofi ba sun tsani suga mahaifinsu na nuna kulawa akan dan uwansu ba kuma sa kaunar wani alkairi ya same shi hassada suke masa sosai suna ganin kamar mahaifin nasu yafi kaunarsa saboda yana namiji. Magajin sarki yace."Allah sarki aunt's d'ina banji dadi ba wallahi amma babu komai in Allah ya yarda duk zamu bi gidajensu daya bayan daya muyi musu bangajiya." Tana dariyar yake tace"Haka yayi kyau Tabbas zasuji dadi idan kuka ziyarcesu yana da kyau ma idan zakuje kuje musu da amaran naku." Shatima yace."Insha Allah hakan za'ayi." sallama sukayi mata mikewa tayi tabi bayansu sai surutan banza take musu wai ita a ganinta tana musu nasiha akan zamantakewar aure! Suna fita Shatima yace."Wannan matar kana ganinta kaga mara gaskiya gabad'aya halayenta na munafukai ne." Murmushi yayi yace."Shiyasa ai nake kallonta ita da yaran nata nasan dukkaninsu ba kaunata suke ba kome suke na ganin idone idan babu idona a gurin Allah ne kadai yasan sharrin da suke shirya mun." Shatima yace."Addua zaka dage dayi ka kuma dinga azkar safe da dare insha Allah duk wanda ya nufe ka da sharri zai koma kansa." A hankali yace."Ina godiya dan uwa insha Allahu zan kula da shawarwarin ka." Kai tsaye sashen mahaifiyarsa suka nufa, suka sameta ita da Maimartaba a falon suna tattauna abinda ya shafe su, cikin girmamawa suka gaishe su Maimartaba ya dinga kallonsu yana jin dadi da farin ciki a zuciyarsa, addua mai kyau yayi musu ya kuma yi musu nasiha mai ratsa jiki itama Fulani ta d'ora ta tace"Dukkaninku yanzu wani nauyi na mussaman ya hau kanku mussaman kai Babana ka kula sosai kayi adalci a tsakanin matanka Allah yayi muku albarka ya sanya alkairi a cikin zamantakewar auranku." Gabad'aya suka amsa da "ameeen." suna kokarin mikewa tace"Babana na manta ban fada maka ba Sumayya na can gurin iyayenta na tura ta suyi sallama da juna watakila ma a can zata kwana." Jim yayi kafin yace."to shikkenan Mamma babu damuwa ai." Maimartaba yace."Gobe da safe sai kaje ku gaisa da iyayen nata daga nan sai ku tawo da ita." Yace."To ranka ya dad'e Allah ya kaimu lafiya." suka amsa da ameeen.'' sallama sukayi musu suka fita koda suka fita din basu jima a a tare ba sukayi sallama da junansu kowanne ya nufi sashensa, Magajin sarki zama yayi a falonsa yana jin takaicin abinda Sumayya ke masa tunda suka samu sa'bani kwanakin da suka gabata ya dauki fushi da ita bata ta'ba bashi hakuri ba, idan ta gaishe shi shikkenan sai ta fita sabgarsa ko kiransa a waya ba tayi kawai sabgar gabanta takeyi tana nuna tamkar bata damu dashi ba! abin yana bashi mamaki mutuka a ganinsa shine yake sama da ita koda shine bashi da gaskiya tunda itace a kasa dashi ita zata bashi hakuri amma saboda ta dauki kanta wata mai matsayi ta'ki kallonsa da mutunci dole ya nuna mata shi ba tsaranta bane tunda dai an riga an daura aure zata gane bata da wayo tsarinsa kuwa dole tabi ko tana so ko bata so. Wanka yayi yasa kananun kaya ya sauko kasa da wayarsa a hannunsa Lawisa ya kira domin tazo ta d'ebe masa kewa aikuwa ko minti ashirin ba'ayi ba ta shigo cikin ado har yafi na dazu! kusa dashi ta zauna tana kwarkwasa kamshin turaranta ya kashe masa jiki hannunta ya rike yana mata wani irin kallo yace."Muje sama ko."? kanta ta daga masa ya mike tare da ita, kugunta ya rike ta sosai tare da manneta jikinsa suka nufi saman rungume da juna. Bangaran Sumayya kuwa tana cikin farin ciki da annushuwa tana tare da iyayenta sai walwala sukeyi sai dai a duk sanda ta tuna da mutumin nata gabanta sai ya fadi! tana tunanin irin bahaguwar rayuwar da zasuyi ita dashi tunda dai ita tayi rantsuwa akan cewar ba zata amince da tsarinsa ba shi kuma ya tabbatar mata da cewa dole tana karkashinsa tayi masa biyayya mutukar tana bukatar zaman lafiya dashi inda ita kuma take ganin babu yanda za'ayi ya sata ta kauce hanya ba za tayi tsarin iyali ba sai dai shi yaje yayi tsarin iyalin amma ita ba zata cutar da kanta ba......Wannan dalilin yasa gabadaya ta kasa sakin jikinta dashi domun tana so ta nuna masa cewar har yanzu fa tana nan akan ra'ayin ta babu gudu babu ja da baya idan Lawisa tana iya yi taje tayi amma itakam bata da ra'ayi. Magajin sarki da Lawisa soyayya sukayi sosai kafin kuma ya rabata da budurcinta sai da ya bata kwayoyi tasha tukkuna suka cigaba da gudanar da abinda suke a daran ya kar'bi sadakinsa alhamdullh kwalliya tabiya kudin sabulu dan yaji dadin kasancewarsa da ita bukatarsa ta biya ya dinga alfahari da ita shine yayi mata wanka ya gasa mata jikinta tsaf suka fito daga toilet din a tare, kayanta ta mayar a sanyaye take kallonsa yace."Kada ki damu nasan abinda kike tunani! sunkuyar da kanta tayi yace." Kinzo dakin ki kenan ba zaki koma ba kuma inaso na sheda miki cewa na sameki cikakkiyar mace ina alfahari dake." ajiyar zuciya ta sauke tana kallon bedshirt din daya 'baci da jini! tace."Wannan zanin gadon zaka sa a leda nasan da safe Hajiya zata aiko a kar'ba.'' yace."Lawisa wannan tsohuwar al'adace bana san tonan asiri wallahi." cikin alfahari tace"Ni dai gwara kowa ya gani ya sheda na kawo mutuncina." yace."To babu damuwa." bedshirt din ya cire yace'' kar'bi abinki kisa a leda ki daure." da sauri ta kar'ba! wardrobe dinsa ya nufa can kasa ya dauko sabon zanin gado ya fara kokarin shimfidawa, karba tayi suka shimfida a tare, kwanciya yayi yana kallonta gaskiya yaji dadinta sosai gata da ni'ima ta kowanne fanni tayi ta burgshi lumshe ido yayi yana tunanin irin ni'imar da zai kwasa gurin Sumayya. Hajiya Karima sashe sashe ta dinga bi tana nuna zanin gadon amarcin Lawisa Jakadiyarta sai rangwada buda take tana fadin"Yarinyar arziki ta cika mace ta kai mutuncinta dakin mijinta! Hajiya Karima ta kalli Fulani cikin farin ciki tace"Fulani inaso ki ajiye wannan zanin gadon idan Maimartaba ya shigo sai ki nuna masa." Fulani na kokarin magana na shigo tare da sallama! gabadaya suka amsa min Hajiya Karima ta wani dauke kanta tana girgiza kafa, a nutse na zauna kusa da ita nace"Mamma barka da asubah." tace"Barka dai Sumayya ya kika baro iyayen naki."? nace"Suna nan lafiya lau sunce suna gaisheki da kyau." tana murmushi ta amsa, ta cigaba da cewa"Tare kuke da babana ne."? girgiza kaina nayi alamun A'a, tana kokarin magana Hajiya Karima ta katseta da fadin" In banda abinki Fulani ina za'a ga Magajin sarki yana can tare da yarinyar arziki aini nayi alfahari da faruwar wannan abu.'' Fulani rai a 'bace! tace"Hajiya Karima maganar nan ta isa haka na sheda na tabbatar Lawisa takai matuncinta dakin mijinta amma banga ammafanin nunawa Maimartaba zanin gado ba ki tafi dashi gurunki.". Hajiya Karima tace"Aikuwa dole a nuna masa ya sani yarinyarsa yar arziki ce idan ke ba zaki nuna masa ba zan kaiwa Huwaila ta nuna masa." Tana gama maganarta ta mike a fusace! Jakadiyarta tabi bayanta tana rangwad'a bud'a! Jikina ne yayi sanyi na riga na fahimci abinda keda akwai har yaushe Lawisa ta tare a d'akinta wata Mu'amular aure ta shiga tsakaninsu! wani irin kishi mai zafi ya tokare min kirjina! Muryata ce ta dawo dani nutsuwata. shuru nayi dan banda abinda zance akan al'amarin, ta cigaba da cewa"Kiyi hakuri da duk abinda zaki gani kinji ko ki zauna lafiya da Lawisa kada ki dauketa a matsayin kishiyarki 'yar uwarki ce duk sharrin da za tayi miki ke kiyi mata alkairi Allah zai kare ki daga sharrinta! a sanyaye nace"Insha Allah Mamma." Tana kokarin magana suka shigo a tare, Sunyi ado na sarauta ita dashi sunyi kyau sosai! Mamma sakin fuskarta tayi tana amsa sallamarsu, ni kam gabana ne ya dinga faduwa ina mamakin sharrin d'a namiji har yaushe suka shirya suka daina fad'a da juna! shakuwar su ta bani tsoro tamkar masoyan da suka shekara dubu suna soyayya, gabadaya ji nayi na tsargi kaina, na kasa dago kaina na kallesu ina ji suna magana da Mamma amma fargabar kallonsu nake sabida bana son yayi min kallon wulakancin daya saba." Sai kawai na yanke shawarar barin gurin domin ina ganin kamar hakan shine ya dacewa dani. "A'a Sumayya ya zaki tashi kuma ana hira ni banga ma kun gaisa da junanku ba."! Dauriya na aro nace" Mamma zanje na kwanta ne wallahi duk na gaji." Lawisar na kalla nace"Ranki ya dade barka da safiya." a takaici ta amsa da "barka dai." na kalleshi tare da daure fuskata nace"Ranka ya dade barka asuba." Da d'an murmushi a fuskarsa ya amsa da "Barka dai gimbiya." kallonsa nayi ina mamakin murmushinsa A gaskiya mutumin nan shu'umi ne baka ta'ba gane inda ya dosa wai harda kirana gimbiya. gurin na bari ina mamakin sauyawarsa.... *Na kudi ne* Kada ki karanta min littafi baki biya ba, keda kika futa da littafin keda Allah! idan kina so ki biya ga yanda abin yake....Vip gruop#600 normal gruop#300....account... 0542382124...Binta umar gtbank....idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:28 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 93 Koda na shiga dakin kasa aikata komai nayi nai zaune a gefan gado tare zabga tagumi ina mamakin abubuwan da suke faruwa, al'amarin Magajin sarki da Lawisa ya tsaya min a raina mutuka na dinga mamakin sanda suka shirya tsakaninsu, dan ganinsu a yanzu yasa na fahimci a kwai k'auna a tsa'kaninsu, " Watakila ita din ta amince da tsarinsa shine dalilin da yasa kika ga sun hade kansu." zuciyata ce ke fada min haka..... gaskiya kam da akwai alamar haka dan da bata amince da bukatarsa to da ba zasu samu jituwa irin haka ba girgixa kaina nayi ina mamakin wauta da rashin dubara irin nata gaskiya idan da gaske ha sashena ya tabbata gaskiya ne to gaskiya tayi wauta! a maimakon ta bari taga ta haihu kafin ta amince masa kawai saboda tana jin tsoron 'bacin ransa ta cutar da kanta('Kalubale ga matan dake yin tsarin iyali bai tare da sun tabbatar suna haihuwa ko basa haihuwa ba kawai kiga mace saboda rashin wayo ta biyewa miji saboda so yayi ta dibga mata kwayoyi daga karshe ciwo ya hanaki haihuwa shi kuma yaje ya auro wata babu abinda ya dame shi mata muyi hattara) ajiyar zuciya na sauke ina sake mamakin al'amarin, ni kam duk rintsi ba zan amince da wannan tsarin ba...........Shigowarsa dakin ce tasa na saurin kallon bakin kofa, ya mayar da kofar ya rufe dakin, a nutse ya karaso inda nake, tsayuwa yayi a kaina yayi min rumfa, na dago kaina ina kallonsa sai naga fuskarsa a sake sa'banin kwanaki........"Ka zauna mana." nafada ina nuna masa gefena." murmushi yayi yace."Kin bani ikon zama kenan."? shuru nayi masa, ya zauna inda na nuna masa, zamana na gyara ina kallonsa. ya kai hannu zai tsokane min ido nayi gaggawar dauke fuskata , yace."Tun a falo kike kallona ko na sanja miki ne."? girgiza kaina nayi nace"A'a ina mamakin halinka ne." Dan bata fuska yayi yace."Wane irin hali ne dani."? shuru nai, ya kamo hannuna na dama yana duba lallen da'a ka zana min." a baki yasa yana tsotsa! tsigar jikina ce ta tashi da sauri na janye yatsuna ina kallon gefe guda Matsoni yayi sosai cikin taushin murya yace."Kin samu Labarin tarewar,Lawisa ko." shuru nayi gabana na bugawa kusancina dashi yasa naji wani irin bakon yanayi yana ziyartata! wuyana ya sumbata "Mylov." A sanyaye na kalleshi dan gabadaya jikina ya mutu saboda abubuwan da yake min. 'Kan'kance ido yayi yace."Yaushe ne zaki tare a naki dakin." ? dan janye jikina nayi nace" Nima ban sani ba." shuru yayi yana cigaba da ya mutsa min jiki. "Dan Allah ka bari." nafad'i maganar can kasan makoshi! Yace."Wannan kamshin dake jikinki nake so." Fuskarsa na ture na mike daga gurin, jikin mudubi na jingina ina kallonsa gabadaya sha'awa nake ji a jikina duk na rasa yanda zanyi ban'taba riskar kaina cikin irin wannan yanayin ba sai a wannan lokacin. daf dani ya tsaya hucin numfashinsa na sauke a fuskata, kauda kaina nayi cikin damuwa nace"Dan Allah ka fita." fuskata ya tallafo da hannayensa yace."Ba zan fita ba sai nasha bakinki." da sauri na kalleshi gira ya daga min yana kokarin kamo bakina da nasa, yun'kurin barin gurin nayi ya matseni jikin mirror kayan shafar dake jere a kai suka zubo kasa, bakina yasa a nasa ya shiga tsotsa yana shashshafa jikina, kasa hanashi nayi kawai na tsinci kaina da lumshe ido sosai nake jin dadin abinda ke faruwa a tsakaninmu......Ido jawur ya kalleni yace."Da dadi ko."? gurin na bari da sauri ya biyo ni ya zauna kusa dani, hannuna ya rike ya kira Sunana, kallonsa nayi ina kokarin daidaita nutsuwata yace."Ina fatan kin shirya zama dani da ra'ayina." gabana ya fadi nace"Ban fahimci maganarka ba." yanayinsa ya gyara babu wasa a tare dashi yace." Kin manta maganar mu ta kwanaki kenan."! ta'be bakina nayi nace"Gaskiya na manta." Ya shiga girgiza kai yana kallon kasan kafet, yace." Nasan kawai kin fadi hakane ba wai dan kin manta da maganata ba to inaso na kara tuna miki cewa "Ni Ali ina nan kan ra'ayina koda zaku haihu ba yanzu ba tukkuna sai na gama morewa." Kai tsaye nace"Idan Allah ya kawo haihuwar kuma ya zakayi."? "Allah ba zai kawo ba insha Allahu ina da matakan Kariya." mirmushin takaici nayi nace"Kada kayi mamaki da hukuncin ubangiji duk dabarunka idan ya zartar da ikonsa babu yanda za kayi.'' Hannu ya daga min yana kallona da wata irin fuska. dauke kaina nayi daga barin kallonsa, rai a bace ya mike ya fita, tsaki naja a fili nace"Wallahi ba zan yarda da wannan yahudancin ba sai dai duk abinda za'ayi ayi. A daran ranar Mamma ta shiryani sosai kana ta kama hannuna ta kaini har dakina kafin kuma tayi min sallama sai da ta jima sosai dani tana min nasiha kuka sosai nayi da kyar! na bari ta tafi yanda na lura itama tana alhinin rabuwa dani daurewa kawai takeyi.......haka na kasance tsayin dare ni kadai a daki ba tare da ya shigo gurina ba har garin Allah ya waye! sosai nayi mamakin lamarin wato fushi yake akan abinda ya faru tsakanina dashi, idan kuwa hakane zai dade yana fushi dani sai dai idan ya gaji ya daina dan bazan yarda ya cutar dani ba. Wanka nayi tsaf na shirya jikina na fito falo nan na samu sabbin hadimai suna ta goge goge zubewa sukayi suna gaishe ni, na amsa cikin sakin fuska, zama nayi kan kujera duk suka tsuguna a gabana nace"Ya sunanku.'"? "Ni sunana Mariya" "Sunana Sakina" "Ni kuma Sunana Sadiya." Nace"To ina so ku zauna dani tsakani da Allah dan Allah ku rike amana da gaskiya kuma kada ku bari a cutar da wani ta hanyarku'' Suka ce "Insha Allahu zamu kula." Mariya tace"Ko a kawo miki abin karin kummalo nan."? girgiza kaina nayi nace"Barshi zan karasa dainng din.'' godiya sukayi nace"Kuje ku cigaba da aikin ku." Gabad'aya suka mi'ke da sauri suka bar gurin, waya ta nake dubawa text dinsa ya shigo, da sauri na duba. _"Ina fata kin tashi lafiya."?_ Abinda ya rubuta kenan, kamar na bashi amsa sai kuma na kyaleshi idan so yake ya tabbatar da lafiya ta ai yasan inda nake, mikewa nayi da wayar a hannuna na nufi gurin cin abincin. 'Bangaran Yarima kuwa yana can gurin Lawisa yana cin amarcinsa so yake ya nuna wa Sumayya kuranta a ganinsa wannan halin ko'in kular da yake nuna mata zai sanya tayi laushi tabi ra'ayinsa, gabadaya ya manta da cewar Sumayya mai taurin kai ce akan Gaskiya ba kuma ta munafurci shi ya kamata ya fad'awa kowa halinta amma ya manta halinta yake tunkarar ta da abinda shi kansa yasan ba mai kyau bane. Ina kokarin barin daining ya shigo cikin jallabiya milk kallo daya nayi masa na kauda kaina, cigaba nayi da duba wayar hannuna, tsayuwa yayi a kaina yana fadin"Salamu alaikum." a nutse na dago kaina na amsa da "Wa'alaikassalam." Dan ta'be baki yayi yace."Ya kike."? share shi nayi dan naji ciwon abin.'" "Sumayya." dagowa nayi muka hada ido. yace."Kina ji ina gaisheki kinyi shuru." "Wace irin gaisuwa ce.'' nafada da rashin walwala." Mirmushi yayi yaja kujera yana kallona, nace"Barka da asubah.'' hankalinsa kan tea din dake gabana ya amsa, cup din tea din ya dauka yana sha, nace"Ka bari na hada maka wani mana." girgiza min kai yayi sunkuyar da kaina nayi ina dube dube a waya. "Sumayya." dagowa nai ina kallonsa da mamakin yanda yake kiran sunana kamar shi ya rad'a min." "Na'am." na amsa cikin rashin walwala, yace." Ba kiga text dina ba." shuru nayi yace."Ko bakya ji ne."? "Na ganshi." nafada kaina a kasa..."Okey kin gani me ya hanaki bani amsa ko ban isa ba."? Girgiza kaina nayi nace"Ka isa har kayi yawa kawai ban samu lokacin baka amsa ba ne." Tsira min ido yayi yana kallona, yace."Baki da lokacin kirana a waya sannan baki da lokacin amsa min text ko."? mirmushin takaici nayi nace"Wai baka san inda nake ba meye na damuwa yanzu gashi ai kazo ka duba ni." Shuru yayi ya cigaba da kur'bar tea d'in, mikewa nake kokarin yi yace."Kada ki tashi ina da magana dake." gabana ne ya fadi na koma na zauna. Cup din ya ajiye ya tsira min ido.....ni kam wannan jarababban kallon nasa na damuna, nace."Ina sauraranka." "A ina maganar mu ta kwana."? yafada babu wasa a tare dashi....cikin dakiya nace" Wace magana."? Tevur din ya buga a hasale! yace."Ke! bana son rainin hankali ya ina tambayarki kina tambayata." Shuru nayi saboda ganin yanda ya hasala sai huci! yake! cikin tausasawa nace"Yi hakuri dan Allah zauna muyi maganar na tuna." Zama yayi yana hararata.........."Ina fatan ka huce!" na fada da murmushi a fuskata! tsaki yaja yace."Ban huce ba sai naji daga gare ki." Ajiyar zuciya na sauke nace"Yallabai tsarin iyalin nan wai dole ne."? kansa ya daga min da fadin"Dole ne." Girgiza kaina nayi nace."Okey to ni dai bani da ra'ayi amma kai ko Lawisa babu wanda na isa na hana yayi na tabbata ba mata kawai ke tsarin iyali ba har da maza kai kayi ina ganin haka sai yafi." Ya jima yana kallona kafin yace."Wannan shawarar kika yankewa kanki."? kai na daga nace"Eh ita na yanke." Yace."Okey babu damuwa zanyi tsarin iyali tunda haka kika bukata amma ina gargadin ki da kawo min 'korafi anan gaba." Dan Mirmushi nayi nace"Haba wane irin k'orafi nifa nace kayi babu damuwa." Yace."Magana ta wuce ai." Shuru falon yayi na minti uku kafin yace."Nayi kwana biyu a gurin Lawisa yau anan zan kwana sai ki shirya kin san yau akwai abubuwa." Wani irin kallo nayi masa! ya wani langwabe kai da fad'in"Oh! wannan kallon fa ina tsoro ki ritsa ni a gado wallahi." Dariya nasa saboda yanda yay maganar sai kace wani dan daudu! yace."Da gaske fa nake miki ni dan koyo ne." Had'e fuska nayi nace"Ni dai mu bar maganar nan bana so." Yace."Hira mai dadi da lada itace bakya so."? kaina na d'aga masa, yace."Okey to bari na daina idan mun had'u da daddare sai muyi." murmushi nayi! yace."Kije ki dauko mayafin ki muje can gurin Lawisa ina so na zauna daku." a nutse na mike na nufi daki.....ajiyar zuciya ya sauke bayan barinta gurin ya shiga tunanin abinda zai faru a tsakaninsu, Allah-Allah yake dare yayi yasha shagalinsa..... *Na kudi ne...* Kada ki karanta min littafi idan baki biya ba, keda kika futa da littafin keda Allah idan kina bukatar biya ga yanda abin yake....Vip group #600 normal group.. #300 account... 0542382124...Binta umar gtbank....idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:28 PM - ???: *JAR UBA! WAI DA YARIMA DA SUMAYYA WA YAFI MASOYA NE! VIP GROUP KOWA YA FITO YA ZA'BI GWANINSA🥰 NIDA INA TEAM DIN 'DIYA TA SUMAYYA✊?* *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 95 Ido a lumshe ya kira sunana, amsawa nayi ina kallonsa yace."Yana da kyau mu gabatar da sallar godiya ga Allah ko."? A sanyaye nace"Eh hakan nada kyau." yace."okey to tashi kije ki daura alwala." kasa tashi nayi kawai nayi kasa da kaina haka kawai na tsinci kaina da fargabar fada masa halin da nake ciki. Zamansa ya gyara ya bude idonsa sosai yana kallona yace."Kije kiyi alwala." dagowa nayi muka hada ido, nace" Bani da tsarki." wani irin kallo yayi min kafin yace."Ban fahimce ki ba." ina wasa da yatsun hannuna nace"Ina nufin ina al'ada ne." kawai yasa min ido yana kallona, na kalleshi naga yanda ya wani ci kunu. Kauda kaina nayi a raina nace"Nasan za'a rina dama!........Mi'kewa tsaye yayi yazo ya tsaya a kaina, gabana ya dinga bugawa na kalleshi, yace."Idan karya kike dan ki kubatar da kanki to zan duba nagani" Murya na rawa nace"Akan me zanyi maka karya kai kasan ba halina bace." kafad'a ya daga alamun bai yarda ba, jikina na janye ya sake matsoni da fadin"Ki bude min na gani na tabbatar dan ni ban yarda da maganarki ba." Nace"Wallahi da gaske nake dan Allah ka yarda da magana ta mana! tura ni yayi na fadi rigingine a gadon kafin nai wani yunkuri ya danne ni! gabadaya ya sakar min nauyinsa sai da nayi tu'bis!!! sannan naji ya soma sa min hannu a cikin dogon wandon baccin dake jikina!."' Tureshi na shigayi ina mamakin kazantar sa wai pad din yake kokarin zarowa daga jikina! na dinga cire hannunsa ina fad'in "Ya bari amma sai da ya zaro pad din bukatarsa ta biya! zaune na mike ina haki! nace" Ni kam banta'ba ganin kazami irinka ba wallahi! yanzu dan Allah meye amfanin abinda kayi." Shuru yayi min bece komai ba ya dauki wayarsa ya kunna haske yana duba pad din, mamaki ne ya rufe shi ganin jini a jikin pad din yasa ya amince da maganarta da ya dauka k'arya take masa shiyasa ya danneta domin ya tabbatar, cike da takaici ya jefa mata pad din a jikinta ya nufi toilet gaskiya ransa ya 'baci da al'amarin yaso a yau ya kawar da sha'awar ta da ta dameshi. Cike da takaici na dauko pad din na nufi toilet din yana tsaye daure da towel nayi abinda zanyi a toilet din na fito ba tare da mun kula juna ba.....cikin bacin rai na kwanta ina addua a cikin raina.........Bacci mai dadi ne ya dauke ni naji kwanciyarsa a kusa dani, lamfo nayi har ya daidaita kwanciyarsa jikina sosai ya matso ya ratsa hannuwansu a jikina breast d'ina yake matsawa da dukkanin hannuwansa, shiru nayi gabana na dukan uku-uku bana so nayi kwakkwaran motsin da zai dauka idona biyu. Saukar numfashinsa na dinga ji a wuya na, tsigar jikina ta dinga tashi, kawai sai jikina ya shiga rawa sha'awar da nake dauke da ita ta tashi, gabad'aya nipples dina suka rikice min da kyaikayi na dinga jin dadin yanda yake sosa min.......zazzafar ajiyar zuciya na shiga saukewa ina takure jikina sanyi ne kawai ke ratsani, birkitoni yayi ya rungume ni tsam! tsam a kirjinsa muka dinga sakin wani irin nishi!!! gabadaya jikinmu rawa yake ya sake ni ya mike zaune dago ni yayi ya shiga kici-kici tu'be min riga, ban hanashi ba ina kallo ya cire rigar ya ajiye a gefe dama ban sa breziyya ba kawai ya had'ani da jikinsa tsintar kaina nayi dasa hannuwana a bayansa na rungumeshi kam! ina sakin zazzafan nishi! Had'uwar fatar mu yasa dukkaninmu muka fita hayyacinmu muka dinga birgima a bed din muna manne junanmu, kasa hakura nayi da kaina na kamo bakinsa ya bani harshensa na dinga tsotsa tamkar alawa, shi kuma ya dinga tsotsar le'buna yana murza nipples d'ina! mun jima a haka kafin ya sake ni, ya cire boxer din jikinsa dauke kaina nayi ganin yanda gabansa yayi wani irin girma gabana ya dinga bugawa kokarin barin gadon nayi ya kamo hannuna ya dora a gurin, cikin wata sha'kakkiyar murya yace."Kiyi min wasa my love." kasa aikata masa komai nayi hannuna sai kyarma yake a gurin, yace."Kada ki bani kunya mana my love ki kula dani zaki samu lada" A sanyaye na shiga shafa jijiyar ina lailaya kanta! wani irin nishi! ya dinga saki! yana sake bud'e jikinsa! ganin yana nema ya zautu yasa na dauke hannuna! kamar mahaukaci ya kamo ni jikinsa na rawa yace."Dan Allah ki cigaba idan da hali ma kisha zanfi gamsuwa." Kallonsa nayi naga duk ya koma wani iri tausayi ya bani! sai zufa yake jikinsa na kyarma! cigaba nayi dayi masa na kuma sakar masa jikina sosai yayi wasa da kirjina iya yanda yake so, aikuwa yaji dadin hakan ya kuma samu cikakkiyar gamsuwar da yake bukata, tare muka shiga toilet dashi, na dinga dauke kaina ina jin kunyar had'a ido dashi! murmushi kawai yake min har ya gama wankasa ya daure towel yana kallona yace." Har na gama abinda nake kina tsaye kina kallona ko akwai matsala ne."? girgiza kaina nayi na wuce shi! yace."Kiyi sauri ki gyara jikinki kk fito mu kwanta dare yayi." Shuru nayi masa sai da ya fita da toilet din na samu nutsuwar gyara jikina, na fito daure da towel kai tsaye wardrobe na nufa ba fito da wasu kayan baccin nasa a jikina, bed din na nufa na sameshi babu a kwance amma ya cire bedshirt din ya ajiye guri guda. Nace"Ka tashi asa zanin gadon." yace."Bacci nake ji kizo kawai mu kwanta da safe sai ki shimfid'a." ajiyar zuciya na sauke na kwanta kusa dashi, jawo ni yayi ya rungume ni a jikinsa kawai sai na tsinci kaina da kwantar da kaina a kirjinsa nasa hannuwana duka na rungumeshi! a haka bacci mai dadi ya dauke ni. Da safe ma tare mukayi wanka gabad'aya ya rikitani da zazzafar soyayyar sa tun ina no'kewa har dai na saki jikina muka dinga wasanni kafin muyi wankan mu fito cikin towel d'aya! ganin yana kokarin kwantar dani a gado yasa da sauri na 'kwace jikina cikin shagwaba nace"Kai kam wannan abu baya isarka ne." ido a kankance yace." Ya za'ayi na gaji dake my love cikin ko wane irin yanayi ina sonki duk da kina al'ada amma kin gamsar dani! kuma bana kyamar had'a jikina dake sa'banin wasu mazan da idan matansu na al'ada suke kaurace musu.'' Girgiza kaina nayi nace"Gaskiya kam nima na gazgata irin kaunar da kake min insha Allahu nayi maka alkawarin baka cikakkiyar kulawa." murmushi yayi yace."To nagode sosai yanzu sai da daddare zakiyi min irin na jiya ko."? rufe fuskata nayi da hannuna! kunyarsa ce ta rufe ni janyo ni yayi jikinsa ya rungume tsam! yana shafa gashin kaina! kwanciya nayi a jikinsa ina sauke numfashi, a hankali yace."Kince na bari kuma kinyi kwance a jikina wallahi duk kin tayar min da hankali.....mikewa nayi ina gyara towel din jikina nace"Ka bari sai da daddare zan kula da kai yanzu ka tashi ka kimtsa jikinka kaje ku gaisa da Mamma.". Mikewa yayi yace."Ai tare zamuje kema ki gaisheta." cike da farin ciki nace"Gaskiya nayi farin ciki dama kwana biyu nayi kewarta." Yana kokarin fito da kaya daga wardrobe yace."Na manta ban fada miki ba jiya nida Shatima munje can bangaran mahaifanki munyi gaisuwar surukai." Murmushi nayi nace"Amma naji dadi sosai ina fata suna nan lafiya."? Yace."Lafiyarsu lau yana da kyau idan kin fito daga gurin Mamma kije ku gaisa ko." Cikin farin ciki nace"Nagode.'' Tsaf! muka shirya muna fitowa falo muka ga mata a zaune!! gabana ne ya fad'i!! nayi saurin sunkuyar da kaina kasa ina mamakin abinda ya kawo ta. A nutse muka zauna kan kujera muna gaisheta! ta amsa fuska a sake sai dariya take tana tsokanata ni dai gabadaya hankalina bai kwanta da ita ba.. A nutse yace."Ina fata baki dad'e a zaune zaman jiran mu ba." girgiza kanta tayi tace"Ban wani dade sosai ba nazo na samu hadimai na gyare-gyare sune suka tabbatar min da cewar kuna ciki baku fito ba shiyasa na zauna zaman jiran fitowarku.". Ajiyar zuciya ya sauke yace."Ina fata dai lafiya." Cikin yar dariya tace"Lafiya lau! nazo ne domin na kar'bi zanin gadon da kuka kwanta a kai ana so ayi shela saboda kowa ya tabbatar da nagartar matar daka aura, alhamdullihi dai Lawisa ta fitar iyayenta kunya." Tun kafin ta 'karasa maganar gabana ya dinga bugawa! wannan wace iriyar rayuwa ce ace da sassafe azo ace ka bada zanin gado, a gaskiya wannan al'adar bata da kyau! haramune fallasa sirrin aure. Uwargida Huwaila tace"Ali ya naga kayi shuru ne ina fata dai wannan yarinya ba fanko bace."!!!! Kallonta yayi a cinkushe! yace."Wai don Allah hajia ba zaku watsar da wannan al'adar ba! meye amfanin ta"? Cike da mamaki! tace"Al'ada mai tsohon tarihi da muhimanci kake cewa masarauta ta watsar! haba Aliyu! wannan magana sam bata dace ta fito daga bakin ka ba tunda dai kasan tun kafin a haifeka wannan al'ada take shin wai kodai baka sameta cikakkiyar mace bane."!!! A fusace! take maganar.. Yace.''Hajia wannan yarinyar bana kokwanto a kanta koda jini ko babu jini Sumayya kamila ce ba zata sarayar da budurcinta a hanyar banza ba, inaso na sheda miki cewa ni Ali ban taki Sumayya ba saboda tana cikin rashin tsarki koda mu'amula ta aure ta shiga tsakanina da ita to nayi al'kawarin babu me ganin sirrina."'' Cike da mamaki take kallonsa kafin tace"Wannan dai ba magana bace Ali idan kana so jama'a su dauki matarka da mutunci to ka dauko min zanin gadon da kuka kwana a kai a duba aga zahirin abinda ke faruwa dan gaskiya ni ban yarda da maganarka ba kawai kana kareta daga barin surutun mutane."! Kuka ne yake kokarin kwace min da sauri na bar gurun ina shiga daki hawaye suka wanke min fuska zubewa nayi kan gado bakin cikin duniya ya sheni........ shikkenan kuma yanzu za'a sani a bakin duniya! tunda na ganta dama nasan ba alkairi ne ya kawota ba, kwanciya nayi ina tunanin abinda zai faru anan gaba. Rai a b'ace! ya shigo dakin ya tsaya a kaina da fadin"Tashi muje." Girgiza kaina nayi tare mi'kewa zaune. Yace."Bangane abinda kike nufi ba, nace ki tashi muje sashen Mamma kamar yanda mukayi niyya! Ina magana hawaye na zuba nace"Kaje kawai ba zan iya zuwa ba." jikinsa ne yayi sanyi yace."Kiyi hakuri ki daina kuka koda mutanan duniyar nan za suga duhun ki akan wani abu ni nayi miki alkawarin baki kariya sai inda karfina ya 'kare! na riga nagane abinda suke nufi to koda nayi auratayya dake babu wanda zai ji ya gani wannan banzar al'adar ba dani ba." A sanyaye nace"Ni dai gwara ka nuna musu domin su tabbatar ni budurwa ce bana so mutane suyi min wani kallo na daban.'' Tsaki yaja ba tare da yace min wani abu ya hau duba wayarsa. Wayar ya kara a kunnansa yana gaisheta, jin muryarta yasa na nutsu ina jinta tana tambayata yace."Gata nan a kusa dani yanzu zan kawo miki ita ku gaisa." cikin jin dadi tace."To nagode Babana." Yace."Mamma yanzu nan Uwargida ta fita daga sashena wai tazo kar'bar zanin gadon da muka kwanta a kai." Fulani tace"Ikon Allah yanzu da kanta taje a maimakon ta tura Jakadiyarta." Yace."Mamma nifa wannan tonan asirin ne bana so tazo tana wasu maganganun da basu dace ba! raina ya 'baci sosai da abinda tayi wannan dalil.......Katse shi tayi tace"Babana sai wata irin magana kakeyi shin wannan yarinya da budurci ka sameta ko kuwa."? kai tsaye yace."Nifa babu abinda ya shiga tsakanina da ita." A d'an sanyaye tace"Saboda me Baba na."? yace."Sabida bata da tsarki shiyasa! Fulani shuru tayi tana nazarin maganarsa! tace"Babana sai dai kayi hakuri da wannan abu haka al'ada take tun zamanin iyaye da kakanni banji dadin faruwar wannan lamari ba to amma babu komai duk ranar da Sumayya tayi tsarki ka kwanta da ita inaso ka bada zanin gadon a duba sheda. Cike da takaici yace."Mamma bana jin zan iya bayyana sirrina.''' cikin mamaki tace"Me yasa ka bayyana sirrinka da Lawisa babana yanda kake hanya-hanya yasa jikina yayi sanyi akan yarinyar nan! duk da bana kokwanto a kanta amma rashin amincewarka yasa ni zargin wani abu. Jin abinda take fada yasa jikina ya mutu lallai ina cikin kalubale mutukar ba'a ga jinin amarcina ba! Yace." Mamma bana so na dinga jayayya dake akan maganar nan dan Allah ki cireta a ranki Wallahi ko haufi ba nayi zan samu budurci a tare da sumayya saboda haka dan Allah ki bar wannan magana. Tace."To shikkenan na bari amma yanzu yanzu zanyiwa tufkar hanci sabida bana san surutai da qananun maganganu irin na mutane Zan kira Ita uwargidan mu zauna akan maganar......Yace."Yawwa haka shine yafi dacewa." Insha Allahu yanzu zamu shigo da Sumayya ." tace"To shikkenan sai mun shigo." Sallama sukayi da ita ya kashe wayar yana kallona.....wasa na shiga yi ya yatsuna, yace." Hankalinki ya kwanta ko."? kaina na daga masa, yace." To kije ki wanke fuskarki ki sake sabuwar kwalliya bana so muje gurin Mamma ta fahimci wani abu." mi'kewa a sanyaye na nufi toilet ina addua akan mak'iyana dake cikin masarautar.......... 2/11/21, 2:28 PM - ???: *SADAUKAWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 94 A nutse na fito jikina nad'e da lifaya, mirmushi yayi ya mike tsaye kallon da yake min yasa duk na tsargu, d'an harararsa nayi nace"Naga kana kallona ko da akwai matsala ne."? still da murmushi a fuskarsa yace."Baki da makusa my love kinyi kyau har na kasa tantance tsakanin keda Lawisa wace tafi iya ado da kwalliya." shuru nayi dan bana so muna magana yana kiran sunanta, hannuna ya rike muka fita, nan muka samu hadiman dake gurin suna ta aikace-aikace ganinsu besa yayi yunkurin sakin hannuna ba a haka muka dinga ratse su yana amsa gaisuwarsu dan ni kunya ce tasa na kasa dago da kaina na kallesu. Tana hakimce akan kujera tayi ado sosai ni kaina dana ganta sai dana razana saurin daidaita nutsuwa ta nayi muka karasa inda take hannuwan mu a hade, sai da zamu zauna ne ya sake ni, kallonmu tayi babu yabo babu fallasa a tare da ita, a nutse nace"Ranki ya dade barka da safiya kin tashi lafiya."? babu walwala ta amsa. falon yayi shuru na kusan minti biyar kafin yayi gyaran mirya dukkaninmu muka kalleshi yace."To Alhamdulillahi nagodewa Allah daya nuna min wannan rana mai albarka a tare dani daku bakidaya ina rokon Allah ya tabbatar mana da alkairi yanda Allah ya had'amu zama a duniya ina rokon Allah ya hadamu zama a aljannar firdausi." Nice kawai na amsa da ameen, ya cigaba da cewa" Lawisa da Sumayya dukkanin ku na aureku ne da ra'ayin kaina saboda haka inaso na tabbatar muku da cewa babu wacce tafi wata a gurina sai wacce tafi kyautata min gami da bin umarnina! ina sonku ina kaunarku kuma ina bukatar ku zauna lafiya da juna, ke Lawisa kece babba yana da kyau ki kama girmanki bani da matsala da Sumayya domin nasan halinta zata girmamaki ta kuma mutuntaki! ki ajiye maganar sarauta a gefe bana so ki dinga nuna mata asalinki ki dinga daukar kanki daidai da ita Sumayya ba mutuniyar banza bace." Wani irin kallo Lawisa take masa ya za'ayi ma ta daidaita kanta da baiwa abinda ba zai t'aba yiwu bane." Ya cigaba da cewa" Kowacce na zaune a gurinta ban amince ku dinga ziyartar junanku ba sai da k'wakkwaran dalili ina ganin hakan shine maslaha a gare mu baki daya. daga karshe nake mana adduar fatan alkairi tare da rokon Allah ya dawwamar mana da zaman lafiya a zamantakewar auranmu." Cikin nutsuwa na amsa da "Ameen ya rabbi." Ajiyar zuciya ta sauke a cinkushe tace"Naji ni kayi min fada amma ita ba kace mata komai ba.'' Cikin kulawa yace."Bangane abinda kike nufi ba."? "Kace na dauki kaina daidai da ita na zauna lafiya da ita ka nuna min muhimancinta amma me yasa ita baka nuna mata cewa ina da muhimanci a tare da kai ba." Shuru yayi yana kallon kasan kafet! ni kam mamaki ta bani na dinga kallonsa ta gefan ido ina jiran naji abinda zai ce, a nutse ya kalleni yace."Ke Sumayya Lawisa nada mahimanci ba sai na fada miki ba ki bata girma a matsayinta na uwargidanki." Murmushi nayi nace"To insha Allah zan cigaba da bata girma da muhimanci, ranki ya dade kada ki damu ni ba zan raina ki ba Insha Allahu." Murmushin dole tayi ta kauda kanta gefe, yace."Lawisa kin gama kwana biyun ki yau bangaran Sumayya zan tare nayi mata nata kwana biyun." Ya mutsa fuska tayi da kyar tace"To shikkenan." yace."Ina fatan kina shan magungunan dana baki kuma ina fatan gurin ya dena zafi."? Cikin shagwa'ba tace"Wallahi har yanzu yana zafi da kyar ma nake tafiya ni kam gwara ka kwana a gurinta ko na huta." Dariya ya kyalkyale da ita yana kallonta tana matso hawaye. Takaicin abinda suke yasa na mike a dake! nace"To ni zan tafi ." da sauri ya kalleni ya wani marairace fuska yace."My love kina jina da Lawisa ko wai ni take kora daga sashenta sabida na ina jin dadi da ita." kamar na kwad'a masa mari saboda 'bacin rai! na ta'be bakina had'e dayin gaba ba tare dana tanka masa ba." Da sauri yace."Kada ki fita kizo ki taimaka mata da ruwan zafi! idan yaso itama sai ta ramawa kura aniyarta." Murmushi nayi na juyo ina kallonsu nace"Haba ai kai da ka 'bata kai zaka gyara ni meye nawa wallahi ranki ya dade kada ki yarda ki barshi ya fita sai kin hukuntashi." Dariya ya dinga yi yana kallona ita kam kallon mamaki naga tana yi min, na saki mirmushi duk dan na nuna mata cewa banji haushi ba nace" Sai anjima." juyawa nayi da sauri na fita daga falon da kyar na k'arasa gurina na zauna kan kujera tare da rufe fuskata da hannuwana! innalilihi na dinga ja a zuciyata kafin na samu sassauci cikin sanyin jiki na mike na nufi daki kwanciya nayi ba tare dana warware lifayar jikina ba, tsabar bacin rai da nake ciki ya dinga nema ya sa min ciwon kaina hawaye ne ke kokarin zubowa ina mayar dasu, nasan idan basu zuba ba bazan samu kwanciyar hankali ba, sai kawai na barsu suka dinga zuba a kuncina haka na dinga juye-juye a bed din ina mamakin kaina! kishi ne dani irin mai wahala idan banda abin son zuciya irin nawa menene na damuwa dan yayi auratayya da matarsa.........Zuciyata tace"Duk da haka abinda sukayi miki basu kyauta ba abin kamar da akwai cin fuska a ciki, meye dan sunyi rayuwar aure sai sun fito suna fad'a miki gabad'aya ita dashi basu da addini........Hannu nasa na goge hawayen fuskata na gyara kwanciyata rufin dakin na tsirawa ido ina tunani yanzu yana can yana rarrashinta dan naga sai wani lalla'bata yake kafin na fito, gaskiya halin namiji sai shi, wallahi banta'ba tsammanin zai so Lawisa ba sai gashi lokaci guda yana nuna mata kauna da kulawa a gabana. Agogon bango na duba har nayi mintina ar'bain da fitowa daga sashen bai shigo ba, na sake jin 'bacin raina ya nunnku! rufe idona nayi na cigaba da nanata kalmar innalillahi wa'ina ilaihi raji'un! da haka bacci mai nauyi ya dauke ni. Bacci nayi sosai sai wajejen la'asar na tashi! na dinga mamakin tsayin lokacin dana dauka ina bacci! jikina a mace nai wanka na kimtsa jikina kana na tsaya kan dadduma domin gabatar da sallah! ban tashi daga kan daddumar ba sai dana gabatar da la'asar tukkuna na tashi daddumar na ninke tare da ajiyeta a inda aka tana da kai tsaye falo na nufa ba tare da na cire hijab din jikina ba. Suna zaune a guri guda ganina yasa duk suka mike tsaye, cike da mamaki! nace "Meye haka daka ganina duk kun razana." Sunkuyar da kansu sukayi ba suce komai ba, nace"Daga yau dan Allah kada wacce ta sake ganina ta razana kuma bana so kuna sa gwiwarku a kasa gurin gaisheni." Mariya tace"Ranki ya dade ai dole ne mu girmamaki domin kin cancanta." Nace"Nasan da haka ai ni bana so ku d'aura min izzah ne! duk girman da zaku bani ku bani mustad'a'a kada yayi yawa." Gabad'ayansu suka amsa da "To ranki ya dade insha Allahu zamu kiyaye." ajiyar zuciya nayi tare da zama kan kujera, Sakina tace"Ranki ya dade ko a kawo miki abinci nan."? A nutse nace." Me kuka girka." ? "Ranki ya dade damubun shinkafa ne." murmushi nayi nace"Aikuwa kun burgeni wallahi jeki kawo min." da sauri ta mike ta nufi gurin cin bincin, waya ta na cigaba da dubawa har ta gama jera kayan abincin a teble din dake gabana, Kokarin zuba min take na ajiye wayar da fadin"Kuje kawai zan zuba da kaina." godiya sukayi min da sauri suka fita. Ina kokarin bud'e fulas naji zubowar abu a pant d'ina, gabana ne ya fad'i! da sauri na mi'ke na shiga toilet domin na tabbatar da zargi! ina tsugunawa shine ya fara zuba! "shikkenan! abinda na fad'a kenan ina girgiza kaina, kai amma wannan abu bai kyauta ba! ruwa nasa na wanke jikina na gyara gurun na fito, na kimtsa jikina, falon na koma na zauna gabadaya jikina ya mutu da ganin al'adata ango naso ya gwangwaje abu yayi masa cikas! ta'be bakina nayi a zahiri nace" Gwara haka sai muga 'karyar kwad'ayi! ko yaya zaiyi idan ya ankara! dariya nayi na girgiza kaina fulas din abincin na bud'e! 'kamshi ya bugi hancina dambun yayi shar-shar dashi yaji gyada da zogale sai kamshin man gyad'a yake, da sauri na zuba wanda zai isheni nayi bisimillah a nutse na fara ci ina gyada kaina tamkar kunnena ya tsinke dan d'adi gaskiya sunyi kokari sosai domin dambun ba 'karamin dadi yayi ba. To a haka na kasance a sashena ni kad'ai har bayan isha'i bai shigo ba raina ya 'baci mutuka gashi girman kaina ya hanani kiransa a waya babu irin sa'ke-sa'ken da zuciyata ba tayi min ba, daga karshe dai daki na shige nayi shirin kwanciya zama nayi gefan gado da romot a hannuna tashar larabawa na kama naga suna drama irin tasu, kawai sai na shiga bargo na kwanta tare da cigaba da kallon film din kasancewar ina dan jin labaraci yasa na dinga fahimta sosai film din ya dauke min hankali! kawai naji an turo kofar dakin. Ido muka had'a dashi yana sanye da shadda fara kal! tasha aiki kafarsa sanye da bakin takalmi kansa kuwa hula ce 'baka irin mai tsayi wacce ake d'ora nad'i a kai. Mi'kewa zaune nayi ina masa barka da zuwa! ya zauna kusa dani yana kallona yace."Kinji shuru ban shigo ba ko."? kaina na daga ina kallonsa, sosai yayi min kyau a ido kayanmu na hausawa nayi masa kyau sai dai bai fiye sakawa ba yafi amfani da 'kananu ......Ya cigaba da cewa"Bayan barin ki gurin Lawisa nida Shatima muka nufi can masarautar kazaure domin gaisuwa da bangajiya dawowar mu kenan yanzu." Nace"Ayya! sannu gaskiya kunsha hanya dama nima da naji shuru baka shigo ba nace mybe ko kaje asibiti ne ashe tafiya me nisa kukayi.'' 'Kure ni da ido yayi yace."Da kikaji shuru ban shigo ba me ya hanaki kiran waya ta." ? shuru nayi dan saboda nasan ban kyauta ba." Yace."Lawisa tafi ki wayo ke kuwa kin zauna girman kai kin dauki kanki daidai dani kina ganin idan kin kira wayata kin zubar da ajin ki ko.'?? Da sauri nace"Wallahi ba haka bane nima yini nayi ina bacci sai gefin la'asar na tashi sai nasa wayar a chaji dama kuma yanzu nake tunanin kiran ka." Ta'be bakinsa yayi yace."Kyaji dashi dai.'" a sanyaye nace"Dan Allah kayi hakuri idan hakan ya 'bata maka rai." Sakin fuskarsa yayi yace."Na yafe miki yanzu dai ina bukatar abinci.'' cikin jin nauyi nace"Sai da nayi maka yanzu." cike da mamaki yake kallona yace."Kada dai kice min baki ci abinci ba har yanzu." "Naci abincin mana." yace."Karya kikeyi kin zauna da yunwa tun safe." Nace"Wallahi naci abinci na koshi dan kafin na tashi a bacci hadimai sun shirya komai." Ajiyar zuciya ya sauke yace."Amma kuma kika ce zaki shiga kicin." ina wasa da yatsun hannuna nace"Ai nafi bukatar na girka maka da hannuna domin na samu lada." Kallona yake yana murmushi yace."To nagode amma kada kiyi abu mai wuya kiyi min indomee.'" cike da mamaki na kalleshi! girarsa ya daga min girgiza kaina nayi nace"Ranka ya dade indomee ba abincin bace ba zata gamsar da kai ba." Shuru yayi yana kallona yace.'' Okey to ai bana so ki wahala ne shiyasa nace kiyi min indomee amma tunda kina bukatar ki bani abinci mai gamsarwa babu damuwa nima nafi son haka naci na koshi na samu kwarin jikina." Yana min wani irin kallo ya karashe maganar, murmushi nayi na mike a nutse nace"Bari na shiga kicin din! mikewa yayi da fadin"Okey kafin ki gama bari na shiga gurin 'Yar uwarki muyi sallama." shuru nai masa muka fito tare ni na nufi kicin shi kuma ya kama hanya ya fita. Fatan doya nayi masa na gama aikina tsaf na shirya masa duk abinda zai bukata tire din abincin na kai dakina na ajiye a gefa agogo na duba ina mamakin dad'ewarsa daga zuwa yin sallama ya share gindi ya zauna awarsa daya da fita, zuciyata tace watakila yana gurun mahaifiyarsa ki dinga yi masa uzuri! ajiyar zuciya na sauke tare da dauke kaina daga kallon agogon dake kafe a dakin............Mikewa nayi na shiga toilet domin sake kimtsa jikina pad na sanja na fito sai na ganshi a zaune gaban kayan abincin yana bud'awa, da sauri na karasa kusa dashi, yace."Kinji shuru ban dawo ba ko."? "Umm." nace, yace." Ina can gurin Mamma! ga wannan ma tace a kawo miki wai ke kadai zaki ci kada ki bani." akushin dake gabansa na kalla! ya mi'ko min, nasa hannu na kar'ba a nutse na bud'a kaza ce guda anyi mata dahuwar magani sai kamshi take! da sauri na rufe ina kallonsa, hankalinsa nakan abincin gabansa, da sauri na kar'ba ina kokarin zuba masa yace."Mamma ta huttashe dani da kazar amarci." Kallonsa nayi da mamaki a tare dani! yace."Ai na bud'a na gani ta dafo miki kaza tayi lugub! wai harda cewa ko roma kada na d'and'ana." yanda ya fad'i maganar a sakarce ya bani dariya nace"Ban hanaka ci ba idan kana bukata sai na baka." "Kawai ki bud'e ina bukata." nace"To shikkenan ka gama cin abincin." Shuru yayi yasa spoon din dake hannunsa a nutse ya fara cin abincin...........Kad'an ya rage nace"Ka daure ka karasa ladan ka." girgiza min kai yayi yace."Na koshi haka ko kina so na kasa moruwa."? girgiza kaina nayi na mika masa tissue ya goge bakinsa, nace"To ya na zuba maka roman kazar ne."? ya mutse fuska yayi yace."Kici kayanki bana jin zan iya cin wani abu yanzu." Nace"To shikkenan nima ba yanzu zanci ba sai da safe zansa a d'umamin." "Okey." yace ya dan kishingida yana kallon guri guda, a zuciyata nace"Abin yazo kenan! mikewa nayi na harhad'a kwanakun abincin na dauka na fita dashi, firji na kicin na bude nasa kwanon kazar na rufe da safe nake so naci a tsanake.........Dakin na koma na sameshi a inda yake har yanzu kuma guri guda yake kallo, sai dana zauna sannan ya dago kai yana kallona.... *Na kudi ne* Koda zaki ganshi a gruop na sata ne idan kina bukatar ki biya kudin karatu ga yanda abin yake....Vip gruop#600 normal group #300 account... 0542382124....Binta umar gtbank....idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:28 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 96 Fulani na kashe wayarta ta kira Jakadiya tace maza taje fada ta shedawa Maimartaba cewa tana son magana dashi. Jakadiya da sauri ta tafi domin cika umarnin uwar gijiyarta, Maimartaba tunda yaji wannan kiran na gaggawa yasan ba lafiya ba. Koda Maimartaba yazo ta sheda masa abinda yake faruwa ransa ya baci yace"Yanzu ashe har yanzu ba daina wannan al'adar ba."? Tace."Wallahi basu daina ba sunayi shiyasa na kira ka na sheda maka abinda ke faruwa saboda bana so su watsa mummunar magana akan wannan yarinyar babana ya tabbatar min da cewa babu wata mu'amular aure data shiga tsakaninsa da ita saboda tana cikin hali na rashin tsarki! yanda yayi min bayani haka yayi wa uwargida bayani amma ta nuna bata yarda ba tana ganin kamar yana kokarin kare matarsa ne shi kuma ya tabbatar min da gaskiyar magana." Maimartaba yace."Na rasa ranar da Huwaila za tayi hankali yanzu ace da girmanta da komai taje kar'bar zanin gado ai wannan zubar da kima da mutunci ne da kin fada min tun na kan Lawisa dana dauki mataki amma yanzu ma bata 'baci ba da kaina zan shiga sashenta na gargad'eta akan abinda suke shirin aikatawa." Maimartaba na shiga sashen Uwargida ya samesu su biyu ita da Hajiya Karima sai 'kus-'kus suke, ganinsa yasa duk suka nuna alamun rashin gaskiya, a nutse ya zauna yana kallonsu sai rige rigen gaisheshi suke. Ya dinga amsawa yana nazarinsu duk alamun rashin gaskiya ya bayyana a tare dasu. Ya kalli Uwargida rai a 'bace! yace."Yanzu abubuwan da kukeyi a masarauta shine daidai."? Sunkuyar da kanta tayi a sanyaye tace"Allah ya taimakeka me yake faruwa ne."? Yace."Ashe tambayata kike abinda ke faruwa bayan kin san komai." Tace."Ranka ya dad'e a gafarce ni nasan akan abinda kake magana kasan wannan abu al'adar masarauta ce babu laifi dan duniya ta tabbatar da nagartar matan da Magajin sarki ya aura Ita dai Lawisa kowa ya tabbatar cewa cikakkiyar macace ita wannan d'iyar bayin ce bamu tabbatar ba tunda babu yanda banyi dasu ba akan su nuna min abin kwanciyarsu suka qi kaga wannan na nuna mana cewa akwai lauje cikin nadi watakila yarinyar nan ba cikakkiyar mace bace." Cikin takaici yace."Huwaila wannan abun da kuke jahilci ne tsantsa, a shakarun baya da masarauta ta mayar da abun al'ada akwai jahlici da duhun kai a tare da ita, yanzu kai ya waye muna da ilimin addini daidai gwargwado to me zai sanya mu dinga fallasa sirrin aure! to daga rana irin ta yau na soke wannan al'ada kuma kada naji kada na gani wata a cikin ku ta tayar da wata magana akan matar Ali ba lallai sai jini ya fita a jikin mace za'a san budurwa ce ni wannan yarinya Sumayya bana shakka akanta saboda haka magana ta mutu anan ba na ganku kuna magana kasa-kasa ba to mutukar naji maganar nan ta watsu dukkanin ku sai na dauki mataki akan ku."" Hakuri suka shiga bashi suna sunkuyar da kansu, mikewa yayi ya barsu gurin ba tare da ya tanka musu ba. Yana fita Uwargida taja tsaki tana girgiza kafarta tabbas Fulani ce ta turoshi yazo yaci mata mutunci.....Hajiya Karima tace"To wai da yazo yana wannan fad'an waye ya fada masa halin da ake ciki ne."? cikin takaici tace"Waye zai fada masa idan ba Fulani ba itace ta turoshi yazo yayi mana tujara." Hajiya Karima taja tsaki da fadin"Kin san Allah Huwaila na tsani na bude ido na ganta da ina da yanda zanyi a kanta to da tuni nayi shegiyar mata ce da asiri baya cin jikinta. Uwargida ajiyar zuciya ta sauke tace"Babu abinda banyi ba amma na kasa tasiri a kanta Fulani ta riga tayi nisa tasha gabana tunda itace mai d'a namiji ai sai abinda na gani duk abinda Maimartaba yake da umarninta baya san 'bacin ranta ita da d'anta yanda yake nuna mana rashin kulawa nida 'ya'yana yana damuna mutuka wallahi na rasa yanda zanyi na tarwatsa rayuwar su ita da d'anta. Hajiya Karima cikin 'bacin rai tace"Huwaila sai dai kiyi hakuri kina gani dai Muddibo garin yunkurin 'kwatar hakkinsa aka kasheshi muna ji muna gani muka hakura muka rasa shi! kema hakuri zakiyi ki zubawa sarautar Allah ido idan kuma kina da wata hanya sai kibi ki 'kwaci hakkin ki." Cikin damuwa tace"Bani da wata hanya da zanbi dik hanyoyin da nake bi sun toshe amma dole zamu zauna da 'ya yana mu yanke shawara a tsakaninmu." Hajiya Karima tace"Hakan yayi ni zan tafi gurina sai mun sake haduwa." Uwargida ta mike domun yi mata rakiya, suna tafiya suna tattauna yanda za'ayi su cutar Fulani da d'anta Hajiya Karima na isa sashenta kiran Lawisa tayi a waya tace"Lawisa kiyi rawa kiyi juyi kishiyarki fanko ce dan ba'a samu shedar budurci a tare da ita ba saboda haka ke din kin zama abin alfahari a kan kishiyarki. Lawisa farin ciki ya rufe ta ta dinga dariyar murna tana fad'in"Gaskiya Hajiya naji dadin wannan labarin na kuma yi alfahari dan haka yau na tabbatar da cewa nice matar da Yarima zaiyi tunkaho da ita." Hajiya Karima na dariya nishadi tace"Ai shiyasa na kasa hakuri nace lallai sai na kira ki a waya na sheda miki saboda haka ki nutsu ki kwantar da hankalin ki kicigaba da zaman aurenki lafiya amma kada ki manta da dubarun dana koya miki kinji ko." Tace"Nagode sosai hajiya insha Allahu ba zan manta ba." sallama sukayi kicin nishadi da walwala taje tai wanka ta d'and'ansa ado ta hakimce akan kujera tana jiran shigowarsa. Koda ya shigo kasa dauke idonsa yayi daga kanta, ya zauna kusa da ita suna gaisawa! tana fari da ido tace"Ranka ya dad'e ina ta yaka jajen abinda ya faru. Hankalinsa ya mayar kanta yace."Wane abune ya faru kike min jaje''? Kai tsaye tace"Shedu sun sheda cewa matarka ba budurwa bace."!! wani banzan kallo yayi mata yace."Ke waye ya fada miki hakan "? cikin rashin wayo tace" Yanzu hajiyata ta kira ni a waya take sheda min." Kai tsaye yace." 'Karya take." cikin mamaki tace." Hajiyan ce ke 'karya."? kansa ya daga rai a 'bace yace." na fada 'karya tayi miki ni nasan wacece Sumayya na hana zanin gado ne saboda bana son tonan asiri shine suke zargin rufa mata asiri nayi wanda kuma ba haka bane sumayya cikakkiyar budurwa ce kamar ke." Murya na rawa tace"Gaskiya banji dadin maganganun ka ba aiko hajiya bata haifeka ba yana da kyau ka girmamata bai kamata ka kirata da makaryaciya ba." Mi'kewa yayi ya hau sama ba tare da yace mata komai ba. Hawaye suka wanke mata fuskarta, tunanin take akan dalilin da yasa bai bada zanin gadon Sumayya ba, wato itace baya so shiyasa ya fallasa sirrinta! koda yake ai itace tace lallai sai an fita dashi an nunawa duniya, hannu tasa ta goge hawayen fuskarta ta bishi saman. A kwance ta sameshi bacci na kokarin daukarsa, zama tayi kusa dashi a sanyaye tace"Ina so muyi magana." Hannu ya daga mata ransa a bace yace." Kin ta'ba min rai saboda haka ba zan saurareki ba sai na huce."! Cike da mamaki! tace"Saboda kawai nace Sumayya bata da budurci shin........Mari ya kwad'a mata yana tsuma yace"kada na sake ji kin fadi wannan kalmar akan Sumayya Wallahi duk sanda na sake ji sai ranki ya 'baci! ki tashi ki fitar min daga daki."!!!!!! Lawisa ido ta zura masa tana mamakin marin da ya kwada mata Zabura! yayi a kanta, da sauri ta sauka daga gadon ta fita daga dakin tana kuka. Bacci ne ya daukeshi mai cike da mafarkai marasa dadi da ma'ana. Ni kam tunda naje na samu iyayena cikin koshin lafiya na watsar da damuwar dake damuna muka yini cikin walwala da farin ciki, sai biyar na yamma na koma gurina, na samu ko'ina tsaf kamshin turaran wuta sai tashi yake a ko'ina, wanka nayi na kimtsa jikina ina fitowa falo na samesu a jere gaisheni sukayi na amsa cikin sakin fuska nace"Kuna iya tafiya tunda kun gama aikin ku." sallama sukayi min suka fita, kafin na zauna sai da na duba agogo naga bakwai shaura, zama nayi kan kujera na dinga tsammanin shigowarsa a lokacin, bai shigo ba sai wajejen tara da rabi, koda ya shigo kasa gane kansa nayi dan magana ma sama - sama yayi min ya shige daki, minti biyar nabi bayansa na sameshi a kwance, a sanyaye nace"Baka da lafiya ne."? kallona yayi da fadin"Me kika gani."? nace"Naga jikinka babu kwari ne." tsaki yaja yace."Wannan abun naki ne ya 'bata min rai bayan haka kuma Lawisa ta kara min wani." A sanyaye nace"Sai hakuri." kallona yay yace."Kwana nawa yake kafin ya dauke."? ban 'boye masa ba nace"Hudu ko biyar." ajiyar zuciya ya sauke yace."Yanzu dai yau kwana nawa."? nace"Kwana daya." 'bata rai yayi yana kallona, dariya nayi nima na tsira masa idona, yace"Dariya kike min saboda mugunta ko."? girgiza kaina nayi alamun A'a. Mikewa yayi tare da rike hannuna "Muje toilet kiyi min wanka." ban masa gardama ba na rike hannunsa muka nufi toilet din, Abin mamaki zir yayi bai bar komai a jikinsa ba, na rintse idona da fadin"Dan Allah kasa wandonka." jawo ni yayi muka fada cikin kwamin wankan ya hau tu'be min tufafin jikina! na dinga hanashi ina kokarin fitowa yana mayar dani! gajiya nai na kyaleshi ya tu'bemin kayan jikina tas, murya na rawa nace"Dan Allah ka bari na fita a ruwan nan kaga da najasa a jikina kada na 'bata maka." Girgiza kansa yayi yana cigaba da shashshafa jikina! "Ba zan iya bari ki fita ba kawai ki dauki soso da sabulu ki cud'ani! hannunsa na cire daga breast dina nace" Ka bari to nayi maka wankan." Kwanciya yayi cikin kwamin wanka na dauko soso da sabulu na fara cud'ashi! kasa hakura yayi ya janyota tsam ya matse a jikinsa tare da sa bakinta a nasa.......haka muka lalace a toilet tsayin lokaci mai tsayi, kafin muyi wanka mu fito................A daran ranar na bashi kulawa sosai sai da na tabbatar da cewa ya samu biyan bukata sannan hankalina ya kwanta muka kwana cikin farin ciki da kaunar juna....... *Na kudi ne* Kada ki karanta mun littafi idan baki biya ba! keda kika futa da littafin keda Allah idan kina bukatar ki biya ga yanda abin yake....Vip group #600 normal gruop#300 account... 0542382124.....Binta umar gtbank idan kati zaki turo #400 sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:28 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 97 Kiran wayar Lawisa ne ya tayar damu daga bacci! wayar ta karaci ringing d'inta ta mutu bai daga ba, zaune na mike ina kokarin kare jikina da bargo wani kiran ya sake shigowa, a maimakon ya daga wayar sai naga ya mike daga shi sai karamin wando ya nufi toilet, wayar na dauka ina dubawa da mamakin wanda yake buga wannan kiran da sassafe! My Lawisa, sunan dana gani kenan yana yawo kan fuskar wayar, da sauri na ajiye inda take ina mamakin al'amarin, koda wayar ta katse bata sake kira ba, na tsirawa kofar toilet din ido ina fargabar shiga saboda nasan halin fitinarsa........'daure da towel ya fito da wani a hannunsa yana goge jikinsa, kai tsaye wardrobe ya nufa domin kintsa jikinsa, ina kokarin mikewa kira ya sake shigowa wayarsa, sai naga ko kallon wayar beyi ba yana ta kokarin fito da kayan sa, a sanyaye nace"Ranka ya dade ana kiran wayarka tun dazu." Juyowa yayi ya kalleni babu walwala a tare dashi yace."Ina da kunne ai."! kallonsa nai ina mamakin yanda ya amsa min magana kamar wanda nayi wa laifi! jiya lafiya lau muka kwanta muna soyayya amma ya tashi da d'acin rai! girgiza kaina nayi na wuce toilet ina mamakin baud'ewar halinsa. Tsaf na fito na sameshi ya shirya dakin sai kamshin turarukansa yake yana zaune a gefan gado yana daura igiyar takalminsa, na 'karasa gurin a sanyaye nace"Fita za kayi ne."? Shuru yayi min ya cigaba da abinda yake.........Zama nayi kusa dashi duk jikina ya mutu da abinda yake nace"Dan Allah ka fada min idan laifi nayi maka naga lafiya lau muka kwanta bacci amma ka wayi gari cikin 'kunci da 'bacin rai! gashi laifina yana nema ya shafi Wata. Babu fara'a a fuskarsa yace." Sumayya baki min komai ba raina yana 'baci akan wannan jinin da kike dan wulakanci bai tashi zuwa ba sai a lokacina gashi daga yau ranar ki ta amarci ta 'kare." A sanyaye nace"Ranar amarcina bata 'kare ba tunda baka kar'bi budurcina ba har yanzu ina da sauran ranaku masu muhimmanci ka kwantar da hankalinka insha Allahu zaka samu abinda kake so a tare dani." Girgiza kansa yayi yace."Sumayya zanso kema jama'a su sheda cewa ke cikakkiya ce sai dai kash! lokaci ya shige miki yanzu koda na kar'bi budurcinki kin fitar da jini jama'a da yawa ba zasu yarda ba zasu ce 'karye ne idan na tuna hakan raina yana 'baci sosai wannan jinin naki yayi mana illah." 