Downloaded from GNOVELS.COM.NG This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG For feedback and support Facebook : https://facebook.com/gnovels Twitter : https://twitter.com/gnovels Telegram : https://t.me/gnovels ο»Ώο»Ώ[8/18, 6:26 PM] πŸ’žIt's @lh@jiπŸ’ž: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ Ψ¨Ψ³Ω… Ψ§Ω„Ω„Ω‡ Ψ§Ω„Ψ± Ψ­Ω…Ω† Ψ§Ω„Ψ± Ψ­ΩŠΩ…. (30/06/2017./11:42 Am) *BANDIRAWO* pg 1⃣ Na *Aysha Ali Garkuwa* πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ Pure moment of life writer's P.m.l.w ```Godiya ta tabbata ga Allahu (S.W.A) mai komi mai komai da ya yini musulma ya kuma cikamin zuciyata da imani ya kuma bani rai da lafiya sannan ya k'aramin da konciyar hankali nagode wa Allah da ya bani damar fara rubuta wannan littafi nawa lfy Allahu rabbi ya nufeni da kammalashi lfy Ameeen ya rabbil izzati```!.. ```Dan Allah masu juya min novels na Ku bari bana so naga wata ko wani ta juyamin NAMIJI BAYA KADAN har da cire sunana ko mene dalili ban sani ba zancen gsky a kiyaye bana so sam``` Wasu motacin Hilux ne kusan guda goma suka fita daga cikin harabar makarantar sojojin dake jihar Kaduna wato *Jaji* a jere suka danno anci nansu kan babban titin da zai kaisu su zuwa cikin k'oryar birnin kadunan Hilux biyar ne a gaban wata kyakkyawar mota mai matukar d'aukar hankali k'irar BMW 7series kalar color ta bak'i mai kyau da sheki hatta glass d'in mai duhuce, sai Hilux biyar kuma dake binta a baya tafiya suke cikin gudu da k'aran jiniya da suka karad'e kan titin dashi , Sojojin dake cike cikin Hilux d'in gaban BMW 7series da biyar da suke bayan shi duk fuskokin su a mirtuk'e suke ga hancin bindigogin su da suka watsa ta fuskar sauran ababen hawan da ke kaucewa gefen titi suna basu hanya dan jin wannan jiniyar ke shaidawa ma zauna cikin Kaduna cewa yaufa Brigadier general Aliyu Muhammad Umar Rumoh, ya shigo gari. Cikin BMW 7series yake zaune a baya cikin shigar kakin su na sojojin mai cike da tabburan girma kala-kala da ganin kafad'arsa zai ganar da mai kallonshi tabbas wannan babbane ya taka mata kai da dama. Cikin lumshe ido da yana yinsa na fuskar kad'aici a hakan yana kallon meke gudana a fad'in garin na kd. Kai tsaye Ugguwar Sarki suka nufa cikin tafiyar su ta tsarin sojojin kwarai. Ido ya tsurawa kan titin yayin da yake ganin wuce warsu ta dakatar da al'ummah da dama da yawan cikin su masu kai yaransu makaran ta ne dan tun da a kayi sallah yaune makaran tu suka daddawo hutun sallah, Phone d'inshi yazaro tare da kallon time cikin d'an jan gajeren tsaki ganin har (7:50 Am) tayi a ranshi, yake tuna wannan fitowar tasa yau yara nawa zata jawa makara zuwa makaran ta? waya san adadin yaran da za'a zane a sana dinshi? cikin jin abin bai mai dad'iba ya juya kanshi d'aya gefen titi nan ma motoci ya gani a jere a baking titin sun basu hanyar wucewa yayin da wasu kuma ma da k'afa suke tafiya wasuma matane suna rike da hannun yaran da nufin kaisu makaran ta wasu kuma yan matane. Kai ya kuma juyawa cikin jin wani yanayi na sauk'ar mai ganin wata mace a gefen titi ta jawo d'anta da yake ta sa hannu yana tare fuskar sa dan idon rana yana kashe musu ido ganin haka ta cire tafin hannun ta a fuskar ta, ta tare mai nashi tare da jawoshi jikin ta tana mai shafa kanshi. Ajiyar zuciya ganeral Aliyu ya sauk'e tare da rumtse idon shi cikin ranshi yake jinjina soyeyya irin ta uwa a kan d'anta so da tausa yawa da k'auna da kulawar uwa abinda shiko tasa uwar ta kasa bashi. Ido a lumahen ya bud'e baki cikin bada umurni yace. "Kai Sani kauce bakin titi ka tsaida motar ban son tafiyata ta tsare ta wasu." Cikin bin umurni ya juya linzamin motar zuwa gefen titi yayi parking sannan Hilux 5da ke binsu suma suka tsaya, suma guda biyar dake gaba jin k'arar tsayuwar motocin yasa suka tsaya tare da dirowa daga cikin motocin suka dawo suka zagaye motar da Aliyu ke cikin suka tsaya cikin yanayin bada tsaro ga uban gidan nasu. Sani dake gabanne yayi saurin fitowa ganin Ogan nasu na shirin fita , cikin hamzari ya bud'emar marfin motar tare da sara mai. Cikin zafin nama da jarum ta ya diro daga cikin motar yayin da duk sauran sojojin suka sara mai tare da k'amewa a wurin. Kai tsaye kan titin ya nufa suko ganin haka yasa suka biyo bayanshi tare da d'ana kunamun bindigogun su . Jin karan d'anawa wan kata-k'ak'at ya sashi d'aga musu hannu alamun su sauk'e ! ba tareda bata lkciba sukayi k'asa da bindigogin sannan suka tsaya suna masu mmkin me zaiyi kuma me ya fitar dashi yayin da d'aya bank'aren kuma suke tsoron kar wani abu ya sameshi domainko shi jigone ga wannan k'asa tamu ta Nigeria kuma shi Garkuwa ne ga al'ummar wannan k'asa tamu Aliyu shine soja d'aya da sauran rund'unar sojojin k'asa ke jin zasu iya bashi ransu da lfy yarsu dan tsaron lfyarsa domain ko shine daya tamkar da 1000. yayin da jama'ar gari ko, ke mmkin ganin Wanda suke kaucewa suna bashi hanya sai kuma gashi ya fito yana basu hannu alamun suzo su wuce duk da fuskar sa ba walwala ko fara'a Amman hakan yasa al'ummah sun samu nitsuba dashi yayin da matasa ke bid'ar ganin shi ido a rude a man sai dai su ganshi a fuskar TV da jarida saiko suji jiniyarsa ko suga tawagar sojojin da ke tsaron lfyar sa haka yasa matasan dake cikin ababen hawa suka rink'a sara mai da cilla mai Addu'ar, "Allah ya tsare mana kai ya barka ekon bawa mutan kasarmu kariya". Cikin minti 5 duk ababen hawan sun wuce sai sauran masu tafiyar k'afa sai kuma gashi ababen hawan sun yanke ganin haka ya juya gun matan nan da d'anta daya fara k'olloh yana cewa. " Mami ni dai bazan jeba don ko naje nayi letti za'a dokeni", cikin kula ta sunkuyo kan yaro tare da cewa "inkaje ka gaya musu uzurin ka na tabbata zasu barka" k'arisawa yayi cikin sanyi tare da kauda kai ya mik'awa yaron hannushi, shima yaro sai yasa nasa hannun cikin nasa yana mai tsoron lek'a fuskarsa shiko jan hannun yaron yayi tare da juyawa zai tafi dashi, cikin sanyi matar ta bud'e baki da nufin gaya mai makaran da zata kaishi, hannu ya d'aga mata tare da yin magana a dakile yace. "ai nasan makaran ta zaki kaishi". k'ara binsu tayi tare da cewa. "toh ai bakasan sunan school din nasu ba kuma baka san inda makantar takeba." cikin kauda kai yace . "ai kinga ni makaho ne banga inifon d'in dake jikin shiba bare na game ina zan kaishi, shi kuma yaron kurma ne bazai min bayanin inda zan kaishi ba ko?". kai ta jinjina tare da juyawa tana mmkin wannan mutumi daga mgn sai fad'a. Shiko kai tsaye ya d'auki yaron ya kaishi makarantar tasu da taima kon yaron ya kuma hanesu da tab'a yaron. Kai tsaye suka sake d'iban hanya har cikin Ugguwar Sarki inda gaba d'aya suka cika ugguwar da sowar jiniyar tasu. wani kata faren gida gidane nagani na fad'a suka dosa kafin su isoma an wangale musu gate cikin iyawa da k'orewa suka kutsa cikin gidan yayin da farfajitar gidan dauke motocin har yana neman k'ari cikin sauri Sani ya fito tare da bud'e mai motar ya fito, suma sojojin suka rik'a d'iriwo tare da Sara ma, kai a sunkuye ya d'aga musu hannun tare da yimusu alamar su sauran su tafi lkci d'aya hilux 5 na bayanshi suka juya suka tafi 5 biyar na gaban shi kuma ya wanda ko wanne da sojojin 5 a cikin suko sai suka firfito tare da tsare farfajiyar gidan. cikin takun kad'aici ya nufi cikin gidan k'ofar ya bud'e tare da kutsa kai cikin wani babban parlour taku biyu yayi ana uku ya tsaya cak tare da d'ago kanshi cikin tsuke fuska. Ido ta tsura mai cikin murmushin mugunta da salon isa ta watsa mai mugun kallo murya a gadaran ce tace. "Kai dakata me kake shigo mana gida da gad'ara? da isa ka dai san nan ba cikin Jaji akekeba bare kai mana mulkin mallaka! ka kuwa san nan ba hurumin ubanka bane bare kai! bare ka shigo mana kai tsaye cikin gadara!". Ido kawai ya tsura mata cikin jin zafin kala manta kai ya kawar tare da kaucewa gefen ya nufi wani babban corridor kanshi a k'asa, cikin sauri ya rumtse idonshi jin furucin ta. gabanshi ta kuma tahowa tare dayin murmushi cikin cusa bak'ar mgn race. " Ba laifin ka bane tarbiya ce baka samu ba tun fari, koda yake ina zaka samu tarbiyar tunda kai rain non gourone dama ina gouro zai iya bada tarbiya!, ko daya take duk ba laifin Ku bane shi ya k'asa zaboma uwa ta garine tunda gashi ta watsar da kai, ka zama tantirin d'an duniya! itama ta shiga tata duniyar ! ta watsar da kai ! wai a hakan kake ganin kai d'an sunnane?! waya ma san tsiyar da take shukawa? kai kuma a hakan kakejin uwace ta haifeka? ai duk uwa ta gari zama take ta kula da d'anta !". Cikin jin zafi da d'aci, ya k'ara rumtse Idonshi tare da damk'e hannushi zuciyar sa tamkar wutu cikin kwayar idanunshi yakeji kamar rushu aka cusa mai lkci d'aya kanshi ya ringa wani irin mugun sarawa. Cikin azama ya rab'a gefen ta ya wuce da sauri kai tsaye cikin bedroom ya wuce bindigan shi ya cillah gefen tareda fad'awa kan gadon cikin karfi ya rarumi...... 10:00 Am 03/07/2017 By Garkuwar Fulani [8/18, 6:26 PM] πŸ’žIt's @lh@jiπŸ’ž: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *BANDIRAWO* pg 2⃣ Na *Aysha Ali Garkuwa* πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ Pure moment of life writer's P.m.l.w www.aishaaligarkuwa.blogspot.com *Masoya na yadda baku manta dani ba hakalazali ka bazan manta da kuba har kullum kuna raina dan farin cikinku na fara wannan novel din kuyi hakurin rashin ganin Noor ala Noor kasuwace ta cinyeshi* Kanshi ya raruma ya matse dan jin kanshi yake tamkar zai dare zuciyar sa tamkar tayi bindiga sai wani irin harbawa take, a ranshi yake jin hak'ik'a Mama tana gasa zuciya ta da rayuwa ta da ruhina da mugayen kala manta inama ace zan samu hawaye ya zubo min da na samu sauk'i, kai ya kuma turawa cikin pillows tare da matse kanshi lkci d'aya kuma tunanin shi ya tafi kan lallai jirwaye ne mai kama da wanka Mama ta mai ai ba k'arya tayiba na rasa so da k'auna da gata da kowanne d'a yake buk'ata a gun mahaifan shi, shin laifin me nayiwa iyaye na suka sani cikin rayuwar k'unci da kad'aici ase iyaye zasu haifa su guda, tun yarinta na rasa gatan uwa gashi har rayuwa ta juya dani ga zuwa mata kin girma rashin masoyi a duniya shi yasa na kasan ce Sojo zuwa yanzu na wayi gari a duniya duk wani motsina da numfashi na sun k'are kan kare kasata da al'ummah ta duk bayan minti d'aya mutuwa ke kara matsoni yayin da har yanzu ban samu mai sharemin hawaye naba shin ni Aliyu sai yaushe zan samu kula da k'auna. Tunanin yake tunanin dake kara soya mai zuciya dasashi cikin kad'aici yana cikin azabar kunan zuciya yaji motsin mutun kusa dashi ba tare daya juyoba, ya gane Ya Amir ne dan yasan shi kad'ai ke damuwa da damuwar sa sai Nafeesat. Autar su. Cikin kula Amir ya dafa kafad'ar sa murya a sanyayye yace. "Aliyu kai hak'uri hak'ik'a nasan mahaifi yata bata kyauta maka tabbas nasan tana k'untuka maka bak'in ciki, amman bamu da mafita a kullum zan baka haquri ne tunda ba yadda na iya da ita, d'an uwana kai haquri insha Allah farin ciki zai cika rayuwar ka na tabbata yadda kake kula da qasarka kaima Allah zai kula da farin cikin ka!" Shiru yayi ba tare da yayi mgn ba bare ya kulashi ko ya tanka mai, shi kam Amir inda sabo ya saba da halin rayuwar Aliyu Amman shi ya dangana abin da rayuwar kad'aici d'aya tashi a ciki shi yasa baida yawan mgn ko fara'a ko shiga harkar wani sam shi baida shiga hurumin daba nashiba. Ganin yayi shirun yasashi ya fice daga part en nashi kai tsaye part enshi ya nufa gun matar sa Aysha. A d'akin Mama kuwa Nafeesat ce tabi bayan ta bayan ta gama yiwa. Aliyu rashin mutin ci cikin sanyi Nafeesat ta kalleta murya na rawa tare da zubda qollah tace . "Ayyah Mama meya sa kike yiwa Hamma Aliyu haka meyasa kike banbanta shi damu da kika haifa Mama Hamma Aliyu bai cutar dake da komai ba, kuma ke kinfi kowa sanin da uwarsa da ubansa kina sane Babanmu da Abban Hamma Aliyu uwa d'aya uba d'aya suke .Amman Mama meyasa kike jifarsa da kalmar son shegan tashi, Mama kin san ba abinda kewa Hamma Aliyu ciwo a ransa a duniya kamar rasa kula war iyayenshi ! Amman kullum yazo sai kin tuna mai ! ko kina bin iyayenshi da mugayen kalamai ! Mama kina qoqarin sawa Hamma Aliyu qiyeyyar iyayen shi ! Mama me ribar ki in kika haddasa qiyeyyar?". Cikin fuskar tsana ta kalli 'yartata tare da cewa. " Wlh Nafeesat ko ke da Amir da kuke rabar Aliyu yasa ina jinku kamar ba ni na haifeku ba, Wlh ina dab dana yafewa Aliyu Ku sam baku da kishina. Abdul ne kad'ai yasan kimata , Wlh daga Yau sai Yau ki kuma shiga batuna da Aliyu sai naci ubanki har zakizo kina cemin ban kyauta ba, bai dace nai kaza da kaza ba wato ke ga uwata toh wlh bari kiji muddin ina raye Aliyu bazai yi farin cikiba kuma har a bada bazai samu kulawar uwarsa ba". Cikin tsawa tace "kauce ki bani wuri " Jiki a mace ta miqe tare da cewa. "Mama kiyi haquri ki gafar ceni". Shi kam Aliyu wunin wannan rana ya wuni cikin bak'in ciki da tunani ba abinda ke ta dashi sai sallah ko parlourn shi bai fito ba a haka yai ta saqe-saqe a ranshi haka ya wuni har zuwa dare ba abida ya iya ci sai dan ruwan tea da ya sha abu kamar wasa har zuwa 1 baiyi bacci ba yana konce kan d'an qaramin gado duk da kyauwun gidan da tsarinshi gadon konciyar sa kuma da durowan duk na dane cikin tunanin ya juya rufda da ciki, a hankali ya bud'e baki murya na rawa yace. " Abba na mai nai maka ka hukun tani da sakar min mahaifi yata ? Abbana meya sa kaima ka gujeni ? Ko kana ganin ka barni gidan d'an uwanka ne shi yasa? shin Abba baka san Mama tafi karfin Baba ba ?!" Sai ya kuma juyawa cikin sanyi yaja borgon jikin gadon tare da cewa. "Ammi ashe mutun zai haifa ya gudu ya bari ! ashe mace bazata iya haqurin zaman gidan auren taba ko dan ta raini yaran ta, ta basu tarbiya ta sasu farin ciki! Ammin ashe uwa na qin d'anta? kin tafi kin barni baki tuna ya zanyi yarin tata ba kin barni baki tuna ilimi naba baki tuna tarbiya taba Ashe laifin uba zai shafi d'an da kika haifa ! Ayyah Abba ai duk laifin da Ammi tama yaci kama ta uzuri ko dan ni, sam kun k'asa tuna makomata". Haka yai ta suru tai cikin kad'aici inda sabo ya saba zaman kad'aici tunda tun yana d'an shekara 4 yake kwana shi kad'ai. Gajiya da damuwar ya, ya miqe ya shiga toilet alwala yayi sannan yazo yayi ta nafilfilin da karatu qura'ani har ya fara jin bacci na d'ibarsa cikin sanyi ya ninke shimfid'ar ya bud'e 'yar durowar zai ajiye a hankali idonshi ya sauk'a kan yinifon din shi dai dai kan saman qirjin rigar sa ya duba sunan shi ya karance *Aliyu Muhammad Umar Rumoh* *Rumoh* ya kuma maimata karshen sunan nashi a hankali ya dawo kan gadon ya zauna cikin tunanin ya jawo na'urar yanar gizo-gizo gizonsa laptop enshi, kamar yadda yake binci ken masu laifin a cikin daji haka ya fara binci ke kan wannan suna na Rumoh forko cikin jihar kd ya fara laluba yayi har ya gaji babu anguwa ko qauye mai wannan suna daga kd ! katsina ya tsallaka domai tabbas yasan su fulani ne' katsinanma ba nasara ! daga nan sai Kano ta dabo sam ba nasara a nan ma ! sai kuma ya diro jihar Gombe nan ma ba canji sai ya kuma tsallah kawa bauchi canma babu, haka yayi ta laluben jihonin Nageria har zuwa jihohin kudu a hankali daga Abbah ya dawo da hasashen shi cikin jihar Adamawa Yola ya gama binciken sa sam babu gaba d'aya zuwa yanzu idonshi ya fara rufewa a fili yace. "Rumoh canne asali na tunda ya zama inkiyar iyayena toh amman ya zanyi na ganesu har na gano Zuriya ta, jawo laptop din yayi har zai rude idonshi ya dira kan Taraba Jaligo a hankali yace, "Canma garin fulanine " forko babban lokal gmt esu ya kafawa ido *Gembu* ya fad'i tare da sake cusa kai cikin babban lardinsu can qasa gefen yaga *Membila* daga qasan shi kuwa sai sunayen rigar fulanine dake zagaye da dutsen membilan cikin sa'a yayi tozali da *Rumoh* garin mai cike da Fulani makiyaya ga dutsen membila daya zagaye su yayi musu qawanya daga bayan su kad'an kuma kokin membila ne zagaye dasu, sai babbar gadar da akayi daga saman garin nasu gadar babban sai dai ta kata koce yayin da rigar Rumoh ta kasan ce a bakin gaba bayan garin kuwa dutsen membila ne d'aya kasan ce farin ciki ga d'aukacin al'ummar wurin ya kuma kasan ce abin ziyartar turawa da baqaqen mu ta yadda ya zama lardin wurin ya zama babbar hanyace konce kan dutsen hanya mai salon tafiyar maciji yayin da qasan kuma kogine gefen kuma tabki ne mai girma gaske can daga saman su kuma forres iya ganin mai kallo, garin Rumoh kenan da Aliyu ya gama binci ke a cikin Sa, dukda bai gamsuba Amman ya gudurta tafiya cikin kwana nan biyu masu zuwa yashirya tafiya tun kan hutun shi ya qare!.. Haka Aliyu yayi ta shiryer-shiryen shi shi kad'ai ba tare da neman shawaran kowa ba sai Baba da yacewa an turashi taraba wani bincike. Daga manya shi biyu kuma a wurin aiki an bashi pars na tsawon 2 weeks. Yau jummah tun safe Sani ya had'a kan sojojin da zasuwa Aliyu rakiyi Wanda an hadasu da sabbin Hilux dan sanin hanyar da zasu dosa hilux 6 da sojojin 27 aka had'a sukayi sammako tun sanyin safiya suka nufi hanyar Adamawa Yola, yayin da shiko Aliyu da Sani jirgi zasubi zuwa cikin Adamawa dan babu na Taraba, sai na Kaduna 2 Yola suka samu hakan yasa sai dai su diro jihar Adamawa daganan su ma tawagar sojojin dake ta howa a motocin sun iso daga Yolo sai su kama hanyar Taraba da mota. Su sun tashi tun safe, suko sai 4 na yamma jirgisu ya tashi zuwa Yola. 4:25 pm jirginsu yayi diran mikiya cikin..!!!!!! By Garkuwar Fulani [8/18, 6:26 PM] πŸ’žIt's @lh@jiπŸ’ž: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *BANDIRAWO* pg 3⃣ Na *Aysha Ali Garkuwa* πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *pure moment of life writers* P.m.l.w jirginsu ya dira cikin International Airport na Yola, bayan d'an wani lkcin matafiyan suka rinqa fitowa d'aya bayan d'aya, cikin sanyi General Aliyu ya zuro qafarsa tare da shaqar iskar garin Adamawa Yola , Sani na biye dashi a bayan shi cikin salon shi na murtuqe fuska suka sauqo yayin da Airport din ya ke cike da sojoji maqil, domin ko ya samu tarba daqa shugaban sojoji na jihar Adamawa tare da tarban fadawan masarautar Sarki Muhammad barkind'o, don karramawa ga jarumin dake sadaukar da ransa domin baiwa qasarsa kariya. Kai tsaye daga Airport din cikin Yola suka nufa domin kai gaisuwa ga Sarki Muhammad, daga nan kuwa barrack suka dawo inda nanma suka gaisa sama-sama daga nan suka fito suka kama hanyar Taraba. Tafiya suke cikin gudu dan su samu su isa da wuri tunda Yola 2 Taraba tafiyar awa 3 ne bare su suna tsula gudu, uwa uba kuma su duk inda suka biya basu hanya ake, shi yasa 9:00 pm suna cikin birnin Taraba jaligo ja gari na baba Abasu. Barrack din suka wuce tare da tarbar mutanen jihar a barrack din ya diro sauran sojojin yayinda ya fita shida captain Sani suka wuce jummu hotel dakin Sani na qasan nashi , shi kad'ai ya tare a dakinshi daga shi sai tunanin shi da ya cika mar rayuwa wonka ya samu danyi sannan yazo ya kwanta tare da jawo laptop enshi ya fara aiyukan shi tare da banda umurni ga sojojin da suke qarqashin sa, haka dai baiyi bacci ba har zuwa 12:30: Am sannan ya d'an rumtsa. Kashe gari suna idar da sallah suka kammala shirin su suka kama hanyar Gembu, Tafiya mai dad'i hanya mai cike da abin al'ajibi hanya mai tarin abin sha'awa hanyar da duk fad'in qasarmu ta Nigeria bamu da irinta hanya mai cike da tsirrei da qoramu da koguna da lambuna tare da sanyi mai dad'in ji yanayi mai sanya sanyi a zuciyar bani Adama hanyar Gembu 2 Membila kenan. Shi kam Aliyu zaune yake a bayan yayinda yake tsurawa dajin ido mamaki yake ganin yadda fulani sukawa dajin qawanya duk inda ya cillah idonshi dabbobi yake gani bila adadin sai mata masu fasa cikin dajin da qoren nono da ka shigo sashin wurin zakaga banbanci matan wurin da sauran matan sauran jihohinmu wannan ba shati fadi bane matan Gembu sunyi zarrar da tasa sunka doke matan kamaru ma Kyawun halitta haiba cikar zati uwa uba tsafta duk wanda yasan matan Gembu ya sansu tamkar larabawa suke fararene tas masu yalwar gashi suna da sura ta haqiqa. 10:00 Am Suna cikin garin Membila daga nan Aliyu ya tsaya tare da tara yaran shi cikin sanyi, ya tsura musu ido d'aya bayan d'aya da salon bada umurni yace. "Sani daga nan su Garba zasu tsaya ni da kaine zamu qarisa cikin dajin domin saimun ga yanayin wurin sannan mu shigo baki d'aya". Cikin bin umurnin suka sassara mai tare da qamewa daga nan, ya jaqoran cesu zuwa tantin sojin dake kula da dajin Membila sabida yawan kashe fulanin wurin da akeyi. Sai da ya tabbatar ya sama musu duk abin buqata, sannan suka wuce shida Sani. Tafiya ma budin ilimi taken Mahmoud Nagudu, Tafe suke Sani na mishi hiran yanayin wurin tare da nuna mai tsirrai masu ban sha'awa, shi kam Aliyu bin hanyar yake da ido cikin mamaki tabbas hanyar Membila abin kallone da bada mamaki, tafiyar suke Sani tun yana surutu har yayi shiru. Cikin sanyi ya kalli Aliyu tare da cewa "Oga inaga daga kan dutsen nan hanyar ta tsaya ba ci gaba sai waccar hanyar da muka wuce". Kai ya d'an juya tare da cewa ka zagaya bayan dutsen nan ta gefen dama akwai y'ar qaramar hanya tabin shanu sai mubi ta wurin" Haka suka kutsa cikin dajin yayinda suke ta ratsa tsaunuka wani wurin badan Hilux bane da bazai fitaba. Wasa-wasa sukayi yawo cikin tsaunu kan duk ya zagaye rigar Fulani dake ta wurin baiga rigar Rumoh ba, gashi da zaran sun tsaya a wasu rigan dan sunyi tabbaya sai su samu ba maza sai mata matan ma yara dan mazan sun tafi kiwo matan ko sun tafi tallar nono shiyasa sai yara suko da yaran sun gansu da yinifon din sojojin da bindiga a hannusu sai su gudu. A hakan har d'imuwa ta fara dibarsu cikin jarumta Aliyu yacewa sani " Muyi gaba gancan wani ma ki yayin". suna zuwa gunshi daga d'an nesa dashi sukayi parking sannan suka fito tare da cire rugunan jikinsu suka bar best sannan suka qarisa gunshi cikin sanyi dan gudun kar ya tsorita Aliyu yai gyaran murya tare da cewa. "Akuma *BANDIRAWO*, noi layde e dabbaji men" Sannu dan uwa ya daji da dabbobin mu" Cikin mamaki ya juya gunsa tare da yin magana cikin fillanci yace . "Ra ga Allah Surbajo toi yiftu d'on Mi hetayi on" Kai d'an Saurayi ina kuka fito ban ganeku ba" Daga nan kuma sukaci gaba da magana cikin fillanci yayinda Sani ko ya bushe a tsaye mamaki yake wai ase dama General Aliyu ya iya fillanci ji yadda ya juye kamar cikin su yake rayuwa shi kam sai murmushi yake dan tabbas Aliyu ya burgeshi ase akwai masu adana yarensu dan irin wannan ranar. Suko Aliyu zuwa yanzu d'an fullo har ya masoshi tare da rik'o hannushi ya miqa mai sanda cikin fillanci yace. "Ko zakayi kiwo?" Ba kin shi kawai ya d'an motsa alamar murmushi sannan yace . "Yanzu dai tabbaya muke sai wani jiqon in na kuma zuwa sai muyi kiwon ko". Ido ya tsurawa fuskar Aliyu tare da cewa. " kai ko bakayi fillanci ba wlh zatinka ke muna kai asalin ba fulatanine gaba da baya, dan haka ba matsala menene tabbayar?". Ajiyar zuciya ya d'an sauqe tare da yamutsa fuska yace . "Rigar Rumoh nake nema". Cikin tsoron ya zare ido tare da ja baya gani da nunashi yana fad'in. " kodai kune mutannen birnin nan da kuke zuwa kuna korar mutanen rigar Rumoh! kuna kashe su! kuna kama musu yan matan su! kuna tafiya dasu birnin! sannan Ku sace musu shanayensu! da raqumansu! kuna zalum tarsu?". Sani ne ya buga mai tsawa cikin fad'a yace. "Shi wannan mai gaskiya me baya aiki sai na gaskiya shi ba mugu bane shi mai taimakon wanda aka zalum tame". Cikin tsoron yace "ya zanyi na yarda?". Qara matsoshi yayi tare da cewa. " Shin kana jin General Aliyu Muhammad Umar Rumoh? shin kasan shine shuga ban kare haqqin makiyaya dake cikin fad'in wannan qasa tamu da suke cikin dazuzzuka da tsaunuka? shin ko kasan shine soja na forko d'aya rasa cikin dajin Sambisa ya kuwa ci nasara?". Shiru yayi tare dayin murmushi ya matso kusa da Aliyu a hankali yace. "BANDIRAWO ka makaran kana can kana baiwa wasu sashuka na qasarmu ranka dan ka karesu yayinda masu b'arnar sukazo tushenka suka tarwatsa mutanen ciki suka koresu suna kashe na kashewa suka qona na qonawa". Cikin tafasan zuciya Aliyu ya rumtse idonshi tare da cewa. " Muje ka kaimu Rigar Rumoh na gani". Shiru yayi tare da siyayar da hawaye ya kamo hannun Aliyu cikin takaici yace. *Bandirawo* a inda muke tsayennan cikin asalin rigar Rumoh ce ai an dad'e da watsa rigar Rumoh ta zama wurin kiwonmu yau kimanin shakaru 4 kenan da y'an ta adda suka hana rigar zaman lafiya sabida suka watsasu, Kaga wadan can rigogin dake kusama kullum cikin baraza na ake musu kan dole subar nan ". Jikin jijiyar bishiyan da suke qasanta Aliyu ya zauna tare da dafe kanshi har zuwa d'an wani likaci sannan kuma ya miqe tare da cewa Sani. " Shi kenan na rasa ma dafa na rasa ma dosa mu tafi Sani zan qare rayuwa ta ba farin ciki". Cikin sanyi da tausaya mai Sani ya miqe tare da cewa"oga kaqa yamma tayi kuma ba zamu gane hanyar ba mu roqi Gainako ya rakamu". Matsosu gainako yayi ganin suna tafiya dan Aliyu ya muna baya buqata. da sauri yasha gaban sa cikin sanyi da jin son shi yace. "Bandirawo kalli kan dutsen can da wancan qoraman". Ido ya tsurawa dutsen da saman qoraman sai wani irin farin hayawi ke tashi tuni wurin ya fara rufewa da hayaqin sai duhu ya fara qaruwa". Maganar Gainako ta kuma katseshi cikin fillanci dai har yanzu yace. " kaga wannan yanayin shi muke kira da *Labbare* yanayin ne da yake sauqa da zaran yamma tayi dashi muke kwana sai kuma gari ya waye yake fara tafiya da zaran labbare ya sauqa ko dabbobinmu basu fiye gani sosaiba kuma sanyine ke ratsa ko ina sannan tanan baku da hanya fita sai ta bayan dutsen inko nan zakubi dole sai kun kwana a nan kafin ku samu fita sabida yanzu duk ta inda zakubi zaki hadu da hayaqin labbare da kuma makiyaya sun taso kiwo". Ido Sani ya dan kuma warewa ganin a take wurin ya fara wani irin yanayin duhu da sanyi mai tsananin gaske. Shi kam Aliyu duk bai ganiba don baijin komai Amman gani tako ina dabobine ke faso dajin na fita yasa dole yabi hanyar zagayen yayin da Gainako ke binsu a baya tare da sakin wani irin ihu irin na makiyaye da dabobnsu, aiko sai ga dabobin sun biyishi a baya. Cikin d'aga sauti yace. "BANDIRAWO Ku biyoni zan nuna muku hanya". Jin haka yasa suka rinqa bin shi a baya da motar su. Tafiya mai dan nisa sukayi Sai gasu sun fito ta bayan wata rigar Fulani mai matuqar kyau da tsari rigace mai zagaye da ni'imomi da korayen tsirrei ta bayan rigar shukoki ne masu matuqar kyau daga gaban rigar kuma wata koramace mai ruwan garai-garai ke gudana sai dutsen dake gaban qoramar gaba d'aya wurin sai ya banda wani kalan qamshi da ni'imah. Gainako tsayuwa yayi tare da ajiye sand'ar kiwonsa a wani fili mai farin yashi dake gaban qoramar sannan ya juya gunsu dai-dai lkcin wani farin dottijo ya fito cikin wani gida daga dukkan alamu gidane sai dai yanayin gidane mai zagaye da katanqar manyan duwatsu, kai tsaye gunsu dottijon ya nufo cikin sanyi da tsura musu ido tare da murmushi cikin sanyi yace. (" Surbajo waru d'o") "D'an saurayi zo nan" Cikin sanyi suka matsoshi Sani ne ya gaida shi shiko Aliyu kawai bin shi da ido yake . Cikin sanyi ya juya tare da cewa su biyo shi. Shi kam Aliyu bin shi kawai yake cike da mamaki inane nan kuma Gainako ya kawosu. Suna shiga tsakiyar gidan dottijon yace "Badd'i waru an e Inna waziri" Badd'i kizo keda Inna waziri kuzo da madara da ruwa munyi baqi". dai-dai lkcin wata Yar budurwa mai kimanin shekaru 16 ta fito daga cikin wata bukka riqe da gwaryya a hannuta kanta a qasa tafiya take cikin kula da qoryar karta subuce ta fad'o ta fashe, tazo dai-dai kan Aliyu da yake sunkuye yana qoqarin kwance but din qafafunshi qoryar tai qasa...... *Wasa farin girki masu karu yanzu muka fara shiga cikin labarin muje zuwa* By Garkuwar Fulani [8/18, 6:26 PM] πŸ’žIt's @lh@jiπŸ’ž: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *BANDIRAWO* page 5⃣ Na *Aysha Ali Garkuwa* πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ Pure moment of life writers *dedicated 2 Ummu amhumy tare da Billy A A & baiwar Allah amnoor* Ya d'an kalleta a fakaice ganin yadda take tatsar cikin iyawa da qorewa idonta a qasa kamar wacce ta lumshe su yayinda ta kauda kanta gefe kamar mai gudun kar ta shiqi qamshi nono kanshi ya kawar tare da matsowa gefen Bappa cikin yanayin shi na tsuke fuska ya dan shafa kanshi tare da cewa. "Bappa yanzu nake son zamu wuce dan tafiyar dake gaban mu tana da nisa." Matsoshi Bappan yayi tare da miqa mai madarar da ya tatso yanzu sai tururi take yace. "Gashi kasha maganin sanyi." Kai ya d'an juya a hankali yace. "kai Bappa da sanyin safiyar nan mutun ya kama d'ura nono a cikinsa." Murmushi yayi tare da miqa mai har bakinshi ganin shirin bashi yake a baki, yasa hannu ya karb'a tare da d'an sha, lokaci d'aya ya d'anji sanyi ya sake sa, sannan ya miqawa Sani sauran shima ya sha, Haka sukai ta d'an zagawa cikin garken bayan d'an wani lokaci Bappan ya miqe tare da cewa. "Bodd'i zomu je cikin rafi da aiki a ciki." Sannan ya kalli Aliyu cikin kula yace. " (Surbajo war en yaha) Saurayi zomuje." Shi kam Aliyu ido ya zubawa Sani ganin azarb'ab'in shi tuni shi har yayi gaba ganin haka yasa ya bi bayan su ta gefen dutsen da suka ratsa A hankali yarinyar da ake kira da Badd'i ta bi bayan shi suna tafe har suka isa cikin lambun. A hankali General ya lumshe ido tare da hard'e hanna yenshi a qirjin shi sannan ya rinqa d'an zagawa cikin lambun yana mai mamaki ganin irin ni'imomin da Allah yayiwa ma zauna wannan wurin komai mai sanyi Allah ya basu ba abinda babu a cikin lambun na y'ay'an itatuwa hatta tupa da inabi akwai su kad'an a ciki bar pia kam ayaba lemu goiba abarba kakana maggoro dibino kashu, gefe d'aya kuma rekene iya ganin mutun. yana cikin shaqar qamshin da wurin ke fiddawa yaji Bappa na cewa . "Bodd'i kicire wanda bai qarisa nunan ba sabida su Surbajo zasu tafi dashi kinga kar ya logob'e a hanya da zafin mota." Gunta ya juyo d'an shi yarinyar Sam mamaki take bashi ita bata mgn sai iya barna da jiqa mutane da nono. Itako bata ma san yanayi ba dan ko inda yake bata dubawa aikinta take cikin sanyinta banana take yanka manya-manya sai kuma ta koma gefen pia tai ta sinko manya sannan ta juya gun Inabi da tupa suma ta had'a saida ta cika kondon kabar guda biyu manya da fruits sannan tazo ta ratsa gefen shi cikin sanyi ta matso Bappa a hankali take magana shi dai ba jin me take fad'iba, Amman dai ya lura cikin shogoba take magana abinda shiko ya tsana a rayuwar sa ko dan bai tashi da hakan bane. Kai ya kawar ganin yadda Bappa ke mata magana cikin kulawa harda kama hannu ta yana hura mata iska ko tofi yake mata ne ma oho musu . Daga nan kuma ita ta fara fita ta nufi gida shiko Bappa ya kira Sani dake ta cin banana kamar biri yace . "Sani d'auki wannan kondon mu tafi" shiko ya d'auki d'ayan sannan ya kalli Aliyu yace kai kuma d'auki nonunan ayaban nan mu tafi gida." Toh kawai yace sannan ya d'auka suka kama hanya. Bayan sun fito ne yaga kab ba shanayen sai y'an qananan da aka bari dan bazasu iya nisan kiwo ba wurin yayi shal sai korayen tsirrei dake zagaye dasu. Kai tsaye cikin gida suka shiga Bappa na gaba suna baya har qarqashin bishiyar ced'iya dake tsakar gidan, Inna na ganin su ta shiga d'aki tare da d'auki taburma ta zo ta shimfi d'a musu sannan ta zauna kan kujerar tsuguno dake gefen wurin, Bappa ne zauna tare da kallon Aliyu da ke zaune gefenshi cikin murmushi yace. " Inna Waziri ga jikanki mai irin halin Sayyadi naki!" A hankali ta juyo ta tsura mai ido cikin sanyi tace . "Surbajo me sunan ka?." Kanshi a qasa yace. "Aliyu " Ajiyar zuciya ta sauqe tare da yin murmushi tace . *"Aliyu Haiydar* babu rego ko gafalelle Haiydar Jan zaki gadanga kusar yaqi ." Jin kala manta yasa ya d'ago kanshi ya kalleta lokaci d'aya kuma suka had'a ido da ita sai kuma yayi mamakin ganin hawaye na bin fuskar ta . Sai kuma yaji abun bai mai dad'i ba sai ya rinqa juya mata kai a hankali tare da cewa. "Kiyi haquri " Duk da baisan damuwar taba yaji yana tausaya mata itako sanyi taji da ban haquri shi. Bappa kam sai murmushi yake tare da binsu da ido a filiko yace. "Inna Waziri baki kawowa jikokin naki abinci ba gashi sunce yanzu zasu tafi." Miqewa tayi tare da shiga kitchen ta fiffito musu da abin kari ta jera musu kan taburmar shiko Bappa ya bud'e musa sannan ya biqa musu ruwa a qoryar suka wonke Hanna yensu, tare suka ci abinncin da Bappa yana mai kallon su cikin qauna. Bayan sun gama sukaje sukayi wonka suka shirya tsab Sani yasa musu kayansu a mota ga kondunan fruits har 3 ga qoren gon zabbi har 2 ga jara kunan man shanu guda 3 tare da jarakunan nono 2 sannan ya had'asu da qoryan zuma yar asali har guda biyu. sannan suka shiga cikin gida sukawa Inna sai wata rana har zasu fita suka tsaya cak jin muryar wata tsohuwa cikin matsifa tace. "Kai Bappa wato har zakayi baqi har su gama zaman su, ni bazaka ce suzo su gaida ni ba, Ku kuma baqin muna furci ko Baku San darajan manya ba! ke kuma muna fuka harda kukan gulma toh wlh ki shirya yaune zakiyi kuka mai dalili Yau zaki mai mata kukan da kikayi shekaru 40 da suka wuce! Ku kuwa baqi yau zaku san kun shigo inda ba'a fita dan kun tari kan bala'i da kukazo nan garin! ke kuma Bodd'i ko? Yau kyawun naki zai zama ganimar wasu gara dai!." Cikin mamaki Aliyu da Sani suka juya suna kallon Bappa da inna wacce tuni take zubda qollah murya na rawa take cewa. "Dan Allah Lari karki cutarmin da Bodd'i, Lari kibar baqin nan karki sasu cikin mugun furuci !" Ido suka tsurawa Bappa cikin tuhuma da neman qarin bayani, shiko Bappa hannun su ya kamo har zuwa bakin motarsu cikin sanyi yace. "Aliyu kar ku tsaya neman qarin bayani ba lokaci ku tafi kawai kar masifan bakin Lari ya shafeku ." Cikin jin haushi ganin gaba d'aya yadda suka rud'e da kalaman matar ya kalli Bappa yace. "Bappa wacce ita? kuma me had'inku da ita? me kuma zata yi muku?!" Hannushi ya kuma ja cikin murmushi qarfin hali yace. "Aliyu kubar wannan yanki Ku hamzarta kar lokaci ya kure muku." Ganin bazai basu amsa ba yasa suka juya zasu shiga , Sosai Aliyu yai mamaki ganin irin kaya da Bappa ya had'a musu , Matsoshi yayi cikin sanyi yace. "Bappa wannan kaya ai sunyi yawa". kai ya gyada mai tare da cewa . " a a Ali bayyi yawaba kai dai kuje sai wata rana." "Toh mun gode" yace tare da juyawa har zai shiga mota sai kuma ya juyo da sauri cikin mamaki jin hayaniyar shanaye da raquma da suke ta shigowa cikin rigar a guje ma kiyayan na binsu a baya tako wacce kusurwa shigowa suke. Ganin wannan Gainako da ya kawosu rugar ya nufi Bappa a guje yasa shima ya dawo gaban Bappa . Shi ko Bappa ido kawai ya rumtse tare da cewa. "Gainako yau kuma rigarmu zasu shigo ko ? yau ma Bodd'i suke son d'aukewa ko?." Sai hawaye shar a idonshi shiko Gainako sai haki yakeyi cikin d'auki war numshi da haki yace. "Bappa sunce in muna son kanmu da lafiyar mu a kai musu Bodd'i! inko muka bari suka shigo wlh zasu kashemu su qona rigarmu kamar yadda sukayiwa rigar Rumoh." Kafin yayi magana sai ga mutanen rigar duk sun hallara qofar gidan a gaban su wasu dottijai guda 3 suka kalli Bappa cikin tausaya wa sukace. "Bappa ka samu Ku fita ta qofar baya kaida Bodd'i dan tabbas ita suke hari." Cikin tsoro wani matashin da ya iso yanzu yace. "Wlh suna nan a qofar bayan ma sunce nanda azahar a fito musu da ita da kuma dabbobinmu." Shi kam Aliyu so yake sumai bayani suko sun k'asa sai b'ari suke. Bappa ko jin haka yasa ya matso jikin Aliyu hannushi ya riqe cikin rawan murya da neman alfarma yace. "Aliyu taima konka nake nema zaka taima ka min?." Cikin kaushin murya yace . "Bappa ka gaya min meke faruwa?, ai taima ko shine aikina kodako zan rasa raina sabida nai alqawatin taima ko kafin na fara wannan aiki nawa Bappa aini raina da lafiyata kan taimakon qasata yake ka gaya min suwaye ke son kasheku?." Kai ya rinqa juyawa cikin sanyi ya koma cikin gida , Jim kad'an ya fito riqe da qura'ani mai girma cikin sauri ya miqa mai tare da cewa. "Aliyu kayi alqawari tsaka ninka da Allah zaka taimaka min zaka kuma riqe amana?." Ranshi cike da jarum ta yace. "Nayi alqawari zan taima ka maka kuma zan riqe amana bazan kuma k'asa taima ka maba." Cikin jin dad'i yayi ajiyar zuciya sannan ya kalli mutanen wurin tare da riqe hannun Sani. " yace Sani Kaine shaidan Aliyu a garinku in kun koma." Ya kuma juya ya kalli taron mutanen wurin cikin d'aga murya yace. "Ku kuwa kune shaida na da alqawarin Aliyu." Kusan a tare su kace "Ehh". Murmushi qarfin hali yayi sannan yace. " Aliyu na baka auren Amina Bodd'i bisa alqawarin da kayi min! Kuma yanzu za'a d'aura auren! yanzu kuma zaku tafi da ita!" Shi kam Aliyu ido ya zaro woje tare da bud'e baki zayyi magana . Da Sauri Sani yace. "Alqawari kayi oga kuma tsaka ninka da ubangiji kai wannan alqawarin." Yana rufe baki ya juya ya zaro kud'i masu yawa a cikin moto sannan ya d'auki kondon dibino d'aya cikin sauri ya dawo gaban Aliyu daya murtuqe fuska kamar zayyi ruwan jini. Kud'in ya miqawa Bappa tare da cewa. "Ga sadakin ta dubu 50 sannan ga dibino kawai yanzu a d'aura Aure, shi oga namiji ne ya halatta ya karbawa kanshi Aure." ..... Gaddara ta rigayi fata General Aliyu yanaji yana ganin wata gaddarar rayuwa ta auka mai Wanda dole girman alqawari da bakinshi ya karbawa kanshi Auren Amina. Ana gama daurin Aureb tare da shaidun mutanen rigar Bappa ya shiga cikin gida, cikin sanyi da tausayawa kanshi da matarshi da Bodd'i ya kalli Inna ba tare da wani baya niba ya kamo hannun Bodd'i tare cewa Inna. "Kiyi haquri wannan shine mafita kuma wannan itace sabuwar gaddararmu." Itako Bodd'i sai binshi tai yana riqe da hannuta. Gaban Aliyu ya tsaya da ita tare da miqa mishi hannuta cikin sanyi yace. "Aliyu ga matar ka! Bodd'i kekuma kibi mijin ki!" Ita kam bata fahimci komai ba a zancen nasu sai dai ta fahimci tafiya zaiyi da ita shiyasa sai hawaye ke bin fuskar ta. Shi kuwa kamar makaho Bappa ya jashi har cikin mata Sannan Sani ya shiga suka tafi . Suna fita cikin rugar ta gefen dutsen Membila sai ga motocinsu da suka bari cikin Membila cikin mamaki Aliyu ya kalli captain Sani da neman qarin bayani duk da dai ya gane Sanin ne ya kira su dan suzo su bawa mutanen rugar kariya. hakan ko yace mai . "Oga nina kirasu." Kai ya gyad'a sannan yace . "Toh motoci 4 su isa wanda sojoji kusan 28 a cikin sannan yace . mota d'ayar kuma ta juyo su koma tare. Haka kuwa Akyi matoci 4 suka nufi cikin rugar, suko su Aliyu sunka nufi Hanyar Gembu domain zuwa Yola.. A cikin motar kuwa Bodd'i ta..... By Garkuwar Fulani [8/18, 6:26 PM] πŸ’žIt's @lh@jiπŸ’ž: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *BANDIRAWO* page 6⃣ Na *Aysha Ali Garkuwa* πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ Pure moment of life writers *Wannan shafi nakune ku kad'ai Sisters In Islam Mmn jhadijah tare da Y'ar mutan wudil sa'a tafi manyan kaya nis@ online writers & Hurairayabo and Feedoh* Dungu lewa tai wuri d'aya tana mai wani irin kuka mai sanyi da tausayi dan, gani take shike nan an rabata da tushenta gatan ta ji take kamar an rabata da farin cikin ta, a ranta take tuna meyasa Bappa baiyi tunanin komai ba ya had'ata da wannan mutumin mai fuskar mugaye, cikin jin zafin zazzabin da yake shirin rufeta ta d'an bud'e idonta tana mai kallon tsaunu kan da tsirren da suke ketawa yayin da suke bawa rugar tasu baya a take ta saki wani kuka mai cin rai tare da qamqame jikin ta, ta takure can gefe jikin motar. Shi kuwa Aliyu ido kawai ya rumtse cikin wani irin zafi da ranshi ke mishi , tunani yake shi da yazo neman mafita da samun sauqi sai gashi wani baqin shafi ya shiga cikin littafin qaddarar rayuwar sa, shin ina zai Ajiye wannan yarinyar da wani matsayi zai nunata ga Mahaifin shi? da yayan mahaifin nashi ? shin da wace fuska zai nunata ga sauran abokan aikin shi ?, kai ya kuma juyawa da qara rumtse idon shi tuno Mama da yayi ko me zatace kan wannan batun ! wanne sherri kuma zata bishi dashi !, shi a wanne yanayin yazo duniya da ya kasance ba mai ji bantan lamuran shi . Haka yai ta tubka da warwara, yayin da shiko Sani driving kawai yake, zuciya yarsa cike da farin ciki ko ba komai yasan insha Allah nan bada jimawa ba Ogan shi zai samu sauyi a rayuwar sa a haka suke tafe kowa da abinda ke ransa, Bodd'i ko tayi kuka har muryarta ta dashe fuska ta kumbura. A haka har suka bar jihar Taraba suka fara nausawa cikin jihar Adamawa Yola tafiya suke cikin sanyin safiya yayinda Sani ya samu hanya ba cunko son ababen hawa ya rinqa tsula gudu kamar masu firewa yayin da. motar su Garbe ke biye dasu a baya. 10:25 Am Suka isa dai-dai Gurore inda hanyar ta kasu 3 d'aya hanyar da zata sadaka da cikin birnin Adamawa d'ayar kuma wacce zata fiddaka Adamawa zuwa su Gombe Bauchi Jigawa Kano Kaduna Abuja Katsina Sokkoto da dai sauran sashoshin dake gefen, d'aya hanyar kuma wacce ta kanta suka bullo itace hanyar tafiya Taraba kuma itace ke sada mutun da qasashen kudancin Nigeria kama su Calaba Onitsha Binuye da dai sauran su. Suna zuwa dai-dai wurin Sani ya juyo cikin neman izini yace. "Oga cikin Yola zamuyi ne ?" Ba tare daya bud'e ido ba ya bud'e baki cikin bada umurni yace. "Miqewa zakayi kawai muyi tafiyar mota dan bazan tsaya jiran ✈ bare ma wannan bororiyar bata da komai bare muyi tafiyar da jirgin." Toh yace tare da juya hancin motar suka kama hanyar Gombe, Allah sarki, Badd'i bata taba zaton rayuwar ta zata juya mata haka ba yau gashi tabar rugarta tabar jihar ta gashi har tana qetare sauran jihohin da suke maqobtaka da jihar su, zuwa yanzu tabar jin ko yanayin sanyin jihar ta bare qamshin furannin rugarsu, kuka ne tayi shi har qarfin ta ya qare gashi dama ba abinda taci. Tafiya ma bud'in ilimi Mahmud Yau yai nisa, yauko Amina ce tai nisa inda tabar sunan Bodd'i a rugarsu ta d'auko sunanta. Amina daga Gombe ko taji wani sabon suna a bakin Sani . 