Downloaded from GNOVELS.COM.NG This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG For feedback and support Facebook : https://facebook.com/gnovels Twitter : https://twitter.com/gnovels Telegram : https://t.me/gnovels NANA KHADIJA (littafi na daya) NA BINTA UMAR ABBALE (Maman Abdul Wahabu) NA FARA DA SUNAN ALLAH SARKI BUWAYI ,WANDA YA QAGI SAMA DA KASA SARKIN DA BABU KAMARSHI, ALLAH KAYI DADIN TSIRA GA ANNABI MUHAMMADU(SLW) WANDA KABAWA YA YADDAR KA ,ALLAH KA KARA TSIRA DA AMINCI A GARESHI DA AHALINSA DA SAHABBANSA TSARKAKA ALLAH YADDA KABANI IKON RUBUTA LITTAFIN NAN ,LAFIYA INA ROKANKA KASA IN GAMA LAFIYA, ALLAH KA YAFEMIN KUSAKURAI NA NA CIKI. AMEEN. WANNAN LITTAFIN QAGAGGE NE DA GA NI MARUBUCIYAR BANYI DOMIN WANI KO WATA BA WANDA YAGA YAYI DAI DAI DA RAYUWARSHI A RASHIN SANI NE GARGADI BAN YADDA WANI KO WATA YAYI AMFANI DA WANI BANGARE NA CIKIN LITTAFIN NAN BA BATARE DA SANINA BA ,DUK WANDA YA TABAMIN WANI SHASHE A CIKI ,ZAMU TSAYA A GABAN HUKUMA _WANNAN LITTAFIN NA KUD'I MALLAKIN ME SHI NI MARUBUCIYAR TUNDA 1,23,4,5,6 DIN SA BAN MALLAKAWA KOWA BA IN KANA BUKATA SAI KA BIYA KUDIN KARATU ZAKA SAME SHI DAGA FARKO HAR KARSHE HANNUN MARUCIYAR, WALLAHI DUK WANDA YW FUTAR MIN DASHI HAR 'YAN CIMA ZAUNE SUKA SAMU SUKA SIYAR MIN DASHI BAN YAFE MASA BA, NA FADA CEWAR DUK WANDA YACI DA GUMI NA UBANGIJI YAYI MIN SAKKAYA DOMIN BAZAN TABA YAFEWA BA ALLAHI. NASAN ALLAH BA AZZALIMI BANE ZAI BIMIN HAKKINA KAN ZALINTA TA DA AKAYI. DOMIN SAMUN CIGABAN WANNAN LITTAFIN KAN FARASHI ME SAUKI DARI BIYAR KACAL #500 DAGA 1,2,3,4,5,6 DUK AKWAI A GURIN MARUCIYAR DON HAKA ME BUKATAR KARANTA CIGABANSA SAI YA KIRA WANNAN NUMBAR KAMAR HAKA. 08089965176 07084653262 *BISIMILLAHIR-RAHAMANIR-RAHIM* Lkace kwabo fada ya rin ca6e tsakanin Dije da indo sai faman ko kawa suke Dije sai faman zagin indo take itako indo sai faman dukan ta take dake dama Dije bata da wani karfi sai aikin tsokanar fada gashi bata da wani jiki indo ta fita jikin girma Sa'a ko sai kokarin rabasu take yi suna hadawa da,ita. wata irin tsawa! su kaji an ce "kai wannan wane irin iskanci ne kukeyi anan da dabbanci "? cikin sauri Dije ta saki indo sai haki! take ta juyo jikinta sai tsuma ya keyi ganin yaya Ali ne a tsaye a gabansu ,,sai faman zare ido take harara ya banka mata yace "wato ke dan ubanki bazaki daina wannan iskancin ba ko? kitara yara ki ta kokawa a waje dan rashin kamun kai" ya mutsa baki tafara tana kunkuni dashi "to ina ruwanka za kazo ka wani ta kura mana ni banasan a shiga min sabga" duka ya kai mata abakin cikin zafin nama yace "dan ubanki wakikewa haka nisa anki ne " ? cikin sauri ta dafe bakinta hawaye ya na zuba tace "Allah ya isa mugu" cikin kunkunin tayi maganar mari ya kaimata gami da cewa "wato bakin ki bazai mutu ba ko wallahi sai na gyaramiki zama shashashar yarinya kawai stupid " yafada tare da jan hannuta tana turjewa yadaki kafarta ta fadi kasa ya hau janta a k'asa Su indo kuwa tun lokacin da yaya Ali ya mari Dije suka gudo sabuda sun San halinsa harsu zai hada ya Zane babu abinda ya dameshi,,janta yake yana dukanta da kafarsa itako bakin ta baibar yimai rashin kunya ba Nene, CE azaune a tsakargida tana ta faman gyaran wake ta ji ihun Dije tashi tai da sauri ta tana gyara daurin zaninta tana fadin "wallahi na tsani mugunta irin ta "yayan unguwar nan me kuma marainiyar Allah tai musu suke dukanta" kafin tarufe bakinta ta hango Dije a kasa Ali ya na janta kamar yana Jan tsumma Salati ta tabka tace "kai Ali wannan wane irin abune mai tayi maka dan mugunta "? tafada tare da karasawa tana kokarin kwatar Dije daga hannunsa "wai bada kai nake ba kasake ta mana wallahi ka kiyayeni akan wannan marainiyar Allah sa,arkace ita dazaka dunga dukanta iyi"? ,sakinta yayi yana jan tsaki tare da hararar Nene "yace wallahi Nene ke kike daurewa yarinyar nan gindi take yin abinda tagada ma". "to ina ruwanka da,ita iyi?" cewar Nene. cikin 6acin rai ya kalleta tare da daure fuskarsa yace "samunta nayi fa a waje ta tara yara suna ta faman dan be sai kace wasu dabbobi dan nai mata magana tahau zagina wallahi kija mata kune ta kiyayeni kan in bar garinnan sai na canja za mata kammanni da duka" Harara Nene ta galla masa tace "ka ki yaye ni Ali nifa ba na San ne man magana taya daga zuwan ka zaka ta kurawa yarinya tana wasa da kawayenta gaskiya in dai zaka zo ka ta kura mana ne gwara ka juya ka koma bana son zuwan naka haba ina dalili." Tak'arashe maganar tana gyara daurin zaninta, Fuskarshi babu Walwala yake kallonsu yana Mamakin Abinda Nene tace tabbas Nene in dai a kan yarinyar nan ne babu da Wanda baza ta 6ata ba ,cikin yanayin maganarshi yace "ae ba gurin ki nazo ba gurin "yan Uwa da Abokan Arziqi nazo wancan Mara kunyar yarinyar bata isa ta Sani na bar garin nan ba batare da na shirya ba" Harara D'ija ta galla masa tare da murgude baki tana bayan Nene A la6e Yana kallonta yana Mamakin Rashin kunyar yarinyar, Nene tace "to babu ruwanka da'ita har ka bar garin to kaji!! Bai ce komai ba ya Nufi bakin rijiya domin daukar bota da nufin daura Alwala ganin har an soma kiraye kirayen sallahr magari ba Ya na sane ya zira kafarshi daya wacce ke sanye da takalmi sawu ciki ya mutsikewa D'ija "yan ya tsu yayi saurin dauke kafarsa ya sakai ya fice daga gidan hannushi riqe da bota Wata kara D'ija ta kurma tana kallon kafarta guda domin Sam bata lura dashi ya take mata ba Da sauri Nene ta jiyo tace ke lafiyarki kuwa ?Cikin ihu D'ija tace "Nene kunama ce ta har beni yanzu" Da sauri Nene n ta kafama kafar D'ijan tana duba wa gami da jan yeta da gurin tana sallalami , ta hau duba kafar Tace" kefa kin fiye sangarta haka harbin kunama yake, ko dai wani kwaron ne ? Tashi ki bani guri in kara duba gurin" Da sauri D'ija ta matsa gefe tana jan kafa sai kace wacce tayi targaade Hakadai Nene takaraci dubanta a gun bata ga komai ba juyowa tai gurin dijan tace" Ai sai ki tashi daga gurin ko kije kiyi alwala lokacin sallah yayi na gaya miki kidai nai wa manya rashin kunya kinki ji idan yaje yaji miki ciwo babu ruwa na Ato,,cikin zumbura baki dije ta tashi da ga gun ta nufin inda butocin Al,wala suke ta dau daya dan duk abunta bata wasa da sallah da lokaci yayi take barin abinda take taje tai sallah Shi kam Ali yana gama alwala wani yaro ya bawa butar ya mayar gidan ya huce masallaci bai dawo ba saida ya jira lokacin isha ya gabatar da ita yai adu'oinsa sannan ya dawo gidan. Nene ya tarar ta idar da sallah isha dije kuma tana can gefe itama ta idar da sallahr tana ta faman cin wake da shinkafa wanda tasa nene tayi mata itakam tana bala'in san wake da shinkafa da manja da yaji tai ta zabga yaji tana ci tana zuk'ar baki, ko kallon inda take bai yi bah ya samu gefen Nene ya zauna yana karewa tsakar gidan kallo dan shi kam mutum ne mai tsamtsami abu kadan sai yasayi tashin zuciya yana da bala,in stafta komai nashi a tsare dan baya shiri da kazami gashi da wani irin hali. muskiline sosai sai ya gadama yake magana ko acikin abokansa ma haka dan har suna suka samasa ammafa duk wannan halinnasa bai raina mutum ko mai kankantarshi da iyayansa ya na bala'in sansu da kannansa to suma suna ji dashi sosai sabida ya nai musu abinda suke so Ammafa suna jin tsoransa musaman idan sukasan sunyi wani laifin dan baya musu wasa musamman akan harkar karatunsu, wannnan kenan Nene ce ta jiyo bayan tagama lazimi tace" to sarki kafi sarki mulki kazo kazaune min yanzu zakafara iyayin naka ko"? tafada tana gallamasa harara Murmushi ya saki ya kalleta yace " ke ba ayin abin arziki da ke daga zuwa na ko ruwan kirki baki bani nasha ba kina ta wani naiman fada dani" dariya Nene tayi tace" to ai kaine daga zuwanka ka fara halin naka" Ta shi tai tai nufi madafi wata katuwar kula ta fito dashi ta a jiye a gabansa hade da da faranti tace "gashinan ai mutumin kane nai maka sabida nasan ka ce yau zaka zo" tafada tana kokarin zuba masa tuwon shin kafa ne da miyar taushe wanda taji nama da manshanu sai kamshi ne ke tashi agun tun lokacin da tabude kular ,ta zuba mai ta ajiye a gabansa tace"to gadanga bissimilah"tafada tana murmushi dan in taso tsokanarsa da wannan sunan take kiransa. Gyara zama yai ya ce "saura ruwa ai cika ladanki uwargidana" gyara fuska tai tace "wannan kuma sai ka tashi ka dauko da kanka wai kai komai sai anyi maka" tafada tana harararsa hade fuska yai yace " sai kiyi ai nikuma bazanci ba indai baruwan kika kawumin ba"/ya fada yana kallonta da murmushi a fuskarsa dan yasan halinta indai baici abinci ba tashin hankalinta zata yi. Duk wannan abin da suke dije na gefe tana jinsu dan indai da sabo ta saba indai yazo sai sun ta tabkawa da Nene Nene ce ta kalleta tace" dije na tashi ki dauko masa ruwa a kinji tunda nari ga na zauna bazan tashi" Wani irin kallo yabi Nene dashi daga ita har dijan yace "har indai wannan yarinyar ce zata d'auko min ruwa wallahi bazan ci abincin ba kina ganin yanxu tagama kazantar ta bayan tagama lashe hannunta ko wanke wa batai ba sabida tsabar kazama ce ita kice ta d'auko min ruwa insha ki kwashe abincinki na fasa ci ya Riga yagama yin sanyi ma" yafada yana Dada gyara kwanciyarsa a gefenta harararshi tai ta tashi tana sababi "wannan yaro halinka sai dai kai matar ka zatasha iyayi da feleke" cikin daki tashige inda firji yake tadauko mai ruwa mai sanyi. Dije kam tana gefe sai faman harara take aika masa dashi a zuciyarta take fadin " a kwai babban kazami ma irin ka wai kai mai tsafta kadinga wani tsartar da yawu saika ce wata mace" Harara a duhu Dija take domin shi Ali bai San ma tana yi ba Nene CE ta,ajiye mai ruwa na roba hade da lemo mai sanyi tace "gashinan to sarkin tsurfa" tafada tana zama a gefensa ,,tashi yai yaje fi ya dauraye hannuwansa duk da cewa ba wani abin ya ta6a ba Dawo wa yai ya zauna ya jawo plate d'in abinci yai bisimillah ya fara ci ,humm Ali kenan cin abincinnasa ma abin kallo ne cike da tsurfa yake ci yanaci yana ta6e baki yana kallon Nene yana jiran yaji abinda zata ce Itako kallonsa batai ba sabida tasan Neman magana yake ta cigaba da sabgoginta,, Dije kam tashi daga gun tana faman zumbure zumburen baki taje ta wanke hannunta ta dawo sai taji tana san taci towan gashi cikinta ya cika ba yadda zata yi haka tashige daki ta canja kaya ta haye gadon Nene tai kwanciyarta Yana gama cin abinci ya tashi daga gun ya canja guri bayan ya wanke hannuwansa. haka Nene ta tashi bayya da ta iya ta kwashe kayan ta gyara gurin tana yi tana sababi shida yai mata shiru a zuciyarsa yace da rigima kenan idan kikaji da abinda nazo garin kenan duk wanann da kike shafar mai ne Bayan ta gama gyara gun ta dawo ta zauna tana kallonsa tace "tun dazu nake jiran inji dame kazo min yau kuma ? Murmushi ya saki yace" Nene mu kenan dame nazo miki kuwa inba da alkairai ba" Washe hakora tayi tace "dan nema to ina jinka" tafada tana tsare shi da ido gyara fuskar sa yayi Alamar maganar da zaiyi mai muhimanci ce yace " sako ne da ga ABBA, yace kihada kayanki gaba daya inzan koma in tafi dake dake da waccan marakunyar yarinyar. Wani irin kallo Nene ta watsa masa tace "wallahi ka kiyayeni Ali ka rainani ko bazanje ba" Tun yaushe ake magana daya nace bazan jeba ya kyalemu anan ina ce wancan satin shima basiru yazo nace bazan jeba saime zaku takuramin sai nabar daki na inatafi wata abuja ban zuwa tafada tana gyara zamanta" Kallonta yayi yana kwantar da kai dan ya fuskanci inba haka yayi mata ba da akwai matsala dole sai yai aikin rarrashinta, "Haba Nene wai yaushe zaki gane ne ba fa cewa akai kitafi kizauna acan gaba daya ba zaki dinga zuwa anan lokaci zuwa lokaci ,,kiyi hakuri mutafi kije kidan huta acan kinji uwargidana" ya fada yana murmushi Ko kallonsa batai ba yace "kinji Nene ,, tai mai banza Yace "to shikkenan tunda kinza6i atafi da da dijan taki babu matsala ai" cikin sauri tadago kai tana banka masa harara Dariya ce ta su6uce masa ya din gayi sai da yayi mai isar sa sannan yace " "ai dama zabi biyu ya bayar Abba yace inkice baza kixo ba to a kawo masa dije zai sata a makarantar boko tunda anan kin hana ta karatu" Kallon sa tayi tace "to ai sai ka jamu ka kai mu abuja nace ni bazan zuwa ahe" "To ai shikkenan kin san zan iya ko"? ya fada yana kallonta. Ya cigaba da cewa "wallahi kiyarda kawai mutafi in ba haka ba sai ki wayi gari kiga na tafi da wacan marakunyar inga yadda zakiyi" yafada yana ya mutsa fuskarsa Harararsa tayi tace "to katafin da ita mugani" "Haka kika ce"? Yafada idonshi a tsaye a kan ta. "Eh haka Na ce" tafada tana hararsa a karo Na biyu ,taci gaba da cewa munanan in da mukafi wayo babu wata Abuja da zamu ai nan ma tana karatun To! Kaji"! kallon ta yake yana ya mutse Fuska Na sabo yace"Shikkenan tunda kin fi son A tafi da yarinyar taki zaki wayi gari ki ga ba ta nan domin ba zamu zauna da Yarinya haka ba babu Arabi babu boko kin sangartata" Sanin Halin sa yasa na kaifi d'aya domin baya magana biyu, tunda taga yana wannan murmushin nashi tasan zai ai kata Ta kalleshi gami da gyara,zama tace " yanzu yaushe zaka tafi"? Shiru yayi sai da ta qara maimaitawa ,yace" Nan da kwana biyu" "To shikkenan zan bika Amma bazan Dade ba kwana biyu kawai zanyi in dawo ,domin bazan tafi in bar dakina ba ,da"yan Uwa da Abokan Arziqi" Cikin zuciyarsa yace "Ai sai kidawo mugani Nene kenan in kika tafi kin tafi kenan, Mik'ewa yayi yana kallon Agogon dake daure a hannunsa ,ya kalleta Cike da tsokana yace" Daga zuwana duk kin bi kin rikice sai faman fada kikeyi,kinqi ki barni Na huta" Dariya Tayi gami da gutsirar goron ta tace"ai kai ne Ali halinka sai kai daga zuwa kafara cikin zalin "yar marainiya Allah." Yace "zan shiga ciki in Dan huta" "To to ,cewa zakayi sai da safe kawai ,Ai gwara ka huta nasan A kwai gajiya a tare da kai ,Allah ya bamu Alkairi" Tafada tana kokarin kunna redion ta domin sauraren taskar Labarai A tashar Redio Kano ta bello dan dago. "To Allah ya tashemu Lafiya Uwargida kuma Amarya" yafada yana nufar hanyar dakinshi Na gidan Wanda idan ya sauka garin yake kwana ciki. Murmushi Nene tayi ,tabi bayanshi da Kallo ,Afili tace Dan Nema sarki iyayi da Feleqe kai dai naga matarka ai ka tsaya ruwan ido" Yana jin ta yayi mata shiru domain in ya biye ta tata sai su kwana a gurin gashi shi bacci yake ji ,bayan haka kuma jikinshi yayi masa Nauyi Wanka kawai yake son yi , Shi Mutum Wanda baya son zafi ko kadan. ASALIN LABARI Malam Ibrahim Haifafen garin Kano ne cikin Karamar hukumar Dan batta ,Mutum ne Wanda Allah yayi masa Arziqi a wancan lokacin ,shararan Manomi ne Wanda Mutane da dama suka ci suka bayar ta dalilinsa ,Asabili da Karamcinsa kwata kwata bashi da ganin kyashi ,in yaga baka da qarfi sosai zai talla fa maka har ka tsaya da kafarka. To Allah babu ta inda baya jarrabar bawa duk wannan dukiya da Allah ya Azurtashi da shi ,Allah bai bashi haihuwa ba, Shekararsu goma sha biyu da Aure da Matarshi Hajara, Wannan Abu sam bai tayarwa masa da hankali ba,tunda yasan haihuwa nufi ce daga Allah ,gashi duk fadin Kano babu Asibitin da basu je ba shida matar tasa maganar dai daya CE ,duk likitocin suke fada lafiyansu lau lokaci ne bai yi ba. Shiyasa kawai suka tattara suka barwa Allah ikon shi. Ganin haka ne yasa "yan Uwa da Abokan Arziqi suka dinga kawo masa yaransu ,wai ko zai Aura domin yasamu haihuwa, Yace"duk su kyaleshi ,yasan haihuwa lokaci ne idan yana da rabon haihuwa a duniya zai haihu ,ko yayi Aure ko bai yi ba, Su kyaleshi kawai shi yanzu bashi da bukatar karin Aure Shine fa "yan Uwa suka yi ca! A kan Hajara wato (Nene) cewar ai its ce ta mallakeshi sai Abinda tace yake yi. To Ashe duk wannan Abinda a ke ciki Hajara Na dauke da ciki Dan wata Uku dukkaninsu basu San dashi ba. I ta dai tanaji sauye sauye a jikinta Amma bata kawo ciki gareta ba,yau da lafiya gobe babu ,Malam Ibrahim yace su tafi Asibiti kawai a duba ta. Tashin Farko Likita da ya dubata yayi mata a won fitsari anan ya gano ciki gareta,Dan wata Uku da kwanaki Ya kalli Malam Ibrahim yace"matarka Na dauke da ciki Dan wata uku. "Alhmdullihi Alhmdullhi Alhmdullhi" Shine Abinda Malam Ibrahim yariqa maimaitawa yace"hakika babu sarki sai Allah ,ya Ubangija Na gode maka da kayimin wannan baiwar, Yafada yana kallon doctor din fuskarshi cike da Annuri Dr yace"tabbas Allah ne Abin godiya,yanzu zamu daura ta kan Abubuwan da masu juna biyu ya dace suyi da irin Abinci da ta riqa ci ,bayan nan kuma idan cikin yayi wata hudu sai tafara zuwa Asibiti domin a riqa Auna shi" "In sha Allahu Malam din yafada" Doctor ya rubuta musu Magani masu kyau sosai da kara lafiya ga mai ciki. Sannan sukayi masa sallama suka tafi bayan Malam yayi masa Alkairi sosai da sosai Nene ma tayi farin ciki sosai Amma bata nunawa sabida kunya irin ta fulani ,to haka dai suka cigaba da rainon cikin har lokacin haihuwa yazo. Cikin ikon Allah Nene ta haihu lafiya cikin Dakin ta in da tasamu da Namiji ,farin ciki gurin Malam Ibrahim babu kama hannun yaro "yan Uwa da Abokan Arziqi suka riqa tayashi murna ,shiko ya din ga fitar da hatsi yana rabawa talakawa,ranar suna yaro yaci sunan Bashir. Haka Bashir ya ta so gaban iyayenshi cikin kulawa domin Nene macace mai kula da yara gami da tsabta, Sai da Basir ya shiga pramary 4 sannan Nene ta samu wani cikin lokacin yana shekara goma sha biyu ,wannan karon ma Malam Ibrahim yayi farin ciki haka yayi ta hidima da Nene da cikinta. Lokacin da Bashir ya fahimci Mahaifiyarshi Na da ciki sai yayi ta murna zai samu qani,domin yana da bala'in son yara **** Wannan karon ma Allah ya sauki Nene Lafiya a dakinta in da raqara samun da Namiji ,malam Ibarqhim yayi farin ciki sosai da sosai ,ranar suna a ka sawa yaro suna Lawan, Nene taci gaba da rainon yaranta cikin kulawa,Bashir yana kaunar Dan uwansa sosai ,in babu makaranta shi yakewe Nene raino Dan har makarqntar Allo ya kan tafi da Lawan Allah sarki mai yadda yaso ,shekarar Lawan Uku a duniya Allah ya karbi ran Malama Ibarahim mutuwar da ta gigita Zukatan Al'uma sosai,Nene tasha kuka daga karshe sai ta danga ga Allah taci gaba da rainon yaranta. ***** Bashir mutum ne Na jama'a baya zama ,sosai tunda ya kammala scondry skull yafara harkar Siyasa, A daddafe ,ya tafi ,bayaro univasity dake kano ya samu difoloma ,sai ya watsar da karatun ya shiga siyasa gadan gadan Tun Nene bata so ,daga baya sai ta dawo tana masa Addu'a. Dan Uwanshi kuwa Lawan babu ruwanshi domin magana ma bata dameshi ba, Shima a yanzu yana makarantar gaba da primary Duk Abinda Bashir ya samu Na jama'a ne ,shayasa a kasa ka masa Bashir Mai jama'a Ganin girma yazo masa ya Sa Nene tayi masa maganar yayi Aure domin shine cikar mutum Nan ya nuna mata shifa yanzu bashi da wata budurwa harkar Siyasar sa kawai yake Nene tace to yaje yaga Zainab "yar gidan kawun shi wato Kanin Malam ibarahin tace taga yarinyar tana da hankali da nutsuwa .yace to shikkenan zai je ya ganta Ko da Bashir ya ga Zainab sai yaji ta kwanta masa,sabida haka ba'a dauki wani dogon lokaci ba a kasha shagali Amarya ta tare nan gidan kusa da Nene dake gida ne girman gaske ,haka Bashir ya yanki guri yayi ginin zamani sosai. Yawan kyautarsa da tausayin talakawa yasa matasa da tsaffin yankin Nash suka tsayar dashi takarar Craman ,Aikuwa Abin ikon Allah lokacin zabe yana zuwa Bashir ya lashe yazabe. Zoka ga murna gurin jama'ar gari ,da "yan Uwa da Abokan Arziqi jama'a sun ji dadi domin suna ganin Bashir zai kawo ci gaba a yankin nasu Lokacin Zainab matarshi tana da tsohon ciki ,Haka tai ta taya mijinta murna, Nena ma tayi farin ciki sosai tai tayi masa fatan Alkairi gami da Addu'a Allah ya tayashi riqo,ya sauke nauyi da ya dauko Lawan ko dashi a kai ta fadi tashi ,bakinshi yaqi rufuwa ,Sai murna yake. A taike dai Alh Bashir yariqe mukamai da dama ta fannin Siyasa in da daga baya yasaki harkar Siyasa yafada kasuwanci ,shida wani Abokinshi Alh Auwalu ,sosai suke shi go da motoci Iri daban daban Na zamani Cikin farashi mai sauqi i ta iya da halinshi. Tun yana yaro yake da mugun kyankyami Abu qalilan zai sashi yai ta kwara A mai Nene tayi kewarsa sosai sabida sun shaqu da juna Basu jima da komawa Abuja ba Hajiya Zainab tasamu ciki Alh Bashir yayi ta murna Lokacin haihuwa yazo Allah ya sauke ta lafiya an samu da Namiji Nene tace A sama jamelu To haka rayuwa ta tafi Alh Bashir Arziqi yana kara bunkasa sosai da sosai Yaranshi hudu biyu maza biyu mata *wanene Aliyu* yana da bakar zuciya da miskalnci sai kai mai mgn goma bai kula kaba sai yaga dama zai amsa daya yana da bala,in tsafta dan haka ba abincin kuwa yake ciba in kacire nenensa da ummi bai yadda ko ruwa masu aiki subashi ba indai bai daga hannu ummi ya fito ba duk da cewar ruwan roba ne Yana mutukar san ya ga yazama soja tun yana yaro shiya sa yadage sai da yatafi yai karatu sosai akan aikin yanxu haka ya kammala aiki kawai yake jira ya fara,,, To lawan ma akwai wata daya so anan bayan gidansu yarinyace mai sanyi hali kamar sa sunanta khadija ,, Da nene ta fuskanta tace to baza ai jinkiri ba taje ta sami yayan mahaifinsu tace to aje a ne mar mai auranta ,, Aikam ba,awani dau lokaci ba aka sha shagali bayan duk 6angare biyu sun amince amarya ta tare anan gidan kusa da nene tunda gida ne mai girman gaske bangare bangarene ,, Idan baku mantaba dama mlm ibarahim mai arzikine a wannan yankin nasu a wancan lokacin gidansa ma abin kallo ne Nene tana mutukar jin dadin zama da khadija sabida irin matan nan ne masu kirki da saukin kai babu ruwan ta da hayaniya haka shima lawan din yana jin dadin zama da ita ,, Alh bashir kam yakanzo lokaci zuwa lokaci dashi da iyalinsa yakan dan jima kan yakuma abuja shiyasa yaran sukasa saba sosai musamman Ali mutumin nene tana bala,in sansa ,,shikam Ali bai san tanayi bah Sai tahana kowa abu tace Ali zata bawa sai yazo tabashi yace bayaci ko ya kar6a ya bayar a gabanta ba yadda zata,yi takari mitarta ta gama yai mata banza ,, To haka rayuwa taita tafiya lawan Allah bai bashi haihuwa da wuriba sai da sukai shekara sha uku da aure sannan Allah ya a zurta khadija da samun ciki,, Nene taita murna dan a zuciyarta take cewa shine yagaji irn haihuwata dan har tana ganin ma ko bazai haihu bashi huumm ,,,,,nace nene ai abin na Allah Tunda khadija tasamu ciki take faman shan wahala yau da lafiya gobe babu irin cikin nan ne mai bala,in laulayi ta ke dashi dan haka nene bata barinta tai komai a gidan. gashi nene ta d'au son duniya ta daurawa cikin abu kadan khadija zatai zatahau yi mata fada wai bata kula da kanta itadai sadai tai dariya kawai. To da haka watan haihuwa ya kama ciwo matsawa khadija musamman ciwon kai da mara nene tace suta fi asibiti aikam da sukaje likitoci suka dubata sukace haihuwa da sauran kwanaki amma akan hanya take suka ce ta kula da daukar abu mai nauyi da yin aiki n wahala kuma tadaina cin gishiri dayawa idan da wata damuwa d tasa ranta ta cire,, nene tace ai dama bb wani aiki da take kawai larura ce irin ta masu ciki haka suka dawu gida bayan an bata magani kuma sukace yaron lafiyar sa lau Kwana biyu da zuwansu cikin dare khadija ta tashi da ciwo haka lawan ya fito ya sanarwa nene A gigice nene ta shiga bangarannasu ta tarar da khadija sai faman zubda jini ta ke gashi sai nishi take haihuwa taki zuwa da sauri nene taka mata ta rike tana tofa mata adu,oi sannan ta kalli lawan tace yai maza yaje yakarbo rubutun nakuda a gun malam yahaya wani makocinsun ne anan mai "yan makaran ta Cikin a zama yatafi yana tafiya yana ado,a acikin ran,sa ganin irin wahalar d khadija take sha yana girmama irin wahalar da mata suke sha yayin haihuwa tunda duk a gabansa khadijan tafara nakudar,, a xuciyar sa yake fadin duk wanda bai bi iyayen sa ba yayi asara,, To cikin hunkuncin ubangiji kan yadawu ma Allah ya sauki ta lafiya inda ta haifi diya mace ya dawu wa yai ya tarar nene sai hidmar gyara baby take baki ya washe yana nene me,akasamu ne? Nene jikinta a sanyaye tace mace ce lawan bani rubutun daka kar6o ka kuma waje tukkun kafin a gyara gun,,mikamata yai shima jikin sa da dan sanyi ganin yanayin nene,, Nene kam khadija ta dago tana bata rubutun ganin har yanzu mabiya bata fado ba gashi jini sai zuba yake sosai,, Tayi duk dabarun irin na gida abin ya faskara ,,lawan takira tace maza yatafi ya samu mota suzu sutafi asibiti ,,da sauri yatafi gashi har an soma kirayekirayen sallar asubah ,, Allahu Akabar kafin yadawu rai yayi halinsa kadija ta amsa kiran ubangiji Wayyo duniya abar tsoro,, Innalilahi wa ina,illahi raji,u shine abinda nene take ta fada Wannan yarinya Allah yakar6i shadarki Allah yasa annabi yasan da zuwanki Allah ya kafartamiki shine abinda nene take ta maimaitawa,, Tun a hanya lawan yaji gabansa yanata faduwa yacigaba da nana ta innalilahi a ransa sai yaji kamar anace masa ta mutu ay ,,,gabansa ya yanke y fadi da sauri ya shiga gida ,,sai yatarar da nene a tsaye da wasu mata biyu ,, Yace nene ga mai motar nan ansamu ina khadijan ta ke yafada ya na kokarin shiga dakin nene ce ta rike hannunsa tace jeka sallami mai motar ai tasamu sauki ma ,,to yace jikinsa a sanyaye ya fita yana fita yaci karo da yayar khadija da maihaifiyarta da wasu daga cikin danginta ,,wasunsu nata hawaye ,, Tsayawa yai kawai yana kalloansu sai yaji wata acikin su tana lawan ya hakurinmu ido ya bita dashi kawai ya sallami mai motar yajuya shiga gidan ,, Kai tsaye dakin da khadijanta ke ya sa kai yana so ya tabbatar da abinda kunnuwansa suka jiye mai,, . Bb wanda ya hanashi shiga har nene ,,yana shiga yadaga zanin da nene ta rufe khadija da shi yatsaya y na kallonta ,,a ransa yana ta nanata innalilahi wa innalahi raju,u ,,sai yaji wata dauriya tazo masa ya tsuguna a gefe daya ya fara yimata karatu yana ta nai man mata gafara a gun buwayi gagara misali,, Ya ji ma a gun a zaune babu wanda yashiga dakin ,,dakansa yatashi ya fito ganin gari ya soma washewa yaje ya dauro al wala yai sallah,, To haka rayuwa take dama haka akaima khadija suttura a kaita gidanta na gaskiya,,,,, Haka lawan yaci gaba da karbar gaisuwa gurin "yan uwa da abokan ar ziki"" Alh, bashir shida iyalinsa sun jima kan sukoma abuja ,,,,ganin yadda hankalin nene ya tashi a wancan lokaci ya zauna yadinga rarrashin kanin nasa da ita kanta nene n,,, To yarinya dai nene tace amayar mata da sunan maihaifiyarta ,,wanda nene tadauki son duniya ta daura mata bata san ko tsinke ya sauka a kanta,, ita tasama ta dije wai tunda sunan maihaifiyarta ne da ita ,,Alh bashir ba yadda vaiyi da nene tabashi baby sutafi da,ita tunda a lokacin hjy zainab tana da karamin goyo ta hada ta shayar dasu tare ,,amma nene ta ke kashe tace bata yadda ba a kyaleta a gunta ita zata kula da ita ,,haka suka je asibiti a ka daura baby n da irin madarar da yakamata a bata,, Sai da ya tabbatar komai ya kammala sannan suka tafi bayan yadada kwantarwa da kanin nasa hankali ganin yadda kanin nasa ya koma lokaci qan kani,,,,, Duk wnn abin da yafaru Ali bayanan yanaca london karatu sai dai waya yaji komai shima yaji mutuwar auntynsa ,,sabida yana mutukar kaunarta ,, Haka kawai Allah y hada jininsa da ita ,,a rayuwarsa yana san yaga mutum mai tsabata wanda yasan meye rayuwa ya san abinda yake,,, To khadija duk tana da wnn halin Haka yai mata adu,a acan ,amma yaji mutuwar sosai To nene haka taciga da rainan dije tana bata kulawa yadda ya kamata ,,tai bala,in shagwabata batasan Bacin ranta ,,duk abinda tayi daidai ne a gunta gashi zataje tai tsokana amma in aka doke ta tace anci zalin mairaniya ko makaranta dije batasan zuwa saitace wai dukan ta,ake ita ko nene sai tace tai zamanta,,, Lawan har yagaji ya zuba musu ido dan baya iyawa da bala,in nene in dai akan dije ne,,, Allah sarki rayuwa shekarar dije hudu Allah ya karbi ran lawan ,,ranar wata juma,a da dadddare ciwon ciki farat daya,, Wannan mutuwa ta lawan ta gigita Alh bashir da nene ,,to ya za,ai haka duniya take dama,, Dije tazama marainiya gaba da baya bbu maihaifa ,, Nene kuwa tace ,,yan nan bazakiyi maraici ba indai ina raye,, To ko da Alh bashir yazo bayan an share makoki bayyada bayi da nene ba akan tazo su tafi can abuja n amma nene tace bata zuwa haka yahukara ya kyale ta suka tafi sai dai duk wani abu na more rayuwa yana siyar mata ya a ajiemata kan yatafi shiyasa bata da matsalar komai na rayuwa ,,sai dai lokaci zuwa lokaci yan kazo ya ganta ko yaran su zu hutu ,, Acikin wanan lokacin Ali ya dira a gidan bayan ya kammala karatun sa yadawo gida, baya na ciki ba yaushe ya fita"? nene tafada cikin mamaki Tace" yanxu mana naganshi zai fita bayan nadawo daga gidansu sa,a Nene. Tace" to ai ni banga fitarshi ba inanan ina fama da aiki" Zumbura baki dija tayi tace" wallahi nene bakiji yadda hannuna yake zogi ba Wallahi Allah ya isana bazan taba yafewa hakafa dazu dayaje makaranta yasa aka zane ni wai ni mai nai mai ya tsaneni tafada cikin kuka Kallonta nene tayi tace" bai tsaneki ba dija ai dan uwanki ne kawai halinki ne baya so wanda nima fada nake miki akansa" Sake turo baki tayi tace "to ai ni ba kulashi nake ba haka kawai sai yadinga cemin kazama " Dariya nene tayi tace "ai sai kiyi Halin Ali ai sai shi kowa haka yake kiranshin bake ba" Wucewa tayi tasa mu guri tazauna idonta sunyi ja sabida kukan da ta ci acikin ranta kuwa tayiwa Ali Allah ya isa yafi dubu To Ali daya fita ma bai samu serve's din dayake nema ba kasancewar garin akwai hadari shiyasa zafin yai yawa Zamansa yayi sai da yaji amfara kiran sannan ya mik'e tare da barin gurin. Gidan ya shiga kai tsaye inda botocin Alwala suke ya nufa daya ya dauko ya soma daura alwala Nene ce dake cikin kichin ta kai kallonta inda yake tace "wai inakaje ai nadauka kana daki ai danaji kace ka gaji " Shiru yai sai data kuma maimaitawa sannan yace" ina waje ina dan shan iska yafada ya kokarin barin gidan gannin har wasu massallatai sun so ma tayar da sallah shikam ai baya bari jam,i ya shigeshi Ali a kwai riko da addini,, Dija ce itama ta tashi ta yazo ta dau bota taje takama ruwa tazo tai tata alwalar Domin rai nan Nene ce Nene kam akwai riko da addini Bai dawo gidan ba gidan ba sai da ya tsaya Ya jira isha tayi ya gabatar da ita sannan . Wata katuwar tabarma Nene ta shinfida kamar dai jiya a tsakar gidan tana zaune itama tana Jan carbi gefenta dija CE a kwance bacci yana son kamata Neman guri yayi kusa da nene ya zauna hade da ciro wayarsa daga aljihu ya hau latse,latsensa da,ita Nene kam ganin dija tana son yin bacci gashi bata ci abinci ba ,sai ta hau yin gyaran murya!! a nufinta tanayiwa dija a lama da ta tashi ta ci abinci So take ta karasa jan carbin ta bata so ta katse tunda ta kusa kammalawa Dija kam ai batasn tanayi ba bacci har ya kwasheta,, Ali ta kalla tai mai alama!!da hannuta cewar ya tashe ta ,, Sarai ya fahimchi mai take nufi sai ya nuna kamar bai fahimta ba ya share kawai yana dan ya mutsa fuskarsa ya cigaba da abinda yake Haka nene ta hakura har saida ta idar sannan tace "kana ganin ta tai bacci mai makon ka tashe ta " Kallonta yayi da fuska a ya mutse ya ce "kina nufin wai in tashe ta ta zageni yarinyar da bata da kunya ta Riga ta raina mutane" Nene tace "kai kam ai halinka sai kai haka kawai sai tahau zaginka akan katasheta daga bacci? Don Allah kacanja hali Ali" tafada tana mikewa Kichin ta nufa ta fara debo kulolin abinci. Tana fadin ai "yau mutumin ka nai towan Alkama ne da miyar kubewa" tafada tana murmushi domin tasan yana son towan mussaman in nata ne Ai kam sakin murmushi yayi ya ce "amma kin birgeni uwargida yau inayi dake" yafa da da murmushi akan fuskarsa Dariya nene tayi tace "d'an nema ai ko ka ki ko kaso nice dai takarfen duk wacce za tazo sai dai ta biyo bayana" tafada tana kokarin zu ba masa abincin. Wani iri kamshine yake tashi tunda tafara zubamai abincin, wata miya ce ta daji nama sosai da man shanu sai kamshi yake towan ko a mulmuleshi a leda abin gwanin sha,awa,, Shima Ali gyara zama yai dan tunda tafa ra zuba mai miyansa yake faman tsinkewa jawo flet din da ta zuba mai yayi yai bissimillah y faraci. Hummm nene badai iya girki ba yafada a cikin ransa Nene kam dija tau tashi domin taji abincin itama,, tashi tayi zaune nene tace kinsan banasan ki kwanta baki ci abinci ba gaki da shegen magagi kan ki wartsakema aiki ne tafa da tana tura mata flet din abincin bayan ta zubamata,, Ali kam kallon ikon Allah ya tsaya yana yi ganin dija tana kokarin jawu plate din ta fara ci batare da taje ta wanke bakinta a ganinsa ya kama ta ta wanke bakin ta in ba kazanta ba Tana kokarin tura towan bakinta yaji zuciyarshi tana faman tashi dan shi kam abu kadan sai ya sashi jin tashin zuciya. Cikin wata irin tsawa yace "ke! dan ubanki tashi kije ki wanke baki wawuyar yarinya kawai inbanda kazanta kiyi bacci kitashi kidau abu kisa abakinki sabuda rashin hankali" yafada yana ya mutse fuskarsa Itakam Nene bata lura bama sai da yayi magana sannan takai dubanta inda dijan take zaune tace "ai shiyasa banasan tafara bacci sabida tana da magagi yanzu da a haka zaki ci abinci"? ta fada tana rike baki! Ita kam dija zumbura baki tayi tace "nifa banyi bacci ba duk abinda kuke ina jinku" nene tace "tashi dallah kije ki daurayo bakinki waye yake miki karya anan kin kwanta kinayin magari ba ko isha bakiyi ba kice ba bacci kike ba,, Tashi tai tana faman kunkuni a ranta itafa an ta kura mata ko ina ruwan mutum da,ita oho ita har ga Allah bata ji wani canji abakinta ba ganin ba wani baccin kirki tayi ba ,,daza,ace ta wani wanke baki ta to bakin wa ye ai nata ne tafada cikin kunkuni Nene tace "au!! surutai kike dan anfada miki gaskiya in banda ke dija ai ke kanki sai kinfin jin dadin cin abinci in kika kuskure bakinki" Cikin sauri dija tace "nifa nene badake nake ba" "To dawa kike iyi ? shiru tai nene tace Alin sa'anki ne wai wai."