'Kwalla ce ta cika idona nace"Nima zanso masu kokwanto a kaina su tabbatar da cikar mutuncina to amma ina so ka sani hakan ba addini bane al'ada ce idan kai ka tabbatar ka amince da cewa ni d'in budurwa ce shikkenan dama haka ake bukata ka kwantar da hankalinka. Girgiza kansa yayi yace."Ki kyale Lawisa ina so na koya mata hankali ne mahaifiyarta ce ke sheda mata cewa ke din fanko ce shine saboda bata da mutumci ta tunkareni da maganar." Raina ne ya 'baci dajin maganarsa kawai dai na daure bance komai ba ina jinsa sai surutai yake akan Lawisan "Sumayya koda ke d'in fanko ce wallahi kin fiye min mata dubu ciki kuwa harda ita Lawisan wannan dalilin yasa na'ki daukar wayarta. Murmushi nayi cikin zuciyata nace" Namiji kenan a gabana sai nuna min so yake, duk yanda yake aibata Lawisa a gabana gobe ina iya ganinsa yana rawar jiki akanta na riga nasan halinsa sam bashi da al'kibula amma dai na soma zargin yana sona tuna gashi yana jin haushinta akan ta kira ni fanko. Mi'kewa yayi yana kallon agogo, a marairace nace"Yanzu ina ka nufa."? "Zan shiga mu gaisa da Mamma na wuce asibiti." Nace"Dan Allah ka shiga ku gaisa da matarka ka duba lafiyarta meye dan ta kira ni fanko kake jin haushinta." Tsaki! yaja yay gaba ya barni da baki a bud'e! bayansa nayi yunkurin bi sai na tuna da cewar babu suttura a jikina kuma watakila su Mariya na falon, saboda haka sai na juya da jiki a mace na nufi wardrobe domin kimtsa jikina. Magajin sarki yana fita kai tsaye sashen mahaifiyarsa ya nufa nan ya samu Maimartaba suka gaisa Maimartaba cikin kulawa yace." Naga kayi shirin fita aiki baka dauki hutu bane."? Yace."Ranka ya dad'e hutun bashi da wani amfani gwara na cigaba aikina." Maimartaba yace."To babu laifin hakan Allah yayi maka jagora a cikin dukkanin al'amuranka.'' Ya amsa cikin nutsuwa, Fulani tace"Da alama dai bakayi break fast ba ko.'' yace."Mamma kamar kin sani kuwa ina bukatar tea a gurinki." Tace."Ai nasan ka da 'kiwar cin abinci shiyasa nayi magana bari na kawo maka." Yace."To godiya nake Mammana." Maimartaba mikewa yayi da niyyar shiga fadarsa yace."Aliyu zaman fada a gurinka dai ya gagara aiki ya hanaka kazo ka koyi yanda ake mulki." Murmushi yayi yace."Ranka ya dade mulki ai sai ku jajurtattu wallahi ni kwata-kwata bana sha'awar mulki ranka ya dad'e." Maimartaba ya shiga jijjiga kansa yana murmushi yace."Ali kenan! kada ka bani kunya mana! nasan kasan da cewar duk inda mai suna Ali yake jajurtacce ne a fagen ya'ki da iya mulki mai yasa kai ka karaya kake ganin kamar mulki bai dace da kai ba. Girgiza kansa yayi shima da murmushi a fuskarsa yace."Ranka ya dad'e ba wai na karaya bane! ina ganin yanda kake d'auki ba dad'i akan 'yan uwanka dukkaninsu sunsa ido suna ganin kamar mun kar'be mulki daga hannun kowa muna yanda muke so shiyasa nake ganin nan gaba ya kamata a sakar musu su kar'ba suyi ko sa kwantar da hankalinsu. Maimartaba yayi murmushi yana kallonsa yace."Aliyu kenan! ai muma bamu ne muka tilasta lallai sai munyi mulki ba cancanta da nagarta gwamnati ta duba jama'ar gari sukayi mubaya har Allah ya tabbatar mana da mulki a hannun mu! bama hassada da 'bakin ciki idan Allah ya kar'ba daga hannun mu ya bawa wani dama shi mulki ga wani abin hallita baya dawwama Allah shine yake da mulki madawwami." "Kwarai haka yake Allah shi kadai keda mulki babu wani Sarki ko governor ko shugaban kasar da zai dawwama akan kujerar mulki aro aka bashi komai tsayin shekaru sai ya sauka daga kujerarsa bayan nan kuma ya fuskanci kalubalan dake gabansa domin kuwa dole a ranar lahira Ubangiji ya tuhume shi, ranka ya dad'e ina rokon ubangiji Allah yasa sasaauta maka a ranar al'kiyama." Cike da jin dadin adduar da yayi masa ya d'ora hannunsa a saman kansa yace."Allahumma ameeen Aliyu yaron arziki kwarai nagode da wannan adduar taka." Magajin sarki murmushi yayi yana me sunkuyar da kansa......cikin wannan halin ta fito daga kicin hannuna rike da tire na kayan tea. da sauri ya mike ya kar'bi tire din yana yi mata sannu! zama tayi gurin zamanta hankalinta akan mijinta Maimartaba yace." Kinyi tsammanin na fita ko."? tace."Hakane ranka ya dad'e." Yace."Na tsaya muna tattaunawa da Ali yau munyi hira mai tsayi irin wacce muka jima ba muyi irinta ba." Murmushi tayi tace."Kai amma naji dadi sosai ina fatan kayi masa maganar zaman fada." Yace."Nayi masa magana yace shi baya sha'awar mulki." Fulani murmushi tayi tace"Idan kuma Allah ya bashi ya zaiyi." ? Maimartaba na 'yar dariya yace."Nima abinda na gama fahimtar dashi kenan." Kallonsa tayi yana d'an motsa tea tace"Babana idan Allah ya baka mulki ka kar'ba hannu biyu ka gode masa mu kuma zamu yi maka kyakkyawar addua." Yace."To shikkenan Mamma ina godiya da wannan karamcin." Maimartaba ya sauke ajiyar zuciya tare da fad'in "To ni zan shiga fada.'' Fulani mi'kewa tayi domin yi masa rakiya bakin kofa, Magajin sarki fatan alkairi yayi masa, ya cigaba da kur'bar tea din yana nazarin maganganunsu da mahaifinsa ya fahimci Mahaifinsa na so ya gaje shi a mulki shi kuma ko kadan al'amarin baya bashi sha'awa, amma dai zai cigaba da addua akan Allah ya za'bawa rayuwarsa abinda yafi alkairi. To Sai kusa takwas da rabi na dare ya shigo gidan a jigace tarin yunwa da gajiya sun had'u sun dabaibayeshi, kai tsaye gurin Lawisa ya nufa saboda yasan ita dashi, Hadiman dake karakaina a gurin suka dinga zubewa suna gaishe shi, da kyar yake amsawa da ya gaji shuru yayi musu ya wuce su. Cikin ado kamar koda yaushe ya sameta, tana ganin shigowarsa ta mike tsaye da sauri tana masa barka da zuwa, ko kallonta beyi ba ya haye sama! ajiyar zuciya ta sauke tana data sanin abinda ta aikata, a sanyaye tabi shi saman, ta sameshi yana kokarin shiga wanka, sannu da zuwa ta sake masa ya amsa ciki-ciki toilet din ya shige ya barta a tsaye, a sanyaye ta dauko masa jallabiya da gajeran wando ta zauna tana jiran fitowarsa, yana fitowa taje ta tareshi towel din hannunsa ta kar'ba tana goge masa jiki, kyaleta yayi yaje ya zauna a bakin gado, da sauri ta dauko mai ta fara shafa masa, ajiyar zuciya ya shiga saukewa ko yaya mace zata ra'bi jikinsa sai sha'awarsa ta tashi, kallonta yayi yana tunanin ni'imarta, yunwa da da gajiya basa hanashi fitinarsa lumshe idonsa kawai yake yana lasar lips dinsa, Lawisa ta dinga shashshafa jikinsa da gayya ta dinga tsokano shi aikuwa wawura ya kai mata ta fad'a jikinsa suka shiga ya mutsa juna Sai da suka biya bukatar junansu sannan suka saurara, yaje ya sake wanka ya fito itama ta shiga tayi, ta sameshi na kokarin fita daga dakin, sunansa ta kira ya tsaya yana kallonta fuskarsa da alamun sassauci! tace"Kayi hakuri da magana ta akan Sumayya dan na lura saboda haka kake fushi dani." Kafad'a ya d'aga a dakile yace."Nayi hakuri amma ki dinga kiyaye harshenki akan kici fuskar wannan yarinyar zan iya rabuwa dake." Da wani irin mamaki! take kallonsa yace."Da gaske nake miki naga kina kallona inda kina so ki gazgata magana to ki kuma zuwar min da wata maganar banza a kanta." Yana gama maganarsa yasa kai ya fice daga dakin. Lawisa kasan kafet ta zube tana hawaye! yaushe tayi saken da yarinyar nan tayi mata illah! haka! Zai iya rabuwa da ita akan Sumayya shin wane irin so yake mata haka."? kuka ta dinga shar'ba tana girgiza kanta da mamakin al'amarin. Ina shirin kwanciya bacci ya kira ni, a nutse na daga wayar muka gaisa na tambayeshi aiki yace."Lafiya lau ina fata kin wuni lafiya."? nace"Lafiya lau na wuni sai dai nai ta tsammanin shigowarka baka shigo ba." "Kina bukatar ganina ne."? yafada cikin wata irin murya, dariya nayi nace" Sosai kuwa ina bukatarka na saka a cikin idona." Ta'be bakinsa yayi yace."Sai dai kiyi hakuri sai da safe dan yanzu haka a kwance nake." Jikina ne yayi sanyi raina ya 'baci da dizgin da yayi min! dana san zai watsa min 'kasa a ido da ban zubar da kima ta ba, daurewa nayi nace"Okey to sai da safe." kawai na kashe wayar ina jan tsaki sosai naji takaicin maganar da yayi min. Cikin mamaki yake bin wayar da kallo, lallai sumayya wuyanta yayi kauri wato shi ta kashewa waya, aikuwa zai bata mamaki! ya daina kiranta a waya wallahi........mi'kewa yayi daga gurin cin abincin ya nufi daki domin ya kwanta ya huta. Washe gari da safe kafin ya fita aiki sai da ya sake turmushe Lawisa tana kuka da kun'ci irin cin fuskar da yake mata akan sumayya amma hakan be dameshi ba bukatarsa na biya ya karkad'e rigarsa ya 'kara gaba. Lawisa yini tayi tana bakin ciki da takaici ya isheta kawai ta yafa mayafi ta nufi can bangaran iyayenta, ta shedawa mahaifiyarta irin iskancin da yake mata akan kawai ta kira Sumayya fanko. Hajiya Karima tace"To tunda dai bashi da mutunci kada ki sake yarda ya turmushe ki yana biyan bukatarsa akanki amma yana 'kuntata miki akan wata banzar matarsa ai fanko ce idan gaskiya ne ita din budurwace a nuna mana sheda mugani! kada ki sake yarda yazo ya biya bukatarsa sai kinja masa aji ki nuna masa ke mai daraja ce." Lawisa ta dauki hud'ubar uwarta ta dawo gurinta da kudirin daukar fansa akan irin wulakancin da yake mata. Yau sai bayan goma na dare ya shigo, ya sameta a falo a zaune ko kallonta beyi ba ya hau sama, har ya gama abinda yake ya sauko ba tabi bayansa ba, sosai yayi mamakin haka, gurin cin abinci ya zauna ya shiga bud'awa......"Lawisa! sunanta ya kira murya a sama! amsawa tayi ta isa inda yake zaune, a murtuke yace."Wannan wane irin abinci ne."? Itama a cukune tace"Ka duba ka gani mana ai kana da ido."! a fusace! yace."Dan uwarki ni kike fadawa wannan maganar."? Kallonsa tayi tace"Kana yawan cin fuskar uwata kasan dai ita ba sa'arka bac...........Yankin da kwanukan abincin suke a jere ya d'aga ya watso mata ajikinta..."Ni zaki tsaya akaina kina gaya min magana ki tashi a gurin nan ko kuma yanzu ki gane kuran ki."!!!! Lawisa ta dinga duba jikinta tana zubar da hawaye! tace"Wai wannan wulakancin da kake min na menene me nayi maka."? Tsaki! mai karfi yaja ya tura kujera tayi ta baya da sauri ya bar gurin! Binsa tayi da kallo har ya bude kofar falon ya fita, bangaran mahaifiyarsa ya nufa domin ya samu yaci abinci acan amma bai shigar mata da 'bacin rai ba saboda baya so ta fahimci wani abu. Lawisa gurin ta bari cike da tsantsar tashin hankali da nadama Magajin sarki ya samu abinda yake bukata a gurinta shiyasa yake cin mutuncinta to wai ita kadai yake wa wannan iskancin ko kuma harda Sumayya?? da taga babu mai bata amsa, sai kawai ta nufi toilet ta sake wanka ta fito tana kunci tasa kayan bacci ta kwanta........Can cikin baccinta taji an danneta, duk kokarinta na kwatar kanta sai data hakura dan karfi yasa mata ya shiga biyan bukatarsa......Koda gari ya waye kasa tashi tayi saboda wahala, yana kallonta a kwance ya fice daga dakin hankalinsa a kwance. To nima dai sai da nasha jinin jikina ganin har gari ya waye bai neme ni a waya ba, na dinga zargin abinda ya hanashi kiran waya ta kamar yanda ya saba, yau kwana biyu kenan rabon dana sashi a idona, yau dai nasan dole ya shigo tunda nice da girki in yaso idan ya shigo sai naji laifin da nayi nasan dai ruwa baya tsami banza................. *Na kudi ne...!* Koda zaki ganshi a groups na sata ne idan kina bukatar biyan kudin littafin ga yanda abin yake....Vip group #600 normal group #300 idan kati zaki turo #400 sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:28 PM - ???: *SADAUKAWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 98 Jin danshi a pant dina yasa nayi saurin shiga toilet domin na duba tunda dai nasan tun safe jinin ya dauke dan dukkanin sallolina nayi nasan zai iya dawowa tunda dama wani lokacin kafin ya tafi gabadaya yana wasa, pant din na cire ina dubawa banga komai ba na tsuguna tare dasa ruwan d'umi na wanke gurin sai naga alamun d'auraya ne wanda yake biyo bayan jinin al'ada idan ya tafi, ajiyar zuciya na sauke na sanja wani pant din na fito, ina kokarin kwanciya ya shigo, nabi fuskarsa da kallo ina masa barka da zuwa, amsawa yayi a lokacin da yake 'kare min kallo nasan kayan baccin dake jikina ne suka dauke masa hankali dan irin masu fitar da tsaraicine........A kasalance ya zauna kusa dani kafadarsa ta hadu da tawa. sunana ya kira na amsa a nutse ina kallonsa, yace."Naga alamun musulunci a tare dake ina fatan abin naki ya tafi."? D'an 'bata rai nayi nace" Daga shigowarka da abinda zaka fara kenan gaskiya banji dadi maganar nan ba hakan ya nuna min cewa abinda ya shigo dakai kenan gurina." Ta'be bakinsa yayi yace."Kin damu dani ne kuma idan na shigo gurinki me zanyi miki."? Na kalleshi ina danne bacin raina nace"Yau kwananka biyu rabonka da nan kuma ko a waya ka kasa kirana ka tambayi lafiya Haba dan Allah ka dinga koyi da Annabi Muhammad SAW mana." Cikin wani irin yanayi yace." Yanzu dai wa'azi kike min ko gyara."? nace"Duka." Girgiza kansa yayi yace."Shekaran jiya me yasa kika katse min waya." ? A sanyaye nace"Naji kace a kwance kake kana hutawa shiyasa na kashe domin na barka ka huta." "Ke kika kirani ko kuma ni na kira ki."? " Kaine." nafada ina kallon fuskarsa. Yace."To daga yau sai yau kada na sake kiran wayarki muna magana ki katse kinji ko." "To naji indai wannan ne laifina ina rokon afuwa." shuru yayi yana kallon kasan kafet, nace"Muje falo na shirya maka abinci ko."? Girgiza kansa yayi, nace"Saboda me."? Kai tsaye yace."Sabida naci a gurin Mammana." A sanyaye nace"Me yasa kake mana haka? babu amfanin ka dinga zuwa gurin Mamma kana cinye mata abinci alhalin kana da iyali wane irin kallo kakeso tayi mana." "Kece kike ganin hakan bai da amfani ni duk inda naga dama nan zanje naci abinci banga dalilin da zai sanya kuce dole sai abincinku kadai zanci ba." Kallonsa nake gabadaya na rasa abinda zance masa na kasa gane da wane irin mutum Allah ya had'ani zama. ''Kina kallona baki bani amsata ba." Nace"Wace amsa zan baka ni wallahi duk ka gama d'aure ni." Tsaki yaja yace." Ina tambayarki shin kinyi wankan tsarki ko kuwa."? Nace"Ai dama kwana hudu ko biyar nace maka yau kuma kwana hudu akwai saura bai gama tafiya ba." na fadi hakane domin inga yanda zaiyi.....aikuwa 'bata fuska yayi ya tsirawa kasan kafet ido, cikin zuciyata nace"Wannan mutumin baida hakuri ko kadan......."Za kayi wanka ko."? a hankali nayi maganar, mikewa yayi ba tare daya tanka min ba, murmushi nai na kwanta tare da jan bargo, ina kallonsa ya fito yana goge jikinsa, ya gama shafe shafensa yasa kananun kaya yazo ya kwanta. Jawoni yayi jikinsa na sauke ajiyar zuciya tare da rintse idona! "My lov." kasa - kasa yace."Me zan samu ne." ? a hankali nace "Duk abinda kake so."" Hannu ya dora kan Brest dina yana cud'awa yace wannan zaki bani." Jiki a mace nace"Ai naka ne kayi yanda kake so dasu.'' Da azama ya mikar dani zaune rigata ya cire min ya bar min gajeran wandon dan dama iyakacinsa nan baya ta'ba kai hannunsa 'kasa na Brest dina da iya cibiyata dasu yake biyan bukatarsa, tsigar jikina ce kawai take tashi yanda yake shan breast dina yana murza dayan yasa gabadaya sha'awa mai zafi ta taso min pant dina ya jiqe jagab ni kaina nasan ina da bukata duk da ban san ya al'amarin yake ba amma yanda yake romancing d'ina yasa na kwadaitu da abin, rungumeshi na dinga yi ina sashshefa jikinsa...........Mun jima cikin wannan yanayi lokacin daya samu satisfaction ni kuma a lokacin na dinga jin wata masifaffiyar sha'awa na taso min, gabana ya dinga damuna da kyaikyayi mutsu-mutsu na dinga yi ina rirrikeshi, gabadaya ya kasa gane kaina, yayi kokari sosai dan ganin ya biya min bukatata ta hanyar romancing abin yaci tura daga k'arshe ma kuka nasa ina rike hannunsa, a rikice ya dinga tambayata abinda ke damuna, kasa fada masa gaskiya nayi kawai nace kaina ne yake ciwo, lalla'bani yayi yace bari yai wanka yazo ya bani magani, da kyar na sake shi ya nufi toilet, naja bargo na takure jikina ina zubar da hawaye, masifar dake yunk'uru min itace take nema ta zautani banta'ba shiga halin damuwa ba irin na yau, a gurguje ya shirya jikinsa ya zauna kusa dani "Tashi kisha magani Zakiji sauki kafin asuba insha Allahu. Idona na bud'e ina kallonsa yana zaune da gorar ruwa a hannuna da kwalin magani. Zaune na mike ba ya miko min maganin kar'ba nayi na watsa a bakina na karbi ruwan na kora.. " Sannu kinji." yafada yana dafa kafad'ata, kaina na daga a hankali na sauka daga bed din toliet na nufa domin gyara jikina, tsugawa nai na wanke duk abinda ya fito ta kasana nayi wankan tsarki na fito, samun sa nayi a kwance bacci naso ya daukeshi, ya bude min kirjinsa hade da fadin"Zo ki kwanta." banyi gardama ba naje na shige cikin jikinsa nai luf bargo yaja ya rufe mu ya ratsa dukka hannayensa a bayana ni kuma na shigar da kaina jikinsa, a haka bacci mai dadi ya dauke mu. [ Da asubah kusan lokaci guda muka tashi, ya cire ni daga jikinsa ya nufi toilet wanka yayi ya fito a gurguje ya shirya ya nufi massalaci, bayan fitarsa nima na mike na shiga toilet din wanka na farayi sannan na daura alwala na fito, na kimtsa na hau dadduma na tayar da sallah, bayan na idar nayi addua daidai gwargwado cikin kasala na zame na kwanta kan daddumar ba tare dana cire hijabin jikina ba, har yanzu damuwar jiya ce ke damuna na rasa da wane ma'auni zan auna al'amarin a gaskiya koda yanayin halitta ta to magungunan da Mamma tai ta bani ina banka suma sunyi tasiri a tare dani amma abin yayi yawa........Bacci ne mai dadi ya soma fizgata naji maganarsa akaina Da sauri na bude idona ina kallonsa yana tsaye a kaina, zaune na mike ina mutsika idona, yace."Kin samu tsarki kenan."? Shuru nai na fara kokarin mikewa, ya samu bakin gado ya zauna tare da cire jallabiyar jikinsa, ni kam daddumar na ninke na ajiyeta inda aka tanada ba tare dana cire hijabin jikina ba na zauna kusa dashi ina gaisheshi, yana wani murmushi yake amsawa. Wasa nake da yatsun hannuna yace."Ya jikin ki."? da sauki." nafada ba tare dana kalleshi ba.....Sunana ya kira na amsa tare dago kaina, yace."Naji dadin ganinki kina ibadah ina fata kin shirya tar'bar angonki.' Shuru nayi gabana na bugawa, matsowa jikina yayi yace."My love kinyi shuru ko bakya muradi na ne." A hankali nace"Dan Allah kayi hakuri kaga bani da lafiya." Hannunsa ya dora a wuyana yace."Umm!um my love ba zan iya hakura ba na duba naji jikinki babu zazza'bi." Nace"Ai kaina ne ke ciwo." hannunsa ya dora akan goshina ya girgiza kai yace."Ke! ni likita ne duk wani motsinki na sani jiya ma babu abinda ke damunki sai feeling shiyasa na baki maganin bacci so yanzu tunda kin samu tsarki sai mu biya bukatar junanmu." Kunya ce ta rufe ni! yasa dariya da fad'in "Ko kin dauka zakiyi min dubara ne."? girgiza kaina nayi yace." To maza zo ki bani abinda nake muradi." kwanciya yay ya janyo ni na fad'a saman kirjinsa, sauka nake kokarin yi ya rike k'uguna sosai sai da ya samu nasarar cire hijabin jikina, a gaggauce ya rabani da komai na jikina, ya matseni tsam tsam a kirjinsa!! Sakin jikina nai sosai na kyaleshi yana ta wassani da sassan jikina dani dashi gabadaya mun fice daga cikin hayyacinmu birgima kawai muke a bad din manne da juna bakinmu a had'e sai tsotsar junanmu muke ji muke tamkar mu kadai aka hallita a duniyar saboda tsabar shauqi da nishad'antuwa......sai da mukayi romancing din junanmu iya son ranmu kafin ya fara kokarin kar'bar sadakinsa, yanda gurin yake zubar da ruwan ni'ima yasa lokacin da yake kokarin sa jijiyarsa banji zafi ba sai ma dadin da yake kokarin gigitani! na dinga sakin nishi ina rirri'keshi! lokacin d'aya ya turmutsa katuwar sandarsa a gurin sai da numfashina ya kusa daukewa saboda azabah! hawaye wahala na zubo min na shiga turesa ina masa magiya ya daga ni! shima a nasa bangaran bayan ya tabbatar da cewa ya hud'a jikinta kasa motsi yayi ya tsaya cakkk! a yanda yake a hakan yana ganin zai iya samun gamsuwa dan wani irin bala'in dadi ne yake ratsa shi, jijiyarsa sai ta'bo wani abu take a cikin ramin!! zazzafan nishi! ya dinga saki! kafin yayi yunkurin fara aikin! lokacin ji nayi tamkar an sa reza an yayyanke ni a gurin! jikina ya dinga rawa ina had'ashi da girman Allah akan yayi a hankali, amma kamar kara ingizashi nake buguna yake yana wasu irin suratai marasa kan gado da ma'ana......Hakura nayi kawai na daina motsi saboda ina ganin kamar motsin da nake yi shike kara ingiza shi sai kawai nayi lakwam! na rabu dashi yana ta abinda ya ga dama dani! naci kuka da bak'ar wuya kafin ya sauka daga kaina sai da nayi suman wucin gadi na farfad'o numfashi na ya dinga fita sama-sama! a hankali naja bargo na rufe jikina idona na kulle sam! bana kaunar kwallon kwayoyin idonsa. Hannu yasa ya cire bargon yana duddubawa, kasancewar garin yayi haske yasa na fahimci abinda yake nufi, bedshirt din da bargon dik sun 'baci da jini gefan ciyoyina ma jini da sperm dinshi ne dik a had'e! Ajiyar zuciya ya sauke! ya dauki wandonsa yasa yana kallona, dauke kaina nayi ina goge fuskarta, a kasalance naji muryarsa yace."Allah yayi miki albarka." shuru nai masa, ya mike da kuzari ya nufi toilet, ruwan d'umi ya had'a yayi tsarkake jikinsa ya sake hada wani cikin baho ya fito daure da towel Baccin wahala ne ya dauke ni naji yana kiran sunana, ido na bude ina masa wani irin kallo......a sanyaye yace."Tashi muje ki gasa jikinki kiyi wanka." idona na rufe ba tare da nayi yunkurin tashi ba, ya zauna kusa dani a hankali yace."Kiyi hakuri nasan ban kyauta ba amma ki auna matsayin sonki a zuciyata wannan dalilin yasa na kasa saurara miki. Uffan bance masa ba, ya k'araci maganarsa da yaga bani da alamun tashi sai kawai ya dago ni yana kokarin daukana kuka nasa ina tureshi! jikinsa na kyarma yace."Kina so naje na fad'awa Mamma ko."? Kautar da kaina nayi ina share hawaye......"Sumayya." ya kira sunana muryarsa na rawa, shuru nai ban amsaba, sake yunkurin daukana yayi na galla masa cizo a wuya, da sauri ya sake ni yana kallona! bargo naja na rufe fuskata......Girgiza kai yay ya nufi wardrobe a guruguje ya kimtsa jikinsa, sai jin fitarsa nayi da sauri na bude idona ina kallon bakin kofar. Yunkurin mikewa zaune nayi na kasa! komawa nai na kwanta ina addua akan Allah yasa ba zuwa yayi ya kirawo ta ba, sake k'ok'artawa nayi na mike zaune na janyo hijabi na dake yashe a 'kasa nasa na yunkura na mike tsaye da kyar!! bargon da bedshirt din na fara kokarin daukewa suka shigo dakin a tare, kasa dago kaina nayi na kalleta mirya a dushe na amsa sallamarta, idanunta akan bedshirt din da yayi kaca-kaca da jini da sauri na dinga 'boyewa, tasa hannu ta rik'e kafad'ata bedshirt din ta kar'ba tana murmushi tace"Sumayya 'boye min kike."? Hawaye ne suka kwaryo min." Tasa hannu ta goge min da fadin"Ki daina kuka kinji ko kiyi hakuri ko wace mace na alfahari da wannan rana, hakika naji dadi sosai da kika kawo mutuncinki dakin auranki ina alfahari dake kuma ina rokon Allah ya baku zuria dayyu'ba! hannuna na rike sosai na fara kokarin zama dan gabadaya jikina babu kwari! Da sauri tace"Babana maza sake had'a mata ruwan d'umi ta shiga." da sauri ya nufi toilet sai wani rawar jiki yake......Mamma rarrashina kawai take tana nuna min muhimmancin dake tattare da abinda ya faru tsakaninmu...ya fito daga toilet din da fad'in "Mamma na had'a mata." Ta kamani muka mi'ke a tare, 'karfafa jikina nayi muka nufi toilet, a nutse ta cika ni da fad'in ki shiga ruwan ki gasa jikinki sosai kiyi wanka sai kizo kisha magani." Cikin nauyi da kunya nace"To." fita tai daga toilet din, na cire hijabin jikina a hankali na shiga cikin bahon dake dauke da ruwan zafin, ina shiga naji wani irin dadi! lumshe idona nai na dinga sakin ajiyar zuciya irin ta wahala. "Mamma tace" Ni zan tafi da wannan kayan can gurina sai nasa hadimai su wanke Maimartaba ya hana wannan al'ada da badan haka ba da sai na nunawa masu bin kwakkwafi da kiran Yarinyar fanko to sai suga zahiri cikakkiyar macace tunda gashi nan zanin gado ya nuna. Yace."Mamma koda Maimartaba bai hana wannan al'ada ba ni dama nayi rantsuwa akan babu mai ganin sirrina saboda haka wannan bedshirt din da bargon ki barsu ni da kaina zan wanke." Cike da mamaki take kallonsa kafin tace"Aa babana ka bari dai a bawa hadimai su wanke ina kai ina wanki." dariya yay yace."Mamma menene ai ni ne na 'bata." Murmushi tayi tana girgiza kanta, tace"Bari na dubata." kokarin mikewa take ya dakatar da ita ta hanyar fadin"Bari na dubata Mamma." Mikewa yay ya nufi toilet din. Ina cikin cud'a jikina ya shigo, da sauri na sunkuyar da kaina na fara kokarin tsugunawa, a nutse ya karaso kusa dani! na jingina da bango ( garu) gabana na fad'uwa matsoni yayi sosai ya kar'bi sosan hannuna ya cigaba da cud'a min jiki.....a sanyaye nace"Dan Allah ka bari ka fita kada ka 'bata jikinka." girgiza min kai yayi yace."Gimbiya ai yau ranar kice ki bari kawai nayi miki hidima." shuru nai masa ya cigaba da goga soso a jikina yana watsa ruwa, ajiyar zuciya na sauke nace"to nagode sai ka bari nayi wankan tsarki ko." Ido jawur ya matsa gefe jikinsa dik ya 'baci da kumfar sabulu, yace."Kiyi maza kiyi ina jiranki." Nasan halin nacin sa shiyasa banyi wata maganar ba na fara wankar tsarki kamar yanda addinin musulunci ya tanada.......Babban towel ya miko min. na kar'ba a nutse na daure jikina, ya miko min hijabina nasa, hannuna ya rike muka fito daga toilet din a tare, dakin babu kowa na kalleshi ya kalleni, a sanyaye nace"Ina Mamma."? Yana dan mirmushi yace."Ta fita da bedshirt dinki wai sai ta nunawa mutane kema cikakkiya ce." Kunya ce ta rufe ni nace"Wallahi banji dadin kiranta da kayi ba." Yace."My love kece kika tsaya gardama shiyasa na kirata ta taimaka miki." ajiyar zuciya na sauke na zauna gefan gado.....Vasillin ya dauko ya zauna kasan kafet a nutse ya fara shafa min, kallonsa kawai nake ina mamaki! wai yau shine ke shafa min mai! mikewa yayi ya bude wardrobe doguwar rigar shadda ya dauko min da pant da breziyya, yace."Kar'ba kisa ko na k'arasa ladana." Kar'ba nayi da sauri! ya juya ya sake nufar wardrb din kayansa ya dauko yana canzawa, damar dana samu kenan nayi saurin kimtsa jikina na zauna.........Yana gyara necktie d'in wuyansa yace." Zan dan shiga asibiti amma ba zan dad'e ba zan dawo ki kula da kanki kinji ko." Kaina na d'aga masa, yace." Wad'ancan magungunan nakan mirror ki daure kisha idan kinyi breakfast zasu taimaka miki." Nace"To nagode kai ba zaka tsaya kayi break din ba." Agogon hannunsa ya duba yace."Babu lokaci sumayya akwai marasa lafiya sosai da nayi al'kawarin ganinsu a yau yanzu nasan idan naje zan samesu suna zaman jirana so kada ki damu zan samu coffee nasha a ofis." Nace"To ko dai a kawo maka abinci." ? Girgiza kansa yayi yace." Nace miki zan dawo da wuri okey." binsa nai da kallo yace."Sai nadawo."' a sanyaye nace "Allah ya bada sa'a." da sauri ya bude kofa ya fita.........Na jima a dakin kafin na fita falo, suna zaune ganin fitowa ta suka mike tsaye gaisawa mukayi a hankali na zauna akan kujera, Mariya tace"Ranki ya dade a kawo miki kayan karin nan."? ina kokarin magana Jakadiyar Mamma ta shigo hannunta rike da wani madaidaicin kwando........... *Na kudi ne* Koda zaki ganshi a gruops na sata ne idan kina bukatar ki biya kudin karatu ga yanda abin yake vip gruop#600 normal gruop#300...account... 0542382124....Binta umar gtbank....idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:28 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 100 Koda ya fito daga toilet din kasa kallonsa nayi kaina a kasa har ya gama abinda yake yazo yana kokarin zama kusa dani nai saurin tashi da kokarin dauke bedshirt din da ya 'bata, ba tare da yace wani abu ba ya mike na janye bedshirt din na nufi toilet dashi raina duk a 'bace! koda na fito daga toilet din samunsa nayi har ya kwanta da alama ma bacci ya daukeshi, kayan bacci nasa na kwanta kan kujera tare da rufe jikina da hijabina! da kyar na samu bacci ya d'auke ni............Sai misalin shida shaura muka tashi dan nida shi bacci mukayi sosai sai dana bari tukkuna ya gama uzirinsa sannan na shiga toilet din a gurguje nai wanka na dauro alwala na fito na same shi yana kimtsawa, kauda kaina nayi daga kansa naje ina kokarin fito da kayana........."Sumayya." naji ya kira sunana, juyowa nai ina kallonsa, yace."Me yake damunki ne naga kin tashi cikin rashin walwala ko bakya jin dadi ne."