1:00 pm suna cikin birnin Gombawa diban fari ba'a kwana damuba a tashi. Kai tsaye Shagalin ku Restaurant suka wuce,.Suna isa bayan Sani yayi parking kafin ya fitoh mah su Garba sun fito daga tasu motar a guje suka bud'ewa General Aliyu mota tare da sara mai kab suka qame har saida ya fito, Sannan suka bishi a baya har ciki yayin da ma aikatan wurin suka fara yi musu hidima cikin karra mawa suka isar da Aliyu can cikin wurin na musamman su kuwa suka koma baya gun sauran mutane gaba d'aya aka shirya musu abinci da nasha suka fara ci domain sauri suke Yau suke son zarcewa Kaduna. Shi kuwa General zama yayi cikin nitsuwa sannan ya lumshe idonsa tare da shaqan qamshin wurin wanda ya had'e da sanyin A,C a hankali ya rinqa sauqe ajiyar zuciya har zuwa wani d'an lokaci sannan ya bud'e idon shi cikin furza numfashi ya d'an juya kenan ya haggo Captain Sani ta cikin glass din wurin wanda yake kib da area park daga duk kan alamu magana yakeyi amman bai jin abinda yake fad'in ganin haka yasa ya zaro phone enshi ya kirashi , bugu d'aya ya d'aga cikin tsuke fuska yace . "Kai Sani me ka tsaya yi ka dai san akwai sauran tafiya a gaban mu kai sauri ka shigo kuci abinci muyi sallah sai mu tafi." Cikin kula yace. " Oga Meenal taqi ta fito tazo taci abinci kuma sai kuka takeyi." Baki ya tab'e cikin tsawa yace. "Toh sai me cikin ka ko cikin ta ? ai in taji yunwa zama taci wani bai saniba kar taci mana kai me naka a ciki, kawai dai inma baza taci abinci ba toh ta fito tayi sallah tun kafin su Garba su fito su ganta aikin banza kawai." Ido ta tsurawa Sani cikin zubda qollah dan kab taji abinda yake fad'in ga uban tsawan d'aya buga wanda ya firgitata, cikin zubda qollah ta zuro qafafun ta cikin dishewar murya tace. "Bandirawo a ina zan samu wurin sallan?." Gefen wurin ya nufa da ita sannan ya kaita gun masalacin dake wurin Wanda ga fomfunan da keta zubda ruwa a nan tai al'walah sannan tai sallah duk Captain Sani na tsaye yana mata gadi tana idar da sallah ta komai cikin mota, shiko ya shiga ciki ya d'an ci abinci a gaggauce sannan ya musu Othern abinci yaje ya aje cikin mota sannan suna fitowa sukayi sallah 1:35 pm dai-dai suka bar garin Gombe. Kafin 2 ma sun isa Darazau Dara birnin bauchi daga nan suka harba jigawa dutsen kafin 6 sai gasu a Kano ta sabo tumbin giwa . A nan suka tsaya suka ci abinci sukayi Sallan maggari ba sannan suka jira har zuwa isha bayan sunyi ishan ne suka fara shirin tafiya bayan sun dudduba lafiyar motocin nasu sannan suka kama hanyar Kaduna. Allah Sarki ita kam Meenal gani take tunda take a rayuwar ta bata taba irin wannan tafiya mai nisan ba tun a Yola ta fara tsinkewa da cewa shike nan an rabata da iyaye ta bare yanzu da taga bayan kanon ma gaba zasu qara kawai sai ta ringa tsiyayar da qollah tare da jan wani irin numfashi ta duqqule wurin d'aya. A ganin su Captain Sani wanda ya taso Taraba 2 Kaduna in yazo Kano ai ya iso gida. Dan haka yanzu tafiyar suke a tsanake , 9:00 pm Suna cikin birnin Kaduna kai tsaye agguwar Sarki suka nufa cikin tafiyar shaidawa mutanen gari General Aliyu na gari. Jiniyar su ce ta shaidawa mutanen gidan nasu Aliyu ya dawo, Sani na gama parking ya fito su Garba ma duk suka firfito sauran sojojin dake biye dasu ma duk suka fito kab suka zo gaban General din nasu suna Sara mai tare da yimai sannu da zuwa. Cikin murtuqe fuska ya d'aga musu hannu tare da murza yatsun sa yana kad'asu alamar su tafi kawai ganin haka yasa cikin bin umurni suka juya suka tafi kab d'insu sai Captain Sani daya ke binshi a baya. Cikin gida kuwa Kab suna tare a harabar babban parlon Aysha matar Ya Amir ce zaune a gefen Mama da keta surfa mata masifa sai Abdul d'an goyon bayanta da yake gefen ta yana cillawah Aysha harara cikin izzah yake cewa. "Mama ai ita bata san zafin haihuwa bane shiyasa take mana iskancin da taga dama tunda tasan ni bancin tuwo ai sai ta dafa min abin da zanci." Nafeesat ce ta kalleshi cikin tsoro tace . "Ayyah Yaya Abdul Anty Aysha bata da lafiya fa." Cikin yatsuna fuska yace. "Ke kuma muna fuka waya kasa dake?." Maman ne ta kai mata mari cikin fad'a tace. "Ba nace ki dena as mana baki ba in muna maganar mu." Shiru tayi tana kallon yadda Aysha ke zubda qollah shima ya Amir sai sunkuyar da kai yayi cikin tausayawa matar tasa. Ga masu aiki ya kawo amman dole an maida matar sa y'ar aiki sam baza'a barsu su sake ba. Suna cikin haka General Aliyu Haiydar ya shigo cikin murtuqe fuska da manna baqin glass a fuskar sa dan ya tabbata Mama zata tare shi da baqar magana sanin haka yasa cikin cije lips enshi ya zaro bindi garshi ya d'aga sama ya danna kuna mar ya rinqa sakin harbi ba qaqqautawa gaba d'aya ya cika gidan da qara Captain Sani ma dake bayan shi sai hannu yasa ya kama kanshi tare da to she kunneshi. Su kuwa su Mama gaba d'aya suka waste a guje parlon ya zama ba kowa ganin haka yasa cikin sauri da takun cikar zati ya komai farfajiyar gidan kai tsaye motar ya bud'e sannan ya rarumo hannun Bodd'i ya fizgota woje sannan ya jata sukayi cikin gidan, shi kam captain sai sake baki yayi tare da binshi da ido. Kai tsaye part enshi ya wuce da ita yana janta da qarfi suna shiga ya jata har cikin bedroom kan gado ya cillah ta sannan ya juyo da qarfin ya rufe qofar sai ya kuma dawo kan......... By *Garkuwar Fulani* [8/18, 6:26 PM] πŸ’žIt's @lh@jiπŸ’ž: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *BANDIRAWO* page 7⃣ Na *Aysha Ali Garkuwa* πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ Pure moment of life writers *Na saudau kar da wannan shafi a gareku Salmab Fadeela Fashuna biebie deee Fadeela Lamid'o Firdaus ina al'fahari daku* Tsayawa yayi a kanta cikin d'aure fuska ba fara'a ko kad'an ya kuma tab'e baki cikin fad'a da bada umurni yace. "Ke kina jina ko." Shiru tayi bata kula shiba sai kanta da ta sunkuyar tare da fidda numfashin tsoro da far gaba, shurun nata ya qara tunzura shi cikin tsawa yace. "Ke kina jina ina magana kin wani share ni ko ke kurma ce?." A tsora ce ta d'an d'aga mai kai cikin zare ido da tsoro ta gyada mai kai alamar ehh tana jinshi . Qara murtuke fuska yayi tare da zare mata ido cikin muryar fad'a yace. "Kina jina ko wlh doka ce zan kafa ya miki ! kuma umarni ne ! Wlh kika kuskura kika sab'a abinda zance miki Wlh zaki gane kurenki ." Sai ya kuma d'anyi shiru sannan ya qara tamke fuska yace. "Kina jina ko?." Kai ta gyad'a cikin sauri da tsoro . Cikin bada umurni yace. "Kinga wannan d'aki toh kada ki yadda kada ki kuskura inga qafarki ko a parlon nanne bare kuma ta kai ga kin fita cikin gidan nan, Wlh in kuwa kika yarda kika sab'a umarni nina wlh sai kin gommace kid'a da karatu, sannan kada ki kuskura kice zakiyi wani abu da zai nuna akwai mutun a d'akin nan in kuwa kinqi zaki gane kuren ki." Kai kawai take ta gyad'a mai tana numfashi sama-sama dan tsoro. Shi kuwa ido kawai ya tsura mata sannan ya juya cikin rashin kula, jikin Windows yaje ya rinqa zuge glass d'in yana rufewa sannan ya sassauqe labulayen ya juya ya kunna mata wuta sannan ya fice ba tare da ya kalli inda take ba. A cikin gidan kuwa su Mama duk sun fito parlorn jin shiru qaran bindigar ya tsaya gaba d'aya sukayi cirko-cirko suna kallon Captain Sani da ya tsaya kamar dolo. Mama ce ta kalleshi a yatsine cikin had'e fuska tace. "Kai Sani wato uban gidan nakane yazo yana mana harbe-harbe a cikin gida kamar wani mahaukaci, koda yake ba laifin shi bane mashayi kuma menene bazai aikata ba yaje ya gama d'ura giya yazo yana qoqarin hallkamu banza asararre ." Nafeesat ce ta karya fuska cikin sanyi tace. "Ya Sani ina Hamma Aliyu da gaske tare kuke?." Abdul ne ya watsa mata harara cikin yatsin fuska yace. "Can da Allah kauce banza kawai ji yadda kike wani damuwa dashi sai kace qanin ubanki ne shi." A fad'ace Mama tace. "Banza mashayi kawai yazo ya cika mana gida da yan iskan sojojin su mashaya ." Cikin zage-zagen Abdul ya nufi part en nashi yana. "Bari inje in sameshi wlh ya shiga hankalin shi." Yana juyowa Aliyu dake tahowa ya d'aga mai hannu cikin tsawa yace. "Kai dakata tsaya a wurin kar ka qara ko taku d'aya, dan wlh duk maison kanshi da lfy kar ya kuskura yace zai zo iya kar part d'ina ko wacce ta tsaya matsa yinta daga yau kar wanda ya shiga hurumi na inba hakaba wlh zan iya yin komai ." Baki Mama kam ta saki cikin qanqantar da ido irin na bala'i tace. "Iyeh lallai ka isa yanzu kai ko ubanka ya isa yamin iyaka da wani wurin a gidan nan?." Kai ya kad'a tare da cewa. "Hmmmmm mutun ya goda mana ya gani Wlh" Sannan ya juya gun cikin tsuke fuska yace, Sani je ka kwaso kayan dake cikin motar ka kawo ." Captain Sani kam juyawa yayi cikin bin umurni ya fara kwaso tsarabar da Bappa ya had'o musu yana shigar dasu har cikin part d'in Aliyun na sawa a fridge duk ya lodasu sannan wasu ko ya shiryasu a cikin kitchen d'in dake jikin parlour. Shi kuwa Aliyu a babban parlon nasu ya zauna kan kujera tare da d'ora qafarsa d'aya kan d'aya yana d'an buga qafan ya kuma manna glass a fuskar sa ya murtuqe fuska tamau. Mama ko sai kanne ido take tana juya kai da cije lebenta tana ta huci, shi kuwa Abdul dama duk iskan cinsa yana shayin Aliyu dan baya mai wasa, Ya Amir kuwa da Nafeesat murmushi sukeyi dan dama susan Aliyu sarai tarawa Mama yakeyi inya tashi baya sha yinta, ita kuwa Aysha sai zame jiki tayi ta koma d'akin ta Daddy ko wanda shine mijin Mama kuma Baban ya Amir da Abdul sai Nafeesat kuma Yaya ne ga mahaifin Aliyu, shima yana gefe yana hoggo yadda Aliyu ya tsare yau yana juyawa Matar tasa ido har ranshi yaji dad'i dan dama yana jin zafin abinda matar tasa take yiwa d'an, d'an uwanshi sai dai ba yadda ya iya da masifar ta. Shiko General Aliyu Captain Sani na fitowa yace ya gama shigar da kayan ya miqe yaje ya rufe qofar parlour sannan ya zura key d'in a haljihu suka fice tare. Ita kam Mama bala'i ta rinqa yi bayan ya fita ya Amir da Nafeesat ko kowa ya kama gaban sa, itako da Abdul zama sukayi suna ta tubka da warwara ta yadda shima zasu cusguna mishi. Shiko suna fita kai tsaye Jaji suka nufa suna zuwa ya wuce gidan shi ruwa ya watsa sannan yasa Esther yarin yar dake mai girki su shara da dai sauran su ta kawo mai abinci yad'an ci sannan ya shiga ya konta dan yin baccin gajiya. Esther aiki takewa General Amman ita har ga Allah take sonshi a burin tako koda bai aureta ba sunyi zaman daduro shiyasa take bin duk hanyar da zata iya kasan tuwa dashi, Shiko Aliyu ya rigada Allah ya tsare mai imanin shi da sauran jikin shi duk da kasan cewar sa soja kuma mata shi mai cikar zati. A Gida kuwa Tunda Aliyu yayiwa Mama kashedi da karta shigar mai part enshi har yana "a goda agani mana " gaba d'aya ta rasa yadda zatayi dan tsanar yaron ga Daddy kuma ko da ta kaimai qorafi mijin Hajia sai cewa yayin "in yazo weekend ki mai fad'a ." Yau kwana 3 da dawo warsu Gembu Membila Bodd'i kam tunda Aliyu ya qinda ya mata doka ko bakin qofar parlour bata jeba duk da irin rayuwar kad'aici da takeji ga azabebbiyar yunwar da takeji gashi bata san yadda zatayi komai ba dan ko bayan gida sai a hankali da tab'e-tab'e ta gane har ta samu tayi wonka komai dana Aliyu tayi amfanin kama daga soson wanka da brunch har zuwa towel a haka sai dai tayi wankan ta d'aura towel en ta fito ta d'an goge jikin ta sannan ta meda kayan jikina tun Wanda tazo dashi, tunda shi kad'ai ne kayanta gashi irin kayan nanne na Fulani farine wanda yasha aikin Zane da ulu red da light green sai yellow rigar y'ar qara mace ko cibiyar ta bata gama rufewa ba sai in ta d'aura zanin sama kad'an kanta ko a tsefe yake sai dai ta d'an tub keshi. A haka tai ta rayuwa inda taji yau d'in yunwa na shirin hallakata gaba d'aya jikin ta sai bari yake ko tsayuwa gagararta takeyi kawai sai ta kama kuka. Shi kuwa Aliyu a office enshi Captain Sani da yake kamar shine do garin sa ya shiga bayan ya sara mai cikin sanyi yace. "Oga ya Meenal kwana biyu bamu leqata bafa." A fili kauda kai yayi kamar bai ji ba a bad'iri kuwa ido ya rumtse cikin mamaki ya akayi ya manta da ita shi wlh sam ya manta da itama. Cikin sanyi Sanin ya kuma cewa . "Oga tun da Yau ba wani aikin yi ya kamata mu leqa cikin Kaduna." Kai ya jinjina mai sannan ya miqe tare da cewa. " ba yanzu ba." Shiru yayi shi kam Captain dan yasan Aliyu kaifi d'aya ne . Da yamma liris goshin maggariba ya Amir da Sauran mutanen gidan suna tare a babban parlourn sun zuba ido suna ganin yadda Mama da Abdul suke ta kicini Yar b'allah qofar parlon Aliyu Mama ta dage sai cewa Abdul take. "Wlh yau sai mun b'alla qofar mun shiga har cikin muga tsiyar da ya ajiye a cikin d'akin." Shiko Abdul ya dage sai buga qofar yake ganin bazai bud'u a hakan ba yasa ya fito farfajiyar gidan ya d'auki qaton dutse yazo yanata bugawa wai shi zai ballah qofar bugu 2 ana 3 ya d'aga hannu zai buga kenan yaji ....... By Garkuwar Fulani [8/18, 6:26 PM] πŸ’žIt's @lh@jiπŸ’ž: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *BANDIRAWO* page 8⃣ Na *Aysha Ali Garkuwa* πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ Pure moment of life writers *Dedicated 2 Aishat A Muhammad & Ummyn Yusrah and Ummu yahya musa sisin mama & Sadnaf and Husna Abubakar Bauchi* An kama hannu shi cikin tsoro ya zaro ido woje ganin Aliyu ne tsaye cikin murtuqe fuska ga woni irin cabke mai hannu da yayi ya riqe cikin matsar qashin hannun nashi lokaci d'aya yaji wani irin azaba na ratsa shi cikin in ina baki na rawa yace. "Hamma Aliyu zaka karya min hannu fa ni ka sake ni ." Bai kulashi ba sai qara damqe hannun yayi tare da soka yatsar sa tsakanin jijiyoyin hannun shi d'in. Cikin jin zafi Abdul ya saki qara mai qarfi tare da sunku yawa yana cije hagoran sa a wahal ce yace. "Wayyo Mama Hamma Ali zai karya min hannu Mama zai tsinka min jijiyar hannun." Matsoshi tayi cikin isa ta d'ago hannu ta yarfa mai mari tare da cewa. "D'an iska kawai a gabana zaka karya min hannun d'an nawa dan kai baka san dad'in d'aba sannan baka san yadda uwa ke son d'anta ba, ai ko mutuwa tana jin kunyar uwa bare kai Aliyu." Ihu Abdul ya kuma saki da qarfi har kamar zaiyi fitsari a jikin shi. Jin qaran da ya kuma yine Maman ta leqa fuskar Aliyu da yayi jawur dan takaici bawai dan zafin marin da tayi maiba gaba d'aya idonshi sukayi jazir leben bakinshi sai rawa yake dan fushi hakan yasa ya had'e hannun shi da qarfi wanda har saida hannun Abdul yayi qaran targad'e . Yana tabbatar da ya targa d'ashi ya yarfar da hannun shi cikin fuzgar magana yace. "Next time in kayi gigin bud'e qofar nan karya ka zanyi." Yana kaiwa nan ya bud'e qofar sannan ya shiga tare da cewa Captain Sani ya shigo. Itako Mama kamar ta bishi ta cinye shi d'anye takeji bala'i take kamar ba gobe fad'a take ko numfashi bata ja . Shi kuwa Abdul kan kujera ya koma ya zauna tare da tallabe hannun da hannun shi mai lafiyan yana maida numfashin wahala. Su kuwa su Aliyu suna shiga a parlour ya zauna kan 3 str ya koma ya jingina kanshi tare da lumshe ido yana mai jin zafin kalaman Mama a kanshi ko yaushe bata binshi da kalma mai kyau sai baqin alkaba'i, gefen shi Sani ya zauna riqe da goran Faro mai sanyi cikin fargaba ya miqa mai murya can qasa yace. "Ser ga ruwan sanyi ko zaka Sha?." Baiyi magana ba kuma bai bud'e idon shiba sai kad'a qafa da yakeyi . Ganin haka yasa Sani yayi shiru sai shiga kitchen da yayi ya kunna gas ya d'an d'aura musu ruwan tea. Har yanzu idon shi a lumshe yake a hankali ya farajin zuciyar sa tana d'an sanyi dan addu'a da yake tayi, lokaci d'aya kuma ya fara jin sautin a hankali yaji sautin kukan ta na tashi daga cikin bedroom en sai shesheqa takeyi cikin rawan murya take ta kukan ido ya d'an bud'e sannan ya zurawa qofar d'akin ido zuciyar sa na tafasa. A ranshi yake tuna cewa , Itace qarin matsalar sa ko ya zaiyi ne ma shi bai saniba . A fili yace. "Ni bansan ya ake kula da wani ba dan ban taba samun kulan ba nike kula da kaina sai gashi an had'ani da wata jarabar tsiya." Shiru yayi yana sauraron ta, har Sani ya fito da y'an cup guda biyu da ruwan tea mai kauri a ciki sai qamshin citta da kanamfari yake, yana zuwa ya jawo Stol ya ajiye mai a gaban shi tare da cewa. "Ga tea ." Shiru baiyi magana ba har zuwa woni lokacin, shi kam Sani bai kuma magana ba dan ya ga ogan nashi a sama yake . Can dai ya miqe tare da cup d'in tea d'in a hankali yake takawa har zuwa cikin bedroom en , kan gado ya ganta konce rufda ciki tasa hannu biyu ta riqe cikin ta tana kuka murya can ciki tare da yin magana cikin kukan. "Wayyo cikina wayyo Allah na wayyo Bappa na zan mutu yunwa zata kashe ni qirjina ciwo kaina ciwo." Duk tana maganar ne cikin fillanci shi kuwa tsayuwa yayi dab da ita sannan ya d'aga kanshi sama tare da kawar da idon shi daga kanta murya a daqile yace. "Ke ya isheni haka banson sakarcin banza ya zaki zauna kina mana ihun yunwa." A take ta had'iye kukan nata sannan ta yunqura cikin rawan jiki ta zauna tana bari kar-kar. Ba tare daya kalleta ba ya miqa mata cup din cikin bada umurni yace. "Shanye ki ban cup d'in." A yadda take jin yunwa kamar zata kasheta wai a bata abu a d'an cup d'in nan . Tana cikin tunanin da qoqarin matsowa ya juyo kanta cikin wani irin cilla mata mugun kallo da yana yin zaki karba ko yaya. Jiki na rawa ta karba sannan ta kafa kai ta rinqa zugan shi a hankali shiko sai zuba mata ido da yayi har ta shanye. A take sai ga zufa ta keto mata tako ina lokaci d'aya kuma ta fara damqe cikin ta. Ganin haka yasa ya fito da kofin kai tsaye kitchen ya nufa yana zuwa ya sake had'a mata tea mai kauri sannan ya dawo ya same ta sai riqe cikin take tana murqususu cup d'in ya kuma miqa mata, a wahal ce ta rinqa juya kai hawaye na bin fuskar ta cikin wahala tace. "Cikina zan mutu." Bai kula taba sai murtuqe fuska daya kuma yi dole ta karb'i cup d'in ta k'afa kai tana sha tana kallon yadda ya tsuke fuska kamar d'an zai mareta dole sai data shanye sannan ta ajiye . aiko sai zufa take ta karyo mata dole ta zaune tana yiwa kanta fifita da hannun ta duk da A.C dake fesa sanyi. Ido ya tsura mata tare da tab'e fuska murya a daqile yace. "Ke ba'a wonka a garin kune?." Murya na rawa tace . "Anayi." "Qazan tace ta hanaki yi ?." "Nayi ." "Toh wanna buhun zanin naki kuma na gadone ko?." Zuwa yanzu hawaye ya jiqa mata gaban riga cikin tsoron yadda yake mata mgnan murya na rawa tace. "Banida wani kayan." Mitsss yaja d'an gajeren tsaki sannan ya juya gun y'ar madaidai ciyar durowar ya bud'e cikin durowar ya tsura ido har zuwa wani lokaci sannan ya zaroh wani 3qtr enshi wanda kuma kamar skin teit ne sannan ya zaro riga mai dogon hannu rigar farace qal wondon kuma read ne mai ratsin fari-fari, gaban ta ya dawo cikin tsuke fuska ya miqa mata, ita kuwa hannu tasa ta karba tana mamaki ya zatayi tasa wannan kayan , ganin ya tsare ta da ido yasa ta shiga toilet ta zare kayan jikin ta tasa wanda ya batan sannan ta fitoh tana ta d'aga hannu tana gyara hannun rigar don ya mata tsawo har yatsun ta hanna yen suka rufe sai fama take da rigar ga wuyan rigar ma ya mata yawa wondon ne dai ta samu yayi kib da qugun ta, yana ganin ta fito shima ya fice kai tsaye masallaci suka wuce shida Sani dan maggariba tayi. banya sunyi harda ishah Sani ya wuce Restaurant ya samo musu abinci sannan ya dawo, a parlon suka ci tare da d'an yin kallo har zuwa 8:15 Pm Captain Sani ya kalli ogan nashi cikin sanyi yace, " Oga bari inje in kwana a d'akin Abdul, tunda yanzu nan kam ba fili." bai kulashi ba har ya fita sannan shi kuma ya miqe cikin gajiya ya d'auki ledan abinci ya nufi cikin d'akin , a gaban ta ya dire mata ledan sannan ya juya yaje ya rufe qofar parlour ya dawo cikin d'akin kai tsaye ya nufi....... By Garkuwar Fulani [8/18, 6:26 PM] πŸ’žIt's @lh@jiπŸ’ž: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *BANDIRAWO* page 9⃣ Na *Aysha Ali Garkuwa* πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ Pure moment of life writers *Dedication 2 Anty Fauzah & Neena Cool and Maryama Abdool & Momyn sultan* Toilet ya shiga tare da maida qofar ya datse har ya fara zare rigar jikin sa sai ya lura towel nashi baya cikin toilet en ganin haka yasa ya mai da rigar sannan ya fito. Kanshi a sun kuye ya tsaya tsakiyar d'akin shiru ya d'anyi na wani d'an lokaci sannan ya d'ago kai ya dudduba cikin d'akin bai gani ba . Ita kuwa tunda ya ajiye mata ledan a gaban ta tana zaune ko motsi ba tayi ba sai wasa da yatsun ta da take yi tana ta nad'e hannun rigar da yamata yawan . Murtuqe fuska yayi tare da daqile voice yace. "Ke ." Kai ta d'ago cikin tsoro ganin yadda ya had'e fuska, kuma yasa tai saurin yin qasa da kai. Shiko cika tunxura shi tayi da takaici yana mata magana tana wani mai kallon hadarin kaji. A kufule yace. "Ba ke nakewa magana bako?." Miqewa tayi cikin sanyi da tsoro tace. "Me zanyi?." Mitsss yaja tsaki tare da tsuke fuska yace. "Can tafi ni me zan saki! ina kika d'ura min towel na ? da kika samu a toilet?." Sanin akwai abin da ta d'auka a toilet fine ne yasa ta gane me yake nema, shi yasa cikin sand'a ta wuce gefen shi kan qofar bedroom d'in ta jawo towel d'in da ta shanya data fito wonka. A hankali ta taka tazo gaban shi cikin sanyi ta miqa mai kanta a qasa. Shi kuwa ganin yadda take tafiya da yadda ta wani tsaya kamar marigayin zakara, shi yasa ya tsura mata ido ba tare daya karba ba, jin shiru bai amshi towel d'in ba yasa ta d'ago kai , cikin sauri tai qasa da idon ta tana kallon enda yake kallon. Wuyan rigar ta ya d'an kalla ganin wuyan ya mata yawa ga d'aya botur d'in ya bud'u , itako ganin inda yake kallo yasa ta matse towel d'in a qirjinta sannan ta cukui kuye wuyan rigar ta had'a tare da damqe shi da hannun ta d'aya sai ta kuma tsaya tana d'an zare ido irin na tsoro. Shi ko General harara ya cilla mata tare da jan tsaki sannan ya komo towel d'in ya fizge ya juya ya shige toilet d'in yayi wonkan shi tsab. Itako tunda ya shiga ta koma kan gadon ta zauna tare da yin tagumi fuska na zubda qollah sai numfashi take fizga cikin son yin kuka mai sauti sai dai kuma tsoron shi take ji. Shiko yana fita ya bud'e durowar ya zaro blanket mai taushi da laushi sannan ya zare pillow ya juya ya koma parlour ya konta kan 3str ba tare da jimawa ba bacci yayi awon gaba dashi. Itako ganin shiru-shuru ba motsin sa ga bacci data fara ji ga yunwa yasa ta zauna kan carpet d'in tsakiyar d'akin sannan ta jawo ledar ta samu ta d'an ci abin cin tana mai zubda qollah sannan ta d'an shan juice ta koma tayi konci yarta kan carpet d'in tana cike da kewan yan uwanta da ta kaicin a haka da ker tayi baccin. Haka dai sukayi rayuwar kwana 2 tare a d'aki d'aya kuma tun randa ya tabba yeta towel bai kuma mata magana ba, Sani ke musu hidi mar girki ko yaje Restaurant ya seyo musu in dere yayi Sani ya tafi d'akin Abdul mai targad'e , shiko General ya koma parlour itako tana daga ciki, Mama kuwa da Abdul suna nan suna ta shirin shirya mai gadan zare. Yau Sunday da yamma Sani da General sun gama shirin komawa cikin Jaji Sani kam har ya d'auki jakar laptop d'in ogan nashi zayi gaba, ganin General na zaune dole Captain ya dawo ya zauna . Sukayi gum har zuwa d'an woni lokacin sannan ya miqe cikin d'akin ya nufa a bakin qofa ya tsaya cikin murtuqe fuska da muryar miskilanci yace. *"Meenal"* Shiru bata amsa ba a kufule ya kuma cewa. *"Meenahl* shiru bata amsa ba. Cikin quluwa yace. "Bororiya zaki zo ko na tafi?." Jin haka yasa ta futo da sauri hannun ta na riqe da wuyan rigar ta jikin ta har rawa yake sai fidda numfashi tsoro take. Juyawa yayi ya nufi kitchen, itako sai ido ta zura mai, jikin ta na d'an rawa, bayan ya shige cikin kitchen d'inne Sani ne ya kalle ta cikin rad'a ganin Ogan a kufule yake yace mata. " "In kinji ya kiraki da Meenal ki amsa sannan kome kikeyi inya kiraki kizo yanzu maza bishi kitchen d'in." Kai ta geda cikin sanyi tabi bayan shi. A tseki yar kitchen d'in ta ganshi a tsaye sai ta rab'a gefen shi ta tsaya, Murya a turnuqe yace. "Kin iya girki ne?." "ehh." ta bashi amsa a taqai ce Tsaki ya d'an ja sannan yace. "Ke ni sauri nake ki matso kiga yadda ake kunna gas d'in sanan ki san abinda zaki dafa kuma kiyi iya ciki ki." Ido ya zaro mata tare da cewa. " kina jina ko?." Kai ta geda mai. Harara ya watsa mata sannan yace. "ai baki da bakin magana aikin banza cikin ki ko cikina." A d'an firgice tace. "Ina ji." Tsaki yaja tare da nuna mata komai sannan ya qara da cewa. "Wlh in kikayi garaje da barin gas a banzace, zaki babbaka fuskar ki kuma wlh ni ko a jikina." Toh kawai take ce mai a haka suka gama ya fito parlour tana biye dashi a baya suna zuwa ya cewa Captain Sani . "Mu tafi." suna fita yaja qofar ya rufe saurin da yake yasa ya manta bai murd'a key d'in ba haka suka fita suka tafi. A parlour suka tarar da Mama tare da Abdul tana d'uma mishi hannu qato dashi, wucewa yayi kamar bai gansu ba a ranshi kuwa zafi yakeji shi bai tab'a samun irin wannan kulan ba shi ya rasa wannan gatan a rayuwar sa. Suna fita daga cikin parlour General Aliyu yaji muryar.... By Garkuwar Fulani [8/18, 6:26 PM] πŸ’žIt's @lh@jiπŸ’ž: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *BANDIRAWO* page 1⃣3⃣ Na *Aysha Ali Garkuwa* πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ Pure moment of life writers *Dedicated 2 Zahra Muhammad Mahmoud (Surbajo) godiya mai tarin yawa hak'ik'a bazan manta k'aunar da kike min ba😍😍😘* *My dear Khadija candy Allah ya baki lafiya rabbi yasa zakkan jikina Allah ya baki lfy* ``` Masu karatu kuyi haquri a pages na biyu da suka gabata akwai inda na d'anyi typing error duk da dai nasan kun gane``` Ta mirgino tayi k'asa, Shi kuwa, tsayuwa yayi ya tsura mata ido yana mai yin murmushi mugun ta a cikin ranshi yayin da ya murtuqe fuska kuma. Ita ko Mirgino war da tayi yasa tayi k'a ba tare da sani ba, kanta ya bugi jikin tayis d'in lokaci d'aya azaban ya ratsata a firgice, ta bud'e ido cikin gigin bacci da tsaro ta mik'e tsaye tana dafe da goshin ta, tana ta yarfa hannu da za gaye tsakiyar d'akin tare da sakin kuka cikin sanyi murya tana. "Shiihhh wayyo goshi na k'afata wayyo k'eyana, wayyo Bappa na". Harara ya cillah mata cikin tab'e baki ya ja dogon tsaki tare da juyawa ya koma parlour. Tsakin da yaja ne ya tuna mata ina take kuma dawa take tare. Tsoro ne ya rufeta ita a ganin ta turota akayi ga zogi da goshin ta keyi mata tausa yin kanta da kanta ne ya kamata sai ta koma jikin k'ofar fitan ta rakub'e tare da sakin marayan kuka mai sanyin sauti . Yana parlour dai Amman yana jinta bacci yake sonyi ta addabi rayuwar sa da kuka gashi dama rayuwar takura yakeyi a kan 3str d'in da yake kwana sannan tazo ta toshe mai kunne da kuka, a k'ufule ya mik'e ya nufi d'akin, yana shiga ya tsaya kanta cikin tsuke fuska da murtuqe fuska voice a dak'ile ya nunata da yatsa cikin fad'a yace. " Wallahi ki fita idona in rumtsa kin isheni wallahi kin isheni iya isa, yarinya kina nan kamar mayya dan tsabar fitina yenzu tsakiyar daren nanne zaki tashi ki tasoni da kukan banza." Kai tayi ta girgiza mai cikin fidda ido woje dan tsoron masifar da yake mata jikinta har yana b'ari cikin tsoro ta kalleshi baki na rawa tace. "a a fahh, fahh turoni akayi na fad'o daga kan gado gashi goshi na sai ciwo yake k'uguna ma ciwo yake." Matso ta yayi cikin fad'a tare da nuna mata yatsa yace. "Ciro idonki a kaina wallahi inba hakaba sai na k'wak'ule k'attin idanun nan naki ki rink'a zaro minsu kamar y'ay'an boris mayya fiti nenniya, wazai tureki da kike cewa turo ki akayi kina nan kamar mage sai shegen son jikin tsiya da yawan birgima kina ta faman mirgine-mirgine kina shiga cikin blanket, ba dole ki rikito ba, gobe ma karki nitsu kiyi ta shure-shure a cikin bacci ke da fad'uwa kuma kun k'ullah, wallahi kuma kika kuma bud'e baki da sunan kuka , Hmmmm tam kinsan sauran." Tunda ya fara surfa mata masifa ta koma jikin ginin tana zubda k'ollah sai numfashi da takeyi sama-sama cikin tsoro. Tsawa ya kuma buga mata . "Maza kauce jeki konta." Nur- nur ta juya kan gadon ta konta cikin sanyi ta rumtse idon ta, shi kuma blanket ya zaro cikin durowar ya cillah mata a kanta yace. "Mage kawai ga blanket an k'ara miki sai kiyi ta nad'ewa a ciki sauran kuma kar kiyi Addu'a, sai kin samu abinda zai turokin da hasken wallahi ni ba ruwana ." yana kaiwa nan ya juya ya kashe wutan d'akin sannan ya koma parlour yayi konci yarsa, Ita ko kukan take sonyi kuma tana tsoro ga duhun da ya barta a ciki, a haka dai har bacci ya tsure ta...... Washe gari tun 7:00 Am suka gama shirin tafiyar su, ita kuwa lokacin ta gama kimtsa cikin d'akin ta fito parlour da nufin ta d'auki tsintsiya zata sharo d'akin har zuwa parlour, tana fita ta same su Sani na tsaye rik'e da laptop en ogan nashi shiko yana zaune kan kujera ya sunkuyo kanshi yana d'aura igiyar takal manshi, cikin sanyi ta kalli Sani fuska a d'an sake tace. "Bandirawo ina kwana?." Murmushi yayi tare da cewa. "lfy lau Meenal, kin fito ke nan, dama yanzu zamu tafi kuma gashi bamu sallah meki ba." "Allah ya kiyaye hanya ." tace dashi tare da juyawa gun General murya can ciki tace. "Jam b'an d'una, Ina kwana?." Bai kula taba bare ya amsa sai mik'ewa da yayi cikin bada umurni yace. "Captain mu tafi ." "Toh" yace tare da bin bayan shi , itako ido kawai ta tsura musu , har sunje bakin k'ofar fita ya juyo fuska a had'e yace. "me kike zura min ido? wallahi ki kula ko k'ofar nan bance ki takoba." Kai kawai ta gyada mai, sannan taci gaba da aikin ta.. *Katsina* 10:00Am sun isa Katsina,wani gida ne d'an ma daidaici suka shiga bayan mai gad'i ya bud'e musu gate, Sani nayin parking ya fito ya bud'e mai mota sannan ya fito cikin gidan suka nufa kai tsaye, wani parlour suka shiga tare da yin sallama suna shiga General ya zauna kan chains carpert din dake tsaki yar parlour shiko Sani cikin d'akin ya wuce, Jim kad'an sai ga Sani ya fito shida wani mutun mai d'an girman shekaru Wanda da ka ganshi zaka San shine mahaifin General dan kamar halitta dake saka ninsu farine tas mutu min mai kyawun fuska gashin kanshi mai yelwa da shek'i. Kan kujeren dake bayan Aliyu ya zauna . Murmushi yayi cikin kafe d'an nashi da ido yace. "Haiydar sai yaushe zanga happy a fuskar ka?." Kai ya sunku yar cikin sanyi yace. "Abba Ina kwana? ya jikin ka? kana shan magani ko?." Murmushi yayi tare da nunawa Captain Sani General d'in da ido sannan yace. "Alhamdulillah da sauk'i." Captain ne ya zauna gefen Abban a k'asa cikin sanyi yace. " Abba Yau kam ai zamu tafi tare da kai dan gwara ka koma kusa da oga yafi." Shiru yayi yayin da shiko Aliyu yake jiran amsar sa shima Captain ido ya zuba mai. A hankali ya sauk'e ajiyar zuciya sannan yace . "Me ya rege min da zaman Kaduna? me zanje inyi a can?." Wani irin nannau yan numfashi General ya sauk'e cikin sanyi yace . "Sani aini na saba da rashin iyaye a kusa dukda son kasan cewa dasu dana keyi Abba baya k'auna zama dani bansan laifin da nayi mishi ba." Shiru Abban yayi tare da shafa kansa shi kuwa Captain Sani Abban ya kallah cikin sanyi yace . "Abba General fa yayi Aure yanzu matar sa na gidan kuma Abdul da Mama sun matsa mata." Tunda Captain ya yace Aure Abba ya zura mai ido cikin mamaki yace. "Sani Aure kuma? Haiydar yayi Aure? waya aura ? y'ar waye? yaushe akayi auren banda labari?." Haka ya jero mai tabbayoyin cikin kad'uwa shiko General fuska ya had'e yana kallon Sani cikin yana yin. "Wayace ka fad'a." Shiko Sani ya kalli irin kallon da ake mai amman sai yayi kamar bai gani ba, ya maida hankalin shi gun Abba cikin nitsuwa ya mai bayani yadda akayi auren. Hamdala Abba ya rink'ayi cikin happy yace. "Insha Allah Yau tare zamu tafi." Ita kuwa Meenal suna fita ta gama sharan nata ta goge komai sannan tayi wonka ta fito tana tunanin me zataci ta shiga kitchen gas ta kuna sannan ta d'aura ruwan tea ta dawo parlour, can jimawa kad'an taji k'amshin tafasan tea din da yake tasa citta da kanamfari, ruwan tea din ta d'ebo amti sai sugar sannan tazo tana d'an kurb'a cikin kewan gida, Sallamar Nafeesat ce tasa ta juyo cikin jin dad'i dan tasan zata d'ebe mata kewa, gefenta ta zauna cikin fara'a tace. "Meenal mu je gun Anty Aysha tace naje na tayata girki niko in ason muje tare." Shiru tayi tana tuni gargad'in wannan mugun ita kuma ta gaji da zaman kad'aici dan haka kawai sai ta mik'e cikin sanyi tace. "Muje." Suna fita..... By garkuwar Fulani [8/18, 6:26 PM] πŸ’žIt's @lh@jiπŸ’ž: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *BANDIRAWO* page πŸ”Ÿ Na *Aysha Ali Garkuwa* πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ Pure moment of life writers *Wannan shafi Sa daukar wane ga duk masoyan wannan littafi na BANDIRAWO Ngd da qaunarku gareni* Daddy na ki ranshi tsayuwa yayi ba tare da ya juyoba, shiko Daddy da sauri ya qaraso inda yake yayin da Captain Sani kuma yayi gaba, gefen General d'in Daddy ya tsaya tare da kallon shi cikin tausayi da sanyi yace. "Aliyu anya ko a kwana kinnan kana zuwa gun Abban ka." Shiru bai bashi amsa ba sai ci gaba da tafiya da yake yi a hankali a zahiri da bad'iri Daddy yake sauraro amman kuma bai bashi amsa ba sai tsuke fuska da ya qara yi, shiko Daddy ba tare da ya damu da rashin amsar saba yaci gaba da magana dan inda sabo ya saba dama yasan bazai bashi amsa ba a hakan yaci gaba da cewa. "Aliyu kayi qoqarin a satin nan kaje gun Abban ka, sabida ko jiya naje gunsa bai da lafiya ciwon sugarnshi ya tashi sannan hawan jinin sa ya qara hawa ." Shiru yayi kawai suna tafiya a hankali shiko Daddy ba tare da damuwa ba yaci gaba da cewa. "Aliyu kayi qoqarin ka canza rayuwar ka mana ka samawa kanka farin ciki ka tayani roqar Abban ka ya dawo gidan nan kaji ko Aliyu inason d'an uwana ya kasan ce kusa dani." Kai ya d'an d'ago dai-dai lokacin da suka isa gaban motar. Ajiyar zuciya ya sauqe cikin yace . "Hmmm ." Daga nan kuma yace. "Daddy aini Abba ke gudu zama da nine baiso ya barni tun yarin ta na rayu ni d'aya a part namu tamkar maye, sai yanzu kuma ince ya dawo kuma ni d'in dai ina gidan ai ni d'inne da basa so." Kafa d'anshi Daddy ya dafa cikin kula yace. "Kaje ka duba Abban ka Aliyu!." "Toh" kawai yace tare da shiga mota suka tafi. Shiko Daddy ido ya rumtse yana mai jin zafin yadda d'an qanin nashi ya tashi cikin kad'aici da maraici tamkar maraya al'halin iyaye yenshi na raye, shine ya kamata ya lura dashi shiko Allah bai bashi mata ta gariba, gashi sana din rashin gata daya tashi a ciki yasa ya taso mai tsaurin ra'ayi gashi tun asali dama shi miskili ne ga rayuwar kad'aici ta qara sashi ganin rashin gatan da qaunar iyaye da yake ciki, murmushi ya d'an yi tune yadda yake tsare fuska cikin qin yarda da kowa shi tunda iyayen shi suka bashi yake ganin kowa ma baya son shi, sai dai kuma duk da haka yana mutun ta Daddy kuma muddin ya mishi magana kan abu toh yakan bi shawarar sa. Shi ko Aliyu a Jaji yayi kwana 4 ranar jummah da yamma yake ta shirin komawa cikin Kaduna da zugar yan rakiyar sa. Ita kuwa Meenal tun randa suka tafi batayi gigin yin girki ba sai fruits kawai take sha wanda aka loda mata a firic Yau tun da safe take tajin zaman d'akin ya isheta gani take an binne mata rayuwa ace mutun bazai ga ko idon rana ba. Bayan Anyi sallan la'asar ne Abdul kuma ya shigo gida cikin takai ci ya kalli Mama dake zaune a parlour bayan ya zauna gefen ta cikin bacin rai yace . "Wallahi Mama ni nama rasa me zanyi wa wannan Hamma Aliyu wallahi qofar zan balla kamar yadda ya balla min hannu mugun banza duk horonsu na sojoji yake zuwa ya sauqe a kaina." Fuska Mama ta tsuke cikin takaici tace. "Wallahi ko yanzu zaman da nake a nan mamaki nake dan naje gefen window bedroom d'in shi wallahi naji motsin mutun tsoro na Allah kar dai Aliyu ya fara tsafi ne da cire kan mutane". Ido ya zaro cikin kad'uwa da d'an dariya yace. " Haba dai Mama cire kai kuma? tsafi kuma? Hamma Aliyu d'in?, a a kam Hajia sai dai in karuwar shi ya kawo ta zauna zaman daduro." Ido ta tsura mai tare da cewa. "Ehh haka nefa wallahi kai Abdul kanka na jaa kai kaga ka gane, toh wallahi muje mu balla qofar." Miqewa sukayi a nufin zasu je cikin d'akin sai sukaji motsin ana bud'e qofar hakan yasa suka tsaya. Ita ko Meenal ta window bedroom taga irin qananan tsuntsayen nan wanda ake cewa caccangi so tana son tsuntsayen tun a Membila ganin yana d'an firewa da ker yasa ta fita don ta taima ka mai. Tana fita shiko tsuntsun ya zagoyo ta qofar aiko yana firewa a hankali, aiko tai ta binshi a baya tana ta son kama shi tana ta faman murmushi. Mama kam da Abdul baki da ido duka suka sake suna mamaki lokaci d'aya kuma sai ga Ya Amir da Aysha Nafeesat na biye dasu a baya Daddy da yanzu ya shigo shima sai ido kawai yake binta dashi. Itako ko a jikin ta don bata ma san akwai mutane a wurin ba, ganin bata ko kula suba yasa cikin qufula Mama ta qarisa gunta cikin bala'i da zafi ta yarfa mata wani irin gigiceccen mari. Cikin tsoro ta dafe fuska jiki na bari tuni hawaye ya fara zuba sai tsoro da ya bayyana a fuskar ta, Abdul ne ya matso cikin tsura mata ido da kallon qirjin ta har yana lasan lips enshi murya a sokan ce yace. "Ke qaramar karuwa yanzu ke ayanzun kinnan har kin iya biyo ingarman namiji kamar Hamma Aliyu har gida? lallai ka ruwanci ya zama abin da ya zama." Mama ce ta kuma ture ta cikin masifa tace. "Yau zakici ubanki zaki gane kinzo ka ruwanci shima ai nandin ba gidan ubanshi bane kuma nan ba gidan karuwai bane." Nafeesat ce ta matso cikin tausayin yarin yar da tagani wacce bazata wuce sa'arta ba, murya na rawa tace. "Ayyah Mama zaton fa zunubi ko daya ya kasan ce gaskiya, daga ganin ta kawai Ku bita da qazafin zina Mama kunfa san hukuncin maiyi wa wasu qazafin zina a musulun ce kalle tafa mai kyau da ita". Ture ta Mama ta kuma yi sannan ta yarfawa Meenal wani wawan mari har saida tayi tanggal-tanggal kamar zata fad'i. Dai-dai lokacin General Aliyu yayiwa parlour diran mikiya ganin suna tsaye cirko-cirko gaba d'ayan su, ga Meenal kuma a tsakiyar su sai kuka take yi cikin sheshsheqa. Su duka basuma san ya shigo ba sai da Mamata d'aga hannu zata kuma yarfa mata wani marin, ita kam ido ta rumtse cikin tsoro . Shiko Aliyu cikin. daga burya da zafi yace. *" Meenal* ." Jin muryar shi yasa gaba d'aya suka juyo inda yaken, ita kuwa cikin tsoro da gudu ta juya da gudu tayi kanshi tana zuwa ta tsaya bayan shi tana kuka me cin rai. Hannun ta General Aliyu ya kamo cikin takun isa da fushi cikin yanayin gargad'i ya yawota har...... By Garkuwar Fulani [8/18, 6:26 PM] πŸ’žIt's @lh@jiπŸ’ž: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *BANDIRAWO* page 1⃣1⃣ Na *Aysha Ali Garkuwa* πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ Pure moment of life writers *Dedication 2 Haermeebraeh & One luv and Maryam S bello (MSB)* *Masoyan BANDIRAWO kuyi haquri da wannan page d'in jiya da yau duk baqi nakeyi amman insha Allah gobe zan mana page 2* Gaban Mama ya tsaya cikin murtuqe fuska da yamutsa fuska tare da tsura mata ido cikin tsantsar zafi, Abdul kam a hankali ya rinqa ja da baya cikin tsoro yana kauda kai, Ita ma kanta Mama tabbas Aliyu yana mata korjini tana jin wani iri in ta ganshi ya koma kamar zaki. Ita kuwa Meenal sai kuka takeyi cikin sanyi da tsoro ga wani irin riqo da Aliyu ya mata gashi ganin yadda ya juyen ya qara firgitata sai numfashi take ja cikin tsoro da qamqame jikin ta. Cikin muryar gargad'i da daqilewar voice yace. "Wlh daga yau ko kallon banza aka kuma yi mata, Hmmmm." Sai kuma ya cike lips enshi cikin murtuqe fuska. Cikin qarfin hali Mama tace, "Hmmm zaka had'iye mune ? ko me zakayi mana? aikin banza ka kwaso karuwa ka kawo mana gidan Aure gidan sunan wallahi ko yanzu sai in dakata inga me zakayi?." Turata yayi gaban Mama cikin murtuqe fuska yace. "Gata wallahi gata magoji ya goda aga abin da zanyi." Shiru sukayi sai tsilli-tsilli suke da ido. Hannun ta ya kuma ja tare da matso Abdul cikin watsa mai harara yace. "Duk randa ka kuma tab'ata ko mugun kallo kayi mata wallahi sai na karya ka." Ya Amir kam da Nafeesat sai murmushi suke ganin yadda Abdul ke zare ido cikin tsoro. Daddy kam mamaki ne da dariya da kuma tabbayoyi ne a zuciyar sa, shin ita wannan wacece? me had'inta da Aliyun ? ita y'ar waye?. Haka ya sake ido da baki yana kallon yadda General yake jan hannun ta, itako tana biye dashi parlour suka shiga yana shiga ya maida qofar ya rufe, ita kuwa hannun ta ya yarfa tare da watsa mata harara ya kuma qara tsare fuska cikin fad'a yace. "Waya baki damar bud'e qofar parlour nanma ? bare kuma har ki fita tsakiyar gida ?, dan tsabar iskanci da raini nace karki fita shine kika fita ko!?" Kai take juyawa cikin tsoro da zubda hawaye baki na rawa tace. "a a tsuntsune fa naga zai mutu." Ido ya zaro cikin zafi ya d'aga hannushi zai yarfa mata mari dan in ba bugeta yayiba bazata nitsuba, dan tsabar raini wai ai tsuntsu zata tai maka mari mai zafi ya d'ago zai zuba mata, sai kuma ya tsaya yatsura mata ido ganin yadda ta, rumtse idon ta tare dasa hannu ta kama kanta πŸ™†πŸ»πŸ™‰gaba d'aya jikin ta sai rawa yake sai numfashi take fuzga da qarfi cikin azaban tsoro. Tsaki yaja da qarfi sannan ya koma kan kujera ya zauna ya lumshe ido tare da damqe hanna yenshi yana kad'a qafa, ita kuwa jin shiru bata ji sauqan marin ba yasa ta bud'e idon ta a hankali kan kujeran da yake ta tsurawa ido tana kallon yadda jikin shi ke bari kamar mazari sai ta qara takure wa jikin 2str tana mai zubda qollah, Can dai ya bud'e idon a hankali sannan ya sunkuya yana kunce igiyar takalmin but d'inshi hatta hannushi sai rawa yake dan an tsoka noshi kuma bai samu ya huce ba yana zare takal man ya d'an kalle ta da gefen ido cikin tab'e baki ya miqe cikin fushi ya nufi bakin qofar da ake buga musu a hatsele ya bud'e, A fusashe ya...... *kuyi haquri my lovely fans na wlh naso yau nayi typing 2 page so baqi nayi yanzu ko na dage zan mana ko 1 page ne mai Reed More 3 toh Wallahi tallahi banji shauqi shiko typing dole sai da nitsuwa da shauqi da kuzari toh yau jikina a mace kuyi haquri insha Allah gobe zan mana 2 pages Ngd* By Garkuwar Fulani [8/18, 6:26 PM] πŸ’žIt's @lh@jiπŸ’ž: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *BANDIRAWO* page 1⃣2⃣ Na *Aysha Ali Garkuwa* πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ Pure moment of life writer *Wannan shafi naku matan GARKO group GARKUWAR Fulani na gaida ku a duk inda kuke ina qaunar Ku ina al'fahari daku* Ya juya ya koma kan kujeran ya zauna, Captain Sani dake bakin qofar ganin yadda yake a murtuqe yasa ya shigo cikin sanyi, can gefen Meenal ya dire Trolley da ya shigo dashi tare da qatuwar jaka sannan ya zauna gaban ta kad'an, ita kuwa Meenal ganin shi yasa ta d'an sake tare da share hawayen ta, shiko General ko inda suke bai kuma kollo ba. A hankali ya bud'e trolleyn cikin sanyi yace. "Meenal ga kayan ki." Shiru tayi tare da tsurawa kayan ido. D'inku nane masu kyau na zamani na gani na fad'a sannan ga dogayen riguna zubin larabawa sai kuma riguna da siket yar kanti sabbin zubi sannan ga hijabai manya masu kyau sai su onthis nata masu laushi da tashi sannan d'aya jakar kuma takal mane a ciki masu kyau sai mayuka da turaruka su shampoo dai kala-kala sai man gashi da dai sauran kayan buqata na matan zamani, ido ta kuma tsurawa yan d'inku nan da aka mata masu kyau lokaci d'aya taji sanyi a ranta zata cire wannan riga mai dogon hannu, a hankali ta bud'e baki tace. "Na gode." Ido ya qifta mata cikin rad'a da alama da ido yace. "Oga ne ya saya miki shi zakiyi wa godiya." Kai ta juya ta kalleshi ganin baya ko kallon inda suke yasa ta juya cikin sanyi ta kad'a kai a hankali tace. "Zaiyi fad'a." Kai ya girgiza mata tare da cewa. "Kije kimai godiya." Yana fad'in haka ya miqe tare da cewa. "Oga bari naje na watsa ruwa." Baiyi magana ba kuma bai bud'e ko idon shiba. Shi dai Sani yayi gaba abin shi, Ita kuwa cikin sanyi ta matso gunshi a hankali tace. "( mi yetti masin) na (gode sosai,) Allah ya saka." Bai kula taba sai miqewa da yayi ya shige cikin bedroom d'in kai tsaye ya wuce toilet ruwa ya d'an watsa da sauri-sauri sannan yayi al'walah yana fita ya kimtsa sannan ya fesa turare mai sanyi da qamshi sannan ya fito, a parlour ya same ta zaune tana ta ninke kayan fita yayi ya nufi masallah ci, a qofar fitan ya had'u da Nafeesat dake shirin shiga part d'in nasu tana ganin shi tai sauri ta matsa baki na rawa tace. "Hamma Aliyu zanje gun Meenal ne." tsaki ya d'an ja cikin tsuke fuska yace. "Na tabba yeki ne da zaki tsaya min surutu kamar parrot." Kai kawai take juya mashi tare da rab'awa gefen shi ta wuce cikin parlour tana murmushi a ranta tace . "Nagode dai da baka hanani shiga ba." Shiko fita yayi ba tare daya kuma sauraron taba. Tana shiga cikin sanyi ta isa kusa da ita gefenta, ta zauna a hankali tace. "Meenal kina da kyau." Murmushi tayi tace. "Na gode." Kallon ta ta kuma yi tace. "Wallahi naji ina sonki kinmin kyau gaki da gashi, dama nazo ne inbaki haquri da abinda Mama tayi miki kiyi haquri insha Allah bazata sake ba." Murmushi ta kumayi tana mai tattara kayan tace. "Ba komai ya wuce me sunan ki kekuma?." dariya tayi sannan tace. " Ni sunana Nafeesat kinga daga yau mun zama qawaye ko ga Anty Aysha ma tace tana sonki kin zama qanwar ta wai zaki na zuwa kina taya ta hira ko." "Ehh mana zanje nima ina sonta ." ganin tana tattara kayan ne yasa itama ta miqe tana tayata tana ta mata hira suna shiga cikin d'akin ita ta shirya mata kayan sannan suka fara tattara daga ciki har parlour har zuwa cikin kitchen duk suka gyara ko ina suna gama moping aka kira sallah, al'walah sukayi sannan sukayi sallah suna idarwa Meenal ta shiga wonka riqe da gorar shampoo ita kuwa Nafeesat sai ta zab'a mata kayan sawa , tana fita ta shirya tsab abinta sannan sukayi ihsha parlour suka koma Nafeesat taje cikin gida ta karbi sitirecan Anty Aysha tana zuwa ta zauna kan kujera cikin fara'a tace , "Allah ko in na ja miki gashin kin nan zaizo har gadon bayan ki gashi mai sulb'i." Ita dai Meenal sai murmushi lokaci d'aya ta gyara gashin nan yayi tsab ya miqe sai sheqi yakeyi da qamshi daga nan kuma tace. "Meenal muje cikin gida ." Kai ta jinjina a hankali tace. "a a bacci nake ji." murmushi tare da cewa . "Hmm toh bari in tafi sai da safe." "Na gode BANDIRAWO am Na gode y'ar uwa ta." Tace mata lokacin da take fita . Toh kawai tace ta fita, tana fita shiko General ya shigo Captain Sani na biye dashi a baya riqe da leda a hannun shi . a parlour suka zauna suka d'an ci abin ci itako tana cikin bedroom d'in tayi konci yarta tana jinsu can kuma bacci ya fara d'ibarta kafin woni lokacin tayi bacci dan sanyin AC dake ratsata . Su kuwa suna gamawa Sani ya miqe tare da cewa . "Sai da safe oga." Kai ya d'an dago cikin sanyi yace. "Gobe fa zamuje katsina ka shirya dan da wurin zamuje mu dawo." Toh yace tare da fita a ranshi yana jin dadi dan harga Allah yana son yaga Ogan nashi na zuwa gun mahaifin nashi. Abba mahaifin Aliyu tunda ya rabu da mahaifiyar Aliyu Ammi bai sake zaman Kaduna na tsawon wata d'aya ba sai dai ya kan d'an zo yaga halin da Aliyun ke ciki kuma har yau bai kuma Aure ba ya koma can yana rayuwa shi d'aya kamar wandda akayiwa sihiri da zaman kadunan, shiko Aliyu yakan dan je kad'an-kadan in Daddy ya nace mai da yaje d'in. Captain Sani na fita ya miqe ya nufi bedroom en bai kalli ko ta inda take ba ya bud'e durowar ya zaro blanket sannan ya matso bakin gadon kanshi a gefen yasa hannu da nufin ya d'auki pillow, da sauri ya d'an juyo jin hannun shi ya sauqa kan ququnta ido ya zura mata ganin gaba d'aya ta mirgino sauran kad'an ta rikito qasa. Pillow ya zare tare da Jan tsaki ya juya a fili yace. "In kin rikito ai zaki tashi." juyowan da zai yaga tayi luuu.... *kuyi haquri In na samu time zuwa dare zan qara 1 page* By Garkuwar Fulani [8/18, 6:26 PM] πŸ’žIt's @lh@jiπŸ’ž: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *BANDIRAWO* page 1⃣4⃣ Na *Aysha Ali Garkuwa* πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ Pure moment of life writers *Dedicated to Anty Sis* ```Alhamdulillah ala kulli halin 😍😘😍😘 masoya na ina mai Baku hak'irin rashin ganin posting na akan lokaci Wlh Abu bawa ne sun min yawa na kuwa ga k'orafe-k'orafenku kan in k'afa yawan pages Ngd matuka nasan k'aunace, insha Allah zan dage ``` Kitchen suka nufa, Anty Aysha na ganin su ta kalli Meenal cikin murmushi tace. "Meenal ya gida?." "Alhamdulillah Anty Aysha ya aiki?." "aiki kam na kam mala ma yanzu zan je in shirya kan dainin ne." Kula ta d'auka cikin sanyi tace. "Nafeesat d'ebo sauran mu tafi." Tare suka shirya komai tsab sannan suka koma parlour Anyt Aysha suka zauna suna d'an hira yayin da Nafeesat da Anty Aysha ke ta janta a jiki, har zuwa azahar ganin lokacin sallah yayi ta mik'e tare da cewa. "Anty Aysha zan tafi lokacin sallah yayi." Cikin kula tace. "Toh muyi sallan a nan mana sai muci abinci in yaso sai ki tafi , wota k'il ko zakiyi bacci ne." Murmushi tayi sannan Anty Aysha ta ce mata . "Muje ciki kiyi al'wala." Murmushi kawai tayi tare da binta a baya. Bayan sunyi sallah ne suka zauna suka d'anci abinci suna d'an hira, kafin su ankara har 3:13 pm tayi ganin haka ta mik'e cikin sauri tana cewa . "Kai bari in tafi ." Nafeesat ce ta kuma tsaida ta a dole tayi sallah bayan sun idar suka kuma shiga kitchen tare suna shiga kitchen d'in itama ta zage suna ta aiki tare dan tana son gane kan kayayya kin aikin ba laifi kuwa ta fara ganewa gashi Anty Aysha na janta a jiki Nafeesat kuwa duk abinda zasuyi sai tayi mata bayanin yadda ake sarra fashi, dad'i sosai takeji a wannan d'an taraiyar da sukayi dan ta d'auki darusa da yawa ta fara gane komai bugu da k'ari dama ta iya girki kam tsab. Suna cikin kitchen d'in har zuwa 5 dai-dai zuwa lokacin kuwa sun kammala komai. *Mutan Katsina kuwa* har sun iso cikin gida A gajiye Abba ya zauna a parlour part d'in nasu, yayin da suka wuce babban parlour gidan kuwa ba kowa dan Mama da Abdul sun fita yawon mugun tarsu ya Amir kuwa da Daddy basu dawo gida ba tukun. Captain Sani ne yaje ya kawo musu ruwan sanyi tare da zama gefen Abba yana . "Abba sannu." "Yau wa Sani sannu kai ma dan ai kaine mai tuk'in ka fimu gajiya." Shi kuwa General wucewa yayi cikin bedroom yana shiga yayi shiru a nufin shi ya saurara ko tana cikin toilet d'in, shiru ba motsi hakan yasa ya matso jikin k'ofar a hankali ya dan buga k'ofar , shiru ba motsi tsaki ya d'an ja sanna ya murd'a marfin tare da d'an lek'awa, wayam ba kowa ganin haka yasashi juyawa cikin tsuke fuska kitchen ya shiga nan ma bata ciki ganin hakan yasa ya fito a fusace kai tsaye tsakiyar babban parlour yaje ya tsaya tare da tsurawa tsakiyar parlour ido cikin d'aga murya tare da tsuke fuska ya fara aika mata kira. *"MEENAL"* sai kuma ya d'anyi shiru tare da k'ara had'e fuska dan yasan yanzu Mama zata zo tayi rashin mutuncin nata. Jin shiru bata amsa ba yasa ya fara antaya mata kira ba k'ak'k'auta wa a jere- a Jere. *"Meenal"* *"Meenahhl*" *"Meenahhhl*" Abba da Captain dama tun yadda suka ga ya fita a fusace suka bishi da ido sannan kuma suka jiyoshi yana ta rabka k'ira, Sai suka mik'e tare da biyo bayan shi ganin ya tsaya ya coge yasa suka tsaya suma tare da zuba mai ido, fitan su yayi dai-dai da fitowar Meenal d'in daga cikin kitchen d'in cikin tsoro da rawan jiki ta nufi gunshi tana mai kallon yadda ya tsuke fuska tana zuwa sai ta tsaya gaban shi tayi k'asa da kai tana fidda numfashin tsoro, Anty Aysha da Nafeesat ko na biye da ita a baya , dai-dai lokacin ya Amir da Daddy suka shigo, suna shiga sai ga Mama da d'an kanzagin ta Abdul. Duk tsayuwa sukayi cirko-cirko suna kallon yadda ya tsareta a gaba yana hukun tata da ido. Ya Amir ne cikin mamaki yace. "Daddy kalli Abba a gidanmu yau." Daddy kam da sauri ya k'arisa gaban d'an uwan shi cikin k'aunar juna suka gaisa ya Amir ma ya iso tare da gaida shi . Nafeesat ce ta k'arisa gaban General d'in cikin tsoro murya na rawa tace. "Ayyahhhhh Hamma Aliyu kayi hak'uri wallahi muna kitchen ne muna taya Anty Aysha aiki." Kai ya d'an dago ya kalleta , ganin yadda ya cilla mata wani irin kallo yasa tayi k'asa da kanta cikin sanyi ta juya gun Abba, gai dashi tayi cikin sanyi taci gaba da cewa. "Ayyahh Abba kacewa Hamma Aliyu ya rink'a barin Meenal tana zuwa muna zama gashi muna taya Anty Aysha aiki kaga dama aiki ya mata yawa kuma Meenal zata ji dad'in zaman mu zamu d'ebe mata kewa." Kai Abba ya jinjina cikin sanyi yace . "Ba damuwa insha Allah zai barta." Nafeesat kam sai dariya tayi tare da jawo hannun Meenal cikin raha tana cewa. "Meenal kizo ga Abban mu shine Baban Hamma Aliyu dama yana Katsina yaune yazo." Gaban Abban suka tsaya cikin sanyi ta d'an durk'usa a hakali tace. "Sannu da hanya Abba ." Cikin fara'a Abba yayi maza yace. "Taso Meenal ni mahaifi ne a gareki ni ba surki bane a gunki, ki d'auken kamar mahaifin ki, Allah ya muku al'barka." Cikin jin dad'i tace. " Amin Abba ." Itama Anty Aysha ta matso tare da gaida Abba cikin happy ya amsa tare da cewa. "Aysha kema kinga kin samu y'ar uwa ko, Ke Meenal ai zakina zuwa kina taya Aysha aikin ko?." Murmushi sukayi baki d'aya sannan suka amsa da cewa. "Ehh Abba." Shiko Abdul duk maganar da akeyi idon shi na kan Meenal gaba d'aya ya zauce a kanta sai binta da ido yake baki a sake kamar soko tunda Nafeesat taja hanunta zasuje gaban Abba, yabi k'ugunta da ido har yana lasan lips d'inshi ganin yadda gaba d'aya take tafiya cikin wani salo a ranshi yake jin ya samu garab'asa har gida a hankali yace. "Nagode Hamma Aliyu ka kawo min ganima nima dole na d'ana." Ita kuwa Mama wani irin tsuke fuska tayi cikin salon rashin mutun ci da bak'in cikin dawowar k'anin mijin nata, sannan ga tsanar Aysha da Meenal da take ji cikin bak'ar magana ta kalli Aysha tace. "ai in mace nason ta samu, masu taya ta aiki haihuwa zatayi in ta isa ke kina nan baki da aiki sai ci sai k'aton kashi banza mai maceccen zuciya." Sai ta kuma juyawa kan Meenal cikin gyatsine tace. "Lallai karuwan ci ya fara samun lasisi tunda har ubban korton naki zai baki wurin zama, ko da yake ba bak'on abu bane ai shima ubban zaman banzan yakeyi a katsinan, uwar ma waya san ko yanzu haka tana *TAPA* jigon y'an iska." Wayyo General Aliyu gaba d'aya ya kejin jinin sa na tafasa zuciyar sa na soyuwa ji yake kamar zai had'iyi zuciya ya mutu gaba d'aya jikinshi har b'ari yake cikin fushi ya nufi gaban Maman." Abba ne ya kirashi cikin d'aga murya yace. "Kai Haiydar zo nan banson jin koma daga bakin ka." ai ya k'asa magana sai juyowa yayi ya rab'a gefen Abban kai tsaye bedroom ya wuce ya kasa zama ko tsayuwa sai zirga-zirga yake ranshi na tafasa. Ita kuwa Mama dariya tayi cikin jin dad'i sannan ta juya tare da jan hannun Abdul suka tafi. Ya Amir kuwa da Daddy hak'uri sukayi ta bawa Abba shi ko Abba murmushi kawai yayi tare da jansu Abban da ya Amir d'in yana mai basu labarin yadda akayi auren General da Meenal, fatan alkhairi sukayi tare da sanya albarka . Anty Aysha kuwa hannun Meenal taja tare da cewa Nafeesat. "Ku zomuje mu sharewa Abba d'akin shi." D'akin Abba na cikin part d'in Aliyu Amman inya zo yawan ci a parlour yake zama, gashi yanzu ko General ya tare a parlour koya za'ayi ne rai?. Shara sukayi tare da goge mai komai sannan suka fito tare da bawa Meenal hak'uri da halin Mama. Shiko General da k'er ya samu ya sarrafa zuciyar sa, sannan ya watsa ruwan tare da yin alwala sannan ya fito suka tafi masallaci. basu dawoba saida sukayi ishah. Suna dawowa Daddy yasa kab suka zauna a babban parlour yayin da Meenal da Anty Aysha da Nafeesat suka shirya musu abinci, tsarin gidan kenan duk tare suke had'uwa a parlour suci abinci. Ita kuwa Mama ta samu damar yi musu cin fuska kenan. Shi kam General a cike yake tab ya k'asa cin abincin dan shi dama In dai ba Abban shine yazo ba bai zama a cikin, sai harara yake cillawah Meenal itako tana kauda kai. Hira sosai Abba yayi tayi da Daddy tareda Ya Amir da kuma Nafeesat da Meenal a parlour nasu shi kuwa General so yake ya keb'e da Bodd'i ya casata dan koma menene itace ta jaza masu da tabi dokar sa ai hakan bazai faruba, shi yasa yace shi bacci zaiyi. Hakan yasa suka watse hirar tasu Abba ya nufi d'akin shi, Suma su Daddy duk suka tafi part nasu. Suna fita ya rufe k'ofar sannan da sauri yabi bayan Meenal d'in yana cije lips d'in shi, yana shiga cikin bedroom d'in.......... By Garkuwar Fulani [8/18, 6:26 PM] πŸ’žIt's @lh@jiπŸ’ž: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *BANDIRAWO* pg 1⃣5⃣ to 1⃣6⃣ Na *Aysha Ali Garkuwa* πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ Pure moment of life writers Gaban ta yaje ya tsaya, ya tsare ta da ido yana matso ta, itako tana ja da baya har ta zauna gefen gado, k'afar sa d'aya ya dago ya taka gefen ta cikin fad'a yace. "Ke ba a isa dake bako? duk abin da kika ga dama shi zakiyi ko ? toh wallahi ni zanyi maganin rashin kunyar ki sai anyi magana kiyi ta zaro ido kamar tsohuwar mayyah." Ita kam sunkuyar da kai tayi tare da zubda k'ollah cikin sheshshek'ar kuka . Ranshi ne ya k'ara b'aci ganin shi ba abin da ya mata kuma ta sashi a gaba tana kuka dan muna furci. Cikin fad'a ya damk'o hannun ta cikin masifa ya mik'ar da ita cikin k'uluwa ya nunata da d'an yatsa sannan tare da tsare ta da ido yace. "Wallahi ki had'iye kukan ki maza rufe min bakin me nayi miki da kike min koke-koken muna furci kin iya rashin kunya kuma kice kar ayi miki magana ." Kai ta rink'a juyawa cikin son had'iye kukan amman ta kasa sai hawaye shar-shar . Tsawa ya kuma buga mata cikin k'ara matse hannun ta yace. "Ki had'iye kukan ki da wahayen ki muna fuka yanzu me nayi miki?." Cikin kukan ta d'an d'ago ta kalleshi tana girgiza kai, baki na rawa cikin kukan tace. "Kayi hak'uri ka gafar ceni." Sai kuma kukan ya kufce mata kuka mai cike da k'unan zuciya kukan take har kamar numfashi ta zai d'auke gaba d'aya jikin ta sai bari yake da ker take cewa. "Kayi hak'uri bana son fad'a ina tsoron tsawa kaina na juyawa." Ido kawai ya tsura mata cikin mamakin ganin yadda gaba d'aya ta rud'e tana kukan cikin cushewar numfashi da k'unan zuciya gaba d'aya ta ke d'an layin jin kanta na juyawa." Cikin ta kaici ya kuma watsa mata tsawa. "Kada Allah yasa kiso tsawan wato ke gaki mai iya fidda kai ko ji muna furci toh wallahi ki kiyaye ni ko na fasa miki kan naki da tsawan." yana rufe baki ya hanka d'ata gefe ya juya ya nufi gaban durowa. Ita kuwa hannu tasa ta kama kanta cikin firgici da tsoro kukan da take ne ya cusa numfashin ta sai jiri a take sai duhu ya rufe mata ido sai ga jiri yu-yuh yana d'ibar ta. Blanket ya zaro tare da juyowa zai d'auki pillow, Ido ya tsura mata yana tsaye ba tare daya matso ta ba ganin tayi tangal-tangal zata fad'i yasa ya d'an matso ta cikin rashin sa'a kafin ya isoma ta fad'i k'asa kanta ya buga jikin gado ta kuma sulewa k'asa a take goshin ta yayi wani irin k'aton k'ulu sai wani irin kuka ta kuma saki cikin marayan murya da rauni tana. "Wayyo Allah na wayyo Bappa na kaina zai tsage." Zamewa yayi ya zauna gefen ta cikin sanyi ya jawo ta jikin shi cikin d'an daga murya yace. "Ke hauka ne a kanki zaki kashe kanki ko? yanzu fisabilillahi me nayi miki? ." Ita dai ba magana sai k'anmk'ame hannushi da tayi cikin mancewa da waye ne a kusa da ita dan azabar ciwon da kanta keyi, zaman yayi tare da jingina da jikin gadon, tallabe kan nata yayi ya d'aura kan cinyar sa ido ya tsurawa k'ulun dake goshin ta ido ya rumtse cikin jan tsaki, tafin hannun shi ya bud'e a hankali ya d'aura kan k'ulun sannan ya danna da k'arfi yana murzawa . Mik'a tayi cikin jin wani irin azaba dake ratsa kanta hannu bibbiyu tasa ta zagoyo k'ungunshi tare da k'amk'ameshi tana murza kanta kan cinyar sa. Jin yada ta cikuiku yeshi gaba d'aya ta mak'aleshi tana turmusa shi , lokaci d'aya jikin shi ya rink' bari a hankali yaji wani irin sanyi na shigarshi duk ta inda hudan gashi jikin shi yake, fata idon shi na sama suka fara wani irin motsawa lokaci d'aya sanyi mai tsanani ya rufe shi jikin shi sai kerba yake, cikin jin sanyin ya fara zamewa a hankali har ya konta kan chainis carpet d'in dake gaban gadon cikin rawan sanyin ya jawo pillow ya d'ora kanshi , ita kuwa jin ya dena murza mata wurin dake ciwon sai ta rink'a sauk'e ajiyar zuciya tare da mirgi nowa tayi pillow da damtsen hannushi, lokaci d'aya baccin azaba ya kwashe ta, Shi kuwa. Sanyin ne ya rufe shi tuk'uru cikin rawan sanyin ya yawo blanket d'in da ya d'auko sannan ya woreshi ya rufe su tare da k'ara matso ta yana dan rumtse idon shi. A haka cikin wannan yana yin bacin wani irin bak'on yanayin ya saceshi, baccin suke cikin blanket d'aya tunda suka konta suka fara baccin suka mak'ale cikin blanket d'in. 4:49 Am General ya bud'e ido cikin sanyi tare yin mik'a da yin Addu'ar tashi daga bacci, motsin shi ne ya tasheta cikin sanyi ta bud'e ido, aiko sai sukayi ido cikin ido, a firgice ta mik'e cikin rawan jiki da tsoro, kan gado ta haura tare da yin k'asa da kai tana dafe da goshin ta cikin jin zogi. Shi kuwa a kunya ce ya mik'e zaune hannun shi da tayi pillow dashi ya d'ago tare da yarfa hannun dan yayi tsami ya tara jini mik'ewa yayi tare da suke fuska da jan wani irin dogon tsaki sannan ya watsa mata harara ya wuce toilet. Wanka yayi a gaggauce dan kar jam'i ya wucesa yana fita ya fesa turare tare da ficewa masallaci. 7 dai-dai suka shigo cikin gidan a parlour su ya zauna da Abban shi suna d'an hira sama-sama, Captain Sani ya shigo shima ya zauna cikin girmamawa ya gaida Abba sannan ya kalli General cikin Sanyi yace. "Oga Uncle Ibrahim na baida lafiya ciwon zuciyar sa ya tashi tun jiya, so yanzu ina son inje in duba shi kafin ka gama shirin tunda yau zamu koma cikin Jaji." "Sai ka dawo ka gaida shi." General ya bashi amsa a gajar ce. Abba ne ya kalleshi cikin sanyi yace. "Sani ciwon zuciya kuma? tun yaushe yake tare dashi? kuma meke tayar mai da ciwon?." Kai Sani ya jinjina cikin sanyi da tausayawa yace. Abba Uncle Ibrahim ya kanmu da ciwon zuciya ne a a dalilin b'atan yarshi tilo da yake da ita." Cikin kula General yace . "Y'ar Sa kuma ? ta b'ata kuma? b'ata kamar babyn roba? a ina ta b'ata?." Ajiyar zuciya ya sauk'e cikin sanyi ya fara basu labari. *"Alhaji Ibrahim mai dala* babban d'an binciken ma adannan cikin kasane Allah ya bashi duniya mai tarin yawa Amman sai ya rasa haihuwa mafaifin Sani kuma yayan shine so rashin haihuwar yasa d'an uwanshi ya bashi d'anshi a haka ya reni Captain Sani cikin gata da kulawar matar sa Hajia Amina mace mai mutunci suna zaune a haka. wata rana Alhji Ibrahim ya tafi jihar Taraba wani binci ke cikin dutsen Membila Toh a can Allah ya had'a shi da wasu Fulani masu mutunci , so zamane na tsawon shekara yayi a wurin da fari yaje da Hajia Amina toh yanayin wurin yasa ta k'asa zama ta dawo nan Kaduna,. Shiko yaci gaba da zaman can , Mutanen da yake tare dasu masu mutunci da y'ar su mace d'aya mai suna Aysha , lokaci d'aya Allah ya had'a jinin Ibrahim da Aysha, suko iyayen Aysha ganin mutun cinsa yasa suka aura mai ita. cikin sa'a anayin auren ta samu ciki bayan watanni 9 ta haifi ya mace , a wannan lokacin kuma Alhaji Ibrahim ya gaba aikin shi so sai ya nemi tafi da matar sa Aysha, toh fa a nan iyayen ta suka k'i amin cewa abu kamar wasa ya zama gaske sunce ai sunsan inya tafi da Aysha sun rebu kenan sai dai ya barta a nan tunda itace kad'ai ta rege musu, a haka sukayi ta jani'in jaka har yarinya tayi wata 11 toh sai ga Aysha da wani cikin yayin da Hajia Amina ko take ta farin cikin sun samu yara a gidan su, Ibrahim yaso ya taho da matarsa amman sun hana sunce sai dai in zai bar musu yarshi inyaso ya tafi da Aysha tunda sun san albarka cin y'arsa zai ke zuwa da Aysha suna ganin yarsu suna , a dole ya yarda ganin ai ga wani cikin a jikin Aysha haka ya taho da Aysha da ciki ita kuwa babyn suka barta gun kakannin ta bayan sun dawo ba jimawa cikin Aysha ya b'are daga nan kuma bata kuma ko batan wata ba Alhaji Ibrahim ya shiga damuwa matuka toh amman yazaiyi. Haka Y'ar shi take rayuwa a rigar fulanin toh kwanaki da yaje dan dubata dashi da Aysha sai suka samu wai wasu yan birnin sun taho da ita kuma suma basu sansu ba, anyi neman duniya ko labarin ta ba'aji ba". Numfashi Captain Sani ya sauk'e tare da cewa. "toh kaji abin da yasa shi ciwon zuciya dan tunanin d'iyar shi k'waya d'aya tilo kullum sai yayi kuka yana tuna ko cikin wanne hali take ciki." Abba kam kai kawai yake juyawa cikin tausayi tare da cewa. "Zan sashi a Addu'a Allah ya baya na mai y'arsa ." Shi kuwa General kanshi ya sunkuyar Y'ar cikin tausayawa kanshi , a ranshi yake jinjina yadda iyaye ke son yaran su amman shi nashi iyayen watsar dashi sukayi duk da shi kad'ai suka malla ka a duniya. Ganin shirun da yayi ne yasa Abba yace. "Haiydar kuje tare mana kaima ka gaida shi da jikin!" Jiki a mace ya mik'e tare da shiga cikin bedroom d'in, yana shiga kanshi a k'asa har yaje bakin k'ofar shiga toilet d'in ya juyo a hankali jin sautin kukan Meenal d'in cikin sanyi ya tsurawa k'ulun goshin ta ido ya ciko tab sai shek'i yace gashi sai rawan sanyi take alamun zazzab'i , Ido ya rumtse tare da matso ta yasa hannu ya.... By Garkuwar Fulani [8/18, 6:26 PM] πŸ’žIt's @lh@jiπŸ’ž: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *BANDIRAWO* page 1⃣7⃣ Na *Aysha Ali Garkuwa* πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ Pure moment of life writers Yasa hannu ta bayanta ya tallabe k'eyan ta, sannan yasa d'aya hannu kan goshin nata , ita kuwa ido ta tsura mai cikin tsoron ganin yadda yake murtuk'e da fuska gashi yasa hannu kan goshin ta dake suntume tib, tafin hannu shi yasa ya danna k'ulun tare da fara murzashi da k'arfi, cikin azaban da yake ratsa ta tasa hannu ta kamo hanna yenshi duka biyu tana tsalle cikin azaban da zubda k'ollah tsalle take sosai tare da tirjr-tirje tana kuka da magiya. "Wayyohhhh Allah na wayyoh kaina wayyo goshina zan mutu kaina zai fashe wayyo Bappa na." Bai kulata ba sai k'ara murza wurin da yakeyi cikin tsura mata ido yana kallon fuskarta da yadda take tsalle kamar yar tsana, ita kam Meenal zuwa yanzu tuni ta sake mai hannu taci gaba da tsallen da yarfa hanna yenta hawayen ma ya k'afe sai juya kai take cikin fara ganin duhu. A haka yaci gaba da murza k'ulun har ya b'ace bat, a hankali ya d'an sake ta tare da tsura mata ido ganin sai wani irin lumshe ido takeyi can sai kuma wasu siraran hawaye dake bin fuskar ta. cikin tsurawa fuskar tata ido yaga tana wani irin layi kamar mai maye, tayi wani luuu zata fad'i, ganin haka yasa cikin sauri ya rik'o hannun ta, ta fad'o jikin shi sannan tasa hannu biyu ta zagaye k'ugunshi sai kuma tayi lib kamar maiyin bacci. Haka tasa dole yaja jiki a hankali ya zauna bakin gado da ita, ita kuwa sai k'ara mik'ewa tayi ta narke a jikin shi, a hankali ya rink'a sauk'e ajiyan zuciya tare da lumshe ido, cikin nitsuwa ya kuma bud'e idon ya tsura su kan fuskar ta, Baki ya tab'e tare da jan dogon tsaki sannan ya mirgina ya matsa gefe, ita kuwa sai ajiyar zuciya ta sauk'e tare da gyara konci yar ta, taci gaba da baccin cikin sauk'e ajiyar zuciya. Mik'ewa yayi cikin sanyin jiki a hankali ya shiga cikin toilet d'in, jiki a mace ya samu ya watsa ruwa sannan ya fito, gefen gadon ya zauna hannushi rik'e da towel yana goge suman kan shi, tare da kafeta da ido har zuwa wani lokaci kollon da yake mata ne yake k'ara kashe mai jiki, da k'yer ya samu ya d'an shafa mai sannan ya shirya cikin galila mai matuk'an kyau kalan sararin sama niya sai farin takalmi da farar hula, wani irin kyau shigar tayi mai kalan kayan da takalmin da hular sai ya fita tamkar adon sararin samaniya, kyawun surarsa da cikar haibarsa ya k'ara fitowa ba abin da yakeyi sai k'amshi da shek'i farar fatar sa ta k'ara fito da cikar haibar sa. Yana gamawa ya dawo gaban gadon ya tsaya yana kallon yadda take rawan sanyin, a hankali yasa hannushi kan wuyan ta, jikin zafi kamar wuta, shiru yayi yana tunanin ko me zayi mata? gashi ko ruwan tea d'in ta na jaraba bata shaba yau. Kai ya kad'a tare da fitowa parlour, a tsaye ya samu Captain Sani na jiran shi, yana ganin shi yayi gaba har ya fita sai ya kuma juyowa jin ba alamun ogan nashi na bayan shi, yana juyowa ya ganshi ya fito kitchen rik'e da filas da cup ya nufi bedroom d'in, shi kam Sani murmushi yayi tare da juyawa ya fita yana jiran shi cikin mota. Shi kuma General kan durowar gefen gadon ya ajiye mata sannan ya juya ya fita, a babban parlour ya samu Abba da Daddy sunyi shirin su na tafiya masallaci da yake yau jumma'a ane in sun tafi tun safe sai dare suke dawowa tare suka fito , a hara bar gidan suka samu ya Amir ma da Anuty Aysha tare da Nafeesat zasuje anguwa, a haka suka shiga motocin suka fita suna fita motar Abdul kuma tana shiga, wani irin murmushi mugun ta Abdul yayi tare da cije lips d'in shi sannan ya kuma lasar lips d'in binsu da ido yayi cikin happy ganin duk sun fita mutanen gidan gashi ita kuwa Meenal tana cikin gidan, cikin sauri yayi parking jikin shi har yana rawa ya nufi cikin gidan.. Su Abba suna fita masallaci suka wuce, Su ya Amir ko Zaria suka tafi. Suko su General kai tsaye gidan Alhaji Ibrahim mai dala suka wuce, suna isa kai tsaye cikin gidan suka wuce da jagoran Captain Sani, gidan Alhaji Ibrahim gidane mai girma cike da alfarma da kayan k'awa na rayuwa. Wani Babban parlour suka shiga bayan sunyi slm an basu izinin shiga, suna shiga Captain da General Sani suka wuce gaban Alhaji Ibrahim wanda ke konce kan wani tattausan carpet suka zauna, cikin girmamawa General ya gaida shi tare da cewa. "Uncle ka rege tunani dan gudun kar ya cutar da kai." Cikin rawan jiki irin na mara lafiya ya yunk'ura ya zauna tare da rik'o hannun wani mata shi mai cikar zati Dr Jabeer Muhammad wanda d'an uwan captain Sani ne uwa d'aya uba d'aya, kuma shine wanda Alhaji Ibrahim yayi niya da alk'awarin aurawa yarshi Amina kuma ko yanzu da ta bace bai fasa niyar saba acewar sa tunda bata rayuwa cikin birniba burinshi ya aurawa Jabeer ita dan Jabeer yaro ne mai mutunci da sanin ya kamata ga tausayi kuma dama tun Amina tana k'arama in sunje Membila sai yace itace matar sa shiko Alhaji Ibrahim yayi alk'awari kuma shi Alhaji Ibrahim irin mutanen nanne musu kaifi d'aya fad'a da cikawa ne. Yana tashi zaune ya kalli General cikin sanyi da rawan murya yace. "Aliyu na kasa mantawa na gaza daurewa kuka na ina Amina take? ko a wanne halin take ciki? ko ya lafiyar ta?." Sai ya kuma yi shiru cikin sanyi ya rik'o hannun Dr Jabeer sannan ya kalli su General da sauran mutanen dake parlour yace. "Ita min kena d'aya tak gashi azzalu mai sun d'auke min ita gashi mahaifiyar tama kullum sai kuka." Cikin tausayi General yace. "Insha Allah Uncle zamu maida hankali kan ne mota kuma zamu d'auki mataki." Shi kam Jabeer sai hannu ya mik'awa General tare da share k'ollan dake bin fuska shi murya na rawa cikin sanyi yace. "General kuyi duk abinda ya dace ko nawa ne wallahi zamu kashe dan samun dawo war farin cikin mu, Amina itace burin rayuwa ta itace sanyin idanniya ta bazan iya rayuwa inba itaba ban tab'ayin 2 weeks ban ganta ba duk rintsi a sati sai naje Taraba na ganta Amman gashi yanzu har tsawon wata d'aya ban san halin da take ciki ba." Sai kuma ya juya gun Alhaji Ibrahim cikin kukan yace . "Uncle dan Allah gobe a d'aura mana Aure da Amina ni ko bata nan na yarda a d'aura mana aure kuma duk halin da zata dawo a ciki na amince da ita a matsayi mata." Kuka yake yana magana lokaci d'aya kukan nashi yasa Uncle d'inma kuka Captain Sani shima sai kuka Hajia Amina ma sai kuka yayin da Aysha ko mahaifiyar Amina take cikin gidan bata wurin, sai wata yarin y'ar budurwa wacce itama take ta kukan wui-wui harda majina a hanci kuma sai kallon General take cikin zubda k'ollah, da kyer Uncle ya kama hannun Dr Jabeer yace. "Insha Allah gobe za a d'aura muku auren." Cikin kukan ya kalli General da Captain Sani numfashi ya furzar tare da sauk'e ajiyar zuciya yace. "Aliyu na tsani duk wanda ya nesan tani da y'ata ji nake inama ace gani gashi wallahi ban ma sannan wanne irin abu zan mishi ba, rok'ona a gareku in Allah yasa kuka kamashi kar ku barshi da hankalin shi a mai dashi yadda bazai taba gane banbanci tsakanin mace da namiji ba bare ranshi ya tuna mai ya sace wata." Kai yake gyad'a mai cikin k'arfin guiwa yace. "Insha Allah ." A haka sukayi ta bawa Uncle hak'uri da bashi baki Dr Jabeer kam kamar wanda aka yiwa mutuwa. Sai lokacin sallah suka tafi masallaci daga nan kuma suka wuce cikin Jaji. *Abdul* kuwa cikin farin ciki da mugun ta jikin shi har yana rawa ya kutsa kai cikin ...... By *Garkuwar Fulani* [8/18, 6:26 PM] πŸ’žIt's @lh@jiπŸ’ž: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *BANDIRAWO* pg 1⃣9⃣to2⃣0⃣ Na *Aysha Ali Garkuwa* πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ Pml Wani irin shak'a ya mata tare da mik'ar da ita tsaye sannan ya ingizata kan gado, a gigice ta fad'a kan gadon yayin da guywarta ta bugu jikin gadon lokaci d'aya ta fara ganin wani irin duhu na rufe mata ido jikin ta gaba d'aya ya kama rawa cikin rawan jiki ta sule ta zame k'asa jikin gadon tasa hannunta ta k'amk'ame cikin tattara k'arfinta baki d'aya har jijiyoyin wuyan ta na tashi ta dunk'ule ta had'a k'irjinta da guiwowin ta, ta kafa kanta jikin gadon, tare da sakin wani irin kuka mai cin rai. Shiko Abdul ganin niyarta na dunk'ulewa yasa yayi ta zuba mata mari da gora kanta da jikin gadon yana. "Shegiya taurin kai ko? toh wallahi zaki jawa kanki kisa ko ki mik'e da kanki ki hau gado ki bani abin da nakeso ko na kasheki". Cikin wata iri yar murya tace. " kashe ni ! ka kasheni nace nafi muradin kisan a gareka mugu azzalumi tantiri la'anenne." Ba tare da ta rufe bakin taba yayi wani irin gora kanta a jikin gadon ji kaka gum da k'arfi, wai ina dalili zata la'anceshi' Zafin buga kan da yayi cikin azaba ta rink'a addu'a da kurma ihu tana kiran Hamma Jabeer Hamma Aliyu a jere a jere. "Wayyo Hamma Haiydar wayyo Allah na wayyo dan uwanka zai kashe ni zan mutu Hamma Aliyu kaci amanar yardar da Bappa yayi ma Hamma Aliyuuuuuuuuuuuuu." General kuma yana lumshe idon sai wani irin baccin fargaba ya saceshi baccin yake cikin tsoro da bugawar zuciya, a cikin baccin Allah ya nuna mai halin da Meenal ke ciki har k'iran da take zuba mashi, abin kamar mafarki kamar ido biyu dan kamar a fili yake jin k'iran da take k'wada mashi, sa juya kai yake ya kasa tashi ya kasa bud'e ido. Shi kuwa Abdul yanzu ya samu ya b'amb'aroto daga jikin gadon ya cillata kan gado sannan ya zuge bel din k'ugunsa ya zare dogon wondon ya cilla gefe sannan ya nufi kanta haik'an k'adaran, ganin haka yasa ta rumtse ido cikin k'arfi tace. 'Hamma Haiydar Allah ya isa min kai ka jamin Hamma Haiydarrrrrrr." Jin wannan k'iran General Aliyu Abubakar Rumoh, yayi wani irin firgita jikin shi na rawa ya mik'e tsaye gaba d'aya illahirin jikin shi b'ari yake kar-kar hatta jijiyoyin kanshi dana hanna yenshi idanun shi sun kad'a sunyi jazir sai zufa ke tsatstsafo mai tako ina. Daga cikin d'akin ya fito a gigice cikin tsawa da k'arfi yake zubawa Captain Sani k'ira ba k'ak'k'autawa k'i ranshi ya a jere-ajere cikin kid'ima yana. "Captain! Captain! Captain! Sahniiihhh ". Shiko Captain Sani yana parlon ya b'ink'ire kan 3 str yana bacci sam duk k'iran da ake mashi baiji ba. Shiko General ya fitowa parlour cikin zafin nama da hatsala ya tak'ark'ara ya zabgawa Captain Sani wani irin gigiceccen marin daya sa, Captain mik'ewa cikin azaba da tsoro baki na rawa yace . "Sir lafiya meke faruwa?." Cikin zafin nama yayi gaba tare da cewa Captain. "Banza kawai mai baccin asara, ka biyoni maza yanzu zamu shiga cikin kaduna nan da minti 5 insha Allah inaso in ganni a gida." A firgice Captain Sani ya bishi cikin gudu yana, "lafiya kuwa?." A fusace ya juyo cikin nuna shi da bindiga tare da cewa. "Banza parrot kayi sauri ko na fasa ma kai ." ya fad'a yana nunashi da bindiga, cikin gudu Sani ya fad'a cikin motar General BMW 7series mota mai bala'in gudun tsiya, yana shiga shima General ya tada motar ya danna hon d'in ta wanda yake sanarwa da sauran masu saran Brigadier general Aliyu Abubakar zai fita, ai ko a take sai ga Hilux kusan guda 8 sun bisu a baya, gudu General yakeyi kamar zai tashi sama zuciyarsa sai harbawa takeyi tara-tara. Cikin minti 6 sai gasu cikin Kaduna daga nesa in anji jiniyar su sai a rink'a kaucewa ana basu hanya ganin irin gudun da suke ya bawa mutane tsoro sosai, duk motocin an tsaya a na jiran su wuce a cikin wad'an ke tsaye harda motar ya Amir dasu Anuty Aysha , Nafeesat ce ta kalli ya Amir cikin zare ido tace, "Ya Amir Hamma Aliyu ne fa meke faruwa yake irin wannan gudun?." Cikin rud'u ya Amir d'in shima yabi bayan Hilux din a guje. Abdul kuwa yana zuwa kan gadon zai danne ta tayi yunk'uri cikin tattara sauran k'arfin ta, ta mik'e ta sauk'a kan gadon , k'ara ta saki da k'arfi tare da durk'ushe wa dan ta k'asa tsayuwa dan ya buga mata guiwowin nata rarrafe ta rink'ayi cikin kuka da k'iran Hamma Aliyu ta nayi tana juyawa tana kallon yadda yake matso ta yana k'ok'arin zame gajeren wonddon dake jikin sa, ganin har ya isota ya durk'uso kanta yasa ta rumtse ido dai-dai lokacin da ta gaggara ta fito parlon tare da cewa. "Hamma Aliyuuuuuuuu!." Dai-dai lokacin kuma General Aliyu yayiwa babban parlour nasu diran mikiya cikin gudu tamkar wanda zai tashi sama dan ko parking bai k'arisa yiba ya fito motar, jin ihun ta da k'iran shi da takeyi yasa ya nufi part d'in nasu cikin azabebben fushi da hatsala gaba d'aya jikin shi b'ari yake kamar an buga mishi tambarin yak'i. Yana zuwa ya murd'a k'ofar yaji a rufe take , cikin fushi da rud'ani yayi baya-baya ya sake tahowa a guje ya had'awa k'ofar naushi d'aya sai ga k'ofar ta bud'u. Shiga yayi cikin zafin nama yayin da Anuty Aysha da Nafeesat da ya Amir suke biye dashi, dai-dai lokacin kuma su Abba ma suka shigo cikin gidan. Yana shiga ya hangota durk'ushe tana rarrafe , ita batama lura da shiba shiko Abdul yana d'ago kai ya kalli General da yadda ya juya kamar zaki, kawai sai ya d'ora hannu a kanshi tare da rawan jiki ya rink'a komawa baya-baya yana jan gajeren wonddon shi sama. Ido Aliyu ya zazzaro waje cikin firgici da tsoro ga jikin Meenal da ya gani duk jini fuskar ta duk tayi jazir da jini ta kumbura sintim cikin razani yayi kanta tare da cewa "Meenarrrrl ! me yayi miki ?." Jin muryar shi yasa ta juyo da sauri don, da kallon Abdul take ganin ya fasa, tab'ata, tana juyowa taga Hamma Aliyu cikin k'arfin hali da dauriya ta mik'e a guje da dink'isa k'afar cikin kuka ta nufoshi tana. "Wayyo Allah na Hamma Haiydar ka ceceni zai keta min haddi." Ganin ta nufoshi ne shima yayi maza ya bud'e mata hannu cikin gudu ta fad'a cikin k'irjishi tare da rugume shi, shima ruggume ta yayi cikin matseta a k'irjishi kamar za'a k'wace masa ita matseta yayi tsam a jikin shi yana wani irin numfashi, da ker ya b'amb'arota sai a yanzu yaga ashe a sume take, cikin razani ya talla bota ya mik'ata hannun Anuty Aysha dake tsaye gefen shi, tana karb'ar ta shiko ya nufi kan Abdul gadan-gadan cikin wani irin takun da yafi kama dana zaki , shiko Abdul zuwa yanzu ba fuskar Aliyu yake gani ba fuskar zaaki yake gani a jikin Aliyun yana dumfa roshi, Cikin tafasar jini da zuciya da jiki Aliyu ya rarumo shi wuyan shi ya shak'o cikin k'arfi wanda a take Abdul ya fara wani irin kakari da zazzaro ido waje tuni numfashi sa ya fara tafiya, shak'e wuyan Aliyu yayi har jikin shi na rawa kar-kar bai sakeshi ba har sai da yaga fukarsa tayi jazir sannan ya d'aga shi sama cikin jujjuya shi ya man nashi da k'asa, cikin azaba Abdul ya saki wani irin gigiceccen ihu da kururuwa tare da rik'e wuyan shi da kokkoson shi , ba sararawa General ya rink'a butin dashi tamkar k'olloh naushe yakeyi tun cikin parlon su har ya fito babban parlour su inda Mama tayi kanshi cikin bala'i da da masifa fad'a take tana. "Aliyu hauka ne a kanka kashe min d'an nawa zaka yi kaje ka gama d'ura giyar ka shine za kazo ka kashe min yaro toh Wallahi ka tari bala'i ka samu ka joganowa zuriyar Ku kab tashin hankali wallahi ko ubanwa ya tsaya ma sai an d'aura min kai ." Ina aishi Aliyu baya tare da ita bol kawai yake bugawa da da Abdul yana tatta kashi a haka har ya fitar dashi farfaji yar gidan cikin huci da tafasan jini fuskar nan kamar zata fad'o k'asa ya shak'o Abdul wanda zuwa yanzu ko kanshi baya iya tsayar wa, shak'eshi yayi cikin k'arfi ya cilla shi tsakiyar yaran shi dake kollon su cikin tsoro, cikin bada umurni yace. "Gashi Ku canza mai kamanni ." aiko kamar ma yunwatan zakuna sukayi kan Abdul dukanshi suke kamar zasu halla kashi , Mama kam ganin Aliyu ko inda take bai kala ba kawai sai ta kurma ihu ta nayi tana burburwa ta fad'i gaban Daddy cikin masifa, ta nuna Aliyu d'aya shigo yanzu kai tsaye kitchen ya nufa yana zuwa man gyad'a ya tuttila cikin kasko gas ya kuna cikin k'ure gudun shi ya d'ora mayin a take ya fara tafasa yana damuwa kamar kolta, bai fitoha sai daya d'auko kaskakon yana fita ya nufi waje inda Abdul yake ta rusa ihu, ita kuwa Mama tana ganin ya fito da kaskon soyeyyen mayin gyadan ta fasa wani irin kuka tace. "Daddyn Abdul kana gani Aliyu zai kashe mana yaro d'an k'afa zai kashe amman ka zauna ka sunkuyar yar da kai me kake nufi barin shi zakayi ya kashema d'an ka Aliyu wato tak'ama kakeda kai Soja ne tsinenne mara imani." Cikin tarin bakin ciki da kunya Daddy yace. "Rukayya kin cuceni kinci amana ta kin b'ata min tarbiyar d'ana! shin Rukayya sai yaushe zaki bar cutar dani da d'an uwana ." Sai kuma Daddy ya dafe kanshi cikin kuka kamar yaro yace. "Wayyo ni Aliyu ina zan kai wannan kayan kunya da bakin ciki ashe d'ana mazina cine mazina cin ma kuma zinar ma da matar Aure matar auren ma matar Aliyu d'an uwanshi, Rukayya Allah ya isa ni ban bawa Abdul irin wannan tarbi yarba kin cuceni kin cuci d'anki, Aliyu ka kashe Abdul ko ma samu mu cire najasa a cikin zuciyar mu, Rukayya ki sani ina sane ke kika had'a tuggun da kika rab'a d'an uwana da matar sa sannan kika maida musu d'an su marayan dole, wannan gidan da muke ciki kin sani gidan d'an uwana ne amman masifar ki da sherrorin ki yasa gidan yafi k'arfin shi kin gama dashi kin rabashi da matar sa mai mutuncin sannan shima Aliyu zaki hanashi jin dad'in zama da matar sa ni na yafe Abdul kije na bar miki shi." Sai kuma kawai yaci gaba da kuka, shiko Aliyu farfajiyar gidan ya nufa kawai yayinda Abba ke binshi a baya, yana. "Haiydar ya isa ya isa haka, kasa abar yaron nan Haiydar kar kabari su cutar dashi." Shi kam Aliyu harga Allah ya san dai magana Abban shi keyi amman ya kasa gane me yake fad'i. Yana zuwa cikin bada umurni yace su taliye mai k'afafun Abdul aiko a take suka yimai zaman y'an kaciya, cikin rumtse ido Aliyu ya saiti gabanshi ya rink'a tsulala mai soyeyyen man gyadan nan, wayyo Abdul cikin wani irin azaba yayi zillo tare da cillar wawan ihun wanda saida Daddy da ya Amir da su Mama da Nafeesat suka fito a guje, Allah Sarki Daddy naka koya yake zakiji tsoron rasashi duk sai yaji jikin shi na rawa, Shi kuwa Abba kuka ya saki kamar yaro gashi ko zai kwana cewa sojojin su bar dukan Abdul d'in ba bari zasuyi ba indai ba ogan su ne ya daka tar da suba. Shiko Aliyu yana gama tsulala soyeyyen mai d'in ya cakumo wuyan shi cikin makan cewa ya rink'a gora kanshi a jikin motocin Hilux d'in dake jere a wurin, Shiko Abdul tuni ya fara jin k'amshin mutuwa gaba d'aya jikin shi sai rawa yake sai fitsarin azaba dake min cinyoyin shi, Mama ko cikin ihu tace. "Aliyu ka kashe min Abdul Wallahi niko zan kashe Meenal." tana kaiwa nan ta juya a guje zata koma cikin gida, Cikin zafin nama Aliyu ya yamutso Abdul ya hankad'o mata shi gaban ta ganin yadda d'an nata ya koma sai kawai ta durk'ushe a wurin tare da ruggumo shi, Abba ne cikin zafi da tsoron kar d'an nashi yayi kusan kai ya tsaya gaban Aliyu cikin zafi ya rink'a zuba mashi maruka yana. "Ka cuceni ka cuci d'an uwana a gaban shi ka kashe mai d'an shi dan tsanar zalumcin Toh maza wuce ka fito da wannan yarinyar a gidan nan!." Shiko General cikin rashin sanin me yake yi ya nufi cikin gida ya koma kai tsaye gun Anty Aysha ya nufa yana zuwa, ya ruggumo Meenal d'in cikin sanyi yazo ya kontar da ita kan gado a hankali ya zuge zip d'in rigar ta..... By *Garkuwar Fulani* [8/18, 6:26 PM] πŸ’žIt's @lh@jiπŸ’ž: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *BANDIRAWO* page 1⃣8⃣ Na *Aysha Ali Garkuwa* πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ Pml Kai tsaye cikin gidan ya kutsa kai, yana zuwa tsakiyan parlon ya tsaya cikin kasa kunne da zazzare ido tako wanne kusurwa, murmushi yayi cikin lasar lips d'in lshi jin gidan shiru ba motsin kowa. Part d'in General ya nufa da sauri-sauri gudun kar wani ya ganshi, har yaje bakin k'ofar ya murd'a, cikin rashin sa'a ko ya samu k'ofar a bud'e take, ajiyar zuciya ya sauk'e tare da d'an buga tsalle da tafa hannu , har zai shiga sai ya kuma tsaya jim kad'an kuma sai ya juya part d'in Mama a hankali ya shiga cikin parlon ta cikin sand'a ya lek'a bedroom d'in ta can ya hangota kan makeken bed d'inta tana bacci cikin tsuke fuska daga dukkan alamu mugun ta take tsak'awa tayi baccin. Ganin ta b'ink'ire tana baccin asara yasa, Abdul juyawa cikin sauri ya nufi part d'in General. Yana shiga parlon ya maida k'ofar cikin sand'a ya rufe sannan ya murd'a key d'in ya rufe k'ofar kirib ya kuma zaro key d'in ya jefa cikin aljihun shi. Parlon ya tsurawa ido tare da shak'ar k'amshin da part d'in yake yi. Murmushi yayi tare da shigewa cikin d'akin. yana shiga ya ganta kwonce kan gadon tana baccin wahala duk sai duk'unk'unewa takeyi alamar sanyi da cuta ta dunk'ule cikin blanket sai fuskar ta zuwa k'irjin ta ne a fili, fuskar nan tayi fiyau sai tsuke d'an bakin ta da tayi wanda yake jazir da shi. A hankali ya hau kan gadon cikin sanyi ya rab'a gefen ta ya konta, ajiyar zuciya ya kuma sauk'ewa cikin jin dad'i yasa hannun shi a hankali ya janye blanket d'in. ita kuwa cikin baccin taji alamun kamar akwai wanda ke tsaye a kanta, so take ta bud'e idonta kuma sai taji gaba d'aya jikin ta kamar an zare mata laka ko idon sai nauyi sukayi mata ga zafin zazzabin da takeji ga kanta da yake sarawa kamar zai rebe gida biyu. Tana cikin wannan nazarin sai taji hannun mutun a kan wuyan ta, so zuwa yanzu sai ta fara zaton ko General ne, tuno hakan sai yasa tayi shiru ta lumshe idon ta dan bata son kallon mugun fuskar da hararan ta da yakeyi. A hakan shi kuwa Mugu Abdul sai yaji k'arfin guiwar k'ara matso ta cikin k'arfi ya jawo ta cikin shi tare da sa hannu ya ruk'ume ta, tuni ya fara lumshe ido tare dasa hannu yana shafa gashin kanta. Jin haka yasa cikin tsoro ta bud'e idonta tare da diresu kan fuskar Abdul. Cikin tsananin firgici da tsoro ta bud'e baki da k'arfi tasa ihu ta kuma bud'e baki zata kuma sakin wani ihun, yayi maza yasa hannushi ya rufe mata baki, da k'arfi ya birki tata rigingine cikin tsabar rashin imani ya fara kicini yar zuge zib din rigarta ido cike da zalumci. Ita ko Meenal cikin tsananin bugawar zuciya da razani ta zazzaro ido waje sai wani irin numfashi takeyi fiddawa cikin tsanan tan rud'ani sannan tasa hanna yenta duka biyu tana k'ok'arin cire hannushi da ya rufe mata baki tare da yin zillo da cure-cure da k'afafun ta sai kai take jujjuya mai cikin rauni da zare ido alamar ya jik'anta, ina shiko mugun yayi nisa baya jin k'ira sai tsura mata ido da yayi cikin lasar lips enshi murya a sab'ule yace. "Ki nitsu ki kontar da hankalin ki nima zan biyaki ba wai a banza zanyi ba ke tunda zaman karuwan ci kikeyi me naki nan zab'en wanda zakiyi harka dashi abu na kud'i, kinga zamuyi abinmu ba wanda ya sani daga yau kuma duk randa Hamma Aliyu baya nan, ni zan kasan ce tare da ke." Ido ta k'ara zazzarowa jin irin furucin da yakeyi mata cikin rashin imani, ganin baida imani da tsoron Allah yasa tasa hannu bibbiyu ta rink'a dukanshi tako ina duka take kai mai da yagushi kamar kare, Ashiko maye azzalumi sai mak'aleta yake yi kamar biri yasa hannushi ya danne mata baki tare da matse mata kai yana ta k'ok'arin jawota jikin shi. Cikin tsoro ta bud'e bakin ta da k'arfi takoyi sa'a yatsun sa sukayi cikin bakin ta da iya k'arfinta ta tak'ark'ara ta dasa mai wani irin gigiceccen cizo, har sai da taji k'amshin yatsun suna k'as-k'as a take kuma taji alamun jiki a bakin nata. Shi kuwa Abdul cikin wani irin gigita da azaba ya fisze hannushi tare da dirowo k'asa cikin tosku yasa hannu d'aya ya rik'e kanshi d'aya hannun da ta cizan kuma sai yarfashi yake jini na zuba d'is-d'is hannun sai rawa yakeyi kar-kar sai wani irin juya kai yakeyi cikin azaba. Ita kuwa Meenal tun da ta samu ya sake ta ya sauk'a kan gadon, itama ta diro cikin zafin nama da rawan jiki a guje ta nufi parlon gudu take har taje ta sake gora kanta da jikin durowar d'akin, Amman duk da haka bata juyo ba tana gudun ceton rai sai rik'e kan tayi cikin azaba ta zund'uma ihu baki na rawa tana. "Wayyo Allah zai kashe ni Ku ceceni wayyo Anuty Aysha kizo ki tai maka min." A haka ta nufi parlon cikin azaba, shima a guje yabi bayan ta, ganin yana binta yasa cikin zafin nama ta doshi k'ofar fitan cikin rashin sa'a tana zuwa ta samu k'ofar a gark'ame yake, bugawa ta kamayi cikin k'arfi da razani sai kuka take cikin neman ceto buga k'ofar take tana juyawa tana kallon yadda ya nufota a guje gaba d'aya jikin ta sai rawa yake kar-kar numfashi ta na fuzga ga goshin ta da ta k'ara bugewa da jikin durowa tuni sai jini yake zubdawa, tana ganin ya iso gareta gashi duk ihun da takeyi da k'iran ba wani motsin taima ko sai kawai ta d'ora hannun ta a kai ta saki wani irin kuka mai cike da abin tausayi kuka take cikin azaban tsoro. Yana zuwa ya sa k'afa ya taliyeta aiko tayi k'asa gim kan tayis ihu ta kuma kurmawa cikin azaba ta fara neman taima kon Allah da kiran sunan Bappa da inna cikin azaba ta kuma kurma ihu lokacin da ya shak'o wuyan ta ya mik'ar da ita tsaye, baki na rawa tace. "Wayyo Bappa Na wayyo Abba na wayyo *Hamma Jabeer* ina kake gashi yau za'a keta min haddi Hamma Jabeer ina kake Kaine fa kayimin alk'awarin kare min mutuncina wayyo dan uwana Hamma Jabeer Yau za'a keta haddin k'anwar ka Amina shin ina kake ne?." Cikin rashin imani ya kuma k'ara shak'e mata wuya cikin zalumci yace. "Ni kika zubdawa jini a jiki toh wallahi ki sani yau sai na azabtar dake iya azaba tarwa sai na keta miki haddin da kike fad'in yau ba Jabeer zaki kira ba ko ubanki ne a nan sai na ketaki, kiyi ihu har ki mutu ba mai jinki bare ya kawo miki taima ko sai Mama ita kuwa cemin zatayi in k'ara ba rawan kai kikeyi ba in kinga Hamma Aliyu yana nan ba har zai targad'a min hannu a kanki ko? yau zan k'unsa mai bakin ciki da sai ya kusan halla kashi." Sai kuma ya zabga mata wani irin wawan marin da yasa taga tauraro mai wutsiya atake sai ga jini a bakin ta janta ya kuma yi ya hankad'ata kan 3str fad'awa tayi cikin azaba yayin da ta sake yunk'uro wa ta mik'e tana layi cikin kukan tace. "Dan Allah dan son Annabin mu ka barni kar ka cutar dani zuciya ta zata bug'an zan mutu." Mari ya kuma yarfa mata tare da shak'o wuyan ta yace. "Yau ba mai ceton ki a gidan nan dole na mu'amalan ceki dole ne." Kakari ta fara cikin zare ido da ficewar numfashi dan jin kamar kasheta zaiyi cikin wahala ta saki k'ara mai k'arfi murya a disashe tace. "Wayyo Hamma Jabeer ina kake? Wayyo Hamma Haiydar ina ka tafi ka barni, k'anin ka zai kashe ni? Hamma Haiydar kaci amanar da Bappa na ya baka ka kawo ni inda za'a kasheni Hamma Aliyu Haiydar ni kenan k'waya d'aya tak Abba na ya Haifa amman dan mahimmancin cika alk'awari ya barni na rayuwa cikin rigar Fulani gaban kakana Bappa a zaton Bappa kai mai amanane kamar Abba na shiyasa ya had'a ni da kai dan ya tseratar da raina a gun udawan da suke k'ona mana rigogi su kashemu su tafi da dabbobin mu ashe kaima inda za'a kashe ni ka kawoni?." Kukan take cikin azaban yayin da ya jawo ta da k'arfi ya han kad'ata cikin bedroom d'in ta fad'i gim a bakin gadon, shi ko mugun ya tsaya yana b'alle botur d'in rigar sa. Ganin yana matso ta yasa ta saki wani irin k'ara tare da rumtse idonta sannan ta rink'a kurma k'ara da k'arfi tana. "Hamma Haiydar! Hamma Jabeer!.." Doctor Jabeer dake zaune gaban Alhaji Ibrahim ne ya rumtse idon shi cikin wani irin mutu wan jiki da yakeji a hankali ya kalli Alhaji Ibrahim baki na rawa yace. " Abba bani number General Aliyu." Mik'a mai phone d'in shi yayi, karb'a yayi tare da d'auka number General d'in, k'iranshi yayi a take kuma k'iran ya shiga. Shi kuwa General Aliyu Haiydar tun da suka zo cikin Jaji ya wuce office nashi ya zauna ya k'asa tab'uka komi sai wani irin tsinke wan zuciya da yake ji har yaji gaba d'aya jikin shi na rawa, haka kawai kuma sai yaji kamar ana rabka mai k'ira sai kunne shi kemai dumm can kuma sai ya rink'a jin fargaba abinda ko a fagen yak'i baya jin haka. A haka ya kasa komai dole ya mik'e jiki a mace ya fitoh yana fita ya ranshi suka mimmik'e suka sara mai ba tare daya kallesu ba yacewa Captain Sani su tafi, kai tsaye gidan shi suka nufa suna zuwa Esther ta kawo musu abinci Amman sam ya kasa ci, a take kuma sai yaji hankalin shi ya koma kan Abban shi a fili yace. "Toh ko Abba name jikin shi ya tashi." Cikin kula Sani yace . "Oga ka k'ira Abban mana ai zaifi." Ajiyar zuciya ya sauk'e tare da cewa "Shawara mai kyau." Yana k'iran Abba bugu d'aya ya d'aga cikin kula yace. "Abba kana lafiya?." Dariya yayi cikin k'aunar d'an nashi yace, "Lafiya ta lau Haiydar kun isa lafiya ko?." Ehh yace mai sannan sukayi slm ajiye phone d'in yayi tare da watsar da tsinke war zuciyar da yake jin. Yana Ajiye phone din k'iran Dr Jabeer ya shigo, da fari kamar bazai amsaba sai kuma ya amsa. Suna gaisa wa Dr Jabeer yace. "Kana magana da Dr Jabeer ne yayan Captain Sani naka." "Ayyah nagane ka Doctor ." Cikin sanyi Jabeer yace. "Dan Allah General a tsanan ta nema da bincike plxx kar wani abu ya faru da matata kuma k'anwata Amina wallahi tsoro nakeji kar a cutar min da ita." Cikin sanyi da kontar mai da hankali yace. "Insha Allahu ba abinda zai sameta kuma za'a ganeta kudai ku dage da addu'a." A haka ya kontar mai da hankali sannan ya katse k'iran, bedroom ya tafi a niyanshi yayi bacci Amman kuma sai yana jin fargaban na k'aruwa amman sabida hali irin na maza sai ya share ya konta tare da lumshe idon... A gida kuwa Abdul ne cikin rashin imani yayiwa Meenal........ By *Garkuwar Fulani* [8/18, 6:26 PM] πŸ’žIt's @lh@jiπŸ’ž: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *BANDIRAWO* page 2⃣1⃣to2⃣2⃣ Na *Aysha Ali Garkuwa* πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *Resa tum, mara tum, heb'a tum, seya tum.* *Dedicated 2 my lovely sis Ummu Khamal* Pml Sai kuma yayi sauri ya sake zuge zip din, tare da mik'ewa ya nufi cikin toilet ruwa ya d'ebo cikin sauri ya dawo gaban ta a hankali ya rink'a shafa mata ruwan a fuskar ta, amman shiru sai ya kurb'i ruwan a bak'inshi ya fesa mata shi a fuskar ta da k'arfi, cikin wani irin yana yi tayi ajiyan zuciya sai kuma ta bud'e idon ta a hankali sai hawaye dake tsiyaya a idonta kuma idon suna lumshe alamun ta farfad'o amman bata dawo hayya cin taba, ajiyan zuciya ya sauk'e tare jingina kanshi a jikin ta, Shiru yayi tare da tsura mata ido ganin gaba d'aya Abdul ya kumbura mata fuska tayi jajir gashi duk jikin ta jini cikin tsoro da far gaba ya rumtse idon shi tare da kad'a kai, gaba d'aya ya rasa abinda yake tunawa bere yasan abin da zaiyi mata, Mik'e yayi ya fito Parlor cikin sanyi yana k'iran . "Aysha." Shiru ya tsaya ganin bata nan, hakan yasa ya fitoh babban parlour nasu yana k'iran Anty Ayshan , Mama ne ta d'ago jajayen ida nunta cikin tsantsar k'iyeyya da tsanar Aliyu tace. "Lallai ka dafawa kanka abinci wahala da bak'in ciki da k'uncin rayuwa kuma wallahi sai ka kwashe saka makon wannan aikin da kayi min." Bai kula taba bare ya kalle ta sai tafiyar shi yayi yana k'iran Aysha, Abba ne ya kalle shi cikin tsoro yace. " kai Haiydar zo nan." Kanshi a sunkuye ya dawo gaban Abban shi cikin sanyi ya zauna gaban shi, Ido Abba ya tsura mai ciki tuhuma yace. "Haiydar anya kuwa kai mutum ne ? anya kuwa kana da zuciyar tausayi ? anya ko Haiydar kana tsoron aika ta kisan kai ? shin ka manta nan ba fagen yak'i kakeba ? kana sane d'an uwanka ka kashe? wannan wanne irin rashin imani ne?." Kanshi a sunku ye yace. Abba kuyi hakuri kai da Daddy Ku gafar ceni ." A fusashe Abba ya rink'a zuba mai maruka tare da sakin kuka yana marinshi da tureshi yana kuka yana cewa. "D'an, d'an uwana ka kashe a gaban mu wai kuma kana cewa muyi hak'uri kai wanne irin zuciya ne da kai mugun zuciya ko?." Kai kawai yake juyawa tare da rawan murya yace . "Abba ban kashe shiba ni hukun ci na d'auka a kanshi Abba kasan abinda Abdul yayi kuwa?." Sai kuma ya mik'e cikin sauri, Part nasu ya shiga yana zuwa ya ruggumo Meenal a jikin shi ya fitoh da ita yana zuwa kan 3 str ya kontar da ita yayin da Abdul ke shimfi d'e a k'asan 3 str, cikin rawar murya Aliyu ya kalli Abba da Daddy yace. "Abba kuga abinda Abdul yayiwa y'ar mutane ga yadda ya sauya mata kamannni haddin ta yaso ketawa ganin tak'i bashi fad'in kai yasa ya rink'a dukan ta kamar zai halla kata yaci zara finta yaso ya keta haddin Aure dana shariyar musulmai yaci zarafin mace mai rauni, amman dan na d'auki mataki kan laifin daya aikata shine gaba d'aya kuka k'asa ganin illar abinda yaso aika tawa, ita baku ga halin da yasa ta a cikiba ko dan ita ba y'arku bace Abba yanzu da Nafeesat aka yiwa haka ya zakaji wanne matakin zaka d'auka kalli fa yadda ya fasa mata kai ." Gaskiya dai koya take d'aya ce dai kuma a fili take, gaba d'aya sai jikin su ya mutu sukayi shiru dan tabbas da y'arsu aka yiwa haka hak'ik'a suma zasuyi abinda Aliyu ya aika ta. Ya Amir ne yayi magana cikin sanyi yace. "Wannan zaman baida amfanin mu tafi asibiti dasu yafi." Kai Aliyu ya girgiza tare da cewa . "Kar akai Abdul asibiti." A fusace Mama tace. "ai dole kace kar a kai kashi asibiti mugun uban mugaye wato a barshi ya mutu toh wallahi alhak'in mutuwar sa a kan wuyan ka, banza mai zuciyar fir'auna." Tsaki yaja tare da cewa . "Oho ba dole, in kuna so kuje asibitin ayi ta yad'e farar jikin shi kullum safe da yamma daga nan su nak'asa miki d'a ni wallahi ba ruwana." "Allah ya fika aniyar ka ta koma kanka." Mama ta fad'i cikin tsana. Shi kuwa Aliyu sake daukar Meenal yayi ya maida ta dak'i ya kwantar da ita sannan ya koma kitchen d'in su ya bud'e fridge ya d'auko goran zam-zam mai sanyi, Parlon ya dawo inda ya samu Abdul ya farfad'o sai jujjuya kai yake cikin wahala dan abi yafi gaban kuka bare hawaye. Gefen shi ya zauna cikin kula yace. "D'azu na d'auki hukunci ne a kanka a matsayina na Jami en tsaro mai kare al'ummar k'asar sa, ban hukun taka dan mugunta ko san kaiba na hukun taka kan kaso ka cutar da yarinyar da bata san komai ba kuma na tsaya matane na d'auka mata fansa dan nine kad'ai dalilin zuwan ta garin nan sannan dan nine madadin Uwa da uba a gareta kuma amanarta aka bani, yanzu kuma zan jinya ceka a matsayi ka na d'an uwana jinina, sannan ita kuwa zanci gaba da kula da ita da kawar da duk wani abin da zai cutar da ita a matsayin ta na wacce aka bani amanarta kuma y'ar k'asata kuma mace mai rauni, ka kiyaye gaba ko kallon kirki banson kayi mata bare kallon banza bare ta kai ga kayi niyar cutar da ita , In kuwa kak'i ka goda hmmm zanyi abin da yafi haka." Shi kam Abdul kai yake juyawa cikin wani irin numfashi da nishi sai zare ido yake da damk'e hannushi zufa na keto mai tako ina. Shiko General k'ara matsoshi yayi cikin sanyi ya bud'e marfin robar zam-zam d'in sannan ya saiti inda ya tsulala mishi mayin gyadan ya rink'a zuba mashi zam-zam mai sanyin. Hak'ik'a zam- zama rahama ne, a take Abdul yaji wani irin sanyi na ratsa shi zafin na reguwa sanyin yake ji har cikin ranshi, gaba d'aya kuma k'unan ya fara komawa dan da har ya fara tasowa, (Zam-zam kenan maganin k'unan wutane duk tsananin sa koda ya tashi matuk'ar aka sa zam-zam insha Allah zai koma kuma duk zafin da k'unan ya keyi ana zuba zam-zam sanyi zaiyi), duk cure-curen da Abdul keyi a take ya lafa sai ajiyan zuciya yake sauk'ewa lokaci d'aya baccin sauk'i ya k'washeshi. Mik'ewa Aliyu yayi cikin ajiye robar zam-zam d'in a gaban Mama yace. Gashi a rink'a bashi yana sha kuma ya rink'a amfanin dashi insha Allah nan da 1 week zai samu sauk'i". Harara ta watsa mai shiko bai kulata ba ya wuce part din su . Har yanzu Meenal a konce take cikin zubda k'ollah ganin kamar bacci take yasa ya shiga toilet al'wala yayi dan jin an fara k'iraye-k'irayen sallah yana fita masallaci ya wuce tare dasu Abba da ya Amir. Ita kuwa Meenal yana fita, ta fara motsi cikin tsoro ta fara kuka tana k'iran. "Hamma Aliyu kazo d'an uwanka zai kashe ni zai keta min haddi." Anty Aysha ce ta shigo da gudu jin kukan nata gashi ta ga fitar Aliyun, tana shiga bakin gadon ta zauna cikin sanyi ta dafa kanta tace. "Meenal kiyi shiru ki kontar da hankalin ki Hamma Aliyu yazo ya ceceki, har abada Abdul bazai sake gigin yi miki komai ba bud'e idonki ki gani nice Anty Aysha ce a kusa da ke." cikin kukan ta bud'e , tana ganin Anty Aysha ta k'ara sakin kuka murya na rawa tace. "Anty Aysha kaina wuyana guiwata duk ciwo suke min." Kanta ta shafa cikin tausayawa tace. " bari in had'a miki ruwan zafi kiyi wonka insha Allah zai bari." Ruwan ta had'a mata mai zafi sannan ta dawo cikin d'akin cikin kula tace. "Meenal tashi kije kiyi wonkan ko." Cikin k'arfin hali ta yunk'ura tare da cije lips d'inta ta mik'e ta tsaya. tana tsayuwa wan ta saki wani irin k'ara tare da yin k'asa zata fad'i tana. "Wayyo guiwata." da sauri Anty Aysha ta taimaka mata tare da rik'e ta gam sannan tace. "Sannu Meenal Allah zai saka miki, daure muje kinji ko?." Kai ta gyad'a mata sannan cikin d'ink'isawa da taima kon Anty Aysha taje tayi wonka ta canza mata kaya sallah ma sai a zaune tayi dan k'afar ta cije ga kanta dake sarawa tana idar da sallah Anty Aysha ta kawo mata abinci, amman sam ta k'asa cin tana zaunen sai kanta ke tsuke ga guiwar dake mata zogi, suna cikin haka General ya shigo tare da Captain Sani samun ta a zaunen yasa Captain Sani farin ciki shi kuwa General sai cewa yayi. "Kici abinci kafin doctor yazo ." Kai ta girgiza cikin zubda k'ollah tace. "a a ni bana son wani doctor yazo sabida su sai suce sai sunmin allura wallahi ni bana so." Tsuke fuska yayi tare da cewa . "Toh a haka zaki zauna da ciwon.?" "A a ni dai a barni zai worke." "Toh kici abincin in bakya son Dr yazo." Kai ta karya cikin sanyi gonin tausayi tace. "Toh kacewa Dr kar yazo." Murmushi Captain Sani yayi tare da zaro phone d'in shi ya k'ira doctor Jabeer cikin sanyi yace. "Broz ka bar zuwan ma kawai dama kaima kace baka jin dad'i kuma matar ogan ma tace ita batason allura." Toh kawai Dr Jabeer yace sannan ya katse k'iran. Ita kuwa Meenal cikin zubda k'ollah ta d'an cin abinci sannan tace bacci takeji . Cikin tsurawa Aysha ido tace. "Anty Aysha zan konta." Matso ta tayi tare da talla fa mata ta d'aga ta amman sun k'asa dan yanzu k'afar ta k'ara tsani gashi yanzu a k'asa dirsham take d'azu kuma a kan gado take. Ido Aliyu ya zuba musu ganin sun tsaya suna haki ita kuwa Meenal sai hawaye take da cike lips d'inta, cikin sanyi yace. "Aysha barta bazaki iya ba." Ita kam Aysha sai ta koma gefe tana kallon Meenal Captain ma ido ya zuba musu. Shiko General matsota yayi tare da sunku yowa zai d'aga ta. Ganin haka yasa Aysha da Captain suka fice suna cewa. "sai fa safe," Ita kam Meenal ido ta tsura mai ganin ya d'aga ta cid'ac kan gadon ya kontar da ita ba tare d'aya kalli fuskar ta ba sai tsuke fuska da ya k'ara yi, blanket yaja ya d'an rufeta sannan ya juya ya shiga toilet zai d'an watsa ruwa. Ita kuwa Meenal tana konciya ta lumshe idon sai bacci , tana fara baccin sai ta fara ganin abinda ya faru da rana cikin mafar ki, a firgice ta rink'a kuka cikin mafarkin tana . "Hamma Haiydar zai kashe ni." Yana jin muryar ta ya jawo towel da sauri ya d'aura jikin shi har tsuma yake ya fito, yana zuwa ya sun kuyo kanta cikin d'aga murya yace. "Ke ki nitsu ba komai ki bud'e idon ki ba abin da zai sameki ganin anan." Idon ta bud'e a firgice sai zazza resu takeyi tuni zufa tafara tsatstsafo mata, sai binshi da ido tayi shi kuwa juyawa yayi tare da cewa. "Kiyi baccin ki insha Allah ba abida zai same ki." Ita dai a firgice take shiyasa sai binshi da ido takeyi. Shiko 3qtr da bes ya d'auka ya fita parlour a can ya kimtsa sannan ya koma cikin bedroom , fuska ya tab'e ganin ta kuma komawa bacci. Parlour ya dawo ya zauna yana shan tea saiga Captain Sani ya shigo da ledan magunguna dan yaje yayiwa Dr Jabeer bayani ciwon nata shine ya bashi magungunan ya kawo mata, yana bashi magungunan ya juya ya tafi, shiko yaci gaba da shan tea d'in,. Ita kuwa Meenal Abdul d'in ta kuma gani cikin farki cikin tsoro ta fara tirje-tirje tare da sakin ihu tana k'iran Hamma Aliyuuuuuuuu. A firgice General ya nufi cikin d'akin yana shiga yaja wani irin dogon tsaki ganin baccin take tana kuma ihu da tirje-tirje, kanta ya matso cikin fad'a yace. "Ke da Allah kin toshe min kunne ya isa haka kin zauna kina ta zunduba ihu cikin dare." ai ita batama san yana yiba kukan take tana. "Wayyo Bappa na Hamma Aliyu ya cuceni ya kawoni inda za'a keta min haddi d'an uwanshi zai kashe ni wayyo Hamma Haiydar Abdul zai kashe ni." Ganin tuk'uru tara mashi jama'a zatayi yasa ya sunkuyar yo kanta tare da d'an d'aka mata mari . aiko cikin gigita ta saki k'ara tare da mik'ewa a firgice da kid'ima zata gudu ta hanka d'ashi har saida ya fad'a kan gadon, ta juya zata gudun ne yasa hannu ya kamo hannu ta ya fizgota jikin shi da k'arfi cikin maida numfashi ya ruggume ta cikin faffad'an k'irjin shi sannan ya kuma...... By *Garkuwar Fulani* [8/18, 6:26 PM] πŸ’žIt's @lh@jiπŸ’ž: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *BANDIRAWO* page 2⃣3⃣to2⃣4⃣ Na *Aysha Ali Garkuwa* πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *Kinkid'i kankad'a d'amoni na d'amoni gidd'o mo fina laramo, gaid'omo fina sukoyo ladde Allah yamad'um, πŸ’ƒπŸ» shakka wala 🌲 yoriki tenete ki b'ibb'e sammete b'end'uki yamete ki d'oidi yalete...........* Pml Matseta da kyau tare komawa jikin kan gadon ya jingina , ita kuwa sai tuttureshi takeyi tana fizge kanta ganin tak'i nitsuwa ne yasa shi, k'ara matseta gam a jikin shi kanshi ya sunkuyar dai-dai kunne ta a hankali ya fara hura mata iska a kunne tare dasa hannu shi d'aya yana shafa bayan ta zuwa kanta , jikinta tad'an saki tare da murza kanta, shi kuwa cikin muryar lallashi ya fara magana a hankali. " Meenal ! Meenal kiyi shiru ki nitsu gani gaki Hamma Haiydar ne a kusa dake ba Abdul bane gani nazo ina kusa dake Abdul bazai cutar da keba." Shiru tayi cikin sauk'e numfashi da lumshe idon a hankali ta k'ara sakewa a jikin shi hannu ta tasa ta zagayo k'ugunshi ta rik'eshi gam , Ido ya lumshe tare da shafa bayan ta ya gyara mata konci yarta a jikin nashi , ita kuwa kanta ta kuma murzawa a tsakanin wuyanshi da kafad'ar sa bakin ta na dai-dai kunne shi cikin sanyi ta fara magana. "Hamma Haiydar ka maida ni gun Bappa na." "Me yasa kike so in maida ki gun Bappan?." cikin baccin da ya fara d'ibar ta tace. "Hamma Haiydar Abdul zai kashe ni ina tsoron shi ." Gyara konciyan sa yayi tare da tallab'e kanta cikin sanyi yace. "Gani a kusa dake ba abin da Abdul zai miki bazan sake barin wani abu ya cutar da keba kinji ko Minalin Hamma Haiydar?." Kai ta gyad'a tare da lumshe ido cikin gigin baccin ta rink'a k'iran shi. "Hamma Haiydar!" "Na'am ." "Hamma Haiydar." "Na'am Minalin Hamma." Sake k'iran shi tayi a karo na 3, Murmushi ya d'anyi cikin sanyi yace . "Na'am ." Haka tayi ta ki ranshi yana amsa mata har bacci ya d'ebesu baki d'aya....... 4:40 Am General ya farka cikin sanyi ya bud'e idonshi, cikin kunya da tsuke fuska ya zameta gefen shi sannan ya mik'e yana tab'e fuska, al'wala yayi sannan ya nufi masallaci ita kuwa yana fita bada jimawa ba ta farka cikin tsoro ta sauk'o kan gadon , sai kuma ta saki k'ara tare da dafe gini ta tsaya dn azaba gaba d'aya k'afar ta rik'e tayi zafi amman bai kai na jiya ba sai dai goshin ta ne kam k'ara kumbura ma yayi, cikin dauriya da dafe gini ta d'ink'isa ta shiga toilet, tana shiga ruwan zafi ta had'a mai zafi sosai sannan ta dunk'ule d'an kwalin ta ta rink'a tsomawa cikin ruwan zafin tana d'an dannawa kan guiwar tata sai rumtse ido take dan zafi amman a haka ta daure taci gaba da gasa guiwar har ta daina jin zafin, goshinta ta goda gasawa amman ta kasa sabida zafin shi yafi na guiwar dan shi goshin kusan sau 4 yana goruwa, haka ta bari tayi wonka fuskar ta ko sai sabulu ta d'an shafa, tana fita dogon wondo tasa d'an tsukekke sannan ta zura duguwar riga yar cas da ita , kan sallaya ta tsaya bayan ta zura hijabi a jikin ta, sallan tayi cikin wahala dan in tayi sujjada kamar ta kurma ihu, haka dai tayi sallan sannan tayi fara karatun azkar , tana shafawa ta koma bakin gado ta konta, cikin jin ciwon kai d'in sai hawaye da ke bin fuskar ta. Dr Jabeer kuwa tun wunin jiya yake cikin fargaba da tsinkewar zuciya ya kasa samun sukuni gaba d'aya hankalin shi ya koma kan Aminan shi , a haka ya wuni cikin far gaba ko abinci ya kasa ci , dere nayi wani sanyin zazzab'i ya fara ratsa shi hakan yasa da wuri ya konta bayan yayiwa Uncle saida safe , konci yayi amman ya kasa bacci, daya rumtse idon shi sai , Fuskar Meenal yake gani cikin halin damuwa ga zazzab'i ga rashin konciyar hankali haka tasa ya mik'e yayi al'wala ya fara nafilfili yana nemawa Meenal d'in shi tsari daga dukkan abin cutarwa tsakanin mutum da aljan' haka ya kwana kan k'afafun shi har sai 4:42 ya tafi masallaci , Bayan anyi sallan Asuba an idar Alhaji Ibrahim ya shaidawa liman akwai d'aurin auren da za'ayi , hakan yasa liman ya tsaida mutane daga fita masallaci ya shaida musu akwai d'aurin aure yanzu nan, Shi kuwa Dr Jabeer labarin d'aurin auren ya sama mashi kuzari kad'an tunda yau za'a malla kamishi Amina a matsayi matar sa shiko yayi alk'awarin jiran ta koba dad'e koba jima zai jirata kuma yanzu ya fara k'aunar ta da nemota dan gani yake duk jami'an tsaron nan na banza ne ba gano mai ita zasuyi ba. Cikin sanyin safiya da sa'ar dake ciki aka d'aura auren Amina Ibrahim mai dala (Meenal ) tare da Doctor Jabeer Muhammad kan sada ki dubu 50 tare da shaidawar dubban al'ummah dake rayuwa a ugguwar tasu da kuma yawun Malam Salisu Abduljalal limamin masallaci kenan ... Bayan sun koma gida,. hajia Aysha tare da Hajia Amina basu yi mamaki abinda ya faruwan ba dan sun san Alhaji Ibrahim mai dala kaifi d'aya ne in yace ehh tofa ehh d'inne sannan in yayi alk'awarin toh da izinin Allah sai ya cika, shi kuwa Dr Jabeer cikin happy ya rink'a gayawa abo kanshi. Alhaji Ibrahim ne zaune a d'akin shi , Hajia Aysha tayi sallama cikin sanyi taje ta zauna a k'asa kan carpet kusa da k'afafun shi kanta ta jingina jikin gadon cikin sanyi ta kalleshi ya zauna ya dafe kanshi da hannu bibbiyu sai hawaye da ke bin fuskar sa , kanta ta sunkuyar yar cikin tausayawa kanta da mijin nata murya na rawa tace. "Alhaji kayi hak'uri ka daina zama cikin irin wannan halin wannan yarinyar Allah ne ya bamu ita kuma ya fimu sanin yadda muke sonta da k'aunarta kuma shi ya b'oye mana inda taken da halin da ta shiga, dan Allah kabar kukan nan mu fawwalawa Allah lamarinsa muci gaba da yimata Addu'a Allah ya baya nar mana da ita ya kuma kare mana ita a duk inda take Allah yasa tana hannun nagari." Kai ya sunkuyar cikin rawan murya yace. "Aysha Amina itace kad'ai y'ar da Allah ya bani ban rayuwa da ita wurin d'aya ba dan nayiwa Bappa alk'awarin na bar masa ita gashi tashi d'aya Bappa yace an d'auke ta an tafi da ita kinga ko, ko nace bazanyi kuka ba nayi k'arya." Shiru tayi tana tunanin ko ta gaya mishi gaskiya tunda ita tasan gaskiyan maganar. Lokacin da suka je Membila kamar yadda suka saba su duba yarsu su kawo mata duk wani abin buk'ata na rayuwa, Hajia Aysha tana shiga cikin gida Lari kishiyar Inna tana ganinta ta kwashe da dariyar mugun ta, harda ker keta Hajia Aysha kam tsoro ne ya rufeta matuka dan tasan Lari bata dariya sai abu ya b'aci , gashi Lari irin mutanen nanne masu bak'in abu a kan harshensu wanda in sunyi furucin yakan iya aukuwa wanda a musulunce ake ce musu masu kambbun baka, tabbas kuwa mun san kambbun baka gaskiya ne, toh hakan da Lari ta gane sai take bin kishiyar ta da yarta da jikarta da mugun baki. Ita kam Hajia Aysha a firgice ta shiga d'akin Innarta, halin da ta samu Innar a cikine ya bata tsoro, cikin firgici da kulawa ta matso kusa da mahaifiyar tata wace tun randa Bappa ya d'aura Aure Meenal da General suka kuma tafi tare tun wannan ranan take kuka cikin k'unci da tsoro halin da jikarta zata shiga gashi tana tuna wanne hali Alhaji Ibrahim zai shiga ciki ga tausayi yawa y'artan, cikin kuka ta rik'e hannun Hajia Aysha tana bata labarin yadda abin ya faru , haka yasa gaba d'aya suka riccab'e da kuka suna cikin kukan Bappa ya shigo gefen Hajia Aysha ya zauna cikin zubda k'ollah yace. "Ki gafar ceni Ayshatu banyi haka dan cutar da Bodd'ina ba nayi haka ne dan na kare mutuncin ta na tsera tar da ita daga hannayen udawan nan da suka addabi Fulanin Gembu Membila su kashemu su sace mana yaran mu mata su kora dabbobinmu suna zalum tarmu gomnati ta sani bata d'auki mataki a kaiba sun maida mu tamkar bayin su! ko mu fulanin daji wanda ke bin shanaye da zamanrugogi bamu da hak'k'ine kan shuga banni mu ? ko dan mu a dazuka muke zama ? shiyasa ma zauna cikin birane basa tausaya mana ? basa kula matsalar mu ? ko mu ba raine da muba?." Sai kuma yayi ta zubda k'ollah cikin cewa ban san me zan cewa Alhaji Ibrahim ba akan rashin y'arsa ince mai na Autar da ita ga wani bak'on da yazo mukayi kwana d'aya tan da shi?." Cikin kuka Hajia Aysha ta rink'a girgiza kai murya a disashe tace. "a a Bappa kar kace mai Autar da y'ar shi kayi ga wani wanda baka saniba in yaji haka zai ga kamar baka damu da y'ar shi bane zaiga kamar sakaci kayi da ita Bappa kawai muce mai dauketa akayi mu kuma cemai jami'in tsarone suka d'auke ta , daga nan in mun koma a zuba masu neman ta har Allah yasa a gane ta." Da fari Bappa yak'i yarda da wannan tsarin, toh ganin yadda ita Aysha take tsoron fuskar tar mijin ta da maganar yasa dole ya yarda , a ranshi kuma yake tunanin ya tabbata wotaran Aliyu zai dawo da Meenal daga nan sai ya cewa Alhaji Ibrahim jami'in tsaron d'aya tafi da ita ya dawo da ita.. haka suka gayawa Alhaji Ibrahim yayi kuka har ya godewa Allah. ( toh kunji fa dalilin dayasa Alhaji Ibrahim bai san Aure aka yiwa y'ar shi ba sannan ya kuma d'aura mata wani auren, yake kuma ganin shi sace mishi y'arshi akayi.. Shiru Hajia Aysha tayi tuno yadda sukayi da iyayen ta kawai sai ta kasa fad'a mishi gaskiya dan tana tsoro zaice ta muna furcesa haka suka zauna sukayi ta kukan su .... General Aliyu kuwa tunda aka idar da sallan asuba jikin shi a mace ya dawo gida, cikin sanyin jiki ya zauna a parlour tare da lumshe idon shi ya resa wanne yanayin ya kaji, yana cikin hakan yaji sautin muryar Minalin Haiydar tana kuka k'asa-k'asa kamar bazai ta shiba sai kuma zuciyar shi ta kasa daurewa ya mik'e jiki a mace ya shiga d'akin.. Gefen gado ya ganta zaune tana kuka dafe da kanta, matso ta yayi cikin sanyi yace. "Meenal meke faruwa?." Kai ta d'ago cikin zunda k'ollah tace. "Hamma Haiydar." Sai kuma tayi shiru cikin k'arin macewar jiki ya kalleta dan duk duniya mutum biyu ke ki ranshi da Haiydar Abban shi sai Ammin shi da ta guje shi sai yanzu kuma da yaji Meenal na ki ranshi da sunan. Murya a sanyaye yace. "Meenal me kike so? meke damun ki?." Cikin kuka tace . "Kai na Hamma Haiydar kaina zai fashe." Ido ya tsurawa goshin nata tare kama lips d'inshi na k'asa yana tsotsa . Jin taci gaba da kukan yasa ya d'an sunkuyo kanta hannushi na hagu yasa ya tallabe k'eyarta sannan ya d'aura tafin hannun shi na dama kan goshin nata ya danne tare da fara murza wurin, cikin azaba da gigita ta rik'o hannayen shi tare da sakin kuka mai cin rai tanayi tana janye hannayen shi, shi kuwa k'ara dirza wurin daya kumburan yakeyi dan ya samu ya bace, cikin sakin k'ara da k'arfi ta sank'alo wuyanshi tare da komawa baya zata k'wace kanta , aiko cikin rashin kuzari ta fizgo General sai gashi ya fad'o kant........ By *Garkuwar Fulani* [8/18, 6:26 PM] πŸ’žIt's @lh@jiπŸ’ž: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *BANDIRAWO* page 2⃣5⃣to2⃣6⃣ Na *Aysha Ali Garkuwa* πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *Tabbas wannan babu shakka (MOH ALLAH WUJI FURD'ATA, MOH ALLAH HOKKI B'URI MOH BABA HOKKI)* Pml Kanta cikin wani irin sanyin jiki da jini ya mirgina gefe tare da konciya rigin gine kanshi na kallon saman d'akin yayin da k'afafun shi kuwa ke reto a kasan gadon hannu shi d'aya kuma yana kan cikin ta, so yake ya d'auke hannushi daga kanta amman ya kasa kuzarin shi duk ya tafi dan dama tun sanyin safiyar yake jin kasala ba abin da ke aiki a jikin shi sai zuciyar sa dake harbawa idon shi ya lumshe cikin sauke ajiyan zuciya daga nan ya kasa ko motsi mai k'arfi , a cikin ranshi kuwa sam bawai jin dad'in wannan yana yin yakeba gaba d'aya ya resa me kemai dad'i. Ita kuwa Meenal shiru tayi tare dasa hannu ta rufe kan goshin nata zuwa kan idon ta sai hawaye dake bin fuskar ta sam ita bata san hannushi na kanta ba dan zafin da kanta ke mata shiyafi komai a gareta hawayen take zubdawa tare da fara sheshahekan kukan. A hankali ya fara jin sautin kukan ta mai sanyi wanda sai in mutum ya kasa kunne zaiji, shiru yayi tare da murza yatsatsa ma nunuyiya da babbar yatsarsa a hankali ya fara jin kuzari idonun shi yake son bud'ewa amman sunyi mishi nauyi dole ya k'ara lumshe idon cikin sauk'e ajiyar zuciya sannan ya tattaro sauran kuza rinshi ya mirgino ya juyo ya konta gefe d'aya yayin da fuskar sa ke fuskantar ta, cikin k'arfin hali ya bud'e idon a hankali sannan ya tsura mata idon yana kallon ta, ganin kukan take tayi, cikin sanyi yasa hannun shi ya jawo nata ta mirgino ta fuskan toshi suna kallon juna har hancin General na tab'a goshin ta , cikin sanyi ya bud'i baki tare da cewa. "Meehnarl." Ido ta bud'e tare da tsurawa bakin shi ido, shi kuwa gashin giran ta yake kallo jin bata amsaba yaci gaba da cewa. "Meenarl kiyi hak'uri ki daure kinji ko murza miki wurin zanyi in kin daure na murza shi sau d'aya dai zai b'ace gacan magungunan ki nasha dana shafa insha Allah zai bari kinji ko?." Rau-rau tayi da ido cikin zubda k'ollah ta tura baki tare da cewa. "Hamma Haiydar zafi nake jifa" Numfashin ya sauk'e tare da cewa. "zan miki a hankali kinji ko." Idon ta d'an d'ago ta kalleshi cikin tsoro da d'an zare ido tace. "A hankali sosai fa?." lumshe idon yayi tare da d'aga mata gira d'aya. kai ta juya tare da tsuke bakin ta tace. "A a ni ka amsa min da baki." Yunk'uri yayi ya zauna tsakiyar gadon tare da nad'e k'afafun shi yana fuskar tarta yasa hannu ya kamo hannun ta d'aya ya jawo ta zaune itama ta nad'e nata k'afan ya zama suna fuskantar juna kusa da kusa cikin muryar da tafi kama da mai yin rad'a yace. "Ehh a hankali zan miki, Amman kar na fara ki fara kuka ko ki tureni kisa nima na fad'i na fasa kaina." Cikin d'an tsoron dai tace toh . "Da hannu d'aya zakayi kar tare min kaina da d'aya hannun." Fuskar ta ya d'an kala a fizge sannan yace . "Toh matso." Matso shi tayi har guiwar ta tana gogan nashi sai kuma tana yarfa hannu alamun tsoro. Shi kuwa mamaki yake irin wannan raki da tsoro ga shegen mita duk ita d'aya, hannushi ya d'ago zai kai kan goshin nata , ita kuwa sai kawai ta sa hannu ta kamo hannun nashi yasunta tasa cikin tafin hannushi ta matse tana. "Wayyo zafi wallahi tsoro nake ji." Shi kam General Aliyu shiru yayi tare da tsurawa hanna yensu dake had'e wurin d'aya ido ko k'eftawa ya kasa sai kallon ta yake yadda ta dage tana murza mai tafin hannushi, ganin yayi shiru yana kallon hannun ta yasa tayi k'asa da kanta cikin sanyi ta zare yatsunta daga nashi hannun, sai ta d'an d'ago kan ta tura mishi tare da cewa. "Ayyah Hamma Haiydar a hankali fa." Gira d'aya ya sake d'aga mata sannan ya d'ago hannushi ya manna kan goshin nata , ido ta lumshe tare da yarfa hannu tana. "Shiishhhh wayyohhh." Cikin sanyi da sanyin tafin hannun nashi ya fara goga k'ulun goshin nata, ita kuwa tuni sai hawaye da shan yaji take sai shishita takeyi , jin yana murzawa da d'an k'arfi sai kawai tasa hannayenta ta rarumo cinyoyin shi ta rink'a damk'ewa da yamutsa shi tamkar mai yi mishi tausa, Sai ta matse cinyar sa tace. "Hahhhhhhyi shihhhhh wahhyi Hamma Haiydar zafi." Shi kuwa sai sauk'e ajiyar zuciya yake yana ce mata. "Oh sorry Minali kiyi hak'uri daure kinji ko? saura kad'an." Kuka ta kara saki jin k'ara murza wurin yake sai ta fara fizge kanta tana yin baya, shiko ganin haka yasa shi d'ago hannushi ya tallabe k'eyanta dan ya murza wurin da kyau, ita kuwa jin haka yasa ta k'ara matse cinyoyin shi cikin zafi da kuka tana . "Wayyo Hamma Haiydar zafi." Bai kula taba sai murza wurin yake, Cikin zafin tayi yunk'uri ta afka kanshi cikin k'irjin shi tasa kanta sannan tasa hannu ta zagaye k'ugunshi ta k'amshin k'am jikin ta sai kuma ta saki kuka . Shiko General wani irin numfashin ya furzar tare da rumtse idonshi sannan ya gyara zaman shi tare da sa hannushi a kan bayan ta yana shafawa a hankali cikin yanayin lallashi tare da cewa. "Gud gerl sannu ko Meenarl kinyi k'ok'arin sannu kiyi shiru ya isa bazan k'ara murza wurin ba ya b'ace kinji ko." Ita kam shiru kawai tayi tana jin kan goshin ta yana zut-zut lafewa tayi a jikin shi, shi kuwa shiru yayi ba tare da tuna komai ba. A haka har zuwa d'an wani lokacin sannan ya janye jikin shi tare da tureta gefe ya mik'e ya nufi parlour ba tare daya juyo ya kalleta ba. ita kuwa madubin jikin kan gadon ta juya tana kallon fuskar ta, murmushi tayi cikin goge k'ollan fuskarta taji dadi kumburin ya b'ace. Shi kuwa yana fitawo parlour da niyar zai kira Captain Sani yazo ya ai keshi ya samowa wanna yarinyar abin da zata ci, yana fitowa parlour ya samu kulolin abinci da filas wanda Anty Aysha ta kawo, kan kujera ya koma ya zauna cikin tsuke fuska da d'an d'aga murya yace. "Meenarl ." shiru bata amsaba, "Meenal" ya kuma kira a karo na biyu. Tana jinshi ta mik'e da sauri ta fito parlour, cikin sanyi tazo gaban shi ta d'an zauna gefe, fuska ya kuma tsukewa sannan yace. "Zauna kici abinci." Shiru tayi tare da sunkuyar da kai , A d'an fusace ya tura mata kulolin sannan yace. "Kici nace ko." Ganin yadda ya murtuk'e fuska yasa ta jawo filas d'in cikin sanyi ta zuba d'an ruwan tea a cup sannan tasa a baki tana d'an sha a hankali, har tashanye sannan ta ajiye cup d'in tana kallon idon shi, shiko ledan maganin ta ya jawo sannan ya b'alli d'aya ya mik'a mata, ba musu ta karb'a tare da tsiyayo tea d'in ta had'iye maganin a haka yayi ta bata da k'waya d'ad'd'aya tana had'iye maganin da tea , shi kuwa mamaki yake yadda take shan tea kamar ruwa duk da dai na yanzu kam shan dolene. Mik'ewa yayi rik'e da wani d'an farin roba gabanta yazo tsuguna sannan ya bud'e robar ya lakato maganin ya rink'a shafa mata a goshin nata, yana gamawa ya mik'e tare da cewa . "Zo ki konta kiyi bacci." Baki ta d'an tura sannan tace. "Toh" Haka kamar dole ta konta , shi kuwa wonka yaje yayi sannan ya fito parlour ya kimtsa ya fito tsab cikin bedroom d'in ya koma gaban mirror ya tsaya tare da fesa turare, har ya juya zai fita sai kuma ya dawo bakin gadon cikin tsurawa fuskar ta ido, baccinta take cikin takurewa wurin d'aya kamar maijin sanyi, kai kawai ya girgiza sannan ya jawo blanket ya rufeta, ya juya ya fita. Parlour Mama ya nufa cikin tsuke fuska sallama yayi tare da tsayuwa bakin k'ofar, cikin tsana ziryan a idon Mama ta kalli ya Amir da ya amsawa sallaman General d'in , shi kuwa Abdul rumtse idonshi yayi cikin jin tsanar d'an uwan nashi wanda a halin yanzu baida burin daya wuce daukar fansa . Shi kuwa a tsaye ya mik'awa ya Amir hannu suka gaisa sannan ya kalli Mama fuska a d'an yamutse yace. "Ya Abdul da jiki." "Ban saniba mugun d'an gidan mugaye wallahi a jutyi zuwa rafi dai tabbas wata ran tulu zai fashe wallahi tabbas akwai ranar nadama." Baki ya tab'e sannan ya juya ya fita. Yana fita ya Amir ya mik'e yabi bayan shi suka fitoh tare suna fita ya kira Captain Sani akan zasu biya gidan Alhaji Ibrahim su karb'i pictures d'in yarshi da aka sace d'in su rik'e dan pictures d'in zasu tai maka daga nan kuma zasu wuce Jaji. Suna shiga gidan Alhaji Ibrahim Captain Sani yana gaba General yana binshi a baya, a dai-dai bakin k'ofar General yaci karo da..... *Kuyi hakurin da wannan sisters* By *Garkuwar Fulani* [8/18, 6:26 PM] πŸ’žIt's @lh@jiπŸ’ž: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *BANDIRAWO* page 2⃣7⃣to2⃣8⃣ Na *Aysha Ali Garkuwa* πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *YELAN BANDIRAWO MA KHAIRUJI NUMIN BANDIRAWO MA KHAIRUJI WANNU BANDIRAWO MA DO'A KHAIRUJI, TOH ALLAH JAB'I A LARAI KHAIRUJI D'ER HABARUJI KHAIRU HAMAD'A BE BANDIRAWO MAD'A TO EN NUMI ENFU EN BANDIRAB'E* Pml Da wani dan saurayi wanda bazai wuce sa'an Abdul ba cikin wani irin yanayi yaron ya zubawa General ido tare da mamaki cike a ranshi, shima General d'in kallon yaron ya d'an yi cikin mamakin wannan abu sosai yake mamaki bin yaro yayi da ido jin yadda yaron ke magana. "Ayyah sannu ban lura da kaiba ne." Ido ya runtse cikin son tantance kalan muryan yaron wanda gaba d'aya ya tsaya mai cikin rai, ganin shiru su duk ba wanda ya kuma magana sai budurwar dake bayan d'an saurayin tayi magana cikin kallon General. "Kayi hak'uri bandirawo." sai ta kuma kallin Saurayin wanda ke bin General da ido kawai tace, "Ramadan mu tafi kaga lokaci na tafiya fa." Saurayin da ta Kira da Ramadan ko, sai ajiyan zuciya ya sauke tare da yin murmushi ya shafa sajenshi sannan ya nuna fuskar General ya kuma nuna tasa fuskar, sannan ya matsa gefe tare da jan hannun budurwar nan yace. "Zo mu tafi Husaina ta." Janta yayi suka fita ta gefen General ita kuwa sai yarfe hannu tayi tana cewa. "Can tafi da yawar ka wallahi ka dena kirana Husaaina inba haka nima na rink'a cema Hassan d'in ka." murmushi yayi tare da kamo hannun ta yace. "Na bari y'ar biyu na babyn mu mai kyau nace dake Raihanan ki ko?." Kai ta gyad'a mai tare da cewa. "Harda wani cemin baby ka dai san awa d'aya ka bani ko?." dariya yayi tare da kamo kafa d'anta yace. "Na yarda amman dai na fiki tsawo, mu tafi kawai B'iyaye na." Haka suka tafi suna wasa suna raha cikin k'aunar juna da yawan surutu gashi daga surutun su har mun gano cewa y'an biyu ne su, shi kam General tamkar an kafashi a wurin ne ya kasa shiga cikin gidan sai juyawa da yayi ya hard'e hannu a k'irji ya zuba musu ido har suka je bakin motarsu nan ma suka fara rigima ita Rayhana tace ita zata jasu shiko Ramadan yace sai dai shi, ganin Rayhanan zata bata musu lokaci ya cilla mata key, tare da cewa. "Naci girma karb'i mu tafi." Shi kam General ya kasa d'auke idonshi a kansu su duka biyu ita yarin in yar inya kalleta har tsikar jikin shi yake jin yana tashi. Suma cikin Mamaki ganin yana yin General suka tafi. Yana tsaye a wurin har Captain Sani ya fito tare da Dr Jabeer gaisawa sukayi tare da mik'awa General fayel na bincike kan b'atan Meenal din wanda aka yishi a jihar Taraba zuwa Yola 2 Gombe, toh yanzu an mik'e binci ken a hannu General inda zai fara kafa jamin tsaro da binci ken daga jihar Jigawa zuwa Kano har ya gaggaro nan Kaduna yayin da aka bazai yan sand'an ciki kuma tako wanne sak'o na kasar na. Karb'a fayel din yayi tare da cewa . "Insha Allah zata dawo gareku cikin k'oshin lafiya, yanzu tunda da hotu nanta zamu bada a kafafen yad'a labaru sannan za'a buga jarida da neman ta tare dasa kud'i mai tsoka ga duk wanda ya kawo labarin ta ." Murmushi Dr Jabeer yayi cikin jin k'arfin guiwar,sannan sukayi sallama da juna. Daga nan Captain Sani da General Aliyu suka wuce cikin Jaji , suna isa General ya ajiye fayel d'in a kan kujera sannan yace wa Captain Sani . "Ga wannan ni zan d'an shiga zanyi bacci yanzu wani Abdulkarim zai zo, yana zuwa ka bashi fayel d'in amman ka zaro pic d'aya a ciki ka ajiye sauran kuma ka had'a mai su." "Toh " ya amsa mai cikin girmamawa, sannan shi kuma ya wuce cikin bedroom d'in ya konta, shima Captain Sani konciyar yayi a parlour. Shi kam General tunani ne goma da ashirin a ranshi ko ido ya rumtse fuskasu Rayhana da Ramadan yake gani kunne shi na ajiye mai sautin muryar yaran masu cike da k'aunar juna. A d'aya sashin zuciyar sa kuwa Abdul yake tunowa tunda ya k'oneshin yaune kawai ya kuma fita ya bar Meenal a gidan ita kad'ai sai su Maman ido ya rumtse tuno hali irin na Mama zata iya yin komai akanta da d'anta dan imanin ta reggegene. Ita kuwa Meenal tunda ya fita tana baccin ta , kamar a zahiri kamar a mafarkin ta rink'a ganin General d'in cikin wani irin hali da bata Ganeba kamar dai cikin wahala yake, cikin d'an tsoro ta farka tana tashi ta fito parlour dan a tunanin ta yana nan tana fitawo parlour ta samu Abba a zaune, a hankali ta k'arisa gefen shi ta zauna tare da gaida shi cikin kulawa ya amsa gamida cewa. "Meenal ya jikin naki?." kai ta d'an d'ago ta kalleshi cikin k'aunar Abban dan yana da mutunci komai zai mata cikin kula yake mata shi. "Da sauk'i Abba yanzu kam ma banji zafin sosai." "Masha Allah haka ake so Allah ya k'ara sauk'i ko." "Amin ya rabbi ." Tace dashi tare da yin murmushi, haka Abba ya d'an yi ta janta da hira, kuma ba laifi dama itama tana sakewa da Abban. A d'akin Mama kuwa cikin jinjina kai ta kalli Abdul murya k'asa-k'asa tace. "Abdul yanzu kai a burin ka me kake son ayiwa Aliyu dan d'aukar fansa.?." Cikin cije lips enshi yace. "Mama ni so nake a mishi shegen duka a karya Mashi hannayen da k'afafun shi ." Ido ta kuma tsura mai tace. " shike nan abin da kake so?." kai ya gyad'a tare da cewa. "Ehh." Tsaki taja sannan ta mik'e tana safa da marwa cikin mugunta tace. "Kai ai baka da hankali baka kuma san k'ofofin mugun taba sannan baka San cewa kowa da wurin da za abi naci nasara a kanshi, ai Aliyu indai ta wurin duka ne har a badan da'iman ba zamu cin nasara a kanshi ba, sannan ko munci nasara an karya shi wallahi ni ban huceba, abin da yaso yayi maka Allah bai bashi sa'a ba ni zan masa badai akan mace yaso ya nak'asa min kai ba?." Kai ya gyad'a cikin kallon yadda yake zama ba wondo sai jallabiya ajiyar zuciya ya sauk'e tare da yin hamdala a ranshi yana cewa. "Mugun yaso ya maida ni mace ko mata maza amman Allah ya fishi gani garau da lafiya ta tamkar doki. Yana cikin tunanin yaji Mama tana cewa . " Toh ni yau d'in nan zanje gida boka mai gobe da nisa, zan kashe kud'i ko nawa ne a maida Aliyu Mace ya tashi daga Aliyu ya koma Aliya zan Sa boka ya nak'asa mana shi ta yadda har a badan shi da Mace sai dai gani da ido ta yadda zai rayuwar da wannan yarinyar daya k'ona ka akanta sai dai ido kuma tunda sunce matar sa ce ita ba k'aruwa ba to shakka babu kai d'in, nake so ka mai data karuwa ka zama tamkar mijin ta, yayin da shiko Aliyu zan sa boka ya maida shi tamkar logoni ko tsuma, shi da mace sai dai ya kalleta da ido , wannan Meenal din da yake gadi zata zama haramiyar sa, wanna ne kad'ai zamuyi mu d'auki fansa ta yadda ko wanne wayewar gari Aliyu k'ara mutuwa zai keyi a tsaye, shi zai koma mata maza tunda a fad'an zahiri baza muci nasara ba toh na sunk'uru zamuyi mishi, yadda na rab'a uwarsa da ubanshi haka zan rabashi da ko wacce y'a mace." Ido Abdul ya zuba mata cikin murmushi farin ciki baki na rawa yace. "Mama kin gama min komai wallahi." Sai kuma ya d'anyi shiru sannan yace. "Amman kar a hanashi Aure gaba d'aya in yaso adai rabashi da Meenal d'in kawai." Zama tayi gefen shi cikin rashin imani tace. "Dama ko Aliyu bayyi ma haka ba inason in hanashi aure inko ban hanashi auren ba toh zan hanashi haihuwa bare kuma yazo ya maka wannan abin." Cikin mamaki yace. "Toh Mama me ya miki?." Jinjina kai tayi sannan tace . "Na tsane shi ne, sabida ai kasan dai gidan nan na Abban Aliyun ne ba gidan Daddyn ku bane? Toh tun kafin a haifi Aliyu naso in zubar da cikin sa yafi sau biyar ina bawa Ammin Aliyu maganin tana sha kai harda allura nasa an mata cikin dabara amman da yake wannan Aliyun taurin Kaine dashi kamar shaid'an tun yana cikin uwarsa shi gardama yake min wallahi sai cikin sa yak'i zubewa." Cikin mamaki yace. "Toh Mama meyasa kike son hana matar Abba haihuwa? tunda naga ita ba kishiyar ki bace?." Tsaki taja tare da cewa. "Kaima banza ne naga alama ka fara zama irin yayan ka Amir da k'anwar ka Nafeesat, raguwar zuciya gareku ko toh, abin da yasa nake tsoron kar matar Abban ta haihu sabida kar ya samu Magaji kaga in baida yaro da zaran ya mutu Daddy kune zai gajesa kaga d'en duk dukuyarshi ta zama tawa nida Ku y'ay'ana, toh amman don jaraba da taurin kai saida wannan jarabebben d'an nasu Aliyu yazo duniya gashi ya fito d'an namiji ta yadda duk zai kwakwashe gadon, toh shine yanzu banson Aliyu ya haihuwa tunda ko ubanshi ya mutu ya gaji dukiyar toh in baida y'ay'an dole kune zaku gajeshi daga nan dukiya ta zama tamu, kaga dama shi Daddyn Ku ba abin da yake dashi yana nan kamar b'eran masallaci fak'aru alal larurati kawai." Ido ya ware cikin jin hud'ubar shaid'aniyar uwarsa, cikin zak'uwa yace. "toh Mama ya kikayi ki rab'a iyayen Hamma Aliyu?." Murmushi tayi cikin yarda da kanta tace. "Yanzu kan zan tafi gidan boka mai gobe da nisa dan ya fara min aiki a wannan rana sai gaba zan baka labarin yadda na rabasu a sauk'ak'e." Ido ya zura mata tare da mik'ewa yana tafiyar yan kaciya yasa hannun ya d'an dago jallabiyar sa karta fameshi, Ita kuwa mayafinta ta yafa sannan suka fito parlour anan ya tsaya itako ta wuce gidan bokan nata Wanda yake can cikin k'auyen Zaria kauyen ma a bayan garin. Tana zuwa ta samu gidan a cike da mata anata bin layi gidan boka ya zama tamkar asibiti, Itace bata samu shi gaba sai goshin maggariba tana shiga bokan ya kalleta cikin yin shu'umin dariya yace. "Hajia zulai a gidan lallai mugunta ta motso." Zatayi magana yayi maza yace. "Kiyi shiru nasan meke tafe dake amman kinsan sharad'in aiki na dole yau nine matsayi mijin ki kuma kinsan abinda zamu aikata." Kai ta jinjina tareda cewa. "Ba dai buk'atata zata biya ba?." Cikin zare ido yace . "Sai dai in ban miki wonka ba." Kai ta jinjina tare da cewa. " na yarda" Dariya yayi tare da cewa. "Toh a wannan Daren zan tura aljana kasalau ta zuba mishi kasala da sanyi mai tsanani da zazzab'i ta yadda bazai iya yin nafilfilin daya saba yi da karatu k'ura'ani da azkar da yake duk sai ya kasa yi kafin mu samu nasara a kanshi." *Wa iyazubillah ya Allah ka tsare mana imanin mu hak'ik'a wannan abu ya yawa ita a cikin matan wannan zamini* Shi kuwa General bayan anyi sallan ishah ne ya koma kan 3str ya konta, Captain Sani ne ya kalleshi cikin kula yace. "Sir ya kamata mu koma cikin Kaduna ko?." Kai ya jinjina tare da rumtse idonshi , can kuma sai ya mik'e tare da rarumo.. By *Garkuwar Fulani* [8/18, 6:26 PM] πŸ’žIt's @lh@jiπŸ’ž: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *BANDIRAWO* page 3⃣3⃣ Na *Aysha Ali Garkuwa* πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *JOGU ALLAH BE ANNABIJO BE DEFTERE ALLAH LELDI ANNBIJO MEN BE MAI , TO ALLAH JAB'I TA JOGI D'ONI A HISAI DUNIYA BE LAHIRA* Kan gashin ta saitin idanun nata cikin tsuke fuska yace. "Inafa gaya maki ki daina yimin irin wannan kallon munafurcin inba haka ba sai na k'wak'wulo k'attin idanun naki masu kama dana jinnu- jinnu." Shiru tayi cikin zubda k'ollah tare da zamewa k'asa ta tsuguna ta kifa kanta kan guiwowin ta, ta saki kuka mai sanyin sauti. Shiru yayi a tsaye a kanta ya kafeta da ido, yana jin yadda take fidda sautin kukan nata, tsaki ya ja cikin lumshe ido ya juya ya koma kan gadon jiki a mace cikin jin bacci, dan deren jiya bai samu yayi bacci ba, hakan yasa konciyar yayi tare da jan blanket ya rufe jikin shi, yana kallon ta kamar wasa amman sai kukan take shi kuwa harga Allah ranshi na b'aci en yaji sautin kukan nata idon ya kuma bud'ewa tare da tsura mata su a kanta , kokaci d'aya kuma sai tausayin ta ya rufeshi tunda ya tabbata shine ya rebota da kowa nata shine sana din zuwan ta garin shine aka bawa amanar ta, sannan a kanshi take kuka da zubda k'ollah, jiki a mace ya mik'a mata hannu tare da bud'e baki a hankali yace. "Meenarl " shiru bata kulashi ba sai sautin kukan nata ido ya kuma lumshewa yace. "Meenarl kina ji ina kiranki kinyi shiru bazaki amsa ba." kai ta d'ago tare da zuba mai ido cikin zubda k'ollah, shi kuwa hannu ya kuma mik'a mata tare da cewa. "Taso ki taso kizo nan kinji ko?." ya fad'a yana nuna bakin gadon cikin tsare ta da ido, kai ta sunkuyar tare da mik'ewa a hankali ta matso bakin gadon murya na rawa tace. "Gani." Idon a lumshe yasa hannu ya kamo nata sannan ya jawota kan gadon ta zauna a bakin gadon, shi kuwa ya mirgino ya juyo gareta yana kallon bayan ta jiki ba k'arfi ya k'ara matsota yana kallon fuskarta murya can k'asa yace, "Juyo nan ki gani." juyo wan tayi tare da kallon shi cikin tsoro tana mai murza yatsun ta, Shi kuwa hannu yasa a kanta ya jawo d'an kwalinta sai kuma yayi shiru yana kallon yadda gashin kanta ya zubo kan kafad'un ta, ita kuwa cikin kalloshi kawai take cikin fidda numfashin da sauri-sauri , mik'a mata d'an kwalin yayi tare da cewa. "Ki bar kukan ki share hawayen ki ." Shiru tayi bata kulashi ba sai k'ollan dake zuba, mik'a mata ya kuma yi tare da lumshe idon nashi dan baccin yake ji, jin shiru bata karb'a ba yasashi mik'a hannushi tare da kamo nata cikin sanyi ya jawo ta kan pillow ya kontar da ita yana mai kallon fuskar ta, ita kuwa sai janye jikin ta takeyi tana k'ok'arin tashi, fuska ya tab'e tare da cewa . "Kinitsu fa." kukan ta kuma saki tare da cewa. "Ni zan fita parlour zanje gun Abba." Tsaki ya ja tare da jawo ta jikinshi ya sata cikin k'irjin shi ya matseta da hannu d'aya murya can k'asa yace. "Bacci zamuyi dan jiya kema bakiyi bacci sosai ba." Baki ta tsuke tare da cewa. "Hamma Haiydar ni bana jin bacci." Matseta ya kuma yi a jikin shi kamar maiyin rad'a yace. "Lumshe idon ki, ki rink'a fidda numfashin ki a hankali kisa kanki cikin k'irjin na,. sabida karki ga haske kiyi haka yanzu baccin zai zo kinji ko." Bata kulashi ba, shi kuwa bai kuma mata magana ba sai lumshe idon da yayi tare da jawo blanket ya rufe su. Shiru kawai tayi tana mai shak'ar k'amshin turaren jikinshi, cikin shak'ar k'amshin ne ta fara jin kasala jikin ta na sakewa a hankali ta lumshe idon lokaci d'aya bacci safe mai dad'in nan ya kwasheta, shi kuwa yana jin tayi shiru a jikin shi yasa ya bud'e ido yana kallon ta fuskar ta ya tsurawa ido tare da tsanan ta buga war zuciyar shi, a lokacin daya tuno yaran da ya had'u dasu a dai-dai k'ofar shiga part d'in Alhaji Ibrahim, shiru yayi tare da karewa fuskar Meenalin kallo, cikin sauri ya kuma rumtse idonshi yana tuno kamannin fuskar Rayhana, a fili yace. "Wannan wanne irin kama ne ?." Tsaki yaja tare da cewa. "Kamar tayi yawa duk da ana cewa ko wanne d'an adam yana da masu kamannin sa har 7, gaskiya duk da haka kamar tayi yawa." Yatsarsa yasa yana shafa gashin girarta cikin mamaki ko yanayin gashin girarsu iri d'aya hatta d'an bakin su iri d'aya, shiru yayi tuno sautin muryar Rayhana tabbas sautin muryar ta sak irin sautin muryar da bazai mantaba duk da tsawon shekaru da yayi baiji muryar a zahiri ba tabbas sautin muryar ta irin ta Ammi ce tunda a koda yaushe yana mafarkin Ammin shi kuma yana jin muryar ta. Ido ya kuma rumtsewa tuno fuskar Ramadan sai kuma yasa tafin hannushi yana shafa fuskar shi yana mai mamaki a sanyaye ya lumshe ido tare da sauk'e ajiyan zuciya a haka cikin tunanin bacci mai dad'i ya d'ebeshi suna ruggume da juna cikin shak'ar k'amshin juna... Ita kuwa Mama da gari ya waye bayan sun gama lalalatan su ita da bokan ta ya had'a mata tuggun da take buk'a ya kuma shaida mata aiki ya kammalu daga yau Aliyu ya zamo Aliya bashi ba mace sai dai gani da ido zai zama dashi da logoni basu da babbanci , cikin rud'u shaidan da bacewar imani da mancewa Allah na nan ta yarda da maganar bokan nata ta kamo hanyar ta cikin happy ta dawo gida ita da Abdul suka rink'a had'a zalumci yayin da Nafeesat da ya Amir suke binsu da Addu'a da fatan shirya.. Rayuwa ta juya komai ya fara canzawa yayin da kwanaki sunja har ya koma makonni sun ja , Ramadan da Rayhana kuwa suna ta k'ok'arin had'uwa da d'an uwansu so sai dai basa son kowa ya sani kuma su a Kansu sun k'asa gano ina yake, ganin bazai Ganeba gashi wata d'aya zasuyi su koma hakan yasa Ramadan ya yanke shawaran dole su nemi Captain Sani Wanda suke kira Hamma Sani sunyi shawara dashi a kan haka suka yanke shawaran k'iran shi yazo gida sunyi maganar ... Shi kuwa General Aliyu a hankali rayuwa ta juya mai inda zuwa yanzu ya fara fahimtar akwai abin dake bibiyarsa zuwa yanzu kullum dare Aliyu kwana yake cikin azabben zazzab'i da sanyi da ciwon ciki da kasala mai tarin yawa da tsinke war zuciya da zaran anyi sallan insha wannan yanayin yake zuwa mishi shine bazai samu sa'idaba sai iskar asuba ta fara kad'a daga nan kuma kafin gari ya waye sai ya nemi ciwon ya rasa kab jikin sa sai yayi garau sai dai kuma dole sai yayita yin baccin rana haka yasa gaba d'aya yanzu bai fiye kwana a Jaji ba kuma yamma nayi zai dawo gida haka zasu kwana da Meenarl d'inshi cikin wahala shi baida lafiya ita kuwa tsoron yadda yake wahala da ruggume ta da yakeyi tsam yana rawan jiki shike hanata bacci a hankali ta fara jin tausayi yinshi na ratsata ta yadda take kwana mishi sannu da zubda k'ollah..... Yau jumma tun da yamma General ya dawo gida a parlour ya zauna jiki a mace dan yaune ya gano wata matsalar dake jikin shi hakan ya sashi cikin rud'ani, yana kwancen Meenarl ta shigo parlour kai tsaye gaban shi taje ta zauna kan carpet ido suka tsurawa juna cikin kula da tausayi tace. "Hamma Haiydar yaushe ka dawo?." Shiru yayi tare da kallon yadda take ma shi maga cikin tausayi yawa da kulawa, abinda bai tab'a samuba, ba wanda yasan halin da yake rayuwa a cikin in dare yayi sai ita shiyasa gaba d'aya yanzu tausayawa kanshi yake. K'ara matsoshi tayi cikin sanyin murya tace. "Hamma baka da lafiya ko?." Ido kawai ya tsura mata, ita kuwa ido tab da k'ollah tasa hannu kan wuyan shi cikin rawan murya tace. "Hamma yamma tayi ko? har zazzab'i ya fara zuwa?." Shiru baiyi magana ba sai kanshi yasa ya matse hannun ta a kan wuyan nashi . Ita kuwa cikin zubda k'ollah tace. "Hamma Aliyu kamin magana mana." Ido ya tsura mata cikin tsuke fuska yace. "Ina kika je? bana hanani fita ba?." Kai ta lok'k'osa cikin sanyi tace. "Kayi hak'uri Hamma naje gun Anty Aysha ne." Shiru yayi sannan ya mik'e ya zauna tare da zaro hankicif d'inshi ya mik'a mata yace. "Share hawaye ki ni lafiya ta lau, bari ma inje masallaci, ki tafasa min tea kafin in dawo." Toh tace tare da binshi da ido har ya fice sannan itama ta shiga bedroom din nasu tayi sallan.. 