? "Ba gaskiya ya fada miki ba na hana ki yiwa nagaba dake rashin kunya kinki ji to babu ruwa na ai gaki nan gashi"tafada tana kukarin kunna redio nta. Ali kam bai ce komai ba cigaba da cin abincinsa yai amma sarai yaji irin maganganun da dija take fada ,,shi abin ma yanzu mamaki yake bashi gannin yarinyar kamar wacce ake kara zugawa tai mai rashin kunya,, Gashi shi bashi ga sabgarta yake ba ballantana ace kawai dai halinta ne da kuma rainon da nene tayi mata wanda hausawa suke cewa rokon kaka Tsaki ya ja aransa hade da girgiza kai yace tabbas sai ya tsawatar wa da yarinyar nan kafin ta dai daita hankalinta Dija kam bayan ta wanko bakin zama tai tafara cin abincin tace "nene baki samin man shanu ba" kallonta nene tayi tace gashinan ai kusa dake ki tsiyaya mana" Man shanun ta ta zuba cikin niyar ta cigaba da cin abincin ta kar bata yi laifi ba da sawa kamar batai wani laifi ba Shiru gurin yai in banda sautin ridio nene dake tashi babu wanda ya kuma cewa kala a gun Yana gamawa ya mike daga gun yaje ya daureye sannuwansa domin cin towa dai dole sai da hannu bai ce komai ba ya fuce daga gidan ransa a mutukar bace yana tunanin irin hukunci da zaiyiwa wan yarinyar . Nene ce tace. "Ina zaka naga kana kokarin fita Cigaba da tafiya yai yace "zan dan fita ne insha iska" domin dai ita kanta nene haushi take bashi ganin duk da sa hannuta yarinyar tazama abinda tazama Ficewarsa yai ko kallonta taba baiyi ba yayin da take cewa kai da ba kowa ka sani ba a garin." Shikam Ali a zahiri zama ne bayasan yayi inda dija na gurin dan ji yake zai,iya karyata ya zubar a yanda zuciyarsa take mai zafi Sabuda ya tsani raini rainin ma daga yarinya karama shi abin ma mamaki yake bashi ,,ganin yadda su Na'ima da jamil suke bala,in jin tsoransa ko acikin abokai ne shi nada ban ne sam ba,a kawo masa raini amma abin mamaki wanan kazamar yarinyar bata shakkar ta zage shi a gaban kowa. Lallai kam bazai dauki wanann ba wallahi sai yayi mugun saba mata in dai shi ne a haka take so taje cikin jama,a tayi musu rashin arziki tana zubar musu da kima wannan bazai yiwu ba dole sai ya saita mata tunani Haka ya gama zancan zucinsa da irin tanade tanaden a zabar da zai ganawa dija mudun tace zataje abuja da wannan haleyen nata To nene kam daki tashige bayan Ali ya fita Kokarin sauko da akwati take daka kan siff so take ta zuba musu "yan kayan da zasuyi amfani dashi ,,tunda yace gobe da wuri zasu kama hanya ,, Ace warta bazata dibi wasu kaya dayawa ba tunda bawani dadewa zasuyi ba itakam tabazata wuce sati biyu zata dawu Dija ta kwalawa kira dake tsakar gida gama cin abincinta kenan amsawa tayi tace "Nene menene? Nene tace "zo ki tayani zuba kayannan acikin jakar nan gobe in sha,Allahu da wuri zamu tafi amma ki nikkesu akafin kisa domin sufi zama Dija tace to fara zuba kayan tayi tace nene kala nawa kika ibar min nawa kayan, kuma yaushe zamu dawo? Ai bawani dadewa zamuyi ba baza mu huce sati biyu ba" turbune fuska dija tayi tace "gaskiya nene in munje kar mu dawo da wuri mu bari sai andan kwana biyu kinji ta fada cikin shagwaba nene tace ",inbanda abinki dija makarantar wa zaije miki ita" Dija tai sauri tace basai aje a fada ba,, Shiru Nene tayi taci gaba da ninke kayansu tana zubawa cikin Akwati D'ija ta marai rai ce tace"kin ji Nene. Dan Allah aje a fada" Nene tace"waye zai je ya fada bayan lokaci ya kure" Marairai ce fuska D'ija tayi tace "ba sai Haruna Na gidan baba malam yaje yafada ba" Nene tace"to Allah ya kaimu Ai ba wani dadewa zamuyi ba sati biyu zamuyi mudawo" D'ija ta bata Fuska,tace"gaskiya kar mu dawo da wuri Nene Naji an ce garin yana da dadi" Nene tace"sai kiyi kuma ni bazan je wata Abuja in share guri in zauna ba bayan ga dakina Na bari" .zumbura baki D'ija tayi tana gyara kwanciya,sabida tasan halin Nene duk Abinda tafada ya sauna. Ali ko yana shiga dakinshi Wanka yayi , Yayi shirin bacci ,sai ya zauna gefan katifarshi ya kunna loptp din shi yana duba sakkonin. Duk yawanci sakkonin daga Abokan Aikinshi ne,mussaman ogansu,sai sakon Aminin shi Faruk yana kara jaddada masa dole gobe ya dawo domin Akwai wasu takkadu da zasu cike. Sai sakon mutuniyarshi Siyama Yafara dubawa Fuskarshi a sake lokacin da ya duba wani sakon ta inda take fadin ,ya taimaka ya karbi soyyayar ta zuciyarta ta makance a kansa,Zara iya hakura da Aure har abada mutukar bai Aure ta. Yarinyar ta bashi tausayi ,sabida yadda ta damu dashi da rayuwarshi shi kuma kwata kwata bata gabanshi domin bata da tsarin da yake son Matar da zai Aura,yana son Mace doguwa mai Addini wacce tasan meye rayuwa ,bayan haka yana son Mace mai sharp da tsarin jiki mai kyau. Gami da gashi bayan haka shi duk wani kyalekyalen matan Zamani baya rudashi ,a cewarsa duk qazamai ne a waje zaka gansu tsaf tsaf Amma daga anyi Aure ,sai qazanta ,da rashin iya kula da miji Shiyasa matan da suke burgeshi , Mai hafin Siyama Abokin Abbah ne tare suke harkar kasuwancinsu sun shaqo sosai har ta kai suna son su hada zuri'arsu Aure ,wato Siyama da Ali Siyama sa'ar Na'ima ce kanwar Ali shiyasa tasu tazo daya,siyama Na yawan zuwa Hutu gidansu ,Amma sabida Ali take zuwa ,Wanda bai San tanayi ba Ashe ta cewa babanta soyyaya suke da Ali har sunyi Alkwarin Aure ,da ta kammala karatu zasuyi Aure ,Dady nta cikin farin ciki yasamu Abbah ya sanar dashi,sukaita farin ciki har dai suka saka lokacin daurin Aure duk ba tare da sanin Ali WANAN KENAN WACECE D'IJA? Lawan Dai Kani ga Alh Bashir Mahaifin Aliyu Shine Mahaifin ta, Yayi Aure in da Ya Auri Wata yarinya mai suna Khadija nan bayan gidansu, babu yadda Alh Bashir bai yi ba a kan Lawan ya je Abuja,Zai Samar masa Abin yi,yace yafi son zama kusa da Nene,Dan ko da yayi Auran ma Ciklin gidan suka tare da matarshi Khadija,mai kirki kamar mijinta,Nene tana jin dadin Zama da ita Sosai Shiyasa duk wani Abu da tasamu Na ta ne Cikin ikon Allah ,Allah ya azirta ta da ciki ,Nene ta riqa Murna,ta dauki son duniya ta dorawa cikin, Cikin Khadija Na da wata takwas tafara wani irin ciwon Kai! Mai zafi,sukaje Asibiti likita ya Dora ta a kan Magani, Yace ta rage Aikace Aikace yin hakan yana iya barazana da lafiyarta da ta jaririn. To haka Nene ta hanata duk wasu Ai kace Ai kace Na gida ,ita take yi, ranar wata laraba Khadija ta tashi da wani irin ciwon mara maitsanani lawan ya fita ,cikin daren yaje ya kira Nene, Kallao daya tayi mata ta fahimci haihuwa ce,ta karasa cikin dakin sosai ta rirriqe ta ,tana mata sannu. Ta kalli lawan tace"maza yaje gidan baba malam ya karbo rubutun nakuda(haihuwa) Lawan ya fita da sauri yana addu'a Allah ya sauki Khadija lafiya,tabbas duk wanda bai bi iyayensa ba ya shiga uku,ganin yadda matarshi take shan wahala. Ko minti goma bai yi ba ya dawo gidan hannunshi ruqe da rubutu a daure a farar leda yayi sallama ,gami da mika wa Nene rubutu,sannan ya ja ya tsaya bakinshi dauke da addu'o i na fatan Allah yasa ta haihu lafiya Cikin ikon Allah Khadija na shanye rubutun ta haihu ,Nene tai yiwa Alkah godiya ,sannan ta dauke jaririyar ta nan nade a zani,sai ta dawo kan Khadija,tana yi mata dabaru domin a samu nahaifar ta fado, Khadija sai nishi take na wahala tsawon awa daya da haihuwar ta mahaifa taqi fadowa, Nene hankalin ta ya tashi ,ta kira Lawan ,wanda yake waje a tsaye, Ya daga labule,kafin tace wani abu,yace"ta haihu ne"? Nene tace "e ta haihu" Cikin farin ciki yace"Nene mai a kasamu"? Cikin tausayi Nene ta kalli Khadija dake durqushe tana nishi! ga jini ya tsinke yana zuba mahaifa bata fado ba. Tace"macace maza kaje ka samo mana mota mutafi asibiti mahaifa taqi fadowa" Nene ta fadi maganar Cikin qarfin hali,domin ta gama sarewa da lamarin ganin yadda khadijan take ta salati tana rirriqeta Lawan hankalinshi ya tashi,ganin yadda hankalin mahaifiyarshi ya tashi ya fita da sauri, Nene tayi iya kokarin ta amma abinda Allah ya hukunta babu makawa sai ya faru, ana kiran sallar farko Khadija ta amsa kiran Ubangiji rai yayi halinshi. *innaliliahi wa'ina ilaihi rajinun* Shine abinda Nene tariqa maimatawa ta gyara gawar gami da lullube ta da zani, ta fito daga dakin tana wa Allah tasbihi gami da nemawa Khadija rahamarsa. Tun a hanya jikinshi yayi sanyi zuciyarshi tana tayi masa saq-saq hakadai suka karaso kofar gidan dashi da mai motar. Zai shiga gidan keken yaga Yayar Khadija da wasu daga cikin danginsu sun tawo suna kuka, daya daga cikinsu tace"Lawan ya mukaji da hakuri ,Allah ya jikan khadija Bai ce mata komai ba ya sakai ya shiga gidan gabanshi yana faduwa Ko da ya shiga gidan Nene na tsaye tsakar gidan ita da wasu mata duk sunyi jigum jigum yace" Nene ga mai motar nan" Nene tace"ai ta samu sauki ma ,Allah ya amshi abinsa Lawan kayi hakuri kaji ko Allah ya jikan Khadija" Lawan ya rika salati jikinshi sai karkarwa yakeyi ya bude dakin da Matartashi take kwance,ya ganta a lullube da zani,sai ya tsuguna kusa da ita ya bude fuskar yana kallo tamkar mai bacci haka ya gani innallilahi wa'ina ilayi raji'un kawai yake fada a zuciyara yace"yanzu Khadija kin tafi kin barni,Allahu akabar,zama yayi ya rika yi mata adduoi har a kayi kiran sallah,asubah ya fito ya daura alwala ta nufi masallaci, Duniya kenan ,haka a kaiwa Khadija suttura a ka kaita gidanta na gaskiya, sai bayan sarakar bakwai ne sannan Alh Bashir yafara shirin tafiya shida iyalinshi a lokacin Ali na Engila karatu,sai waya a kayi masa,gaskiya yaji mutuwar auntyshi sabida yadda jininsu ya hadu da ita in yaje gurin Nene tayi ta hidima dashi ,yana son mace mai hankali da fahinta da tsafta shiyasa suke shiri da ita sosai,nan dai yayi mata adduoi na Neman rahamar Allah Alh Bashir yayi yayi da Nene tabashi baby su tafi tare da ita ,Ummi ta hadasu tare da yarinyar ta da take goyo a lokacin Fa'iza ta shayar dasu Nene tace Sam a kyale mata ita zata iya kula da ita,babu yadda ya iya haka sukaje asibiti a ka Dora baby kan madarar da ta dace da ita ,sai da ya tabbatar ya ajiye musu komai na bukata sannan suka wuce abuja tare da iyalinshi, Nene ta dau son duniya ta dorashi kan D'ija bata so ko kuda ya sauka a kanta sabida yadda take rattalinta,lokacin da ta isa shiga makaranta Alh Bashir yazo ya yiwa Nene maganar ya kamata tafara zuwa makaranta ko Ka wai ta bashi yarinyar ya tafi da ita ya hadata da sa'arta Fa'iza ya sakasu a tare,Nene tace Sam bata yadda ba ,ita ya kyale ta,alokacin shi kanshi Lawan yaso Nene ta hakura ta bada D'ijan a tafi da ita abujan amma ganin yadda ta rika fada yasa ,yayi shiru da bakinshi domin dama in Nene tana rigimarta akan "yar tasa yasa yaja bakinshi yayi shiru kawai ya zuba musu ido Haka Alh Bashir ya kammalawa D'ija komai na makaranta sannan ya wuce ya tafi bayan ya tab star da ya ajiye musu komai Wanda zasu bukata D'ija ta taso da rigima gami da kwarafniya yarinya mai wayo sosai gata Sam bata barin takwana shiyasa ko a makaranta yara sa'ointa suke shakkarta ,tana da bala'in son girma kamar gyambo shiyasa Sam basa shiri da kawarta Indo sabida itama indo bata son rai ni ko kadan,kullum sai ankawo kararta Nene tayi ta fada tana cewa sun takurawa marainiya kwata kwata D'ija taqi karatu ko taje makarantar ma babu abinda takeyi sai naiman fada ,malamai duk sun San halinta,Lawan in yana mata fada Nene sai tasa kuka tace"yana nuna mata iko dan yaga "yarsa ce"haka yake hakura kawai amma abinda "yartasa takeyi yana bata masa rai Allah sarki rayuwa,D'ija na da shekara shida a duniya Allah ya karbi ran Lawan sakamakon ciwon ciki farat daya,mutuwar ta girgiza zukatan al'umma mussaman dan uwansa Alh Bashir Nene tayi kuka sosai da sosai ta fawwala wa Allah ikonshi bayan sadakar bakwai nanma Alh Bashir ya rika tausar Nene kan ta bishi abuja ganin yanzu tazama ita daya kadaici zai dameta,Tace Sam bata amunce ba ita dai ya barta a dakinta ai a kwai "yan uwa da abokan arziqi,haka alh Bashir ya tafi badan yaso ba sai Dan gudun bacin ran mahaifiyar tasa Haka rayuwa tai ta tafiya D'ija Sam taqi karatu yau in taje makaranta gobe baza taje ba ,wannan ne dalilin da yasa makarantar boka suka sallame ta gaba daya Nene tace ta nemi guri ta zauna ai ba dole bane a karatun bokon ,sai na addini,ko isilamiyar ma a makare take zuwa ,shiyasa Sam bata gane karatu sosai. To a cikin wannan lokacin Ali ya sauka garin bayan ya kammala karatunsa na aikin Soja a kasar Engila Misalin karfe shida da wani abun ya fito yana sanye da jallabiya ruwan toka tsakar gidan ya rika bi da kallo ganin ko ina a share babu datti ,tsaf iska sai kadawa takeyi gwanin sha'awa ,girgiza kai yayi ,kawai sabida dama tuntuni yasan Nene macace mai bala'in tsafta,kai tsaye kchin ya nufa ,domin bazai iya Wanka da ruwan sanyi ba kasancewar an kwana ana ruwan sama ,duk da yake mutum ne shi Wanda baya kaunar zafi ko kadan hakan bazai sa yasawa jikinshi ruwan sanyi da safiyar nan ba ,Nene na zaune kan kujera "yar tsuguno a kchin din tana joye ruwan zafi cikin fulas ,ya shiga kchin din Ta dago kai tana kallonshi , yana tsaye jikin kofa sai faman ya mutse fuska yakeyi kamar yadda ya saba Tace"ka tashi ashe ,ka ganni nan nima sauri nakeyi in kammala hada kayan karin kummalo ,sai muyi wanka domin bana son muyi tafiyar rana" Gyaran murya yayi kadan ,yace"Nene kin tashi Lafiya"? Ya share maganar da take masa "Lafiya kalau na tashi ni kam" Nene tafada tana juye sauran man kulin da tayi suya da shi cikin wani kwano Ya mutse fuska yayi yace"kina da ruwan zafi ko"? "Me zakayi dashi"? Nene ta tambayeshi kai tsaye Sabida tasan ba ya wanka da ruwan zafi "Wanka zanyi dashi naji garin a kwai sanyi" Cikin mamaki Nene tace"Yau kuma kai ne zaka yi wanka da ruwan zafi,?ashe dai karya ce kawai mutum yace ,shi baya jin sanyi da ko wane lokaci Babu abinda yace mata ,ya sunkuya yana kokarin daukar fulas din da ta juye ruwan zafin a ciki sabida yaga lokacin da take juyewa Nene tace"ai ka tsaya na miko maka ko" Shi dai bai ce mata komai ba ya dauki fulas din zai fita,tace "Muskili kafi mahaukaci ban haushi Dai-dai bakin kofa suka kusa yin karo da D'ija ta shigo kchin din ,yayi saurin ja da baya yana ai ka mata da banzan kallo fuskarshi a murtuke D'ija ma tsorata tayi ganinshi ne tsaye a gabanta ,sai jikinta yafara rawa, Saurin dauke kansa yayi daga kanta ganin kayan da suke jikinta ,riga ce iya gwiwa gashi ta kama mata jiki ,gashin kanta duk a barbaje fatarta luwai luwai , gabanshi ya rika faduwa ,sabida Allah da ya halliceshi yana bala'in son mace mai gashi mai sharp sosai fatar ta tazama kalar coffee ya lura wannan yarinyar duk ta tara abubuwan da yake muradi ga "ya mace duk da take yarinya bata gama cika mace ba amma duk ga alamu nan sun nuna Ficewa yayi yana jan tsaki ko da wasa bai kara kallon ta ba D'ija ta sauke ajiyar zuciya tana tabi bayanshi da harara ta zumbura baki , kawai ta wuce ciki gurin Nene Nene tace "kin tashi ko dube ki don Allah,kai yayi duguzun babu gyara gaki Allah ya baki gashi,amma Sam sai kice baza'a miki kitso ba" Da zaki daure sai kije gidan Delu tayi miki ko manya ne kafin mu tafi" D'ija ta karasa kusa da Nene tace"Nifa Nene bana son kitso wallahi kawai ki taje min kamar yadda kike min" Tabe baki Nene tayi tace"ai shikkenan kanki ne ,ke zai dama, ai Zumbura baki tayi gami da cewa "Ni dai ki kyale min kai na haka" Nene tace",to mai kika ji nace dake ne "yannan"? "Allah ya shiryeki Tashi tayi daga kan kujerar da take zaune ganin sabon ruwan data daura yana nai man tafasa bandaki tashiga tare da dauko baban bahon dasuke wanka tajuye wa Dija ruwan tace " kimaza kije kiyi kifito kin tsaya surutu da fadi ba,atambayeka ba kinsan in yariga fito zai zo ne ya azzalamana ko" Fita tayi daga kchin din ta nufi ban daki tana zumbure zumbure na shagwaba Ita ko Nene kayan Karin nasu ta hau dauka tana shiga dashi daki tana kimtsa gurin da zasu zauna Ali ne ya fito tsaf dashi cikin wata shadda wacce tai bala,in yi masa kyau ga sumarsa da tayi luf ta kwanta a kansa sai sheki take da ,alama ana kula da ita Idanunsa sanye da glass yayin da hannunsa yake daure da a gogo as'usuel fuskarsa kamar ko da yaushe ya shigo dakin yana bin ko i na da kallo Fuska Nene ta hau gyarawa tace " AF ashe kagama kintsawa kaga muma mungama ai ga kayan kari ai yauma mutumin naka nai ma" tafada tana gyara zama itanan lallabashi take karya botsare al halin basugama kintsawaba, bayan hakama tana so tashiga makotan nasu ta yi musu sallama ganin cewar ansaba babu dadi kayi tafiya irin wannan baka sanar da abokan zamanka ba Ya mutsa fuska yayi yana duba a gogo yace "duba time fa Nene yanzu karfe Tara har da "yan mintoci ummm"! yafada yana kallonta tare da fadin sai yaushe kike so mu kama hanya ne"? Cikin sauri Nene tace "yanzu nan ai babu abinda zanyi kuma in ba wanka ba Dija nake jira ta gama nashiga naje nai" Bai CE komai ba ya shige dakin kan kujera ya zauna yana Dada gyara link din hannun rigarsa Nene kam kunun ta hau zubamasa da zafinsa gashi sai kamshi yake yaji kayan kamshi sannan ta CE "ko in hada ma shayi ne kallonta yai yace "me kika mai da nine wanan dinma is ok yafimin wani shayi ni" amman dan zubamin madara a cikin kunun" ya fada yana dan sakin dariya ciki ciki sabida yasan sai tayi magana Ai kam harara ta gallamasa tace" baka da hannu ne zuba ma na da kanka ai gatanan kan ta rufe baki Dija tashigo dakin jikinta daure da wani karamin zani kanta duk rabinsa a jike da ruwa kai tsaye jikin siff ta nufa ta na kokarin futu da kayan da za tasa dan tun jiya da daddare ta waresu a gefe Nene tace "kin fito ba bara nashiga kafin infito sai kihada kayan karin gashinan" "To Dija tace yayin da take kokarin. Saka kayan ta kwata kwata bata lura da mutum a dakin ba kasan cewar dakin yana da girma Nene kawai tagani wacce take daura da bakin kofa,, Cire kayan ta tai tana kokarin saka wando bayan tasaka ta jawo rigar tana kokarin sawa rigar taki shiga kasancewar ta mai botora ce irin rigunan ne dogaye odar dubai wanda Alh bashir ne ya kawo musu iri daya ita f'aiza wani zuwa dubai dayayi Shikam Ali tun lokacin da ta cire kayanta yai saurin dauke kansa abin yana yimasa yawo aka domin dai wata irin hallita ya gani wacce ta bashi mamaki ,,,asace ya kara kallon gefen da take itakam sai kici kicin sa, rigar take takasa gano daga inda rigar takasa shigarta. Kallon ta yake tagefen idon sa yana dan kurbar kununsa hankali kwance aransa yace dubi ba gidajiya ko tayaya rigar zata shiga bayan bata balle botir din taba Cire rigar ta yi daga inda ta makale cikin bacin rai tai hanyar fita da rigar ahannun ta gashi daga ita sai karamin wando Ali kam ganin tayi hanyar fita daga dakin babu kaya a jikinta bai San sanda yace "keeee!! cikin sauri Dija ta waigo cike da tsoro dan batai zaton da mutum a dakin ba bayan Nene Gyara fuska yayi yana ya mutsa ta yana kallonta kasa kasa dan shikam bazai iya jurar kallonta a haka ba duk da ceawa da glass a manne a fuskarsa Cikin maganarsa da isa yace "gidan ubanwa zakije haka da riga a hannu"? domin dai shi a zatonsa zata iya fita daga gidan ahaka da nufin taje a sa mata rigar ganin cewar Nene tashiga wanka Zumbura baki Dija tayi tana kallonsa kai tsaye tace "rigar ce taki shiga jiki na bayan kuma ina sata bata ma tseni ba yanzu kuma nayi nayi ta shiga taki shine zan nunawa Nene "Dallah zo nan bakiga rigar a kwai botira a jikinta ba, bakicire botir din ba ta ina zata shiga a haka" yafada yana harararta tare dajan tsaki "bagidajiya kawai" Mika mai rgar tai tayi tayimasa tsaye a ka dago kai yayi fuska a hade yace " wuce daga kaina ni sa,an kine zaki na tsaya min aka ke ku kunya bakyaji kitsaya ahaka shashasha vileger kawai" balle botir din yai mika mata rigar yace "wuce kije can waje kisa acan" yafada tare da jan tsaki ,,karba tai ta na zumbura baki tai hanyar waje da rigar ahannuta A jiyar zuciya ya saki bayan yaga ficewarta daga dakin ,,yana mamakin yarinyan a ransa yake fadin yarinya karama da wannan dirin.jikin ina ga inta girma kuma huuuuu abin babba ne Nene CE ta fito da ga bayi taga dija na saka kaya a tsakar gida cikin mamaki tace "wai ke meyake damunki? anan kike sa kayan" tafada tana rike baki!! ,cikin kumbura baki tace "cewa yai na fito waje wai bazansa a dakin ba ,, "Ya,asalin kifito waje "? Nene tafada har yanzu hannunta na dafe da ha6ar ta! "Kai wannan yaro Allah ya shiryeshi" tafada tana kokarin daura al,wala domin dai sallar walha bata wuce ta I ta kam Dija bayan tasa rigar dan kwalin rigar ta daura ta nan nade kanta dashi ta sa wani karamin hijab sai tayi wani uban kyau ga fuskar ta tayi fayau kalar fatarta sai ta kuma fito wa,,yayinda kanta data nan nade sai yayi kamar wacce tayi a cuci irin wanda matan wananan zamani n mukeyi😀 Shiga dakin tai tace "Nene ina kika ajiye man shafawa banganshi ba " Tana kokarin tada sallah bayan tasa kayanta itama "tace gashi can gefen kujearar can" Kallon gurin tai still Ali nanan zaune a inda tabarshi gashi man sha'awar yana waje kafafunshi Shi kam Ali air fic ne mane a kunnensa bai San ma me su ke ba idanunshi a lumshe kamar mai bacci azahiri kam baba bacci yake ba music yake ji cikin wakar silendion mai taken becouse love me" shikam yana San wakokin ta acewarsa ta,iya wakokin soyayya masu ma'ana Cikin yanayinta na rashin tsoro ta nufi inda ta hangi man shafar can kar kashin kafafunsa sunkuya wa tai zata dauki man ,,yayinda shikuma ya yunkura da nufin mikar da ka fafunsa Kawai sai ji yai kamar wani Abu a tsakanin kafafunshi cikin sauri ya bude idon sa dake lumshe,,yana kallon gurin me zai gani! Dija CE a tsakanin kafarsa kamar wacce tai wa sarki karya tayi tsilli,tsilli cikin mamaki ya zuba mata idanunsa yana kallonta ,,itama shi take kallo. kallonta yake fuskarsa a hade bai CE komai ba ,, Itama Dija fuska tadan ya mutse ta zira hannuta da nufin dauko man sha'awar cikin sauri yasa kafarsa ya take hannun still idanunsa na kanta shi so yake ya San meya kawuta har inda yake Wani irin azaba Dija taji tana kokarin cire hannuta da ya take Kara mutstsika hannun yai da kafarsa ,,Dija kam jin wani irin zafin a zaba! wani uban ihu! ta kurma,wanda yai daidai da idar da sallar Nene Cikin Sauri takai dubanta gun me zata gani! kafar Ali CE a kan hannun Dija yana ta mutstsikamata hannu Cikin sauri Nene ta bige kafar tace "kai kam Ali muguntarka ta yi yawa wai ko mugunta ka je ka karanta ne"? tafada tana maka maim sa harara! Ko kallonta baiyi ba yace "kina ban mamaki Nene to taya za,ai ma tazo tashiga karkashina ni sa,anta dan ubanta ?" Cikin mamaki Nene tace" ya Asalin ta shiga karkashinka"? man shafawa fa zata dauka gashinan a kasan kafafunka" tafada tana nuna inda man yake Ko kallon gun bai yi ba Yaci gaba da duba wayarsa ,, Tsaki Nene taja tace "mugu dai baji da din halinsa ba " Man shafawar tajawo daga kasan kafarsa ta mikawa Dija dake tsaye a gun rike da hannu Shi dai bai ce mata komai ba yacigaba da danne dannensa a wayarsa. Dija kam zama tai kusa da Nene tafara shafa man. Cikin ranta kuwa in banda tsinewa Ali babu abinda take itakam bataga abin duka anan ba da ga kawai taje dau kar mai To a gurguje suka karya gaba dayansu sabida ganinin lokaci yatafi tunda har goma darabi ta wuce Kallon a gogon da ke daure a hannunsa yake sannan ya kalli Nene yace "ni ina waje in kungama mu hadu amma don Allah ku futo yanzu" Nene kam ko kallonsa batai ba sabida haushin da yabata batace komai ba har ya fice da ga dakin,, Shashen sa ya nufa loptop dinshi ya dauka da wasu tarkacen sa da yazo da su domin dai baya zuwa da kayan sawa kasancewar akwai wasu kayan nasa a gidan Fita yai rike da loptop din da sauran kayan inda ya a jiye motar sa ya nufa ya bude ta hade da bubbuge ta da rigarta ,,sannan ya bude ya ajiye loptop din tare da kayan hannunsa a set din gaba Shiga yai ya kunna motar domin dai yaji lafiyarta duu dacewa kalau take kasan cewar bata wani jima ba, Sabuwa ce da wo warshi daga karatu Abbah ya siya masa to amma kayan nasara bashi da wani tabbas Sai da yattabatar lafiyan ta lau sannan ya kasheta zama yai a ciki ya zuro kafafunshi waje yana sauraro tambihi daga malam Jafar mahmud adam To Nene ma cikin sauri takarasa 'yan kaye kayen ta sannan suka futo ita da Dija wacce ke jaye da jakar kayansu,, Wani katon kwado Nene tasa ta kulle gidan bakinta dauke d ado'o,i iri iri Gidan baba malam tashiga a gurguje tayi musu sallama sannan suka futo suka shiga gidan inna hajara wacce takasan ce aminiyar Nene ce a unguwar to nan ma a gurguje suka shiga suka fito Can gefe Nene ta hangi motar dan haka kai tsaye can suka nufa Ali yana kallon ta wowarsu dan haka ya maida kafafunshi ciki Bakin shi dauke da ado'a ya kunna motar a karo na biyu bayan ya rage sautin radi'oyn motar Nene kam murfin baya ta bude takar6i jakar ta fara turata ciki sannan Dija ta shiga ita ma ta bi bayanta,, Wani irin kamshi ne yadaki Nene ita da Dija da wani irin sanyi sanyi da motar take bayarwa mai dadi ,Nene ce ta kalli Ali yayinda ya ke kokarin juya kan motar tace "barin turare kayi a motor ne? jin irin wanann kamshi da yake tashi" Kallonta yayi ta cikin mirrow din motar yace "Nene kenan ko daya mota na haka take ke dai kawai kinji kamshi mai dadi ba irin turarki ba dan hamsin". Ya fada yana kanne mata ido daya Wannan karon dariya Nene tayi har da kyakyatawa tace "dan banza ai duk da tsofa na bazan shafa turaran naira hamsin ba ehee"! Tace "ka dai jamu a hankali don Allah kar ka fafura mu" Murmushi yayi bai ce komai ba yaciga ba da tukinsa yayinda suka fice da ga layin *To Allah y kiyaye hanya su Ali* Tuki yake cike da kwarewa wayarshi ce tafara kara kallon inda ya ajiyeta yai sunan Abbah ya gani ya na yawo a kan fuskar wayar dauka yai cikin sauri ya makala a kunnesa yayin da daya hannun yake tukin da shi yace "Abbah barka da asubah" Daga daya bangaran Abbah yace "barka dai Ali kun taho ne? "Eh abbah gamu akan hanya" yace "to masha,Allah bani Nene ,, Yace "to tare da dan waiwayawa ya mikawa Nene wayar ya ce "abbah ne Cikin sauri Nene ta karbi wayar takara a kunneta tana fadin "salamu alaikum" Cikin sauri abbah ya amsa yace "Nene antashi lafiya"? "Lafiya lau ai gamunan akan hanya ai kadai matsa bashir to bazan wani da deba zandawo kamar yadda nasaba ,tokaji"!! Abba ya ce "babu mutsala Nene Allah ya kawuko lafiya " "Ameen tace tare da mikawa Ali wayar Dija kam kwanciya tai kan jakar kayannasu tana faman daddana wayar Nene da ke hannuta game take yi da ita Shiru motar tayi in banda sautin karatun alkur,ani dayake tashi kasa kasa cikin kira,ar malam sulaiman Ahamad Tafiya tai ta fiya wanda Dija wayar hannuta har ta subuce ta fadi bacci ya kwasheta to itama Nenen gyangyadi take Ali ya na kallonsu ta mirrow din moto Dan tabe baki yayi yace "dubi wai bacci suke kamar wa,"yanda basuyi baccin dare ba tafiya bata kai ta kawo ba har za,ayi bacci" Ana kiraye kirayen sallahr azahar suka isa abuja D'ija "yar kyauye ta zama kalle kalle kawai takeyi domin wannan shine karonta Na farko da ta taba zuwa Ali yana kallonta ta cikin mudubi sai tsaki yake ja yace shashasha "yar kauye kawai Nene ta bude idonta tare da gyara zama bakinta dauke da salati ta kalli Ali Wanda yake kokarin shiga da motar cikin gidan tace"wato ina can sake da baki kana fafara gudu dani ko" Shi dai bai ce mata komai ba, can inda suke aje motocinsu ya nufa yayi parking Haruna draver tare da Malam Yahaya mai gadi suka karaso gurin da sauri suna musu barka da zuwa Ali ya fito cikin gajiya yana mika musu hannu alamun gaisuwa, Haruna murna duk ta isheshi yau yana hannu da hannun da oga yace"Haruna mun same ku lafiya"? "Lafiya kalau yallabai ya hanya"? "Alhmdullhi" Cikin barkwanci Haruna ya karasa yana tsokanar D'ija tare da yiwa Nene barka da zuwa Nene ta fito daga motar tana amsa gaisuwar Haruna cikin sakin fuska da mutumta dan Adam dama tun asali Nene macace mai sakin fuska gami da wasa da dariya, Haruna ya karbi jakkonan kayansu, yayi gaba dasu,Ali ya kalli Nene yana murmushi yace"ni dai na gama nawa aikin ko"? Nene tace "kwarai kuwa ka gama Allah mungode ma da ka kawo mu lafiy.. Kafin ta karasa sai ga su Na'ima tare da Fa'iza sun fito da gudu suna ihu ,ga Nene ga Nene ,Na'ima taje ta rungumeta kamar zata kada ita ,sai murna take,ita ko Fa'iza D'ija ta rungume tace"kawata yau gaki kinzo gudanmu gaskiya naji dadi,tun dazu nake jiran zuwanki yau har sai da naki zuwa sukul sabuda ke" D'ija ta rungumeta tana dariya tace"nima ina ta murna zanzo in ganki ,Fa'iza na Ali ko tafiyarshi yayi ya kyalesu a gurin ganin abinda sukeyi shifa ya tsani shirme, kai tsaye part din shi ya nufa ,Wanka kawai yakeson yayi sabida yadda yake jin nauyi a jikinshi ,kwata-kwata baya son zafi ko kadan Nene ko hararar Na'ima take tace"ai sai ki sake ni ko sai ki yadda ni" Na'ima na dariya tace"wace ni yadda uwar masu gida,gaskiya naji dadin zuwanki Nene nayi kewarki sosai,sabida kinzo kenan ,baza ki kuma ba" "To ai sai ki rike min kafafu ki hanani tafiya,Nene tafada tana galla mata harara Dariya Na'ima tasa ,ta kalli D'ija tace "ke wai ba zaki gaishe ni ba"? D'ija ta kalle ta tana zumbura baki tace"tabdijam ke zan gai sai tab! Na'ima tace"ni ba yayarki bace to" Zumbura baki D'ija tayi batare da ta gaida Na'iman ba suka wuce ciki gidan ita da Fa'iza sai karadin surutu sukeyi. Girgiza kai Na'ima tayi tana murmushi sabida tasan halin D'ija da tsiwa Gaba dayansu suka shiga babban falon hajiya Zainab tana khicin ita da mai.aikinsu Asabe yau da kanta ta shiga kichin din domin girkin na mussaman ne sabida zuwan Nene bayan hakama tasan Ali bacin abincin masu aiki yake ba duk da cewa Asabe akwai tsabta shikam inda ba ita ce tayi abinci ba to bayaci. Sabida yasan tes din girkin kowa shiyasa babu yadda zatayi take shiga khicin din tai mai dashi da maigidan,, sukuma asabe tayi musu nasu ,,gashi asaben ta,iya girki sosai bata da kazanta ko kadan amman duk da haka Ali bai yadda ba shikam haka Allah ya hallice shi da tsamtsami Cikin sauri Ummi domin haka suke cema ta ,tafito da ga khicin tana goge hannuta Cikin fara,a tace "sannu da zuwa Nene kunsha hanya" tafada tana zama a kujarar da,take kallon Nene "Ai kam dai munsameku lafiya"? "Lafiya lau wallahi ya mutan gida da sauran "yan uwa? "Nene tace kowa lafiya lau duk suna gaisheku", "To masha,Allah muna amsawa" Asabe ce tashigo hannunta rike da wani babban tire ,itama cikin fara,a tace "sannu da zuwa hajiya ,, "Yawwa sannu Asabe mun sameku lafiya Cikin sauri Asabe tace "lafiya lau hajiya tana kokarin budewa mata lemo Cikin fara,a Ummi ta kalli dija wacce suke ta faman surutu ita da fa,iza tun zamansu a gun "tace Dijan Nene babu magana ko? Cike da kunya Dja ta sunkuyar da kanta tace "ummi inayini"? domin itama da haka take kiranta Dariya ummi tayi tace "bazan amsaba sai. Da na roka sannan"kara sukuyar da kanta tayi tana murmushi tace "to kiyi hakuri",ummi tace" nakiyi " "Tace Nene kina jina da mutuniyar taki ko wai sai da na roki gaisuwa sannan" Dariya Nene tayi tace "ai in suka hadu da wannan berar basa ji basa gani" Ummi tace "ai kam dai" "Tace Nene kisauko kasa ma kici abinci zai fi dadi ko" tafada tana kokarin gyara gun Nene tace "me kuka girka ne"? domin dai nikam bazan iya wannan ciye,ciyen naku ba,, Murmushi ummi tayi sabida tasan hali tace "ai Nene wainar shinkafa ce sai tuwon semo sai ki zabi wanda zaki ci,, "To koda naji,samin towan kadan" "Asabe ummin ta kwalawa kira cikin sauri sai ga asabe ummi tace fito da ledar ki shimfida To asabe tace ta juya cikin sauri ta dauko ledar tashin fida a gun da suke zaman cin abinci India ba,akan daining zasu ciba Na'ima ce tace "kakus,zanci tare dake dan inkara karfin ido" "Banza, Nene tayi mata yayin da take kokarin tashi da ka kan kujerar ba ta ce mata komai ba Ummi ce ta hada wa Nene abincin daidai yadda tace ,, Sai farfesu da ta zuba mata shima ta ajiye mata a gefe. Kallon miyar Nene tayi gani wani uban nama da ta zubamata Ga,farfesu a gefe yana jiran ta sai kace wata kura Kallon ummin tayi tace "ina zan kai wannan uban abincin baya ga ha kama wanann naman miyar yayi yawa kwashe shi ki barmin uku ya isa " Cikin sauri Na'ima ta duro daga kan kujera tace "ummi zubamata wata miyar daban bara nazo naci da wannan ni" Harara Nene ta gallamata tace "to kura sarkin kwadayi ke dai kici nama har yanzu kinanan da wannan halin naki" Na'ima tace "to Nene in bake ba wazai ki nama" Ita dai ummi bata ce komai ba illah can zawa Nene wata miyar da tai Kallon N'aimar tayi tace "gatanan ki ka ra wata akai sai ku hadu da kannannaki ai kuci tare" Su dija kam hankalinsu baya gurin hirarsu suke irinta yarinta suna ta faman kyalkyala dariya,, Ummi ce takalli inda suke zaune tace "ke fa,iza haka ake ai sai ki kyale kawartaki ta ci Abinci ta huta kafinan sai kicika ta da labarin naki" laa Ummi yanzu zatazo ai kinsan mun Dade bamu haduba shiyasa" tafada tana dariya dija kam itama dariyar tai fa,iza tace "taso muje muci Abinci kinji ta rike hannun dija Gefen Nene suka zauna Ummi ta ce "Na'ima,ki dibar mu ku yadda zai isheku,, Tare suka hadu sukaci su uku suna ci suna wasa da dariya Nene,ma takan sa musu baki cikin hirartasu Ali ne ya shigo cikin sallama Cikin sauri Na'ima tajuya " ya Ali sannu da zuwa andawo lafiya? Bakin ta sai rawa ya ke itama fa,iza jiki na kyarma take gaishe shi Kallonsu yai yana nazarin su sai kace wasu marasa gaskiya Hararar Na'ima yai yace "wannan rawar jikn da kike nameye? "Babu komai ta fada hade da sunkuyar dakanta yace " ina Ummi ne? Cikin sauri fa,iza tace " ta hau sama yanzu ina jin sallah za tayi" Bai ce komai ba ya Ciro wayarsa daga aljihu n jins din daya ke jikinsa sakamokon jin kira da yaji ya shigo wayar Nene kam tace "mutum sai kace wani mala,ika daka zuwan ka Guri yara sun yi wani tsuru!,tsuru" tafada yayinda take mikewa daga inda take bayan tagama cin abincin So take taje tai sallah itama ganin lokacin sallar yana neman wucewa, Faruk ne ya kira shi Cikin jin haushi yace "wai dallah malam mene wai daga da wiwa kaki barin mutane su huta sai faman kiran waya kake,iyi? Daga daya bangaran Shima faruk din cikin fusata yace" an dame ka din kai dan rainin hankali ne wallahi ya zai,ai in dinga kiran wayar ka kaki dagawa sabida tsabar baka da mutumci " "An ki daga wayar me zakamin to zaka da me ni da kiran waya" yafada yana dan murmushi sabida yasan ya gama kunna faruk din Cikin hayaniya faruk din yace "ubanka zanma dan isa kawai" "Dallah malam kasan wannan takardun suna wajanka kasamu muna ta faman ne masu ehe? Dan dariya Ali yasaki kasa kasa yace " wane takkadu kuma? "Bayan ka zo ka kar6a saga hannuna" yana sane so yake ya kular da faruk din ta kaddun suna hannunsa Tsaki faruk din ya ja yace "ni zaka mayar wani shashasha ko Ai ganin zuwa kafito dasu dan raini wayo kawai " Kashe wayar yai ya mai da ita aljihunsa Ummi ce ta sakko.bayan ta idar d sallahr Tace "kaida waye ne kuke magana naji kamar magana sama sama. Ya mutsa fuska yayi yace "faruk ne "Au ko danaji. Yana ina tafada tana kallon falon,, "Bai zo ba waya mukai mybe kin ganshi yanzu ai akwai wasu takkadu da muka cike zai zo ya karba su" "Ummi mun same ku lafiya ? "Kalau muke" yace " wai ina jameel ne ? Ummi tace " bai Dade da fita ba kasanshi kayan bol yasa yafice ai yau sai an ganshi kuma" Shiru yai bai CE komai ba domin dai bayadda zaiyi da jameel kasan cewar sa tun yana yaro kwallo tashiga ransa yana masifar son kwallon kafa shiyasa ko wace irin bol za,a buga kallonta baya wuce shi ga musu acikin abokai sunayan "yan kwallo kuwa Babu wanda bai sani ba "Ummi.Mai kika girka min ne ? Yafa da yana marai raicewa harararsa tayi tace Babu abinda na dafa " Dariya yai yace "nasan wasa ne Ummi na CE fa,, Nasan tayi min girkinta mai dadi da gamsarwa" Shiru Ummi tayi bata ce komai ba "Kinji Ummi na wallahi wata irin yunwa nake ji please "yafada da yanayin shagwaba Su dija dake gefe kam kallon ikon Allah take ganin irin tabarar da Ali yakewa ummi sai kace wani yaro,, Ta6e baki tayi aranta tace dube shi abin ma ko kyau bai mai ba Ummi tace " ni kam Ali wanann larurar taka ta isheni wanann wane irin abu ne to in kayi aure yazakai iyi? dole dai kaci abincin matar taka domin dai kasan mu nan mun sallama ka ato"! Mikewa tayi ta nufi kchin Dija ce takewa fa,iza magana kasa kasa tace "wai dama haka wannan ya Alin yake sai yaita wani abu wai shi maitsafta yai tacewa mutane kaza mai " Da sauri fa,iza ta kalli inda yake zaune. ta kalli dija tace "ke wallahi Babu ruwa in yajiki tam" Shikam bai San me sukeyi ba domin air pic ne a kunnashi yana jin kira,a tare da shek malam sulaiman ya na masifar son kira'arsa, idanoshi a lumshe,, Ita ma dija kallo gun tai tana ya mutsa fuska bata cekomai ba ,, Tace "wai ina Nene ne? Fa,iza tace" " ta tafi sallah tashi muje muyi muma " Ummi CE tashigo da Abinci cikin wani plete Ta ajiye a gabashi "gashinan ai " Tafada tana zama cikin kujera,, Bude idanowanshi yai yace " iluv ummi na godiya nake" Kallon Cikin plete din abincin yai wata lafiyar yiyar waina ce ta shinkafa taji miya sai kamshi take gefe lemo wanda yake bala,in so da ummin take masa shi kadai zo6o ne ake mai wani irin hadi wanda ummin ce ta,iya shi Sauko wa kasa ya yi ya tankwashe kafafunshin yai bissimillah ya fara ci Sallamar faruk yai tare da shigowa sabida ya saba babu wani shamaki da gidan sabida yazama dan gida abotarsu da Ali tun da kuruciya karatu ma tare sukayi komai na su irin daya sai banbancin hali da kowa ya ke dashi ,, Shi faruk yana da sakin fuska da fara,a sabanin Ali da yake miskili na ,ajin karshe Shigowa yai yace "ummi wanan mutumin ya dawo zai farasaki wahala ko? Yafada yayin da yake zama shima a gefen Ali,, Murmushi ummi tayi tace"kai ma kafada ai faruku" Yace" ummi ke ce kike wani damu wa dashi yai zuciya ya nemo mata ai mai aure kowa ya huta sai ka wai yazo ya dinga saki wahala wallahi kidaina bashi abincin ki yayi girma da cin abincin gida,ehe" Dariya ummi tayi tace "wai baka mai fada ne shi baya ganin kai har ka haihu ko zuciya bayayi ba shima ,, Yace "ummi kuka tsaya wani lallabashi me ake jira wai tunda da matar a hannu mun she da sai kawai a shafa fatiha in yaso takarasa karatun a dakin nata ita siyama n,, Wani irin kallo Ali yakewa faruk din yana faman harararsa Shikam faruk dariya ya kara kecewa da ita sabuda yasan ya gamma kunna Ali ,,a sabili da yasan ya tsani ai mai magana siyama,n Faruk yace "kinga bamu gaisa ba ma Antashi lafiya" tace "lafiya lau ya hjiya binta " yace "tanan lafiya lau wallahi,, Nene ce ta fito daga wani daki acikin falon bayan ta,idar da sallah kwanciya tai tana lazimi sai taji surutu yai yawa ita a tunanin ta ko jameel ne Zama tai da carbin a hannunta tana kallon faruk tace "au! ummaru kai ne ka zama haka" tafada tana rike bakinta dariya faruk yayi yace "me nazama kuma nene,, dan sun saba da nene sosai tunda shi mutum ne mai yawan wasa da dariya shiyasa duk sanda nene tazo garin sun dunga fafatawa kenan,, Tace "kazama wani burgujeje haka aikin sojan ya mai dakai iyi" Dariya yai yace "nene kenan wace irin tsaraba ki kawomin ne? "Wace tsaraba, wancan yabari mukayi yabi yadaga mana hankali wai ana neman ku gurin aiki ,, "Aikam dai wallahi kinsan yanayin aikin namu wani aiki zamu fita muyi gobe