? A nutse nace"Lafiyata lau kawai yanayin rayuwa ne." karasowa yayi inda nake tsaye ya rike kuguna tare da dora kansa a kafadata yace."My love ban yarda ba akwai abinda ke damunki please kada kisa na fita cikin damuwa." Dan tureshi nayi na bar gurin........Kallon mamaki! ya bita dashi kafin ya girgiza kansa, cigaba yayi da shirye-shiryensa ba tare daya sake kulata ba......Kimtsa jikina nayi nasa hijabi na tayar da sallah, ina kokarin sallama ya fice daga dakin, ajiyar zuciya na sauke ina bin kofar da kallo, abin ne yake bani mamaki da haushi! da gaske dai mutumin nan baya son haihuwa tunda gashi nan duk wasu matakan hana haihuwar ya dauka wato idan shi bukatarsa zata biya gurin sex bashi da damuwa wannan al'amarin akwai cutarwa a ciki (Tsarin iyali ne na musulunci wanda Annabi Muhammad SAW ya koyar amma kuma yin hakan baya hana haihuwa idan rabo ya rantse komai tsantsenin mutum sai ciki ya shiga....Sannan kuma ta wani 'bangaran hakan na ragewa ma'aurata jin dadinsu misali idan namiji yazo zaiyi release dole zai fita daga cikin ramin hakan zai rage masa jin dadin ta 'bangaran mace kuwa idan baki da saurin kawowa namiji na samun satisfied zai barki da wahala wani namijin idan ya kawo sau daya shikkenan ya gama duk abinda zakiyi masa ba zai sake tashi ba, kamar dai Yarima yana da kar'fin sha'awa amma kuma baya dogon zango yake gamsuwa kuma idan yayi sau d'aya baya 'karawa! ita kuma Sumayya tana da nisa sosai tana bukatar dogon zango kafin ta gamsu gashi an samu matsala ta 'bagaransa a lokacin da take kan ganiyar jin dadinta a lokacin shi kuma yake gamsuwa kuma saboda gudun haihuwa ya cire jikinsa ya barta da wahala, duk da bata san kan al'amarin sosai ba ta tabbatar da cewa akwai cutuwa a ciki dole ne ta nemawa kanta mafita tun kafin tafiya tai nisa.................Ta jima tana tunane-tunane kafin ta mike jiki a sanyaye ta fita falo ba tare data cire hijabin jikinta ba. To koda ya dawo da daddare ma sabgar gabansa yayi ya fita ba tare da ya tanka mata ba ta lura yaji haushin abinda tayi masa d'azu shine dalilin da yasa yayi watsi da ita da al'amarinta......Sai da tayi bacci ya shigo dan yana can tare da Shatima suna hira, wanka yayi yasa kananun kaya na bacci ya kwanta kusa da ita. Kwanciyarsa a kusa dani yasa na bud'e idona jikina na janye ina addua akan Allah yasa kada ya nemi wani abu, kafin ma na gama tunani naji shi a jikina yana shafa wuyana shiru nai masa ina ji yana kesses din baya yana sake matseni a jikinsa, na dinga jin wani irin yanayi a jikina, janyewa nayi, ya mike zaune rai a b'ace! yace."Wai meye hakane? kina abu sai kace 'Yar kauye." Shuru nayi yace."Kin san duk fushin da kike ba zai hanani biyan bukatata ba me nayi miki tun safe kike fushi na tambayeki dalili kince babu komai." Uffan bance masa ba, ya koma ya kwanta tare da birkitoni kansa, ringume ni yayi tsam! yana kokarin sa bakinsa a nawa, yanda yake min yasa gabadaya sha'awata ta tashi, jikina ya mutu na kyaleshi yana ta juya ni yanda ransa keso. Banji zafi sosai ba kasancewar ina da bukatar al'amarin yasa na sakar masa jikina gabad'aya muka fita cikin hayyacinmu yauma kamar jiya yana jin zaiyi release yayi yunkurin cirewa hanashi nai na rikeshi jikina sai rawa yake ni kadai nasan irin halin da nake ciki! da karfi ya fizge jikinsa kan cinyata ya zubar da sperm din. Ya wani kwanta a kaina yana sakin nishi! takaici yasa wasu zafafan hawaye suka kwaranyo min, hannu nasa da sauri na goge na shiga turesa daga jikina. Ba tare da wata damuwa ba ya mike ya nufi toilet, mikewa zaune nai ina duba jikina da duk ya 'bata min wannan wace irin rayuwa ce sai kace wanda yake auratayya da karuwa! karuwai ne ba'a san haihuwa dasu ake zuba musu sperm a jiki amma matar sinna a dinga yin wata irin mu'amula da ita irin ta yahudawa." Kuka ne yake kokarin kufce mata tana kokarin danneshi...........Yana fitowa daga toilet din ya kimtsa jikinsa yazo yana kokarin kwanciya bedshirt din yake turewa dan a tunaninsa shima ya 'baci! Mikewa nai na bar masa gurin, wanka nayi na fito na kimtsa jikina kujera na nema na kwanta zuciyata na wani irin zafi! "Sumayya."! naji ya kira sunana murya a sama! shuru nai masa. Yace." Wane irin abune wannan kika tsiro dashi zaki bar gado kije kujera ki kwanta.'' ? kamar da dutse yake magana, A fusace! ya mike zaune tare da kunna bedlamp yana kallon inda take kwance. "Bakya ji ne ina miki magana."? murya a cunkushe nace" Ina ji.'' yace."Okey to ki dawo ki kwanta kusa dani." da sauri nace"Dan Allah ka rabu dani nai kwanciyata anan dan banga amfanin kwanciya a kusa da kai ba.'' Shuru yayi na mintu biyu kafin ya d'aga kafad'a alamun rashin damuwa bedlamp din ya kashe ya koma ya kwanta tare da rufe jikinsa da bargo, bacci mai nauyi ne ya daukeshi ni kam sai can dare na samu da kyar bacci ya dauke ni. Kasancewar na jima banyi bacci ba yasa yau ma na makara, lokacin dana tashi har ya gama shirinsa yana zaune gefan gado yana gyara igiyar takalminsa kallonsa nai ina mamakin dalilin daya sa bai tasheni nayi sallah akan lokaci ba, yanayin fuskarsa yasa na gane akwai matsala. Ba tare da nace masa komai na na mike a sanyaye na shiga band'aki......koda na fito samun dakin nai babu shi ya fita ba tare da ya tsaya mun gaisa ba dama baya wani damuwa dayin break haka yake ficewarsa sai yaje ofis din yake kiran mahaifiyarsa ta tura masa da abinci.....a rabar yini nayi cikin tsananin damuwa da tashin hankali na dinga tunanin hanyar da zanbi na warware wannan gagarimar matsalar da nake fuskanta.............Har dare ya shigo gari yay shuru idona biyu ina tsammanin sa bai shigo bai kuma kira waya ba, da dai na gaji shirin kwanciya nai na rufe kofa na kwanta da wayata a hannuna, karfe goma da rabi na dare na nemo number sa.....Lokacin yana kokarin shiga gurin Lawisa yaga kiran wayarta, dauka yayi babu yabo babu fallasa ya amsa gaisuwarta. Ajiyar zuciya na sauke nace"Baka dawo bane.''? kai tsaye yace."Yanzu na shigo yau aiki ya ri'ke ni ina fatan kin wuni lafiya." nace"Lafiya lau.'' yace."To masha Allah sai da safe." kafin nace wani abu ya kashe wayarsa. A sanyaye na kashe wayar tare da ajiyeta a kan bedside naja bargo na rufe jikina ina addua a cikin zuciyata. Gajiya da wahala basa hanashi fitina koda yaci abinci ya gama komai na rayuwarsa zuwa yayi ya zauna kusa da ita....Lawisa ta mike zaune tana kallonsa, babu fara'a a fuskarsa ya mi'ka mata magani da goran ruwa. a sanyaye ta kar'ba ta watsa a bakinta ta kora da ruwa. Goran ruwan ya kar'ba ya ajiye ya hau gadon sosai janyota yayi jikinsa yana sa hannunsa a cikin rigarta Lawisa ajiyar zuciya ta sauke ta sakar masa jikinta sosai suka shiga biyawa junansu bukata. Washe gari da safe ita dashi cikin walwala suka rabu yana jin dadin mu'amula da ita saboda tabi ra'ayinsa da dokokinsa shiyasa yake jimawa akanta yana dogon zango kuma baya fargabar zubar da sperm dinsa a jikinta domin yana da tabbacin ba zata dauki ciki ba, sa'banin Sumayya da idan yana sex da ita yake fargaba sam baya sakin jikinsa saboda gudun abinda ka iya zuwa ya dawo yana jin zai kawo yake gaggawar cire jikinsa.....Ya fahimci cewa hakan na 'bata mata rai! ita da kanta ta nemi hakan tunda babu yanda baiyi da ita ba akan tabi ra'ayinsa taqi dama sai da ya gargadeta kacewar duk abinda ya biyo baya kada tayi kuka dashi tai kuka da kanta. Cikin rashin walwala ya shiga gurinta, ko zama bai ba yana tsaye suka gaisa ya juya ya fita ba tare da ya nuna mata wata cikakkiyar kulawa ba. Kuka sosai tayi a ranar kafin ta yanke shawarar tunkararsa da maganar gwara suyi wacce zasuyi ta gaji da irin wannan zaman da suke mara dadi da ma'ana. Koda ya dawo guri nata kunya da nauyi yasa ta kasa tunkararsa da maganar duk dare haka zai danneta ya biya bukatarsa ba tare da ya damu da tata bukatar ba. ******* *BAYAN WATA BIYAR* Rayuwar dai da suke sai kara tsanani take Sumayya ta shiga cikin wani irin hali na damuwa da bukatuwa yayinda ta 'bangaransa yake gudanar da harkokinsa na yau da gobe ba tare da ya bawa damuwarta mahimanci ba, duk da yasan abinda ke damunta yana saka ta kuka a koda yaushe hakan bai sa ya sauka daga kan ra'ayinsa ba koda yaushe idan bukatarsa tazo zaije gurinta ya biya bukatarsa ya barta cikin matsananciyar sha'awa, lokaci guda ta shiga rama yayinda Lawisa ke 'kara cika tana bunkasa da wata irin 'kiba mara kyau! hakan bai dameshi ba saboda yasan magungunan da take shane suka hura ta yanzu zaman lafiya suke sosai a tsakaninsu ya daina yi mata wulakanci kamar lokotan baya. Cikin shirin fita ya shiga ya sameni a kwance a gado kwana biyu duk na rasa gane abinda ke damuna kullum da zazzabi nake kwana ga yawan fitsari da nake, shigowarsa tasa na mike zaune. Nace"Ka zauna mana mu gaisa." girgiza kansa yayi yana duba agogon hannunsa yace."Babu lokacin zama ina fata kin tashi lafiya.''? 'Dan ya mutsa fuska nayi nace"Lafiya lau zazzabi ne dai yake damuna kwana biyu kullum dashi nake kwana." Tsira mata ido yayi na tsayin minti uku! da sauri yace."Dago ki kalleni." da sauri na kalleshi jin yanda ya fadi maganar! 'Kwayoyin idona ya tsirawa ido kafin ya wani murtuke fuska yace"Bude min tafin hannuwanki." Bud'e masa nayi ya shiga dubawa......."Sumayya watan ki nawa rabonki da al'ada."? gabana ne ya fad'i nace"Wata biyu da kwanaki." Cikin tsawa! yace."Kin san da haka me yasa baki min magana tun wuri ba." nace"Wai duk me ya jawo wannan hayaniyar ne ciki ne dani ai kai baka isa ka hana Allah ikonsa ba duk dubarar ka kuwa." Mari ya kwad'a min a zafafe! yace." Ni kike fad'awa wannan maganar." mikewa nai hannuna dafe da kuncina nace" Gaskiya d'aci gareta kai kuma baka so a fada maka dan ka mareni ba zan damu ba kuma insha Allahu komai abinka sai na haife cikin nan." Zuciyarsa ta dinga tafarfasa yana ji kamar ya zare blet yayi mata dukan tsiya ashe dai yarinyar nan da gaske so take ta rugaza masa tsari! 'kwafa yayi ya kwashi wayoyinsa a fusace! yace."Mutukar kina bukatar zaman lafiya dani sai kin yarda da umarnina idan ba hakaba sai na wulakantaki." Cikin dauriya nace"Duk abinda za kayi min a shirye nake dama ai na saba da wulakancinka ni ba zaka had'a kai dani gurin sa'bon Allah ba." Kansa ya girgiza ba tare da ya sake magana ba ya fita daga dakin kamar zai tashi sama. Tunda daga ranar ya dauke min wuta ya daina shiga sabgata koda a gurina yake baya ta'ba yarda muyi mu'amular arziki fuskarsa kullum a daure idan na gaishe ya amsa a dakile abincina kuwa inda na ajiye anan zan dauki abuna, gabad'aya ma ya daina kusantata yayi tsayin sati hud'u muna cikin wannan hali gashi kullum cikin ciwo nake babu ruwansa dani da lafiyata, ina kuka na sameshi yana shirin fita nace"Wai kai dan Allah baka da imani ne? me nayi maka kake azabtar dani haka? cikin nan fa bani na bawa kaina ba Allah ne ya bani me yasa kake gudun rahamar Allah? dubbanin mutane nacan na nema kai Allah ya za'be ka a cikinsu ya baka kana nema ka butulce masa kaji tsoron Ubangiji ka kar'bi kyautar daya baka watakilama shi kadai zaka haifa a duniya." Hannu ya daga min ya juyo cikin shan toka yace."Sumayya ke kika zalinci kanki ciki kuma na bar miki kije ki haihu amma babu ruwana dashi." Nace"Bangane babu ruwanka dashi kayi cikin kace ka bar min wannan wace irin magana ce." !? Cikin wani irin yanayi yace."Sanin kanki ne bana zubar da k'wayoyin haihuwata a mahaifarki wannan dalilin yasa nace miki kije duk inda zaki da cikin ki." Cikin fitar hayyaci nace"Aikuwa zani duk inda zani dashi zanje na shedawa Mammah duk halin da ake ciki nasan ita din cikakkiyar musulma ce ba zata yarda da wannan yahudancin ba." Cikin tsantsar 'bacin rai yace."Sumayya kada ki fasa zuwa gurin Mamma da maganar nan wallahi kikaje kika tayar mata da hankali duk abinda ya biyo baya kada kiyi kuka dani." Yana 'kare maganarsa ya fice daga dakin a mugun fusace!! kwanciya nayi akan kujera na dinga kuka ina nadamar rayuwa ashe dai auran nan na tattare da babban kalubale maigirma mutum sai kace kafuri ya dinga gudun haihuwa kamar wanda bata wannan hanyar aka sameshi ba..... *Na kudi ne..*! Koda zaki ganshi a gruops na sata ne idan kina bukatar ki biya kudin karatu ga yanda abin yake....Vip gruop#600 normal group #300....account... 0542382124.....Binta umar gtbank.....idan kati zaki turo kiyi min magana ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:28 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 99 Cikin nutsuwa na amsa sallamarta zama tayi kasan kujera ta ajiye kwandon dake a hannunta a kusa da ita Tace "Ranki ya dade barka da safiya." a nutse na amsa da fadin"Jakadiya kin tashi lafiya." ? da dan murmushi a fuskarta tace"Lafiya lau ranki ya dad'e dama Fulani ce tace na kawo miki wannan." kwandon data shigo dashi ta turo min gabana. Nace"Nagode sosai." mikewa tayi da fadin"Ranki ya dade zan koma." nace"To jakadiya kice nagode Allah ya saka da alkairi." ta amsa "Insha Allah zan isar da sa'kon ki." bayan fitar ta na umarci Mariya data bude min kwanukan dake cikin kwandon, kwano daya farfesu ne sai tururi yake da alama ba'a jima da gamawa ba, kwano na biyu gurasa ce manya manya taji kantu! sai kamshi takeyi, a take naji ina sha'awar cinta da farfesun nace"Mariya kawo min ruwan tea na fara d'umama cikina kafin naci wani abun." da sauri tace"To ranki ya dade. " Dainng din ta nufa da sauri! ni kuma na cigaba da tunanin abubuwan da suka faru tsakanina dashi jiya daddare duk da bana cikin hayyacina na d'an fuskanci wani abu da yayi a lokacin da yake kokarin biyan bukatarsa, amma ba zan d'ora zargina akansa ba sai ya sake aikatawa tanan zan fahimci abinda yake nufi. Tea din nasha sosai cikina ya warware, nasa tasa min gurasa biyu tasa min farfesun akai.........Nace"Mariya ku dauka kuje kuci." tace"Ranki ya dade mu mun karya wannan abincin naki ne na mussaman bai kamata muci ba. Nace"Ai ni na baku ku dauka wannan ya ishe ni." Hannu tasa ta dauki kwandon da fadin"Ranki ya dad'e mungode kwarai hakika muna jin dadin yanda kike mu'amula damu munji dadin kasancewarki a matsayin uwargiyarmu." Murmushi nayi nace"Mariya kenan nima ina alfahari daku kuna kulawa dani yanda ya kamata kada ku damu da dukkanin abinda zanyi muku." Cike da jin dadi sukayi min sallama suka fita, girgiza kaina nai ina mamakin al'amarin wai yau nice a wani matsayi mai girma wanda banta'ba tsammanin kasancewa cikinsa ba, koda yake Ubangiji Allah babu yanda baya tsara lamarinsa........Bayan na kammala cin abincin da kaina na gyara gurin, na dauki wayata daki na shiga na kwanta a gado, number shi na kamo na tura masa text kamar haka. _Yallabai ina fatan kaje asibiti lafiya? sannan ina rokon Allah ya kula da kai kamar yanda kake kulawa da masu bukata."_ Ina tura masa text din na ajiye wayar kusa dani, lumshe idona nayi ina janyo bacci da kyar naji ana buga kofar dakin, da sauri na mike zaune ina mamakin irin bugun da ake! anya kuwa! saukowa nayi da sauri ina fadin "Waye ne."'" ? "Ke d'iyar bayi wato har tambaya kike waye ki bude kofar mana sai kiga ko su waye."!! da sauri na bude kofar! Hajiya Karima ce tare da wata mata mai qiba da alama kanwarta ce dan naga suna kama da juna. Cikin fargaba nace" Hajiya barkanku da zuwa ku zauna mana." Tsaki taja ta matsa gefe guda tana watsa min harara!! Lauratu itace ta 'karaso inda nake ta kalleni sama da k'asa yawun bakinta ta tofa min a fuska! kafin nai wani yunkuri ta tsinke sar'kar gold din dake wuyana!! hannu nasa na dafe kirjina ina mamakin abinda tayi! karfi tasa ta bugi! kirjina nayi taga-taga zan fad'i! da sauri na rike 'kofa( 'kyaure) ina kallonta....... hajiya Karima tace"Aa Laure banda duka kici mutuncinta nace kada ki doketa." Laure tace"Hajiya ki kyaleni nayi 'kuli-'kulin kubura da yarinyar nan jiya da takaicinta na kwanta bacci wallahi tunda Lawisa ta kira waya ta tana kuka take sheda min cin mutuncin da Ali ke mata akan wannan 'yar iskar yarinyar nake Allah- Allah gari ya waye nazo naci ubanta! kina 'Yar bayi sama da 'kasa har kina da wata power kwace miji wato ke ga gwana kin cancad'a ado da gold kina zaune lafiya kin dasawa wata ciwon zuciyata to yau sai kin gaya min waye ubanki."!!! tana dukan kirjina take wannan maganar.....Hajia Karima tazo taja hannunta suka matsa gefe tace"Lauratu kada ki doketa bata isa ki had'a jiki da ita ba kawai ki nuna mata matsayinta." Nace"Hajiya wai duk me ya kawo wannan abun me nayi muku ko kuma akwai wacce nake aure a cikin k.......Gwa'be min baki tayi da fad'in "Rufe mana baki fanko bud'add'an gwangwani! har kina da bakin magana wacce ta rako mata duniya." !!! Hawaye suka wanke min fuska, Hannu tasa zata fizge yarin kunnena na rike hannun tare da yarfar dashi!! cike da mamaki suke kallona! Sunkuyawa nayi domin daukar tsarkata dake tsinke a k'asan gurin, da sauri tasa kafarta mai dauki da takalmi mai tsayi ta danne min hannu! rintse idona nayi ina jin wani irin zugi!! ciki zafin nama! na tureta tai taga-taga zata fad'i! kafin tayi wani yun'kuri! na kwad'a mata mari a kunci! a gigice! suke kallona! sabida gudun abinda zai faru yasa da azama na banke kofar dakin, key na murza na barshi a jiki kan gado na zube na dinga rizgar kuka ina jiyyar yatsun hannuna data mutsike min da takalminta. 'Karar waya ta dake daf da kaina yasa nayi gaggawar mikewa zaune wayar na laluba na dauka ina dubawa, gabana ne ya buga ganin miss call dinsa hud'u! da sauri na daga wayar tare da daidata nutsuwata a sanyaye nace"Hello." Yanayin muryarta yasa ya dan ji wani iri........."Sumayya lafiya dai ko.''? da sauri nace"Eh.''' Yace."Okey to me ya hanaki daukar wayata na kira sau uku kin duba ko kuwa kina sane."? "Kayi hakuri wallahi bana kusa da wayar na barta a daki shiyasa yanzu ma na shigo daukar abu sai naga kiran ka." Ajiyar zuciya ya sauke yace."Nifa yanayin muryarki yasa jikina mutuwa ina fata dai ba jikin bane." ? nace"Babu abinda ke damuna sai kasala ina fata kaga text d'ina."? Murmushi yayi wanda har sai da naji sautinsa a kunnena yace."Naga text dinki kuma naji dadi sosai dalilin daya sa ma kenan dana samu sukuni na kira wayarki na ji lafiyarki." Murmushi nai ina kokarin kawar da damuwata nace"Nagode sosai amma dai kasha tea din kamar yanda kace." Girgiza kanshi yayi yace."Har yanzu ban samu nutsuwa ba tukkuna zan nemi coffee nasha d'azu nace miki zan dawo kiyi hakuri bana jin zan dawo gida da wuri inada marasa lafiya sosai." A sanyaye nace"Allah sarki mijina gaskiya bama kyautawa da muke barinka kana fita da yunwa dan Allah ka bari a kawo maka abinci." 'Yar dariyar jin dadi yayi yace."My love bana son wahalar dake shiyasa nace kisha magani ki kwanta ki huta! kada ki damu zan kira Mamma a waya insha Allah zata sa a kai min abinci." Ajiyar zuciya na sauke nace"Har naji dadi a raina wallahi sam bana son zama da yunwar da kake bashi da amfani." Murmushi yay yace."Naga sai wani lalla'bani kike me zan samu idan na dawo."? 'Yar dariya nayi nace"Zan baka duk abinda kake so.' " cikin wani irin voice yace."Kinyi alkawari dik abinda na bukata daga gurinki zaki bani."? Nace"Eh nai al'kawari." ajiyar zuciya ya sauke yace."To nagode kwarai sai na dawo." Ina kokarin magana ya kashe wayar, ajiyar zuciya na sauke na ji sanyi a cikin zuciyata waya ta dashi yasa na samu sassaucin bakin cikin da nake ciki bazan damu da duk wani cin fuska da wulakancin da zan fuskanta tunda mijina yana sona iyayensa suna kaunata to komai mai sauki ne kuma bana jin zan fad'a masa abinda ya faru yanzu zan bari idan sun 'kara sai na samu Mamma na fad'a mata nasan dole za tayiwa tufkar hanci. Sai bayan isha'i ya shigo gidan kai tsaye gurin Lawisa ya nufa dan tun jiya rabon daya taka inda take......Tana zaune tayi ado sosai amma kallo daya za kayi mata ka tabbatar da cewa tana cikin fargaba da tashin hankali, abinda Lauratu kanwar mahaifiyarta taje ta aikatawa Sumayya shike damunta bata ta'ba tsammanin mahaifiyarta zata bada goyon bayan a rugaza mata zaman auranta ba......Tunda ya shigo take kallon fuskarsa bata hango 'bacin ran daya tsallake tunaninta ba, sakin ranta tayi tai masa barka da zuwa ya amsa yana bin falon da kallo, kanta ta sunkuyar da fadin"Kayi hakuri akan abinda ya faru jiya." Shuru yayi bai tanka mata ba! tace"Dan Allah kayi hakuri." Yace."Magana ta wuce ina fata ki gyara halinki sai ki zauna lafiya dani! ajiyar zuciya ta sauke tace"Insha Allah zan kiyaye.....Mikewa yayi yace."Ni zan tafi sai da safe kenan." ta mike tare da rakashi bakin kofa har da cewa ya gaishe mata da Sumayya." yace "Zataji insha Allahu." Yana fita kai tsaye sashen mahaifiyarsa ya nufa domin su gaisa, ya jima a tare da ita kafin suyi sallama da juna. Ado da kwalliyar da sameta dashi ya 'kyatar dashi mutuka ya dinga murmushi yana satar kallonta wai lallai shi ba zata kamashi yana kallonta ba, sai kauda kai yake amma daga ya samu faraga zai ta kallonta daga yaga sun had'a ido zai kauda kansa.....Sumayya dariya kawai take masa tana mamakin halinsa, tun bai gane ba har ya fahimci dariya take masa ya 'bata rai tare da ajiye cokalin hannunsa" Yace." Wato Kin samu mahaukaci kinsa a gaba kina dariya ko."? da sauri na had'a hannuwa cikin sigar bada hakuri nace"Dan Allah kayi hakuri kaci abincin nan ni bakai nakewa dariya ba." Harararta yayi yana sake release akan kujera yace."Sai dai kici kayanki na koshi." Kamar zata fashe da kuka tace"Haba rabin rayuwata dan Allah kada kayi min haka ka daure kaci abincin nan dan Allah kaji."!!! a marairaice ta karasa maganar......Yana dariya yace."Sai kin maimaita sunan da kika saka min. Da sauri nace"Rabin rayuwar Sumayya." wani irin kallon kauna yayi mata yace."Da gaske kike."? kaina na daga nace"Eh wallahi idan babu kai babu Sumayya." ji yayi kanshi na kumbura! ya dinga jefa mata kallon so yace."Ashe kin iya irin wannan kalaman shine baki ta'ba yi min ba." Mirmushi nayi nace"Akwai wasu ma na mussaman kai dai kaci abinci zan fada maka su." Kamar wani shashasha ya dauki spoon din ya ciko da abinci yasa a bakinsa yana taunawa yana kallonta, dariya ta kusa sub'ce mata daka gani abincin yay yawa a bakinsa, tissue ta dauka tana goge masa inda ya 'bata Ya sake ciko spoon har yana zubewa ya tusa a bakinsa yana taunawa yana kallonta! dariya tasa tana gumtse bakinta da hannunta....'Kwarewa yayi da sauri ta mi'ka masa ruwa ya kar'ba yasha ya ajiye cup din spoon din ya dauka zai sake d'ebo abincin da sauri na kar'ba hannu yasa zai kar'ba na janye! tare da fad'in "Baka ci a nutse bari kawai na baka da kaina." cinyarsa ya nuna min wai na zauna! cikin jin nauyi na dauki plate din abincin na zauna a cinyarsa ya rikeni sosai na shiga bashi a baki yana ci yana yi min wani irin kallo wanda na kasa fassarashi. Daga k'arshe ma plate din abincin ya kar'ba ya ajiye kan center teble matseni yayi tsam! a jikinsa! kusan a tare muka sauke ajiyar zuciya, yasa hannu ya dauke dankwalin kaina hannusa guda ya turmusa cikin gashin kaina yana ya mutsawa, tsigar jikina ta mike wani irin sanyi ya dinga ratsa jikina! zafafan kesses yake sakar min wanda suka hautsina min lissafi da k'yar na iya ture kansa dake manne da kirjina murya na rawa nace"Ka daure ka cinye abincin ka." Kansa ya girgiza min da fad'in ''Na'koshi ki tashi muje Daki." Kallon 'kwayoyin idanunsa ya tabbatar min da abinda yake nufi.........Kokarin sauka nayi daga jikinsa ya ri'ke kuguna had'e da fad'in "Ina fata dai baki manta da al'kawarinmu ba." Kallonsa nayi ya daga min gira da fadin" kin manta ko."? Girgiza kaina nayi nace"Ban manta ba." Yace."Okey to tashi muje." gabana na faduwa na sauka daga jikinsa, yana mi'kewa nayi saurin kauda kaina dan ganin yanda girmansa ya bayyana. Hannuna ya ri'ke muka nufi dakin, ba tare da yaja wani dogon lokaci ba ya cire kayansa, nace"Wanka za kayi ne."? Wani kallo yayi min da fadin"Ke bana son rainin hankali wane irin wanka bayan kin san abinda ke damuna." dauke kaina nai daga kansa....Ya mike daga shi sai gajeran wando ya karaso inda nake tsaye jana yayi ya kaini har bakin gadon na dinga no'kewa ina fargabar abinda zai faru dan har yanzu ina jin zafi a gabana. Wasa yake dani sosai wanda ya sanya gabadaya sha'awata ta tashi na daina no'kewa gabadaya na sakar masa jikina ya dinga abinda yaga dama dashi.......Adduar saduwa da iyali naji yana karantowa rintse idona nayi ina addua cikin raina, cikin nutsuwa ya dinga shigata har yaje inda yake so, kafin ya fara wani abu sai da ya dan jima tukkuna ya fara a hankali a hankali hakan yasa banji zafi ba sosai! na saki jikina ina d'an jin dad'i sama-sama! ina jinsa shi yana ta sakin nishi! hade da 'kara 'karfi da kuzari! kawai sai na tsinci kaina da tura masa jikina dan motsawar da nake yana sani nishad'antuwa! haka muka kasance da juna cikin wani irin yanayi mai dadi da shau'ki! gabad'aya fita mukai daga cikin hayyacin mu domin a lokacin daf muke da biyawa junanmu bukata! babu zato babu tsammani naji yay gaggawar zare jikinsa daga jikina yayi ruf da ciki akaina hannuwansa duka yasa kan breast d'ina yana luguda yanayi yana wani irin gurnani! rasa gane yanayin da nake ciki nayi kukan ne yake kokarin kufce min saboda takaicin abinda yayi min a lokacin nake jin zan samu gamsuwa yay gaggawar cire jikinsa kome hakan yake nufi oho!!! jikina ne yayi sanyi gabana ya dinga wani irin tsiko yana zubar da ruwan dake 'kara tayar min da sha'awa! Mi'kewarsa yasa na kalleshi sai naga yana kokarin sa gajeran wandonsa kafin ma nayi wani yunk'uri ya sauka daga gadon, bin sa nayi da kallo bak'in cikin duniya kamar ya kasheni! kokarin mi'kewa zaune nayi hannuna ya sauka kan uban sperm dinshi da ya zubar a kan bedshirt d'in da sauri na dauke hannuna daga kai.......... wato wannan shine matakin daya d'auka a kaina tunda dai na'ki na amince da tsarin iyali to bari ya dinga zubar da kwayoyin haihuwarsa akan bedshirt idan yaso sai subi rariya........ anya kuwa wannan dubara ce? ko kuma dai akwai Lauje cikin nad'i.? *Team d'in Sumayya Anya kuwa zamu yarda da wannan al'amari🤕 Kuna inaaa!! ku fito muyi zanga-zanga akan munahiki😂😂😂* *Na kudi ne.....!* Koda zaki ganshi a gruops na sata ne idan kina bukatar biyan kudin karatu ga yanda abin yake.....Vip group #600 normal gruop#300 account... 0542382124....Binta umar gtbank idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:28 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 101 A ranar yini nayi akwance da damuwa gami da tunanin mafita, sai da naji kiran sallahr la'asar tukkuna na tashi naje nai wanka na kimtsa jikina kan dadduma na hau na gabatar da sallah, bayan na idar na jima hannuna a sama ina addua kafin na shafa a fuskata, daddumar na ajiye inda aka tanada, falo na fito domin samawa kaina abinda zanci, ina fitowa muka had'a ido da ita, Tambaya ce a zaune ita kad'ai yanayin fuskarta yasa na gane cewa lallai babu lafiya, wannan shine zuwanta na biyu tunda tazo da farko taga daki bata sake zuwa ba tsayin wata biyar kenan babana kuwa bai ta'ba zuwa ba sai dai ni duk sati ina zuwa na gaishe su. Cikin kulawa nace"Tambaya yaushe kika shigo."? Tana kallona tace"Na d'an jima lokacin dana shigo kina bacci sai hadimai dake aikace-aikace daya daga cikinsu take sheda min bacci kike shine nace Kada ta tasheki zan zauna ki tashi tukkun." A sanyaye nace"Wallahi yau yinin bacci nayi tun bayan Fitar Yarima na kwanta sai yanzu Allah ya tasheni." Cikin kulawa tace"Ai gwara da kikayi bacci zakiji dadi.'' murmushi nayi da fadin"Ina baba ina fatan yana nan lafiya." ? girgiza kanta tayi tace"Da sauki dai za'ace jikinsa ne ya tashi kwana biyu baya bacci da daddare shine nace bari nazo na fada miki ko da wani taimako da mijinki zai masa. Hankalina ne ya tashi jin cewar babana bashi da lafiya nace" Tambaya babana baida lafiya amma kuma baki fad'a min na dubashi ba." Murmushi mai ciwo tayi tana girgiza kai tace"Sumayya kina cikin damuwa yaushe zan zo na 'kara miki wata." Da sauri na kalleta ina mamakin maganarta nace"Tambaya waye yace miki ina da damuwa."? girgiza kai tayi tace"Sumayya ba sai an fad'a min ba ni nagani da idona dik sanda kika je gurina domin gaisheni cikin damuwa nake ganinki ni na haifeki dole na fahimci halin da kike ciki." Hawaye ne suka kwaranyo min a kumatu! dawowa kusa dani tayi ta rungumeni tana shafa bayana tace'Kiyi shuru ki daina kuka ki fada min matsalar da kike ciki a gidan auranki ni mahaifiyarki ce zan baki shawarwari masu amfani." Zuciyata ce ta karye hawaye suka dinga zubo a kumatuna nace"Tambaya ciki ne dan kimanin watanni uku amma kuma wanda yayi cikin yace babu ruwansa dashi." Cikin tsantsar tashin hankali ta dago ni tana kallon fuskata tace"Sumayya yanzu a haka ciki gareki ? kuma akan wane dalili Yayi wannan mugun furucin akan ki." Cikin sar'kewar murya nace"Saboda kawai bashi da ra'ayin haihuwa." girgiza kanta tayi tace."Kodai bashi da ra'ayin haihuwa dake sabida kina baiwa wacce take 'karkashinsa." Kallonta nayi, tace."Kwarai kuwa Sumayya ni a ganina wannan dalilin ne yasa yake gudun hada jini dake." girgiza kaina nayi nace"Ba haka bane Tambaya shi gabadaya haihuwarce baya so saboda wasu dalilai nasa Ai kinga Lawisa jininsu d'aya to itama baya bukatar haihuwa da ita kamar yanda baya bukatar ya haihu dani." Tambaya jikinta ne yayi sanyi ta kalleni a sanyaye tace."Lallai dole ki shiga cikin halin damuwa Sumayya to amma mahaifiyarsa tasan abinda yake faruwa kuwa."? Girgiza kaina nayi nace"Bata sani ba.'' Tace."Lallai kuwa yana da kyau ta sani domin wannan maganar bai kamata kiyi shuru ba dole ta sani tayi masa fad'a ai wannan ba d'abi'a bace kana musulmi ka dinga gudun haihuwa akan wane dalili ? Kije ki fad'a mata kuma ki daina kuka da damuwa kada wani ciwon ya sameki." Nace" Mutukar bai sanja ra'ayi ba to zan sameta na fada mata duk abinda yake faruwa." Ajiyar zuciya ta sauke tace"Yanzu cikin watansa nawa."