9:23 pm General ne zaune kan carpet d'in dake gaban gadon nasu sai rawan sanyi yake tare da damk'e cikin shi yana mai jujjuya kai, ita kuwa durk'ushi take a gabanshi tana zubda k'ollah cikin rawan murya tana. "Isa Hamma Haiydar sannu ." Kai ya gyad'a mata cikin dauriya yace . "Meenarl jeki rufe k'ofar parlour ki kashe wutan da fanka kizo ki konta." "Toh" tace tare da mik'ewa taje ta rufe k'ofar tare da kashe komai sannan ta shigo ta sameshi ya had'a kanshi da jikin gadon gaba d'aya jikin shi sai rawa yake, da sauri taje kusa dashi cikin tausayawa tace. "Hamma Haiydar ni kam bari inje in gayawa Abba inya so sai mu tafi asibiti." Kai ya juya mata cikin furzar da numfashin yace. "A a Meenarl barshi kinga yayi bacci kar mu tayarmai da hankali kinga yana da hawan jini." Hannu tasa ta share hawayen ta tare da jawo blanket zata rufe mishi jiki ganin yadda yake karkarwa, hannun ta ya rik'e cikin cije lips enshi yace. "Bari Meenarl ai yau da sauk'i ki hau kan gadon ki kwanta nima yanzu zan hau in kwonta." Baki ta bud'e a hankali tace. " toh tashi ka hau." Murmushi k'arfin hali yayi tare da yunk'ura zai mik'e rik'e da hanna yenta dai-dai lokacin da sunkuyo d'in wani irin..... *Kuyi hak'uri da wannan sisters ina kuma k'ara Baku hak'uri rashin ganin nolen d'inna da zakuyi gobe zuwa jibi hakan zaifarune sakamakon zanyi tafiya Adamawa Yola 2 Gombe ina Neman Addu'arku fatan Allah ya kaini lafiya ya maidoni lafiya* By *Garkuwar Fulani* [8/18, 6:26 PM] πŸ’žIt's @lh@jiπŸ’ž: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *BANDIRAWO* page 3⃣1⃣ to3⃣2⃣ Na *Aysha Ali Garkuwa* πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *Wannan shafi sadaukar wane gareki k'anwata ta gari har kullum kina raina Ummee Garkuwa 😍😘* Pml yace. "Ammi kin san abin da muka gani kuwa jiya da hantsi?." Murmushi tayi cikin kula tare da maida hankalin ta kan d'an nata gudan jinin ta mai sata farin cikin mai share mata k'ollah a duk sanda suka koranyo a fuskar ta mai cike da tunani da bagen wani abun da ta rasa. Kai ta jinjina tare da cewa. "Me kuka gani Ramadan har ya rud'aku haka?." Ido ya tsura mata tare da yana yin mamaki yace. "Ammi jiya ba munje gidan uncle Ibrahim duba jikin shiba?." kai ta gyad'a mishi tare da cewa. "Ehh." Matsota ya kuma yi tare da rik'o hannun ta cikin shak'uwa da mahaifiyar tasu yace. "Ammi jiya a gidan uncle ni da Rayhana mun had'u da wani Soja a dai-dai k'ofar shiga part d'in uncle Ammi kin ga yadda Sojan nan yake kuwa?." Ido ta tsura mashi tare da girgiza kai cikin son jin k'arshen maganar. Cikin muryar mamaki yace. "Ammi dana ganshi zuciya ta tayi ta bugawa tsikar jikina gaba d'aya ya rink'a tashi idona sai rawa suke a kan kaman nin fuskar sa hankali na kuwa ya tashi Ammi." Rik'o hannunshi tayi cikin tsoro kar d'an nata yayi gamo ne tace. "Ramadan me ka gani a fuskar sa? shi mutun ne ko aljan?." Kai ya jinjina tare da sauk'e ajiyar zuciya a hankali yace. "Ammi ina da tabbacin mutun ne shi, Ammi kamannin fuskar Sojan nan ya bani mamaki da tsoro, Ammi komai fa na fuskarsa da halittarsa irin nawa ne, Ammi hatta farin mu irin d'aya ni dashi Ammi hatta k'wayar ida nunshi irin nawa ne, Ammi hatta sajen dake fuskar sa irin nawa ne , Ammi wallahi ko yatsun hannushi irin nawa ne, Ammi kamata da wancan Sojan yayi yawa har takai kamar da nakeyi dashi wallahi ko Rayhana da muke tagwaye bamuyi irin wannan kamar ba, Ammi tsawo kawai da d'an k'iba ya fini alamun ya d'an girma ni a haife, Ammi wallahi kwana nayi ina mafarkin shi yana kuka yana k'iran sunan ki yadda muke kiran ki Ammi shima haka yayi ta k'iran cikin mafar kina, Ammi shi kad'ai na gani a mafarkin yana rayuwar kad'aici ba wanda ke kusa dashi dake nuna mai k'auna ko kulawa sai wata budurwa ita kuma tayi nesa dashi sai wani haske da yake tsaka ninsu sai kuma na haggo wani duhu a hannun wata mata tana turawa cikin hasken daga gefen shi kuma Hamma Jabeer ne yana jan hannun wannan budurwa." Sai hawaye cur-cur a fuskar sa murya na rawa ya kifa kanshi jikin gadon , wanda Rayhana ke konce tana jin duk abinda suke fad'a tuni itama sai kuka take yi sun had'a kai wuri d'aya suna kuka a hankalin. Ita kuwa Ammi bugawar zuciyar tane ta tsananta, lokaci d'aya hankalin ta da tunanin ta suka koma kan d'anta Aliyu Haiydar wanda ta rebu dashi tun yana d'an shekara bud'u, a badiri kullum Ammi Aliyu na cikin ranta dashi take kwana dashi take tashi tana son d'anta tana son ta kasance dashi ta bashi kulawa da tarbiya wacce ko wanne d'an yake samu gun mahaifiyarsa, amman ina haka bata samuba dan fushin da iyayen ta sukayi. a lokacin da Abban Aliyu ya saketa, ya kuma karb'e d'anshi haka yasa Babban yayan ta mahaifin Captain Sani da Dr Jabeer ya d'auke ta daga garin Kaduna ya koma da ita Adamawa Yola inda yake aikin sa cikin gidan shi ya ware mata part nata ita da mahaifiyarsu, ya rink'a kula dasu da duk wani dawaini yarsu, Karin konciyar hankali linsu matar sa Hajia Asma'u mahaifiyar su Dr Jabeer da Captain wacce suke kiranta Nenne , macece mai mutunci da sanin ya kamata ta d'auki dangin mijinta kamar denggin ta , ta taimakawa mijinta wurin kula da y'ar uwarshi da mahaifiyarsu du-du yaran Nenne 2 ne Dr Jabeer sai Captain Sani , amman ganin d'an uwanshi bai tab'a haihuba wato (Alhaji Ibrahim mai dala), sai ya d'auki d'anshi na biyu Captain Sani kenan ya bawa k'anin shi, daga nanne Captain Sani ya koma Kaduna da zama. Ita kuwa Ammi bayan fitan ta gidan Abba da wata d'aya ciki ya bayyana inda take laulayi kamar zata rasa ranta, cikin kulawa d'an uwanta Barrister Lawan mai dala ya kaita Asibiti gojin forko aka gano tana d'auke da cikin wata 3 a jikin ta, Ammi tayi farin ciki dan ita a zaton ta ko dan albarka cikin yayunta da mijinta zasu gyara auren ta koma kan d'an ta gudan jininta, haka kuwa sukayi Alhaji Ibrahim yaje ya samu Abba da batun cikin, amman da yake a wancan lokacin asirin da Mama tayi ya kama shi yana aiki a kanshi shiyasa, fir Abba yak'i yace shi wannan cikin ba nashi bane can suje su nemi uban cikin dake jikin ta, shi ba ruwan shi , wannan kalma ta cewa ciki ba nashiba yasa Barrister Lawa fushi mai tsanani Wanda daga nan ya yanke duk wata alak'a da zata had'a Ammi da gidan Abba hatta kadunan Barrister ya hana Ammi zuwa kota-kota, Ammi kam da tajin maganar tayi kuka kamar ranta zai fita sana din wannan abin ta samu hawan jin, inda mahaifi yarta da Jabeer suka zama abokan zaman ta Jabeer yana son Ammi a ranshi fiye da zaton d'an adam Jabeer jin Ammi yake tamkar ita ta haifeshi domin komai a part nasu yake yi Ammi kemai duk abinda Uwa keyiwa d'anta Ammi ce abokiyar shawaran sa itama shine abokin shawaranta tasha zama ta bashi labarin Haiydar shima Jabeer sai yayi ta kuka yana son d'an uwan shi kuma shine kad'ai yasan yadda Ammi ke shiga damuwar rashin d'an nata, yayin da Kaka ke basu kulawa gaba d'ayan su, bayan watanni 6 Ammi ta haifi yan tagwayen ta inda Ramadan ya fito mai kama da Aliyu sak da sak , ita kuwa y'a macen sun rasa dawa take kama ba abin da ta dauko na kowa a zuriyarsu sai muryar tace kad'ai irin ta Ammi da zaran ta bud'u baki tayi magana toh sautin muryar Ammi sak. Haka yara suka tashi cikin gata da kulawa da tattalinsu da ake a cewar Alhaji Ibrahim su yaran basuma ishesu ba bare a wulak'an ta musu y'ar uwa a banza su zasu rik'esu har iya rai da mutuwa, ita kuwa Ammi tun daga nan bata kuma yin aure ba aceqarta zata kula da yaranta, Dr Jabeer da Ramadan da Rayhana sun tashi gida d'aya d'aki d'aya gaban Ammi ta musu tarbiya mai kyau sun tashi cikin k'aunar juna da shak'uwa. Alhaji Ibrahim kuwa duk sanda zaije Taraba Gembu Duba yarshi Amina yakan biya cikin Yola ya d'auki d'an yayan nashi wato Jabeer suke tare, toh shi Jabeer daga nan yasan Meenal haka kuwa yasa kullum k'arshen sati sai ya shirya yaje Yola to Membila yaje ya duba k'anwar shi Ammi ma da su Ramadan da Barrister da Nenne tare da Kaka duk suna zuwa su kaiwa Meenal ziyara, a haka shak'uwa mai tarin yawa ta shiga tsaka ninsu , shiko Captain Sani kasan cewarsa a makaran tar sojoji yake da yanayin karatu shi da aikin shi yasa bai tab'a zuwa canba ko sau d'aya, Sannan Abba kuwa yana sakin Ammi Mama ta kuma mishi asirin da dole zaman Kaduna yafi k'arfin shi saida ya k'aura ya koma Katsina yana Katsina ya karisa ginin gidan da suke ciki a yanzu suka k'aura suka koma can yayin da Aliyu ya tare a part d'in Abba shi yana rayuwa shi d'aya a haka ya girma komai na karatu Abban na mishi, toh sana din k'auran nasu yasa Alhaji Ibrahim bai kuma ganin Aliyu ba bare da ya girma Alhaji Ibrahim bazai gane shi ba kuma shi Alhaji bai tab'a zuwa gidan su Aliyun ba dan in yaje kam zai had'u da Daddy toh dole zai gane Aliyu ..... Toh yanzu sanadin B'atan Meenal yasa Alhaji Ibrahim ciwon zuciya da hawan jini, shine fa Barrister Lawan ya shirya da iyalanshi kab da Kaka mahaifiyar su da Ammi dasu Rayhana da Nenne duk suka zo Kadunan duba Alhaji Ibrahim d'in da jikin yayin da suka sauk'a a gidan Barrister Lawan d'in dake nan cikin kaduna, toh su Ramadan sun zo sun gaida Uncle Ibrahim d'inne sun fito zasu koma suka had'u da General... *Mu koma kan labarin* ajiyar zuciya Ammi ta sauk'e tare da zubar k'ollah tana mai kama hannun Ramadan da Rayhana da Ramadan kuka kawai suke yi cikin kukan Ramadan yace. "Ammi nasan fa akwai abinda kuke b'oye mana nida Rayhana Ammi na fara zargin mahaifimu na raye, Ammi wannan sojan d'an uwanmu ne duk yadda akayi mun had'a jini dashi." Cikin kuka sosai Ammi ta basu labarin abin da ya faru shekaru 26 da suka wuce ta kuma d'ora da cewa. "Ramadan ina ji a jikina Sojan nan d'an uwanku ne yayan ku Haiydar ne shine yayanku Uwa d'aya uba d'aya, Amman ko kunce zakuje yan uwana zasu ha naku dan sun rik'e mahaifin ku a ransu." Hannu Ramadan yasa ya rik'o nata cikin share k'ollan fuskarsa yace. "Ammi mu dai Abba mahaifin mune bamu da wani uba daya fishi kuma mu ya watsar da mugun furucin , mu kuwa nida Rayhana mun yafewa mahaifin mu muna kuma son uban mu zamu kuma nemoshi muna son d'an uwanmu zamu je gareshi zamu raba shi da zaman kad'aici zamu sashi happy a rayuwar sa dan haka karki gayawa su Uncle komai akan zamu nemi Abban mu, bamuga laifin su Uncle ba dan dole suji zafin abin da akayi miki a matsayi su na yayunki." Kai Ammi ta jinjina cikin zubda k'ollah tace . "Rayhana kinji abinda Ramadan yace kuma kema kina bayan shi?." Kai Rayhana ta jinjina cikin kuka sosai tace. "Ammi inason Abba na in ason in ganshi ina son Hamma Haiydar naji tausayin Hamma Haiydar ya rayuwa tamkar maraya alhalin iyayenshi na raye, haba ashe shiyasa fuskar Hamma Haiydar ba fara'a baida sakewa ashe cikin kuncin rashin Uwa da uba yake rayuwa ba d'an Uwa ba y'ar Uwa a kusa dashi ina son d'an uwana Ammi." Cikin kuka Ammi ta dafa Kansu tare da cewa. " Allah ya muku albarka rabbi ya kaddara saduwar ku da mahaifin Ku na amince kuje gareshi." Murmushi Ramadan yayi tare da mik'awa Rayhana hannu, ta d'ora nata hannun kan nashi, cikin yana yin jinjina ni yarsu, itama Ammi murmushi tayi a ranta koba komai farin cikin ta zai dawowa gareta d'anta abin al'fahari ta Aliyu Haiydar.. Shi kuwa Aliyu yana shiga bedroom d'in lokacin daya bi bayan Meenal jikin durowa ya tsare ta cikin had'e fuska yace. "Ke me kike ta min kallon munafurci kina wani zaro ido kamar mayya." Shiru tayi cikin kallon shi a tsorace tana mai girgiza mishi kai tare da cewa. "Mayyahh." Fuska ya kuma tsukewa tare dasa hannu kan.... By *Garkuwar Fulani* [8/18, 6:26 PM] πŸ’žIt's @lh@jiπŸ’ž: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *BANDIRAWO* page 3⃣4⃣ to3⃣5⃣ Na *Aysha Ali Garkuwa* πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *Dedicated 2 Amina Aminu ( Meenah parrot)* Yaji wani irin azababben ciwon ciki, gaba d'aya jikin shi ya rink'a b'ari kar-kar dole ya zame tare da damk'e mararshi, ita ma Meenarl komawa tayi ta zauna tare da jingina da jikin gado cikin rawar murya da tausayawa ido na zubda k'ollah ta rink'a cemai. "Sannu Hamma Haiydar Allah ya baka lafiya ehsa Hamma am." Shi kam Aliyu zamewa yayi ya konta kan cinyoyin ta tare da tura kanshi cikin fatar cikin ta sannan yasa hannu duka biyu ya zagoyo k'ugunta tare da rumtse ido sai karkarwar da yakeyi gaba d'aya ya dunk'ule a jikin ta, ita ma cikin tausayawan ta ruggumo shi da kyau tare dasa hannun ta tana shafa wuyan shi zuwa kafad'an shi tana kuka tana mishi sannu, hannun ta na rawa ta tura hannun kan marar tasa cikin mamaki da tsoron ta zaro ido tare da cewa. "Hamma Haiydar ji mararka kamar wuta ga tauri kamar dutsen." Shi kam kanshi kawai yake turawa cikin jikin ta kamar yaro k'arami a cinyar mahaifi yarshi, hannu tasa kan marar tashi ta d'aura a hankali sannan tasa yatsunta ta rink'a murza marar tashi a hankali tare da sunku yowa tana karan ta addu'oin tana mishi tofi a kai tare da murza marar tana danna wurin tare da murza wurin da taji yayi tauri da zafin. Shi kuwa General K'ara K'ak'k'ame ta yayi tare da murza kanshi cikin jikin ta yana wani irin numshi da k'arfi sai mutstsu kata yake yi tare da yin magana cikin wahalcecciyar murya. "Lahaulawala k'utah illabillahi aliyul azim wayyo Allah na wayyo jikina cikina Meenarl marata zata b'alle." Sai kuma ya k'ara tura kanshi cikin jikin ta yana mai murza kan nashi, murza kan nashi yake cikin wahala har saida ya b'alle boturan rigar jikin ta ya zamana gaba d'aya cikin ta da k'irjin ta suna woje haka ya rink'a tura kanshi yana murza kanshin a tsakiyar k'irjinta tare da k'wak'wume ta. Ita kuwa murza marar tashi take tana mishi tofi tare da rugume shi, a haka ya fara lafawa sai numshi yake sauk'ewa a hankali yana sauk'e ajiyan zuciya, ido ya rink'a lumshewa yana d'an bud'ewa a hankali ya mirgina tare da gyara konciyar shi kan k'irjin ta. Ita kuwa jikin gadon ta koma ta jingina tare da gyara konciyar shi a jikin ta sannan ta jawo blanket ta rufesu, shi kam shiru yayi tare da lumshe idon shi a hankali bacci ya fara d'ibarshi, ita kuwa ido ta tsura mai fuskarsa take kallo ganin yadda yayi wani irin kwarjini sai zufa dake tsatstsa fo mishi, a haka ita bacci ya saceta. 4:27 Am , General ya d'an gyara konciyar shi dan a lokacin ne ya fara jin kuzari cikin baccin yake jin duk ciwon na tafiya juyawan da yayine ya tasheshi daga baccin cikin d'an sauran kasalan ya bud'e idanun shi, shiru yayi yana mamaki ganin inda yake konce lumshe idon ya kumayi tare da sauk'e ajiyar zuciya fuska ya d'an dago tare da tsurawa tata fuskar ido bacci take cikin takurewa a jikin gadon sannan tasa hannu ta ruggume shi sannan hannun ta d'aya kuma ta tura kan mararshi , ido ya rumtse da k'arfi ganin kanshi na tsakiyar k'irjin ta , bud'e idon yayi tare da sake diresu kan k'irjin ta , shiru yayi ya zama tamkar soko ko wani gaulah so yake ya d'auke ida nunshi daga kan abin da yake ganin kuma ya kasa idon yake son lumshewa amman sai idanun sukayi mishi nauyi ba abinda yake ganin sai k'irjin nata, tsikar jikin shi ne ya rink'a tashi tare da fuzgar numfashi hannun shi ya jawo da k'yer a nufin shi ya jawo rigarta da ta bud'u ta zame kad'an zai rufe k'irjin nata , amman yana d'ago hannun sai kasalar jikin shi ta rinja yeshi cikin kasalan ya dire hannun nashi kan k'irjin nata, shiru yayi cikin tsinke war jinin jikin shi ya kara ruggume ta sannan ya murza hannushi kan abinda ke tafiya da tunanin shin ido ya tsurawa k'irjin yana kallon irin halittar da Allah yayi mata kanshi ya kuma murzawa cikin kasala ya rink'a murza kan nashi a tsakiyar k'irjin ta d'in yana gogar abin da ke sashi kuzari a haka ya fara jin kuzari shi na dawowa har ya samu ya mik'e zaune ido ya tsura mata ganin tana ta baccin ta sai kanta da take ta d'an juyawa . Yana tashi zaune ya motsota cikin kauda kai yasa hannun ya jawo rigar tata yana manna mata botur d'in, yana zuwa na saman jin inda yasa hannunshi ya juyo da sauri ajiyar zuciya ya sauk'e sannan yasa hannun ya shafa k'irjin nata sannan ya manne botur d'in mik'ewa yayi ya tallabota sannan ya nufi kan gado da ita, ita kuwa yana d'ago tan tasa hannu ta sank'alo wuyan shi tare da manna kanta a k'irjin shi. Haurawa yayi kan gadon ya kontar da ita tare da gyara mata konci yar tata, zai tashi zaune yaji ta sank'alo wuyan nashi haka tasa dole ya maida kanshi kan k'irjin ta, ita kuwa sai kara shigewa jikinshi take tana tura mai k'irjin ta gaba d'aya ta birki tashi ya gaza gane wanne hali yake ciki ya k'asa babbance shi lafiyeyyene ko ma jinyaci ne yana dai jin wani irin yanayin kam a tare dashi, yadda ta rik'e shin yasa ya maida kanshi kan k'irjin nata sannan yasa hannun yana mata wani irin salon shafa waishi a tunanin shi bacci yake son sata ita kuwa jin yadda yake shafa ta kamar a mafarki kuma tana jin yana sata cikin wani yanayin hakan yasa ta rink'a mik'a mai cike da kasala tana turo mishi k'irjin ta tare da nad'ewa a jikin shi , shi kam zuwa yanzu ya gaza gane a duniyar da yake yadai tsinci kanshi da murza yarinyar yana shafata da tsotse inda yake tsone mashi ido, sarrafata yakeyi sosai sai nishi yakeyi yana jawota jikin shi kanshi ya tura kan k'irjin ta sannan ya manna bakinshi kan farin ganin shi cikin salon cikar zatin haibar ya rink'a mata wani irin abun da yasa ta cikin baccin ta rink'a kamo kanshi tana. "Shihhhhh hahhhhh huhhhhm." Shima tuni ya fara sauya salon fitar numfashi , ita kam sai shafa kanshi take yi jin yasa hannun kan cibiyarta yana mata tafiyar tsutsa yasa ta bud'e ido cikin sauri tare da janye jikin ta baki na rawa tace. "Hamma Aliyu lokacin sallah yayi fa." Shiko shiru yayi tare da yin rufda ciki k'irjin shi kuma na kan nata ya k'asa janye hannushi kan k'irjin nata sai wani irin kunya da yake ji shin me zaice mata kuma me yake mata haushin kanshi ya faraji yana jinta tana ta ki ranshi amman sai ya lumshe idon yayi shiru, a ranshi kuma yana mamaki halin da ta shiga a lokacin da yake murza hannushi a jikinta a ranshi yake tunanin kenan tana buk'atar namiji a tare da ita zuciyar shi ne ta tsananta bugawa d'aya tuni halin da yake ciki a yanzu ya tabbata bazai iya zama da mace ba inko ya zauna da mace toh ya cutar da ita d'an zuwa yanzu ya gane yana da raunin sha'awa. Yana cikin tunanin yaji tasa hannun kan hannushi dake kan k'irjin ta zame hannun tayi tare da d'an tureshi, kanshi ya dago tare da kallon fuskar ta ido ya tsura mata cikin mamaki ganin yadda gaba d'aya idanun ta sukayi jazir kuma ta k'asa bud'e su duka sai ta bud'e su sai ta kuma lumshe su lips d'in ta kuwa gaba d'aya sunyi jazazir sai shek'i suke yi hannayen tama sai rawa sukayi gashi magana take amman muryar ta na rawa, cikin sanyin murya yace. "Minali me kike so?." kai ta girgiza cikin sanyi tace . "Nima ban sani ba." jawota jikin shi yayi tare da tallabe kanta suna kallon juna ido cikin ido cikin rad'a yace. "Bodd'in Hamma Haiydar me yake da munki?." Kai ta kuma girgizawa tare da zubda k'ollah dan har ga Allah ita bata san meke damun taba kuma bata san me take soba gashi gaba d'aya jikin ta wani irin yanayin take ji, hannu yasa ya share mata k'ollah zuciyar shi cike da k'unci murya a sanyaye yace. "Meenarl me kikeji a jikin ki ?." mik'a ta d'anyi cikin shan yaji murya na rawa tace. "Shihhhhh Hamma Haiydar nima ban san ya zance ba kuma jikina ba k'arfi gashi inajin tsikar jina yana tashi kuma inaji kamar abu na tafiya a jikina." Shiru yayi cikin tsura mata ido sannan ya mik'a mata hannushi cikin sanyi yace. "Zoh nan zo jikin Hamman ki." Hannun ta mik'a mai sannan shiko ya jawota jikin shi cikin hikima ya kifata kan k'irjin shi tare dasa hannushi cikin tafin hannun ta ya hadesu gam har jikin shi na rawa yatsarsa ya tura cikin tafin hanuta ya rink'a murza yatsar tasa tare dasa d'aya hannushi cikin rigarta yana shafa bayan ta zuwa cikin ta k'afafun shi kuwa ya had'e su da nata ya rink'a murza cinyoyin ta da nashi bakinshi ya kai dai-dai kunnenta ya rink'a fesa mata iska mai sanyi a kunne ta murya can ciki-ciki kamar maiyin rad'a a hankali ya fara magana. "Minalin Hamma Haiydar." Cikin sauk'e ajiyar zuciya tace. "Na'ammm Hamma Aliyu." Matseta ya kuma yi ciki rad'a yace. "Minalin Hamma Aliyu Haiydar ki matso jikina ki rik'e ni da kyau karki ji tsoro yanzu zaki barjin abin da kike jin matso ni ki had'e k'irjin ki da nawa ke baki da lafiya ni bani da lafiya ba mu da sauran gata a duniya d'aga mahaliccin mu sai kuma mu muzamewa gatan junan mu." Matso shin tayi tare dajin tausayin Kansu da Kansu cikin sanyi tace. "Hamma Aliyu har yanzu jikin ka namaka ciwo ne kaima?." Matseta ya kuma yi sannan ya jawo hannun ta ya tura kan mararshi murya can k'asa-k'asa yace. "Bodd'in Hamma goga min wurin yadda kikayi min dazu." "Toh " kawai tace tare dasa hannu tana murzawa a wurin. Shi kuwa cikin fuzgar numfashi yasa hannushi kan k'irjin ta yana shafa su da murza su iya son ranshi murya na rawa yace. "Nan ma yana miki k'aik'ayi ko?." Cikin yin mik'a tare da sakewa a jikin shi tace . "Ehh Hamma Aliyu amman kuma k'aik'ayin a cikin k'irjin nake jinshi." Kanta ya d'ago yana kallon yadda k'ollah ke bin fuskar ta kai ya jujjuya mata cikin rad'a yace. "Kina son in k'aik'aya miki ne?." Murya a mace tace. "Ehh Hamma Aliyu ." Shiru yayi sannan ya jawo blanket ya rufesu a hankali ya zame yayi k'asa kanshi yasa kan k'irjin ta cikin salon iyawa da wayewar kai ya manna bakinshi kan....N ya rink'a tsotsarta cikin sanyi tare dasa yatsarshi yana shafa cikin ta. Ita kuma hannayen ta tasa cikin sumar kanshi tana yamutsa sumar sai lumshe ido take tare da sauk'e ajiyar zuciya a Jere a jere baki a mace take cewa. "wayyo Hamma na ya zanyi? Hamma Haiydar inajin k'aik'ayin yana fita shihhhhh Hamma Aleeeyurr." Kanshi ya d'ago ya tsura mata ido cikin mamaki ganin yadda takeyi ya kuma jawota jikin shi murya a kasalance yace. "Yanzu kuma me kikeji ne Minalin Hamma ?." Ido a lumshe tace. "Wani irin abun da ban tab'a jin irin shi ba Hamma na ji nake kamar inyi ta kuka." Cikin mamaki yace . "Kuka kuma? kukan me kenan?. Cikin rashin sanin madafar maganar tace. " dad'i nakeji ." Ajiyan zuciya ya sauk'e tare da yin murmushi dan harga Allah yaji dad'i tunda ya sama mata sanyi da nitsuwa ya rege mata k'arfin sha'awar ta , murmushi ya kuma yi tare da fizgota jikin shi ya matseta tsam a jikin shi yana mai shafa gashin kanta. A haka har ta fara bacci . Jin an fara kiran sallah ya d'an zame tare da sauk'owa kan gadon toilet ya shiga kai tsaye al'wala kawai yayi ya fito gabanta ya dawo cikin sanyi yace. "Meenarl tashi kije kiyi wonka kizo kiyi sallah ko." Mik'a tayi tare da tura baki tace. "Hamma wonka Kuma gaskiya ni akwai sanyi." Zama yayi gefen ta cikin kallon fuskar ta yace. "Toh ya zakiyi kiyi sallan ba tare da kinyi wonka ba ai dole sai kinyi wonkan." Blanket ta kuma jawowa cikin tura baki tasa hannu ta shafi sajen fuskar sa tace. "Kai Hamma Haiydar jifa ruwan sanyi kuma kaima bakayi wonka ba niko kace sai nayi wonka bayan kai kullum sai kayi kafin ka tafi masallaci amman yau tunda akwai sanyi bakayi ba." Shiru yayi yana tunanin ya zaiyi ya fahimtar da ita dole tayi wonka kallon ta yayi cikin sanyi yace . "Taso kiji." mik'a tayi tare da kontowa ta bayan shi tasa hannu ta.... *kuyi hak'uri sisters nayi tafiya ne shiyasa kuka jini shiru kwana biyu kuma har yanzu ban koma ba so zan daure na rink'a yin typing ko short paga ne* By *Garkuwar Fulani* [8/18, 6:26 PM] πŸ’žIt's @lh@jiπŸ’ž: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *BANDIRAWO* page 3⃣6⃣to3⃣7⃣ Na *Aysha Ali Garkuwa* πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *Moh Allah seini b'uri sembe suno innu adama Jo* ta zagoyo k'ugunshi tare da turo kanta kan cin yarshi cikin bacci baccin tace. "Hamma Haiydar Wlh ruwan da sanyi ." Shiru yayi yana kallon fuskar ta yadda ta d'an tsuke baki sai faman lumshe ido ta keyi, tana ta shigewa jikin shi, kai ya jinjina cikin lumshe ido ya sauk'e ajiyar zuciya cikin kula ya shafa fuskar ta kamar maiyin rad'a yace. "Hmmm ai na kunna ketil d'in toilet d'in yanzu ruwan yayi zafi dai-dai wonkan, kije kiyi sai kizo kiyi sallah inyaso sai ki koma baccin." Kai ta kuma turawa jikin shi tare da cewa. "Toh ni Hamma yau wonkan dole ne?." Fuska ya tsuke cikin had'e girar sama data k'asa yace. " Eh dole ne sai kinyi ya ina miki magana kina min taurin kai tunda kinsan baki son sanyi meyasa kikayi ta shigewa jikina d'an fitina ." Janye jikin ta tayi daga gareshi dan ganin yadda ya tsuke fuska komawa tayi gefe ta zauna ta kifa kanta cikin guiwowin ta. Mik'e wa yayi tare da juya mata baya cikin muryar fad'a yace. "Ki tashi kije kiyi wonkan tsarki sannan kizo kiyi sallah, ai ke ba jahila bace kin sani sarai kin kuwa san niyar wonka da zakiyi." Cikin tsoron shi ta mik'e ta nufi k'ofar toilet d'in tana tafiya tana juyowa tana kallon shi har ta shige ciki, sannan shikuma ya juya ya tafi masallaci... A hankali rayuwa tayi ta juyawa yana yin zaman General da Meenarl ya fara canzawa wani yana suke rayuwa a ciki kullum dare dukan kwana cikin gida d'aya d'aki d'aya gado d'aya blanket d'aya, sam yanzu General bai yarda da kwana a Jaji dan yana yin ciwon dake damun shi duk daren duniya, Meenarl kuwa har cikin ranta take tausayawa Hamma Aliyu nata halin da yake ciki, yayinda shiko General rayuwar sa ta cika da rud'u tunda zuwa yanzu ya gano tabbas bashi da lafiya sannan ya fahimci halin da Meenarl ke shiga kullun in sun kasannce tare , yana ganin sha'awarta a fili, a zahiri shi da kanshi yasan matuk'ar yaci gaba da zama da ita a haka yana cutar da ita tunda ita da lafiyar ta shiko yasan baida lafiya, abinda yasan da ba haka yake ba tunanin abin na damun shi so amman wazai gayawa tunda shi dai baida wani d'an uwa ko aboki ko amini ko shak'ik'i nashi ba uwa bare ta lura da halin da yake ciki Abban shi ba wani shak'uwa ko sabo a tsaka ninsu tunda basu rayuwa wuri d'aya ba, shiyasa haka yake kunshe da matsalar sa . Ita kuwa Meenarl Hamma Aliyu yana bata tausayi sosai tana bashi kula iya kula.... Yau Asabar tunda su General da captain Sani suka shigo cikin Kaduna Captain Sani ya nufi gidan Alhaji Ibrahim d'an yana son ya kwana aca dan Ramadan da Rayhana sunce da safe zasu zo su sameshi a gidan Uncle Ibrahim d'in zasuyi maganar da tasa suka ki rashin. Tun da Aliyu ya shigo ya samu su Abba da Daddy a babban parlour tare da ya Amir sai Abdul wanda kusan tare suka shigo dan yanzu Abdul ya worke garau tuni yana saka wondonshi yana kuma zuwa ko ina, gefen Abba yaje ya zauna cikin yana yinshi na rashin wolwolah ya gaida Abban sannan ya juya gun Daddy ya gaida shi, ya Amir kuma ya bashi hannu suka gaisa, shi kuwa Abdul sai kallon Aliyun yake cikin yin murmushi mugun ta dan yasan gadar zaren da suka saka mishi ya kuma yi niyar gobe zaiyi abinda zai k'ona zuciyar General wanda harya mutu bazai mance ba d'an ya gama shirin sa sab, shi kuwa Aliyu wanda yana zaune ne kawai a wurin amman ya fara jin kasalar tana rufeshi ga zazzab'i da tsinke war zuciyar da yake kwana dasu kullum. 9:00 pm. dai-dai ya mik'e cikin sanyi ya kalli Abba baki a mace yace. "Sai da safe ." Ido Abban ya tsura mai a ranshi yana jin tausayin d'an nashi tabbas ya fahimci yana cikin matsala toh amman yak'i fad'a ga maraicin rashin uwa da yake gani a k'wayar idon d'an nashi, hakan tasa gaba d'aya shima yanzu baida nitsuwa baida burin d'aya wuce ya nemowa d'an nashi farin cikin sa, kallon Abban yayi cikin kula yace . "Abba kana buk'atan wani abune?." Kai ya juya cikin sanyi yace. "A a ba komai Haiydar ka kula da kanka." "Toh" yace tare da juyawa ya tafi, yana shiga a parlour nasu ya zauna kan 3 str yana jin yadda gab'b'an jikin shi ke macewa suna sakewa igiyar takalmin k'afafun shi yake son kuncewa da bel d'in k'ugunshi ammam ya kasa duk jikin shi ya mace hatta hannushi ya kasa d'agawa, yana ji yana ganin abinda yafi k'arfi ya zamo ya kasa aika tawa, cikin ranshi ya rink'a jin tausayin kanshi da kanshi ya kasa komai sai zuciyar shi dake suya bak'in ciki kamar ya fasa mishi zuciya, a yaune tunanin Ammin shi ya tsanan ta a ranshi lips enshi ya cije tare da tunanin ya tabbata da Ammin shi nan dole zata lura da cewa baida lafiya ya tabbata da zata riga kowa gane cewa yana cikin matsala ya tabbata ko jikokine dashi da Ammin shi zata tallabeshi , baki na rawa ya rink'a magana a hankali yana. "Ammi na banda lafiya ni kaina bansan meke damuna ba Ammi na na rasa lafiya ta bansan meke faruwa da niba Amina ina jin tsoron kar na mutu ban ganki ba Ammi na jikina duk yana shirin mutuwa." Sai kuma ya kife kanshi cikin cije lips enshi tare da furta "Bismillahi" a hakan ya samu ya mik'e yana bin gini ya shiga cikin bedroom d'in. Gaban mirror yaje ya tsaya cikin dafe jikin mirror gaba d'aya ya kasa janye hanna yenshi, Ita kuwa Meenarl tunda tayi sallan ishah ta konta kan sallayar anan bacci ya d'auke ta, cikin baccin can k'asa-k'asa taji muryar Hamma Haiydar d'in. Yana tsaye dafe da mirror jikinshi sai b'ari yake murya a cushe yake cewa. "Meenarl! Meenarl! Meenarl!." Kiranta yake cikin tausawa kanshi da ita dan yasan duk duniya ba mai tai mako shi sai ita gashi ita kuwa yau ta rigashi bacci shiyasa yake kiranta. Ita kuwa cikin baccin ta bud'e ido ganin yana tsaye gaba d'aya jikin shi na b'ari yasa ta mik'e cikin tsoro da tausayawa taje gabanshi cikin rud'u tace. "Hamma Haiydar jinki ko ?." Shiru baiyi magana ba sai idon ya zuba mata cikin cije lips enshi murya na rawa yace. "Meenarl Ammi na Meenarl Ammi na ." Hannushi ta rik'e fuskar cike da k'ollah murya na rawa tace. "Hamma Ali Ina Ammin me kake son tayi maka?." Kai ya rink'a murzawa cikin azaba da tarin damuwa yace. "Meenarl ban san inda Ammi na take ba Meenarl ina buk'atar taima kon mahaifiya ta." Kuka ta rink'a yi cikin kuka tace. " Hamma Haiydar gaya min me kake son in yima." Kai ya rink'a juyawa cikin cushewar numfashi yace. "Meenarl yau ko bel na na kasa kun cewa ko takalmi na na gaza kuncewa kullum ciwo nan gaba yake yi." Gabanshi ta kuma matsowa cikin kuka ta durk'usa k'asa sannan tasa hannun ta fara since igiyoyin but din k'afafun nashi , tana kun cewa ta kuma d'ago tasa hannu kan k'ugunshi ta fara k'ok'arin b'alle bel d'in tana mai sheshek'an kuka tana kuncewa ta jawo wonddon yinifon d'in nashi tayi k'asa dashi, mik'ewa ta kuma yi cikin kuka ta rink'a b'alle boturan rigar tasa saida ta b'alle su duka sannan ta kalleshi ido cike da k'ollah tace. "Hamma Haiydar d'aga k'afafun ka." Kai ya juya tare da cewa. "Meenarl " sai kuma yayi shiru tare da zamewa k'asa kan carpet ya zauna cikin dafe kanshi, ita kuwa tana ganin haka ta zauna tare da jawo k'afafun shi ta d'aura kan cinyarta sannan ta zare mishi ta kalmi tare da wonddon ta kuma Sa hannun ta zare rigar jikin nashi ta barshi daga shi sai gajeren wonddon da bes, sannan ta matso gefen shi ta zauna cikin kuka tace. "Hamma zanje in kira Abba yazo mu tafi asibiti." Shiru yayi cikin zafin rayuwa sannan ya konto ta kanta kan cin yarta ya d'aura kanshi tare da zagaye k'ugunta da hanna yenshi cikin zafin jikin ya rink'a juya kai yana. "Ammi na , Meenarl Ammi ta tafi ta barni tun bansan kaina ba na resa soyeyyar uwa bani da d'an uwa bare y'ar uwa bani da mai tuna halin da nike ciki." Magana yake cikin zubda k'ollah tamkar yaro abinda bata tab'a gani ba, hakan yasa cikin kuka itama tasa hannu ta cikin suman kanshi tare da shafa fuskar sa tana share mai k'ollah dake bin fuskar sa cikin rawan murya tace. "Hamma Haiydar kana da masoya kuma ni nasan halin da kake ciki ina kuma yi maka Addu'a." Haka suka kwana cikin damuwa da k'unci sai asubar fari duk ciwon da yake ji ya bari sai sauran kasalan da yake ji cikin k'arfin hali ya kalli Meenal dake zaune tana tallabe da kanshi , matsota yayi murya can k'asa yace. "Meenarl tashi muje kan gado ki konta kiyi ko baccin awa d'aya ne kafin lokacin sallah yayi." Hannu ta mik'a mai tare da mik'ewa shi kuwa kamo ta yayi suka nufi kan gadon, suna konciya ya lumshe idon shi cikin sanyi yaji Meenarl ta matsoshi kamar yadda suka saba kullum da Asuba sai mak'aleshi tai ta shigewa jikin shi dan ya rigada yanzu ta gama sabawa da salon da yake mata, Shiru yayi cikin tsura mata ido yace. "Minalin Hamma Haiydar ya akayi ne?." baki ta d'an tura cikin sanyi tace. "Hamma nima ban sani ba." Jawota jikin shi yayi cikin bak'in ciki da tunanin yana tauye mata hak'k'in ta tunda ita dai da lafiyar ta, ido ya kuma bud'e wa jin yadda ta ruggumo shi tare da manna k'irjin ta a nashi. Iskan bakinshi ya hura mata a fuskar ta cikin sauk'e ajiyar zuciya yasa yatsa yana zagaye lips d'in ta tare da tsura mata ido, ita kuwa mik'a tayi cikin yin luu da idanun ta , hannu tasa ta kamo yatsar tashi a hankali ta d'aura yatsar kan harshen ta sannan ta rink'a tsotsar yatsar tana lumshe ido, shi kam Aliyu zuciyar sa ce ke bugawa dan tsabar bak'in ciki yana jin tsoron randa zata gaza hakura yana kuma fargaban randa zata gane shi baida lafiya. Cikin tunanin yasa hannu cikin rigarta a hankali yake tura hannun har zuwa kan k'irjin ta , kallon ta yayi jin tana sauk'e wani irin ajiyan zuciya, murya a kasalan ce yace. "Minali na ko in bari ne?." Ido ta lumshe cikin kunya tace. "Hamma k'aik'ayin fa nike ji." Murmushi yayi tare da cewa. "Toh me kike son in miki?." Ido ta rufe cikin tsananin kunya ta zaro hannushi sannan tasa hannu ta zuge zib d'in rigar sai ga k'irjin ta a fili , ido ya lumshe da ya gane nufin ta kawai sai ya manna bakin shi kan b... d'in ta ya fara yi mata salon d'aya saba cikin sanyi, ita kuma sai rumtse ido tayi da sa hannu cikin sumar kanshi.. A haka ya sama mata nitsuwa har saida ta rink'a zubda k'ollah , Sannan ya barta ya tafi masallaci , ita kuwa yana fita itama taje tayi wonka sannan tazo tayi sallah. 7 dai-dai ya shigo ya sameta zaune gaban mirror tana shafa mai tana ganin shi ta rufe idanun ta cikin sauri sannan tace. "Ina kwana Hamma ya jikin ?." Tab'e baki yayi tare da cewa. "Ni lafiya ta lau." Shiru tayi dan dama tasan haka zaice. Shi kuwa wonka yayi cikin sauri-sauri ya shirya tsab sannan ya fito parlour ya sameta ita da Abba suna zaune , bayan ya gaida Abban ne ya mik'e tare da cewa. "Abba bari in wuce Jaji akwai sojojin da zan sallamah zasu tafi borno." "Toh Haiydar Yau ina Sanin naka?." "Yana gidan su Abba nima ba dadewa zan yi ba yanzu zan dawo shiyasa ba sai na tafi da shiba." "Toh" kawai Abban yace, ita kuwa Meenal mik'ewa tayi rik'e da cup d'in tea da sauri tabi bayan shi cikin kula tace. "Hamma Haiydar ga tea kasha kafin ka tafi." Bai kulata ba bai kuma juyo ba, da sauri tasha gaban shi tare da mik'a mishi cup din tace. "Ayyah Hamma Haiydar kasha tea nasan inka tafi baza ka nemi abinda zaka Ciba." Kai ya juya zaiyi magana , tayi maza ta manna mai cup d'in a bakin shi. Ido kawai ya tsura mata ganin yadda ta dago k'afafunta sama tare da d'aga hannu kafin ta samu cup d'in ya isa bakin shi, a haka ta rink'a bashi yana kurba har ya sha rebin tea d'in, sannan yasa hannu ya janye hannun ta cikin kallon juna ya manna mata kiss a goshi sannan ya fice da sauri yana jin dad'in yadda take kula dashi.. Yana fita Nafeesat ta shigo Abba ta gaida sannan ta kalli Meenal cikin murmushi tace. "Meenal yau ne zamuje kitson ko?." Shiru tayi tana tunanin yau dinma bata gayawa Hamma Aliyu ba kuma ya hanata fita kuma gsky tana son yin kitson, Jin tayi shirun ne Abba yace. "Zaku je mama Nafeesatu ai barin kai a tsefen ba dad'i." Cikin jin dad'i tanaga ta samu madafa ko Hamman ta zaiyi fada zata ce Abba ne ya barta, tana happy tace. "Eh zamuje ." Haka kuwa akayi 11:00 na safe suka gama shirin su tsab suna fitowa suka samu Abdul yana shirin fita a motar shi, ganin su ya sashi yin murmushi mugunta cikin mugun nufi yayi... *Sisters wata k'il gob'e bazaku samu ba dan gobe zan koma fatan Allah ya maida in lafiya* By *Garkuwar Fulani* [8/18, 6:26 PM] πŸ’žIt's @lh@jiπŸ’ž: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *BANDIRAWO* pg 3⃣8⃣to4⃣0⃣ Na *Aysha Ali Garkuwa* πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *Damoni na damoni! gidd'o mo fina laramo! gaid'o mo fina sukoyo ladde Allah yama d'um! Kinkid'i kakkad'a! ki d'oidi yalete! yoriki tenete! ki b'ibb'e sammete! b'enduki yamete! Mo Allah hoinani wala ko sad'in ta d'um!