shine dalilin da nai mai waya yatawo" Nene tace "ai kuna kokari aikin ku akwai hadari sai dai muyi ta tayaku da ado,a Allah ya tsare mana ku "Ameen ,Ameen yace "nene kunzo lafiya Ya aka baro "yan uwa "?? "Kowa lafiya lau wallahi ya iyalin naka"? murmushi yai "yace sunan lafiya lau ai zan kawu su ku gaisa kan ki koma " "Ai da ka kyauta kuwa ". yace " insha Allah" Ummi ce tace" ai nazata bacci ki kayi da naji shiru ,, Nene tace "ko daya baccin yaki zuwa kwanciya nai ina hutawa wallahi , wai ina jameel ne"? Ummi tace "ai bai dade da fitaba yagama zaman jiran zuwanki ganin har daya tayi baku karaso ba shi ne ya fita kuma Bai dade da fita ba kuka karaso,, "AF ko da naji" Nene tafada tana kallon Ali da yake cin Abinci tace "kai kam haka ake babu tayi kayiwa mutane shiru iyi? Banza yai mata faruk ne yasaki dariya yace " nene kenan ki rabu dashi ai akan an mai magana shine yake ci wa mutane magani Aure kuwa mutum sai an masa, ko yaki ko ya so" Nene tace " au ! maganar aure ne baya so tafada tana rike baki Ummi da tun fara maganarsu bata samu su baki sai yanzu tace "ke ma kyafada nene" Kallon Alin nene tayi tace "ina ce akwai matar a hannu to me ake jira ehe" Shidai bai ce mata komai ba cin abincin sa yake cikin kwanciyar hankali, "Ko akawo ma abincin ne faruk "? "A,a ummi alhmdulilah wallahi kinsan da zanci bazan tsaya wani sai an tambayeni ba" "Tace nasani ai naji kai shiru ne ai shiyasa na tambayeka" Ali kam tashi yai daga gun bayan ya kammala cin abincin,, Canja gurin zama yai ya zauna yana dan ciccin magani fuskar sa a hade Da kallo nene tabishi dashi tace" haka dai sai dai aci a bar kayan a gun aci ai tusa kai ko kunya bakaji abokin ka har da da kai ka zauna kana faman iyayi " Wallahi kamar kinsani duk cikin abokanmu shikadai ne yai saura amma duk muna d aure,, "Rabu da shi ummaru nasan abinda zanyi bari abban nasu ya dawo in ya so sai inji me ,akatsa Ya jira " Kansa dake sunkunye yana faman latsa waya ya dago yana hararar Nene fuska a ya mutse yace "mezakiyi to? "Sai kaji abinda zanyi " "To wai ke ina ruwan ki ne iyi" ya fada ya na kallon ta "Da ruwa na ehe me kake nufi sai muzu ba maka ido ko to baka isa ba tunda kungama sasanta kanku kai da siyamar to gwara ai a gama" Kallonta yai yace "wayace miki mun sasanta kanmu ehe? "To wai ma ni nataba cewa ina son siyama ne da kuke ta wannan abin ya fada yana kallon ta Baki nene tasaki tana kallonsa tace "au! Mu zaka kamayar kananun mutane iyi Ali" Dariya faruk yayi yace" karya yake nene. Yana sonta yana san dai yai wasa da hankalinku ne" Wani duka Ali yakaiwa faruk yace " wallahi zanci ubanka mara mutumci " Cikin sauri faruk ya kauce yace "au dan nadafadi gaskiya shine har da duka" Cikin Hayaniya Ali yace "dallah malam kai mana Shiru wallahi ko,in ballo ma ruwa kai kasan a inda zan je inyi dan iska kawai" Tsaki ummi tayi tace" kana da aiki Ali wa kake so ka mayar karamin mutum iyi"? tafada tana kokarin tashi d ga gun Umm !! "ke ma dai kya fada inji nene" itama tana kokarin barin gun ganin lokacin sallahr la,asar yayi tace" ai kamar ka auri siyama kagama. tokaji"!! Wani Kallo Ali yakewa faruk bayan nene tabar gun,yace "wai kai wane irin dan iska ne ehe. Haka kawai za kazo ka 6allo min aiki" Dariya faruk Yayi "yan isa ka biyu dai ni da kai nizaka kashewa waya dan rainin hankali kawai " "Malam ina takkadunnan Iyi? Banza Ali yai masa sai da ya kara maimaitawa sannan yace "sai katashi kaje kaduba d kanka " "Wallahi sai Nafisa taji labarin Mufida tunda baka da mutunci " "To taji mana angayamaka tsoranta nake yi ko an ce maka ita kadai zan aure" Ali yace "haka kace ko? "Eh man" Wani murmushi Ali yasaki yace" zakaga aiki da cikawa wallahi banza mayen mata aure ko shekara biyu bakaiba har ka soma hange" Cikin sauri faruk yadawo ya zauna yace. "Rufan asiri wallahi bana iyawa da masibar Nafisa don Allah kar kafada mata wallahi inta ji shikkenan na dai na bacci kishin bala,i ne da,ita" Dariya Ali yai yace "me kagama cewa dazu iyi"? Faruk yace " me nace kuwa ai bakarya nayi ba yaza,ai kadinga yaudarar yarinya alhalin tasaki jiki zaka aure ta kowa ya shaida sannan kace bakasan zancan ba" "Nida bakina na ta ba ce maka zan aure ta?" "Sai kafada meyasa tun farko abun ba kafada ba sai yanzu d magana tai nisa kace bakasan zancan ba ai kasan wa sane" "To dan ubanka sai ka aura min ita tunda kai kahaifeni" Dariya faruk ya kece da,ita yace "to wai mekake nufi ne da kaketa wani hanya hanya ne ,,kasan dai yarinyar nan bakowa take kulawa ba sabida kai sai kafadi dalilin da yasa zakace bazaka aure taba" Cikin yanayinshi kamar koda yaushe yace "ba taimin ba shine dalilina" ya mutse fuska "Baka,isa ba wallahi" inji faruk, Cikin mamaki Ali ya kalli faruk yana mamakin rantsuwar da yayi yace " au rantsewa kake"? "Eh inji faruk banga dalilin da yarinya zata bata lokacinta ba sannan daga baya wata magana ta faru bayan kasan wannan zai zubarwa da Abbah kima da mutunci acikin abokai dashi kansa maihaifin siyamar wannan zai iya jawo zumuncin nasu yayi rauni Dan haka wannan maganar ma ka,ajiyeta a gefe Sam bata,taso ba" yakare magana yana mai da nuffashi. Kallo sa ya ke yace " to dakake wani tada jijiyar wuya dole zakaimin ne ehe" yafada fuska a hade "E dole za,ai maka tunda kai bakasan daidai ba" Wani murmushi Ali yayi yace "na bar maka kaje kai tabiyu da ita tunda da ma amatse kake da mata dan iska kawai" Harararsa faruk yai yace "eh naji laifine dan naso mata ai su ababen a so ne" "Kar kai tunani bansan halin dakake ciki ba da irin magungunan da kake karba a gun Dr Hashim dan iska jarabbabe ai kai mata Biyu ne suka dace dakai domin mace daya bazata iya daukarkaba " Duka Ali yakai mai yace "wallahi zanci ubanka har nakai ka " "To kar ya aikai maka" faruk yafada yana barin gun yace "dallah zo ka dauko min takkadun inkama gabana" Banza Ali yai mai yacigaba da duba wayarsa "wai ba magana nake ba bafanasan raini hankali kasan nawa halin inyatashi " Mukulin shashin nasa ya jefa masa yace "malam kar ka isheni kadauka kaje kadauko da kanka mana " "Daba a hannunka suke ba meye na da womin da su iyi kabi kazo kadamu mutane" Kwafa faruk yayi bai ce komai ba ya dauki key din dakin yai fita sabida yasaba da halin sa a zuciyarsa kuwa shima shiyasan abinda zai kyokyoyamishi na rashin mutunci Shiru falon yayi inbanda Ali da yake zaune yana fama d waya,, Su Dija ne suka fito itada fa,iza suna faman kyalkyala dariya kwata,kwata ba su lura da mutum a gun ba sai da suka zo tsakiyar falon sannan dija ta ankara ,,tsaya wa tai tana gyara fuska fa,iza kam kai tsaye tibi ta je ta kunna tace " yanzu za,afara amma maimaici ne sai kokarin neman tashar a rewa 24 take ,, Ita dai dija batace komai ba tana nan atsaye a gun,, Jiyoyawarwa da zatai bayan tagama kunna musu kallon me zata gani ya Ali ne a zaune yana kallonta da fuska a murtuke Cikin sauri tace ya ali anyi ni lafiya? "zo nan" ya fada batare da ya amsa gaisuwar ba jiki na kyarma taje ta zauna a gefenshi yace "me nagaya muku iyi"? Shiro fa,iza tai tana zare ido yace" badake nakeba dan ubanki " "Imm dama kace mudaina yawan kalle kallen da muke" Wani rankwashin ya kaima ta cikin sauri fa,iza ta rike kanta "Bayannan fa? Iyi " yafada yana kallon dija dake tsaye har yanxu a,inda take ,,hararar ta yai yace "tsayuwar uban mekikewa mutane anan gun? Cikin tsawa yace "zo nan" Kallon sa tai babu digon tsoro ko kadan a fuskarta ita mamaki mata tsaya tana yi ganin irin rawar jikin d fa,iza take yi,, "Bada ke nake ba ko sai nazo nayi kulikulin kubara dake anan " cikin rashin tsoro taje itama ta zauna kusa da fai,za tana dan zumzum bura baki itafa bazata yadda da haka ba ya bar ganin anzo gidansu ta fada a zuciyatta Kallon ta Ali yai yace "ina dan kwalinki" ? sai sannan dija ta tuna ta cire dan kwalin ta tun a dakinsu fai,za "Yana daki" tafada idanonta atsaye a kansa, "Tashi dallah kije ki dauko nan bagidan ar'na bane ,,kika yadda na kuma ganinki babu dan kwali sai nayi miki aski wallahi" Zare ido fa,iza tayi tana kallon dijan tana dan zungurinta da kafarta alamr tatashi taje ta dauko dan Ali zai iya yi mata asikin bakaramin aikin shi bane Itakam in yaiwa dija aski ai ya cuceta a yanda take da gashinan a,zuciyar ta take cewa ina ma ita take da gashin da dija take da shi da an ga iyayi, Tashi dija tayi ta nufi dakin tace "wallahi bazan dawo ba ai ba ubana bane kai sai kadinga ta kurawa mutane "Je ki kiramin Na'ima" yafada yana kallon fa'iza bayan dija tashige Tashi tai jiki a sanyaye tace yau mun shiga uku dakin nasu tashiga ,, Na'ima na kwance bacci take yi "yaya Na'ima kitashi "ta hau bubbuga gadon cikin bacin rai Na'ima ta bude ido " wai meye ne "tafada tana hararar fa,izan "Ya Ali ne yake kiranki " Kallon fa,izan tace" me ye ? "Nima bansani ba ya ce ne kizo" tashi tai tana fadin "wallahi kika jawomin duka akan kin zan rama domin dai ni nasan ba abinda nayi tun tafiyarsa a to" Zumbura baki fa'iza bata cekomai ba ta kalli dija dake zaune tana duba hoto nan su tace "shine kikaqi dawowa ko? "To me zanyi in nadawo iyi" tafada tana tabe baki Bata ce mata komai ta fita daga dakin Na'ima ma barin dakin tai sukabar dija ita kadai Yana zaune inda yake sabanin dazu shida jameel ne yanzu shima da wowarsa kenan Kallonsa Ali yai yace" wato kai bakaji ko"? "Bro menayi" inji jameel din Hararasa Alin yai yace " ban sani ba yanzu a war mu nawa da shigowa garin ehe kafita tun safe ,,wai kai a kwallo zaka kare ne"? Sun kuyar d kai jameel din yai ya ce "wallahi bro wannan mezafi ce shiyasa kasan mune shugabbani shiya sa gobe ma zamu fita,, Kallon sa Ali yake shi ga maganar da yakeyimasa amma yana sako wani zancan daban kwafa yai yace " lallai jameel yayi nisa " Kallon su Na'ima yai yace " ke Na'ima mena fada mu kafin inje kano? "Wato ba kwajin magana ko"? Cikin inna,ina Na'ima tace "wallahi bama fita in dai ba makaranta zamu ba ko gidasun siyama katambayi ummi ma kaji" "Wallahi ku kiyayeni, ban hanaku kallon ba amma ku tabbatar babu wani abu wanda yashafi harkar karatun kar kusa shi a cikin shirmenku wallahi uban mutum zanci ni" Nene ce ta fito daga dakin tace " kamar maganar dan gida na nake ji" Dariya jameel ya ke yace " a,a uwar dakina barka da zuwa" Kafin takaso har yatashi yaje ya rungometa. Yana dariya Ita ma dariyar take tace "mai gida babu awo babu ce fane wai kai haka ake auran ne" Tafada tana zama a daya daga cikin kujerun da suke falon Yace "kece ai ba ai miki gwannita ,,yanzu me kike so? "Babu amma jeka nemo min fura da nono " to jameel yace kin samu yanzu za,a kawo ".ya fada yana kokarin barin gun wanka yake so yai har ya fita ya dawo yace "wai ina wannan "yar kauyan yarinyar ne ko bada ita kikazo ba "? Harararsa nene tayi tace "e" Dariya yai ya fita dan yasan fada tai kawai yasan nene bazata iya tafiya mai nisa irin wannan batare da dijanta ba Kallon su Na'ima tayi wa "yanda sukai tsorutsoru a gaban Ali ko motsin kirki bau wacce take Shikam Ali hankalinsa baya kansu kallon sa yake bayan ya canja tashar da Fa'izaa ta kama Labarai yake saurara a tashar aljazeera,, "Ku kuma meye haka , sai kace wasu masu nai man gafara " tafada tana rike ha6a Shirou sukai babu wacce tayi maganan acikinsu,, Kallon Alin nene tayi tace "miskili kafi mahaukaci ban shaushi kenan,, "Wai me suka yima ne" ? Banza yai mata haushinta yakeji yasan tunda tace zata gayawa abba maganar siyama sai tafada yasan halinta da tada zaune tsaye kawai zatazo ta dama mai lisssafi,, Sai da ta kuma mai maitawa sannan yace "Meye ruwanki to " yafada still idansa na kan tv "Da ruwa na wannan cinzali ne ai , ya zaka zaunar da yara guri guda ka hana su motsi sabida mugunta, ai ba sojojin ne su ba ko masu laifi ballanta kai musu irin wannan horan" Kallon Fa'iza nene tayi tace "ina dija n take ? "Tana dakinmu " " tashi kije ki ki ra wu min ita Kallon Alin tayi yana kallonsu ta gefen idon sa bai ce ko mai ba A darare ta tashi ta nufi dakin nasu tare suka shigo ita da dijan kai tsaye inda nene take ta nufa ta zauna kan hannun kujerar da take kai Fai'za ma kusa da nenen ta zauna dija tace "baki baccin ba nene "? "Yau she zan iya bacci yanzu ai yamma tayi " Kafin ta rufe bakinta ummi ce ta sakko daga sama tana kwala a sabe mai aikinsu kira ,, Kallon Alin Ummin tayi tace "au kananan ashe ba ka fita ba? "Eh nadan tsaya sauraron labarai ne" Bata ce komai ba tane mi guri ta zauna tana kara gaida Nene Asabe ta shigo cikin sauri tace "gani hajiya" Ummi ta kalli Nene tace "meza,a da fa miki ne? "Da ni kuke tambaya iyi"? Nene tafada tana kallon ummi "A,a nene wai ko kina sha,awar cin wani abin " "A,a duk abinda aka dafa zanci bana son tsurfa daga zuwa za,tsiri tambayata " Dariya ummi tayi tace" Nene kenan" Kallon asaben tayi tace "kije ki shirya abincin yadda ya kamata" "To" asabe tace ta bar gun Canja tasha ummi tayi zuwa mbc,maxx Wani shiri suke nunawa na kiwon lafiya ,, Na'ima tace "don Allah ummi mayar mana arewa mukalli dadin kowa duk da cewa sun kusa gamawa" "Ba maimaici suke ba yau"? "Eh ummi ai bamu kalla ba duka ba" Ba tace komai ba ta mayar musu da shi arewa Tsaki Ali yayi kasa kasa ya mike yace " ummi nafasa fita sai anyi magariba zanje in dan kwanta" yafada yana kokarin barin gun "Aikam dai da yafi tunda faruk din yazo gwara ka huta zuwa an jima "tafada tana kallonsa, Yace "ai haka za,ai sai yanzu gajiyar take damuna wallahi ,, "To ai dama dole " Kallonsa nene tayi yayin dayake kokarin barin falon "Ai gwara daka tashi daga gun kazo ka kankane kamar wani kai ne mai gidan sai faman mulkin mallaka kakewa mutane,, Dariya yayi kadan "yace kanki akeji " Ya fita daga falon shashesa ya nufa yattada key din jikin kofar budewa yai yasan. Faruk ne ya barshi yana ganin asarar mayar mai dashi Zama yai gefen katuwar katifar dake dakin yana kokarin balle botoran rigar dake jikinsa ,, Kwanciya yai rigingine ya daura hannayenshi saman goshinsa Tunanin. Maganar dazu yake dasukai da faruk gaskiya shi kwata,kwata siyama ba taima sa ba bayajin sonta ko daya a ransa sai irin na addini isilama To amma maganar faruk abin duba wace tunda hakikanin gaskiya siyama da iyayenta sun saki jiki zai aureta dasu kansu Su Abbanshi da ummin To amma babban abinda suka kasa ganewa game da shi baya ra,ayinta tunda shida bakinsa baita6a gaya musu yana sonta ba ita take haukanta har suka fuskanci hakan ta bangaranta To shikam mutum ne da yake girmama mai kaunarshi baya ga hakama bashi da ra,ayin wulakanta mutum ballanta me kaunarsa shine abinda yake dubawa yakasa furta wa da bakinsa baya ra,ayinta ,, Shiru da yayi shiya basu karfin gwiwar kamar shima yayi na,am da abun Gaskiyar lamari babu wannan a ransa ,,shifa har yanzu bai ga macan da tai mai ba wacce tatara abubuwan da yake so ba Duk da cewa akwai tarin "yan matan dasuke karakaina akansa to amma su dun ma akwai matsala dan duk macen da tayi ma tallan kanta to tabbata bata da kamun kai Shiyasa yake musu kallon dai-dai Shikam bashi da mafita a wannan lamari zai iya auran siyama sabida irin kaunar da take nunawa a gareshi to amma kam. Zai yi aure in yasamu dai dai dashi,, Wannan shine hukunchin da ya yanke ,, To a can falo kuwa yaran samun sakewa sukai sabida dodon su ya bar gun ,,kallon su suke cikin raha suna dariya ,,nene ma takan sa mu su baki cikin surutun nasu Abbah ne yai sallama Hannu shi rike da wa yoyinsa bayanshi kuwa salmanu ne rike da jakar abban da sauran ta muhiman takaddunsa ,, Cikin ihu Fa'iza ta tashi taje ta dane shi "abbana sannu da dawowa "shima cikin dariya ya rike ta yace Fa'iza n abbah ya gida? "Lafiya kalau abbanmu" Rike hannusa tayi suka jera har inda nene take Zama yai a kujerar da take fuskantar nene "Sannu da zuwa nene kunsha hanya ko"? "Yawwa sannu aikam dai mun same ku lafiya?" "Lafiya kalau nene yaya su baba malam da sauran "yan uwa?" Nene tace " kowa lafiya lau suna gaisheku da kyau,, Yace " ai inata saurin in fito daga officee da wuri sai ga baki nayi wallahi naso in dawo da wuri ,, "Ai gwara daka yi zamka ka tawo a nitse tunda ba tafiya zamuyi ba " "Hakane" Ya fada yana kallon dija yace "zo nan doghter " Kanta a sun kuye taje tace "abba inayini munsame ku lafi,a? "Lafiya lau dija ya karatunki " ? Yafada yana sata a jikin shi yana bala,in tausauyin yarinyar kasan cewarta marainiya batasan iyayenta ba. Shikam dan dai nene tafi karfi shine amma da babu dalilin da dija zata zauna babu cikakkiyar makaranta wallahi ya kewa yaran wasu ma ballantana wannan daya ke jin kamar shine ya haife ta Itama dijan kwanciya tai a jikinshi ,tace " abba karutu alhmdulilah" Na'ima dake gefe tace "abbah ni an manta dani ko? Tafada da yanayin shagawaba. Murmushi abbah yayi yace "nina,isa zo nan mai babban suna nimatullah ya fada yana mika mata hannu shi Cikin dariya taje itama tace "abbah an dawo lafiya ya fama da jama,a? "Alhmdulilah mun gode Allah " Nene kam baki tasaki tace "o ni "yasu "! "Haka ka ke wa yaran nan bashir iyi "? dariya abban yai yace "menayi musu nene "? "Yo ai duk abinka mata ne ko wacce aure zakai mata ato in banda abu irin na zamani ai mu bama kallon "yan yanmu mussaman nafari" Murmushi abbah yayi sabida yasan za,a rina yasan halin nene duk da itama fada kawai take domin itama tana da bala,in son yayanta dan dai tana da kawaici ne kawai Yace "shine dalilin dayasa nake jansu a jiki ai nene ganin basu da wani sai ni gashi ko wacce miji ya na zuwa aure zan yimata " Dole in tausaya musu,, Yafada yana kokarin tashi daga gun yace "nene zanje inwa watsa ruwa magariba ta na neman yi " "To a sauko lafiya" nene tafada hankalinta na kan tv da suke kallon Ummi ce ta fito daga khicin tace " naji kamar abban yara ya shigo ko? "Eh yanzu ya hau sama " Itama saman tabi shi cikin sauri ,, Yana shiga dakin itama tashiga "Sannu da dawowa abbah" Juyowa yayi yace " yawwa dama kina kasa ashe "? Tace "shiga ta khicin kenan naji shigowar ka" An dawu lafiya? "Lafiya lau "ya fama da hidimar mu" yafada yana mata murmushi "Alhmdulilah Abbah ai akin lada ne" tafada tana kokarin Shiga toliet tasan wanka yake son yi Ruwa ta hada masa tafi to mai da duk abinda zai bukata Sannan ta fito yana zaune gefen gado yana cire a gogon dake daure a hannusa tace "abbah an hada ruwa wanka jikin sef din dake manne a bangon dakin ta nufa ta ciro mai jallabiya mai yankaken hannu ta a jiye a gefe. Yace "sannu uwar gida uwar Aliyu haidar zakin fama, Yafada da murmushi a fuskarsa ,itama murmushin take tace" abbah kenan" Yace "akwai magana ne " "ehe ai gaskiya na fada dariya tayi tace" to wa yace ma kayi karya" "Yawwa akwai maganar dana keso mu tattauna zuwa anjima game d Aliyu ne" Kallonta abba yayi yace "wani abin ne?? "A,a akan maganar siyama ne?" Tafada tana kokarin barin dakin sabida ta daura musu Abinci shida Alin tunda bata yadda yaci na asabe wannan tsarinta ne Bai ce komai ba shima ya mike yashege toliet din Sakkowa ummi ta taddasu suna zaune har yanzu tace "Na'ima bakuji Kiran sallah bane yakamata kutashi haka " "Eh ummi yanzu zamu tashi ai" "Ba ruwana wallahi Ali ya fito yattada ku anan kar wacce ta nemeni" Ummin tafada tana kokarin shiga khicin Cikin sauri Fa,iza ta tashi. Tace "ai kam dai dan dazu nene ce ta cece mu. Daba dan itaba da sai munsha rankwashi ko ya murmurde musu hannaye haka yake musu in suka yi wani abin Tace "Dija muje muyi sallah ko" Tashi dijan tayi tace "muje dakin nene muyi a can" Kai tsaye dakin da nene take suka nufa Ita kam Nai,ma tanan zaune to bata sallah prieod take sabida haka zama ta gyara wayarta ce a hannuta nema layin siyama take sai ace busy Tsaki tayi a karo na biyu ta kara gwada kiran wayar "Hello Siyama" Daga bangar siyaman itama tace "ya akai ne kanwata " tafada tana dariya dan tasan Na'ima n ta tsani ta ce mata kwanwarta Cikin bacin rai Na'ima tace "wai ke dawa kuke waya ne tun dazu nake kira busy" Dariya siyama tayi tace "Wata friend dina ce wallahi iyabo damu kayi skull tare " "Ok. Ya Ali fah yadawo dazu" Ihu !! siyama tayi tace "da gaske kike? "Ba yace sati biyu zai yi ba" ? "Eh wani aiki ne yata so musu ya zama dole sai dashi shine dole yadawo tare ma suka tawo da nene" "Kai sistar naji dadin labarin nan naki wane tukwici zan baki?" Dariya Na'ima tayi tace "kedai kin shiga uku akan namiji kike haka wanda bai san ma kinayi ba" "To ya zan yi Na'ima Allah jarrabeni da son yayanki shikam naga kamar baya ra'ayina" To itama Na'ima tasan gaskiya siyama tafada ya Ali baya ta tata sabida haka cikin rarrrashi tace "ki kara hakuri komai zai yi daidai kinsa ya Ali al'amarinshi sai shi wani baudandan mutum ne sabida haka ko yana son ki baza nuna ba" "To ya zanyi don Allah kidinga shigar dani a gunshi kinji sistar na " siyaman tafada cikin kwantar da murya Dariya Na'ima take tace "rufan asiri in mutu maza su kaini" "Wai ance wargi ma guri shika samu ke dai din da kikaga zaki iya bissimillah mu dai. "Yan addu'a ne" Daga daya bangaran siyama tace "haka zamuyi dake ko?" "Ai anyi angama ma wallahi bazaki sani a jarfar ya Ali ba a yanxu ma ya , aka kare Kizo kici gaba da kafa gwamnatinki ko Allah zaisa a dace" Ka she wayar Siyama tayi tace "mara mutunci nasan ta inda zan bullo muku da ku da ya Ali" Kai tsaya dakin Momyn ta ta nufa ta tadda ita a zaune gefan gado tana waya da kawarta hajiya ladidi, ta zube kan bed din tana sauke nuffashi,Momy tayi saurin kashe wayar tana kallon "yar tata tace"ya aka yi ne naga kin shi go kina bacin rai ,nifa na tsani in ganki cikin damuwa my daughter" Siyama ta mike zaune tana ya mutse fuska ta ce "Momy kinji ya Ali ya dawo ko ,yanzu wane shiri za muyi"? Momy ta aje wayar kan mudubi tana kallon "yar tata tace"ai tashi zakiyi ki shirya ki cancada kwalliya ta ban mamaki ki dira a gidan domin naga yaron nan in ba haka mukai masa ba a kwai Matsala na lura yana da taurin kai" "Humm! Wallahi momy har narasa yadda zan bullo masa duk wani dabaru na a kanshi sun kare"Siyama tafada tana tausayawa kanta "Ai baza mu yi kasa a gwiwa ba ki ci gaba da kokarin a kanshi ,in yaqi zamu bullo masa ta bayan gida kawai,tunda shi yace dan taurin kai ne" "Yawwa momy dama haka kukayi masa wallahi domin zuciyata tana azabtuwa da so da kaunarsa ,shi ko nunawa yakeyi kamar bai damu da ni ba" "Ai yanzu nan muka gama magana da Hajiya ladidi a waya tace min tana kan hanya ,zuwa nan, zamu shirya yadda komai zai zo mana cikin sauki" Farin ciki ya lullube Siyama ta rungume Momy nata tana fadin "shiyasa nake sonki momcy na wallahi sabida kina son abinda nakeso" Dariya Momy tayi tana farin ciki ganin diyar ta tana farin ciki tace"ai duk inda zan shiga in fita zan shiga ,domin in ga kin auri yaron nan ko da zanyi yawo tsirara sai burinki ya cika ,kuma da ke kadai zai zauna babu kishiya ,kamar yadda nake zaune ni babu kishiya" Siyama ta riqa murna tana ganin burinta ya kusa cika zata auri gwarzon maza Aliyu zaki mazan fama ,mutukar ta aureshi tasan ta gama dacewa,kuma tasan halin momynta inda tace zatayi abu za tayi Sabida haka mikewa tayi cikin qwarin gwiwa tace"Momy bari naje na shirya kawai na tafi" "Yawwa dota kiyi sauri kinji ko kiyi wanka sosai yadda zaki dauki hankalinshi" Dariya Siyama tayi lokacin da take kokarin fita saga dakin momyn nata,tace"sai momyna wallahi Allah ya bar minke" Momy ma dariya tasa tamkar wata ma haukaciya Cikin wata atamfa ta fito da gani a tamfar mai tsada ce sosai, amma dan iskanci anyi mata wani mutsiyacin dinki ,wanda ya fito da sassan jikinta ko ina gashi nan mussaman kirjinta duk sun bullu tso ta saman rigar ,da ta daga hannu hammatar ta a waje sket din ya da meta sosai ,kanta ya sha karin gashi kafarta sanye da wani takalmi mai tsayi ,ta fito hannunta ruqe da key din motarta sai karamar jakarta pose sai taunar cingam take klas!kas!las! Cikin farin ciki Momynta tace"gaskiya kinyi kyau my douhter ,kin ga yanzu ko shi waliyi ne dole in ya kalleki ya kwadaitu dake ,dama nasan yarinya ta bata wasa ba ce" Siyama sai dariya takeyi cike da farin ciki yadda momynta take kwarzanta kyawunta Har har waje nomyn ta rako ta sai daga taga motarta ta fita daga gidan sannan ta koma ciki tana tafiya tana magana ita kadai tamkar wata shashasha lokacin da siyama tashiga gidan ana tafaman kiran sallahr isha'i bayan baba mai gadi yabude mata get din kai tsaye danna hancin motar tayi cikin far fajiyar gidan Tana kokarin gyara faking shi kuma Ali fitowarsa kenan da nufin zuwa massalaci Hannu makale da carbi irin mai dannawa nan kallo daya yayiwa gun ya fahimci motar siyama ce Tsaki yaja ya wuce aransa yace wannan yarinyar bata da hankali meya kawuta da wannan daran oho Mikawa baba mai gadi hannu yayi suka gaisa ya ce " Abba yafito ne? "Eh ai bai shigo ba yana jiran ya sallaci isha ne kasan cewar tun fitarsa sallar magariba bai shigo " Bai ce komai ba shima ya nufi ma sallacin Ita kam siyama ta ga lokacin da ya fito sai taji wani bala,in tsoro da fargaba ya kamata kasan cewar taga ko kallo bata ishe shiba Cikin sanyi jiki damutuwar jiki fito da ga motar jikinta a sanyaye ta nufi cikin gidan,, Duk suna zaune. A falon har jameel ana ta hira sai dariya ake Dija tana zaune kan hannun kujerar da jameel yake zaune sai faman nuna mata hotona yake a wayarsa a cewarsa "yan matansa ne ita kam dija so take ya bata wayar yaki ya bata tana bala'in son babbar waya kasan cewar ta nene karama ce ,, bata da game masu yawa shiyasa duk inda taga waya sai tace abata tayi game Sallama siyama tayi bayan tashiga falon Ummin ce ta, amsa tace "Aa Siyama kece da wannan daran " ? "eh wallahi ummi " siyama tafada yayin da ta ke kokarin zama a kusa da Na'ima Dariya Nene tayi tace "au biyo sawo kikayi sabida kinga yaki zuwa ko"? "To duk abinki nice dai ta karfen sai na ga damar barinsa yaje ehe"! Dariya siyama tayi cikin kissa tace " dama wace ce ni inja da uwar gidan Aliyu ai nima sai yadda kikayi dani" Nene tace" eh "yar nema abaki ba ai nasan zuciyarki tananan tana zafi na hana shi zuwa" Dariya Na'ima tayi tace "me ya Ali zai yi da ke da kai duk fur fura ai shi sai yarinya sabon jini" Cikin kissa siyama tace "ai fur fura bai wace wani yayi mana" Hararar Na'ma Nene tayi tace " ke kuma waya sa dake"? "Sai ansa dani " Na'ima tafada tana dariya Dariya Siyama tayi tace" babu ruwanki sistar wannan abinda ya shafi kishiya d kishiya ne ", Ita kam umma tana zaune tana mamakin siyama da,ita da budewar idon ta gata a zaune ko kunya bata ji ta ke wannan abin lailai zamani wasu yaran basu d kunya,, Siyama takali ummi tana sinqe kai wai ita nan kunya tace " bamu gaisaba bama Ummi ina yini"? "Lafiya kalau siyama ya momy n taki "? "Wallahi tanan nan kalau tace ma a gaisheki wai kwana biyu ba ko haduba" "Ai kam dai ai momy taki ce bata da kirki ba ta ziyara" Dariya siyaman tayi idanonta akan jameel Tace" kai na karfe abun ma babu magana" Kallon ta jameel yayi Ya tabe baki yace "ni dake waye zai gaisar da wani iyi"? "Kai ne" Siyaman tafada tana murmushi domin dai tasan tun tuni jameel baya kaunar ya ga tazo gidan ya dinga harararta kenan in ba,ita ce ta kulashi ko za,a shekara bazai mata magana ba Yace "zaki dade a gun kenan in dai ni kike jira na gaisheki" Itama bata ce komai ba a fili acikin zuciyarta kuwa tace zakaci ubanka kai ma Nayi lis dinka a black book tun da dan adawa ne kai ma" Kallon dija tayi wacce take zaune kamar ta shige jikin jameel din Tace "ummi kunyi ba kuwane "? "Dija ce fa ta nene baki gane taba? "La,a wallahi bangane ta ba kinsan bantaba ganinta a fili ba sai hotonta na sani Haba shiyasa na ga kamar tana yanayi d ya Ali" Kallonta dija tayi aranta tace amman wannan kin cucuni ni ce ma nake kama da wacan mutumin tab dijam Allah ya isa wallahi Fada ranta tanayi tana murmuda baki Fa,iza dake zaune itama hankalinta nakan tv wani series ake yi a mbc tana bala,in son kallo itakam shiyasa suke yawan fada da ya Ali Kallon gefen da siyaman take tace "aunt Siyama ina wuni " Cikin washe baki siyama nta amsa "lafiya lau Fa',iza ya karatu"? "Alhmdulilh "Fa'iza tafada ta juya ta ciga ba da kallonta domin dai ita gaisuwa ce kawai take hadata da siyaman Abbah ne tare da Aliyu suka shigo Cikin sallama kai tsaye Ali teble yanufa bayan ya gama karewa musu kallo fuska a dage Shikam abbah Kai tsaye gurin Nene ya nufa ya zauna kujerar dake kusa da ita Kusa dashi Fa'iza tadawo ta zauna kamar zata shige jikinshi shima abban jawo ta jikinshi yayi Idon shi yana kan Nene yace ' naga kamar akwai magana a bakin ki " yafada bayan ya kuma gai da ita Kallonsa tayi tace "kwarai kuwa kafin ta rufe bakinta Siyama ce ta sakko daga kan kujera tace "abbah ina yini" Kallon gun abban yayi yace "a,a Siyama kece yaushe kika zo gidan?" Yafada bayan ya amsa mata gaisuwar da fuska a sake "Wallahi ban jima da zuwa ba Abbah" "Hakane bakajin tsoron fitar dare ko Dady n naki yanan kika fito yanzu"? "A,a abba momy CE tace nazo kawai" Abbah bai CE komai ba sabida ya Riga yagama fahimtar irin son da Siyaman takewa Ali wannan fitowar ma domin shi tayi mybe tasamu labarin ya dawo garin Ummi kam mikewa tayi ta nu fi dinnnig din dan tasan zaman da Ali yai abinci yake son abashi kamar wani yaro maganar ma bazai ba Yana zaune fuskarshi babu yabo ba fallasa Ummin takaraso gun Sakin fuska yayi yace "my ummi me kika girka ne "? yafada yana gyara zamansa sosai "Zaka gani yanzu ai" Wayarshi dake hannushi ya ,ajiye kan teble din yace "ok " "Ummu Allah ya jamin da ranki ya karamiki lafia Ameen" "Ameen " ummin tace tana kokarin zuba mishi abinci wata lafiyar yiyar jolof ce ta macoroni wacce akai mata mis da dankalin turawa taji bushanshan kifi hade da kayan lambu sai kamshi ne ya ke tashi "Wow my ummi wannan wane irin abinci ne "? ya fada yana da murmushi a fuskarshi ummi CE kawai take ganin murmushin sa sai ko abokanshi shima ba sosai ba sai Nene shi itakam ai in ta tabka wani abin har dariya yake sosai "Bakin ka zai gayama ko wane irin abinci ne " ummin tafada tana kokarin tura mai plete din bayan ta hada mai lemonshi na fama da take masa ko wane kwanan duniya,, "Yawwa son dan haka take kiranshi sabida alkunya tace "akwai maganar da za muyi" Kafin ta rufe bakinta Siiyama ce ta karaso gun cikin kwarkwasa da iyayi ta ce " laa ummi dakin bari na zo na hada mai abinci bana so ki wahala " tafada cike da kissa Gabanta sai faman faduwa yake tana tunanin.irin kalan dizgin da Alin zai mata Ummi n itama cikin wayewar kai tace "ai laifin ki ne kina ganin zamanshi a gun baki taso kin bashi abincin ba ko' Sabida tagama fahimtar yariyanyar makirar yarinyar ce me halin uwarta sabida azahiri za a nuna a nasanka a badini kaman abin bahaka abin yake bah irin su sunanan da yawa a duniyar nan Allah karabamu da masu fuska biyu ameen "Aikam dai " siyaman tafada tana dan murmushi yayin da take kokarin zama kan daya daga kujerun zaman cin abincin Barin gun ummi tayi a zuciyarta tace "ai Ali ne a gabanki yarinya dai dake ne in banda rashin zuciya irn nawasu mutane mutumin da akewa wannan abin bazai gane kora da hali ake masa ba amman sabida tsabar naci anki ganewa Ita dama ba wani son abin take ba sabida tasan halin mahaifiyar yarinyar "yar bin malamai CE da bokaye "yan tsubbu ita tsoronta kar aje a sabauta mata danta Dan ma Alin a tsaye yake gurin tsare jikinsa to amman sihiri waye bazai Ciba tunda yaci fiyayyan halinta Allah dai ya tsare ya kare tafada a ranta yayin da take barin gun Ali kam abincinshi yake ci kamar bai san da wata hallita a zaune a gun ba Cikin rawar baki siyama tace " ya Ali anyini lafiya " Shiru yayi bai amsaba sai data kuma mai mai tawa sannan ya dago kai yana dan ya mutse fuska as,useul yace "lafiya kalau ya cigaba da cin abin cinshi "Andawo lafiya ya hanya"? Bai ce komai ba sai kallonta da yayi akaro na Biyu Fuskarshi shade yace "wannan wace irin Shiga ce a jinki " ?yafada yana nuna sai tin kirjinta da suka bultso ta saman rigar ta da cokalin da yake hannusa Dadi ne Yakama Siyama sabida haka sai ta kuma gan tsaro kirjin cikin fari da ido tace " laa ! ya Ali me shigata tayi domin kai fa nayi" Kallonta yake yana balla mata harara fuska a mutukar murtuke Yace" tashi daga nan stupid haka zan aurekin kina fito da sasan jikinki don rashin mutumchi da sunan kwalliya usseles kawai " Cikin tsawa yace " ba dake na ke ba dan uwarki , wuce kibani guri ni zaki zo kina nuwa wannan abin naki" yafada yana kara kallon kirjin nata a karo na uku Cikin rawar jiki Siyaman ta mike daga gun har tana yin tuntube da kujerar bayanta A ranta kuwa tana kam ba ba irin rashin mutunci Ali Wai wannan abin yana nufi kirjin ta bai birge shiba yanda take ji da abinta amma Allah ya isa wallahi tafada lokacin da take Barin gun Da kallo suka bi Siyama jameel sai kunshe dariya yake a zuciyar sa yana cewa Allah shi kara Samun guri tayi gefen Na'ima ta zauna tana cika tana batsewa Da kallo Na'ima ta bita ganin yanayin Siyama murmushi tayi cikin magana kasa kasa tace "ya akai ne mutuniyar "tafada cike da zolayar ta domin dai sun dan ji irin dizgi da Ali nya tabka mata Basawar wa siyaman tayi tace "normal " To itama Na'ima ba tace komai ba ta cigaba da danne danne nen ta a waya aranta tace in tayi wari maji Dija ta koma inda Fa'iza take zaune itama ta zauna kusa da ita Cikin magana kasa kasa tace "wai wannan wacece ne"? Tafada tana kallon gefen da siyaman take zaune Kallon gurin Fa'iza tayi itama tace " aunt Siyama kike nufi"? "Eh mana" Dija ta fada tana ta be bakinta "Budurwa ya Ali CE ita. Zai aura karatu zata karasa sai ayi bikin" Kallon inda Siyaman take zaune dijan tayi Tab dijam ta hadu da jaraba ita tarasa wazata aura sai shi cab To ai shima ba wani sonta yake ba ita ce ke son sa Abbanmu kuma yace ita zaura sabida "yar gidan amininsa ce fa,izan tafada tana hararar dijan Tabe baki dijan tayi tace aikuwa dai naga tana sonsa yana mata wulakanci watakila in ya auretan ya dinga dukanta tafada cike d yarinta Ai y Ali baya duka shi ko laifi kayimishi Karkarinshi rankwashi ko yasaka daga hannu ko tsallen kwado Tabe baki dijan tayi idanta akan siyaman tana mamakin wai son ya Ali take ita tausayima take bata Nene ce da abba suke magana cikin fahimta da kauna irin ta da uwa hira suke dangane da dangin maihaifinsu Abbah dake can dan batta wasu su suna cikin halin rashi da talauci Sabida haka Nene tace " yakama ta yaje can garin ya fitar da zakka acan Sannan yatai makawa wa "yanda basu da sana,a da jari mai karfi Abban yace "insha Allahu yanda kikace haka za'ayi Nene Kallonsa tayi tace "yawwa sai magana tabiyu " To Abban yace yana kara mayar da hankalinsa kan ta In da Ali yake zaune ta kalla sannan tadawo da kallon ta gurin Abbah Tace" maganar Aliyu ce da siyama wai me,aka tsaye ne yakamata ayi a gama inace ai ya gama karatun kuma yasamu Aiki yana da gurin zama ya cika cikakken namiji tunda yanzu inace she karunsa in banyi karya ba talatin da biyu ko"? "Kwarai kuwa nene hakane" Abbah yafada ya ce "Wai ana jiran yarinyar kammala karatun n nata sai ayi" "To meye laifi in anyi ai sai ta kammala a dakinta bana son ganin Ali babu iyali ganin duk abokanshi kowa da aure dai dai kune babu a cikinsu Numfashi abban ya sauke yace "duk yadda kikace haka za,ayi zan samu dady Siyaman zamu tautauna akan maganar "Yawwa ko da najii" Nene tafada fuskarta cike da murmurshi Shima Abban murmushi yace "ni nata 6a ganin me so kishiya ma Nene in bake ba" yafada yana kokarin tashi daga gurin da nufin zuwa gurin cin abinci "Yo ai ta dole ce amma in tazo dole tazama gora ehee"!! Dariya jameel yayi wanda yake zaune a gefen ta tundazu yana fama da waya Yace" kewa zai iya kishi dake "? Kallonsa tayi tace "kai ashe kana nan " tafada tare da kama ha6a Dariya jameel yayi yace" ai kin soma makan cewa ne shiyasa kikasa ganin inan ko banan ,, Filon kujera ta dauka taje famasa tace "sai dai in kai ne ka makance shakiyyi Kasan masifar rashin ganin kuwa tafada tana hararasa" Tashi jamel din yayi yana dariya yace" to ke wai ke me kike jira ne Kikwantar d hankalin da idannunku zaki zaki mutu munanan munayi yimiki a du,a " Harararsa tayi tace "dallah wuce kaban guri samo dari kawai baka da aiki sai na kwallo n kafa da faman latse latsa a waya" Dariya jameel din yayi Yanufi dannig din shima Ummi kam tun lokacin da Abban ya tashi itama ta mike taje tahada mai abincinshi To duk wannan abin Siyama da Na'ima suna zaune dan kasa kunne Siyaman tayi babu abinda bata jiba Dadi kamar yakasheta tana ta shiwa Nene albarka ai in abin nan ya tabbata