? "Ina tunanin zaiyi wata uku." girgiza kanta tayi tace" Ubangiji Allah ya sauke ki lafiya Sumayya nima banki goyon bayan kibi ra'ayinsa ba duk rintsi kada ki bari ya zubar miki da ciki tinda likita ne zai iya kawo miki magani zubar da ciki kada kisha." Shuru nai ina kallonta da mamakin nisan tunaninta gabadaya banyi tunanin hakaba eh lallai dole nayi takatsantsan dashi dan tabbas zai iya bani wata 'kwayar nasha cikin ya zube bukatarsa ta biya. Sai kusan biyar da rabi Tambaya ta mike da niyyar tafiya, har harabar waje na rakata kana na bata sa'kon gaisuwata gurin babana kafin nazo dubashi...........Cikin damuwa mai tsanani na koma ciki ina tunanin abinda zai faru a gaba. Sanin da nayi cewa ba'a gurina yake ba yasa ina idar da sallahr isha'i nayi shirin kwanciya, waya ta na ajiye a kusa dani wai ko zai kira ni, sai na kunna tv na kwanta ina kallo kafin bacci ya daukeni..............Jin alarm na agogon waya ta ya nuna k'arfe goma yasa na cire raina da shigowarsa wayar na kashe kafin na kashe tv din na ja bargo na rufe jikina ina addua a cikin zuciyata, can cikin baccin daya soma daukana naji sautin muryarsa a kaina, a firgice na bude idona ina kallonsa yana tsaye 'ki 'kaqam! mi'kewa zaune nayi ina kallonsa yasa hannu ya kunna bedlamp dakin yayi haske dauke kaina nayi babu walwala nace"Sannu da zuwa." Ba tare da ya amsa ba ya mi'ko min abunda ke hannunsa " 'Kar'bi wannan maganin kisha na 'karfin jiki ne.'' hannunsa nabi da kallo kwayoyin magani ne a ciki wata 'yar farar leda! Hannu nasa na kar'ba had'e da fadin"Nagode." fuskarsa ya saki ya zauna kusa dani tare da miqa min goran ruwan dake hannunsa. Kar'ba kawai nayi na ajiye kan drowar. Yace."Kisha maganin mana." Murmushi takaici nayi nace"Yanzu don Allah dan Annabi ba kaji kunya ba."? kallona ya shigayi na cigaba da cewa''Nasan fa ko wane irin magani ne kana so ka zubar min da ciki a fakaice mai yasa kake adawa da ikon ubangiji ne? tunda kaga Allah yayi maka haka to alkairi ne kayi addua akan Allah yasa dan za'a haifa maka ya zama alkairi a tare dakai da al'ummar musulmi. Shuru yayi yana kallon kasan kafet da alama maganata ta ratsa shi dan gani nayi duk jikinsa yayi sanyi, naji dadin hakan kawai sai na cigaba dayi masa nasiha ina nuna masa illar abinda yake yi. Kallona yayi da jan ido yace."Bani magani na tunda ba zaki sha ban kuma ce kiyi min wa'azi ba." Ledar maganin na mi'ka masa ya kar'ba tare da kama hanyar fita ba tare da ya sake cewa wani abuba. Girgiza kaina nayi na koma na kwanta ina addua a zuciyata akan Allah yasa ya saduda ya gane gaskiya ya hakura da hukuncin ubangiji. Washe gari da safe daya shigo nake sheda masa rashin lafiyar mahaifina tare da neman izinin zuwa dubashi! ba tare da ya dauki maganata da muhimanci ba yace.'" Zaki iya zuwa ki dubashi amma ni kam banda lokacin amma ana iya kaishi asibiti kamar kowa." Jikina ne yayi sanyi na bishi da ido har ya fita daga dakin, girgiza kaina nayi ina jin takaicin abinda yake nasan duk wulakancin da yake min sabida na'ki nabi umarninsa ne. Yanayin yanda na samu babana a rikice yasa duk hankalina ya tashi, banyi zuciya ba na sake kiran wayarsa na sheda masa cewa yana cikin matsala dan akwance yake sabida galabaita......Cikin tsawa yace." To yanzu ya kike so ayi ko kina so na katse abinda nake nazo na dubashi? nace "Kisa a kawoshi asibiti."!! kashe wayarsa yay ba tare daya bari nace wani abuba. Daure zuciyata nayi na cire duk wata damuwa a cikin raina na shedawa Tambaya yanda mukayi dashi, tace" To shikkenan sai a kaishi Asibitin. nace"Zan koma gurina yanzu zan turo direba da mutum biyu domin su kamashi." tace."To ubangiji Allah yayi miki albarka.'' na amsa da ameeen lokacin da nake kokarin fita. To hankalina bai kwantaba sai dana ga dawowarsu lafiya ikon Allah babana da kafafunsa ya dawo Tambaya ke sheda min cewa 'karin ruwa akayi masa shine dalilin daya sa yaji kwarin jikinsa, ledar dake cike da magani ta nuna min.'' na zauna ina nuna mata yanda zata dinga bashi maganin akan 'ka'ida, ban tafi ba sai dana tabbatar da cewa yaci abinci yasha magani sannan nayi musu sallama na tafi, yanzu naji sassauci ta wannan bangaran. Da har nayi nufin shiga gurina sai na fasa bangaran Mamma na nufa mun kwana biyu bamu gaisa da juna ba. Tana zaune gurin da take hutawa Jakadiya ce a gefanta suna hira irin wacce suka saba, a nutse na karasa inda suke na zauna gabanta ina gaisheta, murmushin da takeyi yasa ni tunani wani abu. gaisuwata ta amsa tare da fad'in "Ya jikin naki.''? " Da sauki" nace ina jin nauyin had'a ido da ita, bayan tashin jakadiya daga gurin ta gyara zamanta cikin nutsuwa tace"Sumayya tun kwanaki nake miki kallon mai juna biyu, sai yau dana turke babana da tambaya yake cewa dani baki da ciki, ni wallahi da naga kina laulayi yau da lafiya gobe babu na dauka ko na kusa samun jika ne". Cikin kunya da jin nauyi nace" Eh hakane Mamma bani da ciki muna dai Addua Allah ya kawo masu albarka." da sauri ta amsa da ''ameeen 'yar albarka Ubangiji Allah ya amsa adduarki." shuru nayi ina murmushin ya'ke! tace"Yanzu babana da sassafe yake fita gashi baya dawowa da wuri ni kaina sai ya kwana biyu bai shigo mun gaisa ba, sai dai kullum muna waya dashi mussaman da safe yakan kirani yace nasa akai masa abinci ofis." Nace"Eh hakane kam aiki ya hanashi sakewa da kowa abinci ma sai da kyar yake ci! Mamma kada kiga laifinmu wallahi muna iyakacin bakin kokarinmu gurin kula daci da shansa kawai dai yafi bukatar naki shiyasa muka rabu dashi. Murmushi tayi tace"Haba Sumayya ai ni zanyi shedarki akan babana kin kula dashi babu aure a tsakaninku ballanatana yanzu da aure ya shiga tsakaninku na riga nasan halinsa da 'kiwar cin abinci shiyasa a duk sanda ya bukaci abinci ta gurina nake sawa a kai masa amma dai duk da haka zan zauna dashi nai masa fad'a ya dinga zama yana cin abinci tare daku." Nace"To shikkenan Mamma mungode kwarai da gaske Allah ya 'kara girma." Ta amsa da "ameeen suma ameeen." Sallama nayi mata tace" Ya muna hira kuma zaki tafi." Murmushi nayi nace" Mamma naga magariba ta kusa ne." tace"Eh hakane to babu damuwa Sumayya Allah yayi miki albarka sai na sake ganinki ." nace "To Mammah a tashi lafiya nagode kwarai da karamci." Murmushi tayi tare da daga min hannunta, cikin nutsuwa nasa takalmana na fita daga falon A daran ranar bai shigo ba shigo ba sai da safe ya shigo, kamar koda yaushe fuskarsa babu sassauci! muka gaisa nace"Nagode sosai da hidimarka akan mahaifina wallahi naji dadin ganin ya dawo lafiya da k'afafunsa." hararata yayi yace."Bana bukatar godiyarki ba sabida ki gode min na kula da lafiyarsa ba ina fata kin gane." Murmushi nayi kawai na sunkuyar da kaina, yace."Ni zan fita." da sauri nace"To Allah ya taimaka." ba tare daya amsa ba ya kama hanya ya fita daga dakin, kwanciya nayi ina dan jin sassauci a zuciyata yau naji dadi sosai mun rabu cikin arziki.........Cikin baccin daya soma daukana naji mugun bugu! a furgice na bude idona ina kallon bakin kofa........... Yunkurin saukowa nake bugun kofar na sake tsananta, gabana na faduwa nace"Waye."? "Ubanki Lawi ne."!!!! Jin muryar Lauratu yasa naji yawun bakina ya dauke Ubana take zagi akan wane dalili? fuskata a murtuke na bude kofar a shirye nake dana kare martabar iyayena........Ko kafin nayi wani yunkurin ta afko dakin! da sauri na bita da kallon mamaki! nace"Baiwar Allah waike dabba ce ne? haka kawai da sassafe zaki zo kina buga min kofa ko kuma kina bina bashi ne."? Yanda take kallona yasa na fahimci cewa tana mamakin lafazai na a kanta, hanya na nuna mata da fad'in " Kizo ki fice min daga daki tun muna sheda juna dake." Murmushi tayi tana durfafo inda nake na tsorata da yanayin kallon da take min amma dai na dake! sabida inaso na nuna mata tsageranci na, cikin zafin nama naga ta watso min abu a jikina! a gaggauce na matsa gefe guda kawai naga wani irin ruwa yana kumfa a 'kasan gurin ties din ya tsage! cike da d'umbin mamaki! nake kallonta tana huci!!! Ta bud'e kofar dakin ta futa a fusace! cikin karkarwar jiki na nemi guri na zauna ina jan kalmar innalillahi wa'ina ilaihi raji'un! shin matar nan wane irin mugun abu tazo tayi min? " asid ne tayi nufin watsa miki a jiki domin ta 'kona ki." zuciyata ce ke fada min wannan magana, nai gaggawar kallon gurin ina mamakin yanda yayi 'baki ties din yayi duhu duk ya tsage! al'amarin ya shiga bani tsoro tare da mamaki! mai tsananin gaske.. *Na kudi ne!* Koda zaki ganshi a group na sata ne idan kina bukatar biyan kudin littafin ga yanda abin yake....Vip gruop#600 normal group #300....account.. 0542382124....Binta umar gtbank idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:28 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 102 Na jima a zaune a dakin ina jimanta al'amarin kafin na mike jiki a mace na fita falo, nan na samesu a zaune ganin fitowata yasa duk suka mike tsaye, sunayi min barka da fitowa, zama nayi kan kujera babu walwala a fuskata nace "Ku zauna inaso nayi magana daku.'' zama sukayi tare da mayar da hankalinsu kaina, nace" Daga yau sai yau kada ku sake barin matar data fita yanzu ta sake shigowa kunji abinda nace ko." Gabad'aya suke ce "Eh ranki ya dade insha Allahu zamu kiyaye." Nace"Mariya ki shiga ki gyara min dakina." da sauri ta mike ta nufi dakin su kuma suka cigaba da aikace aikacen da suke.......... Da wuri ya dawo gida nai mamakin hakan amma ban nuna a fuskata ba barka da zuwa nai masa ya amsa a sake kamar bashi ba, ruwan wanka na hada masa na fito na tarar dashi yana kokarin cire kayan jikinsa, ido muka hada murmushi yayi min na bishi da kallo ina mamakin sanjawarsa jikin mirror na tsaya Nace."Na hada maka ruwan wankan.'' "Nagode." yafada a lokacin da yake kokarin ajiye agogonsa kan mirror wani irin kallo yayi min yace'"Ba zaki taya ni wankan ba."? Murmushi nai nace"Da alama yau kana cikin nishadi .'' yace."Saboda me kikace haka."? nace"Saboda ba haka kake mu'amula dani ba." Shuru yayi still da murmushi a fuskarsa ya nufi toilet din, girgiza kaina nayi na bude wardrobe na dauko masa jallabiya da gajeran wando na zauna gefan gado ina jiran fitowarsa Ido muka hada a lokacin da ya fito daga toilet din da sauri na kauda kaina tsigar jikina duk ta mi'ke ni kaina nasan ina bukatarsa cikin zuciyata nace" Allah yasa dai yau muyi abin arziki da juna. Zama yayi kusa dani yana goge jikinsa da towel nace"Ga kaya na dauko maka." "Nagode." yace na mike a nutse na dauko man da yake shafawa, a nutse na tsuguna kasan kafet na fara shafa masa a kafafunsa. "Sumayya." cikin wani irin voice yayi maganar, kallonsa nayi naga idonsa yayi ja. amsawa nayi tare da cigaba da shafa masa man. Yace."Ya jikin naki."? ba tare dana kalleshi ba nace da sauki.'' Yace." Allah ya rabaku lafiya." da sauri na kalleshi ina mamakin adduar da yayi. girgirsa ya daga min yana murmushi. Ajiyar zuciya na sauke nace"Yanzu ka gane kenan." hannu na ya rike yace.''To ya zanyi tunda kinfi karfina." girgiza kaina nayi nace"Kada kayi sa'bo ba laifina bane Allah ne ya nuna maka ikonsa." Yace."Na sani Sumayya na hakura na bar masa ikonsa." murmushi nayi nace"Nagode kwarai insha Allahu za kayi alfahari da dan da za'a haifar maka." Yace." To shikkenan yanzu me zaki bani." nace"Zan cika maka ciki da abincina mai dadi da gamsarwa.''' da murmushi a fuskarsa yace."Bayan naci na koshi me zan samu." ? Shuru nayi yace."Yau da soyayya nazo gurinki." kallonsa nayi ya kanne min ido......murmushi kawai nai ina mamakin shu'umancinsa dama ai ruwa baya tsami banza. Hannuwana ya ri'ke yana murzawa yace."Baby kinyi shuru ko bazan samu ba." ? nace"Zaka samu mana." yace."To nagode muje ki bani abinci naji karfin jikina." mikewa nayi ya rike hannuna muka fita falo. Da kyar ya iya cinye abincin dana zuba mishi nace"Wai dan Allah me yasa baka san cin abinci."? yace."Haka kawai tun ina yaro haka nake nafi mayar da hankali kan biscuits da sauransu kayan zaqi." nace"Shiyasa mana gakanan kullum jiya i yau ka'ki kumari." dariya yasa yace."Kina so nayi qiba kenan."? kai na daga ina murmushi yace."Idan na zama 'kato zan dinga turmusheki fa." dariya nayi nace"ai yanzu ma turmushenin kake.'' Yace."Ai Banda nauyi kinfi ni nauyi baby." girgiza kaina nai nace" Ban yarda ba." 'yar dariya yayi yace."Sumayya bana san 'kiba shiyasa bana mayar da hankali gurin cin abinda zai janyo min ita, amma kuma ina sha'awar mace mai 'kiba da kumari irin ki.'' dan 'bata rai nayi nace"Wato kana k'arewa matan mutane kallo kenan."? girgiza kansa yayi yace."babu ruwana da matan kowa sai nawa na fada miki abinda ke raina ne." Shuru nai ina kallonsa ya kashe min ido da fad'in muje ciki ko." dauke kaina nayi, ya mike tare da kama hannuna na mi'ke kai tsaye bedroom din muka nufa sai shashshafa jikina yake gabadaya ya gama rikita min jiki. A daran ranar ya nuna kulawa mutuka dan ya saki jikinsa sosai ya gamsar dani tarin sha'awar dake damuna, a tare mukayi wanka na dinga addua a zuciyata akan Allah ya d'orar da zaman lafiya a tsakaninmu.......... Kwana biyu zamana dashi yayi kyau muna mu'amular arziki kuma idan na bashi abinci ko baya so sai ya zauna yaci duk dan ya faranta min rai har zuwa yayi ya duba babana na dinga murna ina sake godewa Allah daya kawo mana zaman lafiya da junanmu. Satin mu uku da shiryawa ranar lahadi da safe na tashi da wani irin ciwon mara, na fito daga toilet na sameshi yana bacci, cikin faduwar gaba na zauna kusa dashi ina tashinsa, ya bude idonsa da fadin"Menene baby please ki bari na huta.'' nace" Ka tashi bani da lafiya.'' idonsa ya bud'e! yana kallona kafin yace." me yake damunki."? murya na rawa nace"cikina ne ke ciwo."? jim! yayi kafin ya cusa hannunsa cikin rigata 'kasan marata yasa hannunsa yana d'an dannawa! nai saurin dauke hannunsa ina ya mutse fuska! yace."baby bashi da lafiya." gabana ya fadi! hawaye na soma zuba nace"Dan Allah ka tashi ka bani magani." shuru yayi min yana kallona..... Cikin damuwa nace" ka zuba min ido kana kallona ka tashi ka bani magani nace." 'Dan 'bata fuska yayi yace." Ke! ni kikewa tsawa haka."? ganin yanda ya hasala ne yasa na shiga bashi hakuri ina hawaye. Yace." Bani da magani a gida kuma tun jiya na fada miki cewa ba zan fita asibiti da wuri ba zan kwanta na huta a gida sai ki bari na tashi tukkuna." Wani irin kallon takaici nake masa yaja bargo ya rufe jikinsa! fizgewa nayi ina kuka nace"Ashe dama munafurci ne."? ya kalleni nace" Wallahi kaji tsoron Allah akan abinda kake." mi'kewa zaune yayi rai a 'bace! yace'Tashi ki fita ki bani guri na huta." hannunsa na rike ina cigaba da zubar da hawaye nace"Dan Allah ka tausaya mana nida babyna." Girgiza kansa yayi yace." Zan baki magani amma sai na gama bacci tukkuna." komawa yayi ya kwanta yana sake rufe jikinsa da bargo! a fusace! na fuzge bargon ai kafin na ankara ya kwada min mari!!! na dafe kuncinta ina kallonsa.......Cikin rashin mutumci yace." Wallahi zan tattakaki idan baki bani guri ba." mi'kewa nai a sanyaye na fita daga dakin, tsaki yaja mai karfi ya koma ya kwanta yana addua akan Allah yasa cikin ya zube ya huta. Koda na fita falon kasa danne damuwata nayi kawai na zauna kan kujera ina kuka domin nasan shi kadai zanyi na samu sassauci a cikin zuciyata, abubuwan da mutumin yake min sunyi yawa akwai abunda nake dubawa shiyasa kwata-kwata bana so na shedawa mahaifiyarsa Mamma macace mai karamci da mutunci zaman da nayi da ita ya sa na fahimci nagartattun halayenta ta nuna min dukkanin kauna da kulawa wannan dalilin yasa kwata kwata bana so naje na tayar mata da hankali bayan haka kuma ina kokarin ganin na rufa asirin aurena sanin da nayi cewar fallasa sirrin aure bashi da amfani ga ma'aurata shiyasa nake hakuri da duk abubuwan da yake min amma yanzu ya zama dole na sheda mata irin halin da nake ciki domin na tsira da lafiya nida abinda ke ciki......hawaye na share na mike na shiga dakin na sameshi yana bacci cikin kwanciyar hankali, girgiza kaina nayi firji na bude na dauko goran ruwa da cup kadan na tsiyaya na zauna kan kujera Fala'ki da nasi kafa uku na tofa a cikin ruwan sannan na tofa ayatulkursiyu kafa daya bisimillah nayi nasha na rage kadan na shafe cikina dashi.....cup din na ajiye na kwanta kan kujera tare da tsirawa rufin dakin ido........cikin ikon Allah na samu sassaucin abinda nakeji Allah nagodewa na gyara kwanciyata bacci mai nauyi ya daukeni. Sai wajejen uku na rana na tashi babu shi a dakin da alama bai jima da fita ba dan gabadaya dakin kamshin turaransa yake, wanka nayi na dauro alwala na fito nai sallah na shirya jikina na fita na sami abinci naci naji karfin jikina, su Mariya sukayi min rakiya can gurin mahaifana, alhamdulillahi naji dadin yanda naga jikin babana yayi sauki na zauna mukayi hira sosai sai daf da magariba na koma gurina.................. Sanin da nayi cewa ba a gurina yake ba yasa na rufe kofa dan ina tabbacin tinda mukayi haka dashi ba zai shigo yayi min bankwana ba, aikuwa har ya gama kwana biyunsa a gurin Lawisa bai shigo gurina ba kuma bai kira wayata ba, nima fushi nake sosai inaso na nuna masa cewar na gane abinda yake nufi dama ashe yaudarata yake yana nuna kamar ya hakura ashe domin ya samu biyan bukatarsa wannan dalilin yasa na dauki al'kawarin bijire masa tunda dai shi baya tsoron Allah. Ko kunya daya dawo gurina ya dinga wani lalla'bani har tambayar jikina ya kawo wani magani wai na ciwon cikine duk sanda naji ciwo nasha zanji sassauci kar'ba kawai nayi na ajiye na bar masa dakin. Falon ya fito wai na bashi abinci na hada masa komai na bar masa gurin, a falo na kwanta na kyaleshi a dakin, can dai da yaji shuru ban shiga dakin ba ya fito ya tsaya a kaina yana min magana! a fusace! na mike nace"Kai! na fa daina yarda da yaudararka na gane har yanzu kana kan bakanka baka kaunar cikina to Allah yana kaunarsa kuma insha Allahu sai na haifeshi lafiya." "Sumayya ni kike d'agawa harshe?" nace"Ai kai ka janyo ni dai dan Allah ka matsa daga kaina bana bukatar dadin baki.'' "Okay naji kina iya tasowa kina bani hakkina ko kuwa."? wani banzan kallo nai masa nace" Ba kaji kunya ba!" shan kunu yayi yace."Kifa shiga hankalinki dani bani da sauki kin dai san halina ko."? A fusace! nace"Ka jima ba kayi min mugun abuba dama ai ka saba nima na saba duk wani mugun sharrin da kuke bibiyata dashi zai koma kanku.''' "Sumayya bayan ni ashe akwai masu binki da sharri.''? nace" Kwarai kuwa kaje kayi binkice." ajiyar zuciya ya sauke yace." Yanzu dai kiyi hakuri ki tashi muje." nace'' Kai komai abinka sai ka hakura ka kyaleni.'' Murmushi yayi yace."Kin san Allah bazan kyaleki ba ko kina so ko bakyaso sai na biya bukatata.'' kafin nayi yunkuri ya fara kokarin daukata, hannunsa na dinga bugewa ina matsawa, kawai sai ya turmusheni akan kujerar gabadaya ya sakar min nauyinsa! rashin karfi da kuzari yasa jikina ya mutu kyaleshi nayi ya biya bukatarsa saboda nasan idan nace zanyi buge buge ni zansha wuya amma ko kusa ban bashi had'in kai ba dan sandarewa nayi yayi kid'ansa yayi rawansa. **** Abinda ya cigaba da faruwa kenan a tsakaninmu dik ranar da yake gurina da kokawa yake samun biyan bukatarsa ni a galabaice shi a galabaice gashi sabida tsabar fitina sai yayi sau biyu farkon dare da kuma asubahi......... *Bayan wata biyu* Cikina ya shiga wata na biyar sai jikina ya soma nauyi nayi wata irin qiba 'kuguna ya sake fad'i cikin gabadaya ya shanye gurin breast d'ina sai dai ya d'an fito tunda ya huda zani ana ganin tudunsa amma sai mai 'kurulla ne zai gane! bani da laulayi mai zafi sai dai nayi haske sosai mussaman kafafuna da hannuwana, 'Bangaran Magajin sarki kuwa kullum cikin 'kunci da takaici yake mutukar zai budi ido ya ganta da cikin sai yaji kamar ya sha'keta saboda haushi! shiyasa kullum cikin yi mata iskanci da wulakanci yake kuma idan dare yayi yazo ya mori albarkatun jikinta. Ina zaune a falo tayi sallama ta shigo, cikin kwalliya, murmushi nai nace"Barka da zuwa." Mansura ta samu guri ta zauna nace" Ba kiyi zuciyaba." mirmushi tayi tace" Na dai kusa." nace"Kiyi hakuri insha Allahu ina nan zanzo musha hira. Tace."Ai ke yanzu dole ayi miki uziri tunda kinyi nauyi.'' nace."Bangane nayi nauyi ba." dariya tayi tace" Ashe baki da hausa ina nufin d'an baba ya kusa zuwa." sai nasa dariya da fadin"Waye yace miki ina da ciki."? tace"Haba Sumayya gashinan har yayi kwari ai mu ba makafi bane." Murmushi nayi ina girgiza kaina, ta mike da fadin"To ni zan koma amma kafin nan zan shiga gurin Lawisa itama mu gaisa da juna." nace"Gaskiya kin kyauta sosai kina da kokarin zumunci insha Allahu zamu zo." tace"Ai ita Lawisa zuwanta uku kece dai baki ta'ba zuwa ba." nace"Kada ki damu insha Allahu zanzo a kurkusa." tace" To shikkenan sai na ganki." har bakin kofa na rakata mukayi sallama cikin mutunci. "Mansura kika ce Sumayya na dauke ciki."? Lawisa ce ke wannan maganar cikin tashin hankali!! Mansura ta girgiza kanta da fadin" Kwarai kuwa wallahi ciki ne da ita dan da alama ma ya kwana biyu tunda gashinan har ya fito. Lawisa taji wasu zafafan hawaye na nema su kufce mata, murya na rawa tace"Mansura ya akayi haka ta faru? ya akayi Sumayya ta dauki ciki bayan Sai da ya tabbatar min da cewar itama yana bata kwayoyin hana haihuwa.'' Mansura tace"Lawisa bangane maganarki ba."? hawaye ta share ta shiga warware mata yanda sukayi, tun kafin a daura aura Mansura tace"Amma gaskiya Lawisa kinyi ganganci waye ya fada miki ana haka? kawai sai ki dinga dibgar kwayoyi ba tare da kin tabbatar da cewar kina haihuwa ko bakya haihuwa ba, a gaskiya Lawisa na raina wayonki." Hannu tasa ta goge hawaye tace"Wallahi Manusura na rasa yanda zanyi ne shiyasa na amince da bukatarsa sai gashi ya ha'ince ni." Mansura tace"Ai a zahiri ya fi sonta shiyasa yake so ya haihu da ita ke kuma yana baki kwayoyi idan zakiyi hankali kiyi idan ba hakaba to tabbas zai kaiki ya baro." Cikin tsantsar tashin hankali da nadama tace"Mansura wallahi nima daga yau na daina shan kwayoyin sai dai duk abinda zaiyi yayi kuma idan baiyi wasa ba sai na samu Maimartaba na fada masa abinda yake aikatawa." Mansura tace"A'a kada kiyi saurin yanke hukunci keda shi ku yankewa kanku hukunci a daki dole ya hakura kema ya barki haka tunda dai kishiyarki ta samu ciki kema sai kiyi kokarin samu amma kika fitar da maganar dake dashi dik sai kunji kunya." Lawisa shuru tayi tana jajanta al'amarin, Mansura ta mike da niyyar tafiya, Lawisa har bakin kofa ta rakata tana mata godiya akan shawarwarin data bata . Koda ya shiga gurinta ya ganta cikin rashin nutsuwa yasa ya tsaya yana tambayarta, kuka ta fashe dashi tace"ashe Sumayya ciki ne da ita shine ka munafurce ni kake ta bani kwayoyi ina sha ashe har kafi kaunar had'a jini da ita akaina."? Jikinsa ne yayi sanyi yace."Ke waye ya fada miki tana da ciki." !? mikewa tayi tana kuka tace"Bana so ka raina min hankali ko ka 'karyata wanda ya fad'a min ba zaiyi min karya ba Matarka nada ciki dan har yayi kwari ma." Ajiyar zuciya ya sauke yace."Sai kiyi hakuri nima hakurin nake akan al'amarin ke kinsan bani da ra'ayin haihuwa a yanzu yanda kika ga cikin nima haka na ganshi.''' Tana kuka tace"Wannan wace irin magana ce kai kayi cikin amma kana cewa haka ka ganshi wato nice baka kauna ko babu komai ai zan samu Maimartaba na fada masa irin cutar da kayi min. Da sauri yace."Duk wannan maganar bata taso ba tunda ciki kike so zaki samu zaki daina shan kwayoyi insha Allahu kuma zan baki maganin da zai kwanke miki mahaifarki ki samu ciki da wuri sannan inaso nayi miki albishir da cewa zamuje America tare akwai taron likitoci da za'ayi a asibitin da nayi aiki a can cikin satin da zamu shiga zamu tafi tare ki rakani." Jin wannan magana yasa taji sanyi a cikin ranta taji dadi sosai daya za'beta domin yayi tafiya mai muhimanci da ita ko banza tasan tafi Sumayya a gurinsa, kwantar da hankalinta tayi ta bashi dukkanin kulawar da yake bukata. *Na kudi ne* Koda zaki ganshi a gruops na sata ne, idan kina so ki biya kudi ga yanda abin yake.....Vip gruop#600 normal group #300 account... 0542382124.....Binta umar gtbank....idan kati zaki turo #400 sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:28 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 103 Sai ana Saura kwana biyu na samu labarin tafiyar tasu, shima ba daga bakinsa naji ba lokacin da naje gaishe da Mamma take min zancen a lokacin hankalina ne ya tashi sosai kishi ya taso min amma saboda kada ta fahimci wani abu yasa na nuna mata cewa nasan da tafiyar hakuri ta shiga bani da fadin"Tunda ni bani da koshin lafiya nai hakuri suje su dawo murmushi nayi na nuna mata cewa babu wani abu dake damuna akan tafiyar tasu tunda ya za'bi tafiya da Lawisa ai duk d'aya ne dani da ita, sallama nayi mata na koma gurina na kwanta abin duniya ya taru yayi min yawa, yini nayi cikin damuwa da 'bacin ran munafurcin da yake min dan zaiyi tafiya da Lawisa meye na 'boye min tunda ban isa na hanashi abinda yayi niyya ba wato daba dan na shiga gurin Mamma ta fada min ba da sai dai idan zasu tafi ya shigo yayi min sallama! girgiza kaina nayi na mike zaune jin alamun za'a shigo yasa na tsirawa kofar dakin ido, Mariya ce ta shigo tace"Ranki ya dade kina da bakuwa." A sanyaye nace"Wacece."? dan jim tayi kafin tace"Wannan matar ce mai qiba wacce kika hanamu bude mata kofa." Nace"Yanzu ma kada ku bude mata kofa ku rabu da ita idan ta gaji zata tafi." Mariya tace"To ranki ya dade." fita tayi ni kuma na mike tare da tsayawa bakin window ina mamakin abinda ya sake kawo Lauratu gurina na rasa abinda nayi mata take kokarin cutar dani na tabbata yanzu ma ba alkairi ne ya kawota ba. Bud'e kofar dakin ce tasa nai saurin juyowa sai muka hada ido dashi ya shigo fuska a had'e! kallo na bishi dashi ina mamakin dawowarsa gida da wuri. "Sannu da zuwa." nace ina kallon fuskarsa, yace."Sumayya yaushe kika koyi wulakanci da 'kin mutane ."? Nace"Ban fahimci maganarka ba." Yace." Aunty Lauratu tazo dubaki kin hanata shigowa hakane ko ba haka bane."? shuru nai na nemi guri na zauna! yace." Kada wani ko wata ya sake zuwa ki hana a bude masa kofa kin gane ko."? Nace"Wai shin wace irin alaqa ce a tsakanin ka da matar da kazo kana tada jijiyar wuya akanta." "Rashin kunya zakiyi min kenan."? sassautawa nayi nace" Kayi hakuri ba zan maka rashin kunya ba na tambayeka ne." Yace." Aunty Lauratu kanwar Hajiya Karima ce mahaifiyar Lawisa ina fata kin gane." Nace"Nagane amma sai nake ganin ni bani da wata alaqa da ita sai ta musulunci dan haka banga dalilin da zai sanya ta dinga wanko kafa tana zuwa inda nake ba." Cikin mamaki yace."Kina nufin tana zuwa kenan kina hanata shigowa."? nace"Kwarai kuwa bazan bari ta shigo ta cutar dani ba." "Sumayya wai me yasa kike da zargi ne.? kallonsa nayi nace" bani da zargi dik abinda kaga nayi magana akai to naga zai cutar dani ne." Yace."To na dai gaya miki kada ta sake zuwa ki hanata shigowa wulakanci bashi da dad'i." Kai tsaye! nace"Wallahi ba zan barta ta shigo ba." Ya tsira min ido yana kallona kafin yace." Akan wane dalili." ? "Duba can gurin ka gani." ya waiwaya yana duba inda nake nuna masa, yace."Ke ni banga komai ba." ajiyar zuciya na sauke na mike tsaye na isa gurin! karasowa yayi gurin. Nace"Sati uku da suka wuce ta shigo har dakin nan da niyyar ta watsa min asid ga sheda nan ka duba a ranar Allah ne kawai ya kare ni daga sharrin da ta shigo min dashi." Cikin mamaki mai tsanani yake kallon gurin yayi duhu sosai lokaci guda ya gane asid ne kuma irin mai mugun karfin gaske. "Sumayya ya akayi baki fada min ba." ? d'an ta'be baki nayi nace"Baka da lokacina ai tunda kaima neman lafiyata kake." hannu ya daga min rai a bace yace.'' ba'kar magana zaki fad'a min."? Girgiza kaina nayi naja bakina nai masa shuru, yace."Saboda rashin hankali kina fuskantar irin wannan matsalar amma kija bakin ki kiyi shuru meye amfanin hakan. Muryarta na rawa nace"Wai dan Allah har yaushe ka zauna dani ka bani kulawar da zan fada maka abinda yake faruwa! nafi kowa sanin halinka zaka iya cewa 'karya ne shiyasa nai maka shuru." Murmushin takaici yayi yace.'' Ai sai ki cigaba da shuru kina cutar kanki duk ranar da suka samu galaba a kanki kada kiyi kuka da kowa." Nace"Insha Allahu dukkanin wanda yake nufi na da sharri sai ya koma masa." Yasan har dashi a ciki shiyasa yaja bakinsa yai shuru ya nufi toilet yana mamakin abinda yake faruwa dole kafin ya tafi yasa matakan tsaro a sashen nata sabida gudun abinda ka iya zuwa ya dawo sosai al'amarin ya firgitashi. Dakin na bar masa na koma falo na zauna, ya fito cikin jallabiya milk kallonsa nai na dauke kaina yace."Kiyi hakuri kizo ki bani abinda zanci." sanyi naji a zuciyata ganin yanda yake min magana, na mike na nufi dainng din ya biyo baya na kujera ya gyara ya zauna yana kallona ni kam na kasa sakin fuskata saboda 'bacin ran abinda yayi min......."Ya jikin naki ina fatan babyna ya wuni lafiya."