* Gunsu kai ya kauda gefe cikin muryar munafurci yace. "Nafeesat fita zaku yine?." Kai ta d'an d'ago ta kalleshi tare da gyad'e mai kai alamar . "Ehh", sannan tace . "Gidan kitso zamu je." Ita kuwa Meenarl kai ta kawar gefe cikin rashin son ganin Abdul d'in dan har ga Allah tsoro yake bata. Kanshi a sunkuye yana k'okarin kunna kid'i cikin motar sa tare da zuge glass d'in motar sama tare da cewa. "Ku shigo in sauk'e ku tunda nima fitan zanyi." Shiru Meenarl tayi tare da tuno Hamma Aliyu yama hanata fitan fa kuma sannan ta fita fitanma kuma da Abdul, itako Nafeesat cikin kula ta kalli Meenarl d'in a hankali ta kamo hannunta cikin yak'ini da karfin zuciya dan ita tanaga har abadan Abdul bazai kuma gigin tab'a Meenarl d'in ba dan ya horu horo iya horo, ita kam Meenarl kai ta rink'a juyawa cikin sanyi tace. "Nafeesat ni bazan shiga motar shiba." kallon ta Nafeesat tayi cikin jinjina kai tace. "Wallahi Meenarl har abadan Abdul zai kasance mai tsoron ya kuma cutar dake kuma gani gaki insha Allah bazai miki komai ba, kuma wallahi Abdul yanzu ya canza kinga yana jin tsoron Hamma Aliyu." Ita dai tsayuwa tayi cikin d'an farga ba, tana ji Nafeesat ta kamo hannuta suka shiga motar, suna shiga suka rufe, shiru tayi cikin jin bugawar k'irji da tsananin firgici da tsoro gaba d'aya zuciyar ta sai duka yake tara-tara. Shi kuwa Abdul lumshe ido yayi tare da sauk'e ajiyar zuciya yana murmushin mugunta da kanne ido a ranshi yake fad'in. "Meenarl kinyi gaggancin shiga motata kinyi wautar saurin mance waye Abdul, Nafeesat kinyi wauta da kike tunanin Abdul zai gani ya k'yale." A haka ya figi motar a 100 suka fito tare da daukar hanyar tudun wada, inda ita Nafeesat bata damu ba don tanaga ai hanyar zata b'ulle dasu inda zasuje d'in, ita ko Meenarl shiru tayi tare da maida hankalin ta kan titi don sam ita bata samu nitsuwa ba kallon titin take da kyau har ta manna fuskarta da jikin glass din ta yadda wanda yake wojema zai ga fuskarta ras, shiko Abdul a ranshi murna yake a nufinshi zaice bari ya biya gidan abokin shi dasu daga nan zai samu ya aiki Nafeesat bakin titin ta seyo mishi katin woya kafin ta dawo kuwa hak'arsa zata cimma ruwa murmushi yayi cikin mugunta da jin dad'in yana mai yarda da kanshi. Gudu yake kamar wanda zaiyi doguwar tafiya gudun yake ba tare daya tuna a cikin gari yake bafa. Gudun yake har ya kamo titin dake bi ta k'ofar gidan gwamnan garin Kadunan ba tare da tuna komai ba ya saki kid'i da gudu kamar mai tashi sama, a haka har ya isa dai-dai wurin da sojojin dake tsaron kofar gidan ba sassauci ya danno kanshi zai wuce ba tare da tuna ya taka doka ba, Captain Garba dake kan titin bai kula da motar tasuba har saida yazo gab dashi karar yadda yake gudun ne yaja hankalin Captain Garban cikin murtuk'e fuska da tsarewa irin nasu na sojojin ya d'ago kanshi tare da sa hanccin bindigarshi yana yin k'asa dashi alamar ya tsaya, shiko Abdul a take tsoro ya rufeshi a zaton shi akan Meenarl yake tsaida shi tunda Meenarl matar ogansu ne ya kuwa tuna sarai randa suka ci ubanshi da duka harda Captain Garban a cikin su, abinda Abdul bai saniba (su kam basuma san akan me General yasa sukayi mishi duka ba a wancan ranar don basu san Meenarl a gun General ba a zahiri sai pictures dinta da General d'in yasa Captain Sani ya reba musu a matsayin ana neman ta ta bata ne, yayin da shiko General har yau bai kalli pictures enba). Shiko Abdul tsoron ko kar Meenarl d'in Captain Garban ya gani yasa yake tsaida shi , yasa yaki tsayuwa sai k'ara gudun da yayi, yayin da shiko Captain Garban Abdul na figar motar ida nunshi suka sauk'a kan fuskar Meenarl dake ta d'an zare ido dan a zaton ta tunda taga sojojin kar Hamma Aliyu yana cikin su, cikin sauri Captain d'in ya juya kan kalandun da suka manna a d'an wurin yana mai kallon fuskarta Meenarl ido ya zaro cikin mamaki ganin tabbas ita ya gani cikin motar nan da ta d'an wuceshi kad'an. Cikin zafin nama ya d'aga bindigarshi sama ya saki harbi 3 a jere hakan yaja hankalin sauran sojojin ganin ogan su na sake harbi, shiko Captain cikin gudu da zafin nama yayi tsalle ya fada cikin hilux d'in su dake Jere a wurin cikin tsawa ya kalli sauran tare da cewa. "Maza Ku shigo Mubi waccar motar." D'aya daga cikin sune ya kalleshi lkcin da suke tayar da moticin yace. "wacce mota d'aya oga ai motocin nada yawa." A fusashe yace. "Waccar black C,R,V d'in can." Aiko cikin sakin sautin jiniya da k'aran bindigoginsu suka bishi a guje shiko Abdul, cikin tsoro da firgici da tsinkewar zuci ya k'ara gudun nashi zuwa 180 gaba d'aya jikin shi sai b'ari yake zufa na keto mashi tako ina dan har ya mutun bazai manta azabar da yasha a hannu wadan nan mugayen sojojin ba gudu yake cikin neman ceton rai, Ita kuwa Nafeesat cikin mamaki ta ke kallon shi baki na rawa tace. "Ya Abdul wannan wanna irin gudune ka tsaya mama ka rege gudun nan a cikin garifa muke zaka kashe mune?." shi dai gudun kawai yake sai zare ido yake yana kuma kallon su Captain d'in ta cikin madubi, ita kuwa Meenarl tuni ta tsinke da gudun da yake kawai sai ta rink'a kuka tare da salati tana. "Wayyo Allah na wayyo Hamma Aliyu shike nan Abdul zai marka d'amu a kan titi dama saida ka hanani fita ashe kasan abinda Abdul yake shirin aika tamin." Shi kam Abdul kai ya rink'a juyawa cikin tsoro yana. "Dan Allah kiyi shiru wallahi ba abinda zan miki Meenarl ki kalli bayan mu sojojine ke bina kuma in sun kamani zasu kasheni." K'ara mai k'arfi Meenarl da Nafeesat suka sake tare da k'amk'ame juna jiki na rawa, dan k'aran fashewar tayarsu da sukaji a lokacin da Captain Garba ya harbi tayar. Fuuuh iskar tayar ta rink'a sacewa Wanda dole motar ta tsaya yayin da ababen hawan dake kan titin kab suka tsaya. Dai-dai lokacin suko sojojin suka iso tun basu gama tsayuwa ba Captain Garban ya diro cikin hilux d'in tare da sa kai cikin motar Abdul d'in, shi kam Abdul tuni yayi mutuwar zaune, ita kuwa Meenarl ba wai tsoron sojojin take jiba dan tasan duk wadan nan bazasu wuce abokan Hamma Aliyu ta bane a zatonta zasu kwace tane daga hannun Abdul, Ita kuwa Nafeesat gaba d'aya ta firgita tana jin tsoron karsu kashe mata d'an uwa. Captain yana bud'e motar ya wani irin rarumo Abdul.cikin zafin nama ya fizgoshi woje, cikin hatsala da tuhumarshi da sace y'ar Alhaji Ibrahim mai dala, ya rink'a zuba mishi maruka ba k'akk'autawa har sai da Abdul din ya zube k'asa daga nan kuma ya rink'a butin dashi a kan titin yana tattakashi, shi kam Abdul zuwa yanzu ba abinda yake sai ihu da neman taimako yana kururuwa, Nafeesat ma da ta fito cikin motar sai kuma take tana . "Ku bar shi me ya muku zaku kashe min d'an uwana." Itama Meenarl fitowa tayi tana zubda k'olloh dan Abdul ya bata tausayi matsosu tayi cikin kukan tana. "Dan Allah karku kasheshi ba kyaufa kisan kai." Shi kam Captain Garba cikin zafi ya cukuikuyo Abdul d'in sannan ya tura shi cikin hilux d'in sannan ya dawo gaban Meenarl d'in ya kamo hannuta ya bud'e gaban motar yace. "Shiga ciki ." Sannan cikin sassaita fushinsa ya kalli Nafeesat tare da cewa. "Zo ki shiga." Cikin tsoro ta shigo sannan ya shiga tare da figar motor suka tafi kai tsaye gidan Alhaji Ibrahim suka nufa yayinda sauran hilux 3 ke biye dasu a baya wanda cike suke da sojojin, tin kafin su isa Captain ya kira Dr Jabeer yashai da mishi sun gano matarsa da ake nema kuma sun kama Wanda suke zaton shine barawon. Shi kuwa Dr Jabeer da yake cikin Zaria cikin asibitin cika tuni ya fito ya nufo cikin Kaduna zuciyarshi cike da farin ciki a d'aya gefen kuma fargaba yake kar dai yaje ya samu ba Ita bace. Shiko Captain Sani suna can cikin gidan Alhaji Ibrahim d'in a inda yake kiran su Ramadan su zo. Su kuwa su Ramadan da Ammi tare da Rayhana Motar su na shiga gidan hilux din sojojin na biye dasu a baya. Shi kuwa Alhali Ibrahim wanda yake tare da yayanshi Barrister Lawan suna Parlour Alhaji Ibrahim din woyar da Dr Jabeer yayi ya shaida musu anga Meenarl kuma yanzu haka ana kawota gida yasa suka fito farfajiyar gidan. Kusan a tare suka firfito cikin motocin suna fitowa Meenarl ta zaro ido cikin tsananin mamaki da kad'uwa ido ta zaro woje cikin rikicewar tunani ta nufi gun Babanta cikin cikar mamaki baki na rawa tace. "Babahhhhhh Babahh." Sai ta kuma kalli Barrister Lawan ido zuru-zuru tace. "Daddyyyyyhh." Baki ta kuma bud'ewa cikin tsantsar farin ciki dan ganin Hajia Amina da Hajia Aysha Wanda suka fito yanzu don jin sautin jiniya a cikin gidan yaki k'arewa. Cikin tsantsar farin ciki ta nufi Hajia Amina jiki na rawa ta fad'a jikinta cikin kad'uwa tace. "Alhamdulillah Momy yau gani a gaban Ku." Sai ta kuma saketa ta nufi jikin Ummin ta cikin dariya tace. "Ummi bakya farin cikin ganina ne.?." Ita kam Nafeesat tuni ta zama tamkar gunki tana sake da baki tana mamakin ina Meenarl tasan wad'an nan mutane?. Ammi kuwa da Rayhana cikin kad'uwa da tsantsar Happy suka nufi gaban Meenarl d'in. Ita kuwa Meenarl tana ganin Ammi ta saki Ummin ta cikin kaunar k'anwar mahaifin nata ta rugume Ammin baki na rawa tace. "Ammi na ina Hamma Jabeer na Ammi ina yake ban ganshi ba." Ita kam Ammi sai dariya take da hamdala shi kuwa Ramadan cikin had'a fuska da yanayin fushi yace. "Bodd'in Bappa wato ni bakiyi kewa taba?." tana jin muryan Yaya Ramadan d'in nata ta juya gunshi cikin murna da salon su na wasan d'an Goggo da y'ar kawu ta mik'a mishi hannu suka tafa tare da cewa. "Kai Yaya Ramadan ai kasan Hamma Jabeer na shima yana sona." Ita kuwa Rayhana ture baki tayi cikin kaunar k'anwar tata tace. "Ai dama ni na sani Bodd'i ni da Hamma Sani baki wani damu da muba." Da sauri ta saki hannun Ramadan ta rugume Rayhana cikin fara'a tace "Anty Rayhana inason ku wallahi duk da bansan Hamma Sani ba ina son shi a raina." Gaba d'aya haka suka cika da tsantsar farin ciki da murna. Nafeesat kuwa ta bushe a tsaye. Abdul kuwa Barrister Lawan yace a dakashi har sai ya fad'i wanda ta saceta tunda shi yace ba shi ya kawo ta garin Kaduna ba. Cikin azaba da rad'ad'i Abdul yace. "Wallahi ni ba satota nayi ba d'an uwanane ya satota shi ya kawota gidan mu san ina ya samota ba yace matarsa ce kuma wallahi zai kasheni in ban maidata gida ba kuyi hak'uri zan kirashi zai zo." Cikin tsawa Captain Garba yace. "Maza kirashi ." Jiki na rawa ya zaro wayarsa dake cikin aljihun wonddon shi ya kira General, Wanda a lokacin ya fito office nashi kenan zai koma cikin Kaduna, kamar bazai amsa kiran ba sai kuma ya d'an zaro woyar a aljihun yinifon d'in nashi , ganin Abdul ne ke kiranshi ya d'an yi mamaki sai kuma ya d'aga kiran tare da cewa . "Uhum." Shi kuwa Abdul cikin kuka da tsoro yace. "Hamma Aliyu zasu kasheni sun kamani sun k'wace Meenarl wai yarsu ce sun saceta Hamma Aliyu kazo karsu kasheni su kashe Meenarl." Cikin tsananin fushi da hatsala yace. "Kai banza kamin bayani su waye ne? kuma a ina suke? a ina suka samu Meenarl d'in? yanzu kuma ina? banza kayi min bayani." Cikin tsoro yayiwa General bayani da kwotoncen gidan, su kuwa Captain Garba tuni sun cika gidan da sojojin da y'an sanda, suna shirin cin uban wannan Hamma Aliyun da Abdul ke kiran. Shi kuwa General cikin zafi da fushi ya kalli yaranshi dake binshi a baya yace. "Tafiya Kaduna zamuyi Ku fito da sauri." Binshi a baya sukayi cikin gudu suka shishshiga motacin nasu sannan suka nufi cikin Kaduna . Shi kam General gaba d'aya a hatsale yake hakan yasa ya gane kwotoncen Abdul amman sam bai tuno da cewar wannan gidan da akayi mashi kwotoncen d'in gidan su Captain Sani bane har suka shiga shiga cikin gidan. Dai-dai lokacin Captain Sani kuma ya fito harabar gidan. A dai-dai lokacin kuma General Aliyu Abubakar Rumoh ya bud'e motarsa cikin cikar haiba da sura ya fito, Tsayuwar motar tasace taja hankalin mutanen wurin baki d'aya, Ramadan da Rayhana kam wani irin farin ciki ne mara adadi ya rufesu yayin da Ammi kuwa tuni ta zuba mai ido fuska cike da k'ollah sai kirjinta dake harbawa. Hajia Aysha kuwa mahaifiyar Meenarl Ummi kenan, ganin Aliyu ya razanata ya cika mata zuciya da zulumi dan tunda yake zuwa basu tana kad'uwa ba, Ido ta zuba mai tana kallon kwayar idanun shi dai-dai lokacin... By *Garkuwar Fulani* [8/18, 6:26 PM] πŸ’žIt's @lh@jiπŸ’ž: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *BANDIRAWO* page 4⃣1⃣to4⃣2⃣ Na *Aysha Ali Garkuwa* πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *La shakkah Moh Allah wuju furd'ata wallahi Moh Allah seini b'uri sembe innu adamajo suna d'um* Lokacin da ya fito ya tsaya fuska a murtuk'e, shi kuwa Abdul yana ganin shi ya mik'e cikin wahala ya nufeshi tare da cewa. "Hamma Aliyu zasu kasheni zasu tafi da Meenarl." Alhaji Ibrahim kuwa ido ya zubawa Aliyu cikin mamaki tare da cewa. "Kana nufin shine ya sacemin yar tawa?." Shi kuwa Barrister Lawan cikin tsantsar hatsala ya kalli tarin sojojin dake gabansu yace. "Maza Ku juya kuje ku canzawa wannan d'an banzan kamannin Ku sumar min dashi asume nakeso ku fita dashi daga cikin gidan nan." Juyawa ya kuma yi a hatsale ya kalli Captain Sani da yake tsaye cikin kullewar kai da cushewar tunani ya zama tamkar wani soko, ido yake bin Meenar da Rayhana yana zaro ido woje shi baima lura da oganshi da ke tsaye ba cikin murtuk'e fuska. Tsawa Barrister ya buga mai cikin takaici yace. "Kai Sani tsayuwa kayi yanzu nake so ku koyawa wancan hankali. Su kuwa sauran zugar sojojin da yan sandan gaba d'aya cikin zafin nama da hatsala suka nufi inda General yake tsaye ya hard'e hannuyen shi a k'irji ya koma ya jingina da jikin motarsa tare da hard'e kafafunshi ya coge cikin isa. Shi kam Abba shiru kawai yayi yana kallon yadda sojojin suka nufi General d'in da gudu, shiko Barrister Lawan cikin fushi yake basu umurnin su bugeshi sai sun sumar dashi. Suko sojojin da sukazo da General sun san duk masu nufo kansu d'in yaran General d'in. Ita kuwa Ammi hannu tasa ta dafe k'irjin ta fuska cike da k'olloh gaba d'aya jikinta na rawa, Shiko Ramadan wurin General d'in shima ya nufa Rayhana kuwa Ammi ta matso cikin rawar murya tace. " Ammi kin ganshi ko kinga Hamma Haiydar d'in ko." Itako Meenarl gaban Umminta ta koma tana kallon yadda Ummin ke juya kai tare da kad'uwa. Gaba d'aya sojojin suna zuwa gaban shi suka yi wani irin tsayuwa a tare cikin mugun tsoro suka d'ad'd'aga hannu suka sara mashi tare da buga k'afafunsu a k'asa, ji kake rib-rib suna "yes sir ". Mamaki ne ya rufe Barrister ganin duk sunje suna saramishi sun k'ame k'am sun tsaya a gaban shi cikin yana yin suna jira ya basu umurni su aikata. Shi kuwa Captain Sani da Captain Garba sai ido suka tsurawa juna cikin tsoro, Barrister kuwa ganin Sani na tsaye gim yasashi hatsala cikin fushi ya juya gun Sani da Garba yace. " wai shi waye shi da Ku sojoji bazaku aikin ku a kanshi ba ko shi yafi k'arfin doka shine fa ya sace Amina, shiwaye a k'asarnan?." Cikin yin k'asa da murya Garba yace. "Shine Brgdl General Aliyu Abubakar Umar Rumoh soja mai kula da rund'unar sojojin na k'asa baki d'aya." Tsaki Barrister yaja cikin takaici yace. "Wannan mai halin sace yayan mutane shine wai aka bawa wakilcin tsaron wannan k'asa tamu?, an bashi daman aikata b'arna son ranshi, yaro ne aka d'auki wannan matsayi aka bashi ba dole ya maida mata abinda yaga dama ba, tunda ya samu dama ga k'uruciya ga matsayi ga kud'i ga kyau ga rashin mafad'i dan wannan da ganin shi zaiyi taurin kai da izzah." Shi kam Sani baki ya sake cikin mamaki da rashin ganewa yace. "Daddy General me yayi muku?." Cikin tsawa Barrister yace. "Shine ya sace Amina yar uwarka banza mara tunani kana tare dashi baka San ya sacema yar uwa ba." Ido ya sake fiddawa cikin rud'u yace. "Daddy ina Aminan take?." Zuwa yanzu Barrister ya gama hatsala cikin fushi ya yarfawa d'anshi Captain Sani wani irin gigiceccen mari tare da janyo hanna yenshi fiii har zuwa gaban Meenarl dake tsaye gaban Ummi, cikin nuna Meernal d'in Daddy yace. "Sani ga Aminan gatanan itace Aminar itace yar uwarka da muke ta nema itace yar d'an uwana Ibrahim wacce take Gembu Membila." Kai Captain Sani ya rink'a juyawa cikin zama wani soko yace. "Daddy wannan itace Amina yar uwata?." Kai Daddy ya gyad'a mai tare da kallon Meenarl wacce ta tsurawa Sani da Daddyn ido fuska cike da alamun tabbaya, shiko Barrister cikin kula yace. "Amina ga d'an uwanki Sani wannan shine Hamma Sanin naki." Ido suka tsurawa juna cikin mamaki shiko Sani tsoro da firgicin me zai faru anan gaba kad'an, naunauyan ajiyar zuciya ya sauk'e ido cike firgici baki na rawa yace. "Daddy kenan Amina itace Bodd'in Bappa sannan itace Meenarl matar ogana General Aliyu Abubakar Umar Rumoh?, Daddy ya akayi haka ta kasance ina mafita? sannan kuma Amina itace watar Hamma Jabeer na? Daddy kaina kulle na rasa tinanina kamin bayani." Ido Daddy ya tsura mai cikin jin haushin d'an nashi yace. "Sani kana nufin dama kasan inda Amina take har kana cewa matar oganka ne?." Kai ya gyad'a tare da cewa. "Ehh Daddy nansata muna tare da ita tun randa aka d'aura aurenta da General." A hatsale Daddy ya rink'a yarfawa Captain Sani maruka masu zafi da gigitarwa har sai da hankali mutanen wurin kab ya dawo garesu. Sannan Barrister yace. "Ashe baka da imanin d'an uwana da taka yar uwar da d'an uwanka kana sane Ibrahim har ciwon zuciya ya kamashi sakamakon batan wannan yarin yar sannan kana ganin halin da d'an uwanka ke ciki. amman wai kana cemin kuna tare wuri d'aya ka barmu cikin rud'u har kuma kana cemin matar ogan kace ita, waye aura masa ita su waye masu aurar da ita a duniyar nan bayan mu, ya sato yarinya yazo yana cema matarsa ce." Dafe fuska yayi cikin rawan murya yace. "Daddy ka manta ni bansa Amina ba ban tab'a zuwa garin da takeba kuma ko pictures d'in ta tun nayarin tane na sani." Mari Daddy ya kuma watsa mishi cikin nunashi da yatsa yace. "Kalli fuska Rayhana ka kalli fuska Amina ko makaho in yashafa yasan yan uwane , Amman da yake kai kifeffen mutum ne mai karamar basira ka kasa gano hakan , sannan inma baka gane da kamannin su ba , Ina pictures d'in Amina da aka baku d'an nemota suma duk basu ganar da kai ita bace?." Kai yaci gaba da juyawa tare da cewa. "Daddy wallahi tallahi ban tab'a lura da kamannin Rayhana da Amina ba sai yanzu da ka fad'a, batu pictures d'inta kuma wallahi tallahi Daddy ban kalli pictures d'in ba d'an muna fita na bawa General su a hannushi kuma shima wallahi bai gansuba d'an a hannun Captain Garba ya dank'a hotunan." Alhj Ibrahim ne ya rik'e hannun Barrister sanda ya d'aga hannu zai kuma yarfawa Sani mari cikin damuwa da kullewar kai yace. "Yaya Lawan barshi haka wannan magana akwai rikici a cikin ta dole mu barshi ya mana bayani a hankali." Ita kam Meenarl sai ido take zarewa cikin mamaki , Ammi kuwa kuka kawai takeyi jin wani rikicin da ya had'e da d'anta da yar d'an uwanta ido take rumtsewa jin mugayen furucin da yayanta Lawan ke yiwa d'an nata sai kuka take tare da sheshshek'a Rayhana na share mata k'ollah itama fuskarta cike da hawaye , Ita kuwa Ummi mahaifiyar Meenarl kuka takeyi tare da nuna General tana. "Wayyo Innata ina kike zoki ga wata fuska mai cike da kamannin fuskar da kike begen ganin tsawon shekaru." Ammi kuwa zuwa yanzu ta durk'usa har k'asa tana fidda sautin kula mai cike da k'unan rai. Shi kuwa General cikin tsuke fuska ya d'aga hannu tare da yiwa zugar sojojin alama su bashi hanya, a take suka yi layi tare da sara mishi. Taku d'aya yayi zuwa biyu yaci karo da Ramadan dake nufoshi cikin tsuke fuska ya tab'e baki tare da ci gaba da tafiyan , shiko Ramadan binshi yayi a baya cikin sanyi kamar rad'a yake cewa. "Hamma Haiydar ni d'an uwanka ne! ni jinin kane! kalli can gacen mahaifiyarmu! da yar uwarmu Rayhana! Hamma Haiydar ina mahaifinmu? Hamma Haiydar nida Rayhana muna begen mahaifinmu." Shiru yayi cikin son yaji abinda yaron ke fad'a da kyau d'an bai jishi da kyauba. Shi kuwa Ramadan matsoshi yayi cikin sanyi zayyi magana kenan, ita kuwa Meenarl ta juyo garesu, cikin mamaki ta nufu gaban General cikin d'an d'aga murya tace. "Hamma Haiydar kazo?." Ido kawai ya tsura mata cikin mutuwar jiki dan kamannin Rayhana da Meenarl din ga maganganun wanna yaron da suke tsananin kama dashi. Tana isa inda yake hannu shi ta kamo cikin happy tace. "Hamma Haiydar zo zokaga mamana da babana ga zuriyata baki d'aya Hamma Haiydar ashe Captain Sani Yaya nane d'an uwanane shi shine Hamma Sani na k'anin Hamma Jabeer d'ina gacan goggona k'anwar mahaifi na ga Yaya Ramadan da Anty Rayhana." Su Alhaji Ibrahim da Barrister kam da Hajia Amina binsu da ido sukeyi cike da mamaki. Dai-dai lokacin Dr Jabeer yayiwa harabar gidan diran mikiya cikin wani irin yanayi yayi parking, marfin motar ya bud'e tare da fita da sauri tin kafin ya k'arisa fitowa yake kiran Meenarl yana. "Bodd'i na inaki ne bangan ki Bodd'i na Hamma Jabeer naki ne ke kiranki." Gaba d'aya hankalin su ya koma kanshi , ita kuwa Meenarl cikin tsananin happy ta sake hannu Aliyu tare da yin tsalle da gudu ta nufi inda Dr Jabeer yake , tana zuwa ta mik'a mishi hannu , shima hannun ya mik'a mata tafin hannun su suka had'e wuri guda Dr Jabeer d'in yasa yatsunshi ya rumtse nata da k'arfi lokacin d'aya kuma suka yi.. Shi kuwa General idonshi ya rumtse da k'arfi...... By *Garkuwar Fulani* [8/18, 6:26 PM] πŸ’žIt's @lh@jiπŸ’ž: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *BANDIRAWO* page 4⃣3⃣to4⃣4⃣ Na *Aysha Ali Garkuwa* πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *Wannan shafi sadaukar wane ga mahaifiyar y'ar uwarmu (Feedo Deedo y'ar ficika) Allah ya jik'an Ummah Allahu yasa ta huta muko in tamu tazo Allah yasa mu cika da imani* *Resa tum! mara tum! heb'a tum! seya tum!* *Happy birthday 2 youuu my lovely Sadnaf Allah ya k'aro shekaru masu albarka* Sai ya kuma bud'e idon nashi ya tsurawa Meenarl da Dr Jabeer d'in ido. Shi kuwa Dr Jabeer jawo hannun Meenarl yayi suka d'an sunkuyo sai yasa hannu shi ya d'an ja k'afan wondoshi ya d'an nad'e tare da cire takalmin k'afar, itama cire takalmin tayi sannan ta d'an janye siket d'in ta sama kad'an ta rik'e da hannu d'aya, matsota Dr Jabber ya kumayi tare da manna k'afarsa da tata k'afar suka dai-dai ta yatsun k'afafun nasu, hannuta da yake cikin nashi ya kara rumtsewa tare da juyowa suka kalli juna murmushi yayi cikin wasa da kulawa da yanayin da suka saba duk randa suka had'u sai sunyi haka sannan su nad'e k'afa d'ad'd'aya sama kad'an sai su d'an yi taku biyu zuwa uku cikin sigar wasa da shak'uwa. Ita ma murmushi tayi tare da cewa. "Hamma Jabeer inka fad'i sweet lede-leda zaka seyo min." kai ya gyad'a mata sannan cikin wasa suka d'aga k'afafun nasu a tare sukayi taku d'aya ana biyu suka dire tare da sauk'e ajiyan zuciya sai kuma ya juyo gareta ya mik'a mata hannun suka tafa tare da yin murmushi. Wannan itace d'abi'ar Dr Jabeer ko ince al'ada matuk'ar suka had'u sai sunyi wannan abin dan Dr tuk'uru yake biyewa Meenarl ya zama kamar abokin wasanta na yarinta. Suna yin hakan sai ta kuma jawo hannu shi da k'arfi har kamar zai fad'o kanta cikin tura baki da salon wasa tace. "Zo nan Hamma Jabeer zo muje ku gaisa da Hamma Haiydar." Dariya Dr yayi tare da cewa. "Wayyo Bodd'in Bappa kinyi k'arfi har zaki kada Hammanki a k'asa." Sai kuma ya kalleta yadda take janshi tana ta dariya har dimful dinta dake tsakiyar d'an gemunta yana lotsewa. kallon ta Dr yayi cikin kula da tsantsar farin ciki yace. "Har wani Hamma Haiydar kika samu bayan mu duk bamu isheki bane?." Ita dai janshi tayi har zuwa gaban General wanda ke tsaye tamkar an dasashi ko ido ya kasa k'eftawa mamaki cike a ranshi "ashe dama Meenarl tana dariya haka? ashe tana da surutu? ashe ita mai faram-faram ce? , kenan shine ya maidata shiru-shiru kenan shine ya cika zasuyar ta da tsoro ta zama ko yaushe a firgice take. Su Barrister kuwa da Abba ido suka zubawa General da Ramadan dake tsaye gefen shi kamar su ta k'ara fitowa ras. Shiko Dr Jabeer yana zuwa cikin happy da yanayin godiya da jinjina ya mik'awa General hannu suka gaisa shi a zatonsa General ne ya gano mishi Meenarl d'in, shiko Aliyu hannun kawai ya bashi cikin sakewar jiki yake binsu da kallo yana sauraron abinda Dr yake fad'i. " A gaskiya General Aliyu bani da baking yi maka godiya ko nuna farin cikina a gareka ba abinda zance da kai saidai ince Jxkllahu bil jannah nagode ka gano min matata farin cikina." Ido ya kuma fitarwa woje baki cikin sanyi yace. "Matar ka? matarka kuma?." Hannun Meenarl Dr Jabeer ya kuma jawowa cikin yanayin farin ciki yace. "Eh matata ce kuma k'anwa tace jinina ce ita kuma tintini an d'aura mana aure da ita." Cikin murtuk'e fuska da b'acin rai ai shi a ganin shi wannan ma ai rainin hankali ne tunda dai shi yasan Meenarl aurenta aka d'aura mai kuma mahaifinta ne ya auramai ita kuma a can taraba cikin dajin gembu Membila iyayenta fulanin daji masu kiwon shanu ma zauna cikin riga, sannan ya kuma za ace ga wasu sabbin iyaye wai natane me ya had'a Taraba da Kaduna me ya had'a babarbare da ba fillatani tinda yasan Alhaji Ibrahim su barebari ne. Tsaki ya ja da tuna wad'an nan abubawan, cikin tsawa da hatsala yace. "Kai Captain Sani zonan." Shiko Captain Sani ido kawai ya zaro d'an tabbas yasan ya shiga tsaka mai wuya sannan duk ta inda ya motsa shine shi kuwa yasan lallai anyi aure kan aure, ciki bin umurni ya matso inda General d'in ke tsaye ya coge sai kad'an yar k'aramar bindigarsa yakeyi. Ita kuwa Ummi jin sautin muryar General ya k'ara tsananta bugawar zuciyar ta tana tuno woni sautin murya irin na General sak hawaye ne ya k'ara wonke fuskarta tuno tun tana k'arama rebonta da jin wannan muryar. Ammi kuwa cikin kuka ta d'ago fuskarta tana kallon fuskar d'an nata cikin kuka ta rik'o hannun Rayhana tare da cewa. "Rayhana kalli fuskar d'an uwanku ji muryarsa ki kalleshi da kyau Rayhana dan komai nashi na mahaifinku ne ba abinda ya rabashi da Abbanku, farinshi tsawonshi fuskarsa muryarsa gashi kanshi sajenshi fushinsa komai nashi na mahaifinmu ne." Ido Rayhana ta zuba mishi cikin kuka tace. "Ammi kenan Ramadan ma da Abban mu yake kama?." Kai ta gyad'a mata cikin kukan. Shi kuwa General Captain Sani na zuwa gaban shi ya juya cikin fad'a ya kalli Captain Garba da muryar bada umurni yace. "Kai Captain Garbage maza kwashi wad'an nan zugar sojojin da ka kwaso kayi woje dasu." "Yes sir" Captain Garba yace tare da juyawa ya kalli sojojin yace. "Ku shiga mu tafi." Shi kuwa Captain Sani kai kawai ya sunkuyar cikin goga k'afarshi a k'asa, shiko Dr ido ya tsurawa General ganin yadda ya murtuk'e duk annurin fuskarsa ya bace, sannan ga Meenarl da ya ganin ta wani Sha jinjin jikinta ta nitsu a gaban shi tana wasa da yatsunta, a d'aya gefen kuma hankalishi ya tafi kan Amminshi goggon shi k'anwar Daddyn shi kenan can kuma ga Ummi dake kuka tana kallon fuskar General d'in. Shi kuwa General lips enshi na k'asa ya kamo ya matse lokacin da yaga sojojin duk sun tafi sai shi da Abdul sai mutanen gidan, cikin tsuke fuska ya kalli Captain Sani da yayi k'asa da kanshi rai a bace yace. "Captain!." Shiru Sani yayi dan a wannan yana yin fuskar General yana bashi tsoro , shiko General jin bai amsa mishi ba ya hatsala shi cikin zafi ya ware hannu shi ya zabga mishi wani gigiceccen mari. Cikin zafin Marin Captain ya d'aga kai murya a d'an sake yace. "Na'am." Meenarl ya nuna tare da cewa. "Wannan wacece a gare ka ? kuma me had'inta da zuriyar Ku? me ya had'ata da yayanka Dr Jabeer? asani nadai Ku musulmaine ni kuma musulmi ne! amman kaji Dr yana cewe Meenarl matarsa ce? me ya had'a Taraba da Kaduna? meya maida matataaah matar Dr Jabeer?." shi kam Captain Sani ya rasa bakin magana sai kai yake juyawa, hakan ya hatsala General yasa shi ya rink'a zuba mishi maruka yana. "Ina magana kana jina kayi shiru ko wani munafurcin ka koyo." Barrister Lawan kuwa dashi da Abba da sauri suka zo Abba ne ya kamo Captain Sani shiko Barrister cikin fushi da b'acin rai yace. "Kai wanne irin tantirin ne? dame kake gadara? da zakazo har gidan da kasace musu yarsu sannan kana dukan d'an gidan shin matsayin hauka ne dan kai General ne sai ka taka wanda make so dan rashin tarbiya toh ka sani da Barrister Lawan kake ja ba sai na gaya maka ba duk mara gaskiyar k'asran tsoro yake a had'a shari arsa da ni bare kai da na kamaka dumu-dumu kasace min yar d'an uwana". Daga nan cikin b'acin rai Abba ya jawo hannun Meenarl tare da nunata yace. "General Aliyu wannan y'atace nine ubanta mahaifi." Sai kuma juya yanuna Ummi tare da cigaba da cewa. "Gacan maihaifi yarta, inda kaje ka sace min y'ata kuwa gidan kakanninta ne ma haifan Aisha." Cikin fushin ya bawa General labarin yadda ya auri Aisha da kuma sanadin zaman Meenarl a can sannan ya karishe maganar da cewa. " kuma na aurawa Jabeer ita yanzu a matsayin matarsa take." Kai General ya rink'a juyawa tare da bugawa Captain Sani tsawa yace. "Kai Sani Meenarl wacece a gareni????." sannan ya kamo hannun Meenarl ya fizgota.... *Kuyi da wannan hak'uri sisters da nayi niyar yin mai yawa so inada wani uzurine* By *Garkuwar Fulani* [8/18, 6:26 PM] πŸ’žIt's @lh@jiπŸ’ž: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *BANDIRAWO* page 4⃣5⃣ Na *Aysha Ali Garkuwa* πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *Moh Allah hokki b'uri moh baba hokku* *Masu tabba yata menene ma,anar BANDIRAWO? toh ga ma'anar BANDIRAWO na nufun D'AN UWA ko Y'AR UWA duk yana d'aukar ma'anar BANDIRAWON* Kusa dashi cikin tsawa yace. "Meenarl dai matata tace! kuma matar auren sunnah aure na halal kuma da waliyinta wanda shine madadin uba a gareta kuma aurene da aka d'aura da shaidu kuma ga Sani wanda ya kasance d'aya daga cikin manyan shaidun, batun y'ar kuce jikar Bappa ce ni duk bansan da wannan zancen ba, dan amanarta aka bani Bappa ya bani amanarta cikin k'arfin guiwa da yak'inin zan rik'e amanar shi yasa ya aura min ita." Captain Sani ya kuma fuzgowa cikin hatsala yace. "Shin Sani kurma ka zama ne ko ka manta lokacin da ka mik'a kudin sadikin Meenarl da hannun ka?." Kai Captain ya rink'a juyawa cikin sanyi ya kalli General yace. "Kayi hak'uri oga tabbas ban manta ba tabbas lillahi ni shaida ne kan aurenka da Meenal." Sai kuma ya juya gun Daddyn shi tare da kallon Abban Meenarl d'in yace. "Daddy kuyi hak'uri wallahi tabbas General ba sace Meenarl yayiba aura masa ita Bappa yayi kuma aure na suna bisa koyarwan Annabin mu, Daddy kune kukayi kuskure kune kuka d'aura aure akan aure Daddy General Aliyu ba mutumin banza bane kamar yadda kuke zaton ba, Daddy ka tuna alkhairan General a kaina, Daddy kasan General mai mutunci ne a gareni." Shiru Captain yayi tare da tsurawa iyayen nashi ido cikin fahimtar wa, amnan ina sunyi nisa bazasu gane ba, Shiko Dr Jabeer cikin tafasan zuciya ya kamo hannun Meenarl ya fizgota jikin shi cikin tsawa da harzuk'a yace. "Kuji zancen banza maganar wofi General zaifi ma kyau kaja motarka kabar gidan nan, dan fad'a kake cikin rashin gaskiya dan Bodd'i tawace matata ce, in kai a sama ka sameta ni tun tana yar Babynta nake rainonta." Hannu shi ya d'aura kan k'ahon zuciyarshi tare dacigaba da cewa. "Meenarl da kake fad'i itace bugun zuciya taπŸ’— tun tana k'arama nake dakon sonta a zuciya ta k'anwata ce matata ce." Daddy ne ya kalli General a fusace yace. "Ina fatan dai kasan nan ba gidan ubanka bane ? so don haka ka b'ace min da gani yaro ba tarbiya ancema yarinya yarmuce ka tsaya kana zuba mana rashin kunya." Abba ne ya kalli General cikin takaici yace. "Aliyu Meenarl y'atace kuma nine ubanta kuma ni zan aurar da ita nike da hakk'in zab'a mata miji." Sannan ya juyo ya kamo hannun Meenarl ya rik'e tare da cewa. "Y'ata zomu tafi." Janta yayi suka nufi cikin gida ita kuwa Meenarl sai juyowa tayi tana. "Abba Hamma Haiydar baida lfy fa Abba d'an Allah Ku kaishi asibiti, Hamma Sani kai kasan baida lafiya dan Allah ka gayawa Abban shi akaishi asibiti." Sai kuwa ta juya gun Dr Jabeer dake binsu a baya tace. "Ayyah Hamma Jabeer ka duba Hamma Haiydar wallahi baya da lafiya." Ammi kuwa zuwa yanzu sautin kukanta ya cika wurin ita kuwa Ummi baki na rawa ta tsaya gaban mijinta da yarta cikin sanyi tace. "Wallahi Abban Bodd'i, Aliyu mijin Bodd'i ne tabbas aurenta Bappa ya d'aura kubi abin nan a hankali." A take fuskar Abba tayi jazir dan b'acin rai a fusace yace. "Toh ya sakar min yata yaje ya rubuta mata takardar sakinta yaron da bansan iyayenshi bane zan bashi auren y'ata waya san asalin shi tunda iya sanina ba a gaban iyayen shi yake ba." Da k'arfi General ya rumtse ida nunshi cikin tarin bak'in ciki gaba d'aya ranshi ya gama b'aci da zafin furucin da Alhaji Ibrahim da Barrister ke mishi, lips enshi ya ciza cikin tafasar zuciya ya juya tare da damk'e hannu shi yace. "Ni dai ba shege bane! ina da asalina! ina da ubana! kuma ni musulmi! ne kuma ni ba tantiri bane! kamar yadda kuke fad'an! kuma ni ba b'arawo bane! bare na sace muku yarku! ga d'anku Sani shi shaida ne a kaina! ba saceta nayiba!, Meenarl kema kina sane ba saceki nayi ba?! Bappa da kanshi ya dan k'amin hannu ki a cikin nawa!, dan Allah Barrister karka sake cemin bani da asali! ina da Ubana! kuma ya raine ni! Uwata kuwa mutuwa ce ta rebani da ita!!." Zuwa yanzu nufashin Sa ya fara fizga cikin zafin rai ya fizgo hannun Abdul murya na carkewa ya nuna Abdul tare da cewa. "Ko a nan wurin ina da d'an UWA! gashi nan ba gidan marayu na rayuba! Captain Sani kai kasan hakan!!!." Cikin zafi da cushewar zuciya ya bud'e motarsa tare dasa Abdul a ciki shima ya zagaya ya shiga ma zaunin direba cikin zafi ya fizge hannu shi da Ramadan ke rik'e dashi yana kuka kamar yaro cikin kukan yake cewa. "Hamma Haiydar kana da UWA mahaifiyar ka bata rasuba tana raye Hamma Haiydar ba Abdul kadai bane d'an uwan ka a nan nima d'an uwanka ne ga Rayhana ma y'ar uwarka ce Hamma Aliyuuu ga Ammin mu tana raye Hamma Haiydar Meenarl d'in kanta y'ar uwarka ce." Ina General tuni ya rufe motar ya figi motar a guje yayi woje k'iris ya rege ya taka mai gadin su gaba d'aya inda nunshi sun makan ce zuciyar sa ta cushe ba abin da yake cewa sai. "Ammi na Meenarl Ammi na Meenarl itace ta fara cireni a halin da nake ciki na rashin ki, itanma rashin ki ya jazamin rashin ta." gudu yake kamar zai tashi sama. Shi kuwa Ramadan ganin General ya fita ya sashi sakin kuka kamar yaro cikin kukan yazo ya durk'usa gaban Abba da Hamma Jabeer sai ya saki wani irin kuka cikin muryar kuka yace. "Ammi kiyi hak'uri ki gafar ceni nasan abinda zan fad'i zai b'ata miki rai yau zan gayawa su Abba gaskiya." Cikin kukan Ammi ta mik'ewa tazo gaban su cikin juya kai tace. "A a Ramadan a a." Kai ya juya cikin zubda k'olloh yace. "Daddy kun ganin ko Abba kalli yadda y'ar uwarku ke kuka da zubda k'ollah kalli har kamar numfashin ta zai yanke, Daddy shin kasan waye General Aliyu ? Abba,General Aliyu Yaya nane d'an Ammi nane shine d'anta na fari wanda ta haifa a gidan Abban mu shine d'an da kuka rabashi da uwarshi tun yana d'an shekara 4 zuwa 5 gashi da kunnen Ku kunji yana fad'in mahaifi yarshi ta rasu alhalin gata a gaban shi Amman bai ganeta ba kun rab'a UWA da d'anta dan laifin Abban mu ya saketa." Ammi kam sai kawai ta yi cikin gida tana kuka cur-cur da hawaye, shi kuwa Dr Jabeer cikin b'acin rai da tarin tausayin Ammin nashi yabi bayan ta. Daga nan gaba d'aya suka shige cikin gidan, A babban parlour Dr Jabeer ya samu Ammi tana zaune kan 1 str tana zubda k'ollah yana zuwa gaban ta ya durk'usa cikin tsura mata ido yasa hannun shi ya goge mata k'ollah baki na rawa yace. "Ammi ke k'anwace ga mahaifi na Amman duk wani gata da UWA keyiwa d'anta ke kinyi minshi tabbas ni nasan kina da wani d'an mai suna Aliyu Ammi wai da gaskene General Aliyu shine d'an uwana Aliyu da kike fad'a min?." Hannun Dr Jabeer ta rik'e murya na rawa tace. "Jabeer General Aliyu d'an uwanka ne ka tuna fuskarsa ka kalli fuskar Ramadan." Cikin sanyin jiki Abba da Daddy suka zauna jiki a mace Abba kam sai juya kai yake yi. Captain Sani kuwa Kuka yake kamar ba soja ba tamkar yaro k'arami yana juya kai ya kalli Meenarl yace. "Habba ashe Hamma Haiydar d'an uwana ne jinina ne shi Meenarl ashe ke jinin Hamma Aliyu ne shi yasa mukeyiwa juna wani irin kauna ashe kula da kauna da Jana a jiki da Hamma Haiydar yakeyi ni d'an uwanshi ne shi yasa." Gaban Daddy ya rarrafa yaje cikin kukan yace. "Daddy General Aliyu akan Meenarl ya kusan nak'asa wannan d'an uwana nashi duk da su basa son shi amman General shi maison y'an uwanshi ne, Abba kune sana din sa General cikin kad'aici a rayuwar sa, kullum sai yayi kukan rashin mahaifiyar shi ashe kune kuka maida shi maraya, kalli ratar dake tsaka nina da General amman ba tare d'aya duba matsayin shiba ya jani jikin sa Daddy kasan cewa a mata kan soja Aliyu yana mataki na 8 niko ina mata ki na 3 shi General ni Captain amman ya zabeni a matsayin mai kasan cewa tare da shi." A haka cikin kuka Captain Sani ya basu labarin tun zuwan su Gembu Membila har abinda ya faru tsakanin Abdul da Meenarl har yadda Mama ke cuszuganawa General d'in da yadda yayi ta lura da Meenarl da bata kariya har zuwa kan ciwon da yake kwana dashi. ya k'ara da cewa. "General bashi da kowa ba wanda yasan halin da yake ciki nima Meenarl ce ta gaya min sai kuma lura dashi da nakeyi." Ramadan ne ya mik'e cikin kuka yace. "Ammi kiyi hak'uri Daddy Ku gafar ceni nagode da kulawar ku nasan zafin abinda Abban mu yayiwa Yar uwarku ne yasa kuka k'i yafe mishi, toh ni kam da Rayhana mun yace mishi kuma ni zan tafi gun mahaifi na da d'an uwana zanje na kula dashi zanje na jinyacesa zanje na d'ebe mai kewa zanje in cireshi cikin kadaici zanje na gaya mishi Ammin shi tana raye kuma tana sonshi." Daddy kam shiru yayi cikin kuny'ar uwar tashi shiko Abba tuni sai k'ollah yake dan dama Barrister ya fishi zafi. Ita kuwa Meenarl tuni ta koma jikin Hajia Amina ta rakub'e sai sautin kukanta dake tashi, Dr Jabeer kuwa hannun Ammi ya rik'e cikin lallashi yace. "Ammi kibar kuka insha Allah farin cikin ya dawo gareki." Ummi kuwa kuka take tana maison kara ganin fuskar General sai yanzu ta gano dalilin da yasa take son Ramadan ashe kama take ganin yanayi da d'an uwanta amman sai yau taga kamar da tafi na Ramadan d'in, cikin kukan ta bawa Alhaji Ibrahim labarin yadda sukayi da Bappan ta kuma fad'i dalilinta na hana Bappa ya gaya mishi. Ramadan kam juyawa yayi ya mik'a wa Rayhana hannu cikin sanyi yace. "Rayhana muje ga d'an uwanmu yana buk'armu a kusa dashi." Hannu ta mik'a mishi suke nufi woje Captain Sani ma mik'ewa yayi cikin share k'ollah a fuskar shi yace. "Daddy nima zan bi su Ramadan zanje gun Hamma Haiydar." Shiru iyayen nasu sukayi har suka fita basuyi ko motsiba. Kai tsaye gidan su General suka nufa, suna zuwa bak'in k'ofar get d'in Captain Sani yayi ta dannan hon Amman shiru mai gadin ya lek'a sai ya koma ya share su cikin hatsala Captain ya fito yazo inda yake yace. "Sajen ka bud'e min get." Cikin girmamawa Sajen din yace. "Oga yace kar a sake barinka ka shiga gidan nan." Kai ya kad'a cikin tausayi dan yasan yau ba mai tausar General d'in , su Ramadan kuma da ya gaya musu cewa sukayi . "Mu banza mubar k'ofar gidan nan ba wallahi anan zamuyi ta zama har sanda zai fito." Haka kuwa suka coge a k'ofar gidan har zuwa dare in lokacin sallah yayi suyi sallah a masallacin k'ofar gidan. Ita kuwa Meenarl Dr Jabeer ya tare a gidan yana ta cikata da salon wasan d'aya saba tuni ta sake suna ta hira da dariya Ammi kuwa yayunta sunyi ta lallashin ta duk da hakan, ita kam Ammi har yanzu hankali ta na kan d'an ta. 10:00 pm Meenarl dake zauna gaban Hajia Amina da Ammin , tayi wani irin razana cikin zaro ido ta dafe kirji gaba d'aya jikin ta na rawa tace. "Momy Hamma Haiydar wallahi daga yanzu ciwon shi ke tashi." Shiru Ammi tayi tare da sunkuyar da kanta k'ollah na zuba. Hajia Amina ce tace. "Insha Allah yau zai samu sauk'e kinga Dr Ramadan yana can gun shi." Ita dai kife kanta tayi cikin cinyoyin ta. Shi kuwa General Aliyu tunda ya figi mota ya fito gidan su Meenarl ko idanun shi basa ganin cikin ikon Allah ya kawosu gidan lafiya, yana yin parking ya bud'e mota ya nufi cikin gida yayin da Abdul kuwa ke binshi a baya cikin tausayawa hak'ik'a yau zuciyar shi ta cika da tausayin d'an uwan nashi a fili yace, "Hamma Aliyu Allah ya kawo ma farin ciki a rayuwar ka." Shi kuwa General yana shiga gidan kai tsaye part ensu ya nufa a parlour su ya zame cikin kuncin rayuwar ya kife kanshi kan kujera ya rink'a kiran. "Ammi! Ammi! Abba! Abba! me yasa baku tuna makomata ba gashi a yau an wayi gari ana shirin shegan tani, Ammi na me nayi mik'a ni kuwa da kika manta ni, kin barni na rayu tamkar maraya." Haka ya rink'a kuka kamar yaro gaba kad'an yau kewar Ammin shi ya zame mai sabo fil a parlour ya wuni cikin kunci sallah kawai ke tayar dashi daga parlourn. 10:00 pm ya fara jin kasalar tana rufeshi a take sai ga zazzab'in ya rufeshi ciwon ciki ma yace bismillah sai rawan sanyi yake. Kanshi ya kifa kan gadon cikin azaba da tausa yawa kanshi murya na rawa yace. "Meenarl bani da lafiya Jabeer shi ya dace da ke me ribata in na zauna da ke bayan nasan banda lafiya banzan cutar da keba,,, banzan bari ciwona ya zama matsalar kiba Jabeer shine mijinki ni kam Aliyu bani da lafiyar da zan zauna da ke Minali Hamma kece mai kula dani gashi munyi nesa da juna." Haka ya rink'a rawan jiki da azabebben zazzab'i. Dai-dai lokacin Abba kuwa da ya Amir motarsu ta iso k'ofar gidan Captain Sani da su Ramadan kuwa suna ganin an bud'e wa su ya Amir gate suna shiga suma suka dannan hancin motarsu cikin gidan. Abba na fitowa Ramadan ya kalli Captain Sani cikin sanyi yace. "Abban mu ko?." Kai ya gyad'a mishi tare da cewa. "shida ya Amir." Fita Ramadan yayi cikin sanyi ya je gaban Abba hannu yasa.... By *Garkuwar Fulani* [8/18, 6:26 PM] πŸ’žIt's @lh@jiπŸ’ž: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *BANDIRAWO* page 4⃣6⃣ *Na* *Aysha Ali Garkuwa* πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *D'erewol gol mi vinddi gol gam nango beldum fulb'e eb'e gonifu had'er duniyaru du, Fulb'e Cameroon eh Fulb'e chardi eh Fulb'e Niger eh Fulb'e Ghana eh Fulb'e laidi am dayirdi am Fulb'e Nagerian min Garkuwa mon on mi sakki on gol d'erewol golfu gol modon,.. Allah accu lawol fulb'e Amin ya Allah* Kanshi a sunkuye ya mik'a hannu ya karb'i brufcs d'in hannun Abba kanshi a k'asa yace. "Barka da dawowa Abba." yana fad'in haka yasa kai yabi bayan ya Amir, shi kuwa Abba bugawar zuciyar sace ta tsanan ta cikin mamaki da rud'ani dan tabbas yana kama da General amman tafiyar General ba irin nashi bane kuma muryar General ba irin muryarsa bace, ido ya sake tsurawa Ramadan cikin kallon tafiyarsa sak irin tashi sannan muryar da yaron yayi maganar sak irin muryar sa, sosai ya tafi duniyar tunani a fili yace. "Toh wannan yaron kuma waye shi? daga ina yake? me ya kawoshi gidan nan? ." Captain Sani ne ya jawo hannun Rayhana cikin sauri yazo gaban abban tare da cewa. "Abba barka da dare." cikin sauri ya juya gun Captain tare da cewa. "Yauwa Sani kana gida ne dama? ina ogan naka?." ya d'an juya ya kalli Ramadan da tuni ya shige cikin gidan, juyowa ya kumayi cikin bugawan zuciya yace. "Kai Sani wancan yaron fa waye ne daga ina yak....!." Shiru yayi ba tare daya k'arisa tabbayar tasaba ya tsurawa Rayhana ido cikin matukar mamaki tabbas bazai mance irin wannanr fuskar ba a rayuwar shi tabbas ko zai manta komai a duniya bazai manta fuskar mahaifiyar shi ba, hak'ik'a tunda ya baro rigarsu bai k'ara ganin fuskar da take kama da fuskar Innarshi ba sai a kan Meenarl shi yasa ya jinta har cikin ransa yana sonta bisa gaskiya da kaunar fuskarta dan tana kama da Innarshi sai gashi yau kuwa yaga wata fuskar da tafi kama da ta Innar tashi ido ya tsurawa Rayhana cikin kad'uwa da k'aunar yarin yar yace. "Sani wannan kuma fa?." Ita kuwa Rayhana sai hawaye kawai dake bin fuskarta tana kallon mahaifin ta cikin kuka tace. "Abba ni y'ar kace amman gani a gaban ka baka san cewa ni jinin ka bace ni tsasonka ce Abba ni da wancan yaron da ya shiga cikin gidan sunan shi Ramadan mu y'ay'anka ne da ka saki Ammin mu tana da cikin mu Abba kace mu ba yaranka bane? amman gashi kamannin Ramadan yau zai nunama mu jinin kane Abba yau gamu a gaban ka muna sonka a matsayin ka na mahaifinmu Abba muna son Hamma Haiydar d'an uwana yana buk'atar mu a kusa dashi." Shi kam Abba tunda ta bud'i baki yaji sautin muryar ta irin ta Innarshi sak sai wani jiri yaji ya d'ebe shi duhu ya rufe mai ido jikin mota ya koma ya jingina kai yake juyawa yana cije lips enshi abinda a gunshi General ya gaji cije lips Abba kam sai jiri yake k'ara gani dan yau tunanin mahaifarshi ya d'arsu a ranshi begen Innarshi da Bappa shi yake tamkar zasu fasa mishi zuciya yau ba abinda yake bege kamar tushensa asalin sa. Cikin jirin yace. "A a, a,a Rayhana Ramadan ku y'ay'anane Allah sarki Fatima data haifeku sai tasa mik'a sunan da yake sunan Innata ta, ina Ramadan ina sonku yarana." Sai kuma kawai yayi luu zai fad'i a sume. Cikin sauri Captain Sani ya tallabo shi tare da rugume shi, Ita kuwa Rayhana kuka ta saki da k'arfi tana kiran. "Abba! Abba ! ka tashi mu rayu a sauran rayuwar da ta rege mana." Sai kuma tayi cikin gida tana. "Ramadan! Ramadan! Abban mu!." Captain Sani ne ya tallaboshi suka nufi cikin gidan yana. "Kai Rayhana kiyi shiru kar ki karawa Hamma Haiydar firgici." Shi kuwa Ramadan bin ya Amir yake har suka shiga cikin gidan suna isa babban parlour ganin ya Amir d'in zayyi part din Mama yasa shi yin gyaran murya cikin sanyi yace. "Ya Amir ina Hamma Haiydar?." Da sauri ya Amir ya juyo dan shi a zaton shi Abba ne dan muryar sak ta Abban sai kuma yayi mamaki Abba ne zaicewa Aliyu Hamma Haiydar. Ido ya kuma zarowa ganin wannan yaron wanda komai nasu irin d'aya shi da Abba da Aliyu sai dai bai kaisu tsawo ba, Shi kuwa Ramadan murmushi yayi cikin k'aunar ya Amir d'in ya matsoshi kafa d'arshi ya dafa tare da cewa. "Dr Ramadan Abubakar Umar Rumoh suna na , ma,ana k'anin General Aliyu Abubakar Umar Rumoh, ya Amir nasan kai kasan Ammi na ni d'an uwanka ne nida Rayhana." Kai kawai ya Amir yake juyawa. "Dan tabbas da kaga Aliyu kaga Ramadan kasan ciki d'aya suka konta da zaran kaga Abba kuwa kasan shine mahaifinsu tabbas kuma shi yasan Ammi dan da girman shi tabar gidan kuma yaji zancen ta fita da ciki ta kuma haifi yan biyu. Kawai sai ya rugume Ramadan d'in fuskar sa cike da happy cikin d'an daga murya yake cewa. " Daddy! Abba! Mama! Abdul! Aysha! Nafeesat! kuzo ! kuzo! ." Nafeesat kuwa tunda suka je gidan su Meenarl ta kalli Ramadan da Rayhana ta kuma ga ana ta tara musu zugan sojoji ta zille cikin kuka ta fito kai tsaye mai a dedeta ta tsare ta shiga tare da cewan. " uguwar sarki." A nufinta zata je ta gayawa Abban ta sai kuma gashi suna fita layin sukayi kicib'is da motar General Aliyu hakan yasa ta samu nitsuwa don tabbas tasan komin yaya In General yaje zusu sake Abdul, shi yasa koda ta dawo gida part d'in Anty Aysha ta nufa, tunda ta dawo take bata labarin abinda ke faruwa toh tun lokacin tana part din su ya Amir d'in dan ita bata fiye shiri da Mama ba sai yanzu da sukaji kiran ya Amir d'in suka fito. Shi kuwa Abdul tunda suka dawo tare da General gaba d'aya zuciyar shi ta cika da tausa yin Hamma Aliyun nasu cikin sanyi ya shiga parlour Mama gefen ta yaje ya zauna a hankali ya bata labarin abinda ke faruwa, sannan yaci gaba da cewa. "Mama Hamma Aliyu bayida lafiya ga tarin damuwa ga rashin Ammin shi gashi Meenarl d'in ma yau bata nan, Mama inajin tausayin d'an uwana." Cikin jan dogon tsaki ta watsa mishi harara tare da cewa. "Toh me had'inka da shi koma mene wallahi ni bani janye guduri na a kanshi." Mik'ewa yayi cikin tsanan halin mahaifiyar tashi yana fita tare da cewa. "Mu daiji tsoron Allah wallahi ni ina son d'an uwana." Ita kam Mama tsaki taja tare da yin dariya mugunta, sannan ta koma ta konta, ta lumshe idanun ta kenan taji muryar Amir yana zuba musu kira da sauri ta mik'e ta nufi parlour... Su Captain Sani kuwa a tare suka shigo da Rayhana dake ta kuka tana. "Ramadan Abban mu." Da gudu Ramadan ya karisa inda Captain ya kontar da Abba yana ki ranshi tare da bashi taima kon gaggawa. Su Mama kuwa da Abdul dasu Nafeesat gaba d'aya sun