bazata taba mancewa da Nene ba a ta rihin rayuwara taba Cikin kan kanin lokaci ta saki fuskarta tana ta jan Na'ima da zance Girgiza kai kawai Na'ima tayi tana tausayawa Siyaman ganin irin wahalar da kanta datake a inda ba ,asan tanayi ba Yin aure da wanda bai sonka akwai babban kalubale aciki amman ta lura Siyaman tayi nisa a halin da ake ciki yanzu duk wanda yace zai mata maganar tarabu da Ali sai sunyi kaca kace sabida bata ji bata gani Ita dai fatanta Allah yahada kansu duk yadda take so Syama bakamar Ali ba tunda wata kusan tafi wata Mikewa sukayi dukkaninsu suka nufi gurin cin abincin suka banda Nene sabida bakasafai take cin abinci a sama ba sakamkon ciwon kafa datake fama dashi kujera suka hau gyara wa kuwa yana kokakarin zama wani kallo ALi yabisu dashi yana ya mutsaya fuska as,usuel ya dauke kansa yama yar da han kalinsa kan abba wanda suke tattaunawa game da yanayin aikin shi wayoyinshi da mukulin motorshi dake kan dannig din ya dauka yana kallon ummi wacce take kokarin sawa kuwa nashi abincin bayan ta kammala hadawa abbah nashi cikin tsawa yakalli Na'ima yace "aikin me kikeyi ke da baza ki hadawa kowa nashi ba " cikin sauri Na'ima ta ajiye wayar datake hannuta kan cin yar Siyama wacce take gefe sai faman kallon sa take kamar wata mayya tana kokarin karbar ummi ummin tace "jeki zamanki nagama ai bakwasan aiki ko kadan sai san jiki da fama da waya ai kun kusa fara shiga khicin din da kan ku ato muga karyar san jiki " ummin tafada bayan tagama hadawa kuwa nashin tsaki Ali yayi ya bar gurin aranshi yace shashashan yara kawai waye ma zaci abincinsu. shi kam abba murmushi yayi bai ce komai ba yana mamakin Alin yadda yake da tsamtsami abin a jinshi yake tunda jininka ma baka barshi ba ummi ma Nene ta hadawa nata takai mata har inda take Nene kam sai sa mata albarka take kai tsaye inda motorsa take yanu fa yana kokarin kiran faruk a waya wayar na makale a kafadarsa yana kokarin bude motar "hello" Ali yafada bayan yaji an dau wayar "kana gida ne " yafada a karo na biyu daga bangaran faruk din cikin shakiyanci yace " ya akai ne kai gwawro"? banza Ali yayi mishi batare da ya saurari maganarshi ta farko ba cikin dan bacin rai yace "kana gida ne" a karo na biyu "ehman ina zani a irin wannan lokacin wannan yawon ai sai irin ku marasa mafadi " faruk din yafada yana sakin dariya kasa kasa sabida yasan halin yan kayansa cikin bacin rai Ali yace " kai dai ka san abinda katsaya yi dan iska jarabbabe wallahi kabi musu da yarinya a hankali dan nafisa baza ta iya da jarabar ka ba " yafada yana faman huci dariya faruk din yake yace " to meye ruwanka da iyalina matanka ko tawa to wai ma da kake tambayar ina gida me zakayimin a wannan lokaci "? "Ubanka zanzo in maka" Ali yafada yana kokarin kashe wayar sabida ya fuska ci rashin mutumcin furuk din ne motsa yasan yana gida bazai fadama masa bane sai yai mai iskanci sabida haka kai tsaye gidan faruk din yanufa wajan tara da rabi ya isa gidan faruk din motar shi ya kule ya fito yana kokarin kiran faruk din awaya mai gadin gidan ne ya tashi.da sauri kunneshi makaleda redio yana sauraron tashar friedom redio cikin shirinsu na inda ranka ya budewa AIi karamar kofar tunda ya fuskanci ba motar zai shiga da ita ba sai faman washe baki yake yace " oga Ali kaine a wannan daren"? kalonsa Ali yayai yaga sai faman rawar jiki yake shi yana mamakin mutane da kwadayi da zubar da mutunci sabida ya saba yana bashi kudi shiyasa duk sanda yazo gidan faruk din kamar yai mai sujjada sabida tsabar rawar jiki A nutse Ali yakalleshi yace "meye haka malam isiyaku kake ? wannan bai dace ba ALLAH kadai shi muke bautawa mu dukanmu bawani dan ADAM ba sabida haka duk daya muke a gurin ubangiji daga yau kar ka kuma yimin irin wannan abin da kake min bana so ko kana so dani dakai mufada cikin fushin ubangiji ne"? cikin sanyin jiki malam isiyaku yatashi daga gurfanan dayayi, gaban ALI kamar wani mai neman gafara yace "tuba nake ranka yadade insha ALLAHU baza a kuma ba" Ali bai ce komai ba ya zira hannushi cikin aljihun jins din dake jikinshi ya fito da kudin ya bashi kamar yadda ya saba duk sanda yazo gidan faruk din hannun narawa malam isiyaku ya karba yana ta godiya "ALLAH ya biyama bukatunka na ALkairi Allah yabaka mace ta gari ALLAH ya azurtaka.da "yaya masu Albarka" "Ameen Ameen " AIi yafada yana kokarin shiga gidan hannushi rike da wayarshi yana kokarin kiran faruk din a karo na biyu ba zai iya shiga kai tsaye gidan ba duk da cewar gidan ba bakonshi bane ba to amma yasan halin Faruk bai da mutumchi zai iya takar Nafisa a ko ina ne ba damuwarshi bane "kafito ina cikin gidan ka " Ali yafada bayan ya tabbatar da faruk din yadau wayar bai bari faruk din yace komai ba yakashe wayar faruk di ne yafito yana kallon Ali cikin dan baciran rai yace "wannan wani sabon salo ne kuma "? banza Ali yayi dashi kai tsaye cikin gidan ya nufa bin bayansa faruk din yayi yace " bafa ka isa ba kazo har gidana kana cimin magani ba sai faman wani muzurai kake wa mutane da girma na da iyali na " faruk din yafada yana tarar gaban sa wata dariya ce ta kama Ali amma sai ya share azuciyar sa yace wai da girmana da iyalina shi abinma dariya yabashi kamar ba yau yabar yawo clob clob ba dan yanzun ma abin yayi sanyi darajar aure hararar faruk din yayi ya bige kafadarsa ya wuce yana dariya ciki ciki sakin baki faruk din yayi yana bin shi da kallo yana mamakin karfin halinshi shi kowa sai ya gwada mai iko da mulki girgiza kai yayi yana dariya a ransa yace kaje can akwai inda zaka yi wannan mulki naka amma bani ba yafada yana bin bayan sa tsayawa yayi dai dai kofar falon yana sosa kunnesa da mukulin motorsa idanunshi tsaye akan faruk da yake ta wo wa da murmushi akan fuskarshi yakalli faruk din yace "to mai iyali fara shiga kai min iso gurin uwarginnaka " yafada yana kanne masa ido daya dan yasan yagama kunna shi bazan faruk din yayi mishi yana kokarin bude falon sannan yace "in kaga dama kar ka shigo dani nake maka iso cikin gidan " dariya Ali yake yace "wallahi kabi ni ahankali in bahakaba in fasa kwai dan kasan zan iya wallahi" da sauri faruk din ya tsaya yana gyara fuska yace " wai meye haka kai fa baka da mutumci kar ka rusamin bajat dina na yau mana wai ma meya kawo ka ne yanzu" faruk din yafada sai faman gyara tsayuwa yake dan yasan halin Ali dariya Ali yake sosai ganin yadda faruk din yashiga taitayinsa kamar ba yanzu ya gama cika baki ba shi mai iyali.shi yana mamakin yadda wasu mazan suke rawar jiki akan mata shikam duk irin son daya kewa mace bazai iya wannan shirman ba shiga falon .yayi bakin shi da sallama Nafisa na cikin kujera a kwance jikinta sanye da kayan bacci masu kauri da hula a kanta da alama bata jin dadi cikin sauri tata shi fuskarta dauke da murmushi tace "ya AIi kaine ashe sannu da zuwa" ta fada tana kokarin gyara zamanta sosai murmushi Ali yake sabida yarinyar tana birgeshe tana da hankali sosai yace " Nine nafisa wannan mijinnaki bai da kirki ya hanani shigowa da kyar ya barni na shigo sabida kawai nace kar yayi miki kishiya shine yake jin haushina " ALI yafada yana kallon faruk din wanda tun shigowarsa yaje ya makale jikin Nafisan yana faman lumshe ido saurin kallon faruk din tayi tana harararsa cikin bata fuska tace " hakane" ? cikin sauri faruk din ya tashi daga jikinta yace "man ta dashi my love kinsan mugun makaryaci ka wai yarasa sharrin da zai min ne dan yana jin haushi ina da iyali na wata dariya ce takama Ali amma sai ya share yana kallon faruk din yace "ni nake maka karya ko"? ok hannusa ya zira cikin aljihunsa yana kokarin fito da wayarshi yace "bara kiga zahiri tunda ina da pic din budurwasa kinsan bazai bari a wayarshi ba dan karki gani shi yasa yake boyewa a nawa wayar" sakin baki faruk din yayi yana kallon Ali yana mamakin sharrinsa cikin zuciyarsa kuwa sai zaginshin yake "wallahi sai nai ma rashin mutunci " maganar tafito daga bakinshi bai shirya ba cikin sauri yatashi yakarsa inda yake ya fizge wayar sai faman muzurai yake yana Aikawa masa sakon harara Ali kam dariyar da take tacinsa tun dazu ya saki yace" meye haka zakazo ka fizgemin waya" banza faruk din yayi mishi ya koma gurin nafisa ya zauna yana gyara fuska mika mata.wayar yayi yace "karbi kiduba ko ina na wayar kigani karya yake wallahi kinsan mugun makaryaci ne" yafada yana faman shishigewa jikinta itakam in banda. harara babu abinda take aikwa da faruk din sannan cikin basawar wa takarbi wayar ta hau dubawa Ali kam yana gefe sai faman murmushi yake yana kallon yadda faruk ya wani firgice lokaci daya shi abin ma mamaki yake bashi shi kam bazai iya zubar da girmanshi ba irin haka ba kallon faruk din yayi yace "dallah malam kabar mutane jiranka fa nake akwai maganar data kawo ni " wani kallo faruk din yake mishi na alamar kafitar dani a gurinta Sarai ya fuskanchi abinda yake nufi ya basar mai da kallonsa yayi kan nafisa yayi yace "rabudashi nafisa yasa scurity a glarey din babu abinda zaki gani amma kisha kuruminki babu ke ba kishiya tunda bakya so" kallon sa tayi ta saki fuska tace "nagode ya Ali ni ba kishiyace bana so ba halinta nake gudu" dariya Ali yayi yace "ki fadi gaskiya dai itama dariyar take tace "wallahi daske nake " yace "to kici gaba da addu'a ALLAH yazabawa mijinki abu mafi Alaikari" "to ya Ali ina yin masa addu'a ai ALLAH yazaba masa abu mafi alkairi amma gaskiya ni kam bana son kishiya shima ya sani" nafisan tafada tana mai da nuffashi kallonta Ali yayi yana nazarinta murmushi yayi aransa yace wai mata me suka dauki kishiya ne su dunga gudun junansu sabida rashin yadda wannan abu ALLAH ne ya hallattashi mutukar namiji zai yi adalci sunna ce babba shi bai ga abun gudu aciki ba mai da kallonsa yayi kan faruk din wanda yake kusa da nafisa sai faman shishshige mata yake yana aikin rarrashi da murya kasa kasa kallon agogon hannusa yayi yaga goma . dara bi kallon faruk din ya karayi akaro na biyu har yanzu abu daya yake tsaki ya ja cikin ransa ya wannan dan iskan ya manta dani a dakin in ce ko tashi faruk din yayi rike da nafisa duk rabin jikinta yana jikinshi yana faman lallabata kallon ALI tayi tace " ya ALI zanje in kwanta bana jin dadi wallahi ka gai da gida agaida ummi da Na'ima cikin dan ya mutsa fuska yace " ok ummi dai za taji amma sauran sakon na ki ne mi dan aike ko ki aiki mijinki" dariya nafisa tayi tace "ni na isa in aiki oganmu ai girman kujerarka ne ALLAH ya huci xuciyar mai martaba" tafada tana murmushi faruk dake rike da hannnuta tun dazu yace "muje ki kwanta kira bu dashi yaje yaji da ya warshi hararshi tayi kasa kasa domin dai har yanxu bata gama sakkowa daga zargin data ke masaba"" ciki bacin rai faruk ya futu daga bedroom dinsu bayan yagama lallaba nafisa da cewar zolayarta kawai ALI yake amma ba gaske bane abinda ya fada da kyar dai yasamu ta yadda ta kyaleshi ya futu gun Ali "wai kai meyasa baka da mutunci ne iyi" faruk din yafada yayin da yake zama cikin kujera eic pic din dake mane da kunneshi ya cire yana kallon faruk din cikin kwanciyar hankali yace "wane irin rashin mutumci na yimaka"? "bansani ba" faruk din yafada yana faman huci dariya Ali ya kama yace " bani zaka nunawa iyali ba dan iska har yaushe kayi auran da zaka dinga magana akai kabari su shamsu da suka jima aciki suyi maganar iyali bakai ba sabon shiga " "eh naji nafi wani wanda yake yawo bashi da shi" faruk din yafada yana hararar sa da murmushi a fuskar AliI yace " to ai baka da matsala tunda kaje kun hada baki da Nene za aimin auran dole to na yadda zan auri Siyama shikkenan burinka yacika ko" banza faruk din yai mishi ya dau romot din tv yana canja za tasha "malam magana nake maka " AIi yafada a zafafe "dama maganar data kawoka kenan "? faruk din yafada yana basarwa banza yayi mishi ya mai da eic pic din shi kunne shi bayan yadan rage volom din "to ai gata za muyi maka katsaya kana faman zabe mace ko a ina zaka samu irin mace mai wannan halayen da kake nema oho duk irin bai war da.ALLAH yayimaka gami da farinjini "yan mata kasan duk cikinmu babu wanda "ya mata suke rubibi irinka ko wacce sai kace batai maka " Kallon sa Ali yayi yace " kwarai basuyi min ba itama siyaman ba wani yimin tayi ba ka wai dan kuna son abun kuma zabinku ce to zan aure tan sai a kyaleni in huta ai amma kasani dole zan auri zabina in sha ALLAHU" Faruk yace "ai ba mu hana ka ba Alhji dama Annabi ya bamu ikon haka ,abinda nakeso ka fahimta shine kabi umarni abba ,ka auri yarinyar nan na lura ita ma tana kaunarka sosai in yaso daga baya sai ka auri zabin naka" Tabe baki yayi yace "ai magana ta kare kuma na bar komai a hannunka ok Allah yasa haka shi yafi alkairi" "Alhmdullhi " Faruk ya fada cikin farin ciki ya ciga ba da cewa zan je in samu abbah da maganar" Mikewa yayi yana Sosa kunnenshi da key din motarshi yace"to mai iyali ni zan tafi" Faruk ya sa dariya ya Mike tsaye yana dukan kafadar Ali cikin dariya yace"ai ba karya ba ne in mutum ya Ji haushi yayi ya huta Dariya suka dukkaninsu suka fito tare Ali ya shige motarshi Faruk Na daga masa hannu har sai da yaga ficewarshi daga gidan sannan ya koma ciki fuskarsa dauke da murmushi,yana mutukar jin dadin yadda suke mu'amala da Ali cikin mutumci da sanin ya kama ta. Washe gari da wuri Ali ya kimtsa tsaf ya shirya cikin kayan aiki Wanda sukayi masa mutukar kyau sosai da sosai ya daura a gogonshi ,sannan ya zauna gefan katifarshi yana daure takalminshi sosai ,sannan ya fito daga part din nashi kai tsaye cikin gidan ya nufa Falo shiru babu motsin kowa yasan Ummi tana kchin ,kai tsaye dakin Nene ya nufa Nene na zaune kan dadduma hannunta rike da carbi tana lazimi ,sai gyangyadi takeyi Ali ya shiga yana ta sallama yaji shiru can ya hangota tana Neman faduwa ,bacci ya kamata Ya karasa da sauri ta taro kan ta da hannunshi ,ya ce"Nene zaki fadi fa ,in bacci zakiyi ba sai ki kwanta in kin tashi kya karasa carbin naki" Nene ta bude ido tana salati race"o yanzu baccin nan sai da ya fizge ni wallahi kokarina in cika carbin nan" Ta dago kan ta na kallon Wanda yake tsaye a kanta Gabanta ya fadi ganin mutum tsaye a kanta kikam da kayan soja Sam bata zaci Ali ne ba Ya gyara fuska yana kallonta Dariya naso ta kwace masa sabida ya lura da yadda ta razana da farko Yace"gaishe ki nazo nayi Uwargida sarautar mata" harararsa take tace "nace kazo ka gaishe ni ne " ? "baki fada ba" yafada yana kallonta fuska ya dan ya mutse yace " wai ke bakya gajiya bacci ne "? "bacci fa na tadda ke ki nayi a zaune saura kadan kiyi "yar dungure dan natasheki shine laifi" "bakai laifi ba " tafada tana kokarin cire hijab din wuyanta a gogo hannusa ya kalla .bakwai da kwata kallon ta yayi yace " antashi lafiya"? "lafiya lau " tafada yace ya" karfin jiki da gajiyar hanya"? "masha ALLAH gajiya tabi lafiya " "zamu fita kimana addu'a " yafada yana kallon ta kallonsa tayi "tace ALIYU ai kullum cikin addu'a muke ALLAH ya inganta rayuwarku da kai da kannanka ALLAH yabada sa'a ALLAH ya tsare min kai a duk in da zaka shiga" "Ameen ameen uwar gida gaskiya ina ji .dake daka ke babu wata " yafada.da murmushi a fuskarsa itama dariya take tace "yo ai duk wacce zaka auro sai dai tazama gora dama" murmushi yayi .bai ce komai ba yakama hanya fita ita kam Nene Dija ta ke tashi tai sallah dan da asubah ba yadda batayi da ita ba tatashi ta aki a cewarta ta kyaleta tagaji duk da cewar sallar asuba bata wuce ta a gurguje AIi ya kammala karyawa ya fita daga gidan dama sun gaisa da abbah tun da asubah bayan sun dawo daga sallar asubah fa'iza ce tafito cikin shirinta na skull Abba ne zaune a falon yana sauraron labaran safe a tashar aljazira kusa dashi taje ta zauna tace "abba barka da asibah dafatan katashi lafiya"? da murmishi a fuskarshi yace "lafiya lau fa'iza na kin shirts" "eh abbah Fa'.iza tafada tana gyara book din ta yace "masha ALLAH Allah ya tai maka " "ameen abbanmu" Nene ce ta fito dija na bayanta samun guri tayi ta zauna a kan kujera tana kallon fa'iza tace "haka kuke tafiya makaranta da wuri "? "ai nene ba asan mu makara sabida in malami yashiga. yai karatu ba kanan ba kuma, yima. zai yiba kuma in ka makara zane mutum ake a skull din mu" dariya abbah yayi yace "ai skull din nan ba daya.suke da na ko ina ba duk da cewar makaratun na kudi ne amma akwai tsaro da bada kulawa " jin jina kai Nene tayi tace " ai karatu duka karatu ne indai yaro zai tsaya ya kula" "hakane abban yace dan bayasan yaja maganar sabida ya fuskanci inda nene ta dosa "Nene antashi lafiya ya karfin jiki? abban.yafada yana kallon ta "lafiya lau masha ALLAH " "Nene ina kwana " in ji fa'iza "daban kwana ba kya ganni" inji Nene dariya fa'izan tayi bata ce komai ba Dija dake kusa da nene tun zamanta.sai kallon fa'iza take ta cike da sha'awa domin bakaramin kyau kayan makarantar sukayi mata ba sai taga unipom din ma kwata kwata ba ta taba ganinin irin shi a kano ba duk da yawan makaratun dake birnin na kano sakowa tayi kasa ta durkusa tace " abbah barka da asubah katashi lafiya"? "lafiya lau Dijana kin tashi lafiya kema ya gajiyar hanya "? "lafiya lau Abbah masha ALLAH" "Zonan "abbah yafada yana kallon ta Tashi dijan tayi ta karasa inda abban yake zaune ta zauna gefen kafafunshi shafa kanta abban yayi yana jin yarinyar har cikin ranshi ga tausayinta da yake ji sosai to amma komai na ALLAH ne yafada acikin ranshi Kallonta yayi yace "dija kina son zama anan ko"? Kallon sa dijan tayi sai kuma ta sunkuyar da kanta, bata ce komai ba "kinga sai a saki a skull dinsu fa'iza ko"? abban ya kuma yin magana a karo na biyu daga kai dijan tayi tace "abba ina so " yace " yawwa daga wane aji kikatsaya"? "Pramary 4 ne abbah" tafada tana kallon sa "Masha ALLAH zansa jameel ya kaiki skull din ai miki intervio sai a samu mai miki lesson ko"? "eh abba " dijan tafada tana dada sunkuyar da kanta "yawwa yarinyata ALLAH yai miki ALbarka kinji" "ameen abba" To.duk wannan tattaunawar da abbah da dijan sukai nene bata ji komai ba domin dai abbah kasa-kasa yayi da muryarsa shiyasa nene bata fuskanci abinda suke cewa ba illa tv da ta tsurawa ido sai kace mai fuskantar abinda suke fada fa'iza kam babu wanda ya kai ta murna domin dai taji komai tunda kujerar da take zaune a kusa da abban ne Ummi ce ta shigo falon asabe mai aikinsu na bayanta rike da kulolin kayan karin kai tsaye daynnig din ta nufa ta hau gyara gun koma wa kcin din tayi ta futu da wani kato flas din shayi ta ajiye ta dauko duk wani abinda tasan za'a nema sannan ta bar gun bayan ta kwashi gaisuwa gurin nene da mai gidan Ummice ta kalli fa'za tace "kitashi mana kije ki karya ki na duba time ne takwas shaura cikin sauri fa'iza tashi abbah ma mikewa yayi yakama hannu dija suka nufi dannig din ita dai dija tayi shiru cikin ranta kuwa tana kara kaunar abban ganin irin kulawar da yake nuna mata duk da karancin shekarunta tana gane mai kaunarta sabida haka abba yana da babba matsayi a cikin ranta dan haka duk abinda yace tayi zatayi mutukar bai sabawa umarnin ubangiji ba zama ummin tayi kan kujerar dake kusa da nene wacce ta tattara hankalinta kacokan kan kan tv tana kallon kamar mai jin abinda suke fada murmushi ummi tayi tace "nene kallo kike ne "? dauke idonta da ga kan tv tayi ta mai da kan ummi tace " yaushe kika shigo dakin ke kuma"? dariya ummi ta danyi tace "yanxu na fito da ga kcin ai ina ta magana bakiji ba naga hankalinki. yana kan tv numfashi Nene ta sauke tace "wato dai musulmi ya shiga uku a gun ya hudawa dubi yanda wa "yan nan yawudawa suke ragargaza gida jan musulmai suke kashe su kamar wasu kiyasai " "to ya za ai nene karshe duniya ne ai dama annabi yafada ALLAH sai yagama zabe nasa yanzu a duniyar nan in dai zakai ruko da addini da bin sinar annabi muhammadu (slw) to baka da kima da mutumci a idanun wasu mutanen in ka tsannata ma a nemi rayuwarka ALLAH kasa mufi karfin zuciyoyinmu Allah kasa mu mutu muna musulmai da darajar annabi" ummin tafada tana girgiza kanta "ameen dan ya rabbi " Nene tafada "bamu gaisa bama nene antashi lafiya" ? "lafiya lau na tashi " "to masha ALLAH akawo miki kayan karin nan ko"? "Me kuka dafa ne"? nene tafada tana kallon ta "Wainar shinkafa ce nene amma nasa asabe tayi miki kunun gyada naga kina sonshi" "kwarai kuwa kin kyauta ai kawo min nan bana iya hawa wancan abin yanxu sai kafata ta kumbura" murmushi ummin tayi tace "hakane abin dama in yahadu da girma sai hakuri" Abba kam yana zaune yana hira da dija cikin sakin fuska ummi takaraso gun itama ummin dariyar take tace "A'a hira ake ne nima bara nazo ayi.dani sunkuyar da kanta tayi tana dariya tace " ummi ina kwana " "lafiya lau kintashi lafiya"? ummin tafada da murmurshi a fuskarta "lafiya lau ummi" fa'iza ta wuce ne"? ummin tafada tana kallon abba kallonta abban yake yace "ina hankalinki yake lokacin data ke ce miki ta tafi" "ALLAH ya huce zuciyar abban yara ina can ina magana da nene lokacin inaji" "eh yanzu muke magana da dija ma tace zata zauna damu a sata skull fa'iza ai " Dariya ummin tayi yayin da take kokarin hada masa abinci tana masa magana da ido ya akai ta yadda nene kuma tasani girgiza mata kai yayi alamar subar maganar dariya ummin tayi cikin ranta tana adduar ALLAH yasa nene dai ta yadda tayi zamanta anan dan itama tana bala'in kaunar dija da tausayawa mata kallon dija ummin tayi tace "daughter duba kiga ni abincin ya isa ko in kara miki"? kallon abincin dija tayi tace "ummi yayi min yawa ma arage " A'a dija kidinga cin abinci kinji ai bawani yawa ne da ita ba hudu ce kawai fa daure ki cinyeta ga tae nan kihada in zaki sha kinji dijana" "To ummi " dijan tafada tana kokarin jawu flas din shayin Siyama ce ta fito daga dakinsu Na'ima jikinta sanye da wata doguwar riga cotton kanta da hula Ta karaso itama cikin iyayi da kissa ta durkusa gwiwa biyu tana gaida abbah cikin sakin fuska abba ya amsa kamar yadda yake wa yaran sa kallon ummi tayi wacce take faman hadawa nene kayan kari tace " ummi an tashi lafiya"? "lafiya lau siyama kintshi Na'ima bata tashi ba kenan"? "eh ummi kin santa da bacci na tashe wai na kyaleta " "to ai shikkenan sai kizo ki karya kira bu da ita duk sanda ta tashi ta karya babu wanda zai tsaya jiranta " ummin tafada tana barin gun hannuta dauke. da kayan karin Nene Ita ma siyama falon ta karasa tace " bara nazo na kwashi gaisuwa a gun uwar gida sarautar mata" Dariya nene tayi tana kallon siyaman tace " da dai ya fi miki domin shima uban gayyar sai da yazo ya kwashi gaisuwa sannan ya fita" Murmushi siyama tayi tace " ai girmanki ne uwar gidan ya ALI ina fatan kin tashi lafiya"? "lafiya lau na kwana" Nene ta fada tana kokarin sakkowa daga kujerar da take kai Ummi kam barin gun tayi bayan ta kammala hadawa nene abincin "Sakko kita yani ci mana zaifi lada" nene tafada tana kallon siyama "A'a nene kici kawai zan tashi in da fa indomee bazan iya cin wai na da safe nan ba" siyama tafada tana dan ya tsine fuska "haka dai ga abincin kirki kin barshi zaki tafi dafa wata indomee sabida kwadayi d son jiki " dariya siyama tayi tace "nene ba kisan dadi ba wallahi, amma kamar naji kince ya ALI ya fita ko"? "kwarai kuwa ya fita mana tun safe" Shiru siyama tayi ta so ta ganshi dan kwana tayi tana mafarkinshi wai gashi an daura musu aure suna rayuwa a guri guda itakam tana mutukar kaunar ALI shiyasa duk irin cin mutumci da yake mata bata gani an ce so hana gani hana ganin laifi dija ce ta taso daga in da take bayan ta gama karyawa inda nene take ta je ta zauna ta na dan ya mutsa fuska kallon ta nene tayi cikin kulawa " tace ke kuma meye" ? shiru dijan tayi bata ce komai ba sai da nene ta kuma maimaitawa sannan tace " nifa babu komai " "to meye zaki zo kina batawa wa mutane rai iyi" "Nifa nene munyi magana da abbah zan zauna anan gidan zai sakani a makarantar su fa'iza dan haka in zaki tafi sai dai kitafi ke kadai " tafada tana tutturo bakinta kallonta nene take cike da mamaki tace "au tanan kika bullo kuma" "To baki isaba tare zamu tafi acan ba kya zuwa makarantar da xaki ce abarki anan ehe"? "Nifa nene nafi son irin tasu fa'iza kinga anayin karatu gashi ta "yan gayu ce " harararta nene tayi tace " sai kiyi kuma tafiya dake babu fashi to kaji"" ta fada tana cigaba da cin abincinta wani irin ihu dija ta zunduma tana turje turje cikin kuka tace " ni kam bazan koma ba nace miki ki barni anan dan ALLAH ke kiyi tafiyarki" a guje Na'ima ta fitu taga dakinsu tana faman rarraba idanunta domin ihun da dija ta zunduma shi ya tashta ta ga bacci Shikam abba tuni ya bar gurin tun lokacin da yaji dija tana ga yawa nene ta barta a anan dan haka yana daga sama ya jiyo ihun dija daman yasan haka zata faru murmushi yayi kawai yana kokarin shiga wanka domin dai shima so yake ya fita offece maganganusu da dija su suka makarar dashi dan haka a gurguje yake shiryawa Ummi ce ta kara so gurin da suke tana kallon dijan wacce ke ta birgima a kasa tana faman gursheken kuka cikin rarrashi taje ta daga dijan ta rungumeta a jikinta tana kallon nene tace "don ALLAH nene kiyi hakuri kibar ta anan mana tunda ta nuna tana son karatun da da take gudun makaranta fa ai yanzun sai mu godewa ALLAH tunda da kanta take son tayi karatun" hararar ummi nene take tace "au! daure mata gindi zakiyi kema wai waya gaya muku a can bata zuwa makaranta ehe? ajin ta hudu fa pramary sai dai kuce ba kullum take zuwa ba amma tana karatu acan daza ku bi ku dame ni da maganar karatu" "hakane nene to amma yawan fashin da take yi bashi da wani amfani kUma bazata fuskaci komai ba a makarantar dole sai da kulawa sosai " ummun tafada tana sauke numfashi kallonta nenen tayi tace " au! ni bana bata kulawa kenan"? "A haba nene bahaka nake nufi ba ina nufin ko da an kai ta skull din dole za asamu mai mata lesson har gida dan kwakwalwarta ta ta da wa she wa shine nufi na " shiru nene tayi bata ce komai ba illa cigaba da cin abincinta da tayi hankalinta kwance N'aima kam harara dija take tace "ke wane irin shashanci ne wannan da zaki na faman kurma wa mutane uban ihu a gida sai kace wacce a ka kona da ruwa zafi wallahi sa'arki daya ya ALI bayanan da kinci kaniyarki yadda ya tsani kwarfniya da iface iface" "umm! kema kya fada sis ni da ta kurma ihun ma wallahi da guduwa zanyi dan nayi bala in tsorata " siyaman tafada tana faman hararar dijan dije dake rike a hannu ummi har yanzu wani kallo take kirmamawa Na'ima da ga ita har siyaman tace "to meye ruwan ku anyi ihun duk abinda mutum zaiyi yayi ai kin banza aikin wofi " tofa baki yasan abinda zai fada amma bai san abinda za'a mayar masaba zare ido siyama tayi tana kallon dija rike da habarta tana mamakin rashin kunyar yarinyar ita kam Na'ima kan dijan tana nufa tana kokarin kai mata duka ummi tana kare ta tace "zan bata miki Na'ima ai da gaskiyarta meye ruwan ku da ita sabida tsabar zubar da girma" "haka zakice ummi kina jifa zaginmu take waye sa anta a cikinmu ehe"? "to ai ku kuka shiga sabgarta tunda tazo ai inaji bata tankawa kowa acikinku ba in banda Fa'iza da suke sabgarsu tare" kwafa Na'ima tayi tace "wallahi sai na hada ki da ya ALI tunda baki da mutumci marakunyar yarinya kawai " tafada tana wuce wa daga gun kunkunni dijan take to " ki ga yamasa mana kar yabarni da rai" in banda ummi da take rike da dijan babu wanda yaji abinda tace su dai sunga bakinta yana motsi murmushi ummu take acikin ranta itama tana mamakin tsaurin idon yarinyar to amma ai khadija sunanta duk inda me suna khadija take tana da tsaurin ido da tsiwa gashi bata barin ta kwana to ammafa suna da bala'in kirki kuma baza su shiga sabgarka ba mudun batasu kashiga ba kuyi hakuri masu suna khadija a gafarceni kadan daga irin halinku nene kam duk wannan abin tana jinsu ko kala ba tace illa data gama cin abincinta ta gyara kwanokan ta matsar dasu gefe ta koma kan kujera ta cigaba da lazimin safen da take wanda yazamar mata jiki da jini sai tayi in batayiba ma bata jin dadi cikin ranta kuwa tace kukarata in dai dija ce gatanan ga ku ai tunda bata kyale ALI ba wazata kyale siyama ko kallo take ta bin dijan dashi tana faman ya tsine fuska lokaci guda sai taji ta tsani yarinyar jiya dai data ganta sai taji tana sonta kasan cewar tana yanayin kama da habibinta ita tunda take babu wanda yataba zaginta baranta na ya mayar mata da magana irin haka dija kam data fuskanci hararar da siyaman take mata itama sai ta fara ramawa tanayi tana murmurdae bakinta sakinta ummin tayi ganin abbah yana sakkowa da sama hannushi rike karamar jakarshi sai wayoyinhshi da ke rike a daya hannun kara so wayayi gurin yana kallon nene wacce ta hakince akan kujera fuskarta babu yabu babu fallasa yace "nene ya zamu fita kallonsa nenen tayi tace "Allah ya bada sa'a amma kana jin irin diban albarkar da yarinyar nan take ko" ? tafada tana kallon inda dija take zaune tana faman zuzzobaro dan karamin bakinta wanda hakan har ya zamar mata jiki kallon agogo abbah yayi sannan ya mai da kallonsa kan nene cikin kulawa yace " babu lokaci nene yanzu in na dawi sai muyi maganar kwata kwata ya nuna bai san abinda yake faruwaba "to babu laifi ALLAH ya tsare ya bada abinda ake nema mai amfani " nenen tafada cike da kulawa "ameen ameen" abban ya fada yayin da yake barin gurin "Abbah ALLAH ya kiyaye hanya" dija ta fada tana kallonsa " ameen dijana" siyama ma Adawo lafiya tayi mishi ya amsa cikin kulawa ummi kam bayansa tabi hannuta rike da karamar jakarsa ta aiki Cikin sauri haruna drevar abban ya tashi wanda dama yana zaman jiran fitowar abban yakaraso ya karbi jakar dake hannun ummin yana gaisheta amsawa ummi tayi tana barin gun bayan takara yiwa abbah Allah ya ki kiyaye da sauri haruna ya karasa ya budewa abba motar shikam abba har ya bude ya shige yana kallon haruna yace "shiga mu tafi bude motar ma sai na tsaya ka bude min da rai na da lafiya ta haruna" murmushi haruna yake yace "ALLAH yaja da rai ALHAJI ai mu kam babu abinda za muce da kai da iyalinka ka ci damu kayi mana aure mu da muke karkashin ka mu za mufadi alkairinka in da masu kudinmu zasu dinga koyi da irin halayenka da dayawa ba'ayi talauci ba" ******* To captin ALIYU yau an shiga offece bakin aiki bakin fama ko wanne da offece dinshi don haka bayan sun gaisa da faruk din kowa ya shige nashi domin akwai tari aiki wanda zasuyi bakinshi dauke da addu'a ya shiga offece din yana karewa masa kallo masha ALLAH babu abinda babu aciki zama yayi kan kujera hade da cire glass din dayake idanshi yana kallon katon teble din da yake gabansa wasu manyan yan takkadu ya gani da dauka yayi ya fara dubawa wayar shi ya dauka yana ne man ogansu yana son yai yi mai karin bayani akan su "hello " ALI yafada bayan yaji an dau wayar daga daya ban garan akace "ALIYU ZAKIN FAMA " cikin barkwanci murmushi ALI yayi yace" oga barka da asubah " "barka kadai ' ogan fada "ina fatan ka na" offece ko "? "eh oga ina son karin bayani ne a kan wannan ta kaddun da nagani yanzu" "Ok rigima nan ce ta jahar taraba jalingo ta wannan ba fulatanin mutuminan wanda aka A ka kashewa iyalinsa yaje garinsu yace bazai yadda ba shine "yan uwansa suka zo suna ta barna in suka yi kisa sai ane mesu a rasa dan haka mun tura captin shamsu da sauran "yan uwansa akan hakan, ina so kayi binkice sosai akan rigimar nasanka da kokari da kai fin tunani" idanunshi kan wata takkada yana nazarinta yace "karkadamu oga insha ALLAH komai zai yi daidai" "ok shima faruk din nasa a ajiye masa ya yi nazarin sosai domin tare nake son in tura ko garin" "ok amma ina tunanin arna garin ne suka yiwa wannan ba fillace wannan aikin lokacin da ya futa kiwo oga ka san cewar yana da karfi arziki da iyali da shanu da ALLAH yai mai arzikinsu" "kwarai kuwa ana tunani wannan abinda ALLAH yayi masa shine yasa sukayi masa wannan ta'annatin sabida shima yanke jiki yayi yafadi lokacin da yadawo daga kiwo yaga rariyar gidansa tana kwararar da jini domin yankan rago suka yiwa iyalinshi bai tsira da komai ba sai shannusa to shine "yan uwansa suke ta barna suma da sunyi kisa sai a nemesu a rasa so muke ane mi sulhu dasu " "kwarai kuwa hakan yakamata ayi " Alin yafada yana kara nazarin abin "gobe in sha ALLAH zakubi su captin shamsu sabida haka ku kwana cikin shiri" "ok oga ALLAH yakaimu " "yawwa ka kara nazari sosai" ogan yafada yana kokarin kashe wayar yana kashe wayar kiran faruk ya shigo yace "Meka fuskanta da rigimar da ake a jahar taraba tsakanin arnan garin da ba fillacen mutuminan"? "Eh ina nazarin al'amarin ne amma fa ina tunanin wa "yannan mutanan yaki da bindiga bazai musu ba tunda ba'a ganinsu sai bayan sunyi barna suke bacewa bat"! faruk din yafada "kwarai kuwa dama sulhu za'a ne ma kawai dasu tunda tabo su akayi " Ali ya fada sannan yace " gobe insha Allah zamubi bayan su shamsu yanzu muka ga ma waya da oga" "Ok ALLAH ya kaimu " faruk din yafada "ameen" Alin yace yana kokarin kashe wayar To acan gida kam dija yini tayi tana faman nukkufurci da bace bacen rai taki kula kowa ciki kuwa har da mutuminta jameel Haka yazo ya karaci neman maganarsa a gun nene tayi mai banza itakam nene zuwa tayi tayi kwanciyarta tace kyayi ki gama kafata kafarki yarinya ko da fa iza ta dawo kin kula ta tayi sai da fa'izan taje ta tambayi nene me akayiwa dija ta ke faman cin kunu Kallonta nene tayi tana mamakin wannan kauna da suke wa junansu gami da shakuwa ita bata taba ganin mutumin da dija ta zauna dashi na awa daya batare da sunyi fada ba sai fa'iza "kyaleta fai'za wai abarta ta zauna anan abbanku yace zai sata a irin makarantar da kike zuwa shine nace ban amunceba shine take ta faman bace bacen rai" bata fuska fa'iza tayi cikin yanayin shagawaba tace " to meyasa bazaki barta ba iyi nene?" "Ai tana zuwa makarantar acan in nabarta anan wazai dinga debe min kewa" kallonta Fa'iza tayi tace to " Nene ai naji abbah yana gayawa ya Ali ranar da yaje zai tawo da ku cewar in kika zo bazaki koma can ba sai dai kidinga zuwa ziyara kuma ma ai dazu abban ne yace wa dija zai sata a skull dinmu kinga sai mu dinga tafiya tare "Fa'izan tafada cike d kuruciya da yarinta wani kallo nene takewa Fa'izan tace " tashi kibani guri ai ban ga wanda zai hanani tafiya ba to kaji"! "ai nasan tunda naga Ali yana wannan murmushi nasa nasan da abinda ya taka zai zo ya sameni ai" Tashi Fa'iza tayi da ga gun tana cewa "dama kinyi zamanki anan to in kin kuma can din ma me zakiyi" Carbin dayake hannunta ta ke kokarin caula mata tace "wuce kiban guri shakkiyar yarinya kema sun koya miki ko kina yawo sumumu dake to ubanki zan koma nayi acan din" cikin sauri Fa'iza ta kauce da ga inda take tana dariya tace "Allah ya baki hakuri ni dai in kince dole sai kin tafi to kibar dija anan don Allah" banza Nene tayi da ita ta cigaba da laziminta to koda Fa'iza ta koma dakinsu Dija ta tarar a kwace yayin d Na'ima da siyama ko wacce take abinda ya dameta Na'ima dai waya ce a hannuta kunneta mane da eir pic Siyama kam loptop dinta take dubawa kallon Dija tayi bata ce komai sannan ta mai da kallonta kan Na'ima tace " ya Na'ima kije ki rarrashi Nene don Allah tabar Dija anan tace wai bazata barta ba" kallonta Na'imma tayi tana rage volom tace "me kikace ne?" sai da Fa'iza ta kuma maimaitawa sannan Na'ima ta kalli inda Dija take kwance tace "au shine dalilin da dama take wa mutane ihu a gida tun dazu taki kula kowa sai faman bacin rai take" "eh Ya Na'ima don Allah kije in kuma taki kigayawa ya Ali nasan zai iya hana ta tafiya da Dijan" dariya Na'ima take tana kallon Dija n tace " to wai ita bata da baki ne ke kike aron bakin nata kici mata albasa in tana so kwai tabari ya Ali ya dawo sai taje da kanta ta roke shi nasan tunda nene ta kafe cewar .da ita zata tafi to kam ba makawa da itan zata tafi "tafada tana kara kallon Dijan ceke da tsokana Dirowa Dija tayi daga gadon tayi tazo ta zauna gefen da Fa'iza take tana kallon Na'ima tace "dan Allah.ya Na'ima ki taimaka min nasan halin Nene in ta kafe akan magana ko Abbah ne yai mata magana da kyar ta yadda " harararta Na'ima tayi tace "dazu wa ki ka gama zagi iyi"? cikin dan zumbura baki As'usuel tace "nifa bada ke nake ba ya Na'ima" kallonta Na'ima tayi tace " to dawa kike dan uwarki akwai sa'anki a cikinmu iyi"? ba tarai Dija tayi don ta tsani a zageta dan dai kawai tana so taje ta hada Nene da ya Ali ne amma da sai ta ra ma ehe sunkuyar da kai tayi bata ce komai ba sai da Na'ima ta kuma maimaitawa sannan ta dago kanta tana kallon inda siyama take zaune ta zuba