? shareshi nai na tura masa plate din abincin gabansa, yace."Sumayya zauna zanyi magana dake, yanda yayi maganar cikin tsare gida yasa na zauna." Yace."Zanje america domin halartar taro irin namu inaso ki kula da kanki wannan abun da yake faruwa dake ya tsoratar dani mutuka kada ki sake yin shuru akan wani mummunan abu insha Allahu zan kawo matakan tsaro domin su saka ido a gurin sannan ita kuma Lauratu dole na dauki mataki akanta zata fada min dalilin da yasa take bibiyarki da mugun abu." Nace"Dan Allah ka bar maganar nan ni wallahi bana san tashin hankali nasan ba komai ne yasa suke nufa ta da mugun abuba saboda abunda ya faru ne tunda dai kai kafi karfinsu to ni bari su huce akaina amma insha Allahu sharrinsu sai ya koma kansu." Yace." Sumayya ba zan bar wannan al'amarin ba wallahi sai na dauki mataki akan dukkanin wanda yake kokarin ta'ba lafiyarki." "Ni dai dan Allah ka bar maganar nan tunda dai nace Allah ai maganata ta kare wallahi bana so ta dalilina a sake samun wata matsalar kayi hakuri ka kyalesu da sharrinsu insha Allah zai koma kansu." Cokalin dake hannunsa ya ajiye ya dauki wayarsa yana dubawa, nace"Ya kuma ka ajiye cokalin.''? girgixa kai yayi yace."Ba zan iya cin wani abu ba." . Nace"Wannan dalilin ne yasa fa nayi shuru da bakina saboda nasan baka daukar abu da sauki gashi kana cin abinci ka ajiye............Kallona yayi yay murmushi wanda ya tsaya iyakacin l'ebanshi yace."Wannan al'amarin ne me sauki a gurin ki ko.''? kai na girgiza nace"Ba haka nake nufi ina nufin idan muka barwa Allah komai sai kaga yayi mana magani nasan suna so su dauki fansa ne akaina." Yace.'" A kaina zasu dauki fansa bake da baki da laifi ba." nace"Ai kai kafi karfinsu dole su kyaleka su dauki hukunci akaina a ganinsu nice na janyo aka rataye Muddibo shiyasa suke so su dauki fansa akaina. Tsaki yaja yace."Basu da hankali gabad'ayansu kin san Allah Sumayya dik wacce tayi miki lahani a cikinsu ba zan kyaleta ba koda kuwa harda hajiya Kariman a cikinsu sai na dauki mataki akansu." Nace"Naji na kuma gode da kokarin ka amma dan Allah yanzu ka hakura ka bar maganar idan suka sake yunkurin wani akaina nima zan baka goyon baya ka dauki mataki amma dai yanzu kayi hakuri ka bar maganar. Ajiyar zuciya ya sauke ya dauki cokalin ya cigaba da cin abincin, lemo na tsiyaya masa a cup na mika masa ya kar'ba ya kur'ba ajiye cup din yayi ya cigaba da cin abincin nace"Amma ba zan 'boye maka cewar naji ciwon abinda kayi ba. Kallona yayi yana tauna abincin dake bakinsa a tsanake yace."Me nai miki."? nace" Sabida ka shirya tafiya da Lawisa america sai ka 'boye min kasan dai ni ban isa na hanaka abinda kayi ra'ayi ba." Tissue ya dauka ya goge bakinsa yana kallona yace."Lawisa ta samu labarin kina dauke da ciki hankalinta ya tashi wanda har hakan yasa take zargina akan nafi bukatar haihuwa dake shiyasa bana baki kwayoyi na nuna mata cewa nima karfina kikafi ta'ki aminta da maganata har tana ikirarin kai maganar gurin Maimartaba wannan dalilin yasa na yanke hukuncin tafiya da ita domin na rarrasheta acan." Girgiza kaina nayi nace"To menene na 'boye min ni shine abinda yafi komai bani haushi sai dazu da naje gaishe da Mamma take fada min a lokacin nuna mata nayi kawai na san maganar dan Allah ka daina irin haka babu dadi." Yace."To shikkenan tunda kin dauki hakan da wata manufa Allah ya baki hakuri." nace"Ai dole na zargi wani abu tunda naga kamar kana 'boye min. Hannu ya daga min da fadin"Maganar ta isa haka kin san dai ke baki isa naji tsoronki ba ko? kallonsa nayi ya cigaba da cewa'' Bana munafurci kamar yanda kika zato kawai Allah ne bai nufe ni da na fada miki da wuri ba tunda yanzu kin samu labari magana sai ta wuce." Mi'kewa nayi na bar masa gurin dan na lura da cewar ba zai fuskanci abinda nake nufi ba idan kuma nace dole sai na ganar dashi shaid'an zai shiga tsakaninmu. Har nayi bacci bai shigo dakin ba......sai can naji motsinsa na bude idona ina kallonsa ya kashe fitila yazo ya kwanta kusa dani, jin shuru bai ta'bani ba yasa nasha jinin jikina ina tunanin ko yayi zuciya dan nasan halinsa da saurin fushi! ajiyar zuciya na sauke jin ya janyoni jikinsa ya rungumeni sai nasa hannuwana duka biyun na ratsa jikinsa kesses din fuskata ya shigayi kafin ya had'a bakina da nasa ya shiga tsotsar harshena da le'bena had'in kai na bashi sosai muka shiga biyawa junanmu bukata. Washe gari cikin walwala muka tashi ni dashi sai abin arziki muke tamkar bamu ta'ba samun sa'bani ba, har bakin kofa na rakashi ya kar'bi wayoyinsa dake hannuna cikin kulawa ya rungumeni jikinsa yace."Ki kula da kanki da babyna." murmushi nai nace"Idan kana kiran babynka sai na dinga jin wani irin dadi a raina wallahi har so nake naga na haihu kana kula dashi." Murmushi yayi yace."Ni kuma kullum da fargaba nake kwana nake tashi ina jin tsoron ranar da naquda zata kamaki ai ina jin kwanciya zanyi sai an k'ara min ruwa." Dariya na dinga yi ina kallonsa, yace."Sumayya ina jin tausayin masu haihuwa wallahi shiyasa gabadaya bata burgeni." nace"Ka bar wannan maganar dan Allah dik abinda kaga Allah yayi to yana da manufa wuya bata kisa idan kuma na mutu gurin haihuwa aljanna zan shiga dan haka ka daina damuwa." Yace"To na daina zan cigaba da yi miki addua." Cikin murmushi nace"Nagode rabin rayuwata." girgiza kansa yayi yana kallona tare da kannare idonsa " 'Dan sake maimaitawa naji sunana." yafada yana min wani irin kallo.......Hannunsa na rike tare da fadin"Rabin rayuwar Sumayya." yasa dariya tare da girgiza kai yace." Wani lokacin idan kina wani abu har mamaki kike bani! duk wannan soyayyar da kike nuna min anjima ba zata hanaki kiyi min rashin kunya ba. Nace" Allah ya tsarani na raina ka kaifa mijina ne wallahi duk wani abu daka ga inayi maka a kan gaskiya ne, gashi dai mun dade a tare amma ka kasa gane halina." Agogon hannunsa ya duba yace."Ni zan fadawa kowa halinki sumayya kina da kirki sosai amma baki yarda da zalinci ba kina da amana uwa uba addini bakya wasa da ibadah ke d'in 'yar baiwa ce ina kuma alfahari da samunki a matsayin matar aurena." Sosai naji dadin yanda yake yabona rungumeshi nayi nace"nagode rabin raina naji dadi daka fahimci wacece ni ina rokon Allah ya dawwamar mana da zaman lafiya a tsakaninmu Allah ya baka ikon adalci tsakanin matanka." Ya amsa da ''ameen my love yau dai kinsa na makara dubi time." da sauri na duba agogon hannunsa takwas da rabi nace" Gaskiya nayi laifi nasan jama'a nacan na jiranka idan kaje kace su yafe min.'' yana kokarin fita yace." Gurin Lawisa zaki nemi afuwa dan kin cinye mata lokacinta a yanzu dai ba zan samu damar shiga gurinta ba sai na dawo." hannu na daga masa da fad'in "Allah ya tsareka a duk inda kake." ya amsa da ameen ya Allah." Ajiyar zuciya na sauke na zauna kan kujera ina jin wani irin farin ciki a cikin zuciyata, inama ba zamu sake samun matsala da juna ba. "Aunty Lauratu bana so wani mummunan abu ya biyo baya akan abinda kuke kokarin aikatawa dan Allah kada kuyi mata lahani ku kyaleta ita da cikinta nima insha Allahu zan samu." Lawisa ce take wannan maganar.......Hajiya Karima tace"Wato Lawisa har kin saduda ko? yarinya tayi sanadiyar da aka rataye d'an uwanki ki dinga nuna tausayinki akanta meye amfanin wannan yarinyar idan bamu bi dare da rana mun kasheta ba."!!! A tsorace! ta kalli Mahaifiyar tata za tayi magana Lauratu tace"Ke! dallah rufe mana baki mara wayo kawai! wato ke har kin amince da dadin bakin da yayi miki ko har kina magana akan mu tausayawa kishiyarki to bari kiji wannan yarinya Sumayya ba zata haife cikin jikinta lafiya ba sai munyi ajalinta." "Aunty Lauratu dan Allah ku bar al'amarin kada ku janyowa kanku wata masifar kunga garin irin haka Muddibo ya rasa rayuwarsa wallahi ni yanzu duniyar gabadaya tsoro take bani kuyi hakuri da daukar fansar nan kada ku janyo mana tashin hankali." Hajiya Karima tace"Kinga Lawisa tashi ki koma gurinki tunda ba zaki bamu hadin kai ba, kije kawai kafin ku dawo daga inda kuka nufa komai ya zama tarihi." Lawisa jiki a sanyaye ta mike ta bar musu gurun, koda ta koma sashenta kasa aikata komai tayi ta dinga tunanin yanda zata 'bullowa al'amarin tana jin tsoron mahaifiyarta da kanwarta su janyowa kansu wata masifar gashi Wali baya gari bare ta sheda masa idan ta kira wayarsa bata shiga abin duniya ya taru yayi mata yawa sam bata so suyi tafiyar nan wani mummunan abu ya faru. Ranar talata ranar ce ta kama ranar tafiya ya shigo gurina cikin shiri sai dai babu walwala a tare dashi, ganin haka yasa na danne damuwata na shiga kwantar masa da hankali ya rungume ni tsam! a jikinsa yana bani hakuri nace"Dan Allah ka daina bani hakuri kana sanyawa gwiwata tana sanyi wallahi." fuskata ya sumbata yana kallona yace."Sumayya dole na baki hakuri tafiyar nan kamata yayi ace dake zanyi domun na kula dake da babyna amma Allah bai nufa ba insha Allahu Allah zai kula min dake." Nace"Ka gama magana tunda kace Allah insha Allahu zai kare ni cikin kariyarsa, hannuna ya rike muka fita falo tare yace."Sati uku kamar yau ne insha Allah ki kwantar da hankali ki.'' nace"Allah ya kaiku lafiya ya kuma dawo daku lafiya cikin nasara." Ya amsa da ''Ameen ya Allah." Hannuna ya saki da sauri ya kama hanyar fita, naji zuciyata ta karye hawaye suka zubo min da sauri nayi gaggawar shigewa daki dan bana bukatar ya juyo yaga halin da nake ciki, kwanciya nayi kan gado na dinga share hawaye ina jin wani irin kewa da damuwa a cikin raina... *Na kudi ne.* Koda zaki ganshi a gruops na sata ne idan kina bukatar biya ga yanda abin yake...Vip gruop#600 normal gruop#300 account... 0542382124...Binta umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne saki kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:28 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 104 Tunda suka tafi na kasa sakewa a gurina haka kawai sai na dinga jin fargaba da tsoro na dinga ganin tamkar wani mummun abu zai faru dani, kawai sai na tsiri zuwa gurin Mamma na wuni a can sai yamma nake komawa gurina, yawan zuwan da nake gurinta yasa ta gane cewa ina da ciki sosai ta nuna farin cikinta a fili tayi ta mamakin al'amarin nidai kunya ta hanani nace mata komai kasa hakuri tayi sai da ta tambayeni watannin cikin na fad'a mata watansa biyar, tace"Amma saboda baku da kirki dake da babana aka rasa wanda zai fada min ga ciki yayi kwari ban san dashi ba haka kuma Maimartaba bai sani ba meye abin 'boyewa a ciki." shuru nayi ba wai dan bani da abin fada ba sabida nasan idan na fad'a mata irin abubuwan da suka dinga faruwa kafin samuwar cikin sai ranta ya 'baci shiyasa nayi shuru domin fada mata bashi da amfani. wayarta ta dauka ta shiga kiran yaron nata, ina daga inda nake ina jin muryarsa suna gaisawa, tace"Babana ashe ka iya munafurci dama."? Da sauri yace."Mamma me ya kawo wannan maganar kuma."? tace"Sumayya nada ciki amma saboda rashin kirki kwanaki dana tambayeka kace babu saboda kana so kayi wasa da hankalina ko." murmushi yayi yace."Afuwa Mammana ni kaina wallahi yarinyar 'boye min tayi sai daga baya na ganshi." tace"To daka tabbatar dashi me yasa baka zo ka fada min ba." Yace."Mamma ki gafarce ni wallahi ina jin kunyar nazo na fada miki cewar Sumayya nada ciki shiyasa nayi shuru da bakina idan ya fito nasan dole ki gani." Tace"Ni ban yarda da maganarka babana watakila dai akwai abinda kake 'boye min." Gabansa ne ya fad'i! yace.'' Haba Mamma me zan 'boye miki kina matsayin uwata dan Allah ki yarda da maganata." Ajiyar zuciya ta sauke tace"To na amince da maganarka amma Sumayya zata dawo gurina ta zauna har sai sanda kuka dawo tukkuna." Yace."To babu komai Mamma ai kamar yau zamu dawo tunda yanzu gashi har munyi sati guda." Tace."To masha Allah ina rokon Ubangiji Allah ya dawo daku lafiya.'' Ya amsa da ''ameen ya Allah." kashe wayar tayi ta juyo tana kallona da murmushi a fuskarta tace"Kinji yanda mukayi da mijinki ko." nace"Naji mamma nima zanfi so na dawo nan din." Tace"To shikkenan bayan sallar isha'i sai kuje tare da Jakadiya ki dauko abunda zaki bukata." nace"To godiya nake ranki ya dad'e." Tana wani irin kuka take fad'in "Wallahi na daina yarda kana amfani dani da kwaroran roba(Condem) sai kace karuwa zaka dinga gudun haihuwa dani wato ita wacce kake so ka bari ta dauki ciki ni kuma ka yaudareni ka dibga min kwayoyi yanzu kuma ka dawo kana sa condem to na gane yanxu wallahi idan baka daina ba sai na tona maka asiri."! cikin kuka na fitar hayyaci take maganar." A fusace! yace." Lawisa kada ki fasa tona min asiri a gida idan kin fad'awa iyayena abinda yake faruwa a tsakaninmu wallahi sai kinyi mamakin hukuncin da zanyi miki! kuma bazan cire condem ba duk abinda zakiyi sai dai kiyi." Da sauri ta janye jikina tana kuka tace"Ni kuma wallahi na daina amincewa da kai kana cutar dani da mugun halinka sai Allah ya saka min."!! mari ya kwada mata yana huci! yace."ai baki fi karfina ba yanzu zan biya bukata ko kina so ko bakyaso." kafin tayi wani yunkuri ya turmushe ya shiga biyawa kansa bukata ba tare da ya cire condem din ba.........sai da yayi me isar sa sannan ya daga ta yaje yai wanka ya fito ya shirya jikinsa ya fita ya barta cikin yanayi na tsantsar damuwa da tashin hankali. Tare mukaje gurina da Jakadiya ta zauna a falo ni kuma na nufi dakina domin harhad'a 'yan kayan da zan bukata, ina sanya 'kafata a cikin d'akin santsi ya kayar dani! wata irin fad'uwa nayi cikina ya daki! 'kasa da karfin gaske! rintse idona nayi tare da kiran sunan Allah da karfi! dakin ne yayi duhu! cikin karfin hali nayi yunkurin mikewa! naji saukar duka akaina! fad'uwa nayi ina kiran sunan Allah da karfin gaske nace"Jakadiya."!!!!!! a guje! ta shigo dakin tana amsawa tare da laluben mukunnin fitila, ji tayi an bangajeta an fita a guje! salati tasa da sauri ta kunna fitilar! dakin yayi haske! ganin ta a kwance tana murkususu yasa hankalinta ya tashi! zubewa tayi a gabanta tana kiran sunanta jikinta sai rawa yake.......Cikin karfin hali nace"Jakadiya mutuwa zanyi."!! hawaye ta share tace"Ba zaki mutu ba sumayya Allah zai toni asirin duk wanda yake kokarin cutar dake......da sauri ta mike ta fita nan ta samu masu tsaron gurin a tsaitsaye suna magana tace''Ina fata dai kun gane wanda ya fito yanzu." gabadayansu suka ce "Babu samu nasarar kama ta ma dan kayan dake jikinta irin na bayi ne shiyasa ba muyi tunanin wani abuba." Jakadiya da sauri ta bar gurin dan ba taga amfanin tsayuwarta ba. Su Mariya ne suka rufu akanta suna mata firfita gabadayansu hankalinsu ya tashi da abinda ya faru da uwar dakin nasu, suna cikin dakinsu suka jiyo ihun ta dalilin da yasa kenan suka fito a gigice! Ganin jini ya 'bata mata zanin jikinta yasa hankalinsu ya kara tashi shikkenan suma suna cikin gariri dole a tambayesu yanda akayi suka bari ta shigo gurin har ta samu nasara. Mamma da Jakadiya suka shigo dakin hankalinsu a tashe! lokacin Sumayya ta galabaita mutuka, mamma ganinta cikin mugun yanayi yasa ta fashe da kuka rungumeta tayi jikinta duk ya 'baci da jini tace"Sumayya Allah ya saka miki." jin miryarta yasa na 'kan'kame! hannunta ina nishi! nace"Mamma Lauratu ta samu nasara akaina shikkenan nasan sun kashe min baby." wasu zafafan hawaye suka shigo zubo min........Rungumeni tayi tana tofa min adduoi...cikin wannan hali Shatima ya shigo hankalinsa a tashe yace."Mamma ku kamata muje asibiti a dubata." Mamma ta mike jikinta duk ya mutu ta riga ta futar da rai da cikin da ta kwallafa rai dashi....... Jin cewar matar mai asibitin ce yasa likitoci suka rufu a kanta sai da suka tabbatar da cewa komai yayi daidai sannan hankalinsu ya kwanta.........Mamma ajiyar zuciya ta sauke mai sanyi lokacin da ta gama sauraran jawabin da Dr Sadiya take mata, tace"Alhamdullh dr dama ni fargabata kada ace cikin ya zube tunda dai Allah ya takaita to sai mugodewa masa kuma sannuku da kokari Allah ya saka muku da alkairi." Dr Sadiya tace"babu komai ranki ya dade an jima kadan zaku iya shiga ku dubata yanzu tana bacci." Mamma tace"To babu damuwa." Dr Sadiya ta bude musu wani daki suka zauna a ciki suna jajanta al'amarin..........A daran Maimartaba da Waziri tare da Mahaifinta Lawi sai da suka zo asibitin suka duba ta basu tafi ba sai da ta tashi suka tabbatar da lafiyarta sannan suka tafi ita kuwa Mamma kasa tafiya tayi tasa Shatima ya shedawa D'an uwan nasa abinda yake faruwa, lokacin yayi ta kiran wayarsa bata shiga tace ya bari da safe sai ya kirashi ya fada masa............... Hannuwana ta rike tace"Sumayya ba kuka za kiyi ba Allah zaki godewa daya kare ki daga sharrin masu sharri Kiyi shuru ki kwantar da hankalinki ki fada min dukkanin abinda yake faruwa." Hawaye na share a hankali na soma yi mata bayanin abubuwan da suka dinga faruwa a tsakanina dasu. Hawaye ta share tana girgiza kanta tace" Wannan rashin imani da rashin tsoron Allah na hajiya karima yana bani mamaki! wato ashe bata hakura ba shine take so ta dauki fansa akanki ai bake kika sa aka rataye danta ba da zata dinga bibiyarki da sharri! ki daina kuka sumayya insha Allah sunyi na farko sunyi na karshe sai an dauki mataki mai tsauri akansu sai sunyi da sun sanin abinda suka aikata miki, dama ita wannan Lauratu shaidaniya ce dan ta kashe mutum ba sabon abu bane a gurinta to wannan karon sai tayi nadamar abinda ta aikata. Da asubah bayan ta idar da sallah, kira ya shigo wayarta koda ta duba sai taga yaron nata ne a nutse ta daga tare dayin sallama............Murya a sha'ke Lawisa ta amsa tare da fad'in "Mamma ina fata kun tashi lafiya." a sanyaye tace"Lafiya lau Lawisa ina fatan kuna nan lafiya?" kuka ta fashe dashi! Mamma hankalinta ya tashi tace"Lawisa lafiya kike kuka ina babana yake."? Lawisa kasa magana tayi ta cigaba da gurshe'ken kukanta. Mamma jikinta dik yayi sanyi tace"Lawisa ki daina kuka ki fada min abinda ke faruwa ko fada kukayi dashi ne."? murya a sar'ke tace"Mamma ki gafarce ni nasan idan kikaji abinda yake tafe dani hankalin ki zai tashi." Tace"Lawisa ai yanzu hakama a cikin tashin hankali nake dan jiya da daddare Kanwar mamakin Lauratu ta shiga har gurin Sumayya tayi yunkurin cutar da ita dan yanzu hakama muna asibiti." Lawisa taji gwiwarta tayi sanyi jikinta na rawa tace"Mamma dan Allah kuyi hakuri Aunty Lauratu ba zata aikata haka ba." cike da mamaki tace"Lawisa kin san halin kanwar mamanki nima na san halinta na kuma nasan abinda za tayi da wanda ba zata aikata ba Lauratu shigarta prison nawa saboda aikata munana ayyuka shine Mahaifiyarki ta hada baki da ita suke bibiyar rayuwar Sumayya saboda su dauki fansa akan abinda ya faru." Lawisa kuka kawai take gabadaya kanta ya kulle ta rasa wane irin tunani za tayi dama tasan dole sai asirinsu ya tonu shiyasa tun kafin su aikata ta hanasu saboda gudun abinda zai faru dasu. Mamma tace"Ki daina kuka ki fada min abinda ya hadaki da mijinki." Hawaye ta share ta dan juya ta kalli toilet yana ciki yana wanka bayan ya gama sasakarta wallahi tai rantsuwa da Allah sai ta tona masa asiri tunda ya kasance azzalimi. Cikin kuka da nadama ta shiga fada mata abubuwan da suke faruwa. Mamma ta shiga tsantsar tashin hankali dajin abinda Lawisa ke fada mata, babanta shike gudun haihuwa har yana saka kwaroron roba sabida kada ya samu zuria! wannan al'amari yayi masifar tashin hankalinta, waiwaya tayi bayanta tana kallon Sumayya dake bacci! cikin zuciyarta tace"Wannan yarinya babu abinda zance dake a duniyar nan kinyi min hallaci tabbas samun irin masu halinki zaiyi wahalar gaske........Ajiyar zuciya ta sauke tace"Lawisa daina kuka ki saurareni." hawaye ta share tace"Ina jinki Mamma." Tace"Kiyi hakuri kinji ko insha Allah haka ba zata sake faruwa ba, sannan duk ranar daya kuma zuwa zai sadu dake da kwaroro a jikinsa kada ki amince dashi! idan kun dawo gida zan dauki mataki akansa inaso kuma ki rufa asirin maganar nan dan idan kin fito kin fada kin tonawa kanki asiri sannan kuma kin tona asirin mijinki amma hakikanin gaskiya babana bai kyauta miki ba amma kada ki damu zan dauki mataki akansa." Zuciyarta tayi sanyi tace"To shikkenan Mamma nagode sosai Allah ya kara girma." Sallama sukayi ta kashe wayar tana jin sanyi a cikin ranta, tana juyowa suka hada ido ya fito tun dazu kuma komai kunnensa. hannu ya mika mata da fadin" Bani waya ta." jiki a sanyaye ta mika masa ya kar'ba yana kallonta yace."Sai da kika fada mata ko."? hawaye ta goge tace"Ya za'ayi ba zan fada mata ba kana cutata.'' Yace'' To kin janyowa kanki saki." kallonsa tai gabanta na mugun faduwa! yace." Na fada miki cewa duk ranar da kika kuskura kika fitar da sirrina wani yaji to zan miki hukunci da bakiyi tsammani ba munyi haka da Sumayya kuma ta kiyaye ke da yake baki da mutunci kika kira mahaifiyata ko? to kisa a ranki cewa daga yau ke ba matata bace."!! Ihu! ta kurma! ta zube a gurin tana kuka da rokonsa akan kada ya saketa ya tausaya mata, fizge kafarsa yayi yasa kayansa ya fita daga dakin ransa a mugun bace. *Na kudi ne* Koda zaki ganshi a gruops na sata ne idan kina bukatar ki biya kudin karatu ga yanda abin yake....Vip group #600 normal gruop#300 account.. 0542382124...Binta umar gtbank....idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number. *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:28 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊? 106 Koda nayi wankan sai naji dadin jikina na shirya tsaf na fito falon kawai sai na samu Tambaya ita da Mamma a zaune suna hira. wani irin farin ciki ne ya lullubeni dama tun ina asibiti nake tunaninta gwara Baba shi yaje tare dasu Maimartaba, fuska a sake na zauna ina gaisheta ta amsa cike da kulawa kallon da take min ne yasa na gane cewar taji dadin ganina kalau tace" ya jikin naki." ? nace"Jiki yayi sauki alhamdulillahi." Mamma tace." Da kikayi wankan Kinji karfin jikin naki ko."? nace"Sosai kuwa Mamma naji dadin dana gasa jikina." tace." To haka akeso sai kici abinci kisha magani nima zan shiga nayi wankan." nace"To mamma a fito lafiya." Tambaya tace"Ranki ya dade a fito lafiya watakila kafin ki fito ni na tafi." Mamma tace"A'a Tambaya kada ki tafi ki bari na fito tukkuna." Tace."To shikkenan ranki ya dade.'' Mamma mikewa tayi ta shiga dakinta..........Tambaya ta kalleni tare da sauke ajiyar zuciya tace" Sumayya naji dadin da wannan mata bata samu nasara akanki ba jiya dai saboda tsabar fargaba da tashin hankali kasa rintsawa nayi sai da na samu labarin dawowarku daga asibiti hankalina ya kwanta dalilin da yasa kenan na shigo domin na duba lafiyarki." Nace."Tambaya duk mutumin daya dogara da Allah to babu shakka Allah na tare dashi, Lauratu tayi nufin cutar dani Allah ya kareni daga sharrinta wannan kad'ai ya isa ya nuna mana 'Kadaitakar Ubangiji sun nufe ni da sharri na mayar da al'amarin gurinsa shi kuma ya mayar musu da sharrinsu kansu Allah nagode maka." Ajiyar zuciya ta sauke tace"Sumayya ni kaina na 'kara jin tsoron Allah a zuciyata wannan abu da ya faru da Hajiya Karima da k'anwarta ishara ce Allah ya nunawa masu irin halinsu." Nace"Hakane Tambaya yana da kyau duk wani musulmi ya tsarkake zuciyarsa ya kuma kadaita Allah shi kad'ai kada ya hadashi da abokin tarayya sannan kada ya zalinci wani idan an zalince sai ya barwa Allah da sannu zai saka masa abisa zalinci da akayi masa Allah kasa mufi karfin zociyoyinmu." "Ameeen tace tana girgiza kanta.......Mamma ta fito daga dakinta cikin kamala gabadaya falon ya cika da kamshin turaranta, Jakadiyarta ce a bayanta hannunta rike da tarin kayan sawa. gurun zamanta ta zauna da mirmushi a fuskarta tace" Tambaya na barki kina jirana ko."? Tambaya ta sunkuyar da kanta tana murmushi tace"Aa ranki ya dade babu damuwa ai ina fata kin fito lafiya."? tace"Lafiya lau Jakadiya bata wannan kayan na hannunki.'' da sauri Jakadiya ta mika mata kayan.....Tambaya tasa hannu biyu ta kar'ba fuskarta yalwace da fara'a. Mamma tace"Kije kiyi amfani dasu daga yau ki daina amfani da kaya irin na bayi a masarautar nan kun zama masu 'yanci insha Allahu idan Maimartaba ya samu nutsuwa zamu zauna dashi za'a sanja muku gurin zama. Cike da murna da farin ciki nace."Mamma godiya suke da wannan karamanci Allah ya saka da alkairi ya kara girma." Murmushi kawai tayi ba tace komai ba, Tambaya godiya kawai takeyi bakinta yaki rufuwa addua take gami da fatan alkairi. Mamma ta dakatar da ita da tare da fadin" Godiyar ta isa haka duk wani abu da taga anyi musu a masarauta sun cancanta ne saboda haka babu kalmar godiya a tsakaninsu. Cikin tsantsar farin ciki Tambaya tayi mana sallama Jakadiya tabi bayanta tare da kayan da Mamma tayi mata kyautarsu Sai Bayan La'asar Maimartaba ya shigo, cikin nutsuwa na gaisheshi ya amsa cikin kulawa tare da tambayata yanayin jikina, nace"Naji sauki sosai." shuru gurin yayi na yan mintina kafin ya kira sunana na amsa a nutse tare da sunkuyar da kaina kasa, Yace."Kiyi hakuri abubuwan da suka faru dake inaso ki daukesu a matsayin kaddara insha Allahu abu makamancin wannan ba zai sake faruwa dake ba." Nace"Ranka ya dade insha Allah magana ta wuce a gurina na barwa Allah komai suma wa'inda suka aikata mugun abu akaina na yafe musu har abada sannan kuma ina nema musu shiriya daga gurin Ubangiji." Yace."To alhamdulillhi dama haka akeso mutum ya kasance mai saukin kai da saurin afuwa." Ya kalli Mamma a nutse yace."Hajiya Karima ta samu nutsuwa kuma tayi mana bayanin yanda duk al'amura suka kasance yanzu haka tana can cikin damuwa da tashin hankali tayi kuka tamkar ruwan hawayenta zai 'kare gabadayanku tana neman afuwa a gurinku keda Sumayya tayi alkawari akan insha Allahu ba zata sake aikata abu makamancin wannan ba, na yafe mata saboda na yarda da tubanta kuma inaso ku yafe mata mussaman ke Sumayya." Mamma ta sauke ajiyar zuciya a sanyaye tace"Ranka ya dade shiriya dai ta Allah ce amma wallahi gani nake kamar karya take so take a kuma sakin jiki da ita ta sake aikata wani mugun abun yana da kyau a dauki mataki a kanta." Girgiza kansa yayi yace."Fulani ki kyautata zaton alkairi akanta a yanda take kuka take rokon gafara yasa na gazgata tubanta saboda haka kema inaso ki cire shakku akanta kiyi mata kyakkyawar addua.'' Tace."To shikkenan ranka ya dade Allah ya yafe mata ya yafe mana baki daya. Yace."Yanzu jikin Ciroma ne yayi tsanani nasa an daukeshi an kaishi asibiti hakika yana bukatar addua dan bai san inda kansa yake ba." Gabadaya daga ni Har Mamman jikinmu ne yayi sanyi dan jin yanda Maimartaban ke mana bayanin yanayin jikin d'an uwan nasa. Uwargida da tawagar 'ya'yanta ne suka shigo falon, kallo muka bisu dashi jiki a sanyaye suka samu guri suka zazzauna.......Maimartaba ya bisu da kallo cikin nutsuwa yace."Ina fatan dai lafiya." ? Hajiya Huwaila ta fashe da kuka tana girgiza kanta, kawai sai suma su aunty Safiyyan suka shiga kuka. Falon ya rikice da koke-koke! Maimartaba yasha jinin jikinsa tabbas ruwa baya tsami banza. Mamma ta matsa kusa da Ita kafad'arta ta dafa cikin nutsuwa ta shiga kwantar mata da hankali akan tayi shuru dukkanin abinda yayi tsanani maganinsa Allah. Huwaila ta kama hannunta ta rike tana hawaye tace"Fulani ki gafarce ni hakika na dade ina cutar dake da d'anki bana kaunarku kullum cikin shirya muku mugun abu nake, babu irin jifan da banyi miki ba Allah na kareki Aliyu kuwa babu irin abinda ba muyi masa ba nida 'ya'yana Allah yana 'kareshi Wannan yarinyar Sumayya ita ta zama garkuwa a gareshi dan duk wani abu na cutarwa da zamu nufeshi dashi itake wargazashi sosai muka dinga tsoratar da ita akan hakan amma da yake yarinyar arziki ce ba taji tsoro ba ta cigaba da bashi kariya hakika samun jajirtattun mutane masu tsoron Allah irin wannan yarinya zaiyi wahalar gaske! a lokacin da hukuncin rataya ya sauka akan Muddibo dukkaninmu hankalinmu ya tashi domin mun dauka zai fad'o sunayenmu a cikin wa'inda suke bashi gudumawa domin cikar burinsa sai mukaji shuru har aka rataye shi sunayenmu basu fito ba wannan abinda ya faru da Sumayya yasa gabadaya jikinmu yayi sanyi muka ga dacewar muzu mu nemi afuwa a gurinku akan abubuwan da suka faru a baya hakika mun tsorata da irin mutuwar da Lauratu tayi ga Hajiya Karima cikin wani irin mugun yanayi mara kyau ga Ciroma a kwance rai a hannun Allah babu shakka hakkin wa'inda suke zalinta ne ya sauka a kansu Ranka ya dade muna neman gafara a gurinka kema Sumayya ki yafe mana abinda muka aikata a gareki." Cikin kuka ta 'kare maganar. Gabadaya shuru mukayi muna jajanta al'amarin, ni banyi wani mamaki sosai ba sabida dama na riga na san abinda yake faruwa.....Maimartaba da Mamma ne naga hankalinsu ya tashi gabadaya ma sun kasa magana. Aunty Bishira tazo ta kama kafafun Mahaifin nata tana hawaye tace"Ranka ya dade kayi hakuri da abinda muka aikata ka gafarce mu kada kace ka yafewa duniya mu." Girgiza kansa yayi a nutse yace."Bishira ni bani kukayi wa Laifi ba gurin Allah zaku nemi afuwa da gurin wa'inda kuka zalinta wato Magajin sarki da matarsa idan kun rokesu sun yafe muku to nima na yafe muku ina kuma rokon Allah ya kara shiryar min daku akan tafarkin addinin musulunci." Hajiya Huwaila ta sauka kasa gaban Mamma ta gurfana tana hawaye tace"Fulani ki yafe min abinda nayi miki na cutarwa." Mamma murya na rawa tace"Na yafe miki Huwaila Allah ya yafe mana gabadaya. Gabana ta gurfana tana hawaye ta rike hannunta, gabadaya 'ya'yan nata suka kewaye ni suna rokona gafara, da sauri nace"Ni wallahi ba kuyi min komai ba idan ma kunyi min na yafe muku har abadah." godiya sukayi suka koma gurin zamansu Maimartaba yace."To Alhamdullhi yanzu sai mu jira dawowar Magajin sarki gabad'ayanku sai ku nemi afuwarsa Allah yayi mana afuwa baki daya." gabadaya muka amsa da "ameeen ya Allah." ******* Bayan sati daya masarautar ta dan samu nutsuwa amma ba sosai ba tunda har yanzu Ciroma na kwance a asibiti an kasa gane abinda ke damunsa ta bangaran Hajiya Karima ana tunanin ma ta samu matsalar 'kwa'kwalwa dan kullum sai anyi mata allurar bacci da daddare ake samun nutsuwa gabadaya dai al'amarin sai addua............Maimartaba guri na mussaman yasa aka gyarawa iyayena komai na bukata aka sa musu sannan yasa aka dinkawa mahaifina manya kaya yana amfani dasu kuma kullum yana tare da Maimartaba a fada, Hankalina ya kwanta sosai ganin iyayena cikin nutsuwa da kwanciyar hankali......... Ana saura kwana biyu su dawo ya kira wayata bayan mun gaisa da juna yace na kaiwa Mamma wayar yana so yayi magana da ita, koda na kai mata wayar k'in kar'ba tayi nayi nayi da ita ta'ki 'karba jiki a mace na koma dakin da wayar a hannuna, ya sake kira a sanyaye nace"Ta'ki kar'bar wayar." Shuru yayi nace"Wai dan Allah wane laifi ka kuma yi mata wanda yasa take fushi da kai haka, kwanakin da suka wuce naga idan ka kira wayarta tana dauka har ku dad'e kuna hira amma cikin satin nan gabad'aya ta'ki sauraranka kusan kullum ma da damuwa take wuni." Zazzafar ajiyar zuciya ya sauke! yace." Lawisa na saki shine take fushi dani." Gabana ya fadi! jin abinda yace, nace"Ranka ya dade mai yayi zafi! kaida 'yar uwarka zaka saketa me tayi maka? haba kai kuwa ka barta taji da abu daya mana iyayenta babu lafiya kai kuma ka saketa ina ganin ko wane irin laifi tayi maka ai bata cancanci irin wannan hukuncin ba." "Sumayya Lawisa ba matar rufin asiri bace " shuru nai ina sauraransa ya cigaba da cewa" A lokotan baya kafin na gane gaskiya na ta'ba cewa dake idan kika sake kika fitar da sirrina wani yaji zanyi miki mummunan hukunci ko."