rude sai dai kowa da abinda ya rud'ashi ita mama tsoro Ramadan ya bata shiko Daddy ciwon d'an uwanshi ne ya firgi tashi. Rayhana kuwa hannun Abban ta rik'e tana kuka shiko Ramadan tafin k'afan Abban ya rik'e tare dasa tafin hannun shi yana murza k'afan Abban a hankali Abban ya bud'e ido cikin rawan murya yayi salati tare da kamo hannun Rayhana sannan ya tashi zaune da k'er sannan ya jawo Ramadan ya rugume su kawai sai ya saki kuka tare da rik'o hannun Daddy murya na rawa ya kalli Daddy yace. "D'an uwana wad'an nan yara nane yaran da Fatima ta haifamin bayan nasake ta." Sai kuma ya juyo fuskar Rayhana yace. "D'an uwana kalli hoton fuskar Innarmu." Cikin murmushi Ramadan yayi musu Introduce kanshi da Rayhana ayyah sai kuma Daddy ya rugumi Abba suka fashe da kuka cikin tunanin mahaifarsu. Ita kuwa Mama zuface ke keto mata tako ina a firgice taja hannun Abdul har parlour ta cikin zare ido tace. "Abdul ina mafita." Zame hannu shi yayi tare da zubda k'ollah yace. "Mama ni yanzu ba Abdul d'in da bane yanzu cikken sunan nake amsawa *Abdulmuminu* ina son y'an uwana wallahi banzan sake cutar da kowa ba." Sai kuma ya fashe da kuka tare da ficewa ya barta a tsaye . Abba kuwa da Daddy d'aya Amir dasu Nafeesat da Anty Aysha farin ciki sosai sukayi. Cikin sanyi Ramadan ya mik'e tare da kamo hannun Rayhana ya kalli Abba yace. "Abba ina Hamma Haiydar ?." Murmushi yayi tare da cewa. "Muje ." Allah sarki shiko General Aliyu da k'er ya yajowo blanket ya rufe jikin shi yana ta rawan sanyi tare da dunk'ilewa wuri d'aya gaba d'aya yaji abinda su Abba ke fad'a a parlour so yake ya tashi amman ya kasa Fuskar Ramadan da Rayhana kawai yake begen gani sai cije lips enshi yake. Shi kuwa Ramadan suna shiga ya fara kira yana. "Hamma Haiydar ina kake? kayi hak'uri d'an uwana ." Abba ne yaja hannu shi suka shiga cikin bedroom d'in yayin da Daddy da ya Amir ke biye dasu shiko Ramadan yana rik'e da hannun Rayhana Captain Sani na bayan su. Shi kuwa General sai karkarwa yake yi, suna shiga Ramadan yayi kanshi cikin kula da tsantsar k'auna yasa hannu shi kan goshin sa, ita kuwa Rayhana hannun Hamma Aliyun ta rik'e cikin sanyi ta saki kuka murya can k'asa tace. "Hamma na ka bud'e idanun ka gamu gareka Hamma Haiydar kalli fuskar d'an uwanka Ramadan Hamma Haiydar kalle ni mu jinin Kane UWA d'aya Uba d'aya." Sai ta kuma damk'e hannu shi . Shi kuwa Ramadan cikin hankali yace. "Hamma Aliyu meke damun ka? Ka gaya min d'an uwana ." Shi kam General ya k'asa koda bud'e ido sai hawaye dake bin gefen idon shi yana d'iga ganin haka Rayhana tasa tafin hannun ta tana share mishi k'ollan, shi kuwa Ramadan sai kallon fuskarsa yake yi, Cikin kasalan da rawan jiki ya kamo hannun Ramadan ya jawoshi jikin shi tare da rugume shi murya can k'asa yace. "Inah Ammi? Ramadan ina Ammi? ko ita bata son gani nah ta cireni a cikin yaran ta ko?." Kai Ramadan ya rink'a juyawa cikin share mishi k'ollah yace. "Hamma Aliyu Ammi tana sonka gari bai tab'a waye wa ba tare da ta tuna kaba rashin ka a kusa da ita shine nak'usun farin cikinta kullum in zata yi mana addu'a sai tayi maka kafin mu." Haka Ramadan da Rayhana da Abba suka kwana dashi cikin tsantsar kulawa Captain Sani kuma yaja Abba da Daddy gefen yayi musu baya nin komai. Aliyu kuwa koda Asuba ta kara to gaba d'aya tunanin shi ya koma kan Meenarl yayin da ko ido ya rumtse sai ya ganta a lokutan da take mak'ale mishi. Cikin damuwan yayi sallan Asuba Rayhana kuwa kitchen ta shige had'a musu breakfast yayin da Nafeesat kuwa ta shigo ta taya ta sauran ayukan Abdul kuwa shida Ramadan tare suka wuce hospital dan samo magungunan Hamma Aliyun, Captain Sani ko duk inda Nafeesat tayi sai ya bita da ido yana d'an kad'an k'afa. Forko ruwan Dr Ramadan ya k'ara wa General sannan suka rink'a bashi kula ta musamman shi kuwa gaba d'aya ya resa meke mishi dad'i a duniya duk da bawai ciwon yake ji ba amman yau har yanzu jikin shi a mace yake. Meenarl kuwa yadda taga rana haka taga dare da zaran ta rumtse idonta sai taga Hamma Haiydar d'in ta cikin halin wahala , a d'akin Hajia Amina take dan Ummi na d'akin Abban ta. Cikin kuka tace. "Momy wallahi Hamma Haiydar bashida lafiya kullum baya bacci cikin wahala yake kwana ni dai wallahi ina jin tausa yinshi Hamma Jabeer ya kaini in dubashi." Cikin kontar da hankali Hajia Amina ta matsota tare da cewa. " takwarata kiyi shiru ki nitsu kinji ko yanzu kinga har k'arfe 4 tayi abinda ya dace kiyiwa Hamman ki Addu'a insha Allah zai samu sauk'i yanzu jekiyi alwala kizo kiyi nafilfili tare da yi mishi Addu'a." Ku kunsan Meenarl bata da musu haka yasa tabi shawarar da Momy ta bata. Koda gari ya waye Meenarl ta k'asa samun sukuni ko abinci tak'i ci ita dai a kaita ta duba Hamma ta, gashi su Ramadan har yanzu basu dawo ba. Abu kamar wasa fa Meenarl tunda dare yayi ta fara zubda k'ollah tana bin Dr Jabeer tana cewa. "Hamma Jabeer muje ka duba Hamma Haiydar wallahi bashi da lafiya baya baccin dare." Sosai Dr yaji zafin yadda take kuka sosai akan Aliyu a ranshi yace yaushe ma kika sanshi. A zahiri kuwa shiru yayi tare da tsura mata ido ganin k'ollah dake zuba a fuskarta cikin sanyi yace. "Mu tafi in kaiki yanzu mu dawo." dan Dr Jabeer mutun ne mai hak'uri da sauk'in kai kuma yana matuk'ar son farin cikin Bodd'insu, sai ya kuma kalli Ammi a hankali yace . "Ammi muje tare mana." kai ta girgiza cikin sanyi tace. "Yaya Lawan yace kar naje sai sun jesu tukun." Haka badan yaso ba suka tafi, da taima kon Meenarl suka isa gidan, yana yin Parking ta bud'e da sauri kai tsaye part ensu ta nufa shima Dr Jabeer binta a baya yayi. Suna cike a parlour suna ta hira Ramadan yana yankewa Abba faratun shi, Rayhana kuwa ta had'a mishi tea, tana shiga Dr na binta a baya gaban Abba taje ta zauna a hankali ta gaida shi tare da cewa . "Abba Hamma Haiydar fa?." "Yana wonka." Abba yace tare da kallon Dr Jabeer dake gaida shi, gaba d'aya kuma sai fuskar Dr ta canza ganin Meenarl ta shige cikin bedroom d'in...! Ita kuwa tana shiga dai-dai lokacin General ya fito cikin toilet din daga shi sai towel dake d'aure a k'ugunshi, Tana ganin shi tayi kanshi da sauri tare da cewa. "Hamma Haiydar." Shi kuwa ido ya lumshe jin yadda ta fad'a jikin shi ta rugume shi ajiyar zuciya ya sauk'e tare da manna ta da jikin shi gaba d'aya jikin sa sai b'ari yake cikin kewan juna ya tura Hanna yenshi cikin ...........! By *Garkuwar Fulani* [8/18, 6:26 PM] πŸ’žIt's @lh@jiπŸ’ž: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *BANDIRAWO* page 4⃣7⃣ *Na* *Aysha Ali Garkuwa* πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *Mi noddi on Fulb'e mi hofni on Fulb'e fulfulde duna Fulb'e fulfulde funa Fulb'e* Hannu shi d'aya ya tura tsaka ninsu cikin sauri ya kamo towel d'in k'ugunshi da ke k'oka'arin sincewa hannu d'aya kuma kanta yasa ya manna a k'irjin shi cikin sauk'e ajiyar zuciya ya lumshe ido tare da k'ara matsota jikin shi zuciyar shi na harbawa da sauri-sauri. Ita kuwa Meenarl hannu tasa ta zagayo k'ugunshi tafin hannun ta ta wore tare da manna su a tsakiyar bayan shi cikin sanyi da tausayawa ta d'an d'ago kanta ta tsura mishi ida tare da tsuke bakinta ta d'an tura tare da karya wuya cikin kula tasa hannu ta d'aya a wuyan shi a hankali tace. "Hamma Haiydar ya jikin ka? har yanzu yana maka ciwon ne?." Ajiyan zuciya ya kuma sauk'ewa tare da karya wuyan shi ya matse hannu ta dake kan wuyan nashi cikin tsura mata ido da fuskar tausayawa kanshi da kanshi yana kallon ta har cikin ranshi yake jin zafin rabuwa da ita yana kuma tuhamar kanshi da jin zafin d'an indai yace bazai rabu da ita bama bayyi mata adalci ba, sannan ya zaiyi da amanarta da Bappa ya bashi, hannu shi dake rik'e da towel d'in k'ugun nashi ya d'an daga tare da kife hannun kan mararshi , har lau dai idanun shi na kan fuskarta matse marar tasa yayi tare da rumtse ido a hankali yace. "Minalin Hamma Haiydar, lafiya tayiwa Hamman ki tsad'a Minalin Hamma! ciwo ya min illah! ciwo ya kama ni a inda ya zamar dani nida babu kad'an ne babban cinmu , Minali na na cutu, na samu k'arin ciwo a kan damuwar da rayuwata ke ciki na rasa mahaifiya ta tun ina karami yanzu kuwa ciwo zai rabani da amanata." Ita kam Meenarl tuni sai hawaye ke bin fuskar ta cikin raunin zuciya ta rink'a zubda k'ollah tana shafa mararshi inda ya kife hannun shi, tana kuma kallon fuskar sa jin yadda wurin ya fara tauri da zafi yasa ta d'an matse wurin da d'an k'arfi. Zillo General yayi cikin dauriya ya rik'e wurin a sunkuye ya isa bakin gado zama yayi cikin fidda numfashin wahala. Matsoshi tayi cikin sanyi ta zauna gefen shi tare da cewa. "Hamma kayi hak'uri muje asibiti." Kai ya juya cikin cije lips ya koma ya konta a rigingine tare da yin mik'a yana mai rumtse idanun shi. ita kuwa sai k'ollah ke bin fuskar ta, tasa hannu tana shafa mishi kan marar tashi a hankali tana d'an danna wurin. ido kawai ya tsura mata cikin sanyi ya jawo hannu ta kan jikinshi ya kontar da ita suna fuskarta juna murmushi k'arfin hali yayi tare da cewa. "Minali Hamma, Hamman kifa bashi da wani amfani a gareki banban cina da macecce kad'an ne ya rigada na gama mutuwa." Ido ta zaro cikin tsoro tare da bud'e baki cikin kuka tace. "A,a a a Hamma Haiydar bazaka mutuba." Sai kuma kawai ta fashi da kuka tanayi tana shafa sajen fuskar sa. Lips enshi ya cije tare da mirgina ta ya kontar da ita kan pillow, cikin sanyi ya yunk'ura yayi mata rumfa da k'irjin shi cikin sanyi yasa bakin shi kan fuskarta yana hura mata iska. ita kuwa sai kukan take tana sheshshek'a k'asa-k'asa . Idon shi ya tsura cikin nata a hankali ya manna bakin shi da nata harcenshi yasa ya rink'a lasar lips enta yana kallon fuskarta. Shiru tayi tare da lumshe ido tasa hannu cikin suman kanshi. Shi kuwa ganin yadda tayi shirun ne ya d'an yi murmushi a hankali ranshi ke fad'a mishi , "Meenarl matar lafiyeyyene." A zahiri kuwa lips d'inta na k'asa ya d'an kamo tare da d'an cizawa. Cikin duniyar nitsuwar da ta tafin taji zafin ya ratsata. Cikin tsoro tayi zillo tare da tureshi tana yarfa hannu da zaro ido woje. Shi kuwa General yadda tayi likimon da yadda ta zaro idon ne ya bashi dariya abinda General bai fiye yiba kenan. Dariya ya rink'a yi a hankali tare da nunata dariya yake cikin danne mararshi dake mai ciwo a fili ta zaro idon shi kuwa abin ya bashi dariya da ta nitsu tanaso ya murjeta dataji sab'anin haka ta wani zoro ido. Ita kuwa baki ta tura tare da kaimai bugu tana. "Allah ko Hamma Haiydar sai na rama wallahi zan rama." dariya ya kumayi cikin d'aga mata gira yace. "Zo zo ki gani Minali." tureshi tayi tare da matsoshi tana cewa. "Maranka zan danna." Kai ya juya cikin dariyar yace. "Kashe Hammanki zakiyi ko." Sai ya kuma nuna mata lips enshi yace. "Zoki rama anan." A hankali ta matsoshi tare da zama kan cinyarshi suna fuskantar juna, lips enta tasa da nufin kamo nashi ta ciza , sai kuma tayi ajiyar zuciya tare da sakewa a jikinshi jin ya manne bak'in shi da nata ya zira harshensa cikin bakinta tare da d'aga mata gira d'aya alamar ki rama. Ina shiru tayi tana jin yadda yake sauk'e mata kasala da salonshi.. A parlour kuwa Dr Jabeer mik'ewa yayi lokacin dayaji sautin dariya General cikin zafin abun ya kalli Ramadan da Captain Sani yace. "Sani mu zamu tafi ." Ramadan kuwa kallonshi yayi cikin girmamawa yace. "Hamma Jabeer Ammi kam su Daddy sun hanata zuwa ko ? bazata zo taga halin da Hamma Haiydar ke cikiba." Tsaki ya d'an ja k'asa-k'asa tare da cewa. "Ba shine yake wannan dariyar ba? ko ciwon dariya yake yi?." Shiru sukayi gaba d'aya d'an sun fahimci Hamma Jabeer a hatsale yake, Ita kuwa Rayhana kallon shi tayi cikin had'a fuska tace. "Hamma Jabeer inka koma ka cewa Ammi ni dai wallahi in bata zoba banzan koma Adamawa ba." Harara ya cilla mata tare da cewa. "Bodd'iiiii, Bodd'iii". Shi kam Abba ido ya zura musu. shi kuwa Captain Sani hankali shi na kan Nafeesat yana nuna mata pic d'in Ammi a phone nashi. A cikin bedroom d'in kuwa. wani irin zafi da takaici ne ya tokari k'ahon zuciyar General jin muryan Dr Jabeer cikin sanyi ya zame bakin shi a cikin nata , cikin had'e fuska ya tsura mata ido a fili yake zaton yadda take mak'ale mishi haka take mak'alewa Dr Jabeer ko?, a take sai zazzab'i ya fara rufeshi sai sanyi da ya fara ji cikin cushewar voice yace. " Meenarl ke da waye kika zo?." idonta a lumshe ta konto kanshi. Cikin zafi ya tureta tare da buga mata tsawa yace. "Ke dawa kika zo?." Ido ta tsura mishi baki na rawa tace. "Hamma Jabeer nane fa." Tureta ya kumayi tare da sauk'owa k'asa baki na rawa ya nunata da yatsa yace. "Ehh ai nasan nakine ba sai kince min ke da Hamma Jabeer dinki bane, nasan shi naki ne, d'an haka tashi tashi ki bishi me ya kawoki gareni?." Gaba d'aya ya juya fad'a yake har muryanshi na rawa kamar zaiyi kuka ga zafin zazzab'i yana zura rigarshi tare da cewa. "Ni ban damu ba karki sake zuwa gareni Allah ne gatana , Ammi nama ta gujeni, Meenarl kema ki tafi gun Jabeer, karki sake zuwa gidan nan tunda iyayenki basa sona tun ina k'arami suka rabani da maifiya ta duk family naku bakwa sona, Insha Allah zan shirya Na tafi Gembu zanje Membila zan koma wurin Bappa zanje na gaya mishi a manar daya bani tafi karfina zan taho dashi na nuna mishi inda kike." Ita kam Meenarl kuka kawai take tana cewa. "Hamma Haiydar ina zakaje?." Tsawa ya buga mata tare da zaro key d'in motarsa, yace. "Ban sanina ki tashi kibi Jabeer din naki kije ya maida ki gun iyayen ki." Parlour ya fito itama biyo shi tayi a baya suna fitow ya kalli Ramadan da Rayhana yace. "Ramadan ku taso mu tafi." Ba musu suka mik'e tare da cewa. "Abba bari muje?." Shima General Abban ya kalla tare da cewa. "Abba zamu fita." Shi kuwa Dr Jabeer hannun Meenarl ya kamo tare da cewa. "Mu tafi a banza zaki tsaya kina kuka." janta yayi ya fice. shi kuwa Captain Sani kallo yabi General dashi ganin yadda yake watsa mishi harara, harce General ya juya cikin fillanci yace. "Abba zamuje mu kwana a Jaji da kanne nah." Murmushi Abba yayi tare da cewa. "Toh saida safe kenan, Amman ko zaku meda Rayhana gun Ammin ku ne, shi kuwa Ramadan zai kula da kai." Kai kawai ya gyad'a mai tare da ficewa. Kai tsaye Jaji suka zo suna shiga cikin gidan nashi suka samu mai aikin a parlour , cikin mamaki suka kalli juna. Shi kuwa General fuska a had'e ya kalleta tare da cewa. "K'anne nane kin tsaya kina kallon su kije ki kawo musu abinci." . Kai Rayhana ta rink'a juyawa cikin tuhuma tace. "Hamma Aliyu wannan kuma wacece? kuma me takeyi? A gidan nan." Baki ya tab'e tare da cewa . "Shara da jiran gidan take yi." Harara Ramadan yayi mata tare da kallon yayan nashi yace. "Gaskiya Hamma tabar gidan nan bai daceba ka zauna da ita." Ido ya lumshe cikin sanyin zazzab'i yace. "Toh ka salla meta tunda baka son zaman ta a nand'in." Ido ta zaro cikin tsoron kar a rabata da aikinta zatayi magana Ramadan yace. "Kiyi hak'uri zaki bar gidan nan kam ki shirya da safe zan salla meki." zata kuma yi magana General yace. "Fita a daga nan gobe da safe zai salla mekin hakan da yace banson musu." Haka ta fita ranta a bace tana jin zafin su ramadan. Shi kuwa General ya biye musu ne d'an ya lura kamar zargin shi da ita su ke son d'arsuwan musu , sannan kuma yana son duk wani abinda zaiyi ya sasu Happy. Ramadan kam tare ya kwana da General a kan gadon shi yayin da Rayhana ke d'aya d'akin , shi kuwa General mamaki yake d'an ciwon shi tun juya yake reguwa d'an jiyama bai mishi kamar na kullum ba bugu da k'ari kuma da asuba yana jin wani yanayi da ke bashi mamaki, sai kuma gashi yau kam zazzab'i ne ma kawai ke damun shi, a d'aya sashin zuciyar shi kuwa, Meenarl yake son yak'i cewa haka ya kwana cikin tunani , da k'udirin washe gari zai wuce Taraba d'an gaba d'aya hankalin shi ya koma wurin Bappa . Haka kuwa. Akayi da asuban fari ya shirya tsab shida k'annen shi , sannan suka sallami mai aikin suka ja gidan suka rufe, sannan suka d'auki hanyar Taraba Rayhana da Ramadan zuciyar su k'al da farin ciki dan suna matukar kaunan wannan garin. Captain Sani kuwa suna fita ya kalli Abba cikin tank'waushe k'afafun yayi k'asa da kanshi tare da cewa. "Abba Hamma Haiydar ya rasa farin ciki da kulawar mahaifiya tun yana k'arami, hakan tasa ya rayu kamar maraya ko yaushe fuskarsa cike take da maraici, hak'ik'a nasan iyayena basu kyauta ba , Amman baya ta wuce yanzu mu gyara gaba, Abba ka maida auren Ammi ka dawo da itakan 'ya'yan ta, wannan ne kawai zamuyi musa farin ciki a zuciyar. Hamma Haiydar a dawo da Ammin shi kusa dashi." Kai kawai Abba ke gyad'a wa cikin gamsuwa da shawarar Captain ya kuma yarda da shawarar , sannan yace. "Insha Allah gobe zan gayawa d'an uwana kuma jibi ko gata zamuyi shiri muje gidan ku, zanje na nemi gafarar Barrister Lawan da Alhaji Ibrahim da Fatima ta dawo kan yaran ta." Sosai Captain yaji dad'i dan yana son ya bawa General mamaki , ya kuma yi niyar dawo mar da farin cikin sa AMMIN shi. ITA KUWA Meenarl tunda suka dawo ta k'asa ta tsare so take tayi fushi da Hamma Haiydar d'in nata amman tausayin shi nacin zuciyar ta, Abban ta da Barrister da Dr Jabeer kuwa abinyana damun su Ammi kuwa tunda Meenarl ta gaya mata halinda General ke rayuwar in dere yayi , ta dage tuk'uru tanayiwa d'an ta addu'a da nema mishi sauk'i da kariyar ubangiji kuka take tana kai kukanta gun mahaliccin mu tana kuka tana yiwa d'an ta addu,a. Tafiya mabud'in ilimi General Aliyu kam tuni yabar jihar haduna ya nausa Taraba , A cikin *Mayo balwa* sukayi sallan magariba sannan sukaci gaba da tafiya, gudu Aliyu yake kamar zai fire d'an so yake a yau dinnan su isa rigarsu Bappa tuk'in yake da sauri a lokacin da suke cikin Membila dan zuwa yanzu mararsa da zazzab'i ga sanyin ciwon da yake ji d'in ga sanyin garin Mambila tuni ya fara karkarwa, ganin haka yasa Ramadan ya karb'i tuk'in dai-dai lokacin da suke za gayawa bayan dutsen mambila d'in. 9:47 pm dai-dai Ramadan yayi parking a k'ofar gidan Bappa cikin rawan sanyi ya kalli General dake ta karkarwa yana damk'e da mararshi. Rayhana kuwa kai tsaye cikin gida ta nufa tana zuwa, Bappa na ganin ta ya mik'e cikin tsantsar farin ciki ya mik'e tare da yin woje yana cewa. "Muta nen Kaduna kai sannun ku da hanya wannan tafi yan deren cikin deren kuka shigo wannan lardi Allah ya k'ara karewa." "Amin" tace. tare da zauma a gefen Inna dake ta faman yi mata sannan . Bappa kuwa yana fita ya nufi inda motarsu ke tsaye cikin mamaki ya kalli Ramadan tare da haska wanda ke koncen yana rawan sanyi. cikin firgici da kad'uwa da mamaki da farin farin ciki yace. "Aliyuuuu, Alhamhadullih Aliyuuu dama nasan tabbas! tabbas wata rana zaka dawo wannan rigar tamu." Sai kuma ya kalli Ramadan cikin kad'uwa yace. "Ramadan meya sameshi ? kama shi mu shiga cikin gida." Bayan sun kontar dashi kan katifar Bappa Ramadan ya d'ebo magungunan shi zai bashi . Cikin fahimta Bappa ya matse matar tashi kai ya juya cikin sanyi yace. "Ramadan ciwon Aliyu bana asibiti bane wannan ciwon kura'ani ne da add'a maganin shi." K'ara damk'o wurin Bappa yayi tare da matsewa da k'arfi. cikin wani irin..... *Allah Yau da k'er nayi typing d'inga* By *GARKUWAR FULANI* [8/18, 8:58 PM] β€ͺ+234 813 799 9565‬: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *BANDIRAWO* page 4⃣9⃣to5⃣0⃣ *Na* *Aysha Ali Garkuwa* πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *Wannan shafi d'uggu ruggum d'in shi nakine ke kad'ai Khaleesat Haiydar Allah bar zumunci da k'aunah ina al'fahari dake, MI YID'I MASIN KHALEESAT* Dr Jabeer shima yayi parking, Ido Aliyu ya tsurawa motar Dr Jabeer d'in cikin takaici, Meenarl ya haggo zaune a gefen Jabeer daga dukkan alamu tare suka fita kuma yanzu sunka dawo tsaki ya jaa cikin murtuk'e fuska yayi shiru yana matse siteri, Bappa kuwa da Inna da Rayhana shiru sukayi dan basu san me yasa shi jan tsaki ba kuma ya tsuke fuska ya k'i ya bud'e musu motar, Shiko Ramadan shima kallon motarsu Meenarl d'in yake tare da son fitowa dan sauri yake yayiwa Meenarl albishir da zuwan su Bappa. Ita kuwa Meenarl shiru tayi tana kallon Hamma Jabeer d'in nata da ya rik'o hannun ta yana murza yan yatsunta cikin wani salon ya k'ara juyowa gareta suna fuskar tar juna cikin sanyi yace. "Bodd'i na ina sonki inason kasan cewa tare da ke inason farin cikin ki, me yasa kike k'untatawa kanki akan Aliyu ai da ya damu dake yadda kika damu dashi da bazai iya korarki ba, Bodd'i nifa d'an uwan kine na jini ki dawo da zuciyar ki gareni zan soki zan kula dake zan riritaki." Shiru tayi fuskar ta na cike da k'ollah tace. "Hamma Jabeer, Ni ina tausayawa Hamma Haiydar bashi da lafiya kullum dere baya bacci kuma ba mai taimaka mishi sai ni." Sai hawaye shar-shar a fuskarta tana juya kai. Shiru Dr Jabeer yayi zuciyar shi cike da k'aunar ta yasa hannu ya tallabe hab'arta k'ara matsota yayi tare dasa hannun shi ya share mata k'ollah. Shi kuwa General da k'arfi ya rumtse idanun shi cikin k'ara matse siterin yana mai juya kai. Ganin haka yasa Ramadan dannan pin d'in bud'e motar sannan ya bud'e ya fito tare da bud'e wa su Bappa da Inna suma suka fito, shima kainshi a sunkuye ya bud'e ya fito cikin tsuke fuska. Suna fitowa , Meenarl ta wore ido cikin tsananin mamaki da farin ciki cikin sauri ta fito tare da yin gudu tana zuwa ta rugume Inna cikin kewar juna Inna ta rugumeta Bappa kam sai murmushi. Ita kuwa Meenarl sai hawayen farin ciki, sai ta kuma sake Innar tayi cikin gida da gudu tana. "Ummi! Ummi ina kike ? Ummi ga Bappa na da Inna ya Ramadan ya kawo minsu." Su kuwa bin bayan ta sukayi suna dariya a babban parlour suka tarar da mutanen gidan baki d'aya, cikin farin ciki da k'aunar juna suka gaggaisa. Shiru Bappa yayi ganin Aliyu bai shigo ba cikin kula ya kalli Ramadan dake gefen Ammin su yace. "Kai Ramadan ina Aliyu ." "Yana woje yace shi bazai shigoba tunda masu gidan basa so." Cikin girma Bappa yace. "Shima ai nan gidan sune." Sai kuma ya mik'e ya fita yana zuwa kai hannun shi ya kamo yayi cikin gida dashi suna shiga parlour. Ammi da ta zubawa k'ofar shigan ido tana ganin shi ta rink'a sauk'e ajiyar zuciya tare da tsura mishi ida wasu hawaye masu zafi suka kwaranyo mata cikin rawan murya tace. "Haiydar." Shi kuwa General Kanshi a sunkuye yabi Bappa dake rik'e da hannu shi , gaban Ammin yaje ya ajiye shi sannan ya zauna gefen shi cikin kula yace. "Aliyu ga mahaifiyar ka gata a kusa da kai gata a gaban ka." Shiru Aliyu yayi tare da tsurawa yatsun k'afafun ta idanu lokacin d'aya yaji wani irin karayan zuciya gaba d'aya sai yaji zuciyar shi ta raunata. Ita kuwa Ammi hannu tasa ta jawo kanshi ta d'aura kan cinyarta yayinda kan Ramadan yake kan d'aya cinyar Rayhana kuwa ta rakub'e a jikinta, cikin sanyi ta d'aura hannun ta kan tsakiyar kan Aliyu baki na rawa tace. "Aliyu Haiydar ina sonka d'ana ina tunako ako wacce rana ban tab'a yin sallah na idar ba tare da nayi maka Addu'a ba Ammin ka tana sonka kaine farin ciki na Nagode wa Allah daya kare min kai." Shi kam General manna kanshi yayi da jikin Ammin kamar mai tsoron kar a saceta a hankali yaji hawaye masu zafi irin hawaye da yake ji a duk randa bagen mahaifiyar shi ya dame shi, ita kam Ammi fad'ar farin cikin ta bazai yiwu ba, General kuwa zuciyar shi cike da k'aunar mahaifiyar shi a d'aya gefen kuwa har cikin ranshi yake jin zafi da haushin yayun mahaifiyar tashi dan su suka mishi Katanga da ita tun yana k'arami suka mai dashi marayan dole. Bappa ne ya gyara zama cikin halin girma ya kalli Barrister Lawan da Alhaji Ibrahim sannan ya kalli mahaifi yarsu a hankali yace. "Wannan shine babban kuskuren da mutanen mu sukayi a wanna zamanin, aiki da zuciya fushi da tunzura a duk inda aka samu saki ya gifta a tsakanin ma'aurata, mata kin forko da za d'auka shine hak'uri sai kuma a duba darajan Aure sannan a koma a duba makomar yaran dake tsakanin dan gujewa aikin dana sani, babu wani riba cikin yin fushi dan anyi saki a reba uwa da d'an ta domin ko a shariyance yara suna gefen uwane har sai sun shekara 7 yanzu kai Lawan ribar me ka samu daka reba y'ar uwarka da d'anta kalli hawaye dake bin fuskar ta, kalli illar rebesun da kukayi yasa Aliyu ya rayuda Bodd'i tsawon lokacin Amman baisan y'ar uwarsa bace itama bata sani ba, kuna ne manta a can gefen bakusan tana kusa da kuba." Shiru sukayi baki d'ayansu dan tabbas gaskiya Bappa ke gaya musu, gaba d'aya zuk'atan su sun cika da nadama, Barrister kuwa har cikin ranshi yake jin kunyar y'ar uwarshi. Haka Bappa yayi ta musu nasiha da fad'a da nuna musu illar yin fushi dan an saki y'ar uwarka kace zaka rebata da yaran ta. Gaba d'aya sun maida hankali kan Bappa shi kuwa cikin girma ya sake gyara zama tare da yin gyaran murya yace. "Ibrahim wai ka d'aura auren Aminatu da Jabeer." Cikin sunkuyar da kai Alhaji Ibrahim yace. "Ehh Bappa na d'aura musu Aure ." "Yaushe ka d'aura musu auren?." "Bayan munje Membila lokacin da kukace an saceta toh damuka dawone da wata 1 na d'aura musu auren tunda shi Jabeer yana sonta." Kai Bappa ya jinjina cikin kafeshi da ido yace. "A lokacin kana da yak'inin Aminatu tana rayene? a lokacin kana da yak'inin zata dawo ne? kasan inda take a wanna lokacin ne?. Ajiyar zuciya Alhaji Ibrahim ya sauk'e tare da jin saurin tabbayoyin Bappa sai kai kawai yake gyad'a wa tare da cewa. " a a, bani da sanin wannan Bappa." Gyaran murya Bappa ya kumayi sannan ya kallesu baki d'ayansu tare da cewa. "Lawan ana d'aura Aure da babu ne? ana d'aura Aure da wanda ba san inda take ba?." Cikin goge zufa Barrister yace. "A a tabbas ba,a d'aura auren da babu matar , Amman nima wallahi Ibrahim bai gaya minba sai kawai cemin yayi ya d'aura musu aure." Cikin ilimi Bappa yaci gaba da cewa. "A cikin rashin sani kukayi aure a kan Aure! toh cikin wadan nan auraki biyun wanene ya zauna wanda akayi da fari ko na biyu?." Dr Jabeer kam tuni tabbayoyin Bappa ke tsinke mishi hanjin cikin shi sai ido yake bi Bappa da shi, shi kuwa Aliyu jinsu kawai yake dan ya gama yanke hukun ci a ranshi shi dai Ammin shine zai tafi da ita. Cikin sanyi Barrister yace. "Na farin dai tunda shi na biyun kan na farin aka daura shi ." Murmushi Bappa yayi tare da cewa. " toh zab'i yana gun Amina ita zata zab'i wanda take so a cikin su dan haka shariya ta bata dama, zancen gaskiya kuma Aliyu ni na aura mishi Amina Aure bisa koyarwan addinin mu ga sadakin Amina a hannuna ko sisi ban tab'aba, kuma ko a wancan lokacin Aliyu bashi yace yana son Amina ba nine na rok'eshi dan sirar da mutun cin ta." Sai ya kuma juyawa gun Aliyu yace. "Dan haka Aliyu in baka sonta ka saketa ga sadakin ka sai a maida maka, inko kana sonta saita zab'a a cikin Ku duk wanda tace bata sonshi sai a maida mishi sadakin shi ." Gaba d'aya su yarda da maganar Bappa dan gaskiya ce. Barrister ne ya kalli Meenarl cikin sanyin jiki yace. "Meenarl wa kike so a cikin su in Aliyu kike so ki fad'i shima d'an uwanki ne." Ita kam Meenarl sai kawai ta juya kan Dr Jabeer tana kallon shi ido cikin ido fuska cike da k'ollah ta k'asa magana sai kuka an kad'a an rawa tayi magana ta k'asa sai kallon Dr da takeyi tana kuka. Shi kuwa Aliyu ba k'ara min hatsala yayi ba ganin yadda take kallon Dr Jabeer tana kuka cikin cije lips enshi yace. "Ni banzan rabata da d'an uwanta ba dan nasan zafi da ciwon dake cin zuciyar wanda aka raba da d'an uwanshi dan haka ni zan barwa Jabeer ita , dan shiyafi cancanta da ita kuma shi ya tashi cikin farin ciki dan haka niko banzan zo rana tsaka na rabashi da farin cikin da ya rayu a cikiba , niko dama bansan menene farin ciki ko dad'in d'an uwa ba dan haka haka ni zan bar mishi ita." General yana maganar ne da iya gaskiyar sa dan a can cikin ransa yana jin zafin yadda Minalinshi ke kallon Jabeer tana kuka shi kuma ko inda yake bata kallah ba a d'aya gefen zuciyar sa kuma yana tuna cewa shifa har yanzu lafiyarsa nada rauni. Shi kuwa Dr Jabeer cikin tsantsar farin ciki da jin k'aunar General d'in yace. "Nagode d'an uwana Allah ya bar zumunci da k'aunar juna." Ita kuwa Meenarl zuciyar ta cushewa tayi sai wani irin sautin kuka ta saki cikin tsurawa Jabeer d'in ido. General kuwa ganin duk sunyi shiru ne ya kara b'ata mishi rai a zuciyar shi yace. "Ai dama su ba sona suke yiba." Bappa kuwa ido ya tsurawa General dan ya gano Aliyu yaudaran kanshi yake yi. Bappa ya bud'e baki zaiyi magana kenan Captain Sani ya shigo parlour cikin sanyi yace. "Daddy ga Abban su Ramadan yazo tare da d'an uwan shi." Cikin kula Alhaji Ibrahim yace. "Maza je ka shigo dasu kace su iso." "Toh" Captain yace tare da juyawa ya taho da su. Bappa kuwa haka kawai yake jin wani irin farin ciki mara adadi Inna kuwa da Ummi mahaifiyar Meenarl sai zuk'atan su ke harbawa da sauri-sauri. Shi kuwa General Captain Sani ya watsawa harara dan ya naga shine yayi shishshigin kawo Abban shi gidan, Ramadan kuwa sai murmushi yakeyi. Suna shigowa parlon Captain Sani ne a gaba sai Abba dake binshi a baya. Inna ce ta mik'e tsaye cikin tsananin mamaki da d'an rud'ewa gaba d'aya jikin ta sai rawa yake yi cikin firgici ta nuna Abban Aliyu baki na rawa tace. " *WAZIRI* Kaine nake gani ko kamace? Bappa waziri juyo ka gani ga waziri da Usmanu." Cikin sauri Bappa ya juya tare da sauk'e k'wayan idanun shi kan fuskokin ya ranshi da suka bace masu dere d'aya yau kimanin shekara 38 kenan." Bappa kam ba abinda yake cewa sai. "Alhamhadullih ala kulli halin, Allah na godema da wannan rahawa da kayi min na godewa Allah daya bani aron rai da damar sake sa yarana a k'wayan idanuna." Abban Aliyu da Daddyn Nafeesat kuwa, gaba d'aya jikin su rawa yake kamar mazari kai tsaye gaban Bappa suka durk'ushe kamar yara kuka sosai sukayi cikin kewar iyayen sun. Inna kuwa gani take kamar mafarki takeyi shi yasa ta matsosu tare da rik'e Hanna yensu tana. "Alhamhadullih Abubakar Usman nagode wa Allah ." Barrister Lawan ne yayi magana cikin rud'ewa yace. "Bappa su waye wad'an nan din a gareka ? ka sansu ne?." Aliyu ma kai ya jinjina cikin zubawa Bappa ido. Ajiyan zuciya Bappa ya sauk'e tare da nuna Abban Aliyu da Daddyn Nafeesat yace. "Lawan wadan nan da kake gani yaranane na jinina nine mahaifinmu su Inna waziri itace uwarsu mahaifiyar su wannan mai kama da Aliyun shine d'anta Wazirin da kukeji ina kiranta dashi , wadan nan sune yayun Aysha mahaifiyar Bodd'i , yayunta uwa d'aya uba d'aya , sun bar rigarmu ne a wani deren munwayi gari babusu ba labarin su munyi nema har muka kareya daga bisani muka fauwalawa Allah tare da saka ran watarana zamu gana, lokacin da suka bar gida Aysha tana k'arama , ashe Aliyu jika nane ban sanina." Wannan abin al'ajibin ya saka farin ciki a zuk'atan su baki d'ayansu. " Ummi da Ammi kam sai murmushi sukayi.. Sun zauna sun tattauna sosai sannan daga bisani . Bappa yace . "Toh a maida auren Abban Aliyu da Ammi." Barrister Lawan da Alhaji Ibrahim ne suka kalli juna cikin son nemawa k'anwarsu enci sukace. "Bappa bamuk'i maganar kaba amman a bari sai gobe in munyi shawara." Kai Aliyu ya dago tare da zuba musu ido zuciyar shi cike da tsanar su, ya za'ayi ana son maida auren Ammin shi sukuma suna dojewa. Cikin hatsala ya mik'e su Aliyun a goshi yace. "Ni na bar muku y'arku, Inma nine bakwaso a cikin zuciyar ku, sannan yadda kuke ganin zaku hana Ammi na komawa gidan Abba na toh, Shima yana iya d'auke mahaifiyar Meenarl tunda k'anwar sace, sannan kuma zamu dauke Ramadan da Rayhana tunda yaran shine , ni kuwa a karan kaina ni Aliyu zan dauke Ammi na tunda mahaifiya tace, Ku Kurik'e zuciyar ku muma mu rik'e tamu zuciyar." Yana kaiwa nan ya fice yana cewa, "kuyi tunani da kyau." Yana fita ya figi motarsa yayi gida. Barrister Lawan kuwa shiru yayi yana tunanin a zahiri fa Aliyu zai iya tsanarsu ya dauki gaba dasu , tuno hakan yasa shi yarda a take a wurin aka d'aura auren Ammi da Abba , Barrister yayi haka ne dan Samar da fahimta, sannan batun Meenarl kuwa, Sukace tunda shida bak'in shi yace ya hakura shike nan. A ranar Abban Aliyu ya dauki matarshi da iyayenshi da su Ramadan ya koma dasu cikin gidan shi. Gidan su Aliyu ya cika da farin ciki da wolwola sai dai sam Aliyu baya sake wa da Ammin shi. Meenarl kuwa tunda General ya fita take ta kuka DR Jabeer yayi iya yinshi tak'i sai cewa take. "Hamma Haiydar bashi da lafiya wallahi inajin tausayin shi." Captain Sani ne ya kalli d'an uwanshi cikin sanyi yace. "Hamma Jabeer wallahi tausayin shine jigon so da zaran tausayin ya zauna toh akwai so maitarin yawa, inka yarda ka meyarwa Hamma Haiydar matarsa shi take tausayawa ni nasan irin zaman da su kayi." Washe gari da dare Wannan magana ta Captain ita tasa Dr Jabeer karaya ganin tun jiya take kuka tak'i ko cin abinci haka ta wuni har zuwa yanzu na d'arfe 9 na dare gaba d'aya ta tsanan ta damuwan , hakan yasa Dr ya yankewa kanshi hukunci yanzu zai kaita gun Aliyu shi zai hakura da ita zai bar mishi ita, ko dan hadisin nan da ya horemu da mu sowa yan uwanmu abin da zamu sowa kanmu. Haka yasa ya kalleta cikin sanyi yace. "Muje en kaiki." Haka kuwa ta biyoshi suka taho gidan su General d'in. Shi kuwa General a dai-dai lokacin ya sallami Ammin shi ya fito da nufin wucewa cikin Jaji. A bak'in get ya tsaya ganin motar Dr Jabeer na shigowa, fitowa yayi ganin Dr Jabeer d'in ya fito rik'e da hannun Meenarl kai tsaye gaban General d'in ya tsaya cikin sanyi ya kamo hannun Meenarl ya had'a dana Aliyu cikin karfin guiwa da zuciya yace. "D'an uwana ga matar ka ni na bar maka ita har a bada dan na gane cewa a kanka Meenarl tasan so." Shiru General yayi cikin mutuwan jiki ya k'asa ko magana, Shi kuwa Dr sai murmushi yayi tare da cewa. "Fatana zaka bani auren Rayhana." Shima Aliyu sai murmushi yayi, tare da cewa "uhummm." Daga nan shikam Dr Jabeer ya shige cikin gida gun goggonshi Ammi, Shi kuwa General hannun Meenarl yajawo tare da cewa. "Minalin Hamma Haiydar zomu tafi Jaji a can zamu kwana." Sai kuma ya jawota jikin shi tare manna... By *Garkuwar Fulani* [8/26, 8:11 PM] πŸ’žIt's @lh@jiπŸ’ž: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *BANDIRAWO* page 5⃣1⃣to5⃣2⃣ *Na* *Aysha Ali Garkuwa* πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *Wannan shafi naki ne ke kad'an Fiddausi sodangi Allah ya bar zumunci* *Hak'ik'a mai sonka shike kawo maka goron gayyata da nufin kaje muhallin sa tare da baka kulawa da karramawa ta mussam man tabbas nasan kuna k'aunata k'uggiyoyin da kuka nemi da na kasance a cikin ku , ku sani bazan mantaku ba kuma har kullum a duk inda nake kuna raina Garkuwar Fulani takuce kamar yadda kuke nawa INA k'aunarku 😍😘🀝🀝 ina al'fahari daku ina kuma mai kyau tata zaton zakuyi min uzurin da kekyawan fahimta na rashin karb'ar goron gayyatar ku gareni. ina k'aunarku inamai al'fahari daku 😍😘🀝* Manna ta a k'irjin shi yana sauk'e ayijar zuciya, ita kuwa Meenarl tureshi tayi tare da janye jikinta daga gareshi cikin had'e fuska ta tura bak'in tare da juyawa tayi bak'in gate d'in da nufin zata fita gidan. Ganin haka yasa General yin sassanyan numfashin tare da binta a baya cikin sanyin murya yace. "Minalin Hamma Haiydar , fushi kikayi da Hamman ki ne?." Shiru bata kula shi ba sai ci gaba da tafiyarta tayi tana zubda k'ollah. Matsota ya kumayi cikin kula ya mik'a hannu da nufin jawota jikin shi , da sauri ta kauce tare da k'ara saurin tafiyar tata. Shi kuwa General gabanta ya sha tare da tsura mata ido fuska a tsuke yace. "Tun da bakya son ganina zoki koma gun Dr Jabeer ai shi kina son kasan cewa tare da shi." Cikin fushi da kukan da ya kufce mata tare da ci gaba da tafi yar tace. "Ehh zan tafi d'in nima zan tafi gidan mu shi ma Hamma Jabeer ai bayada zuciya ne ina jinka ai jiya kace ba ruwan ka da ni harda cewa su Abba su rik'e zuriyar su kuma ku rik'e taku dan haka nima bazan je gidan kuba." Kamar wasa yaga tuk'uru tafiya take har ta fita harabar gidan ta mik'e kan titin tana tafi yar ta ga uguwar shiru kowa na cikin gidan shi sai haske da ya gauraye kan titin ganin haka yasa shi juyawa cikin gidan cikin motar shi ya shiga tare da jan motar a hankali ya fito tare da bin bayan ta. Bappa dake cikin masallancin k'ofar gidan kuwa murmushi yayi tare da binsu da ido. Shi kuwa tafiya yake a hankali har yaje gab da ita sai kuma ya tsaya tare da bud'e mata marfin motar , tsuke baki ta kumayi k'ollah na bin hab'arta sai tafiyarta take kamar ma bata ganshi ba. Shi kuwa k'ara binta yayi a hankali har ya iso gefen ta sannan ya kuma bud'e mata motar, nan ma juyawa tayi tare da tsuke baki ta tura shi ta d'anashi sama kamar k'arin kunama. Shi kam General haka kawai yake jin shauk'in yana yin da suke cikin sai murmushi yake yi tare da shafa sajen shi. Matsota ya kumayi da motar, Amman sai ta kauce tayi gaba da sauri. a hankali Meenarl ta fara juyo sautin kukan kare yana dumfaro inda take, gaba d'aya sai ta kame jikin ta dan harga Allah tana da tsoron kare a rayuwar ta gashi titin uguwar shiru kamar ba mutane . shi kuwa General binta ya kumayi tare da tsayuwa a gaban ta ya bud'e murfi tare da tsura mata ido cikin karya wuya. Share shi tayi tare da d'aga k'afar ta taku d'aya tayi a nabiyun ta d'ago kanta cikin zare ido dan haggo karnu ka har guda 4 sun nufo kan titin da taken cikin gudu da haushi, ido ta zaro tare da juyawa ta kalli Hamma Haiydar d'in nata, ganin haik'an k'adaran kanta zasuyi yasa ta juyo cikin tsoro da fushi ta shige cikin motar tare da jawo marfin ta rufe gim. Shi kam General kai ya sunkuyar tare da sauk'e ajiyan zuciya ya figi motar a guje, tafiya yake kamar bai san da ita a cikin moton ba , ita kuwa tura baki tayi da had'a fuska ga yunwar dake k'wak'wular hanjin ta sai kawai tayi luf a jikin sit d'in tana zubda k'ollah. a haka cikin lokacin kad'an suka isa cikin Jaji kai tsaye gidan shi ya nufa dasu. Yana yin parking ya fito tare da yin mik'a sannan ya bud'e baya ya sunkuye tare da jawo laptop enshi sannan ya koma gaba ya dauko phones enshi, sai kuma ya rufe k'ofofin tare da zaga yawa gunta bud'e motar yayi ba tare da yayi magana ba, Ita ma shiru tayi sannan ta fito , tana fita ya rufe motar sannan ya mik'e ya nufi cikin gidan, da fari kamar ta tsaya so sai kuma taga gaba d'aya harabar wurin cike yake da sojojin , hakan yasa ta bishi a baya, a parlour ta riskeshi yana since igiyoyin takalmin shi, ita kuwa sai ta koma gefen ta tsaya cikin fara kuka kasa-kasa dan harga Allah yunwa takeji, Shi kuma yana cire takal man ya mik'e tare da balle beld'in k'ugunshi , ya zame wondon kakin dake jikin shi, sai kuma ya fara balle boturan rigarshi, yana gamawa ya zare rigar ya bar bocs da bes sannan ya had'e su a hannun shi ya wuce cikin bedroom. Yana zuwa kai tsaye toilet ya shige cikin sauk'e ajiyan zuciya yayi wonkan shi pes tare da murje jikin shi da sabulai masu k'amshin gaske, towel ya d'aura a k'ugunshi tare da rataye d'an k'ara min towel d'in a kafad'an shi yana fitowa gaban dressing mirror ya tsaya , hannu yasa ya rink'a murje jikin shi da mai tare da feshe duk sashin jikin shi da turaruka masu sanyin k'amshi da sanyaya zuciya gaba d'aya d'akin ya d'auki wani irin k'amshi da sanyin A,C. Ita kuwa Meenarl zuwa yanzu ta gama iya dauri yarta sai kawai ta saki kuka mai k'arfi tare da yarfa hannu tana d'an dire k'afafun ta tare da cewa. "Wayyo Allah na! wayyo Bappa na! ni dai wallahi yunwa nike ji kirjina ciwo wayyooo." Kai General ya d'ago cikin tab'e baki ya ajiye rigar baccin sa d'aya zaro sannan ya fito parlour yana gyara d'aurin towel d'in dake kan k'ugun shi. Yana zuwa gaban ta ya tsaya tare da Sa hannu ya jawota gare shi, itako sai yarfa hannu take tana d'an dukan k'irjin shi tare da cewa. "Ni dai ka maidani gun Ummi na wallahi ni gun Bappa na zaka kaini ni yunwa nikeji." Fizgota jikin shi yayi da k'arfi sannan ya matsota a jikin shi cikin had'e fuska yace. *"Meenarl* ki nitsu ki tsaya me kike so?." Cikin kuka tace. "Ni yunwa nake ji jiri nake ji k'irjina ciwo." Kai ya juya tare da Jan tsaki a ranshi yace. "Ba ga irinta nan ba RAMADAN YA KORE MIN MAI AIKI, yanzu ya zanyi." Ita kuwa jin yaja mata tsaki yasa ta tureshi ta koma kan kujera ta zauna taci gaba da kukan. Ajiyar zuciya ya sauk'e tare da jawo phone enshi , Captain Garba ya kira tare da bashi umurnin ya somo mishi d'an abin da zaici. Cikin k'ank'anin lokacin sai ga Captain Garba da aiken ogan nashi. Yana karb'a ya juya tare da rufe k'ofar gaban ta yazo ya ajiye mata ledodin sannan ya mik'e tare da shigewa kitchen pilet da cup ya d'auko, yana zuwa ya wore ledan wanda kaji ne a ciki wanda sunsha kayan had'i sai k'amshi yake tashi , kan pilet din ya baje mata shi sannan ya d'auki cop d'in ya tuttula mata juice mai sanyi, sai ya tura mata su gaban ta cikin murtuk'e fuska yace. "Sauk'o kici a cici kawai mai kukan yunwa." Tura baki tayi tare da sauk'owa k'asa ta zauna cikin share k'ollah ta fara tsakuran naman gefe-gefe tana cin tana d'an shan juice d'in, shi kuwa phones enshi da laptop nashi ya tattara zai mik'e kenan ta ture pilet d'in tare da mik'e wa tana tura baki tace. "Hamma ya isheni wonka nake son yi kuma girjina yana min ciwo." Pilet d'in ya kalla sannan ya d'ago kanshi tare da tab'e baki yace. "Ai dama ba yunwar kike jiba mai jin yunwa harda kukan ne zai cakalkali abinci yace ya k'oshi." A hankali tace. "Zanyi wonka fa." Juyawa yayi ya shige cikin bedroom yana. "Toh zoki hau kaina kiyi wonkan!." Kai ta kad'a tare da tattare pilet din ta kaisu kitchen sannan ta shige cikin bedroom d'in, shi kuwa dama yana shiga kan gado ya haura tare da watsa laptop enshi da phones nashi a gefenshi shi kuma yayi rigingine ya had'e tafin Hanna yenshi yayi pillow dasu gaba d'aya k'irjin shi a woje sai towel dake k'ugunshi. Ita kuwa tana shiga bata kalleshi bama ta shige toilet d'in cikin jin bacci ta zare doguwar rigar dake jikin ta sannan fesa wonkan ta, sannan ta kalli. towel d'in dake wurin d'an k'ara mine gashi ita kuma bata son maida rigar da ta cire yanzu, shiru tayi tare da jawo d'an bireziyar da ta cire wanda kab Momy ce take saya mata su duk da dai ita ba sakawa take yiba asalima yau ta fara sakawa dan ya bata sha'awa, mak'alashi tayi da k'er sannan ta d'aura towel d'in kan k'irjin ta kai ta sunkuyar ganin bai kai guiwarta ba, amman sai ta yi k'asa da kanta sannan ta fito , gaban mirror taje ta d'auki man shafawarshi ta shafe jikin ta sannan ta koma kan turaru kanshi ta rink'a feshesu a jikin ta tana lumshe ido, shiru yayi yana kallon yadda take feshe turarukan fees, saida taji kanshi ya isheta sannan ta je gaban shi a bak'in gadon cikin sanyin bacci da sanyin AC ta kalleshi tare da cewa. "Bacci nake ji ina zan konta ?." Lumshe ido yayi tare da nuna mata gefen shi. Ita kuma sai tsuke baki tayi tare da cewa. "Ni wurin nan ya min kad'an gashi duk ka ajiye tarka cen woyoyin ka." Shiru yayi tare da bud'e idanun shi a hankali ya tsurawa fuskar ta ido, sai ya kuma nuna mata kan k'irjin shi murya a kasalan ce yace. "Tunda ke giwace uwar birgima zo ki hau kaina ki konta tunda nan duka bazai isheki ba." Hannu ta fara yarfawa tana d'an buga k'afa tace. "Ni dai bacci zanyi gashi k'irjin yana ciwo." Haka ta rink'a mita har kusan 12 ganin hanashi bacci zatayi ya sashi mik'o hannu a hankali ya jawota jikin shi kan k'irjin shi ya kifata, hannu yasa a tsakiyar bayan ta ya rink'a shafawa a hankali murya can k'asa yace. "Dere yayi Minali kiyi baccin ki kinji ko." Kanta ta rink'a juyawa tare da murza k'afafun ta a kan nashi har tana shirin zame mishi towel d'in jikin shi cikin jin bacci tace. "Hamma kirjina wallahi kirjina ciwo yake min numfashi na yana tafiya." "Dama kina da ciwon k'irjin ne?." "A a ni Yau na fara jin ciwon." Hannun shi ya cusa cikin towel d'in jikin nata a hankali ya cusa yatsun shi biyu ya kamo robar bireziyar nata sannan ya sake shi pet a bayan ta cikin rad'a yace. "Yaushe kika fara saka wannan abun?." "Yau ne nafa ta sakawa." Ido ya lumshe sannan yace. "Toh zan cireshi dan shine yake saki ciwon k'irjin." Shiru tayi tana shak'an k'amshin jikinshi . Shi kuma hannun shi ya saka tare da ture laptop nashi da iPhone nashi can gefen sannan ya murza k'afafun shi ya waresu, ita kuma ta gyara konciyarta, k'ara tallabeta yayi tare da had'e hanna yenshi duka biyu kan tsakiyan bayan ta sannan ya balle brzyar , a take Meenarl taji gaba d'aya ciwon girjin ya sake sai ji tayi kamar an kunceta . Shi kuwa a hankali ya tura hannun shi a tsaka nin k'irjin su, kamo jikin brzyar yayi tare da zaro shi ya fidda shi gefe, ita kuwa jin zafin zarowan yasa ta d'an d'aga k'irjin ta sama. Shi kuwa General idanun shi ya rumtse da k'arfi dan k'ok'olwarshi bazata iya juran ganin k'irjin ta a hakaba. Ita kuwa cikin jin kunya tayi sauri ta kife k'irjin ta a kan nashi k'irjin tare da lumshe ido. Shi kam General wasu irin ajiyan zuciya ya rink'a direwa a jere a Jere gaba d'aya jikin shi ya rink'a tsuma ida nunshi suka k'asa bud'uwa ya koma tamkar makaho, sai manneta da ya karayi a jikin shi k'irjin shi na duka