mata ido domin tunda lokacin da taji tace bada Na'ima take ba ta bar abinda take tana kallonsu to dawa take yarinyar nan tana nufin da ita take kenan kara kallonta Na'ima tayi tana kallon inda take kallo itama girgiza kai tayi tana mamakin yarinyar kwata kwata bata da munafurci wato tana nufin da siyaman take Siyama kam ranta a bace ta juya tana cigaba da duba loptop dinta tana saqa irin matakin da zata dauka akan yarinyar cikin harara Na'ima take kallon Dija tace "wai ke wace irin yarinya ce ne iyi"? kin san matsayinta a gidannan kuwa to babu ruwana duk abinda ya biyo baya, ki ciga ba da zaginta da yimata rashin kunya wallahi babu ruwana in ya Ali ya ji domin matarshi ce kin san zaneki zaiyi" kara kallon Siyaman tayi tana dan harararta kasa kasa cikin ranta tace ya kasheni kar ya barni da rai na A fili kam shiru tayi bata ce komai ba domin dai so take Na'ima taje takara lallashin Nene akan maganar dan haka shiyasa ta kyale ta itama gyara kwanciyaNa'ima tayi tana kara kallon yaran sunyi mata tsoru- tsoru a gabanta wata dariya ce ta so ta kufce mata amma sai ta dake bata yiba tana mamakin kaunar da sukewa junansu sai taji sun bata tausayi don haka sai tace "ku tashi zanje in na tashi daga bacci kunxo kunyimin tsoru-tsuru agaba " a tare suka tashi suka bar gurn cikin farin ciki suna cewa "mun gode ya Na'ima " ita kam Na'ima kallon inda Siyama take zaune tayi tace "besty kiyi hakuri da abinda fa yarinyar nan tayi miki haka halinta yake wallahi muma bata kyale mu ya Ali kawai take dan jin tsoro da shakka shima dan yana cin ubanta ne" murmushi Siyaman tayi cikin siyasa tace "haba Na'ima ai nima kanwata ce kuma akwai kuruciya a tare da ita shiyasa wataran in an ce tayi ma bazata yadda ba " tafada tana kallonNa'ima nan ko cikin ranta ita tasan irin matakin da zata dauka akan yarinyar don wata irin tsanar yarinyar take ji cikin ranta dariya Na'ima take tace " yawwa matar ya Ali haka nake sonki da fahimta don haka daka ke babu wata cikin gidan ya Ali " wani murmushi Siyaman take domin tana jin dadin yadda Na'ima take kaunar al'amarinta da ya Ali shiyasa itama take sonta ita kam Na'ima iyawa kawai tayi domin ta fuskaci Siyama saida siyasa shiyasa take mata ta "yan duniya itama domin a zauna lafiya amma tasan a zahirin gaskiya ya Ali bai son ta ita take haukanta tashi tayi tace " bara naje gurin Nene '' "Ok Siyaman tafada tana cigaba da abinda take Samun Nene tayi a kwance a inda fa'iza ta tafi ta barta tana cigaba da jan carbinta Zama tayi kusa da kafafun ta tana jan kafar A hankali ganin gyangyadi yana dan fuzgar Nene bude ido Nene tayi tana kallon Na'ima sannan ta tashi zaune tana gyara daurin dan kwalinta tace "ke kuma yaushe kika shigo "? dariya Na'ima ta dan yi tace " yanzu nazo na tarar kina faman gyangyadi ke kam Nene bacci baya yimiki wahala wallahi " itama Nene da murmushi Akan fuskarta tace"Ai lafiya duk mutumin da kika ga yana yawan bacci to yana samun lafiya musamman kamar irin masu shekararun mu Anfi son su dinga samun i shashen bacci domin in ganta Lafiyar su , "kwarai kuwa Nene domin sukansu likitoci suna bada shawarar haka "Na'ima tafada tana kallon Nene "yawwa Nene da Akwai maganar da zamuyi don Allah " Na'ima tafada tana kallon Nene A karo na biyu itama Nene cikin kulawa tace "wace irin magana ce zamuyi "yar nan ki ke hadani da girman Allah " dariya Na'ima tayi ganin yadda Nene ta hada hankalinta guri guda tana jiran taji zance "dama kan maganar Dija ne don Allah Nene wai meyasa bakya son ki zauna damu ne ba fa kya zuwan mana da kinzo ma zaki ce zaki tafi don Allah ki zauna damu mu ma muna bukatarki anan" kallon ta Nene take tace "wannan ce maganar dama ,? to in zauna inyi muku me na bar dakina nazo na tare anan can ma "yan uwa da Abokan Arziki suna bukatata" Nene tafada tana dada gyara zamanta hankalinta kwance "mu munfisu bukatar ki wallahi muna so mudinga ganin ki kullum Nene" Na'ima tafada tana karyar da kai domin ta fuskanci in ba haka tayi ba Nene bayadda zatayi ba "ke bazan zauna ba nace wai tashi kibani guri wato hada baki kukayi ke da "yar uwarki itama tazo tagama ke ma kinzo kina yi ko nace bazan zauna ba ehe! shima Aliyu zai zo yasame ni domin ai bahaka mukayi dashi ba mutumin banza babu wanda zai sakani in zauna a wata uwa duniya "yan uwana suna can wani guri ni ina wani guri gashi suna bukata ta sosai sabida haka bari Abban naku ya dawo gobe zamu kama hanya mutafi na fasayin sati dayan dana ce zanyi to kaji""""" kallon ta kawai Na'ima take tana kunshe dariya domin Nene sai wani masifa take batasan ko kasa da sama zata hadu babu wanda zai mai data sai dai in ta tafi ita kadai "to tunda kin ce bazaki zauna ba kibar mana Dija anan don Allah" Na'ima tafada cikin rarrashin Nena banza Nene tayi da ita tana cigaba da laziminta ita ma Na'ima bata kuma cewa komai ba illah zubawa Nene ido da tayi kusan minti goma babu wanda ya kuma cewa komai cikinsu ita Na'ima tana tunanin yadda zata bulluwa abin ne yayin da Nene take tunanin yadda zata iya zama ba tare da tana ganin "yan uwanta ba domin dai Nene maca ce mai zumunchi kusan kullum atafe take kai wa Jan kai was "yan uwa ziyara da Abin arzikinta shiyasa sukan su"yan uwanta suke ji da'ita domin tana tai maka musu ba kadan ba to a zahirin gaskiya tasan nan dinma suna da bukatarta to Amma gwara nan domin su Acikin dadi suke kuma basu ne mi komai sun rasa ba tasan Allah ne mai ciyarwa da shayarwa Amma mutanen da take taimakawa da abinci suna dayawa kama daga dafaffe zuwa danye.yanzu ya zasuji in sukaji zamanta ya dawo nan gabada daya tashi Na'ima tayi tace "Allah ya huci zuciyar uwar dakina ni dai zan gayawa yaya Ali cewar kin ce bazaki koma ba kin fison nan yafi dadi dabida haka ke kar Asake a mai dake kano" Na'ima tafada cike da tsokanar Nene itakam Nene bata ce komai ba har Na'ima ta karaci neman maganarta ta fice daga dakin to har dare Dija taki kula Nene tasaki ranta tana walwala da kowa Amma taki zuwa inda Nene take har Abba yadawo yagama sabgoginsa asama ya sauko cin Abinci Dija bata cewa Nene kala ba gashi An hadu a babban falon Anata hira cikin nishadi jameel sai tsokanar Nene yake yana dariya kowa sai dariya yake Amma banda Dija wacce ta kame Akan kujera tana faman zumzumbura bakinta Nene kam itama ko kallonta batayi ba tace kyayi kyagama ni ko A mafarki ma ban yi zaton zaki.ce zaki zauna Anan ba sabida rashin sabonki da jama'a Nene take fadar haka cikin zuciyarta jameel ne ya kalli inda Dija take zaune yace "ke wai me A kayimiki kike ta faman cin kunu tundazu" banza Dija tayi dashi ta dauke i danunta daga inda suke zaune dariya yakama yace "wa kike harara da wannan kwala kwalan i danun naki " ? harararsa ta yi tace "tubarkalla masha Allah " ta dauke i danunta da ga kansa dariya ya kuma yi A karo na biyu yace "zo kiga wata sabuwar game mai dadi ce " yafada yana kokarin ciro wayarshi daga Aljihun gaban rigarshi banza tayi dashi bata ce komai ba ummi dake zaune tun dazu bata ce komai sai yanzu tace "dan Allah ka kyale ta mana kazo kabi ka damu mutane da surutu ba gaira babu dalili" murmushi yayi yace "wai don Allah ummi me A kayi mata ne"? "ina ruwanka to" ummin tafada tana harararsa fa'iza ce da sauri tace" ita da Nene ne fa wai baza ta barta A nan ba " kallon Nene yayi yace "kamar yaya bazata barta A nan ba"? ita ma Nene shi take kallo tace" e bazan barta A nan dinba ka wani zuba min ido " "to ke ina zaki da ta keso kibarta Anan din"? "bansani ba gobe in sha Allah zan kama hanya na koma in da nafito tunda A bin yazama haka" Nene tafada tana kara kallon inda Ummi take zaune dariya jameel yake yace "wasa ma kenan Ai sai dai kitafi ke kadai Amma Dija baza ta biki ba tunda tana son zama A nan " ko kallonsa Nene batayi ba ta ciga da kallonta hannuta rike da carbinta Abba ne yai sallama domin kai tsaye da ya sauko bai zauna A falon ba masallaci ya nufa sai da ya jira yi isha'i sannan yai A ddu'oinsa sannan ya bar masallacin kallon jameel din yake yace " ba ka wuce masallaci ba kanaji A na sallah ko"? "eh Abbah yanzu zan tafi" jameel din yafada yana sunkuyar da kansa "Ai sai dai kayi taka kai kadai tunda yanzu babu masallacin daza su tsaya jiranka " Abba yafada yana kokarin zama kan kujarar da take fuskantar Nene tashi jameel din yayi yana faman sosa kansa ita kam Nene harara tabishi da shi tace "sai Aukin surutu jam'i yana huce ka" bai ce komai. ba ya fice gaba daya daga gidan to suma su Na'ima ta shi sukayi bayan sun sake gaishe da Abbah A kabar Nene da Abba A falon Ummi kam tun lokacin da Abbah ya shigo ta tashi ta nufi daynnig domin ta hada masa Abinci gaishe da Nene Abbah ya kuma yi yace "munyi lafiya Nene"? cikin kulawa Nene tace " lafiya lau ya Aiki da fama da jama'a"??? "lafiya lau Alhamdulilah "Abban yafada "masha Allah Allah ya taimaka yayi jagora " "Ameen ya Allah Nene" "dazu kina magana babu lokaci ko" Abbah yafada yana kara mai da hankalinsa kan ta "eh ni da Dija ne baka ga irin rashin kunyar da takewa yarannan ba suna Na'ima ita da wannan yarinyar matar Ali" "Assha "! Abban yafada yana gyara zamansa hankalinsa gabadaya Akan Nene "yawwa sai magana ta biyu tasa rigimar wai sai nabarta Anan wai kace zakasa ta A makarntar da fa'iza ta ke zuwa to Ai acan din ma tana zuwa makarantar sabida haka gobe nace dama zamu kama hanya mu koma tunda kun zugata da kai da sauran yaranka" murmushi Abba yake acikin ransa yace "nasan za Arina dama " kallonta Abba yake cikin rarrashi yace "haba dai Nene Ai munyi da ke cewar sati biyu zakiyi sai in sa A mai dake ko ni in mai da ke da kaina ko" "kwarai kuwa haka nace to yanzu na canja shawara gobe nake so in tafi tunda Abin ya zama haka dama kadade kana so ka dauke min Dija daga gaba shine yanzu kuka taro da kai da yaranka kuke zugata yarinyar da bata so natafi ko ina na barta yau ita ce take cewa baza bini ba" dariya ta kama Abba ganin yadda Nene ta wani hakikance ita fa da gaske tafiya.zatayi yace "kiyi hakuri Nene kikara kwanaki ko sati ne kiyi don Allah kuma ina rokon Alfarma kibar min Aron Dija don Allah in hadata da "yan uwanta guri guda tana gama skull zan mai do miki da ita " "wai karatu duk ba karatu bane da za ku wani dame da zancan karatu ehe Acan din ma Ai tana zuwa makarantar " "Ai nasani" Nene Abba yafada cikin rarrashinta sannan yace "karatunmu.na nan ba daya suke.da na can ba nan zatafi samun kulawa sosai sannan tana ganin "yar uwarta zatafi mai da hankali" Shiru Nene tayi bata ce komai ba Abbah yace "ke nake sauraro Nene in baki Amince ba sai kutafi babu damuwa tunda tana debe miki kewa yarinyar" Ajiyar zuciya Nene ta sauke tace 'shikkenan Ai tunda kun matsa sai ta zauna Amma nasan halin Dija zata iya bijerewa in An kwana biyu tace A maida ita to wannan ne ban Amince ba tunda har kun zabi zamanta Anan din ita ma tana so to sai dai in ce Allah ya bada mai Amfani ilimin" "Ameen" Abba yace fuskarsa cike da Annuri bai zaci zai shawo kan Nene cikin sauki haka ba yace "in sha Allahu haka baza faru ba Nene Dija zata zauna samu ilimi mai Amfani" "to Allah yasa gobe kasa A mai dani Ai mun gaisa ko to zaman me zanyi" "Aa ' Nene kikara hakuri kiyi mana sati daya mana" Abba ya fada kan Nene tayi magana Ali ne yayi sallama cikin falon fuskarshi babu yabo babu fallasa shigowarshi kenan wata irin yinwa yake ji tun safe rabonshi da yasa wani Abin Abakinshi don haka,da ya shigo gidan bai nufi bangarensu ba ya shigo gidan so yake ya fadawa ummi cewar tasa Akai masa Abinci can domin wanka yake son yayi tun A mota ya cire rigar saman yabar ta cikin wacce suke daura rigar kakin Akai wata mai yan kakakke hannu don haka A hannu ya shigo da rigar daya hannunashi rike da wayoyinshi da key din motarshi da ma loptop dinshi A motar yake barinta sun kuyawa yayi yana kwance igiyar ta kalmin shi wanda tun da ya sashi bai cire ba sai dai in zaiyi Alwala kara sowa yayi tsakiyar falon ya karasa in da Abbah yake zaune yana mika masa hannu shima Abba hannu ya mika masa sukai musabaha A junansu Alin yace "Abbah barka da dare Abbah" "yawwa barkanmu dai haidar ya Aikin na ku" ? "Alhmdulilah mun gode Allah Abba, gobe ma Insha Allah zamu wuce can jahar taraba jalingo domin kwantar da wata tar zoma da ta ke faruwa" "to masha Allah Allah yakiyaye ya bada sa'a" "Ameen Ameen" Alin yafada to duk wannan Abin da suke hannayensu nanan rike da na junansu kamar wasu Abokai wannan shakuwar haka take tsakanin Abban da Aliyu cikin murmumushi Abba yace" yawwa sai ka zauna ka rarrashi uwargidan naka gatanan tace wai gobe take so ta tafi" kallon inda Nene take zaune Ali yayi yana dan ya mutsa fuska na sabo ita kam Nene tana zaune zukudinm tana mamakin wannan shakuwa tsakanin uba da dansa kamar wasu Abokai ita ma shi take kallo tace "meya ka tsareni da wa "yannan ida nuwanan naka kamar na masu jin bacci ko ince kamar na mashaya sai ka dinga faman kikkiftamin ido eh ! , nace zan tafi kuma bance kai zaka mai dani ba ehee!" kallonta yake fuskarshi A hade sabida dama shi haka yake in dai ya gaji ba ko wane yake gane gajiyarsa ba sai umminsa ita ce take fahimtarsa in dai tanganshi babu wal wala duk da cewar dama ba kasa fai yake dariya ba cikin ransa kuwa cewa yakecewa wannan Nene masifarfiyace dubi sai wani masifa takewa mutane fuska babu walwala yace mata "Nene kin Wuni lafiya"? Ya bar maganar da take tabi ruwa "lafiya lau " Nene ta fada tana dauke i donta daga kan sa ta daura A kan Abba sannan tace " ka tambayeshi ya muka yi dashi da yaje tawo damu " kallon Alin Abbah yayi yace" to kai kaji yaya kuka yi da ita ne"? Abbah ya nuna kamar bai son Abinda suka shirya mata shi da Alin ba lokaci da zai je daukota cikin yanayin maganarshi yace " bangane A tambaye ni yaya mukayi ba ke ce fa kika ce zaki zo sabida kin dade bakiga danki ba da sauran jikokinki " Alin yafada ida nunsa Akan Nene gashi fuskarsa A hade kamar da gaske kallonsa Nene take tace "Af Ai ka kware wajan kulla sharri kamar wata mace kai wata macen ma in kana guri duk sharrinta sai ta kauce " Nene tafada tana faman hakikancewa wata dariya ce ta so ta subucewa Ali Amma ya dake yana yinta A zuciyarsa ganin yadda Nene take kokarin fadowa daga kan kujera sabida masiba Abba dake gefe shima dariyar ke cinsa Amma ya dake yana kallon Alin yace "kai bana son shirme tambayarka nake ya kukayi da ita lokacin da kaje dauko ta" gyara zama Ali yayi yana duba A gogo dake daure A hannusa.sannan ya kalli Abba yace "lokacin danaje ne Abba na tarar da yarinyar nan suna dambe da yara gashi lokacin makaranta Nene bata tura ta da nai mata magana sai tace,Ai makara tayi shiyasa bataje ba,to A dan zaman danayi na lura da yarinyar bata son karatu gashi bata da kunya shine nace kace in tawo da itanan zaka sata A makaranta shine fa,Nene tace ita ma zata zo to kaji yadda mukayi fa Abbah" kafin Abbah yace komai Ali yaji saukar Abu Ajikinshi kallon gurin yayi romot din tv ne Nene ta cillo masa tana faman harararsa kamar idanta zai fado ita kam bazata iya da sharrin Ali ba ta fada cikin ranta murmushi yake yana kallonta sannan yace "me nayi miki daga fadin gaskiya kefa kika ce in fadi yadda mukayi dake" banza Nene tayi dashi bata ce komai ba'shi kam Abbah mai da hankalinsa kan Nene yayi yace "kiyi hakuri Nene duk yadda kika ce haka za'ayi Amma ina neman Alfarma A karo na biyu kiyi hakuri kiyi mana sati daya Anan don Allah in ya so sai in mai dake da kaina " shiru Nene tayi bata ce komai ba ta mai da hankalinta kan tv da take ta faman yi.ita kadai wannan ya nunawa Abbah cewar Nene Ta Amince da hakan Ummin ce ta sakkon daga sama yayin da Dija da fa'iza suke biye da bayanta kara sowa tayi falon tana kallon Ali tace "kai kuma yashe ka dawo"? kallon Agogo dai ya kara yi Akaro na biyu sannan ya kalli inda umminnasa take yaca "ban jima da shigowa ba ummi kinyini lafiya"? "lafiya lau nayi ni ya Aikin"? "Alhmdulilah Ummi. " ya fada "masha Allah Allah ya tsaremana ku duk inda zaku shiga" 'Ameen ummi" "gobe in sha Allah zamu tafi jahar taraba can jalingo ummi kiyimana A ddo'a " kallonsa ummin tayi tace " Addu'a kam kullum cikin yinta muke insha Allah zakuje lafiya kudawo lafiya" "in sha Allahu " Abbah ya fada yana kokarin canja tasha hankalinshi na kan tv fa'iza dake kusa da Abbah tun zamanta A gun kallon yaya Ali take cikin kayan sojoji sai taga kamar sojojin da suke gani A tv mussaman A tashar mbc 2 bakinta na rawa tace" yaya Ali ina wuni 'kallon inda yaji A na gaidashi yayi dan yasan muryar fa"iza ce Amma bai san sanda ta shigo falon ba sai waccan marakunyar ya gani tunda gurin zaman su daya da umminsa kallon f'iza yayi fuska babu yabo babu fallasa yace " lafiya lau fa'izan Abba " mikewa yayi tsaye yana kallon Nene wacce tayi gurum A zaune ta tsurawa tv ido kamar wata mai fahimatar Abinda suke fada 'yace "wai haka A ke yi An barni ko ruwa baza 'A bani ba in magana Ace duk wacce tazo sai dai tazama bora ni dai babu ruwana duk wacce tafi kyautatamin itace mowa A gurina" ko kallonsa Nene batayi ba domin ta san neman magana yake dariya yake kasa kasa wanda nene ce kawai ta fahimci Abinda yake kallon ummi yayi bayan ya mike yace " ummi kisa Na'ima ta kai min Abinci zanje nayi wanka " "to.ummi tace 'kan tarufe bakinta ma sai ga Na'ima sun fito ita da siyama dama sallah suka shiga yi jiki na rawa Na'ima take kallon Ali wanda ya ke kokarin fita daga falon tace " yaya Ali barka dare Andawo lafiya"? yana kokarin sanya takalmansa yake Amsawa "ita kam siyama jikinta ne ya mutu tun lokacin da taga Ali cikin kayan sojoji domin bakaramin kyau su kayi masa ba sai. taga kamar bashi ba domin Allu Arjun ya ko ma mata na kasar hindu dan haka da wani irin mayataccan kallo ta bishi har ya fice da ga falon bata samu damar gaisheshi ba domin kasa motsa bakinta tayi sabida tsabar mutuwa da jikinta yayi jiki A sanyaye Siyama taje tasamu guri ta zauna zuciyarta sai wani irin bugawa take jikinta yai bala,in sanyi sabida wani irin kwarjini da yaya Aliyu yayi mata kallonta Ummi tayi tace " Siyama zo muje ki kai wa yayan ku Abincinshi domin Ummi bazata tura 'Na'ima ba kamar yadda yace Sabida dalili Siyama ita ce yafi dacewa ta kai masa domin ita yake shirin Aura 'tashi Siyama tayi har yanzu jikinta babu kuzari A ranta take fadin ga bikin zuwa Amma babu zanin daurawa dan ita yanzu shakkar tun karar yaya Aliyu take wallahi bayan Ummi tabi kchin din tana ta faman zancan zuci sai da Ummi ta kammala hada masa komai sannan ta kalli inda Siyama take tsaye tace ''gashinan ko" "to" siyama tafada tana tana kokarin daukar Abinci da Ummin ta hada cikin wani kwando mai kyau gabanta na faduwa ta fara bubbuga kofar dakin yana zaune gefen katifarshi daga shi sai gajeran wando 'wani irin gashi duk yayiwa fatar jikinshi rumfa dama tun Asali shi mutum ne mai gargasa A jiki tun yana yaro rigarshi yake kokarin ya jawo wacce take gefe A ajiye fitowarshi kenan daga wanka ya zauna yana tsane jikinshi da towol ya ji wayarshi tana kara shine ya zauna yana Amsa kiran wayar kafin ya saka rigar yaji An turu kofar dakin An shigo me zai gani Siyama ce A tsaye rike da kwando Abincinsa''ita kam siyama da taji An yi shiru ba 'a ce mata ta shigo ba shine kawai ta yanke shawarar shiga domin ita A tunaninta ko yana toilet ne sabida haka shine kawai tai tunanan bari ta shiga ta A jiye masa ta tafi domin har yanzu bata gama da wowa daidai ba tun ganin da tayi masa dazu Wani irin kallo Ali yake wa siyaman gashi ya tsareta da idanuwanshi masu rikirkikita mata lissafi'"fasa sanya rigar yayi ya mayar ya A je a inda take 'har yanzu idanunshi yana kan siyaman ya zuba mata su kawai bai ce komai ba Zubewa tayi A gun domin ji tayi gangar jikinta bazata iya daukar kafafunta ba wanda sukayi mutukar yin sanyi A sabili da irin kallon da Aliyu yake watsa mata 'ji take kamar wani magana diso yana fizgarta zuwa gareshi dan haka da rarrafe takarasa har inda yake zaune ta gyara zamanta sosai sannan ta sunkuyar da kai kamar wata mai mummuna tace " yaya Aliyu barka da dare An dawo lafiya ya Aiki" ? duk A lokaci daya tayi masa wannan gaisuwar har yanzu Idanunshi yana kanta yana nazarinta ganin yadda ta wani firgice lokaci daya 'shi yarasa meyasa suke firgita idan sun ganshi tunda shi ba wani shiga sabgarsu yake ba Amma yana mamakin hakan shiyasa yake mamakin irin Abinda Dija take masa kwata kwata babu tsoransa A idanta A yadda yake ganinta 'dazuma cikinsu babu wanda bai gaida shiba banda ita yana kallon lokacin da take ta faman harara fa'iza lokacin da take gaisheshi dauke i donshi yayi daga kan Siyama wace take zaune dabas A kafet din dake malale A dakin domin baza ta iya kallonshi ba A yanayin da yake ciki ba gaskiyar magana zata iya zuwa ta rungumeshi sabida ta shiga cikin wani yanayi shiyasa kwakwkwaran motsi ta kasa Muryarshi ta ji yo kamar baya so yace "me kika shigo kiyimin A daki dama ke nace ki kawu min Abinci "?? bakinta yana rawa tace "A'a ummi ce tace in zo in kawo maka" shiru yayi yaci gaba da danne danne A wayarshi tafi minti Ashirin A zaune A gurun sannan ya dago kai yana kallonta yace ''zaman me kike yimin A daki har da wani tankwashe kafafu dan ubanki" Jiki babu kwari siyama ta mike daga gaban yaya Ali ranta in banda tukuki babu Abinda yake ita tarasa yadda zatayi ta shawo kan gayan nan wallahi Amma babu damuwa Allah ya kai damo ga harawa wallahi in Ali ya shiga hannuta sai ya raina kansa "ita ka dai take fada A cikin ranta ko kallo bai bita dashi ba don shi A rayuwarsa ya tsani mace mara kamun kai wallahi shiyasa kwata kwata bata burgeshi siyaman sabida ya fuskanci itama tana daya daga cikin irin wannan matan A jiye wayar yayi gefe sannan ya jawo kayan Abincin yana dubawa fuska.A ya mutse dambun shinkafa ne wanda A kai masa hadi da kayan lambu sai hanta yaji kayan kamshi sai turiri yake kamar yanzu A ka sauke shi ' gefe kuma farfesun kifi ne shima da zafinsa sai hadin lemonsa nafa wanda kullum sai ummi tayi masa sai dai in baya gari' saukowa yayi ya tankwashe kafafunshi 'da kansa ya hada Abincin yadda yake so don ba zai iya yadda siyama ta zuba masa sabida ita ma bai yadda da tsabtar taba. To Acan falo rigima ce ta hautsine tsakanin Dija da Siyama 'siyama ce ta zo wucewa bata gani ba ta takewa Dija "yan yatsun kafarta ta 'ita kam siyama sam bata lura da kafar Dija A gurin ba sabida ba 'a cikin hayyacinta ta shigo.falon ba ta shi ne Dija tayi ta rike kugu tace ba zata yadda ba Sabida ita.ba dutse ba ce da zata taka ta don haka sai ta rama' dama gashi A cikin hadin zafinta take masifa sai cin ta take ' kallonta Siyaman take cikin mamaki ganin yadda Dijan take wani girgiza kamar wacce take fada da sa arta ' "ke Dija meye haka ki ke sa'arki ce ita"? Ummi tafada tana kallon Dijan "Ummi taka ni fa tayi kina kallonta ita me yasa bata kallon gabanta in tana tafiya ' ni dai kawai ta A jiye kafarta in rama in tana so .na bata hanya ta wuce " Dijan ta fada tana kuma kankane hanyar "wai ita lallai Siyama baza ta wuce ba sai ta rama Nene kam uffan bata ce ba ta zuba musu ido tana kallonsu ita tana mamakin tsiwar da take cin Dijan Na'ima ce ta taso A fusace tayi kan Dija gadan gadan tace "zaki ci ubanki wallahi "yar iskar yarinya mara kunya ' bata hanya ta ko in zab zab ga miki mari" ko gezau Dijan batayi ba tana tsaye tirmin danya tana magana kasa kasa " wallahi badai ubana ba kuma ni ba "yar iska bace " mari Na'ima ta kaiwa.Dija tace " Au! nima zagina zakiyi mara kunya eyi"? wani irin uban ihu Dija ta kurma wanda yasa Na'ima barin gurin babu shiri Siyama kam babu bakin magana 'domin bakinta ya mutu dama da tarin bakin cikin Abinda Aliyu ya kunsa mata sai gashi wannan marakunyar yarinyar tasa ta A gaba tana cin mutuncinta kamar wata sa'arta zama tayi gefe dan ita ma ihun da Dija ta kurma ya bata tsoro saura kadan tasaki fitsari A wando Nene kam ko A jikinta kallonta ma ta cigaba dayi kamar batasan Abinda A ke a gurin ba Na'ima kam ranta A bace ta fita daga falon ta nufi bangaransu.yaya Aliyu domin taga shine daidai da Dijan in tana ta kama da taurin kai da rashin kunya bugu daya tayi tajiyo muryarshi yana tambaryar wanene? "Nice yaya Ali" Na'ima tafada da sauri "menene"? yafada sabida ya fahimci muryar Na'ima ce cikin inda inda Na'ima tace "dama Dija ta tare hanya wai siyama baxata wuce ba sabida ta taka ta bata sani ba shine take ta zaginta Ummi ma tayi mata magana ta kiji sai rashin kunya take yiwa mutane" wata irin tsawa Alin ya kwatsawa Na'ima n yace "in kika sake na fito nan na sameki sai kar kar yaki wallahi kar finku tafi Dijan da har sai kunzo kun fada min iye" ? guda nawa Dija take 'stupid kawai" yafada ransa A mutukar bace '' sabida yaji lokacin da Dija ta kurma Ihun don yasan sai ita ba shiri Na'ima ta bar gurin tana tafiya tana zagin Dija cikin ranta ganin tana neman ta jawo mata salalan tsiya gurin yaya Alin wandon shi ya zira 3Quater sai singlet yabi bayan Na'ima ransa A bace hannunshi nan nade da blet sai faman huci yake A fusace yashiga falon yana bin su da kallo fuska A murtuke 'Dukannisu sunga shigowarsa Siyama ce da Dija basu ganshi ba sabida Dija na kan Siyama A tsaye rike da kugu sai faman rashin kunya take mata ita kuma Siyama n tana zaune kamar wata mai neman gafararta A i kam Ali bayi wata wata ba yayi kan Dija wacce ta bashi baya ' ya zabga mata blet din dake hannushi A sittin Dija ta juyo tana sosa bayanta kafin ta An kara ya kuma kai mata wani dukan wanda yafi nabaya zafi wani irin Ihu Dijan take kurma wa tayi kansa tana sosa cikinta dan ba karamin shiga jikinta dukan yayi ba 'kara zabga mata yayi A karo na uku ' Ai kamar wata filfilwa Dija ta je ta dane jikinshi tana kurma uban ihu wanda ya cika falon gaba daya kokarin cireta daga jikinshi .yake tana kuma ma kalkalemasa tana ta zun duma ihu ''tsigar jikinshi yaji tana tashi sabida irin cakumar da Dija tayi masa duk tabi ta cukwikwiyeshi ''numfashi ya dinga sauke A hankali ransa A bace ya finciketa daga jikinshi ya jefar da ita kan kujera ya bita ya kama hannunta na dama ya hau murdeshi cikin mugunta wani irin kuka Dija ta dinga yi gwanin tausayi ta na rokonshi da ya saketa baza ta sake ba Ummi ce da taga Abin yayi yawa tace " wane Abu kake ne Ali 'wannan Abin yayi yawa ka kyaleta haka " Nene kam bata ce komai ba dan rashin kunyar da Dijan take ita ta fara isarta gwara ya zane ta ko zata yi laushi shiyasa batace masa komai bugo da kari kuma.da ma tana jin haushin Dija n shiyasa tana ji ta tana neman taimakonta tayi mata banza farin ciki fal cikin zuciyar Siyama kamar ta zuba ruwa A kasa tasha dan dadi ""fa'iza kam sai faman kuka take taya Dija to babu bakin magana tana jin tsoron kar ya hada da ita'ita kanta Na'ima da ta kira yaya Aliyu n ta tausayawa Dijan ba karami ba' sai da yaga Dija tana shiri n shidewa sannan yasaketa 'fuska A murtuke yace da " Dijan tashi kije kibata hakuri " yafada yana kallon inda Siyama take zaune "farin ciki fal cikin zuciyarta Dija kam bata san yanayi ba domin jinyar hannuta take sabida wanin irin radadi da zogi yake mata ji take kamar "yan yatsunta sun karye sai sharben kuka takeyi "bada ke nake ba dan ubanki kitashi kije ki bata hakuri "marakunyar banza sa 'arki ce ita iye" ? Da sauri Dija ta daga kai tana kallon sa fuskarta jagab da ruwan hawaye wani hanzan kallo yake yi mata yace "wallahi duk sanda na kuma jin labarin kin yiwa daya daga cikinsu rashin kunya ko ki zagi mutum " ko basu bama inji labarin kinyiwa wani rashin kunya tunda ga kan baba mai gadi zuwa kan su haruna' da duk wan da 'suke shige da fice A gidan nan , sai na kar yaki na zubar da,banza kuwa ya huta tsit falon yayi sai shashshekar kukan Dija ne kawai yake tashi A gurin Ummi kam sai faman fada takewa Ali ganin irin yadda zage ya.lablabtawa Dija blet.kamar wani wanda yasamu gardi ko wanda yake filin daga""ita Ummi ko kallonta bai yiba 'don ga dukan Alamu Allurar ce ta mutsa tashi Dija tayi ta je gaban Siyama tace "Allah ya baki hakuri bazan sake ba" tafada kamar 'yadda Alin ya Umarceta da ta fada Siyama kam dadi duk ya isheta sai wani munafikin murmushi take yi 'cikin kissa tace ''yawuce Dija nasan kuruciya ce take damunki ,dan Allah ki dai na raina na gaba da ke kinji ko " Banza Dijan tayi mata cikin ranta tana tunanin Abinda zatayi mata ta huce tashi tayi zata bar gurin Ali ya buga mata tsawa 'yace koma ki zauna A nan'" komawa tayi ta zauna kusa da siyaman tana kallonsa cikin yanayin tafiyarshi ya karaso gurin daga Siyaman har Dijan tsuru'tsuru sukayi suna kallonshi Siiyama gabanta sai faman bugawa yake tana tsoron kar yace fa zai 'dake ta itama dukansu binshi da kallo sukayi yayin da yake tsugunawa A gabansu 'fuskarshi babu digon Annuri ko kadan kallon Siyama yayi yace "kinji kunya kinji kunya da kike fada da kanwar kanwar bayanki. 'sabida haka wannan yazama shine na farko shine na karshe " cikin rawar jiki Siyama tace " in sha Allah haka bazata kuma faruwa ' kayi hakuri ya Ali" dauke Idon shi yayi daga kan Siyama ya daura kan Dija wacce ke rakube A jikin kujera rike da hannuta wanda yake tayi mata bala,in radadi da zogi cikin ranta take Addu"ar Allah yasa bai karya mata "yan yatsuba Nazarin ta yake yana murmumshi cikin ransa ganin yadda bakinta ya mutu lokaci daya yau babu murgude murguden baki gami da kunkunin da ta saba yimasa' kallon Siyama ya kuma yi A karo na uku ya kalli inda Dija take zaune sannan yace "'mare ta sau uku" yafada cike da bada umarni 'ida nunshi tsaye A kan Siyaman Zare ido Siyama ta kama yi tana kallon Ali cikin mamaki domin batayi zaton zai yan ke wannan hukuncin ba Ummi dake gefe A zaune tace" wannan kuma shine A binda bazai yuhu ba 'ya zaka zane yarinya kuma kasa A mare ta duk duk dukan da kayi mata bai ishe ka sai kasa An dake ta dan mugunta " shiru yayiwa Ummi bai ce komai ba ya cigaba da kallon Siyaman yace "'mudun baki yi A binda nasa ki ba to babu makawa zan sa ita Dija n ta mareki " Dija kam tana gefe sai faman sharben kuka take cinkin ranta kuwa sai tsinewa Ali take '.gami da wata irin tsanarsa da taji tanayi A cikin zuciyarta fidda hannu Siyama tay babu zato ta tsinkawa Dija mari 'kafin ta An kara ta kuma kai mata wani haka har sai da ta yi mata mari uku kamar yadda ya Umarce ta da tayi ita kanta Siyama duk muguntarta sai da ta tausayawa Dija ganin irin A zabar da Ali yayi mata lokaci kankani 'gashi yasa ta mareta' tasan halin Dija ba zata ta yadda ba komai daran da dewa ' to bata da yadda zatayi ne tasan tunda yace zai sa ita Dijan ta mareta in ba tayi zai Ai kata shiyasa ta mareta sabida tasan in Dija n ce ko ba 'asata Abu ba tanayi ballanta An sata sabida haka jikinta A sanyaye ta A jiye hannuta tana jiran karan batta da za suyi da Dija don ta san ba yadda zata yi ba Tashi daga gurin yayi ya tsallake Dija dake zaune rike da kuncinta tana kuka ' mai ban tausayi 'fa'iza ce ta taso da gudu tazo ta rungume Dija n tana kuka ' itama Na'ima kam bata ce komai ba Amma ranta ya 6aci ganin yadda Siyama ta fidda hannu ta zab zab gawa Dija mari ko tausayi babu 'tai da tasanin kiran yaya Alin don bata yi tunanin irin hukuncin da zai yimata ba kenan ' ganin ba ya dukansu yake ba in sunyi 'laifi hunkuncin su kawai yasa su daga hannu ko tsallan kwado gurin su Dijan ta je ta mikar da ita takamata ta rungume ta tana rarrashinta tace " kece Ai bakyaji wallahi 'don Allah ki rage rashin kunya da tsiwa 'ki daina raina na gaba dake kinji ko" banza Dijan tayi mata cikin ranta tace ba ke kika jawo min ba tunda ke kika kirashi Allah ya isa ban yafe ba tafada cikin zuciyarta domin tana tsoron maganar ta fito Na'iman takara ji taje tafadawa yaya Alin shiyasa tai shiru da bakinta' harara Nene ta bisu dashi tace " munafurcin banza 'meyasa lokacin da yana dukanta baki zo gurinba kin ceceta iye" babu A binda Na'ima tace ma Nene suka wuce ko ' kallon Siyaman batayi ba domin bala'in haushinta take ji domin duk son da take mata ba kamar Dijan ba domin hausawa nacewa wata kusan tafi wata haka Na'ima tahadawa dija ruwan zafi ta gasa Mata jikin ta 'sannan tasa mata Robb A hannayenta duk ta mutstsike mata in da yake zogi. Ummi ta kalli in da Nene ke zaune'tace Nene kina kallon A binda Ali yayiwa mutuniyarki baki CE komai ba'' "yo me zance ai ita ta jama kanta da rashin kunya, in banda A bin dija duk girma irin na Siyama tace zatayi fada da ita'sabida tsabar tsaurin idon ta 'ai gwara da ya Zane mata jikin ta gaba bazata kuma yiwa wani haka ba" Murmushi ummi tayi tace "yau kuma haka zaki CE Nene ke da 'mutuniyar taki" ''wane mutuniyata kina. Ganin gaba take da ni sabida nace baza ta zauna A nan ba'' Nene tafada tana riqe ha6a Dariya ummin take ganin yadda Nene take nema ta mai da A bun Babba' " tace wannan kuma tsakaninku ne ba mai shiga tsakaninku duk Wanda ya shiga tsakaninku shi zai ji kunya" "A da ba Amma. Banda yanzu yarinyar da take guduna fafur Ai na bar mu Ku ita " Nene Tafada tana ta 6e bakinta Cikin Murmushi ummi n tace "Alhamdullih Allah ya tayamu riko '''Ameen " Mai da kallonta tayi kan SIyama 'wacce ke zaune gefe jikinta A sanyaye domin ita kanta tasan ba ta kyauta ba"""to Amma Ai yarinyar ita ta jawowa kanta Don haka ko gobe 'ya kara cewa ta mareta sai ta mareta''domin ba karamin tsanar yarinyar tayi ba Ummi tace " haba Siyama ko kara babu 'ki daddage ki dinga Marin yarinya iye"? Cikin jin kunya Siyama tace "Ummi kina jin Abinda yace fa cayayi in ban mare ta ba zai sata ta mare ni'' Nasan tun da Ya fadi haka zai Ai kata. ''Kuma nasan halin ,Dija tsab zata mareni shiyasa" Kwafa ummi n tayi tace " Ai shikkenan Kece A wahale tunda kece matarsa sai kije ki ta Abinda kika saba 'Amma ki sani shi namiji duk ta inda ka bida shi da haka yake tashi sabida haka sai ki . Zauna kiyi nazarin wane irin miji zaki Aura Maganganu ummi tagaya mata masu A Lamar jirwaye me kamar wanka "Insha Ummi zan Kiyaye da Abinda kina CE" Siyama tafada 'tana kokarin tashi daga gun Kallon Nene tay tace '' ran uwargida na ya Dade kina ta gyangyadi A zaune kije ki kwanta mana" Gyara zama Nene tayi A kan kujearar ida nunta A kan Siyama ''tace yanzu kuwa zan tashi "yar nan" To "Ummi sai da safe Siyaman tafada tana Barin gun " cikin walwala da farin cikin domin ji take kamar wacce A kayiwa Al bishir da gidan Aljanna ' yau ta sauke baciran da dija take had a mata shiyasa take jin wa sai A cin zuciyarta To Allah ya tashe mu lafiya Karfe biyar shaura na Asubah Ali ya fito domin zuwa masallaci'sai da Ya tsaya ya tashi jamel sannan ya wuce masallaci'A can suka hadu da Abba To cikin gidan ma hakane duk sunyi sallah 'sallahr Asubah bata wuce su 'sai Abba ya tabbatar da kowa ya tashi. Yake wucewa masallaci wannan shine Abu mai kyau *Allah kasa mu dace* Anyi Anyi da Siyama taki tashi ba yadda Na'ima bata yi da ita ta tashi ba Amma taki haka ta hakura ta kyaleta ta koma ta yi kwanciyarta Duk Abinda yake faruwa A'idon Dija domin da'ta idar da sallar bacci bai dauke ta. Ba sabida haka tana jin nacin ' da Na'ima take Wa siyama A kan ta tashi taje tai sallah taki tashi' Sai da Ta tabbatar 'bacci ya dauke Na'ima' sannan ta'ta tashi Cikin Sanda ta nufi 'friji' da ke gefen gadon da Siyama' take kwance' ta' ta dauko Ruwan' gora mai bala'in sanyi Dan har ya soma yin kan kara ' ta ' bude 'ta dai dai ci' fuskar siyaman 'ta. Hau zuba mata shi A gigice Siyama ta tashi 'tana rike fuskarta' domin ji tayi kamar An daura mata' kankara A fuskarta' sabida nauyin da ta yimata'' Dago fuskarta tayi ganin 'I nuwar mutum A tsaye A kanta me zata gani' Dija CE rike da robar ruwa A hannuta' ta zuba mata 'ido tana yi mata kallon ' wana kama "Ke wane Dan iskan ne yace ki wa TSA min ruwan me kankankara A jikina iyi"? Shiru Dija tayi mata bata CE komai ba' sai da ta kuma mai maimaitawa' sannan 'dijan ta magantu' Kai tsaye Tace ''yaya Aliyu ne yace A tashi ki kiyi sallah ' kowa ya tashi yayi ban da ke wai Nan ba gidan 'Ar na bane'' Kan ta Siyama n tayo tace " zanci ubanki ''wallahi makaryaciya 'banza yaushe yaya'Ali yashigo da zaki 'masa karya' yau zanga uban da ya tsayamiki A gidanan" "Wallahi badai ubana Ai uba baifi uba ba Dan 'haka A dai na zagar min iyaye na domin 'ni nasan Mutum cinsu" Cikin bacin rai' Siyama ta kaiwa DIja wani ba hagon mari tana fadin ''Dan uwarki ' karki sake hada 'iyaye na da naki domin 'iyayena sunfi Naki komai jahilar yarinya 'yar kauye kawai" Saurin kaucewa Dija tayi 'Marin da Siyaman'ta' kai mata ya bi iska ma tsawa tayi baya ta tsai da idanunta kan Siyaman ' sannan tace "Ai mun San komai 'Ai fa'iza tace ma dady' din naki ma Dan 'Aiken Abbah ne' kullum sai yazo Maula gun Abbah" A fusace Siyama ta nufi 'Dija ta rufe ta 'da duka ' ko 'ta 'INA Ihu Dija take kurma wa' na ne man dauki A gigice Na'ima ta tashi tana mutsika ido ' tana son taji daga INA take jin kuka' sai taji kamar kukan 'Dija "Wayyo ya Na'ima zata kasheni ki CeCe ni'' Saurin kallon gadon Siyama tayi 'domin A nan ta me jiyo kukan Me zata gani Siyama CE ke ta faman dukan Dija babu ji babu gani Da A zama Siyama ta karasa gun tana Kokarin ' janye Dija wacce ke kawance kasa tana kokarin shigewa kar kashin gado 'ita kuma 'Siyama ta kama gashin ta 'ta rike sai faman ja take' ita kuma. 