? Nace."Eh kwarai haka ya faru." Yace."A lokacin da kinyi gangancin fad'awa mahaifiyata bana san haihuwa zan sake ne sai Allah yasa kika kasance mai hankali da hangen nesa mai kuma rufe sirrin mijinta wannan janyo miki kima da martaba a idona sannan kuma ba kiyi zuciya ba kika cigaba da nuna min gaskiya har Allah yasa na gane na dawo kan hanya madaidaiciya hakane ko ba haka bane."? Da sauri nace"Eh hakane." Yace."Ita Lawisa saboda ta raina ni ta kuma raina maganata sai ta kira Mamma a waya ta fad'a mata duk abunda yake faruwa, wannan dalilin yasa na yanke igiyar aurena dake kanta." Murya na rawa nace"Gaskiya wannan ba hukunci bane! me yasa ku maza daga zarar mace tayi muku laifi sai ku saketa ku dinga adalci mana laifinka shine a kan gaba akan nata me zai sanya ka yanke mata irin wannan hukuncin a kan gaskiyarta ni dai don Allah ka mayar da ita dakinta shine farin cikina." Yace."Sumayya ba zan mayar da Lawisa ba dama can ni bana sonta wallahi ke nake so." Kuka nasa nace"Ni kam idan baka mayar da ita ba bazan ji dadi ba kuma idan kana so na tabbatar da maganar kana sona to ka mayar da ita dakinta shine farin cikina." Da sauri yace." Bana so kina kuka bana kusa dake my lov akan me zaki dinga zubar da hawayenki akan Lawisa kiyi hakuri ki bar maganar nan ni ke kadai kin isheni rayuwa." Nace"Ni dai bazan yi hakuri ba har sai ka mayar da ita zan daina zubar da hawaye kuma ko ka dawo ba zakaga walwalata ba." murmushi yayi yace."To shikkenan ki daina kuka zan duba maganarki." Hawaye na share nace'' to zuwa dare ka yanke hukunci kuma kada naji sa'banin abinda nake tunani." murmushin dai ya kuma yi yace."Sumayya zuciyarki tana da kyau wallahi wace macace ce take son kishiya ai na dauka murna zakiyi dana saketa." Murmushin takaici nayi nace"Haba sai kace ba mace ba zanyi murna dan ka saki matarka ciwon ya mace na 'ya mace ne kai da kanka kace dani na fitar maka da sirri sai ka sake ni to me zai sanya nayi farin ciki akan hakan nasan nima hakan na iya kasancewa dani." Girgisa kansa yayi kamar tana gurin yace."No Sumayya ba zan iya rabuwa dake ba idan kuwa kaddara ta gifta a tsakaninmu nasan nida jin dadi har na qare rayuwata.'' Murmushi nayi nace"To na amince da maganarka yanzu sai naji labari mai dadi akan Lawisa." yace."Okey to inaso dan Allah ki cigaba da rarrashin Mammana kafin na dawo." nace"Kada ka damu insha Allahu zata yafe maka mutukar ka janye sakin da kayiwa Lawisa." Yace."Zanyi tunanin hakan." sallama mukayi da juna na kashe wayar tare da ajiyeta a kusa dani.... *Na kudi ne..* Koda zaki ganshi a group na sata ne idan kina bukatar biyan kudin littafin ga yanda abin yake.....Vip gruop#600 normal gruop#300 account... 0543282124.....Binta umar gtbank....idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:28 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 105 Cikin tsananin damuwa ya shiga kiran wayar mahaifiyar tashi, Mamma na ganin kiran wayar da sauri ta daga dan ta dauka Lawisan ce ta sake kira, jin muryarsa yasa da sauri ta datse kiran ta ajiye wayar gefanta, sake kiran wayar yayi ta dauka rai a 'bace tace"Me kuma za kace dani babana."? a sanyaye yace.''Mamma dan Allah kiyi hakuri kada al'amarin nan kada ya d'aga miki hankali Lawisa karya take duk abinda ta fada miki." Girgiza kanta tayi tace"Babana in dan duk jikina kunne ne to bazan yarda da maganarka ba, Lawisa gaskiya ta fada min nasan halinka babana nasan abinda za kayi da wanda ba zaka aikataba wato zama da turawa yasa ka dauki d'abi'unsu kana gudun rahamar Allah har kana dibgawa iyalinka kwayoyi dan kar su dauki ciki ko."? Murya na rawa yace."Mamma dan Allah ki tsaya ki fuskance ni kada ki dauki al'amarin nan da zafi ya janyo miki bacin ra......Katseshi tayi ta hanyar fad'in" Na fada maka fa duk abinda zaka fada min bazan yarda dakai ba, aini babu abinda zance da yarinyar nan Sumayya tayi namijin kokari data tsaya kai da fata taki daukar hud'ubar ka da tuni wannan cikin dake jikinta babu shi inda ta amince da tsarinka na rashin son haihuwa yanzu na gane dalilin da yasa kake 'boye min tana da ciki saboda ka samu damar zubar dashi cikin ruwan sanyi to insha Allahu bukatarku ba zata biya ba dakai da Lauratu kuma ka tabbatar da cewa sai Maimartaba yasan da wannan magana." Tana gama maganarta ta kashe wayar ta barshi da tasa a kunne, zamewa yayi yai zaman dirshan a inda yake, yana cikin tunanin mafita kira ya shigo wayarsa yana dubawa yaga Shatima ne hannu na rawa ya daga, Shatima yace."Wai ya akayi ne tun jiya ba'a samunka a waya.'' Jiki a mace yace."Matsalar network ne.'' Yace."Nima sai dana zargin hakan to ya mukaji da wannan abu da ya faru."? Gumin goshinsa ya goge yace."Wai shin Shatima me yake faruwa ne yanzu muka gama waya da Mamma amma ban fahimci inda maganarta ta dosa ba." Shatima ya sauke ajiyar zuciya da fadin"Dama yanda take cikin tashin hankali ai bai zama lallai tayi maka bayanin da zaka fahimta ba......... abinda ya faru shine..............Shatima ya warware masa dukkanin abinda ya faru. cikin tashin hankali da damuwa yace."Shatima ina fatan Yarinyar nan sumayya bata hadu da wani tsautsayi ba wallahi gabadaya jikina yayi sanyi jin yanda kace ta zubar da jini da yawa ina jin tsoron wani mummunan abu ya faru da lafiyarta. Shatima yace."Ka kwantar da hankalinka ma'aikatanka sunyi kokari sosai akanta a daran suka tsaya a kanta sai da komai yayi daidai sannan hankalinsu ya kwanta yanxu haka. ita da abinda ke cikinta na cikin koshin lafiya." Sanyi yaji a cikin ranshi yace."Shatima nagode kwarai da kulawarka yanzu ina Labarin Lauratu kasan Allah sai na daureta." Shatima ya girgiza kansa cikin takaici yace." A daran nasa ayi binkice akanta ba'a ganta ba, sai da naje na turke Hajiya Karima tukkuna take sheda min cewa wai itama bata san inda take ba yanda take yi min bayani yasa nagane cewa bakinsu d'aya yanzu dai binkice ya nuna mana cewa Lauratu ta gudu dan babu irin neman da ba'ayi mata ba." Cikin zafin zuciya Yace."Shatima tun kafin na dawo ku d'aure Hajiya Karima dan wallahi bazan saurara mata ba." A sanyaye Shatima yace." Kayi hakuri abi komai a hankali mana." murmushin takaici yayi yace."Shatima matar nan fa idan ba'a dauki tsatstsauran mataki akanta ba to ba zata fasa abinda take ba kasan Allah tasan inda Lauratu ta gudu idan taji matsa zata fadi gaskiya.'' Shatima yace."Wallahi ina jin nauyin yaron nan Wali bayan haka kuma ga Lawisa a matsayin matarka wannan dalilin yasa gabadaya na kasa wani abu akai shi kansa Maimartaba har yanzu bece komai ba nasan yana tunanin irin hukuncin da ya kamata a dauka a kanta." "Shatima babu ruwana da wani dangantaka mutukar akan gaskiya ne me yarinyar nan tayi musu suke neman rayuwarta watannin da suka gabata Lauratu har cikin daki ta sameta da asid zata watsa mata Allah ya kareta yanzu kuma sun shiga da niyyar kasheta sai kuma kace akwai dangantaka to inaso na fada maka cewa a yanzu ni Lawisa ba matata bace na saketa.'' Shatima yace." Innalillahi wa'ina ilahi! raji'un! Magajin sarki me yake damunka ne? wane irin abu Lawisa tayi maka da har zaka saketa duka auranmu wata nawa ka yanke wannan d'anyan hukuncin.!!!! Jin yanda Shatiman ke magana a fusace! yasa ya sassauta miryarsa yace."Shatima wannan maganar mu barta dan Allah idan na dawo koma me zai faru sai da ya faru, babban burina a yanzu shine ka cigaba da kulawa da yarinyar nan Sumayya wallahi ita kadaice damuwata a yanzu saboda duk wani abu da zai faru da rayuwarta ta dalilina ne tayi min hallaci a rayuwata tilas nabi mata hakkinta akan dukkanin wanda yayi nufin cutar da ita." Yace."In dai ta wannan ne kada ka damu Sumayya zata cigaba da samun kariya daga gurina insha Allahu zanyi iyakacin bakin kokarina a yanzu dai babban abinda ya d'aga miki hankali maganar sakin nan shine damuwa ta dan Allah inaso ka fada min abinda yarinyar nan tayi maka ka saketa.'' Ajiyar zuciya ya sauke yace."Shatima yanzu ba zan iya yi maka bayani ba saboda bana cikin nutsuwa amma nayi maka al'kawari idan na dawo zaka san dalilin da yasa na saketa." Jiki a sanyaye yace."Okey to babu damuwa Allah ya dawo da kai lafiya." Sallama sukayi da juna kowanne ya kashe wayarsa cikin tsananin damuwa da fargaba. "Mamma dan Allah ki yafe masa kada kiyi fushi dashi akan abinda ya aikata kiyi masa uziri insha Allahu Allah zai ganar dashi gaskiya.'' Da sauri ta juyo tana kallona nasan bata san da cewar na tashi a bacci ba shiyasa take mamakin maganata. A hankali na mi'ke zaune ina kallonta tare da marairace fuskata Karasowa tayi ta zauna a gefena hannuwanta ta ri'ke a sanyaye tace" Sumayya abunda Babana ya aikata ya zama dole a hukuntashi haba sai kace ba musulmi ba ya dinga abubuwa irin na kafurai sumayya meye abin gudu a haihuwa sabida tsabar butulci irin nasa Allah ya barshi da ransa da lafiyarsa ya bashi kyauta amma saboda butulci ya nuna baya so mutane nawa ubangiji ya jarraba da rashin haihuwa suna so suna nema ido rufe Allah bai basu ba amma ya za'be shi ya bashi rabo irin na haihuwa ya dinga kyamata dole sai na hukuntashi Sumayya saboda ina jin tsoron abinda zai faru anan gaba. Hawaye na share nace"Wallahi Mamma abinda nake taso ya fahimta kenan ba kowa Allah kewa baiwa irin wannan ba amma idanunsa sun rufe ya kasa fahimtata Mamma idan kinga irin rigimar da mukayi dashi akan wannan cikin dake tare dani sai kinyi mamaki! hakuri nai tayi ina masa addua kullum ina nuna masa gaskiya Alhamdulillahi kafin yayi wannan tafiyar naga fa'idar adduar da nake masa da kansa ya dawo kan hanya ya cigaba da nuna kulawarsa akaina da cikin da nake dauke dashi Mamma kema don Allah kiyi hakuri kiyi masa uziri akan abinda ya aikata na rashin kyautawa." Shuru tayi tana girgiza kanta, nace"Mamma kada kiyi fushi dashi don Allah insha Allahu Allah ya ganar dashi gaskiya." Kallona tayi tace"Shikkenan Sumayya saboda ke zan yafe masa amma dai duk da haka sai nayi masa fada akan abinda yayi saboda ya kiyaye anan gaba." nace" To Mamma amma dan Allah kada ki fadawa Maimartaba maganar nan bana so hankalinsa ya tashi kuma bana so jama'a suyi masa wani irin kallo." Murmushi tayi tace."Sumayya babana ku yayi wa laifi amma bakyaso ya tozarta a yau na tabbatar da cewa ke matar rufin asirinsa ce insha Allahu zan bar maganar nan a tsakaninmu kamar yanda kika nemi alfarma ina rokon Allah ya tabbatar da alkairi a tsakaninku. Cikin farin ciki na amsa da "ameeen Mamma nagode kwarai da gaske." Dr Sadiya ce ta shigo dakin, ganina a zaune muna magana yasa tayi murmushi tace"Alhamdulillahi jiki yayi kyau ko."? Mamma tace"Aikuwa jiki yayi kyau Allah ne abin godiya." Tace."Yanzu Dr ya kira ni a waya yake tambayata ya yanayin jikin naki dalilin da yasa ma kenan na shigo na duba na gani amma naji dadin ganinki a haka ina fatan babu abinda yake miki ciwo." ? ina kokarin magana kira ya shigo wayarta murmushi tayi ta daga wayar cikin ladabi tace"Eh gani ma a dakin muna tare da ita alhamdulillahi jikinta yayi sauki Dr baby kuma na cikin koshin lafiya." shuru tayi tana sauraransa kafin tace"Okey to bari na bata wayar." da sauri ta miko min na kar'ba a nutse na gaisheshi, ya amsa cikin kulawa yana tambayata nace"Babu abinda ke damuna baby lafiya lau kamar yanda Dr Sadiya ta fada maka.'' Shuru nai ina sauraransa, nace"Eh yana motsi sosai." Hamdala yayi ga Allah yace."Sumayya nasan Mamma tana cikin 'bacin rai dan Allah ki tayani bata hakuri kafin na dawo." Cikin tausasawa nace"Kada ka damu insha Allah zanyi maka kokari Allah ya dawo daku lafiya." ajiyar zuciya mai sanyi ya sauke yace."my lov banda kamarki a duniya." da sauri na kalli Mamma ina jin tsoron kada taji abinda yace...... ya cigaba da cewa'' Tun dana sauka a america nake cikin kad'aici banta'ba tsammanin ina sonki da gaske ba sai da nayi nesa dake." ajiyar zuciya na sauke sosai nake jin dadin kalamansa yace."Idan na dawo koni ko Lauratu ko hajiya Karima dan ba zan barsu sukai labari ba.''' Da sauri nace"Kayi hakuri komai ya wuce insha Allahu dama nace maka Allah ba zai barsu su cimma manufarsu ba kada kayi saurin yanke hukunci." Yace." wancan karon haka kikace nayi hakuri na kuma hakura wannan karon kam ba zanyi ba sai na dauki mataki." shuru nai ina sauraransa yace."Yanzu Dr Sadiya zata sallameku kuje gida ki kwanta ki huta kisha maganguna kinji ko." nace"To shikkenan." Shuru yayi na minti biyu kafin yace."Me kike so nazo miki dashi."? dan murmushi nai wanda yasa Mamma barin gurin kunya ta kamani nace"Komai ka siyo min inaso. " kawai sai na kashe wayar da sauri na mika mata ta kar'ba a nutse tace"Zakuje gida yanzu zan kawo miki magunguna insha Allahu duk sati zan dinga zuwa har gida ina dubaki." nace."To shikkenan nagode." Murmushi tayi tana kokarin fita tace"Ranki ya dade kinfi karfin komai a wannan asibitin." Lokacin da muka shiga masarautar a hargitse muka sameta jama'a sun cika a bangaran Ciroma sai surutai ne ke tashi yayinda kowa ke fadar albarkacin bakinsa akan abinda ya faru da Hajiya Karima da Kanwarta Lauratu. Kai tsaye Mamma ta umarci Direba daya wuce damu gurinta ko zama bamuyi ba jakadiya ta shigo hankali a tashe! Mamma ta kalleta cikin alhini tace"Jakadiya wai shin me yake faruwa ne a masarautar nan ko'ina ya hargitse shin ina Maimartaba da 'Yan uwansa." ? Jakadiya jiki a mace! tace"Ranki ya dade Allah ne ya saukar da ikonsa akan Hajiya Karima da kanwarta Lauratu........Tun sanda da Lauratu ta gane cewa asirinta ya tonu sai tayi yunk'urin 'barin gari tare da kayanta Allah cikin ikonsa sai ya saukar mata da tsautsayi mai munin gaske! a titin Zaria tayi mummunan had'ari! motar da take ciki ta 'kone k'urmus! ita kanta ta gama 'konewa labarin faruwar al'amarin yasa Hajiya Karima ta yanke jiki ta fad'i a gurin gabadaya dai yanzu an rasa yanda za'ayi da ita dan gabadaya ta sandare babu abinda yake amfani a jikinta sai numfashinta dake fita sama-sama! Khalisat itace ke kuka tana farfad'ar irin sharrin da iyayenta suka dinga k'ullawa gashi tun ba'aje ko'ina ba ya koma kansu......Yanzu haka Maimartaba da sauran 'yan uwansa suna tare da Maigirma Ciroma domin shi kansa a lokacin rud'ewa yayi ya dinga hawaye yana nadamar abinda ya aikata a baya da kyar aka kamashi aka shiga dashi daki ana tausar zuciyarsa. Jikina a sanyaye na nemi kujera na zauna ina mamakin hukuncin ubangiji na yarda da cewa Allah baya bacci kuma baya barin hakkin wani akan wani tun aduniya yake fitar dashi Hajiya Karima da 'kanwarta sun nufe ni da sharri sai gashi Allah ya mayar dashi kansu babu abinda zance da Ubangiji akan sakayyar da yayi min. Mamma kuwa cewa "Tayi dama ai alhaki kyukoyo ne sukenan kullum cikin shirya mugunta gashinan Allah ya mayar dashi kansu Allah ya karemu yasa mufi karfin zuciyoyinmu." a tare muka amsa da ameen nida Jakadiya, Tace."Ki had'awa Sumayya ruwan wanka tayi ta samu karfin jikinta." Jakadiya da sauri tace"To ranki ya dad'e." ta kalleni a nutse tace"Kinga yanda Allah yayi musu ko." ? nace" na gani Mamma wallahi jikina duk yayi sanyi na rasa me yasa mutane suke shagala da duniya suke mantawa da Allah da ranar lahira wannan al'amarin da faru ya kamata ya zama izina ga masu irin halinsu." A sanyaye tace" Sumayya kin san ita shiriya ta Allah ce sai yaso zaisa mutum ya shiryu amma idan ba hakaba ai yaci ace hajiya Karima ta gane gaskiya a lokacin da hukuncin rataya ya sauka akan d'anta Muddibo amma da yake beso ba sai ya rabu da ita ta cigaba da tafiya akan rashin gaskiya watakila wannan abu da ya faru da ita shine zai zama sanadiyar shiriyarta." A sanyaye nace"To ubangiji Allah ya shiryeta da dukkanin masu hali irin nata." Ta amsa da ameeen ya rabbi kije kiyi wanka sai kici abinci kisha magani." Nace."To mamma nagode da kulawarki akaina." murmushi tayi tace."Sumayya babu kalmar godiya a tsakanina dake dukkaninn abinda nayi miki kaina nayiwa.'' murmushi nayi na mike a nutse na kama hanyar dakin da nake, ina kokarin shiga jakadiya ta fito tace"Ranki ya dade na hada miki ruwan wankan na kuma fito miki da kayan da zaki sanya.'' nace"Sannu jakadiya nagode da kulawa." murmushi tayi ta wuce ni kuma na shiga dakin ina jin wani irin farin ciki a cikin raina insha Allahu karshen matsalata yazo zan cigaba da samun nutsuwa da kwanciyar hankali na har abadah. *Na kudi ne* Koda zaki ganshi a groups na sata ne idan kina bukatar ki biya kudin karatu ga yanda abin yake....Vip gruop#600 normal gruop#300 account.... 0542382124....Binta umar gtbank....idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:28 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 108 *Sumayya Allah ya baki lafiya👏🏻* Bugun kofar da akeyi ne yasa na shiga tureshi daga jikina murya na rawa nace"Dan Allah ka saurara min haka kana ji fa ana bugu nasan Jakadiya ce tazo tayi aikinta dan Allah ka dagani kada Mamma ta fito. Yana cigaba da abinda yake yace."Sumayya bazan iya ba ki barni kawai." kirjinsa na ture hawaye na kokarin zubo min nace" Dan Allah ka sauks." hannu yasa ya rufe min bakina ya kalleni da jajayen idanunsa kansa ya girgiza min alamun nayi shuru. kallonsa kawai nake ya mayar da kansa kirjina ya cigaba da sha'aninsa..........Jakadiya dai sai hakura tayi da bugun ta bar gurin, tana tsaka da gyare-gyare a falon Mamma ta fito daga dakinta ta shirya tsaf sai kamshi take, ta kalli Jakadiya a nutse tace" Sumayya bata fito bane."? Jakadiya tace"Eh ranki ya dade na jima ina bugun kofar bata bude ba watakila bacci take." Mamma tace" To babu damuwa zuwa anjima sai a tasheta ta karya." Jakadiya tace"To ranki ya dade a kawo miki kayan karin nan gurin ko zaki hau daining din." Tace."Kawo min nan jakadiya bana san hawa daining din saboda kafafuna." Jakadiya da sauri ta nufi gurin cin abincin ta shiryo komai a tire ta kawo gabanta ta ajiye. A nutse ta hada mata tea kana ta zuba mata sinasir da miyar taushe wacce taji tantakwashi da man shanu! Mamma tace"Ikon Allah Jakadiya aiki baya miki wahala yanxu tashinki har kinyi wannan girgikin."? Jakadiya tai murmushi tace."Ranki ya dade ai jiki ya riga ya saba shiyasa aiki baya min wahala tunda na fahimci Sumayya tana san wainar shinkafa da sinasir yasa yau na shirya yi muku a matsayin abin karyawa.". Mamma tace"Aikuwa kin kyauta Jakadiya mungode yau kam sai ki huta kada kiyi abincin rana wannan ma ya ishemu." Jakadiya tace"To ranki ya dade godiya nake." gurin ta bari taje ta cigaba da ayyukanta. Mamma ta gama karyawa jakadiya ta gyara gurin tsaf ta kunna tiraran wuta ta dawo ta zauna kusa da ita suka cigaba da hira. Lawisa ce tayi sallama ta shigo tayi ado sosai tai kyau.! cikin sakin fuska Mamma ta amsa mata tace"Lawisa kece a tafe."? Lawisa cikin ladabi ta samu guri ta zauna da fadin"Eh wallahi Mamma nice ina fatan na sameku lafiya."? Mamma tace"Lafiya lau alhamdullilahi." Jakadiya ta gaisheta ta tashi ta basu guri. Gurin ne yayi shuru na minti uku Mamma tace"Ina maigidan naki ne nasan yau dai baya fita da wuri." Lawisa tace."Ai na dauka yana nan gurinki tunda ya fito sallar asubahi bai koma ba." Mamma tace" Bai shigo ba watakila ya tsaya wata sabgar ne ko suna tare da Shatima." Ta bude baki kenan za tayi magana sukaji motsin fitowarsa. Yanda ya fito a hargitse ido jawur ko waye dole ya gane abinda ke faruwa.....Mamma ta bishi da wani irin kallon mamaki! Sunkuyar da kansa 'kasa yayi yana shafa sajensa.....Simi-simi ya karaso gurin, Lawisa kasa tayi da kanta tana jin wutar kishi a kirjinta. Mamma tace"Babana ashe dama kana ciki.''? A sar'ke yace."Eh wallahi Mamma tayi kirana a waya ne wai cikinta na ciwo lokacin dana shigo kina daki baki fito ba shiyasa baki sani ba.". Kallonsa take cike da zargi tace"Cikinta na ciwo idan akwai wanda zai fara sani nice ko kuma jakadiya kadai kasan munafurcin daya shigo dakai." Gyara fuska yayi yace."Mamma wane irin munafurci kuma? idan Sumayya ta fad'a miki tana ciwon ciki ai baki da maganin da zaki bata shiyasa ni data san ina da magani ta kirani a waya ta sheda min." Tsaki taja ta kautar da kanta, tasan 'karya yake kawai ya shigo ya biya bukatarsa ne ta rasa abinda yake damun yaron nata duk kulawar da take akan yarinyar sai da yabi dare da rana yazo ya haike mata. A fakaice ya kalli Lawisa ya wani maze! yace."Ki taso muje ki hada min ruwa nayi wanka." Lawisa taji kamar ya d'aba mata wuka a makoshi wato ya gama jin dadinsa ita zata hada masa ruwan da zai wanke janabarsa. Daurewa tayi tace"To ta fara kokarin mi'kewa, Mamma kamar ta hanata sai da ta rabu da ita tabi so da ido a lokacin da suke kokarin fita daga falon. Ajiyar zuciya ta sauke a nutse ta mike ta nufi dakin.....yanda ta samu shimfidar gadon a hargitse yasa ta sake gazgata zarginta tana tsaye a tsakiyar dakin na fito daga toilet, wata irin kunya ce ta rufe ni, nai sauri dauke kaina ina kokarin komawa toilet din. Tace."Sumayya kunyata kikeji."? kofar toilet din na rike gabadaya na kasa fitowa ta karaso a nutse ta rike hannuna muka fito. Gefan bed muka zauna cikin kulawa tace"Sumayya wato babana sai da yazo ya yaudareki ko."? a sanyaye nace"Mamma kiyi hakuri." kanta ta girgiza tace"Ke nake tausayi Sumayya shiyasa kikaga ina sa ido akanki bana so ya takura miki da tsohon ciki a jikinki." Shuru nai tace"Ina fatan dai babu inda yake miki ciwo."? nace"Babu mamma." tace"to masha Allah ki kimtsa jikinki ki fito yau Jakadiya tayi miki abinda kike so sinasir " Murmushi nayi nace"Kai masha Allah naji dadi sosai Mamma ayi mata sannu kafin na fito." mikewa tayi da murmushi a fuskarta tace"To babu damuwa sumayya." hanyar fita ta nufa na bita da kallo ina girgiza kaina..........a gurguje na kimtsa jikina na fita falon na samesu a zaune suna hira.. **** Sati biyu da faruwar al'amarin ya sake lalla'bowa ya shigo da sassafe lokacin ina toilet ina wanka kawai naga ya fado toilet din tsabar tsorata sai da d'an cikina ya wuntsila bakina na motsi nake kallonsa naga ya cire jallabiyar jikinsa yana kokarin cire gajeran wandonsa soso da sabulun dake hannuna na jefar na fara kokarin fitowa daga kwamin wankan rintsani yayi a ciki ya ri'keni tsam! a jikinsa zafafan kesses ya shiga sakar min gabad'aya jikina yayi sanyi na kyaleshi yayi ta jagwalgwalani yanda ransa yake so, hannuna ya rike muka fito da kwamin wankan ya dinga jifana da wani irin kallo yana marmatsa sassan jikina, narkewa kawai nake a jikinsa tsabar feelings din da yake taso min, ganin bukatarsa ta biya a kaina kawai ya daukeni bai dire ni a ko'ina sai a gado, sarrafani ya shigayi ni dashi mu dinga fitar da wani irin numfashi mai wahalar gaske. Tsayin awa guda muna abu daya kafin mu samu gamsuwa, ya mike cikin farin ciki da annushuwa ya nufi toliet wanka yayi ya fito cikin jallabiyarsa tamkar wani abu bai faru ba Dauke kaina nayi daga barin kallonsa ina dan zum'bura bakina. Nesa dani ya tsaya yana kiran sunana, kallonsa nayi 'kwalla na taruwa a idona." Yace." Allah yayi miki albarka Sumayya hakika kina faranta min rai da tarin ni'imar da Allah yayi miki sumayya ba zan 'boye miki ba wallahi ina mutukar alfahari da auranki." Wani farin ciki ne ya lullubeni nayi dubarar mayar da hawayen dake kokarin zubo min nace"Nagode sosai amma don Allah ka daina zuwa kana wani abu dani kada Mamma taga kamar mun raina maganarta. Yace."Sumayya Mamma hakkina take tauyewa a'ina akace idan mace tana da ciki shikkenan sai ta kauracewa miji bazan iya ba sumayya ko gobe bukata ta taso min zan zo na kawar da ita a gurinki." Nace"Duk da haka dai dan Allah ka daure kamar yau zan haihu ai." Yace."Ba zan iya ba Sumayya ke kadai kike iya gamsar dani.'' cikin mamaki nake kallonsa ina kuma zargin maganarsa ni kadai nake gamsar dani kodai dadin baki yake min dan ya ganshi a gabana watakila haka yake zuwa gurin Lawisa yayi ta sakin baki. Girgixa kaina kawai nayi nai shuru saboda nasan duk abinda zance masa akan al'amarin ba zai fahimta ba. Hanyar fita ya nufa yace.''Xanje na shirya na tafi aiki." A sanyaye nace"To Allah ya bada sa'a." ya amsa da ameen kafin ya bude kofar dakin ya fita. Hada ido sukayi da mahaifiyar tashi, sunkuyar da kansa kasa yayi alamun rashin gaskiya sun bayyana a tare dashi. Tace"Yau kuma wace karyar za kayi min."? dariya yasa yana kallonta tace"Babana baka da kunya ko? ka dinga tsallakowa kana zuwa kana haikewa yarinyar mutane a gurina.". Yace."Mamma abinda yafi sauki kawai ki bani ita mu koma gurinmu dan gaskiya ba zan iya hakuri ba." ta dinga kallonsa tana mamakin maganarsa "Babana ba zaka iya hakura ba."? kansa ya daga mata kamar wani maraya. Tace" Shin wai ita kadai ce matarka."