'Dija' sai zaginta. Take ta Uwa Ta uba Ba zato suka ga 'Ali A gabansu Dan dukan su ba su ji shigiowarsa ba Kallonsu ya ke daya bayan daya 'fuska babu Annuri ko kadan Ga Siyama rike da gashin Dija A hannu tayi tsili ttsili ' ita ma dijan tsuru-tsuru tayi tana zare 'ido min har yanzu bata gama watsakewa daga dukan da ta Sha jiya ba Kallon Na'ima yayi wacce ke tsaye ita ma tana zare ido 'yace me ya hadasu"? Bakinta yana rawa tace "wallahi bansani ba ma nima bacci na ke yi suka ta she ni" Mai da kallonsa yayi kan siyama wace har yanzu kan Dija yana rike A hannuta ta Kasa saki "Me ya hadaku"? In da In da ta fara ''um ''um zuwa tayi ta watsa min ruwan sanyi ina bacci " ta fada cike da rashin gaskiya hannuta ya kalla Wanda ke rike da gashin Dija' yace ' " cika mata kai '' cikin Sauri ta saki kan don ita ta manta ma tana jama Dija gashinta "Me na CE dake jiya iyi"? Ke wace irin mace CE Mara kamun kai yanzu ke baki ji kunya ba kina fada Da kanwar,kanwar Ki"? Sun kuyar da kai siyama tayi " Tace 'kayi hakuri' bazan kara ba'' banza yayi da 'ita 'ya mai da kallonsa kan ' Dija fuska A hade yace "wato ke ba kyaji ko? Meya sa kika watsa mata ruwa 'A jiki iyi"? Cikin kuka tace ''ban wa TSA mata ruwa ba tashin ta nayi tayi sallah 'ganin kowa ya tashi yayi 'shine. Ta tashi take ta zagina na wai iyayena talakawa ne sannan "yan kauye ne ja hilai ne" "Wayyo kai na yana yimin ciwo Dan Anga in marainiya CE shine A keta cin zalina Allah sai ya saka min " tafada cikin gursheken kuka Wanda sai da ta ga ,Alin ta kirkireshi Ranshi yaji ya na masa zafi 'ganin yadda Dija take kuka 'ya tsani kuka A rayuwarsa ' sai yaji kukan da take yana taba masa zuciya Kallon ta yayi yace " tashi daga gurinan "tashi Dijan tayi tana kuka A hannuta rike da Kanta ta nufi hanyar fita da ga dakin " Cikin tsawa Ali yace INA zakije A haka dawo kisa Dan kwalinki " Dawo wa tayi taje ta dauki hular rigar baccin da ta ke jikinta ta sa ,,ta kama hangar fita daga dakin "Koma ki zauna " yafada A karo na biyu yana dauke ',,, ido daga kanta Dan wani irin yanayi yake ji A jikinshi in ya kalleta A haka ,domin kan shi babu Abinda yake birgeshi A jikin mace kamar ,gashi' da kyakyawar sura ,,to ya fuskanci duk yarinyar ta Tara A bubu wan gashi dai karama CE Amma Alamar karfi A Na ganewa Kallon Siyama yayi fuska A murtuke yace "kina nufi har yaanzu baki sallah ba"? Sun kuyar da kai tayi bata CE komai ba Kwance blet din dake daure A jikinsa yayi domin dama cikin shirin fita yake ba zato Siyama taji saukar duka 'A jikinta 'domin kanta A sun kuye ya ke A gigece ta dago kai tana kallon Ali ' kafin ta dawo dai dai ya kuma shinfida mata wani dukan Dur kushewa tayi A gurin tana Sosa jikinta Dan ba karamin shiga dukan yayi mata ba bai bari ta gama watstsakewa ba ya kuma shinfidama ta wata Sai da yayi mata sau shida masu Shiga jiki sannan ya kyaleta ' ya mai da blet dinshi ' jikinshi hankalinshi kwance, Tana zaune A gun tana hawaye ya kalleta Fuska 'babu walwala yace " wannan shine hukuncinki na kin yin Sallah 'A kan lokacin ,daga yau A kuma tashin. Ki kiyi sallah ki ki tashi 'dukan da zan miki sai yafi wannan Domin nan gidan musulumai ne ba na Arna ba " Shiru Dakin yayi ba ka jin komai sai sautin kukan Siyama zuwa sannan lokacin gari ya soma wa shewa da ga duhun Asubah Ko kallonsu bai kuma yi ba ya fice daga dakin yana Jan tsakii Tsaki Na'ima taja bayan Ali' ya fice daga dakin ' tana kallon 'siyama' tace " wai me yake damunki ne sis"? "Kamar ki ki tsaya kina fada da 'karamar yarinya kamar 'Dija wacce kuriciya ke da. Munta ' Ai ko wani Abin tayi miki ba kya yi kokawa da 'ita ba ' wannan Ai zubar da girma. Ne" Wani kallo siyaman take wa 'Na'ima tace " A binda zaki CE.) Kenan kema"? "To me kike so in CE bayan wannan 'iyi" ? "Ba kiga irin ta shin da nayi miki ba 'domin kiyi sallar Asubah Ki ka ki kowa ya tashi banda ke Ni kam 'Dija tayi min dai dai wallahi da ta wa tsa miki ruwan" Na'ima tafada hankalinta kwance Don bakaramin 'dadi taji ba 'ganin Ali ya Zane ta'' Tun ba'Aje ko INA ba 'Al hakin Dija yakamata. "Kwarai kuwa Ai gwara ki nuna min cewar Dija Jininki CE dole ki fifita ta A kai na Na gode Na'ima " siyaman tafada Ranta A mutukar bace "Ba haka bane sis , kece wallahi da A bin haushi 'A CE kamar ki bakya yin sallah A kan lokacin sai rana ta fito 'ko kunya ba kyaji wannan ba dai dai bane wallahi kinsa '',dole in gaya miki gaskiya 'domin haka tunda zaman Amana ne A tsakanin mu..................... "Eh gwara ki ci mun mutunci tunda kin ganni A gidanku 'duk A binda kukayi min ba laifin Ku ba ne 'nawa ne tunda ' ni na kawo kai na, Wai kamar ni Ali' zai zage ya Zane da blet A gaban yara, Wannan 'wulakanci da me yayi kama " Wata dariya CE ta su6ucewa 'Na'ima ba shiri ta dinga kyakyatawa dama ta Dade tana kunsheta' taki yi ne don' kar Siyaman taji haushi 'Amma yanzu Kam ba zata 6oyo ba Sai da tayi mai isarta su Dija suna taya ta ita Da fa'iza. Domin ita ma A gaban idon ta komai ya faru Kallon Siyaman tayi tace " Allah ya baki hakuri sis kinga da tun lokacin da nake tashin ki ne kin tashi da duk haka ba ta faru ba'' gashinan" kinsa A n Zane ki babu Gaira babu dalili " Banza Tayi da ita da ta fuskanci 'zolayar ta take Ta yun kura ta tashi 'tashi ga 'toliet domin jikinta yai bala'in zafi da radadi da take Mata dama fatar ba wani kwari ne gare ta ba kasan cewar tasha 'bleecing da sabulai Masu masu karfi da ta ke Amfani dasu Sai da suka tabbatar ta shige 'toilet din suka kyalkyale da dariya, Dija har da faduwa daga kan gado, tana gwada yadda Siyama Ta dinga Gan tsarewa lokacin da yaya Aliyu yana dukanta " Zan ci ubanki 'Dija wallahi in baki bar wannan Dariyar ba duk ba ke kika jawo mata iye"? "A,a wallahi ya'Na'ima ita CE dai ta jawo wa kanta da taki tashi tayi sallah da kuma Al hakina bata na jin dadi back jiya A n dake Ai Allah ba Azzalimin sarki. Bane 'gashi Allah ya sakamin Nima" "Kwarai kuwa hakane Dija" "Ammafa 'INA kuma gargadinki' kirage gashin kunya da tsiwa kinji ko kuma daga yau 'kar ki kuma ,raina ta ' tunda ba sa'arki bace ita " "To ya Na'ima bazan kara ba in sha Allah ' in kawai ji nayi na tsaneta wallahi shiya na ke raina A mma daga yau bazan karaba " "Yauwa kanwata. Daga yau 'tsanar da kike yi mata ma ki dai na kinji ko' domin,(Annabi Muhammad Slw ) yace duk inda musulmi yake Dan uwan musulmi ne yace kada musulumi ya 'kyamaci" Dan uwansa musulmi ' sabida haka ki dai na babu kyau ki dinga karrama 'Dan Adam ko Da ko baki San . Shi ba" "To ya Na'ima in sha Allah Bazan karaba '' "yawwa shiyasa nake sonki kanwata sabida kina jin magana ta ' ku kuma kuyi kwanciyarr ku zuwa bakawai Sai in tasheku ke fa'iza kin San A kwai skull ko"? "Eh ya Na'ima" " to'kar kiyi bacci mai nauyi ''Na'ima tafada tana gyara kwanciya ita ma domin ita kam Allah yasa mata son bacci A rayuwarta '. Domin wani lokacin ko karyawa batayi da safe tana can tana faman bacci Sai ta tashi sannan. Take kar yawa wani lokacin kuma sai dai taci Abincin ' rana kawai To Aliyu' bayan fitarshi daga dakin su Na'ima kai Tsaye sama ya nufa dakin Ummi A gurguje domin 'karfe shida ta wuce tun dazu yana fitowa daga masallaci' ogansu' yake ta waya ,ya fito da wuri Domin baya San takwas tayi basu bar garin ba. A gurguje suka gaisa da 'ummi tana ta yi mishi Addu'a tace " baza ka tsaya ka karya ba sanan " "A,a ummi nasha lipton ya isa kamar ya ,isa" "tsaya in dauko maka shauran dabun nama da ma yau nake cewa ' zan hada wani sai kata fi dashi'" "Ok ' ummi da kin barshi ,bazamu rasa A binda za muci ba" " A'a gwara kata fi dashi' in kai baza kaci ba Ai Akwai masu ci tun da kuna' da yawa ko"? "Hakane ummi" yafada yana duba A gogon da ke daure A hannushi " "Bari mu gaisa da Nene " yafada ' yana kokarin sauka daga kasa itama bayansa tabi suka sauka tare cin karo sukayi da Abba ya dawo daga massalac dama shi ka'ida ne ' baya shigowa sai gari yayi haske sai yayi Azkar sosai A massalacin 'sannan yake dawo wa gida A kwai mabukatan,da suke kawo masa kukan rashi da na wannan yanayin rayuwa da muke cikibna tsabarta lauci da rashin Abinyi' don' haka " yana zama' yayi ta' rabon kudi' dan wani' lokacin ma har kayan Abinci yake sawa 'A fita r dashi ga mabuka ta Kai tsaye ummi kchin ta nufa ta barsu suna Anan suna kara gaisawa "har ka fito kenan?" Abban yafada yana mika wa Ali hannu domin suyi musabaha "Eh wallahi' in banda 'lyara nan sun tsayar dan Ai da tuni mun yi nisa A hanya Rigama natarar dasu sunayi har da ko kawa'' Kallon sa Abbah yake yana mamakin wane yara ne suke rigima har da kokawaA junansu' shidai ya san ba tarbiyarsu Na'ima bace haka "Wan yara ne wannan?" Abban ya fada yana kallon Alin ,tsaki Ali yaja yace " waye in ba wannan ,yarinyar ba ita da Siyama sosai rigima suke tun jiya taki karewa" Cikin mamaki Abba yace "Siyaman ce take ko kawa da 'Dija' dan zubar da girma'? Tabe baki Ali yayi yace "kwrai kuwa " "to' meya hadasu"? In jiAbbah murmushi Ali ya yi shifa Dija ta birgesh wallah da tayiwa Siyama haka yaji dadin watsa mata ruwa da' tayi in ban da' rashin tarbiya kamar Siyama A ce bata yin sallah A kan lokaci' sai da rana ga tse ga tse Tsaki ya dan ja kasa - kasa yace ''ita Dijan ce ta watsawa ,siyama ruwa wai ta tashi ' tayi sallah, kowa ya tashi to shine siyaman ta hau dukanta'' Dariya Abbah ya saki yace" Amma yarinyar nan ta burgeni'Ai haka Ake ma' irinsu Siyama suka qi tashi' ta dadi' rai' in suka ji su' A cikin danshi Ai kaga sa tashi dole ko'' Girgigiza kai 'kawai Ali yayi bai ce komai ya kama hanyan dakin Nene Tana zaune A kan sallaya haannuta rike da carbi ' ya shiga dakin' cikin' sallama' gyaran murya tayi tayi masa Alama ya zauna tana nu na masa ta kusa kammalawa Murmushi yayi ya samu gefen daddumar da take kai ya zauna hade da ciro wayarsa faruk yakira bugu daya ya daga ya ce "ya akayi ne' kafito ne"? "Eh gani Akan hanya kaifa''? Faruk din yafada "Ga nin gurin Nene bata gama sallamata ba' har yanzu'' Alin yafada Dariya faruk din yake yace kami kamin gaisuwa gun uwar gidannan ka" "Ok ' zata ji in sha "Allah nima yanzu zan fito' in sha Allah " Kashe wayar yayi yana kallon Nene wacce ke kokari cire hijab din da tayi sallah da shi' tana kallonsa tace " badai har ka fito ba"? "Eh man ')Ai lokaci ma ya kure' mun so mu fita cikin dare ko da A subah hakan bai yu wu bah " "Hakane Nene tafada tana girgiza kai tace wannan Ai kin naku Ai sai Addu'a da ku wane' lokaci kuna tsaron rayukan jama'a ni ban san wanda yafi' wani taimako ko da ma'aikatan 'Asibiti Allah dai ya tsare ma na ku A duk inda zaku shiga" "Amen ya Allah my love dina " Alin yafada fuskarsa cike da da riyar da ya dade bai yi irin ta ba' Harara Nene ta maka masa tace '' wace ce kuma my love A na zaune 'lafiya"? Dariya ya saki yace "Ai kinji irinta ke baki iya soyayya ba dan na ce miki my love kike harara ta ina da wata ne bayan ke" "A'a bana so Ni ba Ar ni ya bace ka dai na ki rana da sunan Arna to kaji'"! Me Ali zai yi in ba dariya b sai da yayi mai isar sa sannan yace " toum shikkenan kada 'in kawo Amarya ta kiji 'l ina kiranta da haka kice, ban miki A dalci ba babu ruwa " Ita ma dariyar take tace"e naji din kuje ku karata da in dai za kai Adalci Ai shi kenan" Girgiza kai yayi yana 'cigaba da dariya shi kam yana bala'in kaunar kakarshi Nene kamar yadda take kaunars da damuwa Al' amarinshi' shiyasa baya iya sakewa da kowa' in ba ita ba zai zage yai ta zaulayarta yana kwasar dariya' domin ' ita ke ganin dariyarshi' A arha "Kin ga kin zaunar dani zaki sa na kara bata lokaci na ko gaisawa,ba muyi ba kin fara rigima " Yafada yana kallon A goga hannusa "Ka tashi ka tafi ga faruku can' yana jiranka ko bada shi' zaku tafi bane ?" "Tare zamu muna da yawa sosai Ai ba shi kadai bane " yafa da yana mikewa ita ma mikewa tay' ta biyo bayanshi tana ta faman yi masa Addu'a iri -iri A gurguje ya karbi tarkacen kayan da ummi ta hada masa naci kamar wani ,yaro shi kanshi' yana mamakin,yadda umminshi take kula,dashi sai ta tabbatar da yaci Abinci hankalinta yake kwanciya shiyasa bashi da'Abinda zai saka wa da iyayenshi da shi' sai Addu'a Sai da suka rakashi har gun motarsa suna yi mishi Addu' a sannan suka koma cikin gidan *to Aliyu haidara Allah ya tsare Allah yabada nasara* Misalin bakwai da rabi Aliyu ya shiga brack din nasu dukkanninsu suna tsaye ,A jere ogan yana kuma horar dasu cikin sauri yayi faking din motar ya fito yakarasa gurin ,Akaciga ba da yi dashi Sai bayan sun kammala sannan sukayi Addu'oi suka dau hanya cikin shirin ko 'lta kwana, jikin su sanye da bindigogi To A can gida kuma Cikin sanda'Dija ta ta shi tana yiwa Siyama dariya har da gwalo bayan ta tabbatar da bacci ya dauke Na'ima sarai siyama ta fahimci Abinda take mata Amma sata kyale ta cikin ranta tana saka irin hukuncin da zata dauka'Akan Dija dominwallahi ko za tai yawo tsirara sai ta sabautawa Dija rayuwa sai taga da wanda take'taqama, A doran duniyar na Fita tayi Daga dakin tana cigaba da Dariyar da take babu Abinda yadameta dakin Nene ta nufa tana cigaba da dariyar cikin walwala Cikin mamaki Nene take kallon Dija"tace ke kuma meye yakawo ki inda nake har kin gama gabar da kike dani?" Zun bura baki dija tayi tace "yaushe nake gaba dake kece Ai nace kiyi hakuri ki barni kin ki sai da kika sa wannan mugun ya daken kina kallonshi baki hana shi ba" Dariya Nene tayi tace" ai naji ' dadi daya zane miki ' jiki 'ai rashin kunyar ki tayi yawa babu babba babu yaro duk baki kyale ba'' Shan kunu Dija tayi tace "Ai shima nai masaAllah ya'isa ban yafeba tunda ni ba jaka bace da zai ai ta duka na dan yaga ni marainiya ce kuma itamaSiyaman Ai ya dake ta dazu da Asubah sauran Ya Na'ima itama sai nasa dake ta tunda ita ce taje ta kirashi A lokacin" Cikin mamaki' Nene take kallon Dija " tace kina nufin kece kikasa Aliyu ya daki Siyaman'?" "Eh man kin tashi tayi tai sallar Asubah kowa ya tashi ni ko naje na watsa mata ruwa shine ta tashi ta hau zagina ta hau kaina ta dinga duka '' "Ni kuwa nai ta kurma' ihu har sai da yaji',ya shigo dakin shine ya Na'ima take gaya masa shine ya zane ta ita ma " Dija' ta karasa maganar tana ta kyalkyala dariya har da kwanciya Sakin baki Nene tayi tana mamakin Dija hannuta Akan ha6arta tace yanzu Abinda ki kayi kenan ko D'ija" Tana cigaba da yin Dariya tace "Allah ne ka wai ya sa kamin Ai bani na kirashi' ba da kuma Alhakina'' "Umm "!to Allah ya shirya ki Dija" Nene ta fada tana kara mamakin Abun "Nene Amma kin hakura da tafiya ko? " "Aa gobe ko jibi' zantafi' ke ai tunda kin nuna kuna son zama anan din Ai shikkenan gaki ga'Aliyu' nan in kika cigaba da wannan halayen naki duka zaki dinga ci A gurinshi babu Abinda ya dameshi to" kaji" Ta6e baki Dija' tayi tace "yo' ni ina ruwana da shi Ai ba kula shi nake ba ,ni din ce kawai ya tsana yake duka na ai baya dukan su fa'iza' da ya Na'ima" "Ke ma bai tsane ki ba halayenki ka kwai ya tsana kuma ki sake ki cigaba da yi mishi fitsara da rashin kunya da kai na zan sa shi ya zane ki " Shiru Dija tayi bata ce komai ba 'Amma fuskarta babu walwala Nene taciga ba da cewa "kuma saura A saki a makarantar kije ' ki yi ta shirme da shiri,rita wallahi ki tsaya kiyi karatu da kyau' domin baki da gatan da yafishi In kuma kika qi dama 'Alin zan dinga sawa ina daga' can ya dinga zane' miki jikinki to' kaji" Nene ta fada tana sauke numfashi' Zumbura baki' Dija tayi tace "duk kun bi kun tsaneni Yanzu harda ke Nene 'l kin dai na sona yanzu kinfi son ya'Ali yanzu" Harararta Nene tayi tace "Ai se kiyi Ai tun ba yau ba nake miki fadan yawan fitsar da rashin kunya da kike tunda yanzu na samu mai ladabtar min dake Ai haka na ke so" Sai da Nene tagama tsorar da Dija A kan cewar in dai bata dai na haleyenta ban tanabdaga can zata dinga yiwa Ali waya ya dinga dukanta duk Abinda tayi Sannan ta mike tayi tafiyarta falo ta bar Dija cikin wasuwasi da faduwar gaba tana jin ko kawai tabi Nene su kuma can domin tana bala'in tsoron dukan da yaya, Aliyu yake mata gami da murmurde mata hannaye da yake' wanda duk sanda yayi mata wannan A zabar hannuta yana dadewa bai daina radadi da zo gi ba Wata zuciyar tace Ai ba kula shi kike ba kuma in ya da ke ki ba sai kiyi masa Allah ya isa b Haka tagama saqe - saqen ta ta tashi tabi bayan Nene falon domin tun dazu take jiyo hayaniyar su Na'ima da siyama kamar masu fada Suna zaune kan dannig kowa yana kokarin hada Abinda zai ci yayin da' fa'iza ke tsaye cikin unipom tayi shirin zuwa 'skull Kallonta Abba yake har ta karaso gurin yace ''zo nan'' Dija zuwa tayi ta dur kusa tana gaishe shi ,cikin sakin fuska yake Amsawa yana kara jin son yarinya A cikin zuciyarsa shi duk wani ' rashin kunyar ta' da ' Ake fada bai da meshi ba tunda ya tabbatar da kuruciya ce in ta girma zata dai na "Ummi ina kwana" Dija tafada "lafya lau Dija kin tashi lafiya?" "Lafiya kalau ummi '' "A she ba bacci kike ba' Ai nazata bacci ki ka koma ganin tun dazu ' Nene ta fito daga dakin" "Bacci ne yaki zuwa shiyasa na fito ummi " 'Dijan tafada gyara kujera tayi ta zauna itama tace '' ya Na'ima ina kwana'' Cikin mamaki Na'ima take kallon Dija' yau ita Dija ke gaisarwa ta6 lallai za'ai ruwa da kankara Ita ma 'Na'ima cikin sakin fuska ta Amsa tace "yau ni kike gai sarwa kuma lallai nasamu babban matsayi' yau A gidanan" Zumbura baki Dija tayi bata ce,komai ba ta dau cup tana kokarin hada tea Dariya Abbah yake yana kallon Na'ima yace " da bata gaisheki ne? Bana son sharri fa" Tana Dariya tace "ta6 Abbah Dija ce ta ke gaisheni Ai ko zuwa mukayi gidan Nene bata min magana har mu baro garin sai taga dama take kulan tafi kula jameel sai kawarta kaga ko dole inyi mamaki Abbah" Da murmushi A fuskarsa ya dago kai yana kallon fa'iza wacce ke tsaye kusa da Dija suna magana kasa,kasa yace "fa'iza na me kika tsaya jira maza ga Haruna can yana jiranki kar ki makara " kallonsa fa'iza n tayi tace "to Abbah " kamar zatayi' kuka tace yaushe za akai Dija skull din iyi?" "Mondey insha Allahu jameel zai je yagama komai ki kwantar da hankalinki Auta na kinjiko" dariya fa'iza ta saki tace "to Abbanmu" sannan ta kama hanya ta tafi' "Allah ya Bada sa'a " ummin tafada Nene kam ranta A bace yake ganin,irin Abinda Dija tayi yanzu ta gaida kowa Gurin ba ta gaida siyama ba wannan, Ai raini ne sabida haka cikin bacin rai ta kalli Dijan tace "ita kuma siyama, me tayi miki da baza ki gaida ta ba duk da dukan da kika sa,A kayi mata da sanyi safiyar Allah ko kuma kuna kallonta baza kuce komai haka zan tafi in barta sai Abinda taga dama zata yi kuna kallonta kun zuba mata ido Ai ko A gurina ban yimata irin wannan tarbiyar ba" tafada tana kallon Abbah da Ummin "Kwarai D'ija baki kyautaba yanzu nake so na yi mata fada wallahi sai kika yi magana " ummi tafada Ta6e baki Nene tayi tace "da nai magana ba Ai Amana ce A gurinku kuma A mana daya ce'' "Kwarai kuwa kiyi hakuri Nene Allah ya bamu ikon rike Amanar da kika bamu" Abbah kam murmushi' yake yace "Nene kenan to Ai itama Na'ima ba gaida ta take ba sa'a taci yau ko baki ji Abinda Na'ima tafada ba Akwai kuruciya A tattare da Dija yanzu ki kwantar da hankalunki in sha'Allah zakiyi mamakin Dija kwanannan'' " to Ameen dai " Abunda Nene tace kenan tacigaba da shan kunun gyadarta "Da yau nake so in tafi Ai " tafada tana kallon Abbah wanda ya mike shima daga gurin da nufi tafiya ofis dama A shirye yake "A,a kibari zuwa gobe in sha Allah sai na kai ki da kaina " Abba yafada yana kallonta "To babu komai Ai yau da gobe duk na Allah ne Allah ya kaimu lafiya" "Ameen ya Allah" yafada ya ce "to sai na dawo ko" "To Allah yabada sa'a "Nene tafada ummi kam bayanshi tabi kamar ko da yaushe suma su Na'ima Allah ya kikyaye su kai masa gaba dayansu har da Siyama wacce tun zamanta A gurin kanta yake' A sunkuye gaba daya ta mu zanta tana mamakin waye ya gayawa su Nene yaya Aliyu ya dake ta duk kunya ta isheta tasan Dija ce zata gaya musu kuma ta san sai tafadi dalilin da yasa ya dake ta To haka dai Siyama ta karaci jin kunyarta ta dena ita ko Dija babu Abinda ya dameta ko kallon siyama bata kuma yi ba' taci ga da sabgarta babu Abinda' ya sha mata kai ummi kam ta ci Al washin zatayiwa Aliyu magana kar ya kuma dukan siyama duk lalacewar mutum fada Ake masa ba duka, ba gashi' ita zai Aura in ya saba da dukanta haka, zaije yai ta labtar yarinyar mutane............................... To washe gari ranar Nene takama hanya bayan sun sha kuka ita da Dija Na'ima sai dariya take yimusu tace, "Nene babu fa dole ki kama hannunta kitafi da ita tunda kukan rabuwa take dake kema haka ina dalili kun sanyamu agaba sai koke koke kuke yi" Hararata Nene tayi tace "ina ruwanki in nace zan tafi da ita zaki hana ne' iye? Zare ido Na'ima tayi tace " ni Asuwa " "to rufemin baki " Nene tafada shiru Na'ima tayi tana dariya kasa kasa ita ko Siyama Nene take rarrashi ko Kallon Dija batayi ba itama Dijan ko kallonta batayi Ahaka Abba da ummi suka sauko suka same su Cikin mamaki ummi take kallo'Nene tace "lafiya naga sai koke koke Akeyi"? "Wai Dija'take ta yawa kuka ,,shine nace kawai' in taga da matsala ta kama hannuta tai tafiyarta da ita" Na'ima tafada tana dariya Harararta ummi tayi tace "ke kam Anyi babbar kwabo wallahi ni matsa kibani guri " ummi tafada Kama Dija tayi ta rungume tana rarrashinta tace "kiyi hakuri duk sanda Akayi hutu sai A dinga kaiki kinayi Acan gurin Nene kinji ko" Shi kam Abba babu Abinda yace musu ya kalli Nene yace "to Nene sai tafiya ko? "In sha,Allah'' Nene tafada tana tashi daga inda take zaune gabadayansu suka rufa mata baya har gun motar shima jameel fitowa yayi domin hayaniyar da yaji idonsa A kan Nene wacce ' ke kokarin shiga mota yace "ina zuwa Nene "? cikin Dariya Na'ima tace " tafiya zatayi wai" " kamar ya tafiya zatayi ina ce ta dawo nan da zama ko sanja shawara Abban yayi "? "A,a tace ga Dija nan Anan tabarta' ita kuma tace bazata zauna ba" cikin mamaki jameel yake kallon Nene yace " wai don Allah da gaske tafiya zakiyi''? Hararasa Nene tayi tace "ga zahiri kana gani ko zaka hanani tafiya ne"? "Ban isaba Amma fa yau kwananki uku A garinan fa ina laifin ko sati daya ki kara" "banzan kara satin ba" Nene tafada kamar wacce zata kai masa duka dariya ya ka mayi yace "Allah ya baki hakuri Nene A sauka lafiya" "Ameen Ameen "tafada fuska babu walwala to haka dai suka, dauki hanya kowa yana jimamin' ta fiyarta domin Nene macace me shiga rai da saurin sabo da jama' a ga wasa da dariya hatta masu gadi ma sunji kewar tafiyar Nene sabida karamcinta bata raina mutum komai kan kantarsa domin tace Allah da kansa shi ya karrama dan Adam sabida haka babu wanda yafi wani A cikin jinsin bani Adam sai wanda yafi kyautata masa Humm rayuwa kenan zaman Dija A birni Abuja babu Nene haka suka koma gida duk jiki A mutukar sanyaye Dija kam sai hawaye take ummi nakara rarrashinta......................... Ranar mondey' Dija ta fara zuwa skull ku zo kuga Dija cikin unipom sunyi bala'in yimata kyau karamin sket ne iya gwiwa An dan tsagashi kadan sai rigar itama bata kai gwiwa ba mai kwala ce da dogon hannu an dan tsaga gefe da gefen ta sai karamin hijab kalar kayan fari da blu ne sket din ne blu rigar kuma fara sai farar safa mai tsayi wacce ta kai har gwiwarta tayi bala'in kyau Dija ga uban gashinta wanda tayi donott dashi Atsakiyar kanta tunda babu' hula A unipom din gefe da gefen kanta ko wani kwantaccen gashi ne A gun baki' sidik dashi Haka jameel ya sasu A mota ita da fa'iza wacce itama 'tayi kyau da'ita sai suka zama kamar wasu ta gwaye dasu Abin gwanin ban sha' Awa sai da jameel ya tabbatar komai ya kammala sannan yakama hanya ya tafi Class din su fa'iza Aka Ajiye Dija sabida sunga tasan Abubuwa da dama tunda sai da kai mata inter vio Amma dole Asamu' A dinga yimata lesson koda sau daya ne rana domin kwakwalwar ta kara budewa Bakaramin dadi fa'iza taji ba haka, itama Dijan sukai ta murna fa'izan nakara nunawa Dija'Wasu Abubuwan Su Aliyu kam suna can suna fafatawa domin dai' yadda suka dauki mutane sun wuce tunaninsu barna suke yi sosai kuma babban Abin mamaki da tashin hankali in sukayi kisa sai Ane mesu Arasa Yau dai Ali ya yi rantsuwar sai yaga ta inda mutanan suke shigowa cikin jama' a misalin daya darabi' na dare' suna zaune a ma6oyarsu cikin shirin ko ta kwana Aliyu ya ga gilmawar mutum kamar walkiya cikin sauri ya tashi yanufi gurin da ya hangi Abun sauran ma dukansu suka rufa masa baya cikin shirinsu sawun tafiya sukeji Amma basu ga mai ta fiyar ba cikin rashin tsoro Aliyu yafito daga ma6oyarsu ya durfafi gurin cikin jarumta ya fara haska fitilar da suke Amfani da ita dukanninsu suna kallanshi basuce komai sa suma suka rarrabu kowa i junansu Tsit kake jini gurin sai kukan tsinstaye dake tashi A gurin sai ko sawun ta kalmansu wani mutum Aliyu ya gani A gabanshi yana murmushi cikin sauri Aliyu ya bude baki zaiyi magana mutumin ya rufe mai baki hade,da kama hannun Aliyu suka nufi bayan wata katuwar bishiya A gurin Cikin mamaki Aliyu yake kallon dattijon mutumin yace "baba mai ya fito da kai a wannan daran"? Babu tsoro ko fargaba a idan mutumin yace "sabida ko nafito a cikin daran nan naji labarin cewar kunzo domi ko lafar da wannan kurar da take faruwa A wannan garin, ko"? "Kwarai kuwa " Aliyu yafada yana kara nazarin mutumin domin yana masa kallon mara gaskiya "Ni ne mutumin da Aka kashewa Iyali kisan gilla tare da kona min gida da garke shanu babu Abinda na tsira dashi, sai raina da lafiyata haka nadawo daga kiwo nazo na tarar rariyar gidana na kwararar da jini kamar mayanka" mutumin yafada tare da fashewa da kuka sannan yaci gaba da cewa "yanzu '"yan samari in kai akaiwa haka wane irin mataki zaka dauka''? Cikin jimami da mutuwar jiki Aliyu yake kallon dattijon mutumin sannan yace "zan dauka jarrabawa ce daga gurin,Allah zanyi kokari' inga na cinye jarrabawa ba zanyi yun kurin ramawa ba sabida yin haka yana nufin kamar ina ja da hukunchin da ubangiji ya saukar A kaina da iyalina wannan shine Abinda zanyi sannan zan kai maganar ga hukuma domin suyi binkice Akan wa " yanda suka Aikata haka domin gaba karsuyiwa wani makamancin haka Amma bazan dauki mataki da hannunaba" A jiyar zuciya dattijon mutumin yayi yana kallon Aliyu sai yaji yaro yashiga ransa mutuka girgiza kai yaci gaba dayi yace "duk wannan Abin da yake faruwa bada sa hannunaba " yan uwana ne suke wannan Aikin A cewarsu baza su yadda ba sai sun dauki fansa suma sai sun karar da duk jinsin mutanen da suka Ai katamin haka yanzu halin da Ake ciki cikin shiri' suka fito yau ko ku ko su domin sun ce kan me uwa da wabi zasu yi mutukar kuka hana su shiga garin" Cikin rashin tsoro ko fargaba Ali yake kallon mutumin yace "kar kadamu baba babu Abinda zai faru da izini Allah yanzu zanyi garkuwa da kai A gurin "yan uwannka" kafin ya rufe baki suka dunga jin sautin bindiga kota ina sai sawun' tafiya cikin ciyayi cikin sauri Aliyu ya kama wannan dattijon ya makure masa wuya hade da sai ta masa bindiga A saitin wuyansa ya durfafi' gurin da yake jin sawun tafiyar cikin sauri sauran suka rufa masa baya kowa bindigarsa A sai ce Da can nesa a ka dunga hasko fitila suma fitilar suka haska kowa yana haske kowa babu magana Da gudu daya daga cikin su ya yan ko domin ya fahimci wane A rike A hannun Ali sai da ya kusa cin musu Aliyu" ya sai ta bindiga ya sakar masa A kafa Ai kan kace kwabo su ka kwaso A guje domin dukannusu sun hangi Abinda yake faruwa A gurin Ko gezau babu wanda yayi A cikinsu sai da suka karaso gurin suka fuskanci dan uwansu ne A hannun Aliyu sabida haka cikin zafin nama daya daga cikin su ya murza Wani Abu dake daure A qugunshi sai gashi kamar walkiya dare dare A wuyan Aliyu yana kurza masa wani makami dake hannushi Cikin zafin Nama Aliyu ya han tsilo da shi kasa, yasa kafa ya take masa kafa daya yana murzata Ihu yadinga yi yana kiran "yan uwansa,, Kallonsu Aliyu yayi ya ga jikinsu yayi sanyi dukannisu ganin " yan uwansu uku a kwance babu mai kyakykyawan motsi' Cikin daga murya Aliyu yace " kowa ya Aje makamin da ke hannushi" yafada yana kara saita bindigar cikin wuyan dattijon mutumin nan wanda ya riga ya gama galabaita domin ba rikon wasa Aliyu n yayi mishi ba One by one suka dinga Aje makaman dake hannuwansu jikinsu A sanyaye daya bayan daya Aliyu yake kara nazarinsu babu wanda yai magana shiro gurin kake ji sai sautin kukan dabbobi still wannan dattijon mutumin na hannu Aliyu A rike ya yi masifar gajiya sabida rikon tsauri Aliyu yayi mishi Shi kam Aliyu yana sauraron ko da wani siddabarun da za suyi shiyasa ya ki zartar da Abinda ya shirya musu Wajan mintuna talatin babu wanda yace uffan acikin dukannisu kawunansu ,A sunkuye burinsu kawai suga dan uwansu A hannusu shiyasa, suka gaza ta buka komai su faruk kuwa suma a shirye suke suna sauraren Abinda zai biyu baya cikin daga murya Aliyu yace "wanene yasa ku wannan Aikin"? Yafada muryar shi na Amsa kuwwa a gurin............................... Shiru babu magana sai daya kuma mai maitawa sannan daya daga cikinsu yace "babu kowa' Asali ma shi wanda Abin ya shafa bada sa hannusa ba kawai mun fito mu daukarwa dan uwanmu fansa Akan wannan Abinda A kai masa" "Sai a kace ku dauki mataki A hannuku ku dinga yawo da makamai cikin dare kuna barna baza ku kai maganar gurun jami'an tsaro ba domin A dauki mataki Akan abin" "Mun kai bamu ga An dauki kwakwaran mataki ba shine muka ga gwara ka kawai' mu dauki mataki da kan mu" mutumin yafada yana kallon Aliyu wanda ya dallareshi da fitular dake hannusa "To sulhu ko ke su ko kuma mutafi da mutumin da kuke wannan barnar Akanshi ko kuma yanzu nan in kashe shi kowa ya huta" Aliyu yafada da barazana tare da kara gyara bindigar hannusa akan wuyan mutumin Cikin ihu suka hau fadin "A'a oga kar ka kashe ma nashi shi kadai ya rage mana A matsayi uba yan zu shikai dai yake mana Abinda muke so shiyasa duk wanda ya ta6ashi bama saurara masa" dukanninsu suka fada cikin hayaniya kan kace kwabo gurin ya kaure da hayaniya sai hakuri suke bayar wa "Kif quit"!! Aliyu ya fada da mugun tsawa shiru sukayi dukanninsu fuska babu walwala Aliyu yake binsu da kallo sannan yace " to magana daya ko biyu zamuyi da ku yanzu" ya cigaba da cewa "kar kusa ke yin kisa ko qona gida jen jama' a ko tare mutanen dasu ka Ai kata hakan ku sassaresu mutukar kuka kuma Ai katawa to babu shakka dukanninku ya muzo mutafi da ku, zamu dauki mataki mai tsauri A kan haka, kuma duk inda zakuje ku 6oya sai mun nemeku zamu kaiku mutsare har qarshen rayuwarku tare da bada horo mai tsanani da azaftarwa" ya cigaba da cewa "Mu kuma munyi muku Alkwarin duk inda wadannan mutanen dasuka Aikata wannan danyen Aikin suka shiga zamu nemesu zamu zartar musu da hukuncin da hukuma ta tanadar a Kansu" "Kun yarda da hakan"? Aliyu yafada cikin tsawa fuska babu Annuri ko kadan A tare dashi "Eh oga"! "eh ogo dama rashin daukar matakin ne'yasa muka fito muna ramawa da kanmu Amma tunda yanzu mun samu to mun A jiye makamanmu" dukannusu suka fada Kallon faruk Aliyu yayi yai masa inkiya yasan Abinda yake nufi sabida haka kai tsaye gurin mutanen ya durfafa sauran suka rufa masa baya one by one suka dunga ca jesu sai gashi suna kwanto wani Abu A daure Qugunsu dukannusu sannan suka dauke makamansu da suka zube A gurin Sai da suka gama hada komai guri daya sannan Aliyu ya saki dattijon mutumin nan wanda ya gama galabaita yana shirin faduwa kasa cikin sauri Aliyu ya tare shi kan ya kai yace kozu ku kama shi gaba dayansu suka zu daya daga cikinsu shiya sa6a mutumin A kafada suka kama hanya suka wuce To su Aliyu ba subar gurun ba har sai da gari ya waye sosai suna kara nazarin gurin sai da suka tabbatar babu wanda zai dawo A cikinsu sannan suka bar gurin wannan shi ya nuna musu cewar su suke da nasara A tafiyar sabida haka cikin farin ciki suka bar gurin To basu bar garin ba sai da suka yi kokarin kama mutanen da suka Aikata Abun cikin su goma sha shida sun kama mutum tara uku sun mutu hudu kuma sun gudu Murna "yan uwa dattijon mutumin suka dinga yi tare da yiwa su Aliyu godiya dama su burinsu Kawai A daukarwa dan uwansu fansa Haka suka sa su A moto suka dauki hanya bayan sun tabbatar da babu wani Abin tashin hankali da zai kuma biyo baya a garin Wannan nasara da suka samu ta kara dau kaka Aliyu A gurin manyan kasa domin suma Abin yana damunsu ganin an kasa shawo kan Al'amarin da wuri sai gashi kan kanin lokaci yaron da ya fara Aiki ko sati daya bai ba shine ya kashe case din wannan Abin Alfaharine A gurinsu dashi kanshi Aliyun Kan kace kabo magana, ta kan kama kafafen yada labarai tare da hasko Aliyu yana jawabi cikin tv game da nasarar da suka samu haka jaridu ma da sauran gidajen redio babu zancan daya ke tashi sai wannan Su ummi suna falo dukannisu A nata hayaniya fa'iza gwanar kallo ta dauki ' remot tana kokarin canja tasha sai ga jameel ya shigo da sauri yace "ummi ba kusan me faruwa ko"? "Meya faru" ummin ta fada tana kallonsa karbar remot din dake, hannun fa'iza yayi yana kokarin kama tashar da aka ce masa ya duba yace bara kigani fuskar Aliyu suka An hasko Ana ta faman dau karshi hoto "yan jaridu sunbi sun kewayeshi shi kuma sai faman bayani yaake musu cikin wani irin turanci sai kace wani A kasar waje sai ka rantse cewar black America ne sabida tsabar yadda yake turanci *nikam nace dama Aliyu ya iya turanci haka ko da yake ai kan Aikinsa yake kuma tsan tsar ba haushe ne shiyasa bai fi ya yin yaran nasara ba in ba kamawa tayi ba Shiru falon yayi kowa yana kallon Aliyu cikin farin ciki ganin yadda Aka kewaye kowa yana so yaji ta bakinshi haka dai daya bayan daya suka dinga zan tawa da sauran sojojin tare da hasko fiskokin wadannan "yan ta Adda daya bayan daya tare da daukar hotonan su Dija ce ta ta6o kafar fa'iza wacce ta zubawa tv ido sai faman farin ciki take tace "fa'iza bakya yiwa wancan mutumin da Ake ta haskowa A tv kallon sani gani nake kamar na san shi wallahi" tafada tana nuna Aliyu domin ita kam bajin turancin da suke take ba shiyasa bata fahimci me su ke cewa ba Ga badayan su dariya,suke wa, Dija ganin da gaske take bata gane yaya,Aliyu ba cikin dariya Na'ima tace "ke kam Anyi "yar kauye wallahi, yanzu yaya Aliyu ne baki gane ba" da sauri Dija ta kuma kallon tv tana so ta tabbatarAikam shine tafada Acikin zuciyarta dama kyakykya wane Ashe ta ke tambayar kanta domin ita bata ta6a kare masa kallo ba irin yau ta6 tafada cikin ranta hade, da ta6e baki bata kara cewa komai ba' ta cigaba da duba book din dake hannuta Ita kam Siyama wani irin dadi da da farin ciki ne ya lullu6eta tare da da dagawa tana me Alfaharin da cewar ,zata Auri Aliyu ko da baya santa Amma tasan in ta Aure shi tagama kashe boss din domin dole yaso ta ko da zata rasa zanin daura A doran duniyar nan kuma' ita kadai ke' da shi duk shegiyar datai gigin shiga tsakanita dashi saita sabautata ciki kuwa har da uwarshi wacce ta tsoguna ta haifesh Kara kallon tv n tayi A karo mara A dadi tana murmushi yanzu friend dinta suna can suna can suna kallon Aliyu wannan ba karamin Abin Alfahari ne A garetaba Wannan Abu yakarawa Aliyu daraja da mukami sabida namijin kokarin da sukayi gurin kawo karshen wannan badakala dake faruwa A can garin sai misalin sha biyu darabi na dare ya shigo gida kai tsaye cikin gidan ya nufa bayan yayi faking din motarsa A gajiye ya shiga dakinshi hannushi rike da tarkacen wayoyinshi da wasu muhiman abubuwan Am faninshi Zube su yayi kan katifa shima ya zauna cikin gajiya bai yi tunanin shiga cikin gidan ba sabida ya san sun ruga sunyi bacci gashi coffe yake son sha sosai kwan ce takalminshi yayi yade da balle whatch dake daure A hannusa na zallar Azirfa A gajiye ya ke zare kayan jikinshi babu Abinda yake son yi sai wanka Amma ba zai samu ba sai yasha coffe tukunna da gashi sai 3qtaer sai karamar shart yanufi cikin gida ko ina shiru yasan duk sunyi bacci sabida haka kai tsaye kchin ya nufa da kansa zai hada cofee din Kokarin kunna gas yake yakasa ya kunna Amma wutar tayi yawa sai faman tsaki yake rai Abace yakashe ya fita daga kchin din dakinsu Na'ima ya nufa kai tsaye domin dai Asabe mai Aikinsu tana can boys'Quoters bangaren masu Aiki bazai iya zuwa ya ta so ta domin da dafa masa ba Tura kofar yayi fuska babu walwala yashiga yana kare musu kallo daya bayan daya so yake ya gano wa cece Na'ima domin dai shi kam bazai iya wani gane wace A cikinsu ba Bubbuga gadon ya hauyi yana kiranta "Na'ima ke "Na'ima " shiru bata motsa ba kafarta ya ja yana kara kiran sunanta wani irin hannu Siyama taji mai sanyi da taushi taji yana ta bata in batayi karya ba kamar kamshin turaran ya'Aliyu take ji sabida cikin sauri ta yaye blanket din data lullube jikinta ta tashi zaune tana kallon inuwar mutum a tsaye A kanta wa zata gani yaya Aliyu ne ta6 tsuntsu daga sama ga shashshe tafada cikin ranta sabida haka cikin magagi irin na masu bacci ta mike a zabure ta yi kan sa ta makalkale shi tana ihu A hankali irin na munafurci wai ta tsorata Wata Ajiyar zuciya Aliyu ya dinga sauke wa A hankali' tsigar jikinshi tana tashi ya sauke A jiyar zuciya' ta kai sau goma jin wasu Abubuwa masu taushi da yake ji tudunsu A jikinshi shiru yayi yana kallonta zuwa yanzu yasan wa cece A jikinshi ita ko Siyama jin yayi mata shuru bai ce komai ba sai ta kuma kama shi harda zagaya hannayenta A qugunshi tana faman shinshina jikinshi kamar wata mayya babu zato suka ga haske ya gauraye dakin cikin sauri Aliyu ya kalli gurun Dija ce A tsaye ta zuba musu ido cikin tsuru saura kadan fitsarin da ya matseta ta sakeshi a wando domin shiya tashe ta dama bin su da kallo ta dinga yi ganinsu a tsaye manne da juna idanunta A tsaye kan Aliyu tana kallonsa babu kiftawa shima ita ya zubawa ido yana kallo fuska a murtuke ita kam Siyama tasamu Abinda take so sai kara narkewa take A jikinshi bata san wainar da ake toyawa ba domin ta bawa Dija' baya tunda idon ta A lumshe yake batasan ma Haske ya gaureye dakin ba balle ta Ankara da mutum A tsaye Aliyu ko yana sane ya kyaleta A jikinshi so yake yaga karshen jarabarta da iyakacin iskancinta sannan Magana yakewa Dija da ido yana mata Alama da me yatasheta fuska A hade ta kallonsa take ido kir tana, mamakin Abinda suke tunda ita dai kullum in sukaje isilamiyya malaminsu yana fadar duk namiji da macen da suke ta6a junansu haramunne kuma "yan iska ne mutukar babu Aure A tsakaninsu hararasa ta hauyi sabida ta ga Abinda yake mata ko kallonsa bata yi ba ta wuce daga gurin tana faman zum6ura baki ranta A bace toliet ta shiga zuciyarta kamar ta fashe take ji tana kara tsanar Aliyu A cikin zuciyart" tace dan iska kawai sai yai ta faman dukanmu gashinan shiya kamata a doka toliet ta shige ta bugo kofar da da karfi Kallo ya bita da shi yana girgiza kansa sannan ya mai da hankalinsa kan Siyama wacce tayi male male A kwance A jikinshi Da hannu daya ya daga ta ya tsayar da ita tana fuskantarsa sai ga Siyama tana neman faduwa kasa kafafunta sai karkarwa suke bude idanta tayi ta zuba masa su wanda suke jazir gasu A lumshe sai faman kikkifta shi take ji' ko kunya' babu Kallonta yake yana Na zarinta dariya yake cikin ransa yana kara kallonta ganin yadda ta kuma sabida jarabar dake cinta yarinyar nan ta kamu fa yafada A cikin zuciyarshi yana mata dariya fuska babu walwala yace "wuce kije ki hadamin coffe" ya fada cike da bada umarni Ko kunya babu Siyama ta fara kame kame da inda'inda wata shegiyar tsawa Aliyu ya kwatsa mata yace "yimin shiru wuce kije kiyi Abinda na saki' " yar iskar yarinya kawai me zaki gayamin bayan kin gama iskancinki zanga karshen iskancin naki Ai " Simi simi Siyama ta wuce tana dariya cikar burinta yau ta ta6a jikin da ta jima tana muradi gaskiya yaya Aliyu karshe in na Aure shi nagama morewa jikinshi kawai ya isa ya di mautar da mace humm daya ke cewa ni " yar iska ce shi din ma Ai shine tunda yana sane ya bar ni Ajikinshi zai wani kare kanshi haka take fada cikin zuciyarta Kallo ya bita da shi yayi da take ficewa daga dakin tsaki ya ja a cikin zuciyarsa yace dobe ta don Allah shi babban Abinda yada meshi A yanzu yanda ta tayar mai da wata irin sha'awa gashi Abinda ya dade bai yiba ji yake A halin yanzu babu Abinda yake so' in ba sex ba gashi babu hali wani irin kyarma jikinshi ya ke Ya nan A tsaye ya kasa motsi so yake yadan sai saita kansa,Abun yaci tura gashi ita da ta tayar mai da,fleeng din kwata kwata baya sha'awarta zuciyarsa na can tunanin wani Abu da ban haka ya dunga ciccije lebanshi idanunshi A lumshe motsi yaji A bayanshi jiki babu kuzari ya bude idanshi ya sauke kan Dija wacce, ta fito daga toliet' tana faman ciccin magani ko kallonsa batayi ba ta wuce ta nemu guri tayi kwanciyarta kallonta yake sosai kamar babu gobe yana mamakin kirar yarinyar sabida wasu irin mazaunai yagani lokacin data wuce masu bala'in ka yatarwa A cikin wata rigar bacci iya gwiwa, da wandon ta kayan sunbi jikinta sun lafe duk takawa daya sai sun juya kan kace kwabo Aliyu ya rikice sai motsi' yake da bakinsa yana mamaki yarinya karama "yar shekara goma zuwa shadaya ita ta mallaki wannan boss din inaga in ta girma cikin mutuwar jiki yabar dakin bayan yagama karewa Dija kallo wacce bata san wainar da yake toyawa ba domin baya ta juya masa ta ciga ba da baccinta babu Abinda ya dameta wannan shi ya bawa Aliyu damar kare mata kallo kamar babu gobe sai faman Ajiyar zuciya yake saki A daddafe ya karasa dakinshi mararshi tai bala'in daurewa babu Abinda yake muradi A yanzu sai mace kuma macan ma Dija Sallama Siyama tayi hannuta dauke da wani karamin tire dauke da butar shayin sai kananun cup ta A jiye A kusa da shi cikin kwarkwasa da son iyawa tace "yaya Aliyu' in hada ma ne"? "Get out dan Ubanki "yafada yana nuna mata kofa ransa A da gule domin shiyasan' cikin halin da yake ciki " yar isa duk ba ke kika jawo min ba " maganar ta su6uce masa bai shirya ba, Jiki na kyarma siyama ta mike cikin ranta kuwa tace oho dai naji dai tunda nadan lashi zumar sai kaje ka qarata Amma da masifarka jarababbe Tana fita ya yunkura da kyar yana ciccije le6e toliet ya nufa yana tafiya yana hada hanya A daddafe ya hada ruwa,mai sanyi ya dinga kuzawa jikinshi wai ko yaji' releif" Amma ina kamar karawa Abun kaimi yake hajiya ta kai ta kawo so take A bata Abincinta kallonta yake rai A6ace A tsaye car babu Alamar zata risina haka dai Aliyu sai da yayi karamin hauka A toliet' din nan sannan A daddafe ya fito daga shi sai gaje ran wando ya durfafi inda ya A jiye motarsa Yana tafe yana hada hanya kamar wani dan maye bude motar yayi ya hau lalube yana haskawa da fitalar wayarsa wani Abu A kwali ya fito da shi ya mayar da motar ya kulle ya juya, tun kan ya karasa dakinshi ya kunna sigarin yafara sha zuqa biyu yayi mata ta kare ya jefar da to tuwar ya kuma kunna wata,A taikace dai A ranar nan Aliyu bayi bacci ba sigari, kam yasha babu Adadi sai daf da A subah baccin ya daukeshi Wayar faruk ce ta tada Aliyu daga baccin wahala da ya dauke shi jiki babu kuzari ya dinga laluben inda wayar take kallon screen' din wayar yayi tare da jan tsaki ya daga ciki ciki yace "malam meye zaka tadani ina bacci da sanyi safiyar Allah"? "An tashe ka din" faruk din yafada shima A hasale yace "An kiraka ya kai sau biyar baka daga ba dan rainin hankali " "Kai dallah karka dame ni ka kyaleni inji da damuwata malam " Aliyu yafada cikin 6acin rai Dariya Faruk din yayi yace "dan iska kai kana da wata da muwa dama"? Ajiyar zuciya ,Aliyu ya saki yace "zaka shigo ne bana jin dadi' faa serios" "Eh nima Nafisa ce bata ji dadi ba shine nake so kazo mu kaita hospital A duba ta shine dalilin wannan kiran da nayi maka" "Ok "Aliyu yafada yace "kashigo kawai ina jiranka sai muje nima ina so inga Dr hashim A kwai shawarwarin da zan ne ma A gurinshi" "Ok sai mun zo din "faruk din yafada yana kokarin kashe wayar A daddafe Aliyu ya tashi yayi wanka jikinshi babu kwari ya fito yana kintsawa hutun kwana biyu za suyi sannan su kuma bakin Aiki cikin wando jins da shet me kayan kakken jiki ya shirya kayan sun fito da Ainihin sa da zatinsa da kwarjininsa fuskarsa ta yi fayau kwantacen sajen da ya kewaye fuskarshi sai sheki yake tsakiyar goshinsa ko tabon sallah ne ya fito yayi ran dau Abinka da farin mutum sai Abun yabada sha'awa hannuwashi ko gashine A kwance har "yan yatsu A goge ya daura sai glss da ya manna A fuskarsa mai duhu black domin har yanzu kwayar idan shi bata gama da wowa daidai ba zauna wa yayi gefen kati farshi yana sa safa A kafafunshi farare tas kamar wanda baya taka kasa ko daya ke duk yawancin ta kalman Aliyu boot ne zuwa sendal sai ta kalmasu irin na sojoji da wuya kaga kafarshi sai dai in zai yi Alwala ko yana gida yanzu ma wani matsiyacin boot yake kokarin sawa bayan ya saka safar mai balain kyau kai da gani shi kasan takalmin zaiyi kudi fuska babu walwala ya nufi falon cikin yanayin tafiyarshi ta gwarzon Namiji Cikin sallama ya shiga falon yana bin ko ina da kallo rige rigen Amsa wa suka dinga yi " yan matan gidan ummi kam tana can khicin ita da Asabe suna kokarin kammala kayan karyawa TSit falon yayi duk suka shiga taitayinsu shi kuma ya dinga bin falon da kallon fuska babu Annuri ne man Nene yake tsaki yaja cikin ranshi yace, "ko bata tashiba" domin kwata kwata bai kawo cewar zata tafi da wuri haka ba Can kan dannig din ya karasa ya nemin guri ya zauna yana faman' ya tsine fuska As'useal daya bayan daya suka gaisheshi da ike dukannisu suna falon babu yabo babu fallasa ya dinga Amsawa tsai da idanunshi yayi kan Dija wacce ke zaune' A kan kujera cikin shirin zuwa skull fa'iza na gefenta itama cikin unipom din suna duba wani book Mamaki yake ganin duk sun gaisheshi Amma banda ita ita wannan yarinyar wai da meta ke taqama ne iyi shi kadai yake tambayar kansa yau zai ga karshen rashin kunyarta ko Aljanu ne da ita yau sai ya sauke mata su Cikin tsawa yace " ke zo nan" dukanninsu suka juyo suna zare ido karda Siyama taji labari domin A tsorace take dashi tana tunanin Akwai matakin da zai dauka A kanta Bada ke nake ba yafada yana kallon Dija wacce ta zuba masa ido yace "zo nan " A karo na biyu ko tsoro babu Dija ta tashi ta nufi inda yake zaune kallonta yake ta cikin glass din yana mamakin yadda kayan makarantar sukayi mata bala'in kyau A zuciyarsa yace yarinyar kamar Aljana kizo ki dame ni kullum cikin bacci zanci ubanki yau Ai Tsayawa tayi A kansa kerere tace "gani' banza yayi mata tafi minti goma A tsaye A kansa bai ce mata komai ba cikin kunkuni tace "nifa na gaji gani fa nace" tafada tana zumzumbura baki' hade da bubbuga kafarta kallonta yayi A karo na farko tun lokacin da ta zo gurin "zauna nan " ya nuna mata kasa kan tayal kallon jikinta tayi tace "ta6 da unipom din zan zauna A kasa wallahi bazan zauna ba " tafada babu Alamar tsoro ko kadan Gwiwarta ya daka da hannusa sai gata A kasa tayi zaman "yan bori babu shiri bude bakin tayi zata kurma wannan ihun da ta saba yasa hannu ya rufe bakin hade da kamo lebenta na kasa ya hau murzawa yana kallonta ta cikin glass din Ita ko Dija' ji take kamar kafarta ba A jikinta take ba sabida bala'in sagewa da tayi sai wani ya mami take mata Alamar kafar ta tara jini gashi takasa daga kafar ko kadan Hawaye ne kawai yake zuba babu halin kukan ya fito tunda Aliyu ya rike bakin sai lugwigwitashi yake cikin mugunta Abbah ne ya sauko daga sama shima cikin shirin fita Aiki idanunshi A kan Aliyu yace "me nake gani ne Ali"? Kallon Abbah Aliyu yayi ya dan saki fuska yace "Abbah barka da Asubah" bai Amsa ba illa kallon Dija da yake A zaune A gaban Aliyu bakinta rike A hannusa yace "me ta yimaka da sanyi safiyar Allah" ? "Abbah yarinyar bata da tarbiya wallahi , wai ni takewa kallon banza bani da matsayin da zata gaisheni shine nake dan koya mata hankali, duk Nene ce ta 6ata ta wallahi wai ina ma Nene take"? "Ban sani ba " Abbah yafada yana kokarin 6an6are hannu Aliyu' daga bakin Dija wacce ke zaune cikin galabaita "kana so Amanar da Aka barmana ta cimu ko sakar mata baki " Abbah yafada Dariya Aliyu ya ke yace "wace irin Amana Abbah" ? Wannan yarinyar in Aka danganta ta da Amana sai takarasa lalacewa gwara Adinga horar da ita yadda yakamata domin bata da kunya ko kadan" Bige hannusa Abbah yayi yace "dallah malam matsa kai kowa sai ka gwadawa mugunta babu babba babu yaro A ciki" Murmushi Aliyu yayi ka wai bace komai ba ya bisu da kallo yana so yaga ta inda Dija zata iya mikewa tsaye A yanzu domin domin yana sane ya sagar mata da gwiwa dan yaga karshen rashin kunyarta ta Abu kamar wasa Dija takasa mikewa tsaye da ta yunkura zata tashi sai ta koma ta zauna tana kara ga le6enta na kasa ya yi jazir dashi har dan kumbura sai da yayi in banda radadi babu Abinda yake mata hawaye ne ka wai yake zuba mata babu halin kuka sabida ita tasan A zabar da take ji Miker da kafar Abbah yayi duka biyun ihu 'Dija tasa jan kafafun ya dinga yi yace "meyasa me ki A kafar iyi"! Cikin kuka tace " duka na yayi A gwiwata shine nafadi tunda nafadi nakasa tashi ban san me nayi masa ba ya tsaneni sai yai ta cin zalina" cikin gursheken kuka take maganar Kallonsa Abbah yayi yace "yanzu ka kyauta Ali irin horon da kukewa masu laifi' shine zakazo kayiwa yarinya marainiya sabida mugunta laifin me tayi maka iyi"? "Abbah ka daina kiran yarinyar nan marainiya shi yake sawa take yin Abinda take Ai marayu ba haka suke ba kawai tsabar sangarta ce da irin shagwabata da Nene tayi " hararasa Abbah yayi yace "An shagwabatan malam kar ka kuma zage karfinka ka dakar min yarinya wallahi in ba haka ba zan zage in rama mata kaji ko" dariya ce take so kama Aliyu ganin yadda Abbah ya ke fada an dakar masa yarinya Amma sai ya dake baiyi ba cikin murmushi yace "to baza a kuma in sha Allah Amma itama kayi mata fada babu ruwan ta dani ta daina hararata in ta ganni ni ban damu da gaisuwarta ba" Aliyun yafadi maganar kamar gaske Kallonta Abbah yayi yace "wai hakane Dija kina harararsa "? Shiru tayi bata ce komai ba " to ki daina ba sanki bane kinjiko" daga kai tayi kawai zuwa yanzu ta bar kukan data ke kafar ma ta rage zafin da take mata so take ta tashi daga gurin cikin ranta kuwa tayi rantsuwar babu ita babu Aliyu ko inda yake bazata kuma kalla ba balle yace tana harararsa zata dinga kokarin gai sheshi domin tagaji da nau'in muguntar da yake gwada mata ita kadai A cewarta baya yiwa "yan uwnsa sai ita sabida haka yanda ya tsane ta itama haka ta tsane shi Kama hannuta Abbah yayi suka nufi dannig din wanda dama Asabe ta riga tagama shiryashi ummi ce ta fito daga kchin tana goge hannuta tace "wai hayaniyar me nake ji ne ina kchin"? "Tam bayeshi gashi nan A zaune " Abbah yafada yana kallon Aliyu kallonsa ummin tayi tace "Ai fa kwana uku dakayi baka gari yara sun samu sakewa Amma dubi yanzu yadda kasa min yara sukai tsuru- tsuru dasu sai kace sunga dodo" Kallonta yayi yana ya mutse fuska na sabo yace "babu ruwana ummi me sukayi min' iyi su su kasan Abinda yake damunsu'' 'to me kayiwa ' Dijan iyi"? "Babu Abinda nayi mata ummi kinsan shagwa6a6iyace, to me zanyi mata ma da safiyar nan" Aliyu yafada yana duba Agoge dake daure A hannusa kallon fa'iza yayi dake tsaye yace" zo nan sweet na" wani ban bara kwai fa'iza taji jiki babu kwari taje zaunar da ita yayi kanciyarsa yace " kidinga karatu da kyau kinji kar kisa wasa kar ki dinga kula daqiqan Aji da marasa kunya sukai ki su baro kinji ko' ko bakya so kizama "yar jarida ne"? da sauri fa' iza tace "ina so mana yaya Aliyu yace "to ki dage da karatu karki sa wasa kin ji qanwata" "to ya Aliyu " "yawwa tashi kije ki karya" tashi tayi daga kan cinyarsa sai munna take can kan kujerar kusa da Dija taje ta zauna ta6e baki ummi tayi' tace "kowa yayi zagi A kasuwa yasan da wanda yake ita ma Dija' Ai zata yi karatun Yanda yakama ta " yana dariya yace "ummi wana zaga ni yanzu" "ban sani ba yau ni na koma Nene kenan ko"?,ummi tafada tana kokarin hadawa Abbah kayan kalaci "Ummi wai ina Nene take ne''? Kafin ya rufe baki jameel ne yayi sallama cikin shirin kayan kwallo tu6e ta kalma yayi ya Ajiye a gefe ya karaso gurin kai tsaye gurin Aliyu yaje yace "bro barka da Asubah' hade da mi kamasa hannu yana dariya shima hannu Ya mikamasa yace "barka kadai jameel "din yace" kadawu lafiya"! 'Lafiya Alhmdulilah" cikin farin ciki jameel din yace "gaskiya nayi farin ciki nasarar da kuka samu lokaci kankani ba kaga yadda Ake maganar ba da ganin kokarin ka gurin wannan Aikin da kayi mutane da yawa suna ce da tai makon Allah da hikimarka A kasamu yankewar rikicin tunda An dade da kasa shawo kan matsalar" "Allah ya kare mana kai A duk inda zaka shiga ya tsare gabanka da bayanka" "Ameen Ameen" Aliyu yafada yana jin dadin Addu'a da dan uwansa yaayi masa kallon jameel din yayi yace "sai ina yanzu da safiyar nan" ? Yana dariya yace "zamuje mu dan ta6a ne yau A ta yamu da Addu'a" girgiza kai Aliyu' yayi yana murmush yace "Allah ya tsare bro" Amee" jameel din yace yana dan tsalle irin nasu na "yan kwalo domin baiyi tunani yaya'Aliyu zai sauko da wuri haka ba tunda kullum ya ganshi cikin kayan bol fada yake masa "Abbah barka da Asubah" "yawwa barka kadai Antashi lafiya lafiya"? "Lafiya lau Abbah" "masha Allah" "ummin Antashi lafiya"? Jameel yafada yana zama cikin kujera shima "lafiya lau na tashi " "Bro baka kyewar matarka ko"? Na'ima tafada tana kallon jameel kallonta yayi yace "wacece matata kuma"? Cikin dariya Na'ima tace "Nene mana hararata yayi yace "me zanyi da wannan tsohowar da kai duk furfura Ni kinga matata nan" yafada yana nuna Dija' dake zaune kusa da Abbah tana kalaci cokalin dake hannusa Abba ya jofo masa yace "uwar tawa ce Abin rainawa iye"? , dariya suka kama yi wannan karon harda Siyama wacce tun zamanta A gurin bata ce komai ba bayaga gaishe da Abbah da ummi da tayi Yace "yi hakuri Abbah Ai Nene ce ta tsofa ni kuma sai yarinya sabon jini " ummi kam hararasa ta yi tace " kai kam baka da kunya wallahi jameel" Dariya ya hauyi kasa-kasa ya sunkuyar da kansa yana cigaba da cikin Abincin ita kam Dija sai faman harare harare take taki yin magana Aliyu kam bai kara magana ba dif yayi kamar babu shi A gurin yana cin Abincinshi yana lure da irin irin mayataccen kallon da Siyama take masa kamar zata cin yesh danye cikin ransa yace wannan yarinyar in mayyace ta kama mutum sai taga bayanshi zata hakura "yar iskar yarinya jarababbiya kawai "domin ya gama fahimtarta irin matan nanne masu jarabar maza daga nin ta shi kuma ya rantse sai yaga karshen jarabarta ta bari dai A daura Auren zata san wata Aura Tashi yayi daga guri bayan ya kammala can babban falon ya karasa cikin tafiyarsa da sassarfa da kallo suka bishi dukannisu har ,Dija sai taga yazama wani kato dashi sabida kayan da yasa masu fito da sufar jikine wata irin power ce A dan tsen hannusa A murmurde da ita ga rigar kamar zata yage sabida kama jikinshi da tayi sumar kansa kuwa tasha gyara' sai sheki take da kyalli gata ba qiqqirin da ita yayin da sajen sa yafi fatar fuskarshi ya lafe ya gewaye fuskarsa hade da' siririn bakin shi kai gaskiya yaya Aliyu kyakykyawa ne Ajin farko domin ni kaina ban ta6a kare masa kallo ba irin yau wai gaskiya ya hadu Siyama kam jikinta in banda tsuma babu Abinda yake yau take tunanin tafiya dole taje ta samu momy'nta dan gaskiya ita kam tagaji gwara A san yadda za,ayi ji take A wannan lokacin zata iya yiwa Aliyu fyede dan gaskiya ba zata iya jurar ganinshi A kusa da ita ba wani irn hali take shiga in yana kusa da ita Wayarshi ya fito da ita yana kokarin kiran faruk bugu daya ya daga yace kaifa nake jira malam ganinan ina kan hanya Ai Ok sai ka karaso yafada hade da kashe wayar' kira'a ya sa yana ji hade da sa eir pix a kunneshi yayi kwanciyarshi kan kujerar hade da lumshe idonsa shi kadai yasan Abinda yake cin zuciyarsa kullum' ta Allah Haruna drever ne yayi sallama ya tsaya daga bakin kofa yana gaishe da Ummi yace "uwar dakina takwas saura fa" yafada yana kallo fa'iza cikin sauri suka tashi ita da Dija suna yiwa "ummi sai sun dawo" domin Abbah ya tashi daga gurin shima sai su Na'ima "to Allah ya bada sa'a " ummi ta fada "ya Na'ima sai mun dawo" "to sisters dina Allah bada me Amfani Ameen" ita ma Siyama da ba'ai mata magana ba cewa tayi "sai kundawo fa'iza ce kawai ta Amsa dama kuma ita take ki danta take rawarta uffan Dija bata ce ba haka suka kama hanya suka tafi' Yananan zaune A gurin faruk yayi sallama Nafisa na biye dashi A bayansa kai tsaye wajan ummi suka nufa "A,a lale maraba Amarya ce" ummi take fada bayan Ta Amsa sallamar da sukayi dariya Nafisa take tace "yawwa ummi sannu da gida" "yawwa sannu" ummin tafada tana tashi daga kujerar daynnig din da take kai tace "zo mu karasa can ki zauna sosai" "to Nafisa tace ta mike tsaye daga tsugunun da tayi' Dariya Na'ima take kunshe wa tana kallon Nafisa tace "zama da kyar tashi da dabara sannu da zuwa A lallai Abu ya girma" tafada harda rike ha6a harararta Nafisa n tayi bata ce komai ba ta wuce Bayan sun gaisa da' Siyama sama sama dama bawani shiri" da juna suke ba duk da cewar An taso A tare gashi skull ma kusan tare su kayi ko wacce tana da Siyaman ce ma tasa shashanci shiyasa suka rigata kammala dgree dinsu bata sa komai ranta ba sai biye biyen kawaye da samarin banza A lokaci Faruk kuwa cikin barkwanci suka gaisa da Na'ima tace "yaya faruk na kwana 2 banganka ba sai jiya da Aka yi hira da ko A tv" yana dariya yace "bata barina fita kulleni take A gida wai idona na ganin mata ne kiyi mata fada yadda ya kamata, kawartaki kishi gareta harda na siyarwa gashi ni kuma mijin mace hudu ne" yafada kasa-kasa yana dariya rike baki Na'ima tayi tace "babu ruwa na wallahi'' yana dariya yace "ni da ruwa na Ai ba tsoranta nake ba ko ya kika ce Uwar gidanmu" yafada yana kallon Siysma dake zaune' kamar mutum mutumi ta na can tana tunanin ta yaya zata mallaki Aliyu ita kadai Wani kallo ta watsawa faruk din jin sunan da ya Am bace ta dashi wai uwargida ita fa tsani a danganta ta da wannan sunan wallahi dama bawani shiri' suke da faruk din ba, tunda matarsa basa shiri gashi Aliyu bashi da wani Amini sama da shi kuma ta lura yana daukar shawarshi wallahi ya sake yasa Aliyu yayi mata kishiya sai ta lalata masa rayuwa ta bar mai Abin kwatance A duniya yabar ma wani rawar kai Yana kallon irin kallon da take watsa masa cikin ransa yace nasan za ki Ai kata shashashar yarinya kawai A fili kuwa sai ya cigaba da janta da zance A daddage ta dinga Amsawa kamar me ciwon baki barin gurin yayi ya karasa can babban falon yana fadin " wai ina Nene ne"? Ga kawarta na kawo su gaisa" yafada yana zama gefe Aliyu "Ayya Ai Nene ta tafi tun she karan jiya" ummi tafada tana kallonsa' "ta tafi " faruk din ya mai mata maganar yana dariya ummi tace "kwarai kuwa girgiza kai yayi yace "lallai Nene A she da gaske take dama dariya ummi take tace "kasan in dai tafadi magana to babu ja Aciki" girgiza kai yayi yace "ita tace A kawo mata'Nafisa su gaisa A she babu rabo" "Ai kam dai sai An hadu wataran A gaisa tunda ba dai na zuwa tayi ba" "hakane" faruk din yafada yana gaishe da ummin cikin girmamawa' Ita ma cikin mutumci ta Amsa tana tambayarsa mutanen gida da Sauran" yan uwa yace wallahi kuwa lafiya lau ummi yawwa masha,Allah ummi tafada sannan ta juya suka cigaba da hira ita da Nafisa Na'ima ce kawai ta dawo falon ita kam Siyama daki ta nufa so take ta hada " yan ko matsanta yau take son barin gidan domin tafara' zuwa ta Ai watar da Abunda ta shirya "Kai mutumin kana hutawa" faruk yafada yana mikawa Aliyu hannu hannushi ya mike masa suka cafke irin na Abokai Ya yunkura ya tashi daga ki shingidar da yayi yana mai da wayarsa Aljihu ya kalli faruk din yace "har ka gama zubar da girmannaka kai duk inda kaga taron mata ka dinga rawar qafa kenan ko kunya ba kaji ka tsaya gemai gemai da kai A gaban wadan can yaran kana wa she baki wai kai wane irin jinsin mutum ne' A cikin jerin mutane'iyi"? Yafada fuska babu walwala hararasa kawai faruk din yake ya marasa tace wa wai shi yake cewa shi wane irin jinsin mutum ne' baya duba kanshi shi A cikin wane jerin jinsin mutane nen zai saka kansa sai da ya mula sannan cikin murya kasa-kasa yace dan ba yasan ummi taji' wane topic suke yace "An tsaya din kasa kani A jerin duk jinsin mutane da kaga dama An so matan dan iska kawai kai har kana da bakin da zaka yi wannan zancan" faruk din ya fada A kule shiru Aliyu yayi ya bar maganar tasha ruwa yace "tashi mutafi" yafada yana duba A gogon shi "Anki din wai me ma zai kaika gurin dr hashim ne''? Gaka dai radau da kai kace kuma baka da lafiya ko wa zaka raina wa hankali oho'' faruk din yafada tana dauke idonsa daga kan Aliyu "yaya Aliyu ina kwana" kallon Nafisa yayi A karo na farko tun zamanta A gurin yana ya mutse fuska yace "yanzu kikaga da mar Gaishe ni ko ko kema ya koya miki halin nasa"? tana murmushi tace " yi hakuri Oganmu Ai bai isaba shi din me' Ai nazata bacci kake ne danaga idon ka A rufe " "ina kallonki da ido daya tunda kika zauna gurin bacci da safiyar nan sai kace wani irinki " yafada yana mata murmushi "Ayya Nima bana baccin safe ya Ali'' harararta yayi yace "kin mata sanda naje nai ta bugu na kai A wa daya A tsaye baki bude ba sai da mijikin yadawo ya haura sannan muka taddake kina ta bacci ko"? Cikin mamaki Nafisa tace "yaushe hakan ta faru yaya'Aliyu bansani ba" still' da murmushi A fuskarsa yace "kin manta dai yarinya ki zauna ki tuna ko ki tambayi mijinki gashi nan A zaune shi be manta ba Ai" Faruk ko haushi duk ya qume shi ganin yadda Aliyu yake ta shirma Nafisa ita kuma takasa ganewa sai biye masa take kallonta yayi yace "yaushe ki ka koma marokiya ne iyi sai faman yi masa banbadanci kike harda cewa wani oganmu' oganki ke kadai dai ni wannan ba oga na bane'' yafada yana gyara kwalar rigarsa kin tsaya kina biye ta tashi kamar baki san karyarshi ba wallahi sai ya mai dake mahaukaciya yanzu in dai Wannan ne yafada yana dukan ka fadar' Aliyu ransa A 6ace Me Aliyu zaiyi in ba dariya a ba ya dinga yi yana kallon faruk din wanda yaci mur yaki ya kalli inda yake balle ya tan kamasa sai da yayi mai isarsa sannan ya kuma kallon faruk din hade da kara kallon Agogo dake daure A hannushi ya mike tsaye yace "in kagama shan mur din ina jiranku A waje " ya sa kai ya fice daga falon bayan yayi wa ummi sai ya dawo Kwafa faruk din yayi yana kallon Nafisa wacce suka kacame da hira da Na'ima dan Ummi ta tashi daga gurin yace "tashi mutafi in kika samu hira ba kya gajiya ke Dariya Na'ima tayi tace "kai yaya 'faruk yaushe rabon damu hadu kasan in muka hadu sai Allah" Sakin fuska yayi yace "Ayya yanzu zamuje hospital ne kibari zan kawi miki ita ta yini har sai kin gaji tana dariya tace "kafin kama kawota ni na zo dan nasan fada kake" dariya yayi yace "haka dai kika ce "yafada yana kokarin fita yace in ummi ta sauko kya gayamata mun wuce kinji ko "ok zan gaya mata in sha Allah" A cikin mota suka tadda Ali' ya zuro kafarshi daya waje daya na ciki yana sauraron wakar mutuniyarshi janeefer cikin wakarta me taken (na nanaye) idonshi A rufe motsin mutum yaji yasa shi bude ido daya yana kallon faruk din wanda yake kokarin bude motar ita kam nafisa tuni ta kame A kujerar baya gyara zama yayi yana mika wa faruk din key' din motar yace "waye drever ka kar6i key' kaja matanka ka bani wannan kujerar da kake zaune banza faruk din yayi masa yasa hannushi can kasan motar yana laluben jarida" fuska babu walwala "kar6i mana Alin ya kuma fada A karo na biyu yana dariya kallonsa faruk din yayi A karo na farko ' yace "wai kai meyasa baka da mutunci ne iyi"? A gaban iyalina kake yi min wannan Abun sai kace wani yaron ka " "to da meye" Aliyu yafada yana kokarin tashin motar faruk din yace "kar kayi dreving din mana wallahi sai na rama" 'kai kasani" murmushi Aliyu yake yace "sai dai karame'' Alhaji" yanzu ma A rame kake sabida kasa jaraba cikin ranka banza faruk din yayi masa ya ciga ba da duba jaridarsa haka dai suka je Asibitin Aliyu yana ta faman jan Nafisa da zance faruk kuwa yi yayi kamar bai san yanayi ba kai tsaye ofis din Dr hashim dama Aliyu yayi mishi magana tun jiya yace zai zo misalin takwas ko tara yana zaune yana duba wasu takkadu sukayi sallama tashi yayi tsaye yana dariya yace " mazaje mazaje," wannan in ki yarsu ce tun suna yara hannu Aliyu ya bashi suka tafa suna Dariya haka shima faruk din' kallon "Nafisa yayi yace "Aa madam bissimilla mana'' yana nuna mata kujera fuska A sake zama tayi tare da gaisheshi lafiya kalau "ya jikin naki"? "Alhmdulilah doctor" "to masha Allah" ya fada "Kai mutumin haka Akayi A she"? Yafada yana kallon Aliyu " naji dadin nasara da A kasamu wallahi na kawo karshe wannan badaqala data ki taqi cinyewa sai ta sanadinka jiya na saurarin jawabinka A tv sosai naji dadi sosai Allah ya kara daukaka Ameen" Hade baki sukayi gurin Amsawa da Aliyu da shi faruk din cikin farin ciki sosai 'Aliyu ne yakalli Doctar hashim yace" kai gashinan fa iyalinshi ya kawo ka dubata yadda ya kamata kasan yakusa zama dady" yafada yana kallon faruk din yana dariya Dariya Dr yayi yace " kai sai yanzu kasani Ashe? ka zauna Kai Ai kowa ya wuce ka kazauna kana faman tuzuranci sai faman banka wa kanka kwaya kake da ranka da lafiyarka' sannan da kuruciyarka'' "Rabu dashi da Allah hashim kana batawa kanka lokaci ne Ai baya ro bane shi daza A dinga faman magana daya babu ji babu gani kar yayi Auran mana lafiyarshi Ai bata wani ba" A dage Aliyu yake kallon faruk din yace " Ai ni ban isa Aure ba da kake cewa ni ba yaro bane yaro ne mana A kanka tunda ni ban san Abinda Ake yi ba har Asamu ciki" Yafada yana sosa kunnesa da key din mota dariya hashim kawai yake yace "kai fa baka da mutunchi Aliyu har yanzu kuna nan da halinku ko daga kai harshi faruk din" "dallah inzaka rabu da shi karabu dashi malam" faruk din yafada A kufule idanshi A kan doctor yace "kaje ka duba miin mata kun zauna kuna faman wani zance " kallonsa Aliyu yayi yace "sorry baban boy' me ka keso Ayima iyalinna kane"? Duka faruk din ya kaiwa Aliyu yace "yafa isheka wallahi " wai yau dame katashi da shi ne iyi" ? dan iska kawai me fuska biyu wataran sai kayini ba kayi wa mutane magana ba sai kace wani kurma yanzu kuma kana nema ka' buwayi mutane " Tashi dr yayi ya nufi kujerar da Nafisa ta ke kai yace "Ai kun saba dama kai faruk man tawa kayi ko lokacin da muna pramary' skull haka kuke yi ha A dunga tunani fada kuke' A class sai daga baya A ka fahimci ba haka ba ne" Kallonsa Aliyu yayi yace "don Allah duba mana ita da kyau tana yawan kwanciya ga shi bata san cin Abinci yace ko ba haka bane "? idanshi A kan faruk yace " ka tambayeta mana gata nan Ai A gabanka ok " Tashi daga kan kujerar da yake kai yayi yakarasa can kusa da su Nafisa yace "kifada ma dr duk Abinda ki kasan yana da munki kinji ko?" "To yaya Aliyu'' "mara tace take daure sai rashin cin Abinci da nake in natashi tsaye jiri yana diba na " duk dai Nafisa tayiwa'dr bayanin Abinda yake da munta sannan Aliyu ya kuma inda yake ya zauna yana kallon faruk din yace "wai kai meyasa baka da hakuri ne iyi"? Duk da ban karanci likitanci ba Amma nagane me ke damun Nafisa ga yadda tayi bayani tace marararta ce ta ciwo sosai sai bayanta ga jiri yana damunta gaskiya faruk kana ta kurawa yarinyar nan gurin sex in kayi wasa zaka iya sanadin wannan cikin da muke ta murna Akai kallonsa faruk din yayi yana gyara fuska yace "kwarai kuwa gaskiyar magana ina yawan yi yanzu tunda ta samu ciki nan dan fisabillahi daya baya isata A rana sabida kwata kwata yarinyar ta sanja min gaba daya tunda ta samu ciki nake jinta wata da ban kai kanka kasan yawan jima'i bai da me ni ba in banda yanzu" Nuffashi Aliyu yaja yace "to yazama dole yanzu ka tsahirta tukun har cikin yayi kwari in yaso kome zakayi sai kaje can ka yi" Dr hashim ne ya kara so inda suke zaune hannusa rike da wata farar takadda kujerar zamansa ya nema ya zauna yana zare glass din da yake idonshi hankalinshi A kan faruk yace kasan me faruk sai kafada faruk yace' yace madam lafiyanta lau 'baby ma haka Amma Akwai hanzari wane hanzari ne inji ' faruk yafada kamar bai san Abinda yake nufi ba' zaka rage yin 'sex da madam duk jarabarka indai kana son babynka'ya zauna lafiya tunda, kaga baiyi wani kwari ba satin cikin yanzu goma sha shida' dana Auna yanzu shawara ita ce ba'a ce ka dai nayi ba gaba daya A,a karage kadinga daga kafa lokaci zuwa lokaci " in cikin ya kai wata biyar ko shida sai kaje kai tayin yadda ka gadama domin ita ma A wannan lokacin zaka temaketa ita da dan da ke cikin ta wannan shine Nima Abinda nake gaya masa kenan yanzu Aliyu yafada yana kallon dr hashim yacigaba da cewa " sai Anyi magana yace" shi jima'i bai da me shi Alhalin ga zahiri muna gani ko zai kife oho' dariya' dr yasa " yace kaifa mutumcinka kadan ne " Ali shima dariyar yake yace A shi ya koya min dallah malamai naji wannan kawai sharri ne da tsari irin na likitoci ya za,a Ace mutum da iyalinshi bazai nema ba sai lokaci zuwa lokaci to iyayanmu da ka kanninmu kenan da suke haihuwa lafiya me suka yi' sai kaga mace daya da da goma sha biyar kai har da me A shirin da wani Abu kuma ga ciki ga goye suke yi su me ya same su iyi? Faruk" din yafada yana kallonsu daya bayan daya" Kaji gaskiya ta fito ko' Aliyu' yafada bakinshi' yana rawa ' idonshi kan dr Yace Ai kaji da bakinka ni' yanzu ya gama ce min shi" sex bai da meshi ba' to ' kaga tun kan mutashi daga gurinnan ya karyata' kansa ' wallahi kaja mishi " ya yadda ya sa cikinnan ya zube' sai munyi " shari'a dashi ' Aliyu ya fada rai A 6ace''Allah yaso duk wannan Abu dake faruwa 'Nafisa na can kwance A wani daki " bayan dr yayi mata' scannin' yace taje ta kwanta ta huta ' Kallonsa ' faruk yake' yana murmushi ' hankalinsa A kwance dama neman hanyar da zai rama Abinda Aliyu n yayi masa yake' yace da kake wani tada jijiyar wuya zaka hanani' Abinda naga dama ne " matanka ko nawa' iyi ko kai kai mata cikin ? Banza Aliyu' yayi mishi' fuskarsa A daure kamar bai ta6a dariya ba yace ka san Allah " dr Hashim har kai zan hada mudun baka jawa wannan" gayan" kunne ba kasan kanshi " rawa yake ' da Anyi magana yace " wani iyali" ko yaushe yasan' wannan kalmar ma oho' yannda ' na ke son wannan baby ko shi ina tsammani bai damu da shi ba tunda yana sa wasa A'lamarin ' dukanninku zan iya daukar mataki A kanku wallahi ' Dariya kawai suke daga dr har faruk" din ganin yadda Aliyu yake zuba ruwan bala'i sai kace wani ubansu' mikewa yayi yana kallon Dr hashim yace bani" tablet' dinnan na wuce' bangane ka wuce ba baza ka tsaya A gama kashe cese' din ba ' wane irin ' cese Aliyu yafada yana kallon " Dr kai kasan shi mikewa ' dr yayi sai munje 'dakin' Ajiye magunguna" domin madam' Akwai wanda zamu daurata A kai zai taimakamata sosai yayi' kayau Aliyu yafada yana kokarin fita daga ' ofis din ko kallon " faruk din baiyi ba Tashi faruk din yayi' shima yana dariya' yace kai ka ke daure masa gindi ya ke zama Ahaka ko " duk sanda 'sha'awasa ta motsa sai yazo kabashi magani ko dukanniku " zan hada ku da Abbah wallahi" dan iska kawai' kai ba matar ne da kai ba yafada yana kallon Dr hashim din" bata fuska Dr yayi yace baka fini jin ciwon zaman Ali haka babu Aure ba " kasanshi da mugun taurin kai " ba irin sha warar da bana bashi " cewa wannan magani n da yake sha babu Abinda zai kara masa lokacin da yayi Amfani da shine kawai Aikin shi Daga zarar yaga zai dawu ruwa' kaga kuwa babu Abinda yaka ce shi in ba Aure ' ba sai Anyi magana yace' har yanzu bai ga wacce tayi mishi ba duk "yan matan garinan ' da irin matan da suke rubibi Akansa " gashi "A irin hallitar da Allah yayi masa mutum ne mabukaci sosai' tunda ba'ayin sati yake zuwa kar6ar "teblet din To duk wannan hirar da suke yi ' Aliyu ya dade da barin ofis' din " sabda haka kwafa " faruk din yayi yace ka kyaleni da shi " na san ta inda zan 6ulu masa ' wallahi sannan yace ina A kajiye min mata ne ko duriyar ta bana ji" dariya dr yayi yace gata can dakin ko bacci ya dauketa ne sai kaje ka tada ita " yana dariya ya nufi dakin yace Ai kam yanzu kuwa zan ta da ita duk da cewar ba'a tashi masu juna biyu A barci' To har baki motar dr hashim yara ko su suna