? girgiza kansa yayi yace."Mamma kin san ko wace mace akwai irin baiwarta baxan boye miki ba nafi samun nutsuwa da ita.' Girgiza kai ta shigayi kafin tace"Ni kam na gaji da wannan rashin kunyar idan ka dawo daga aiki kazo ka dauketa ku tafi Allah ya raba lafiya." Sakin fuskarsa yana kokarin magana na katseshi....."Mamma dan Allah kiyi hakuri wallahi ba laifina bane." Girgiza kanta tayi tana kallona tace"Nasani sumayya ba laifinki bane shi yake zuwa ya takura miki wannan dalilin yasa nace kawai yazo ya daukeki ku tafi.' Hawaye na share nace"Mamma ni dai nafi bukatar na zauna dake." shuru tayi tana kallon kasan kafet! jikina a sanyaye na juya na koma cikin dakin.....shi kam cike da farin ciki ya fita yana murna ya fiso dama mahaifiyar tashi tai zuciya shiyasa data yanke wannan hukunci bai dameshi ba. **** Tunda na koma gurina ya samu sake ko tausaya min bayayi a ranakun girgikina yazo yayi ta damuna da fitina haka dai nake hakuri dashi da halayensa. Koda cikina ya shiga watan haihuwa haka na dinga fuskantar matsala iri iri yau ciwon kafa gobe ciwon baya jibi ciwon 'kugu! kullum dai da abinda yake damuna Mamma ta sake yunkurin daukata ya hana ya zauna yana mata tsari dole ta hakura ta kyaleni amma kusan kullum sai ta turo jakadiya ta dubani, Tambaya ma takan zo sa'i da lokaci ta dubani ta koma gurinta, gabad'aya dai kowa ya mayar da hankalinsa a gurun yi min addua da fatan rabuwa da cikin lafiya, duk wanda keso na haihu ba kamar ni ba sabida ni kadai nasan irin wahalar da nake sha ciki farin idan ya kasance na tagwaye dole a dinga fuskantar damuwa! wata rana idan wuyar ta isheni haka zan zauna naci kukana na koshi, kafin na daga hannu sama na roki ubangiji da ya rabani dashi lafiya. A ranar da zan haihuwa ya kasance ni nake da girki dama tunda naga ya dawo da wuri jikina yayi sanyi nasan zai isheni da fitina sai na fito falo na zauna na barshi a dakin shi kadai. Bayana ya biyo daga shi sai gajeran wando da singlet kallo daya nayi masa na kauda kaina murya na rawa nace"Don Allah ka rabu dani naji da abinda yake damuna wallahi kaje gurin Lawisa na yafe." Zama yayi kusa dani ya sani a jikinsa yana shafa bayana yace."Kiyi hakuri ki barni nayi watakila hakan ma ya janyo miki naquda" Girgiza kaina nayi nace"Bana bukata kawai dai kaje gurin Lawisa na yafe maka." shuru yayi yana kallona yana marairaice fuskarsa Jikina na janye ya sake matsoni yana marmatsa min jikina, hawaye na goge nasan halin nacin sa idan ba bashi nayi ba zamu iya kwana a zaune......da kyar na yunkura na mike tsaye ina cije bakina saboda jin yanda marata ke suka, ya kama hannuna ya rike muka nufi daki. Yana gamawa ya mike a shiga toilet na mike da kyar ina kiran sunan Allah! kokarin mikewa tsaye nake na kasa sabida jin yanda marata ta cika tai taf da fitsari addua na shigayi a cikin zuciyata, can naji kamar zanyi kashi! na shiga nishi!!! da sauri na sauko kasa na dukufa tare da dafe gadon! nishi kawai nake ina kiran sunan Allah! ya karaso gurin a gigice yana rirrikeni nai wani wawan nishi! a take naji fad'owar abu a karkashina! kukan babyn ya cika dakin. Tarairayoni yayi jikinsa yana tasbihi ga Allah ikon Ubangiji haihuwa mai sauki irin wacce ba'ayi tsammani ba, babyn ya janye ya dan gyara min kwanciya a jikinsa na cigaba dayin nishin ina rirrikeshi! cikin ikon Allah d'ayan ya fito fit kafin mahaifarsu ta biyo baya." "Alhamdulillahi." ina fada yana fada! yasa hannu ya sharce gumun goshina a hankali ya kwantar dani a gurin ya shiga kimtsa babys nashi! Ina kwance ina kallonsa ya gyara babyn duk ya sasu a towel ya ajiye su saman bed! ya tsuguna gabana tare da fadin"Sannu." kaina na daga masa, yace."Bari na sa miki ruwa kiyi wanka ko."? shuru nai ya mike yana fadin"Sumayya ke 'yar baiwa ce shiyasa Ubangiji ya baki nakuda mai sauki wannan abin alfahari ne a garemu." toilet din ya nufa, na mike a hankali na tattare towel din dake jikina, hannu nasa na dauko daya na duba naga namiji ne ajiyar zuciya na sauke nace"Allah ya albarkace ka." a hankali na dauko dayan na duba shima namiji ne tamkar an tsaga kara da dan uwansa, dukkaninsu sun dauko kammanin mahaifinsu, addua nai masa ina jin wani irin farin ciki a cikin raina, haka ya fito ya sameni ya murmushi yace"Jarumata kinga kyautar da Allah yay mana ko.''? murmushi nayi nace"Wallahi nagani kuma nagode masa daya bani kyautar 'ya'ya biyu a lokaci guda.''' Yace.'' Ina mutukar alfahari dake Sumayya ke kikayi namijin kokari har na samu wad'annan yaran." Murmushi kawai nai na fara kokarin mikewa, ya taimaka min muka nufi toilet, komai na wanka ya hada min yace ki fara shiga ruwan dumi tukkuna sai ki gasa jikinki idan ba zaki iya ba nayi miki."? Nace"Ka bari kawai zanyi.'' yace."Kin tabbata."? kaina na daga masa yace."Okey bari kafin ki fito na sanar da Mamma." Da sauri ya fita daga toilet din na girgiza kaina a nutse na shiga cikin ruwan zafin daya had'a min. *Na kudi ne* Koda zaki ganshi a gruops na sata ne idan kina bukatar biyan kudin littafin ga yanda abin yake....Vip gruop#600 normal group #300 account.... 0542382124....Binta umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:28 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 107 Jin sheshshe'kar kukanta ya cika masa kunne yasa ya juyo da fuska a murtuke yana kallonta, a sanyaye tace" Dan Allah kayi hakuri ka janye sakin nan da kayi min nasan ban kyauta ba dana fadawa mahaifiyarka amma idan za'a bi gaskiyar magana kowa yasan kaine mai laifi bai kamata ka yanke irin wannan hukuncin akaina ba kayi hakuri ka janye sannan na roke ka da Allah da annabi ka daina amfani dani da condem nima inaso na haihu na samu sanyin idaniya a duniya kada ka cutar dani ka lalata min mahaifa." Tausayi ta bashi ganin yanda take kuka gabad'aya tayi sanyi dan tun ranar daya saketa ta rasa nutsuwa kullum cikin bashi hakuri take tabbas kamar yanda Sumayya ta fada masa yanxu babban laifi shike dashi dan Lawisa ta gaji ta nemawa kanta mafita ba laifi bane tunda shi kansa yasan yana cutar da ita saboda yasan illar kwayoyin daya dinga dibga mata idan kuwa hakane yana da kyau yayi mata afuwa akan abinda tayi masa ya yafe mata ya mayar da ita dakinta kodan ya samu sassauci daga gurin mahaifiyarsa.......Ajiyar zuciya ya sauke yana kallonta da alamun sassauci a fuskarsa yace." Lawisa zan mayar dake dakin ki saboda matata Sumayya ta wuce komai a gurina kina ji dai da kunnanki yanda take kuka akan hukuncin da nayi miki inaso ki dauketa a matsayin 'yar uwa ba kishiyasa ba duk wasu mugwayen halayen ki ki sanja su zama masu kyau mutukar kika cutar da Sumayya wallahi bazan barki ba, ina fatan ki gane." A sanyaye tace"Nagane na kuma gode da naci albarkacin Sumayya domin ta cancanta ta kowane fanni wallahi tuntuni na dauketa a matsayin 'yar uwa a shirye nake dana zauna lafiya da ita babu cuta babu cutarwa kaima inaso ka kamanta adalci a tsakanina da ita tunda azahiri ka nuna kafin sonta dani." Girgixa kansa yayi yace."Ba wai nafi sonta akanki bane Lawisa Sumayya ta cancanta a sota saboda kyawawan halayenta yarinyar ta bada gudumawa mai yawa a rayuwata wannan dalilin yasa nake nuna mata kulawa wanda har kike ganin kamar nafi kaunarta dake kema ina kaunarki inaso kisa a ranki cewa ni dan uwanki ba zan kara cutar dake ba saboda yanzu nagane gaskiya insha Allahu kuma na daina amfani dake da condem kuma ki kwantar da hankali da ikon Allah kema zaki haifa min 'ya'ya masu albarka." Murmushin farin ciki tayi tace"Nagode sosai ina rokon Allah ya dawwamar mana da zaman lafiya ya kuma bamu zuria mai albarka." amsawa yayi yana murmushi yace."Tunda kin zama amarya ki shirya muje musha iska daga nan sai ki rakani store nayi wa baby siyayya." Cikin farin ciki ta mike da fadin"To shikkenan bari nayi wanka na fito." toilet na nufa ya bita da kallo yana girgiza kansa. Akwati uku suka ciko da kayan baby komai biyu ya dinga dauka, Lawisa ta dinga mamaki da dai ta gaji tai magana kai tsaye yace."Jikinsa na bashi twins zai haifa sabida haka kawai ta kyaleshi aikuwa ido ta zuba masa yayi ta labtar kaya, itama Sumayya ya siya mata 'kananun kaya masu yawa.......mota cike da kaya suka dawo gida. Can masarauta kuwa tana cikin alhini da damuwa sakamakon rasuwar mai girma Ciroma dab da magariba Allah ya kar'bi rayuwarsa bayan yasha fama da jinyya.......Mutuwar maigirma Ciroma ta girgiza jama'a da yawa suka tsorata mussaman Uwargida da 'Ya'yanta, duk sun rud'e sai koke koke suke a gidan.....Hajiya Karima duk da bata hayyacinta sai da taji a jikinta, da kyar Wali ya sheda mata mutuwar mijin nata faduwa tayi a gurin ta suma ko bayan data farfad'o ma kasa gane kanta akayi ta dinga surutai tana kuka, Wali da kansa ya dauko Dr Sadiya tayi mata allurar bacci. Tunda suka wayi gari suka rasa abinda ke damunsu da kyar suka karya kummalo suka shirya jikinsu suna jiran abokanan tafiyar tasu su fito domin su hadu su tafi airport...... Kira ya shigo Wayarsa dake saman drowar....Ita ta dauka ta mi'ka masa ya karba yana dubawa ganin Number Shatima yasa ya sauke ajiyar zuciya ya daga da sallama a bakinsa, gaisawa sukayi Shatima nata tunanin ta yanda za'ayi ya fada masa mutuwar.....Yace."Shatima yanzu nan zamu hadu mu tafi airport insha Allah karfe daya na rana mun sauka a gida.'' a sanyaye yace."To masha Allah ina rokon Allah ya kawo ku lafiya." yana gama maganar sai ya kashe wayar cikin zuciyarsa yace bari kawai ya bari tunda dawowa zasuyi, shi kuwa magajin sarki jikinsa ne ya bashi akwai matsala, sai ya kara kiran wayar shatiman ya dauka, yace."Ka fada min abinda yake faruwa dan jikina ya bani akwai abinda kake 'boye min kodai wani abu ya samu Sumayya ne."? Shatima ya sauke ajiyar zuciya yace."Magajin sarki masarauta tayi babban rashi." gabansa ne ya fad'i! yace."Waye ya rasu."? jin maganar mutuwa yasa da sauri ta dawo kusa dashi. Shatima yace."Allah yayi wa Baba Ciroma rasuwa jiya da daddare yanzu haka har mun kaishi mun dawo."! "Innalillahi wa'ina ilahi raji'un! kalmar daya fada kenan jiki a sanyaye ya kashe wayar ya juyo suka had'a ido Lawisa baki na rawa tace" Da gaske baba ya rasu."? kansa ya daga mata sai kawai ta zube kasan dakin ta hada kai da gwiwa ta dinga rusa kuka tana jan innalillahi wa'ina ilahi raji'un.! zama yayi kusa da ita ya rungumeta a jikinsa ya dinga rarrashinta cikin kalamai masu sanyi da tausasawa. Lawisa tashin hankali mai tsanani ta shiga a lokacin da taga halin da mahaifiyarta take ciki.......cikin 'kunar zuciya ta rungume d'an uwanta Wali dake tsaye akan mahaifiyar tasu, tana kuka tace"Wali Baba ya mutu ga Hajiya ta had'a da lalura mai wahalar magani ga aunt Lauratu tayi mutuwa irin wacce ba'aso ta mutu ba tare data tuba ga Allah ba, kafin muyi tafiyar nan sai da na zauna dasu na hanasu aikata abinda suka kud'urta saboda nasan dole Ubangiji ya tona musu asiri tunda ita wacce suka nufa da sharrin bata da hakki akansu amma da yake shaid'an ya riga ya gama shiga jikinsu sukaqi saurarata sabida naqi basu hadin kai hakan yasa ko sallamar arziki bamuyi dasu ba na tafi cikin damuwa da tunanin abinda zai biyo baya akan abinda zasu aikata hakika nayi nadamar kasancewar hajiya a matsayin u........Katseta yayi yana girgiza mata kansa ido jawur yace."Kada kice haka Lawisa duk lalacewar uwa uwace gabad'ayanmu mun san mahaifiyarmu bata da nagarta abinda yafi kamata muyi mata a yanzu shine addua domin ita kadai tafi bukata Lawisa a yanzu ina mai tabbatar miki da cewa Hajiya tayi nadama dan tsabar tension (damuwa) ne ya sanya mata shiga cikin wannan yanayi kullum yini take tana kuka da sambatu sai anyi mata allurar bacci ake samun lafiyarta saboda haka kada ki sake kamanta wata mummunar magana akanta insha Allahu Allah ya ganar da ita gaskiya, shi kuma baba addua zamu bishi da ita dan yayi mutuwa irin wacce ake bukata alhamdulillhi ya mutu da kalmar shahada a bakinsa wannan shine babban abin alfaharinmu." Lawisa zama tayi kasan kafet tana kuka tana kiran innalillahi Khalisat kanwarta tazo ta rugunmeta suka cigaba da zubar da hawaye, Hajiya Karima kukansu ne ya tasheta daga bacci ta mike a firgice! ganin Lawisa yasa ta sauko daga gado ta zauna a gabansu kawai sai itama ta fashe da kuka tana girgiza kanta. Muniru yace."Shikkenan kun tasheta yanzu idan ba Allah ne ya takaita ba zata fara surutai." kallonsa tayi tana girgiza kanta tace"Munniru kun mayar dani mahaukaciya ko. "? girgiza kansa yayi yana kallonta! ashar! ta d'ura masa tana wata irin zabura! tace" Nayi maka karya kenan."? ganin tana kokarin mikewa tsaye yasa Wali yace da Munniru maza ya fita, sai kawai ta dawo kan Wali din ta dinga cusa masa ashar yana rirriketa.....Lawisa ta taimaka masa suka zaunar da ita akan gado, sai kawai ta fashe da kuka tace"Lawisa Babanku ya mutu Lauratu kanwata data rage min itama ta mutu wuta ta cinyeta ni yanzu meye amfanin zamana a duniya wayyo Allah na shiga uku na lalace."!!!! da karfin gaske take maganar tana buge buge hade da d'ora hannu akanta.....Wali hankalinsa ya tashi da sauri ya fita daga dakin Lawisa da Khalisat suna kuka suka rirriketa tana fizgewa. Wali tare suka shigo dakin da Magajin sarki da sauri yace."Ya dauko masa allurar da ake mata, Wali ya dauko ruwan allura da sirinji ya karba da sauri ya had'a allurar yace su rike da kyau Wali ya rirriketa yayi mata allurar.....Lumshe idonta tayi tana kallonsa magana a hard'e tace"Magajin sarki ka yafe min zalinci da mukayiwa matarka." Tausayi ta bashi sosai cikin nutsuwa yace."Hajiya mun yafe miki insha Allah." Daga kanta tayi sai kawai ta 'bingire a jikin Wali bacci ne ya dauketa, dukkaninsu ajiyar zuciya suka sauke. Ya kalli Wali a nutse yace."Insha Allahu yanzu zan kira Dr Nasir 'kwararran likitan 'kwa'kwalwa ne shi zai tsaya akan lafiyar Hajiya da ikon Allah zata dawo daidai gabadayanku inaso ku kwantar da hankalinku." Wali yace."Mungode kwarai magajin sarki Ubangiji Allah ya saka maka da alkairi." Ya amsa cike da tausayinsu ya kalli Lawisa dake share hawaye yace."Kiyi hakuri ki daina kuka addua zakiyi mata." Kai ta daga murya a dushe tace"Insha Allahu zan cigaba dayi mata addua." To bayan sadakar bakwai na Maigirma Ciroma masarautar ta d'an samu nutsuwa dan Maimartaba sauran 'yan uwansa sun cigaba da zaman fada, Shima Magajin sarkin ya koma aiki yayin da hajiya Karima ke samun kulawa tare da taimakon Dr Nasir wanda yake tsaye akanta alhamdulillhi ana samun cigaba sosai tunda ta daina surutai da zage-zage sai dai kuma yawan koke-koken da takeyi ne yake damun 'ya'yanta Dr yace su kwantar da hankalinsu shima kukan da yardar Allah zata daina tunda dai tana cigaba da shan magani. Tunda suka dawo yake tare da Lawisa tsayin sati biyu kenan tsakaninsa da Sumayya sai ido dan ko sashen Mahaifiyar tashi ya shiga gaisuwa ce kawai take shiga tsakaninsu sai hirar yau da gobe babu wata mu'amular aure da suke yi saboda Mamma ta kafa ta tsare bata barinsa ya ke'be da matarsa komai idonta akai ita kanta Sumayyan abin na damunta kawai dai tana daurewa ne amma tana bukatar mijinta a kusa da ita, Yau lahadi baya fita da wuri ya shigo sashen lokacin Mamman bata fito ba yaji dadin haka dan haka kai tsaye D'akin da take ya nufa, ya bude kofa a hankali ya mayar ya rufe harda murza key! ajiyar zuciya ya sauke ganinta a kwance tana bacci ga santala santalan cinyoyinta a waje! Xama yayi kusa da ita tare dasa hannunsa kasan mararta yana shafawa, da sauri ta bude idonta jin yanda d'an dake cikinta ya ke motsi shi kansa yana jin yanda babyn nasa yake naushin hannunsa. Ido suka had'a ta mike zaune tana gyara rigar baccinta data tattare, gaisheshi tayi ya amsa tare da fadin"Kina kina kwance kina bacci babu abinda ya dameki dani ko."? A nutse tace"Bangane maganarka ba." yace."Ina nufin kina cikin kwanciyar hankali ni kin barni ina watangaririya." murmushi tayi tace."To ya kake so nayi maka? nima wallahi kwana biyu ba jin dadi nake ba baby yana damuna da motsi.'' Ya cigaba da shafa mararta yace."Lafiya kenan idan basa motsi ai ke kanki ba zakiji dadi a jikinki ba yanzu ma zuwa nayi mu gaisa dasu." Tace"Su waye zaku gaisa."? Kai tsaye yace."Twins d'ina mana." Dariya tasa tana kallonsa yace."Kema kin mayar dani sakarai ko."? girgiza kanta tayi yace."Hakane ma Lawisa nayi min wani irin kallo a lokacin da nake siyan kayan baby iri biyu ke kuma yanzu kina min dariya jikina na bani tagwaye zaki haifa min."... Shuru kawai nayi ina kallonsa da mamakin maganarsa, wai tagwaye koda yake babu yanda Allah baya shirya lamarinsa.....Kafafuna yaja na kalleshi yace."Ki kwanta yau ni zanyi miki awo." tank'washe kafata nayi ina jin tsoro kada ya tsiro da fitina dan tunda naga kwayoyin idanunsa sun sauya nasha jinin jikina......"Wane irin awo kuma bayan wanda Dr Sadiya tayi min jiya." a kasalance yace "Nawa awon na mussaman ne." A dan tsorace! nace"Aikuwa bana bukata." kokarin sauka nake ya hawo gadon nace"Dan Allah ka sauka kaje falo gani nan." Girgiza kansa yayi yace."Kada ki bari aji kanmu dake kawai ki barni nayi abinda ya shigo dani domin kin san duk abinda zakiyi ba zan janye ba gwara ki hakura ki bani hadin kai." Jikina ne ya mutu na dinga kallonsa, ina jin tsoron abinda zai faru......kwantar dani yayi a hankali yayi dubarar cire min rigar jikina, tunda ya fara sarrafa ni gabad'aya jikina ya rikice sha'awar dana tara ta tashi jikina na sakar masa muka shiga biyawa kanmu bukata... *Na kudi ne* Koda zaki ganshi a gruops na sata ne idan kina bukatar biyan kudin karatu ga yanda abin yake....Vip group #600 normal group #300 account... 0542382124...Binta umar gtbank....idan kati zaki turo #400 sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* 2/11/21, 2:28 PM - ???: *SADAUKARWA NE* *GA* *HAJIYA SHAFA'ATU S YARI* (Kainuwa dashan Allah✊?) 109&110 Koda na fito daga toilet din tsaf na samu dakin jakadiya sai goge goge take ita kuma Mamma na zaune a gefan gado ta dauki yaran duka ta rike a hannayenta kallo guda za kayi mata ka hango tsantsar farin ciki a tare da ita, Jakadiya da sauri tazo ta rike ni tana fadin"Sannu Sumayya." kaina kawai na daga mata muka karasa bakin gadon ta rike dani, Zama nayi a hankali nace"Mamma sannu." cike da kulawa tace"Sumayya aike za'ayi sannu." sunkuyar da kaina nayi ina murmushi......Tace "Amma nayi mamaki da wannan haihuwar taki sumayya me yasa kina jin ciwo tun yamma baki fada ba. Kaina a kasa nace" Mamma wallahi ban tashi da wani ciwo mai tsanani ba kawai dai Allah ne ya kawo min haihuwar da sauki." Girgiza kanta tayi tace"To Alhamdulillahi ina rokon ubangiji Allah yasa ki d'ore da haka ina fatan kuma babu inda yake miki ciwo."? nace"Babu Mamma sai dai ciwon mara kadan kadan.'' tace"Sannu insha Allah shima da ankwana biyu zaki daina ji." Ta kalli jakadiya da fadin" Ki duba mata kaya masu kauri tasa a jikinta sai ta kwanta ta huta." Jakadiya da sauri ta bude wardrobe tana dubawa Riga da zani na atamfa ta dauki min ta taimaka min nasa a jikina, rigar sanyi nace ta dauki min nasa a jikina, ina kokarin kwanciya Mamma tace"Ki daure kici abinci sumayya." nace"To Mamma. Jakadiya ta fita da sauri minti biyar ta shigo hannunta da plate din abinci. Kar'ba nayi a nutse nayi bisimillah na fara ci muna hira Jakadiya ta kunna turaran wuta a dakin ta nufi bandaki ruwan wanka ta hada ta fito dashi a madaidaicin baho, Mamma tace"A wanke musu jikinsu sai a goga musu zaitun.'' jakadiya ta mika hannu domin kar'bar babyn Mamma ta mika mata hassan din da fadin" shi zaki fara wanke wa dan na lura kamar bashi da hakuri sai tsotsar hannunsa yake da alama acici ne." Jakadiya na dariya ta kar'beshi Tace."Kinga shi kuwa wannan bacci yake tunda ya bude idonsa sau daya bai sake ba yana ta bacci." Dan murmushi nayi bance komai ba, Tace."Ai da safe su Tambaya zasuji labari mai dadi sumayya kin iya haihuwar a tsanake babu fargaba da tashin hankali." Nace"Mamma kullum dama ina rokon Allah ya sassauta min idan nazo haihuwa Allah maji rokon bayinsa ya amsa min adduata." Mamma tace"Aikuwa dai sumayya dukkanin wanda zai rike addua yana tare da nasara a rayuwarsa...........Tare suka shigo dakin shida Lawisa, Mamma tace"Yanzu ashe sai da kaje ka taso ta da tsohon daran nan." Yana kokarin magana Lawisa tace"Wallahi Mamma gwara da yaje ya tasoni nazo naga irin kyautar da Allah yayi mana." zama tayi a kusa dani fuska a sake tace"Sumayya sannu." Nace"Yauwa sannu ranki ya dade.'' tace"Ina fata dai baki manta dani ba a lokacin da kike nakuda." Dariya nai ina kallonta nace"Haba yaushe zan manta dake nayi miki addua sosai kuma insha Allahu ta kar'bu." Mamma tace"Aikuwa Lawisa ki kwantar da hankali adduar mace mai naquda bata da hijabi insha Allahu kafin tagwaye su girma kema kin samu rabonki." Tace."Ameeen ya Allah Mamma." A nutse ya karaso kusa damu ya tsaya, Mamma ta kalleshi taga duk yayi wujiga wujiga tace."Babana wai tare da kai akayi nakudar ne."? girgiza kansa yayi yace."Ko daya Mamma ni a lokacin ma data haihu ina toilet wallahi sai fitowa nayi naji kukan baby.'' Tace."Ai abun da mamaki sai dai ba'a mamaki da ikon Allah!! naga kayi firgai firgai ne shiyasa nayi zaton ko ka taimaka mata." Dariya yasa yace."Mamma ina ni ina wannan ya'kin ai sai ku na dai sha matsa a gurinta kafin Husaini ya fito." Mamma ta kalli yaron tana murmushi tace."Allah sarki ai daka ganinsa zai yi hakuri." Murmushi yayi yana leqa fuskar yaron. Koda Jakadiya ta gama wanke Hassan din Lawisa ce ta kar'beshi ta shiryashi tsaf tasa shi a towel yace na kar'beshi na gwada bashi nono. kunya ta hanani na fito da nonon kawai sai yazo yana kokarin daga min riga a nufinsa ya fito da nonon.....a fakaice na buge hannunsa, na fito da nonon ina kokarin sawa yaron a baki, ko kunyar mahaifiyarsa baya ji ya tsuguna yana nuna min yanda zanyi, ni dai gabadaya kunya ce ta rufe ni itama Mamma basarwa tayi sabida ta riga tasan halin rashin kunyar yaron nata. Cikin ikon Allah yaron ya janyo ruwan nonon cikin dubara irinta 'ya'yan zamani ya shiga zu'kar nononsa gabadaya muka dinga mamakin wayon yaron, Mamma tace"Dama yaran yanzu da wayonsu ake haifarsu, sai dana tabbatar da cewa nonon ya isheshi na cire masa sai na mikawa Lawisa shi ta karbeshi tana goge masa baki, Hussainin na karba na fara kokarin sa masa nonon a baki, yaron kasa kamawa yayi sai ya fara kuka, Mamma tace" Allah sarki shi bashi da wayon dan uwanshi ki kama masa nonon a hankali zai iya." Cikin dubara na kama kan nonon nasa masa a baki yana mamula a hankali kafin ya kama sosai ya shiga tsotsa, ajiyar zuciya na sauke ina godewa Allah a bisa ni'imar da yayi min. Washe gari da safe kowa ya samu labarin haihuwar aikuwa sasheh cika yayi da jama'a wasu na fita wasu na shigowa kaina ya dinga ciwo saboda hayaniya, aikuwa Lawisa na sheda masa cewa kaina na ciwo yace a rufe sashen kada a sake bari kowa ya shigo kana ya umarceta data bani wayar yana so muyi magana. Kar'ba nayi tare da sawa a kunnena yace."My lov kada ki janyowa kanki lalura garin san gwanintarki kin son jama'a suna ta damunki da hayaniya please dan Allah ki kwanta ki huta nace kowaye yazo kada a bude masa kofa, sannan kuma kada kisawa jikinki ruwan zafi sosai ki sirka kafin kiyi wankan." Nace"Kayi hakuri ni kaina wallahi so nake na kwanta abin ya gagara gabadaya mutane sun hana duk wanda yazo burinsa na saurareshi wannan dalilin yasa nake tsayawa muna gaisawa.'' Yace."Ni dai na fada miki ko auntis d'ina ne suka zo ban bada damar a bude musu kofa ba." " Yar dariya nayi nace Babbar magana kenan." Yace."Kwarai kuwa keda kin dauka abin wasa ne my lov lafiyarki ita kadai nake bukata kin haihu lafiya bana so hayaniyar mutane tasa miki ciwon kai." Nace"Ka kwantar da hankalinka babu abinda zai sameni insha Allah jama'a kuma dole kayi hakuri dasu." Yace." To shikkenan zanzo na kasa na tsare a sashen duk wanda yaga ina gurin sai ya juya ya tafi " Dariya nasa ina mamakin rashin kawaicinsa, yace."Wato kin mayar dani sakarai ko."? da sauri nace"Aa ranka ya dade kayi hakuri sai kadawo ko." ajiyar zuciya ya sauke yace."Ki bawa Lawisa wayar zamuyi magana." Sai da yay maganarta wallahi na tuna tana dakin, cikin jin nauyi na mika mata wayar ta karba a sanyaye sukai magana. To haka kwanakin haihuwata suka cigaba da tafiya cikin kwanciyar hankali da kulawa ta kowanne bangare Mamma na iya bakin kokarinta a kaina haka nan itama Tambaya nayin nata kokarin akaina da 'yan tagwayena da suka amsa sunansu Hassan da Hussaini Maimartaba kullum sai ya aiko da safe an daukesu an kai masa yayi musu addua sukan jima a gurinsa kafin a dawo min dasu..........Uwargida Huwaila ita ke shigowa kullum da Yamma ta gasa min jikina tayiwa yara wanka, ita kuma jakadiya itake kula damu da safe su aunty Safiyya kuwa shatara ta arziki suka had'o mana nida tagwayena kowanne da akwatinsa saqe da kaya, na samu kyautuka muhimmai ranar suna kowa kokarinsa ya faranta min nida 'ya'yana taro akayi sosai kuma aka tashi daga taron cikin koshin lafiya *Bayan wata hud'u* Yara sunyi wayo sosai dan har an fara koya musu zama......a lokacin ne kuma Allah ya azurta Lawisa da nata rabon ranar da suka tabbatar da cikin ita da mijin nata suka dinga murna da farin ciki......Ina zaune a kan kujera da Hussain a hannuna yana min rigima Ya shigo tunda na ganshi cikin walwala nasan akwai magana. Zama yayi kusa dani tare da kar'bar yaron yana jijjigashi yace."Wai kukan me yake."? nace"Watakila yunwa yake ji wallahi kaga hassan duk ya shanye ruwan nonon." Hannu yasa kan nonon yana latsawa, na ture hannunsa da fadin"Kai kam kafiye wasa." Yace."Sumayya ban yarda ba kodai mitsininsa kikayi nasan Hussani da hakuri fa.". 'Yar dariya nayi nace"Sai dai idan kaine ka mintsineshi." shiru yayi min yasa yaron a kafada yana jijiigashi! Mariya ce ta fito daga kicin hannunta rike da fida cike da madara....har kasa ta durkusa ta gaishe da sauri ta miko min fidar ta bar gurin, nace"Kawoshi na gwada bashi madarar ko zai sha. miko min shi yayi na kar'beshi sai harbe harbe yake ina sa masa fidar a baki ya kama yana tsotsa Ajiyar zuciya muka sauke a tare dashi, dan tsokana yasa hannu yana jan kafar Hassan dake kwance a gefena, Murya na rawa nace"Dan Allah kada ka tsokaneshi kasan rigimarsa tafi ta Hussani." yace.""Ai so nake suyi ta baki wahala idan kikayi zuciya sai kiyi musu kani ko kanwa." Wani irin kallo na watsa masa." dariya yasa tare da lakuce min hanci.....nace"Haba kai yanzu idan na samu ciki sai kayi murna ka duba fa kaga irin wuyar da nake sha da yaran nan." Yana mirmushi yace."Meye a ciki sumayya a wuya bata kisa ko yanzu kika samu ciki ina farin ciki wallahi nasan ke 'yar baiwa ce Allah zai rangwanta miki." A sanyaye nace"Hakane amma dai ni inaso yaran suyi kwari tukkuna idan kuma Allah ya kawo sai nagode masa." Yace." Yawwa 'yar albarka kinsan Lawisa ma Allah ya bata nata ko.'' na kalleshi cike da farin ciki nace"Ya za'ayi na sani tunda ba fada min kayi ba.". Yace."Yau muka tabbatar da cikin tana can sai murna take." Nace"Kai kuwa ai dole tayi murna wallahi nima na tayata farin ciki Ubangiji Allah ya rabasu lafiya." Ya amsa da ameeen yana min kallon kasa-kasa.....walwalar fuskata na rage nace"zaka fara ko."? Yana munafikin murmushi yace."Ki kira wa'innan yaran su dauki babys d'in nan muje daki." Zum'bura baki nayi nace"Ni babu wani daki da zanje." Matsoni yayi yana sumbatar wuyana yace."Idan kuwa hakane lallai za'ayi abun kunya dan zan iya danneki a falon nan babu abinda ya dameni da hadimanki." A sanyaye na kalleshi, girarsa ya daga min daso ya tabbatar min da maganarsa Mariya na kwalawa kira da sauri tazo nace Ki goya Hassan kuje can gurin Mamma." da sauri tace"To ranki ya dade." Mikewa yayi ya shiga daki......ban bi bayansa ba sai da na tabbatar da cewa Mariya ta tafi da yaran sannan na bishi dakin. *BAYAN SHEKARU GOMA* Alhamdulillahi abubuwa masu kyau da marasa kyau sun faru a cikin wannan shekarun da suka wuce a cikin abubuwa masu dadi da suka faru a cikin shekarun da suka gabata Allah mai kowa da komai ya azurta Doctor Aliyu da da zuria maza da mata guda goma Sumayya nada shida hudu maza biyu mata yayinda Lawisa keda hudu mata biyu maza biyu, bayan wannan baiwar da Allah yayi masa sai ya daukaka darajarsa ta bangaran aikinsa na likitanci gwamnati ta d'orashi a kan babban matsayi saboda irin gudumawar ya dinga bayarwa a zamanin daya wuce Doctor Aliyu Abdul-aziz babban likita ne da duniya tasan da zamansa..............Abubuwa na rashin dadi da suka faru a masarautar kuwa shine rashin Jajirtattun mutane da akayi wato Baba Waziri da Lawi mahaifin Sumayya, mutuwar wad'annan bayin Allah ta girgiza jama'a Maimartaba Sarki Abdul-aziz yasha kewa da alhini kafin ya barwa Allah sabida yasan shi kansa idan lokacinsa yayi tafiya zaiyi inda sukaje, sai ya kwantar da hankalinsa ya cigaba da gudanar da mulkinsa cikin tsari gami da bin dokokin ubangiji gefe guda kuma yana nunawa 'Ya'yansa Ali da Shatima yanda ake gudanar da mulki akan bigire na gaskiya da adalci! Aliyu da Shatima yanzu suna a matakin shekaru ar'bain da biyar a duniya kowanne ya mallaki hankalin kansa a cikinsu Allah ne kad'ai yasan wanda zai gaji mulkin masarautar........... *Daga karshe nake cewa Ubangiji Allah ya za'ba abinda yafi alkairi a tsakaninsu".* *'KWARYA TABI 'KWARYA* *END🔚* *ALHAMDULILLAHI* _Jama'a nan na kawo 'karshen wannan littafi mai suna 'KWARYA TABI 'KWARYA Ina rokon Ubangiji Allah ya yafe min kusakuraina ladan dake cikin littafin Allah ya sadamu dashi bakid'aya masha Allah ina mi'ko sa'kon godiyata gareku masoyana wanda na sani da wanda ban sani ba ina godiya kwarai da gaske ina kuma alfahari daku mutuka ina rokon Allah ya bani ikon da zan cigaba da nishad'antar daku da kuma fad'akar daku..........Taku akoda yaushe take muku fatan alkairi🙋🏼‍♀️_ *_DAN DARAJAR ALLAH DA MANZON ALLAH KADA KI/KA HAD'A MIN DOCUMENT NA LITTAFIN NAN BAKU SAN YANDA NAYI NA RUBUTA ABUNA BA KADA KU HAD'A MIN DOCOMENT KUYI MIN SHARING A GRUOPS BAYAN KUN SAN NA KUDI NE KU BAR MIN LITTAFINA NA IYA HADA DOCOMENT DIN👏🏻👏🏻 KAJI TSORON HAKKIN DA BA NAKA BA_* *Na kudi ne* Koda zaki ganshi a gruops na sata ne idan kina bukatar ki biya kudin littafin ga yanda abin yake........Completed #600 ne sai ayi min magana ta WhatsApp da wannan number *07084653262* *BINTA UMAR ABBALE* * Downloaded from GNOVELS.COM.NG This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG For feedback and support Facebook : https://facebook.com/gnovels Twitter : https://twitter.com/gnovels Telegram : https://t.me/gnovels