ta barkwanci " tuni Aliyu" yana ciki jiran fitowarsu yake suna shiga ya tada motar yana dagawa Dr Hannu ' shiru motar kamar ba bu mutane A ciki ' sai sautin 'music' da yake tashi kadan kadan sakamakon rage' murya da Aliyu' yayi' kallonsa Faruk " din yayi yace' wai cin maganin me kake ne iyi' wai kai ina ruwanka ma ' ka kyaleni inyi yadda nagadama "" tunda nima ban isa in gayama kaji ba to nima ka kyale ni in yi yadda na gadama kowa yayi yadda yake so''''''''' kallonsa Aliyu' yake yana cigaba da driving" din yace me ka gayamin naki yi da har zaka ce kana gayamin ina kinyi " Magana daya dai A keta maimai tata ' faruk' din yafada ' wace irin magana ce " in ji Aliyu Maganar Siyama ce' in bazaka Aureta ba ka fito da wata daga cikin " yan matanka kawai ka Aure wannan shine ' magana ta'' wani irin tsaki Aliyu' yaja yace baka da hankali' da kake maganar in fito ' da wata daga cikin' "yan mata na in Aura " waddan "yan isakan ragowarku ' saurin jiyawa ' faruk din yayi yana kallon' kujerar baya ' yana 'Addu'ar Allah yasa 'Nafisa bata ji ba ' cikin 'sa'a kuwa ya ganta A kwan ce bacci ya dauke ta domin ' cikin Allurar da ' Dr yayi mata A kwai mesa bacci ' sabida tace masa bata bacci sosai' shine yayi mata ta dinga samun isashan baci Dawu da hankalinsa kan Aliyu yayi yace wai kai me yasa in zaka fadi magana baka taunata ne kake yin Abu gaba gadi ' yanzu in ta fahimta fa kace me,,,,hararasa "Aliyu yayi yace karya Akayi muku' iyi kunbi" kunga latse yaran ' mutane A titi sannan dan Baka da mutumchi " kace in je in nemi Aurensu " sai dai in zauna babu Aure kuwa " dariya faruk' din yake yace wallahi' Ali' sharrinka yawa gareshi" wasu "yan matan naka ma bansan da ina suke bulluwa ba' sai dai inga suna binka ' kai dai kasan in da ka kwa so su dan iska' har kura ce zata ce da kare maye ' dariya Aliyu' yake yana girgiza kai ", yace mubar wannan chafter" kana min maganar Siyama ko' yea' faruk din yafada' yana kallonsa ' girgiza kai' Aliyu yayi yana murmushi ' ya dade yana murmushi hade da girgiza kai shi kadai yasan Abunda ' yake hangowa A game da auransa da Siyama " sai da ya " mula' tukunna ya kalli ' faruk' din yace 'nabaka huqa da nama' kaje kayi' duk wani Abinda kasan Anayi Na Amince zan Aure ta "shikkenan ko? "Abinda yafi maka kenan yau din nan Zan sanarwa da Abbah wannan maganar kuma kar kayi tunani za,a dibi lokaci mai tsayi ' sati hudu za,a diba wallahi tunda babu Abinda aka nema aka rasa " ita Siyama ce Abin dubawa " ganin bata karasa' hnd dinta ba' Amma na lura kwata kwata babu son karatun A cikin ranta yanzu itama Auran take muradi' ruwanka ne kabar ta takarasa " kai in nine ma wallahi bazan barta ba tunfa tayi wasa da damarta ' faruk ' yafada yana sauke numfashi ' tsaki Aliyu' yaja yace' wannan kuma ruwanka ne kai da 'ita ni babu Abinda ya dame ni ' ruwanta dai faruk yafada yace Ai ni nayi mai wuyar ' tunda na yi mata kukari gurin ganin Auranta da kai ya tabbata ' banza ' Aliyu yayi mishi yaciga ba da dreving, motsin ,Nafisa yayi tana kokarin tashi hade da mamakin bacin da ya dauke ta ' kallon ' faruk din tayi' tace "my one" bani ruwa kaji magwogarona ya bushe A she bacci ne ya dauke ni ' eh man ba,a Allura Akayi miki ba dama yaya lafiyar kura' keda bacci yafada yana mika mata rubar ruwan "swan" yace ki kuma ki kwanta ko sai na dawu nan ki kwanta A kaina yafada yana kashe mata ido" hararasa tayi tana nuna masa"Aliyu " da ido" ta6e baki yayi yace rabu dashi _' me ma yasani shi wannan " Aliyu " yana jinsu uffan bai ce ba shi kadai yasan Abinda yake sakawa" To haka suje gida "faruk da Nafisa suna ta soyyaya Babu Abinda ya damesu ' shi kam Aliyu ransa A6ace yayi ,faking' din motar daidai get' din gidan " faruk , yace malam sai kafito , ko kaje can ka karasa A gida ' A fita Abar min mota na' cikin jin kunya " Nafisa ta fito kanta A sunkuye ' tana murmushi' yace 'Ya'Aliyu ' Asauka lafiya sama sama ya kalleta ' yace ' Ameen shikam' faruk bude motar yayi yace to ya san ranka,Alhji' me za,afasa ' shiru Aliyu yayi masa sabida ya fahimci ne man magana yake ' kokarin tafiya yake ' faruk din yace ina nan shigowa da magriba' in sha'Allah ' ok sai ka shigo din Aliyu yafada yana daga masa hannu To can gida kuwa ' suna zaune A falo sukaga' Siyama ta fito tana jan jakar kayanta cikin shin " tafiya ' kallonta ummi tayi tace' A,a Siyama ba dai tafiy ba ? Eh ummi jiya mukai waya da 'momy' wallahi kaninta babu' lafiya ,zamu tafi 'jos gobe in sha,Allah zamu duba shi ' tafada kamar da gaske' Ayya Allah ya sawake kuma me ma kon kifada tun jiyan sai kiyi shiru sai dai kawai muga kin fito da jaka cikin shirin tafiya yanzu kinyi daidai ke nan ? Cikin jin kunya 'Siyama takama yake tace ,laa Ashe ban fadamiki ba ummi wallahi na sha,afa ne''' hararata Na'ima tayi tace ko ni da muke kwana daki daya baki fadamin ba sai yanzu na sani wannan bai dace ba sis dariya ta hauyi tace Allah y huci zuciyar ki sisi na kada ma inje ki hanani tafiya kinsan dole sai da izininki sabida kece shugaba ' Dariya Na,ima tayi tace ni na isa " tunda kinriga kin gama shiryawa kije kawai Allah y kiyaye hanya " Ameen tace tana yake wanda hausawa suke cewa yafi kuka ciwo' Ita dai ummi bata ce ko mai ba tana ' mamakin yaran zamani da ba kunya Siyama tafito tsaf cikin shirin tafiya gida "ummi zan tafi baki da sako gurin momy ne" "A,a bani da shi ki gaisheta da kyau "ummi tafada " to shikken zata ji in sha,Allah sis sai munyi waya ko "tafada tana kallon Na'ima dake zaune tana kallonta da irin shigar da ke jikinta sai kace ba "yar musulmi ba tace " to Allah ya ki yaye hanya taciga da duba wayarta tana Ala wadai da irin tufafin dake jikin siyama' A tamfa mai tsada Anbi An ci mata mutumci Tana fita ta ci karo da Aliyu shigowarsa kenan yana kokarin kulle mota kallo daya yayi mata ya dauke kai yana ya tsine fuska ,Ransa A bace ganin irin kayan da tasanya gurin motar ta ta nufa wacce ke daf da inda yayi faking din tashi motar cikin iyayi da kwarkwasa tace sannu da zuwa" ya Aliyu yawwa ya fada batare da ya kalleta ba ya kama hanya zai huce da dan sauri " tace don Allah ina son magana da kai ka taimakamin yaya Aliyu tsayawa yayi jin ta hadashi da girman Allah ya jiyu yana kallonta kasa-kasa fuska babu walwala yace menene? Sai faman kar kada jiki take tana wani fari da ido irin na " yan duniya ta matsa kusa dashi kamar zata shige jikinshi hade da kama hannusa ta rike ta marai raice fuska tace yaya Aliyu ina Azaftuwa da sonka da kaunarka don Allah kasa mamin gurbi ko yayane A cikin zuciyarka duk yana jin Abida take sai faman nanikarsa take hada da murmurza masa hannu " ware mata idanunsa yayi gaba daya A kanta yana kallaonta dama gasu tubarkallah ba,kasafai yake bude idonsa ba duka sai ranshi ya 6aci sabida Allah yayi masa baiwar ido masu bala,in kyau da haske da kwarjini kallon daya yayi wa mutum ,sai ya firgita ,in dai ya bude su gaba daya sakar min hannu yafada yana kallon hannusa da ke cikin nata baka ce min komai yayana cikin ya tsine fuska ,yace me kike so nace miki yanzu bayan kin sani gaba kina neman kiyimin fyade wai ke wace irin yarinya ce mara kamun kai dubi shigar da ke jikinki haka zaki keta maza duk da a mota kike ke ko kunya ba kyaji ina tunanin tunda nake da ke banta 6a ganinki da hijab' ba sai kananun mayafai kina rabama, gayu jikin ki ko yafada idanunshi duka A kanta ransa A 6ace''' kuka tasa na kissa sabida ta fahimci baya son kuka tace nice zam ma fyade yaya,Aliyu' to me kike shirin yi yanzu dan" uwarki wannan shine wayewa ko dan kinga jiya na kyaleki shine kibari mana A shafa fatiha mana niba nasan mace mara kamun kai da nutsuwa in ma zaki gyara ki gyara " hawaye kai wai Siyama take yi tace ni kam soyayarka ta zamar min wahala inatayi baka san inayi ba ' dan Allah kadinga kula ni wallahi zan iya mutuwa in ban Aure ka ba' tafada fuskarta jage jage da ruwan hawaye har yanzu idanunsa yana kanta yana nazarinta yana mamakin wannan wane irin so take mushi ya tabbata babu karya a cikin maganar ta duka gsky ne Girgiza kai yayi cikin zuciyarsa yace Allah mai yanda yaso shi kam ko digo daya baya jin birbishin sonta cikin zuciyarta sai irin na Addinin isilama shi kam ya zaiyi ne " kallon idanta yayi sai yaji tabashi tausayi " yace ki min shiru meye Abin kuka A nan iyi? Kin kasa fahimtata ne Siyama ba wai ina kinki bane a,a haleyenki ne bana so kije ki canja halaye ' ni kuma zanyi kokarin kula da ke wani irin dadi ne ya lullu6e 'Siyama n bata san sanda ta daka tsalle ta rugumeshi ba' wanda yayi dai dai da shigowar su Dija' ciki gidan A bakin get' haruna ya Ajiyesu sakamakon kiranshi da Abbah yayi A waya cewar yaje ya kar6o kayan cefane ,A kasuwa ya biya kudin' tun jiya " Dije ce kawai ta gani saurin dauke idonta tayi daga kansu tana kara mamakin Abun " cikin ranta tace Ashe "yan iska ne dama babu ruwana da su wallahi kada zunubinsu ya shafe ni ,Allah ya shiryesu tafada cikin ranta da ta tuno jiya da daddare ma A haka tagansu sauri shigewa tayi ko sauraron jiran fa,iza bata yiba domin ita yanzu Abinda zai hadata da Aliyu ma ba kaunarshi take ba . Shi kam Aliyu da kallo ya bita yana mamakin da baya iya yi ma yarinyar kallo daya sai ya kara shida bai cika kallon mutum ba in ya kalleka sau daya shikkenan duk maganar da zakuyi zakuyi ku gama hankalinshi yana kan Abinda yasa gaba sai dai in ransa ne ya 6aci shine zai zuba ma ido da idanun yake horar da mutum har sai kai laushi sabida kwarjini da Allah ya bashi Cire Siyama yayi daga jikinshi yace "meye haka yanzu ? Ke kam bazaki bar halinki ba" sai faman yake take tace "son ka da kaunarka ne duk suka ja'' ta6e baki yayi yace "ina zakije yanzu? Duk dadi ya isheta sabida ganin ya'Aliyu yana sauraronta bakinta na rawa ta shirga masa karya kamar yadda tayiwa ummi Ok Allah ya sawake in kinje kiyi masa sannu da jiki kinji ko ki gaishe min da momyn yafada yana tafiya to zata ji in sha Allah tafada tana buga tsale ganin baya kallonta tace kafara zuwa hannu' dan rainin sense sai ma munje gurin uban Arna sai ka raina kanka duk wannan miskilacin naka sai ya sauke makashi Yana tafiya yana mamakin yarinyar A ransa yace girgiza kai yayi kawai yace yaro bai san wuta ba sai ya taka shi kadai yake dariya cikin ransa yana tuna irin tanadin da yayi mata zaiga karshe iya iskancinta in da ya tsaya Falon ya shiga kai tsaye dukanninsu suna zaune harda Asabe me Aikinsu" Ana ta hira sai dariya sukewa Dija wace take zaune kusa da ummi Sai faman masifa takewa" Fa'iza wai tana gani malamin engilish dinsu yadake ta Akan wani subjet' da,yayi wanda ita Dijan takasa fahimtar ko mai Aciki sabida Abin yayi mata tsauri tana ganin fa,izan ta bada Amsa, Amma takasa ce masa ita bakuwa ce a makarantar shine take faman jin haushinta Sallama yayi yana kallonsu kai tsaye idonshi A kan Dija ya sauke shi " yana kare mata kallo kanta babu dan kwali duk ta cire har guntun hijab din gashin A daure himili guda a tsakiyar kanta tana zaune sai faman masifa takewa fa'iza ita kam fa'iza cewa tayi wallahi babu ruwana haka kawai in baki Amsa A zaneni to kawai sai in ce masa ke bakuwa ce salon yaha da dani ya daka kowa tasa ta fi sheshi hayayyaqo mata Dija tayi tayi kanta tace to wallahi sai na rama dukan Akan ki kan kace kwabo Dija ta haye kan Fa'iza zata daka Ita kam fa'iza tsayawa yayi kawai tana kallonta domin bata saba da wannan wasan ba karaso wa yayi gurin fuska babu yabo babu fallasa, yasa hannu daya daga ' Dija daga kan Fa'iza kamar wata "ya tsana ya Ajiye A kan kujera ko kallonta baiyi ba domin tsigar jikinshi yaji tana tashi kadan kadan fa'iza ya mikawa hannu wacce ke kwance a kasa tana jiran dukan Dija kamma hannu tayi ta tashi zaune yace ke kam kinji kunya duk wannan girmab jikin naki kibari wannan ta kayar dake harda " hayawa kanki kin tsaya kina kallonta wacce kina nai mata duka daya zata fadi """ dariya falon ya dauka, harda ummin Asabe ma ba,abarta a baya ba ita kam Na'ima kamar tafado daga kan kujera dan dariya harararta Aliyu yayi yace meye ,Abinda dariya Anan dan ubanki shiru tayi tana mai da dariyar ciki ummi tace har damu zaka zaga tunda muma munyi dariya ba,abin dariya Akai ba kuka fa,iza ta fashe dashi domin ita hawa kanta da Dija tayi bai mata ciwo ba illa dariyar da suke mata wanda harda ita Dijan Yaya Aliyu kaganta tana yimin Dariya ko tafada tana nuna Dija kyaleta zan nuna miki yadda zaki dinga yi mata kema, in ta kuma hawa kanki da kokawa "kice mata yar kauye mai hawasan jakai' kinjiko tunda ita kunne kashi gareta'' shuru Dija tayi bata ce ko mai ba Amma ranta ya 6aci kallonta Aliyu yayi yace "malama ina dankwalinki ban hanaki zama babu dan kwaliba iyi? Dago kai Dija tayi tana kokarin kallon inda ta zaauna hijab din skull din ta hango can kusa da kafar ummi sabida haka bata ce komai ba ta tashi taje ta dauko ta zira ta kama han yar dakinsu Cikin magana kasa kasa take cewa "ko ina ruwansa da dankwalina oho kawai sabida a dinga ta kura mutane " bata yadda yaji Abinda take cewa sabida tana jin tsoron dukan da zai mata in yaji dakin tashige ta kwa6e unipom din tasamu zaninta ta daura iya kirji tashiga toliet wanka dan ita ma gwanar wanka ce a rana tayi sau uku zuwa hudu wanka tayi tafito daure da zanin taje ta dauko wasu riga da wando na fakistan'' tasa mai kawai ta safa a jikinta bata yi tunanin yin wata kwaliyya ba kayan sunyi masifar yima ta kyau sun fito mata da Ai nihin qirar jikinta '' bom,bom din ta ya fito a cikin wando duk da wando bayi da 'shaf' Amma yafito ya zauna das das sabida rigar me shaf ce ga tsaga da ta ke dashi a gefe da gefenta cikinta kuwa A shafe kamar wacce bata cin Abinci """ kirjinta kuwa sun fito sunyi cir cir kamar goroba Alama ce da bata jima da fara irgar dangi ba tunda wani lokacin ma ba'a gani in dai ba kurawa gurun ido kayi ba Alamun bayyanar fara girmanta sunfi ga mazaunanta dan karamin hijab dinta take nema gaba daya tafito da duk kayan sif' din har na fa,iza ma basu' tsira ba ranta a 6ace tace to ina hijab dina tun ranar da suka zo bata ne meshi ba sai yau dashi tazo garin kuma haka takaraci ne mansa bata ganshi ba ran ta a 6ace ta fita daga dakin Still dai kanta babu dan kwali domin ta manta ma dama hijab din take so tasa, kan fa'iza ta tsaya tace ke fa'iza baki ga hijab dina ba ? Da kallo suka bita har Aliyu shima yana falon har yanzu suna hira da ummi kallonta fa,iza tayi tace' ni zaki tambaya banganshiba to ba dole na tambaye ki ba kije ki duba min cikin kayanki ko yana ciki' bazan jeba fa,iza n tafada tana tashi daga gurin da nufin zuwa ta cire unipom dinta ''' ya Na'ima kiyi mata magana ta dauko min hijab dina Dijan tafada' idonta a kanta kamar zata yi kuka ummi ce tace "ban da Abunki Dija" hijab din daya ne da ke kije kisa wani mana mybe, shi wanda kike ne ma yana gurin wanki ko kallonta Dija tayi tace shi daya ne dani ' ummi Ai '' ok yi hakuri ke Na'ima dauko mata A ran naki tasa kafin gobe sai ku shiga kasuwa" ayimata siyyaya A binda bata da shi kin ji ko '' to Na'ima tafada ta mike tana kallon Dija tace "ko meye Abin kuka Anan oho kwai sabida bakiga hijab sai kidinga 6are wa mutane baki" sabida shagwa6a tafada tana dariya'' "ke kam kin cika zubar da girma ummi tafada tace' yanzu kuma in tarama kice zaki dake ta sai kace wadda kuka samu jaka' tana tafiya tace "ke dai ummi bakya son laifin Dija' tace "e ba naso din" ummi n tafada Shi kam Aliyu tunda yayi wa dija kallo daya yayi saurin dauke kansa fuska ya dinga ya mutsewa bai ce komai ba cikin ransa kuwa yana mamakin yarinyar gaskiya duk Namiji' da ya san mace yasan menene mace to ya kalli "Dija yasan tana cikin jerin mata masu Amsa sunansu babban Abin bada mamaki ma yarinyar bata gama cika mace ba Amma ko mai ya fito masha Allah"" sabida haka hannusa ya zira cikin Aljihun jins din daya ke jikinshi yana laluben glass dinshi fuska babu walwala ya dauko ya zira sannan ya dago kai yana kare mata kallo tunda ga kafafunta har zuwa tsakiyar kanta lokaci guda sai ya dinga jin wani matsanancin kishinta yana damunsa fuska A mutukar murtuke yace " wuce daga kan mutane yarinya mara tarbiya kawai kinzo kinyi wa mutane kerere Aka wallahi wataran sai na raunata ki na ji miki ciwo shasha " vileger" kawai " sai zuba ruwan bala,i yake wanda shi kanshi bai san dalili ba' Amma baya rasa nasaba da jin wani irin bala'in kishinta yana kamashi Cikin kujera taje ta zauna tana zumbura baki bata ce ko mai ummi kam cewa tai "kai kam kana da ta kurawa me tayima ne ' shiru yayi bace komai domin sai yaji zaman a gurin ya gundureshi wayarsa ya dauko yana daddadannawa bai kuma kallon in da take ba Ummi tace "da yamma Na'ima sai ta kaiki salon ko Dija ? A wan ke miki gashin nan naki ko baya damunki ne"? Sakin fuska Dija tayi tace 'yana damu mana ummi' Ammafa bana son kitso Abar min haka" ummi tace "da har ina cewa Ayi miki kitso zaifi miki kuma zaki ji dadi kan" "A,a ummi ni dai " Dija' tafada kallonta Aliyu' yayi yace "to wallahi kitso za,ana yimiki bazaki dinga yi mana yawo da gashi a gida ba kina hana mala'iku rahama su shigo mana gida in ba haka ba sai dai ki wayi gari kiga nayi miki kwal kwabo sosai zan Aske miki kan tunda bakyajin magana'' ya hakikance sai faman bala'i yake zuba masa ido ummi tayi tace " wai kai ina ruwanka da yarinyar nan ne iyi? Kabi kadamu da lamarinta' don Allah karabu da ita ta sake mana'' Saurin gyara fuska yayi yana kallon ummi' yace "rayuwar da tayi abaya baza tayi ta ba yanzu lokacin da tana gaban Nene sai Abinda ta gada ma take' Anan kuwa wallahi ummi bazatayi ba" sabuwar tar biya za ayi mata can daban nan daban" duk yanayin wanan fadan ne sabida yaji ummi tayi maganar zuwa gurin saloon so yake ya soke fitar kallon ummi yayi yace Akwai wata mata data ke zuwa tana yiwa Nafisan faruk kitso ita Na'ima n tasan yarinyar kice tayima 'Nafisa waya ta turo yarinyar sai ta dinga zuwa tana yi mu su kitson gaba daya Amma daga yau na soke zuwa gurin saloon kitso ko wankin kai Hararsa ummun tayi tace "to sannu ubansu ka hakikance sai faman fada kake kamar wani wanda Akai wani Abun " zo nan " Dija ummi tafada tana dauke idonta daga kan" Aliyu' zuwa Dijan tayi gun ummi n ta zauna A kasa kusa da kafafunta kama kan ummi tayi tace "wannan gashin naki dole sai An wanke shi sosai kafin Ayi kitson " kiyi hakuri ana minki kitso kin ji ko " to Ummi Dija n tafada" Tsaki Aliyu ya dan ja kasa kasa shi kadai yasan Abinda yake da munshi'' mikewa yayi yana kallon ummi yace "zanje in kwanta zuwa biyar na yamma" kallonsa ummi n tayi tace '' to Abinci fa? "Ok kibarshi kawai ummina inna tashi naci yanzu ban jinyunwa'' "shikkenan Ai " ummi n tafada tana cigaba da warwarewa Dija tufkar da take kanta gashinnata kallo daya yayi musu ya sa kai ya fice daga falon To Siyama kam lokacin da taje gida momy n ta tana zaune A falo ita da babbar Kawarta hajiya ladidi suna ta hira cikin farin ciki hajiya ladidi tana bata labari sabon malamin da tayi A can da garin nasu cikin zumudi momy tace haba dai yaushe zaki rakani " kin tabbatar ya iya Aiki in ce ko? rike baki hjy ladidi tayi tace "Ai shi wannan akin shi kamar yankan wuka ne karki damu sabida haka duk sanda kika shirya sai kizo in rakaki " Amma Asubanci zamuyi " domin Akwai layi A gurin " jiki na rawa momy tace "ni kam ko yanzu ma A shirye nake wallahi "kallonta hjy ladidi tayi tace " me kike ci na baka na zuba mubarwa gobe mana sai mutaki sa'a" "to Allah ya kaimu momy tace" tana Allah Allah gobe tayi suje' domin ita kam duk inda taji sabon malami ko boka "yan tsubbu da sauransu jikinta har 6ari yake" shiyasa dadyn Siyama gashin Asusuce kamar wani shashassha kullum ka ganshi tsabar ta wanke ta bashi ya shanye To suna tsaka da wannan hirar ne Siyama tayi sallama kai tsaye cikin kujera taje ta zauna tana ya mutse fuska Wallahi na gaji momy tafada ko sallama batayi ba washe baki momy n nata tayi tace "dama yau zaki dawo doughter ko waya Ai kyayi min ko insa delu mai Aiki tai miki girki na mussaman tafada tana faman washe baki ya tsine fuska tayi tace yanzu Aikin me take ki kirata mana tayi min Ai kam yanzu kuwa kuwa momy tafada tana kwalawa delu kira hjy ladidi ce ta kalli Siyama cikin washe baki tace babu " magana ne yar gidana '' kallonta Siyaman tayi tace "o momyn Samha yakike"? "Lafiya lao nake " tafada tana wangame katon bakinta ko kunya bataji ba *nikam nace kunyi Asara wallahi kudinga yiwa "yayan cikinku biyyaya* "baki tambayi mutuniyar taki bah " in ji hyj ladidi " Ayya yaushe ne mukai waya da,ita ne ki gaishe ta bani da numbar ta yanzu Ai " jiki narawa hjy ladidi ta zaro wayarta daga cikin jaka tace "kawo in sa maki numbar tata " Ai tana can tana korafin kin daina mu,amala da ita ko Ayawa ne" "laa habadai numbar ta ce in nakira bata shiga" "e Ai tacanja ne mi kamata wayar tayi tasa mata numbar sannan ta tashi ta nufi dakinta'' momy , kam sauke numfashi tayi tace "Ai koda zan rasa zanin daurawa Sai Siyama ta Auri yaron nan dubi yadda yarinya ta kyakyawa tabi ta susuce sabida son data kewa yaronan" "Wane yaro ne wai ta kwallafa rai A kanshi iyi" hjy ladidi take tambayar momy "hummm!! dan gidan Alh bashir craman mana danshi na fari Aliyu gashinan yana Aikin soja' ko kwanaki rigimar da taki ci taki cinyewa A can jahar taraba da taimokosa Aka kawo karshenta bakya kallon tv ne Ai har hira,Anyi dashi da sauron ,sojojin da " yan ta adda da ya kama jiya, dady' Siyama yake cemin har karin girma Akayi masa'' sai zuba momy take' ita kuwa hjy ladidi bata sauraronta tun lokacin da ta fahimci' wa take nufi ''' ta tsunduma cikin tunani tana girgiza kai cikin zuciyarta tace ta6 dijam lallai za ,ayita yaron da "yarta take mutuwar so take nufi" Ai kam itama yadda taci Al,washin ,"yarta Samha sai ta Aureshi itama sai ta cikama ta burinta kamar yadda ta daukar mata Alkawari Yaqe kawai hjy ladidi take wanda hausawa sukance yafi kuka ciwo tace "ina bayanki hajiyata gobe karkisa wasa zan fito da wuri sai mu dau hanya Allah ysa muje mutaki sa'a Amin " momy tace cikin farin ciki ta samu wani malamin tana da tabbacin ya'iya Aiki tunda taji hjy ladidi tana wasashi Gab da magarb Aliyu yata shi daga wani nannauyan bacci da ya dauke shi tun bayan da ya sha maganinshi na fama ya kwanta A gajiye yana ta faman sake sake cikin ransa har bacci ya sidado yayi A wun gaba dashi jiki a mace ya tashi yafiti minti goma A zaune kafin ya mike cikin mutuwar jiki' A gurguje " yashiga toliet ya hada ruwa mai dan zafi ,ya watsawa jikinshi sannan yayi brush ya daura ,Alola yafito daure da guntun tawol jalabiyya me yan kakken hannu ya zura sa gaje wando" sannan ya feshe jikinshi da turaranshi wanda ya riga yaga kama jikinshi sabida yawan Amfani da yake dashi komai na dakin kamshin turaran yake mussaman tufafinshi "carbin shine A maqale A dan ya tsanshi sannan ya zira wani silifas na zallar fata' mai uban taushi kafafun nan kuwa sunyi kyau Acikin ta kalmin' kamar ka matsa jini ya 6illo tas dasu Kai tsaye ma sallaci yanufa jin An fara kiraye kirayen sallah bakin shi dauke da tasbihi ga *Allah jallah wa Azza* baba mai gadi ne ya tashi yana kokarin bude masa A karamar kofa Aliyu ya da katar dashi yace haba baba Kofar ma sai ka bude min Alola fa kake to ko ba Alolo kake ba kawuce ina tsaye ka bude min kofa ni Aiki me nake iyi " bude get da kake wannan Akan Aikin ka kake, hannu baba me gadi ya ya daga yana dan rankwafawa yace "godiya nake, uban gidana "Ai girmanka ne yafada yana dariya shima Aliyu, dariyar yayi kadan yace "ka gode wa Allah domin shine Abin godiya'' yafada yana kokarin bude kofar ........................................... Yana fita motar Abbah tana sawo kai layin "haruna drever" yana jansa dan tsayawa yayi sai da ta karaso sannan ya dan rankwafa yana wa "Abbah barka da zuwa "" sannan haruna, yaja motar bayan ya gaida oga Aliyu" dan haka suke kiranshi Sai da ya jirayi isha'i sannan yafito daga masjid" din yana fitowa suka hadu da Abbah sabida haka tare suka jera zuwa gida suna hira kamar wasu Abokai Tare suka shiga falon wanda kowa ya hallara Aciki har jameel yana nan bayan ya gama yawon boll dinshi Dija tana zaune kusa dashi wayarsa na hannuta tana ta faman gem da ita saurin dauke idonshi yayi daga kansu yana jin wani matsanincin bacin rai kan kace kwabo ya hade fuska tamau ! tamkar wanda bai ta6a dariya ba tunda Allah ya halliceshi can dannig ya nufa jameel kam cikin sakin fuska yace "broth barka da yamma" yana tafiya yake Amsawa " "yawwa barka kadai ya yau kashigo da wuri ko babu , kwallo ne"? Yafada yana kokarin danne Abinda yake taso masa yanzu nan A game da jameel din' wanda shi kanshi bai san me nene ba"" cikin dariya jameel din yace, "yau kam babu Amma gobe muna da me,zafi " "to Allah yabada sa'a" Aliyu yafada ya na kokarin zama cikin kujerar cin abincin """ Dukkansu suka hada baki gurin yiwa Abbah barka da shigowa duk da lokacin da yashigo sunyi masa to A gurguje ya Amsa,Sabida yana saurin wucewa massalaci kada jam'i ya shigeshi can kan kujera ya zauna yan fito da wayarsa ya mikawa ' Na,ima wayar yace " kiramin Nene wai tunda ta tafi ma kun kirata kuwa yafada yana tsayar da idonsa kan jameel'' dariya jameel din yayi yace "ni kam kullum sai mun gaisa da ita Abbah, ito Na'ima cikin shagwaba tace "Abbah bani da credit, A wayana ne shiyasa """ ita kam Dija tsalle ta buga ta tashi daga kusa da jameel ta koma kusa da Abbah tana dariya tace "yawa Abbah A kirata mu gaisa " Allah sarki Nene tana can ita kadai" Bugu daya Na'ima tayi A ka daga da sallama wa,alaikassalam Na'ima tafada tana mikawa Abbah wayar daga can 6angaran kuwa Nene sai faman rafka sallama take cikin sauri Abbah ya kar6i wayar yace Nene barka da dare yawwa barka kadai ya mutun gida Nene tafada sabida ta fahimci Abbah ne kowa lafiya lao ya jikin naki ? Yaya su baba malam jiki Alhamdulih Ai gajiyar hanyace kuma na warware su baba malam sunan lafiya lau yace ma,a fada maka yaga sako Allah yakara budi yajikan magabata " to masha Allah Abbah yafada sannan yace haba Ai su yanzu muke gani A matsayin iyayenmu in bamu yimusu ba waza muyiwa ,Allah dai yaja mana da ransu"" Ameen ya Allah Ai' nima haka nake cemasa meye' Abin godiya Ai yiwa kai ne duk gaba daya An zama daya shine yace Ai godiya dole ce''' dariya Abbah yayi yace baba malam kenan" sannan yace Nene ga Dija zaku gaisa da sauran yara" daga can 6angaran Nene tace "Au Ai nazata ta mance dani Ai " dariya Abbah yayi yace " ita A wa Ai gatanan ma tana ta murna" ya fada yana mikawa Dija wayar cikin zumudi Dija takar6i wayar tana dariya tace "Nene ina yini"? itama daga can Nene dariya take tace " yar nema da banyini ba Ai bakyaji muryata ba in ce ko kin fara nutsuwa'' Nene tafada tace domin jameel yaga yamin kin fara zuwa makaranta ko? ''Eh Nene" "to kitsaya kiyi karatu sosai kinji ko'' "to" Dija tafada tana Allah Allah ta fara tambayar Nene kawayenta su indo da sa'a Nene tace "duk suna nan lafiya lo suna ta kewarki dariya , Dija tasa tace wallahi nima ina ta "kewarsu kice ina gaishesu da kyau ''Abbah yace "duk randa Aka samu hutu zamu zo hutu' suyi min tana din kyan dadi dariya Nene take tace to za'a fada musu hakadai Nene da Dija suka dinga shira A waya kamar ba kudi Ake kwasa ba daga' bisani Dija ta mikawa Abbah wayar sannan daya bayan daya "su Na'ima suka kar6i wayar suka gaisa da Nene sai tsokanarta suke musamman jameel ummi ma sun gaisa cikin mutumta juna da karamci Faruk ne yayi sallama ya shigo falon kai tsaye kujerar kusa da Abbah ya nema ya zauna yana kara gaishe da ummi ummi tace ''dazu kuma sai kuka tafi babu sallama ko"? Murmushi faruk din yayi yace "munyi laifi ummi Amma ba laifi na bane kinga mai laifi can'' yafada yana nuna inda Aliyu yake zaune "to Ai babu laifi'' ummin tafada lokacin da take tashi A gurin Mai da hankalinsa yayi kan Abbah daya fahimci ya gama wayar da yake cikin ladabi ya mikawa Abbah hannu hade da dan risinawa daga kujerar da yake kai yace ''Abba barka da dare " shima Abbah cikin sakin fuska yamika masa, hannu sukai musabaha sannan yace "barka kadai umarulfaruk ya daran ya Akin naku''? lokaci guda Abbah yayi mishi wannan Tambayar ''komai lafiya lau Abbah" "to masha Allah Allah ya taimaka'' jameel ne ya mikawa faruk hannu yace barka da dare rike hannu faruk yayi yace barka kadai' sannan yace "wana kama'' ? Cikin dariya jameel yace "ni'' shima dariyar yake yace" idonka kenan ko jameel ka6uya ka 6ata 6at ball' ta 6oye ka ko"? da kana zuwa mu gaisa yanzu ka daina zuwa ko? Har yanzu dariya jameel din yake yace " kayi hakuri bro kasan A binne sai A hankali wallahi Amma zan dinga daurewa ina zuwa' Ai mugaisa'' "da ka kyauta wa kanka'' faruk din yafada yana sakin hannunsa. Su ko su Na'ima dariya kawai suke wa jameel sannan suka shiga gaishe da faruk din cikin bar kwanci ya dinga Amsawa sabida dama can shi mutum ne me wasa da dariya sa6anin Abokinshi da yake muskili wanda magana bata da meshi' ba in basa kansa yayi ba tsayar da idon shi yayi kan Dijawacce ke zaune cikin kujera sama sama ta gaisheshi sabida ta fahimci Abokin' ya'Aliyu ne ita ko duk wanda ya shafi Aliyu bata kaunarshi in ka cire " yan uwanshi sabida haka dauke' kanta tayi ta mai da kan tv tana turo bakinta As'useal yace "ke yar kauye yaushe kika zo birni ma da har ki ka'iya kallon tv iyi? Dariya Na'ima tasa tana kallon Dija' wacce ta kurawa' tv ido ranta'A6a ce da ta fahimci cewa da ita faruk yake jameel yace kaima kafada ta kurawa tv ido kamar wacce take fahimtar' Abinda Ake fada jiyo wa Dija tayi tana gallawa jameel wata, harara hade da girgiza kai Dariya yasa yace'Ai ba karya A kayimiki ba "yar kauyan ce ke dariya, falon ya dauka" harda fa'iza kuka Dija tasa tana kallon Abba tace "Abba ka gansu ko'' gyaran murya Abbah yayi yana kallon jameel yace "meye haka kai ma har da kai ko faruk iyi ku kyaleta zo nan uwata "Abban yafada yana nuna mata kusa da shi tashi tayi ta ko ma kusa da Abba n tana share hawayenta Shi kam Aliyu yana daga can kan dannig sai tsaki yake ja yana zagin faruk din A cewarsa ya zauna yana shirme da yara sabida tsabar zubar da girma to su Na'ima da suka fahimci Y'a Aliyu ya kammala cin Abinci sabida haka sai suka nufi dannig din suma domin cin nasu A ka bar Abbah da faruk din Yana ganin sun doso gurin cin Abin ci ya tashi daga gurin barin falon ma yayi gaba daya ya huce can bangaransa Faruk din ne ya gyara zama yana kallon Abbah yace "Abbah Akwai maganar da takawo ni dama gurinka'' "To'' Abbah yace yana kallon faruk din' yace "ina sauraron ka " hade da mai da hankalinsa kan sa din kacokan "yawwa dama Akan maganar Aliyu ne da Siyama Ataikaice dai' dazu ya tsayar da magana daya cewar ya Amince Ayi komai A gama daga, nana zuwa sati uku masu zuwa ko sati hudu in Allah ya nufa Annuri ne yadinga sauka A fuska Abbah fuska Asake yace "ma dallah da Aboki nagari ma dallah da Aminci na gaskiya naji dadi da wannan maganar da ka zo min' da'ita in sha'Allahu yanzu nan zanyi yiwa dady' Siyaman magana, sabida dama mu suke sauraro Allah ya shige mana gaba Ameen" ''Ameen Ameen kawai" faruk din yake fada cikin farin ciki daga bisani ya mike yana yiwa Abbah sallama' Abbah yace "A'a tsaya mana umarulfaruk muci Abinci ko'' "Alhamdulilh'' Abbah A koshe nake wallahi'' "to masha'Allahu" Abbah yafada hade da cewa "ka gaishe min da mahaifinnaka da kyau kaji ko'' "zaiji in sha' Allahu Abbah " yafada sannan yayiwa sallama ya fice daga falon Kai tsaye 6angaran Aliyu ya nufa domin yasan ba fita yayi ba fuskarsa cike da walwala Yana zaune gefe katifarshi yana duba loptop dinshi faruk din yashi ga da Sallama daga kai Aliyu n yayi yana Amsa masa sallama gefen shi ya zauna yace "yanzu muka gama magana da Abbah yace yau dinnan zai samu dady' Siyama za'atsayar da magana daya A she suna can suna sauroro daga nan 6angaran Ai Abbah yaji dadi' sosai sosai Kai dai Allah ya nuna mana lokaci" yafada yana kallon Aliyu banza, Ali yayi masa yaci gaba da duba loptop dinshi hankali kwance dariya faruk din yasa yace "wai fati' nawa ma zamu fita ne kasan dole mu raqashe mu dagargaji biki yadda ya kamata" kallonsa Aliyu yayi A karo na farko tun zamansa A gurin yace "A wane biki zaku dagargaji fati? Ba dai A wannan ba ko" "yes" ya san ranka kasan baza muyi biki lami ba' dole sai mun dan ta6a girgiza kai Kawai Aliyu yayi yace "Allah ya bada sa'a Amma duk A binda zakuyi kuje kuyi ku kadai kar wanda ya nemeni in bahaka ba kasan zan iya warga za ko mai sabida babu ni A cikin wannan bidi'ar " "sai kayi kuma duk Abinka sai mun cashe yadda ya kamata ehe"! faruk din yafada, yana dariya yace "Ai ban hana ba cewa nayi kar wanda ya sakani cikin Al'amarin dan wallahi zan' iya lalata wa lokaci guda kasan dai' halina" Gyara fuska faruk din yayi sosai yace "bafa na son rashin mutumci kai baka ga irin kokarin da A kema bane iyi? Da zaka ce babu ruwanka A ciki kai ne mai ruwa kuwa tunda tilas duk fatin da A ka shirya sai ka hallata don Allah kar kabamu kunya mana haba Alhji yarinyar nan fa tana sonka sosai kayi kokari ka fitar da Abbah, kunya mana" Tsaki Aliyu yaja yace "Auran dole fa za'amin me kake so nayi don Allah ka kyale ni tunda na ce na Amince ba shikkenan ba meye kuma za'a dame ni da wani Abu'' girgiza kai' faruk din yayi yace wai "kai wane irin mutum ne'? Sai An taroka Acan sai ka zille ka kuma wani guri kaifa ba yaro bane" kallon faruk din yayi ganin ransa ya6aci "to me kake so inyi yanzu bana ce na Amince ba" "eh Abinda nake so dakai shine kasaki jikin ka don Allah Ayi komai da kai kar kabamu kunya" faruk din yafada yana kallon Aliyu cikin rashin walwala "shikken Abinda zanyi"? inji Aliyu "eh shikkenan sannan kayi kokari ka saki ranka Akan yarinyar har Ayi a gama in yaso duk Abinda zakayi sai kayi bayan bikin" "to zanyi Aliyu yafada yace sai kuma me"? Banza faruk,din yayi dayaga yana nema ya maida Abun wasa kai nake sau raro Aliyu yafada .......…….............................. "Ka mai dani dan iska ko wato Abin zaulaya na zama Ashe" faruk din yafada yana kokarin mikewa yace "bara na kama gabana ina da Abinyi A gida kaje kayi Abinda kaga dama'' yafada yana daga kafada sama Alamun Abun bai da meshi ba dariya Aliyu yasa yace "zaka kama gabanka Anan to kayi sauri katafi gida yana can yana jiranka A bi dokar likita A zauna lafiya Dariya faruk din yasa yana girgiza kai hade da girmama irin rashin mutumcin Aliyu yace eh duk Abinda zaka ce kace ya fada yana kokarin barin dakin' cikin sauri' Aliyu ya mike ya tari gabansa yace " ina zaka Ai bamu gama magana ba" "wace irin magana zamuyi bayan kana nema ka maidani mahaukaci'' "sorry Abokina na ji duk Abinda kafada duk yadda kace haka za'ayi yafada da murmushi A fuskarshi ta6e baki faruk din yayi yace "wannan kuma Abinda ya shafe ka ne" yana dariya yace " ya shafemu dai " sannan yakama hannu faruk din suka koma suka zauna suka cigaba da hirara su irin ta Abokai To A daran ranar Abbah ya nemin mahaifin Siyama suka tsai da magana cewa nan da sati hudu za'ayi biki dady Siyama yaji dadi sosai sabida haka cikin zumudin ya shiga bangaran momyn Siyama zai gayamata wannan Albishir din ya tarar tayi bacci haka ya hakura ya barwa gobe sabida haka bayan ya sauko daga sallahr Asubah yashiga bangaran domin yatashe ta tayi sallah duk da bayi take ba Alokacin in ya tasheta zata'tashi yana fita take komawa Abinta tacigaba da baccinta yana shiga yaga wayam babu kowa yadan saurara wai ko tana toliet nan ma yaji shiru yafi minti goma A tsaye sannan yafita daga dakin yana mamakin ina tatafi da Sanyin safiyar nan baiyi tunanin Siyama ta dawo gidan ba sabida haka kai tsaye bangaransa ya koma yana mamaki ina,momy siyama taje A irin wannan lokaci Ita ko momy Siyama biyar na'Asubah zakara yabata sa'a tafita daga gidan cikin motarta da nufin haduwa da hajya ladidi A inda sukai shawarar haduwa domin zuwa gun sabon malaminsu kafinta ta fita dama Sai da ta tashi Siyama da bacci tagayamata inda zata tare da hajiya ladidi duk domin Akan maganarta da Aliyu tashi Siyama tayi tana kara karfafawa momyn tata gwiwa sannan momy takama hanya tatafi Can wani guri suka hadu da hajiya ladidin lokacin gari yadan Soma yin haske suka dauki hanya can wani kauye cikin jos. Downloaded from GNOVELS.COM.NG This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG For feedback and support Facebook : https://facebook.com/gnovels Twitter : https://twitter.com/gnovels Telegram : https://t.me/gnovels