tara-tara ba abinda yake fad'i sai. "Meeenarrhl zaki kashe Hamman kifa." Itama gaba d'aya jikin ta sai kerma yake ta k'asa magana dan kab tsikar jikin ta ya mike' tsaye sai yatsun ta ta cusa cikin suman kanshi tana murzawa. A hankali General ya mirgina ta cikin rawan jiki ya tsurawa fuskar ta ido murya can ciki yace. "Minalin Hamma ?." Sai kuma yayi shiru yana sauk'e nannauyan numfashi. Ita Kuwa mik'e wa tayi cikin rawan jiki ta zauna a tsakiyar gadon , shima tashi yayi ya durk'usa tare da jawota gare shi rugume ta yayi da k'arfi sannan ya d'ago fuskarta tare da lumshe ido ya manna lips enshi kan nata cikin wani yana yin ya rink'a sauk'e mata muguwar kasala sai sakewa tayi a jikin shi tare da rugume shi tana lumshe ido tare da murza k'afafun ta, a haka har ta ture mishi laptop enshi, Amman ina basuma san ya fad'in ba. Jawota yayi suka konta sannan ya jawo blanket ya rufe su , ita kuwa hannu tasa tana tureshi jin yana kauce zatonta , sai kawai ta saki kuka cikin tsoro tace. "Hammahh kayi hak'uri barni inyi bacci ka barni." Jin haka ya sashi juyawa da k'arfi ya kifu tare dasa hannun shi d'aya ya rugume ta cikin wani yana yin yace. "Nah.. Nha.. Nah bar ki kar kiyi kuka Meenarl tunda ba kya so na barki." Haka suka kwana rugume da juna. Da Asuba General ya mik'e cikin lumshe ido yaje yayi wonka tare da yin alwala, masallaci ya wuce dan bin jam'i shine bai dawo ba sai 7 dai-dai. A parlour ya samu Meenarl konce kan 3 str fuska ya murtuk'e dan har cikin ranshi yake jin zafin abin da tayi mishi a daren jiya gani yake ko Dr take so. Fuska a murtuk'e yayi kanta tare da... By *Garkuwar Fulani* [8/26, 8:11 PM] πŸ’žIt's @lh@jiπŸ’ž: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *BANDIRAWO* page 5⃣3⃣to5⃣4⃣ *Na* *Aysha Ali Garkuwa* πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *Yebon goni ya zama dole hak'ik'a rigar mutunci kan sanya a zatawa mai sanyashi mutunci kinkai a yebi ki, mu matan arewa muna yebawa da halin ki da shigarki Namecy tawa AISHA LAWAN UMAR jarumar ma aikaci mai mutunci tauraruwar AREWA 24 Garkuwar Fulani ke mik'a sak'on jinjina a gareki🀝😍😘* Sunku yowa kanta yayi pillow d'in da ta matse a k'irjin ta ya zare a hankali sannan ya d'an durk'usa murya can ciki yace. "Meenarl a nan zakiyi baccin ai wuyan ki zaiyi ciwo." Kai ta juya cikin jin dad'i baccin safiyar ga garin yayi lum alamun hadari ga iska mai dad'i ga kasan cewa cikin tsabta ceccen wuri mik'a ta d'an yi a hankali ta kai hannun ta kan, fuskar shi sajen shi ta shafa a hankali, Ido ya lumshe tare da sauk'e ajiyan zuciya shima hannun shi ya d'aura a kan goshin ta tare zubawa kirjin ido murya a raunane yace. "Muje kan gado kiyi baccin anjima zan shiga cikin KD zan dauko miki kayan ki." Ido a lumshe cikin muryar bacci tace. "Uhmmm Hamma." Matsota ya kuma yi a hankali yace. "Na'am Minali ." Sai ta kuma lumshe ido tace. "Bacci nake ji Hamma jikina ya mutu bazan iya tashi ba." Murmushi yayi tare dasa hannu ya gyara mata wuyan rigar ta dake zamewa sannan ya mik'e a hankali hannu yasa ya tallabo ta tare da manata a jikin shi , bedroom ya wuce da ita kai tsaye kan gadon ya direta cikin kula yasa mata pillow sannan ya jawo blanket ya rufe ta , sai kuma ya juya tare da d'ago laptop enshi da iPhone nashi juyawa yayi gareta ya ajiye su kan y'ar karamar durowar dake gefen gadon , a hankali yace. "Saura kiyi birgima ki turomin laptop na ki karasi min shi haka jiyama da dare kika rad'a min su da k'asa." Ita dai baccin ta fara tare da tura mishi baya. Shi kuwa kai tsaye parlour ya koma ya sassake labulayen sannan ya rufe windows d'in sai kuma ya shige kitchen cikin sauk'i ya had'a musu breakfast mai sauk'i sannan ya kimtsa komai, tea ya d'an had'a sannan ya dawo parlour tare da kunna TV yana kallin CNN, tea d'in yake sha yana d'an sauri d'an yana son yaje yaci abincin Ammin shi , shiyasa ya d'an Sha ruwan tea d'in kad'an sannan ya mik'e ya shige bedroom d'in . murmushi yayi ganin yadda Meenarl ke takure dan sanyin dake kad'awa ga kuma sanyin AC murmushi ya kuma tare da shige wa toilet a ranshi yana . "Ai kin saba sanyin garinku ba irin wannan bane." Wonka yayi tsab sannan ya fito yana fitowa yaje gaban mirror ya kimtsa tsab da sauri-sauri a nufin shi kafin ruwan ya sauk'o ya isa gida. Yaje gaban durowar da nufin fito da kayan da zai saka, a dai-dai lokacin kuma ruwan ya sauk'i kamar da bak'in k'woriya ruwan mai sauk'a a hankali sai iska mai sanyi. Shiru yayi a ranshi yaso sai ya isa kafin ruwan ya sauk'a. gashi gaba d'aya wani irin duhu ya rufe ko ina. Parlour ya nufa tare da gyara d'aurin towel d'in dake k'ugunshi, TV ya kashe sanan ya kashe bok d'in baki d'ayansu, Komawa yayi ya dauk'o phone nashi yazo parlour kan 3 str ya zauna tare da shiga yanar gizo-gizo a nufin shi ya d'an zauna kafin ruwan ya d'auke . Shiru ruwan sai sauk'a yake har yafa rajin sanyin na ratsashi gaba d'aya jikin shi yayi bacci kasala ta rufeshi, Hakan yasa dole ya mik'e cikin yin mik'a bedroom ya nufa yana zuwa ya ajiye woyar sannan a hankali ya konta gefen Meenarl tare da Jan blanket d'in ya rufe su , matsawa gefen ta ya kumayi d'an baya son abinda zai had'e jikin su wuri d'aya , ita kuwa hajiar birgima daga jin alaman mutun ta k'ara mirgi nowa cikin sanyi ta d'aura hannun ta kan k'irjin shi ,kai ya juya ya kalleta da kyau tabbas bacci takeyi , fuska ya tsuke d'an shi harga Allah gani yake muguntan ce , kanshi ya juya da nufin cire hannun ta sai kuma kawai yaji ta sake d'aura mishi cinyarta kan nashi cinyar sannan a hankali ta cusa kanta a kafad'an shi, gaba d'aya ta kanai nayeshi sai faman baccin ta take. Shiru yayi yana kallon ta ita ko a jikin ta yayin da shiko ta rabashi da nitsuwar shi, sai ajiyan zuciya yake direwa a kai akai. Cikin lumshe ido ya juyo gareta baki d'aya , hannun shi yasa a hankali ya zuge zib d'in rigar ta ido ya tsura mata yadda ta k'ara k'amk'ameshi lips enshi ya lasa a hankali ya jawota jikin shi, manna ta yayi da k'irjin shi da kyau sannan ya jawo blanket ya rufe su da kyau, sai kuma ya fara sauya salon konciyar tasu da darrusan sa masu wuyan fad'i. Cikin baccin taji wani sabon salo ido ta bud'e a hankali ta diresu kan fuskar General da ya gama yin mutuwar konce, a hankali ta fara janye jikin ta murya can k'asa tace. "Hamma." Janta ya kumayi tare da cewa. "Ina zaki je?." Ido ta rumtse tace. "Ni baccin ya ishei zan koma parlour." Matsota yayi sosai yace. "Me yasa kike son azab tar danine ? me yasa bakya son na rabeki alhalin kuma kece kike fara shige wa gareni." Kai ta juya cikin rashin son abinda yake matan tace. "Ni dai wallahi bana so ka barni ." Mik'ewa yayi sannan ya shige bathroom wonka yayi ciki sauri-sauri, Yaya fitowa y kimtsa tsab cikin shadda maikalan sararin samaniya ya fito rasa kamar tauraro sai k'amshi yake zubawa ya k'afa hularsa ras , ita kuwa dama yana shiga wonka ta dawo parlour. Parlour ya fito rik'e da tarkacen sa bai kalli ko inda take a yanufi hanyar fita, ganin haka ta mik'e da sauri ta bi bayan shi tana . "Hamma Haiydar ina zaka je?." Bai ko kalleta taba, cikin sauri taje gaban shi kanta a k'asa tace. "Ayyah Hamma na , ina zaka je ka barni a nan kasan fa ina tsoro kuma ba kowa a gidan." Fuska a tsuke yace. "Ni ba Hamman ki bane ai kinsan waye Hamman ki da kike so, batun ina zanje kuma gidan mu zanje, zanje gun Ammi na kuma ke kin ce bazaki je gidan muna." Da sauri tace. "Toh zanje gidan mu nima." Ci gaba yayi da tafiya tare da cewa. "Ban hanaki ba ai gaki ga hanya kije gun Jabeer d'in." Yana kaiwa nan ya fice tare da Jan k'ofar ya rufe. Kai tsaye gidan su ya nufa. Ita kuma yana fita ta koma tsakiyar parlour ta zauna ranta a b'ace ya zaiyi ya barta a gida ita kad'ai haka ta zauna cikin fushin. Shi kuwa General yana shiga cikin gidan a babba parlour su ya samesu kab dinsu Bappa na zaune a cikin su kamar sarki gaba d'aya zuriyarsa a had'e sai Mama ce da Abdul basa wurin. Gefen Bappa ya zauna cikin son tsohon yace. "Bappa barka da rana." Kanshi ya shafa tare da cewa. "Barka dai Aliyu , ya gida ina Bodd'i na?." Murmushi yayi tare da cewa. "Na barta tana bacci tace a gaida Ku." Murmushi Inna tayi gami da cewa . "Aliyu ka barta ita d'aya a wancan gida naka mai cike da sojoji ." Rayhana ce dake gaban Dr Jabeer yana yanke mata farce tayi shiru tana jinsu shiko Dr yanke mata farce yake yana kallon ta cikin k'aunar da ya dad'e yana yi mata a zatonshi Meenarl yake so sai yanzu ya gane Meenarl tausayawa ce a tsaka ninsu. Aliyu ne ya mik'a mishi hannu suka gaisa . Murmushi Dr yayi tare da Sosa k'eya yace. "Hamma Aliyu ai nizan zo na kawo gaisuwa dan ka zama surki." Kanshi General ya d'an buga tareda cewa. "Inma tson kana ta zakayi ka sani dai na fika da wattani har 8." Dariya sukayi baki d'ayansu. Sannan Ramadan ya kalli General cikin rawan kanshi yace. "Hamma Aliyu har Hamma Sani ma ya zama surkin ka , d'azu Abban Meenarl yazo ya nema wa Hamma Jabeer auren Rayhana ya kuma nema wa Hamma Sani auren Nafeesat kuma duk an basu saura biki kawai." Sai ya kuma matso kusa da General tare da karya wuya yace. "Hamma Aliyu toh ni kuma da Abdul yaushe zamu auru? gaskiya muma a aurar damu? wallahi inba haka ba muyi tawaye dan mun gani da zaman gida ayita maida mu yara." Gaba d'aya parlour suka kwashe da dariya Captain Sani harda buga tafi, Bappa ma dariya yake sosai , Dr Jabeer ne cikin murmushi yace. "Ashe yaushe zaku auru?." Sai suka kuma dariya. Ya Amir kuwa dariya yake harda rik'e ciki ya jawo Ramadan jikin shi yana. "Insha Allah kuma zaku auru Ramadan, kaida Abdul zamu kai sadakar Ku a masallaci wata kil a samu masu tayawa." Daga nan kuma suka cin gaba da dariya . Daddy da Abba kam sai kallon su suke cikin nisha d'in da happy. Abdul kuwa dake zaune gaban Mama yana kuka tana kuka tana cewa. "Abdul na cucu kaina Na bata lahirata Abdul na cucu Ammin Aliyu na bita da sharri gashi ita kuma sai nasara ke bin rayuwar ta, gata ga mijin ta ga yaran ta ga surkana yenta kowa sonta yake ga yan uwanta da 'ya'yan y'an uwanta gida duk ya cika da family enta , nayi asirina rabata da mijnta ba tare da hakkin ta ba gashi asirin ya karya ya barni da tarin zunubai." Cikin kukan Abdul ya mik'e tare da cewa ni dai zan nemi gafarar yan uwana kema ki nemi gafararsu sannan ki tuba ki koma ga Allah ki kuma kisan duk abinda kikayi Allah na ganin ki ni zanje cikin su kinga yadda kika samun tsanan Hamma Aliyu kalli yadda Ramadan ke sona har kunya nake ji." A haka ya dawo parlour akaci gaba da yin hira da dariya dashi. Shi kuwa General mik'ewa yayi ya nufi bedroom ensu a daa yanzu kuma na Ammi ne. Murmushi yayi ganin an canza mata kayan d'akin sannan suma na dad'in sunan. A hankali ya zauna gefen ta a kan sallayar da take zaune tana k'ara tun qura'ani mai girma. Ganin ya zauna ya tonk'oshe k'afafu yana sauraron sautin kara tun nata yasa , ta d'an k'ara k'ara tun shafi 3 sannan ta d'aga hannu ta rink'a yin addu'oi , shima hannu ya d'aga yana amsawa da Amin-Amin, suna shafa wa Ammi ta kalleshi cikin sanyi tace. "Babana yaushe ka iso? ina Meenarl d'in kuma?." Murmushi yayi tare da lonk'oshe wuya ya gaida ta sannan yace . "Ammi me kike buk'ata." Murmushi tayi itama sannan tace. " ba komai Haiydar duk abinda nake so Abban ka ya gama minshi." Haka sukayi ta hira cikin soyeyya irin ta UWA da d'anta. Ahaka Ramadan da Rayhana tare da Dr da Captain da Nafeesat suka shigo suma akayi ta hirar dasu. Ammi sai nan nan take da d'anta gudan jinin ta. A haka suka wuni cikin Happy yayinda Bappa ya kara had'a wa General wasu addu,oin a cikin zam-zam ya wuni yana sha. Bayan sunyi sallan la'asar ne suka shigo gida . General ya kalli Ammi a hankali yace. "Ammi a had'a mana kayan mu zan tafi dashi ." Cikin k'aunar d'an nata ta had'e musu kayyaya kinsu kab sannan su Ramadan da Abdul suka kaimishi su cikin motarsa. Shine bai tafi ba har 8:28 pm . Bappa ne d'aya shigo yanzu ya kalleshi tare da cewa. "Aliyu har yanzu baka tafi ba? , ga hadari ya kuma had'uwa." Nafeesat ce tayi dariya tare da cewa . " Bappa hadari kuma? da safe akayi ruwa fa." Ya Amir ne ya mik'e yana cewa. "August d'in kenan ai." Abba ne ya kalleshi tare da cewa. "Kar ruwan ya tsare ka gashi ka kabar Meenarl d'in ita kad'ai." Haka ya musu allama sannan ya fito , har ya shiga mota Ramadan ya fito rik'e da kuloli guda biyu ya bud'e bayan motar ya ajiye mai cikin k'aunar Hamman nashi yace. "Inji Ammi a kaiwa Bodd'i." Toh kawai yace sannan sukayi saida safe, ya shiga mota ya kama hanyan Jaji, sauri General yakeyi dan baya son ruwan ya tab'a shi shiyasa ya kama hanyar cikin wani irin shauk'i da jin dad'in yana yin garin, a ranshi yakeji yau zai kasan ce cikin wata rayuwa mai dad'i d'an yana jin wani yanayin da yafi karfin ya jumre. A dai-dai lokacin da... By *Garkuwar Fulani* [8/26, 8:11 PM] πŸ’žIt's @lh@jiπŸ’ž: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *BANDIRAWO* page 5⃣5⃣to5⃣6⃣ *Na* *Aysha Aliyu Garkuwa* πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ A dai-dai lokacin da yayi parking a harabar tasu , ruwan ya kece kamar da bakin kworriya, ruwan ne yake zuba da k'arfi sai wolk'iya da rugugi akeyi , hannu General yasa ya dafe siterin tare da komawa ya jingina da jikin sit d'in yana kallon ikon Allah ruwane yake sauk'a harda k'ak'k'ara yana jin yadda suke sauk'a kan glass d'in tabbas badan ko bulet bazai fasa glass d'in ba toh da k'ank'aran ya fasa, Ido ya lumshe cikin jin sanyi na ratsashi lokaci d'aya kuma wutar NEPA ta d'auke gaba d'aya wurin yayi duhu , Juyawa yayi ya kalli cikin motar kab ba leima gashi ba jacket ko wani abin da zai saka a kanshi ko a jikin shi, gashi gaba d'aya sojojin sun shige cikin mafakarsu A hankali yake fad'in. "Allah humma saiyi ban nafi an" sai kuma yayi shiru yana tuno Meenarl ita kad'ai, zaman ya gyara a nufin shi sai ruwan ya d'an sahirta amman sai kuma kamar karuwa ruwan yake ganin haka yasa dole ya bud'e motar a hankali ya zuri kafarshi wojo, tsilum ya jishi cikin ruwa ga wani irin sanyi daya ratsashi, fita yayi cikin k'amk'ame jikin shi , gaba d'aya ya jik'e cakab a lokaci kad'an , tuni ya fara karkarwa da sauri ya bud'e bayan moton ya d'auko kulolin da Ammi ta had'oshi dasu, sannan ya tura phones enshi cikin jakar laptop enshi sannan ya rataya a kafad'an shi, hannu shi rik'e da kulolin ya juya cikin duhun ya nufi cikin gidan tafiya yake cikin duhu sai hasken walk'iya ke haska mishi hanya kad'an-kad'an, tuni ya fara rawan sanyi, sai d'iga yake tol-tol , da sauri-sauri gudu-gudu ya isa k'ofar parlour nasu cikin rawan hannu yasa key ya bud'e k'ofar tare da shigewa ciki yana shiga ya ajiye kayan kan dinning table cikin rawan sanyi ya zaro woyarshi tare da kunna torch d'inta gaba d'aya haske ya gauraye parlour, cikin rawan sanyi ya fara lek'a cikin parlour tare da kiran. "Meenarl! Meenarl! Meenarl! ina kike Bodd'eee ina kike ne?." Shiru ba ko motsinta, Ita kuwa Meenarl tunda General ya fita ta zauna cikin fushi a parlour ta wuni saida taji yunwa na sata jiri sannan ta je dinning area ta d'auko abinci tazo taci , sannan taci gaba da yin kallon ta sai kusan karfe 6:20 ta tashi taje tayi wonka tare da yin sallah, qur,an d'in General ta d'auko tayi ta karatu har lokacin ishah yayi sannan tayi sallah , duk a lokacin tana jin hayani yar sojojin da suke zagaye da gidan , har tana haggosu ta windows d'inta haka yasa bataji tsoro sosai ba, dan inda sabo ta saba zama ita d'aya tunda ta shigo rayuwar General, Karfe 8:30 pm ne taji wurin yayi shiru ba motsin kowa ga iska dake kad'a wa , lokaci d'aya kuma ta fara ganin duniyar tayi lum ko ina yayi shiru sai walk'iya dake ratsa ko ina , hakan yasa ta fara jin wani irin tsoro na ratsata jin shiru hakan yasa ta mik'e da sauri dan ta d'an watsa ruwan ta zo ta konta kawai, cikin sauri sauri tayi wonka tare da d'aura towel a k'irjin ta, sannan ta bud'e k'ofar da nufin ta fito zuwa cikin bedroom d'in tana sa k'afar ta, a dai-dai lokacin aka d'auke wuta wani irin duhu ya mamaye d'akin gaba d'aya ba abinda take gani koda tafin hannun ta, cikin wani irin mugun tsoro ta zoro ido dan a duniya ba abinda Meenarl take tsoron kasan cewa a ciki kamar duhu dan tsawa da rugugi da walk'iya basa bata tsoro kamar duhu , cikin k'ank'anin lokaci ta fara zubda k'ollah tare da kiran. "Hamma ! Hamma Aliyu na shiga muku ni kad'ai a gida ga duhu ga tsawa! wayyo Bappa na." Sai kuma ta lalubo zata hakura kan gado sai ji tayi ta gum a jikin gini haka kawai sai idonta yake mata gizon Abdul, haka yasa ta zame a wurin tsakanin durowar da gini ta kife kanta cikin guiwowin ta ta saki kuka cikin tsoro. Hakan yasa bataji kiran da General yake mata ba, Shi kuwa cikin rawan sanyin ya shige cikin bedroom d'in yana . "Meenarl kizo gani na dawo." Cikin lugun da taken ta fara ganin haske cikin kukan ta d'ago kanta ganin Hamma Aliyun ne yasa ta mik'e cikin gudu ta fad'a jikin shi baki na rawa take fad'in. "Hamma Aliyu tsoro nake ji duhu a tayar manada generator Hamma duhu yayi yawa." sai kuma kawai ta fashe da kuka tare da rugume shi , shi ma rugume ta yayi gaba d'aya jikin shi rawan sanyi yake har haqoran shi na bugar juna kat-kat, a kid'ime ya k'ara rarumota yana magana cikin rawan murya yace. "Meenarl sanyi sanyi nake ji Meenarl sanyi zai kashe ni ." Gaba d'aya ya birkice Dan shi General matukar ruwan ya tab'a shi toh baya hanya cinsa, Ita kuma sai cewa take. " Hamma ka kira Captain Adam ya kunna generator." Kai ya juya cikin rawan sanyi yace . "Toh zan kirashi." Woyar ya d'ago da niyar kira a dai-dai lokacin kuma charge woyar ya kare kab sai tut-tut phone d'in ya mace duhu ya cuna na bayan gaba d'aya ko fuskar juna basa gani. Ita kam Meenarl rarumo General tayi ta rugume shi tsam a jikin ta, tana . "Hamma! Hamma duhu fa duhu Hamma ." Cikin rawan sanyin yace. "Meenarl gani gani ba komai ki nitsu kinga sanyi najeji har cikin k'asusuwana ki matsa zan cire kayan nan a jik'e suke." Ina Meenarl sai k'ara k'wak'umoshi takeyi ganin haka yasa cikin rawan sanyi, ya zuge mazargi wondon jikin shi cikin rawan sanyi ya sab'ule k'afafun shi a ciki sannan ya balle botur din wuyan rigar tashi tare da d'an janyewa jiki ta ya zare rigar ya wurga a k'asa , ita kuma sai k'ara motsishi tayi tana mik'e hannun shi , a hankali ya zare bes d'in jikin shi dake d'iga ya ajiye a gefen, cikin rawan murya yace. "Meenarl sake ni zan nemi kayan sakawa sanyi nake ji ki matsa zan cire kayan nan. Hannu shi ta kuma rik'e wa tare da manna kanta a damtse hannu shi cikin kuka tace. "Wayyo Hamma nace a duhu ni ina tsoro." Kai ya juya cikin d'an janye k'ugunshi ya Sa hannu a hankali ya rink'a yin k'asa da bocss d'in shi ya zame k'asa ya rege daga shi sai fatan jikin shi, cikin kunya ya janye hannun shi dan baya so tasan a haka yake tsaye cikin rawan murya yace. "Haba Meenarl ki sakeni kayan zan saka." Janye hannun shi da yayin, yayi dai-dai da lokacin da aka buga tsawa, hakan yasa cikin tsoro Meenarl ta fad'a jikin shi hakan ya sa Towel jikin ta ya sule k'asa. rugume shi tayi tsam a jikin ta dan ita tsoro ya ma hanata gane a yanayin da suke ciki, Shi kam General wani irin marayan numfashi ya fitar tare dayin tagal-tagal kamar wanda ke ciki maye cikin wata iriyar murya yace. "Wayyo ni Aliyu , Meenarl! Meenarl! ." Sai kuma kawai ya rugumota cak a jikin shi cikin Marisa da lalube ya dire da ita kan gado , gaba d'aya jikin shi rawa yake yi , blanket ya jawo ya rufe su cikin wani sabon salon ya jawota jikin shi murya can k'asa yace. "Meenarl kece maganin sanyin dake son kasheni, Meenarl ki tawo gareni." Ita dai mak'ale shi kawai take tana shigewa jikin shi. Shiko General gaba d'aya ya susuce da albarka tun k'irjin ta hannu da bak'in shi kab aiki sukayi , sai juya ta yake a jikin shi yana murza ta. cikin sanyi ya maidata kan ruwan cikin shi, yana shafa gadon bayan ta, ita kuma gaba d'aya ta narke mishi sai juyi take tana goga jikin ta a nashi , cikin rawan jiki General ya yunk'ura zaune jawota jikin shi yayi hab'arta ya tallabo cikin sanyi ya manna lips enshi kan nata, kissing d'inta ya rink'a yi cikin iyawa da salon jarumta, ita ma rugume shi tayi cikin lumshe ido ta kamo hannu shi ta d'aura kan k'irjin ta, Ajiyan zuciya ya sauk'e cikin yanayin da zai iya suma ya zare bakinshi daga nata kanshi ya kife a k'irjin ta cikin jawo hannun ta ya cusa a mararshi cikin rawan murya yace. "Minali zan mutu Minali ki jikai na kar na zauce Meenarl ki bani hakk'i na." Hannunta ta janye cikin yin mik'a tace. "A a ni wallahi kana bani tsoro Hamma kaji yadda kake numfashi fa ga yadda kakeyi ni ka barni." Matsota yayi kamar yaro ya dora kanshi kan cinyarta yayin da hannu shi ke kan k'irjin ta murya a hargitse yace. "Meenarl kefa ba jahila bace kina da ilimi kinsan mene Aure toh meyasa kike son na k'asa ni?." Ture kanshi tai cikin tsoro tasa k'afa ta sauk'a tana. "Ni bana son duhu ni dai ka nema min haske." A zahiri kuwa yanzu ba duhun take tsoro ba General d'in ne ya bata tsoro ganin gaba d'aya ya koma kamar zaucecce. Shi kuwa cikin rawan jiki ya mirgino bak'in gadon murya can k'asa ya kamo hannun ta ya fizgota jikin shi gaba d'aya ya kanainaye ta, k'irjin ta ya rink'a murza wa murya na rawa yace. "Ba kya sona! bakya son na rab'eki! toh meyasa kike son na tab'a ki? meyasa kwana ki keda kanki kike kusan toni? wato dan kinsan a wannan lokacin bani da lafiya ko ? shine kike wasa da jikia da hankali na ko? Nikuma na biye miki duk da ba abinda nake ji a wannan! lokacin zanyi duk yadda zanyi na sama miki sauk'i! Amman ke yanzu ko mutuwa nayi ba ruwan ki ko?." Tureshi tayi tare da cewa. "Toh ni in tsaya ka kasheni ne Hamma ji yadda kake yamushe ni fa?." Cikin lallashi yace. "Dan Allah Meenarl kiyi hak'uri wallahi banzan iya jurewa ba , karkisa na miki abinda kike tsoron da k'arfi nima ina sane ke baby ce wallahi zan biki a hankali banzan wahala da keba, Pls Minalin Hamma ki tausa yawa mijin ki ." Baki ta tura tana . "Ni dai wallahi a a da dabana nan fa." Zuwa yanzu ya gama hatsala cikin fushi yace. "Toh Meenarl barni barni na mutu Amman wallahi ki Sani ina gab da turnuk'eki koda karfin tunda ina tausaya miki baki tausaya min,." Sai ya koma gefen ya konta a kife cikin rawan murya irin na maison yin kuka ya kife tare da cewa. "Muguwa kawai Meenarl Ashe muguntarki a kaina zaki gwada shi , Amman na barki da Allah, Allah zai saka min." Sai kuma ya mik'e jikin duhun ya shiga toilet ruwan d'umi ya sakewa kanshi yana mai zubda k'ollah tamkar yaro a haka ya fito cikin duhun ya lalubo towel ya d'aura kenan NEPA ya dawo, gaba d'aya ko ina ya cika da haske, ita kuwa Meenarl dama zaune take ta jawo blanket ta rufe iya cikin ta,k'irjin ta kuma yayi tirtsi-tirtsi yana shek'i, da sauri taja blanket d'in ta rufe jikin ta tare da kallon General dake damk'e da maraya yana tafiya a hankali , bai kalli ko inda take ba ya d'auki woyarshi parlour ya koma ya had'a abubuwanshi a charge, sannan ya koma kan str 3 ya konta tare da rumtse ido hawaye na bin fuskar sa, lokaci d'aya zazzab'i mai zafi ya rufeshi. Kanshi yake tausa yawa shi wato bazai tab'a samun abinda yake so ba a lokacin da yake son abin ba. Ita kuwa Meenarl ganin yadda ya fitan ne ya cika mata zuciyar ta da tausayin shi gaba d'aya sai taji bata kyauta ba. Parlor ta fito gaban shi ta durk'usa cikin sanyi tace. "Habba baka da lafiya ne?." Idon shi ya bud'e wanda gaba d'aya sun rine, cikin takaici ya buga mata tsawa yace. "Ban sani ba Meenarl me had'inki da ni ki fita harka ta bana son ganinki ki barni inji da cutar da kika samin muguwa kawai." Jiki a mace ta juya ta tafi tana kallon yadda idanun shi suka rine. Haka General ya kwana cikin halin k'ak'ani k'ayi ga zazzab'i, koda asuba tayi ko masallaci ya k'asa zuwa da k'er yayi wonka sannan ya dawo parlour yayi sallah yana idarwa ya koma ya konta yana ta rawan sanyi. Ita kuwa Meenarl wonka tayi sannan tazo tayi sallah ganin ta gaji dasa Riga d'aya , kawai sai ta bud'e durowarsa cikin sa'a ko ta samu wata y'ar jallabiyar shi da ta mishi kad'an ta zura a jikinta sannan ta yane kanta da gyelen ta, parlour ta fito lokacin har 12 tayi, a hankali tace. "Hamma Ina kwana." Bai kulawa ba sai woyarshi da ya zaro cikin sanyi ya fara magana. "Ammi ina kwana.?" "Lafiya kuwa naji muryar ka haka?." Kai ya juya a hankali yace. "Ehh lafiya ta lau Ammin." "A a kam Aliyu baka da lafiya daga jin muryar ka, ga Jabeer yanzu zaizo ya duba ka." Kafin yayi magana ma ta katse kiran, sannan tasa Dr Jabbe da Rayhana suka taho Jajin. Suna zuwa Dr Jabeer ya dubashi tare da bashi magani itako Rayhana tuni taja Minali suka shige kitchen suka had'a musu abinci. Meenarl sai dariya take dan taji dadin ganin Rayhana , shiko General gaba d'aya ya cika da takaici dan gani yake ganin Dr jabeer ne ya sata happy hakan yasa ko maganin bai shaba abinci ma yak'i cin a ranshi yake cewa. "Zanyi maganin ki insha Allah zan miki abinda bazaki sake kallon Jabeer a namiji ba." Shiko Jabeer gaba da hankalin shi na kan Rayhana narshi. Sune basu tafiba sai dare. 11:12 pm Aliyu ya shige cikin bedroom d'in fuska a had'e yace. "Ke tashi kije kiyi al,wala kizo." Cikin sanyi tace. "Ni nayi sallah fa." Tsaki yaja tare da cewa. "Ina magana kina min gardama ko nace kije kiyi alwalah kizo." Sum sum ta mik'e taje tayi sannan ta fito , hijabin ta ya cillah mata tare da shimfid'a sallaya cikin tsuke fuska yace. "Motso nan nafila zamu yi." Ba musu ta matso dan ta lura yau ya koma General a fili ba Hamma yake ba. Nafila sukayi raka'a 2sannan bayan sunyi sallama ya juyo gaban ta suna fuskar tar juna cikin tsuke Fuska yasa hannu shi a tsakiyar....... By *Garkuwar Fulani* [8/26, 8:11 PM] πŸ’žIt's @lh@jiπŸ’ž: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *BANDIRAWO* page 5⃣7⃣to5⃣8⃣ *Na* *Ayshah Aliyu Garkuwa* πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *Alhamhadullih lillahi Allah kulli halin Masoyan JANNART LAMID'O (Y'AR GATAN GARKUWAR FULANI) mu godewa Allah Jannart dai tana Raye! BATA MUTUBA sai dai INA rok'onku da kusata a Addu'a Allah ya bata lafiya My dear Jannart Allah ya baki lafiya Mommonki Garkuwa tana miki fata da addu'ar samun lafiya Allah ya tashi kafad'an ki I love you so much my dear Jannart* *tun 1:13 pm nayi typing wannan labarin ya hanani samun damar posting nayi kuka har idona ya kumbura sai yanzu naji Sanyi a raina da naji muryar Baby Na Jannart* *Wayyo na kusa inyi tuya na manta da albasa kuji ku kuma sani ku shaida tabbas har cikin raina hakane kuna cikin raina wlh ina al'fahari da ku groups d'in zaman lafiya da k'aunar juna da mutun ta kai groups dina ina sonku *TABITAL FULAKU tare da GARKUWAR FULANI GROUP da kuma GARKUWA AYSHA & UMMEE novels Group tare daku BANDIRAWO FANS Group ina k'aunarku ina al'fahari daku😍😘😘😍🀝* Hannu shi yasa a tsakiyar kanta cikin sanyi ya rink'a jero addu'oi hannu shi dafe da kanta, ita kuwa ido ta d'an d'ago tana kallon fuskarsa dake murtuk'e a haka har ya gama Addu'ar sannan cikin lumshe ido ya juya tare da jawo qura'ani mai girma ya fara karatu cikin cikekken tajwid, gyara zama Meenarl tayi cikin jin bacci tayi hammmah tare da mik'a sai juyi take, bai kulata ba har zuwa wani lokacin sannan ya mik'e tare ajiye Qur'anin. Kanta ya juyo murya can k'asa yace. "Kinci a abinci?." Kai ta gyad'a cikin jin shayinshi tace. "Ehh." Parlour ya fice kai tsaye kitchen ya shiga cup ya d'auko tare da tsiyayo madara mai sanyi da gard'i sannan ya fito parlour ya kashe komi tare da sassake labula yen sannan ya nufi bedroom d'in. Ita kuwa Meenarl dama yana fita tayi maza ta haura kan gado cikin kasala ta jawo blanket ta rufe kanta, jin motsin shigo warsa ya rufe k'ofar ne yasa tayi maza ta rufe idanun ta ita a dole bacci tayi. Yana rufe k'ofar ya zo gaban ta murya a cushe yace . "Tashi ." Jin muryar a cushe yasa ba musu ta mik'e zaune, ido ya kafa mata tare da mik'a mata cup d'in madarar yace. "Karb'i ki shanye." Ba musu ta karb'a ta kafa kai ta rink'a zuk'a a hankali tana lumshe ido dan sanyin shi na ratsata. Shi kuwa Gaban durowa yaje a hankali ya zare jallabiyar jikin shi sannan ya bar bocss da bes sai kuma ya koma gaban mirror turare ya feshe jikin shi tsab gaba d'aya ya cika da k'amshi ga sanyin yanayin gari ga sanyin A,C ga k'amshin furanin tsirren dake bayan d'aku nan nasu. Kusa da ita yazo rik'e da woyarshi hannu yasa ya karb'i cup d'in sannan ya ajiye a kan y'ar k'aramar durowar, jikin gadon ganin ya nufa ta, itako sai ido take binshi da su ganin gaba d'aya yau a General d'in shi yake, cikin tsoro ta zaro ido ganin ya kashe wutan d'akin, baki na rawa tace. "Hmm. Hamm. Hamma. ka kashe wuta kuma? kalli duhu fa." Bai kula taba sai zuwa yayi ya konta gefen ta cikin lumshe ido , ita kuwa laluboshi ta farayi tana. "Hamma ina jin tsoro fa." Hannun shi yasa ya kamo hannuta da ta dire kan mararshi murya can k'asa yace. "Waya baki damar tab'a ni?." Shiru tayi tana jin yadda ya matse hannun ta a hankali tace. "Hamma duhu fa." Fizgota yayi ta fad'a jikin shi cikin rad'a yace. "Duhun nake so ! kuma wallahi tunda kika tab'a ni tabbas nima zan.." sai kuma yayi shiru yana jin yadda take son kwance kanta a hannun shi. Rugume ta ya k'arayi cikin sanyi yasa hannun ya zare rigar ta ya cillashi gefen ya rege daga ita sai d'an gajeren wondo , bayan ta ya rink'a shafa wa a hankali yana sa hannu yana murza gajeren wondon nata har yayi k'asa dashi, ya zame shi duka. Ita kuwa sai tirje-tirje takeyi tana. "Wallahi ni dai bana so." Bai kulata ba sai juyawa da yayi da ita cikin rawan jiki ya zare kayan jikin shi sannan ya jawota jikin shi hab'arta ya tallab'e cikin lumshe ido ya manna bak'in shi da nata, cikin wani yanayi ya rink'a kissing din lips enta tamkar ya samu sweet, ita kuma cije hak'oran ta tayi wai a nufin ta hanashi sukuni, gane hakan yasashi mirgina ta murya can k'asa yace. "Ni in a so Meenarl inason hak'k'ina kinji tsoron Allah ki daina azabtar da ni." Baki ta bud'e tana haki tace. "Ni bana so wlh ni ka barni." Shiru tayi jin ya manna bak'in shi da nata cikin rawan jiki ya lalumo harshenta mai sanyi , cikin wani yana yi na fita hayyaci ya rink'a juyawa da murza ta, yana shafeta, ganin baya ji baya gani kawai sai ta saki kuka tana ture k'irjin shi . Cikin rikicewa ya birki tota ya kontar da ita gaba d'aya hannu shi rawa yake yi k'irjin ta ya rink'a murzawa yana fidda wani nannauyan numfashi, gaba d'aya ya birkice. Meenarl kam bak'in ta da idon ta, ta nema tana kuka tana tureshi da d'an buga k'irjin shi. Saketa yayi cikin fizgar numfashi murya na rawa yace. "Meenarl kiyi hak'uri ki dena tsoro na wallahi zan biki a hankali banzan cutar da keba ki nitsu karki yi injimi ki ciwo Meenarl ni fa mijin kine ya kike so nayi wallahi banzan iya hak'uri ba." Jin ya d'an saketa yasa cikin zafin nama da tsoro ta mik'e da sauri tana k'ok'arin arcewa. A hargitse ya jawota da k'arfi ta fad'a jikin shi cikin k'arfi ya jawo hannun ta ya d'aura kan mararshi murya na rawa cikin gigita yace. "Meenarl kiji fa! kinji halin da nike ciki kiyi hak'uri ki gafar ceni." Hannunta ta janye da sauri tare da k'ollah k'ara tana yarfa hannun gaba d'aya jikin ta sai b'ari yake kar-kar idanunta, ta zaro woje kamar zasu fad'o k'asa cikin kuka da gigita take fad'in. "Wayyo na shiga uku." Wani irin numfashi ya fitar tare da kontar da ita kan pillows tare da yi mata rumfa da faffaf'an k'irjin shi cikin tausaya mata dan harga Allah yana tausa yawa Meenarl dan yasan tabbas yarin yace gashi gaba d'aya ta tsorita dashi . Ita kuwa yanzu ta gama karya ta fara kuka cikin rauni murya na rawa tana. "Wayyo Hamma Aliyu kayi hak'uri wallahi banzan sake tab'aka ba har Abadan na tuba Hamma kayi hak'uri." Shi ma cikin tausayawa juna ya shafa kanta tare da cewa . "Kiyi hak'uri Meenarl banzan iyaba." Ido Meenarl ta zaro d'an gaba d'aya ya rufe su da blanket sannan a hankali taji yasa bak'in shi cikin kunneta murya can k'asa yace. "Ψ¨Ψ³Ω… Ψ§Ω„Ω„Ω‡ΨŒ الله‍م Ψ¬Ω†Ψ¨Ω†Ψ§ Ψ§Ω„Ψ΄ΩŠΨ·Ψ§Ω† ΩˆΨ¬Ω†Ψ¨ Ψ§Ω„Ψ΄ΩŠΨ·Ψ§Ω† Ω…Ψ§ Ψ±Ψ²Ω‚ΨͺΩ†Ψ§" Kawai sai Meenarl ta rik'e damtsen hannu shi tana juya kai cikin wani irin yanayin da bata tab'a jin Rayuwar ta a cikiba, faratunta tasa ta matse damtsen hannu shi tana juya kai tare da zubda k'ollah masu zafin gaske murya na rawa cikin yanayin wahala da azaba ta rink'a cewa. "Wayyo wayyo wayyo Allah na Ummi na Hamma Aliyu kashe ni zaiyi wayyooo Bappa na zan mutu, Wayyo Hamma Aliyu." Sai ta kuma saki wani irin marayan kuka tare da d'an d'ago k'irjin ta sama fuskarta ta cusa cikin k'irjin shi tana murzawa tana. "Wayyo wayyo wayyohhh." Ina General kam yayi nisa baya jin kira shi kanshi baisan halin da yake ciki ba bare yasan halin da Meenarl ke ciki baya iya fidda numfashin sa da kyau. Ita kuwa Meenarl kuka datayi da azaba gaba d'aya har muryar ta ta dashe ida nunta sunyi jazir sun kumbura sintim tana kukan har yanzu Amman babu mai jin sautin kukan, k'arfin ta kuwa gaba d'aya ya kare hanna yenta sai wani irin rawa suke sun sake kamar basu da kanshi da jijiya cinyoyin ta kuwa kamar ba a jikin ta suke ba, tuni tayi wani irin galabaita, tana jin azaba na ratsata amman bazata iya taimaka kanta da kanta ba. General kam ya manta waye Meenarl ya manta matsayin shekarun ta gaba d'aya ya k'asa gano duniyar da yake ,.haka yayi ta had'a mata wahala da gajiya, har sai k'arfe 2:37 Am. Gaba d'aya sai yanzu ya samu wani irin nannauyan numfashin sa ya fizgota tare da kuka kamar yaro, kuka yake jikin shi na rawa ya k'ara k'amk'ame ta, zuciyar shi pal da tausa yinta haushin kanshi yake ji yadda ya k'asa control na jikin sa,.har cikin ranshi yake jin tausayinta na ratsashi, zuciyar sa cike da farin ciki, cikin gamsuwa ya zame gefen tare da jawota jikin shi cikin fidda numfashi yake magana . "Meenarl! Meenarl sannu Minalin Hamma Aliyu kiyi hak'uri ki gafarci Hamman ki." Ido ya d'an zaro jin gaba d'aya jikin ta ya wani sake duk inda ya tab'a ta sai yaji ta lugui gashi yana ta kiran ta bata amsawa, cikin tsoro ya diro kan gadon toilet ya shige ya d'auko towel ya d'aura a k'ugunshi sannan yazo ya kuna wuta cikin sauri ya koma kan gadon , jawota jikin shi yayi yana kallon fuskar ta idonta a bud'e Amman sai hawaye ke bin fuskarta ta zubawa fuskarsa ido tana mai zubda k'ollah. Kamota yayi cikin rawar murya yace. "Meenarl kiyi min magana dan Allah kibar kuka mana kinsan cewa ." Gaba d'aya ya resa irin furucin da zai mata da Hausa ko fillancin ko English kawai sai tsintar kanshi yayi yana mata magana cikin larabci dan yana ga a Yau ba yaren da zai sata sanyi sai larabci cikin sanyi ya rugume ta a hankali yake cewa. *"Haxal yauma huwa a'axamu minna,* (Wanna babbar ranace a gareni) *Anti fak'at fee hayatee,* (Kekad'aice rayuwa ta) *Meenarl kan atruki Abadan,* (Meenarl banzan tab'a barin kina har a bada) *I'ilam uhibbuki hubbub azeem,* (Kisani ina sonki so na hak'ik'a) *Insha Allah sana iyshu ma'aki ma'a habbah:* (Insha Allah zan rayu dake tare da soyayya)." Gaba d'aya ya gigice ya juye ya koma balara be a fili zantu kan soyayya kawai yake zuba mata kamar ruwan sama, k'ara rugume ta yayi yana shafan k'irjin ta yana kissing duk wani sashi na jikinta hawaye ta ya share mata da tafin hannun shi cikin sumbatar lips enta ya tsura mata ido tare da cewa. *"Meenarl Anti tamamu sururi* (Meenarl Kece farin cikina) *Lak'ad kinyi k'urata ayni min k'abal*: (Tun tuni kece sanyin idanni yata) *Lana kunu fissakina hatta uk'arribaki, ankuntu ma'aki*: (Bani samun nitsuwa har sai na kasan ce kusa da ke)." K'irjin ta ya shafa cikin zubda k'ollah yace. "Meenarl kina jina ko?." Ido ta lumshe k'ollah mai zafi ya zubo mata , da sauri yasa hannu ya tare k'ollah da tafin hannun shi cikin tsantsar k'aunar ta yace. "Har Abadan indai ina kusa dake toh banzan bari hawaye ki so zuba a k'asa ba sabida ke d'in, *kunti ba'adu jasadi* (kin kasan ce wani sashi na jikina)." Gaba d'aya ya gigice ya gigita Meenarl da salon shi da kalam shi masu tsadan samuwa. A hankali Meenarl ta bud'e baki tana magana a hankali ganin baya jin abinda take fad'a yasashi kawo kunnen shi kusa da bak'in ta. Cikin zubda k'ollah tace. "Hamma Aliyu zan koma gun Bappa na dan Allah Hamma ka maida ni gidan mu karna mutu anan." Kanta ya sunkuya ya rink'a sakar mata kiss tako ina. A hankali ya talla bota kan cinyarshi tare da cewa. "Bazaki mutuba insha Allah zamu rayu tare dan., *kuntil lagamee* (Kin zamo tawa)." A hankali tace. "Hamma jikina kamar ba nawa ba Hamma zafi nake ji." Mik'ewa yayi rugume da ita kai tsaye toilet ya shige da ita, ruwan d'umin ya had'a sannan ya ajiye ta cikin kula. K'ara tayi tare da jawoshi tana yarfa hannu tana. "Wayyo Hamma zafi." sai kuma ta saki kuka mai cike da tausa yi. A haka General ya susuce ya mata wonka sannan yace. "Minalin Hamma kiyi niya ko sai kiyi wonkan tsarki." Tana kuka tayi wonkan shi kuma ya d'ago ta ya kamo ta d'aki, bak'in gadon ya ajiye ta sannan ya fita woje motar shi ya bud'e ya d'auko mata kayan ta. Yana dawowa shi da kanshi ya samata kayan riga da siket ne na atampa sai hijabinta, kan sallah ya ajiye ta, sannan ya ned'e zanin gadon, ya shimfid'a wani sannan ya shige toilet d'in wonka yayi tsab , yana fitowa ya shirya cikin manyan kayawa ya fito a aggon ras sai k'amshi yake zubawa. ganin ya makara ne yasa sukayi sallah a tare , suna idarwa ya sunkuye ta sai kan gadon , suka konta yana cewa. "Banzan sake yi miki komai ba Minali na kiyi hak'uri ko Hamman ki bai kyauta ba." Ina ita kam Meenarl sai hawaye cikin dashewar murya tace. "Hamma ni dai gida zan koma ka kaini gun Inna." Cikin tura hannunshi a rigar ta yace. "In nakai ki me zaki ce mata? zaki gaya mata abinda mu kayi ne?." Cikin kuka tana zaro hannu shi a k'irjin ta tace. "A a wallahi banzan gaya mata ba." Wasa-wasa tuk'uru Meenarl tak'iyin shiru sai kuka take ita dai ya maida ta gida ko abinci tak'i cin gaba d'aya ta gala baita ga jiri ga tafiyarta sai d'ink'isawa takeyi. Kallon ta yayi yadda take tafiya cikin tausa yinta yace. "Toh mu tafi." Haka suka rufe gidan suka nufi cikin Kaduna. A mota kuwa General hannu shi d'aya na tuk'i d'aya kuma ya cusa shi cikin..... By *Garkuwar Fulani* [8/26, 8:13 PM] πŸ’žIt's @lh@jiπŸ’ž: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *BANDIRAWO* page 5⃣9⃣ *Na* *Aysha Ali Garkuwa* πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *Ban manta da keba takwaracy tawa kuma bazan manta ki ba Aisha Aliyu Tsamiya kina raina inayi miki fatan alkhairi* A cinyoyin ta yana d'an matsawa kamar maiyi mata tausa, gaba d'aya hankalin shi baya kan titin ko idonta ta lumshe sai yace. "Sannu Minali na." Ita dai Allah-Allah take su isa dan har cikin ranta take jin tsoron shi da nauyi shi gaba d'aya kunyarshi take ji . Suna isa tasa hannu zata bud'e murfin motar , da sauri ya juyo gareta hannu yasa ya kamota a hankali ya jata jinkin shi rugume ta yayi da kyau cikin lallashi da salon k'aunar ta da rad'a yace. "Meenarl! meya sa kike saurin barin inda nake?, Meenarl bana so kiyi nesa dani bazan iya jumrewa ba, kada ki nesanta gaggar jikin ki da nawa, Plss karki hukun tani da kaura cemin, *Ana aspet ya Habeebatee*." Shiru tayi kanta na lafe a kafad'an shi tayi shiru tana jin yadda zuciyar shi ke bugawa ido ta lumshe tana mai shakar k'amshin jikin shi , hannu tasa a hankali ta zagoyo k'ugunshi tare da k'ara lumshe ido tana jin wani irin dad'i yana ratsata yadda Hamma Aliyu ya mace ya susuce a kanta duk wannan tsare fuskar babu sai kalawai masu sanyi da dad'i yake furta mata. Shi kam General jinshi yake kamar a saman gajimare yana ta nink'aya cikin duniyar masoya, hannu shi d'aya ya cusa cikin yar rigar ta ya rink'a shafa cikin ta hannun shi d'aya kuma hab'arta ya tallebe cikin tsura mata ido ya manna lips enshi a kan nata ya rink'a mata wani salon da yasa ta lumshe ido ta da sauri tana mai fidda numfashi a hankali hannun ta kuma ta d'an d'ago ta d'aura kan wuyan shi zuwa k'eyanshi ta rink'a murzawa a hankali. Har zuwa wani d'an lokacin sannan ya zare bak'in shi a nata cikin rawan murya yace. "Meenarl! Meenarl! *Laa shakka anti mukhtalifun fee k'albee* (Shakka babu ke ta dabance a cikin zuciyata)." K'ara matsota yayi tare da cewa. "Meenarl bud'e idon ki ki sashi cikin k'wayan ida nuna kiji abinda zan gaya miki zaki gaskanta hakan a cikin idanuna." A hankali ta bud'e idon ta cikin jin kunya da d'an cije lips enta. Idon shi ya kafe cikin nata murya can k'asa cike da kasala yace. *"Meenarl ta shattatul aqlee min jarra'i hubbuki* (Meenarl tsantsar soyayyar ki ita ke kesa hankalin ya gushe), tabbas hak'ik'a , *As attu li wajattu xawajiki*, (nayi farin cikin da samun auren ki). Sai ya kuma ya rugume ta tare da cewa. *"Laisa liyal'huzni inkunti ma'ee*, (In kina tare dani bani shiga k'unci), *Habeebatee laisa lee mu'allim gairuki"*, (gareni babu wani mashawarci bayan ke mosoyiyata). Ido Meenarl ta lumshe tare dasa hannu ta rik'e Hanna yenshi dake tallabe da fuskarta wani sassanyar ajiyar zuciya ta sauk'e dan jin dad'in kalaman shi gareta wani irin murmushi mai sanyi tayi. Shi kuma hannun shi ya tura zaman k'irjin ta cikin rad'a yace. *" Ibtisamaki yuquwwi basaree*, ( murmushinki ke k'arawa ganina k'arfi)." Rugume shi tayi da iya k'arfin ta cikin lumshe ido jin yadda yake kashe mata jiki cikin kunya da sanyi murya a mace tace. "Hamma! Hamma! Hamma na zan shiga cikin gida bacci nake ji." Murmushi yayi tare da cewa. "Toh mu koma gida kiyi baccin ki acan yau Hamman ki ko k'ofar parlour bazai fitaba zanyi jinyan ciwon da na jimiki." Kai ta d'an d'ago cikin sanyi ta shafa sajen shi a hankali tace. "Ina son ganin Inna ." "Toh muna shiga inkin ganta zamu koma ko?." "Ayyah Hamma ba yanzu yanzu ba mana." Murmushi yayi tare da kontar da ita kan cinyarshi hannu yasa yana shafa fuskarta tare da cewa. "Toh Amman fa in mun fita sai ki daure ki gyara tafiyar ki." "Toh" tace tare da tashi zaune. Har zata fita ya kamo hannun ta fuskar ta ya tsurawa ido a hankali yace. "Fuskar ki tayi ja idonki ya kumbura da zaran an ganki ansan baki da lafiya kuma za'a gane kinyi kuka mai tsanani, in sun tabba yeki me zaki ce musu?." Shiru tayi cikin karya wuya tai rau-rau alamun zata zubda k'ollah, hakan yasa ya sake hannun ta da sauri tare da cewa. "Muje kar kiyi kuka kinji ko Babyn Hamma Aliyu." Fita sukayi suka fara tafiya a hankali tana gaba yana binta a baya, yana kallon yadda take dink'isawa a hankali. Suna shiga cikin gidan a babban parlour suka same su baki d'aya suna zaune sunyi shiru basa ko motsi sai sautin kukan Mama ke tashi cikin tsantsar nadawa tana durk'ushe gaban Ammi tana bata hak'uri da neman yafiyar ta, Abdul kuwa shima k'ollah yake zubdawa yana durk'ushe gaban Abba da Daddy yana neman yafiyar su, Daddy kuwa shima sai k'ollah yake zubawa cikin tsananin takaici da jin kunya yake cewa. "Kai tona kaitona ni Usman na auri makirar mace ta cutar min da d'an uwana da matarsa da d'an shi, Maman Abdul kinji kuyan duniya da lahira me zaki gayawa ubangijin mu da wani idon zaki kalli Aliyu da mahaifiyar sa me zaki cewa su Ramadan wallahi Allah ya isa tsaka nina da k.." Cikin sauri Abba yace. "Kai Usman in rai ya bacci kad'a hankali ya gushe , Kar kajawa matarka Allah ya isa kayi mata afwa ka yafe mata, tunda dai gashi a gaban ka kaji Ammin Aliyu dasu Ramadan sun gafarta mata, toh nima na yafe mata, kaima ka yafe mata kuma insha Allah Aliyu ma zai yafe mata, sannan batun kace tayi asara duniya da lahira kuma bata tasoba dan ba mai shiga tsakanin bawa da ubangijin sa kai dai ka yafe mata abinda ka sani abinda baka sani ba kuma ita da ubangiji ta sannan kuma munsan Allah nason masu afuwa da kuma masu tuba Allah kuma Allahu gafurun rahim ne dan haka kad'a kayi mata baki, Abdul kai kuma Allah yayi maka albarka." Bappa ne yayi ajiyan zuciya tare da cewa. "Tabbas ba a shaga tsakanin bawa da ubangiji sa muna zata mata Allah zai gafarta mata dan gaba d'aya ta cika sharudan tuba." Ammi kuwa kama hannun Mama tayi cikin zubda k'ollah tace. "Na yafe miki duniya da lahira Allah ya gafarta mana." Amin Amin suka rink'a amsawa. Ya Amir da Nafeesat kam sai kuka suke cikin jin kunyar halin mahaifiyar su cikin kunya suka yiwa Ammi godiya. Ramadan ne ya kalli General dake shigowa parlour Meenarl na gaban shi, Fuska d'auke da murmushi yace. "Laa Hamma Haiydar yaushe kuka shigo?." Murmushi ya d'an yi cikin k'aunar k'anin nashi yace. "Toh ba gamu yanzu muke shigowa ba." Ammi kuwa da Inna ido suka tsurawa Meenarl cikin son gano wani Abu Inna ta kalleta ta a dai-dai lokacin da ta zauna kusa da ita cikin sanyi tace. *"Bodd'i a jamo bo?*, (Bodd'i lafiyar ki kuwa?." Kai ta gyad'a mata cikin sanyi tace. "Inna Bacci ne nake ji." Shiru Ammi tayi tana kallon yadda General ya tsare Meenarl d'in da ido. Ita kuwa Meenarl kanta a k'asa ta gaggai shesu tana ta lumshe ido alamun baccin. Shima General gaishe da iyayen nashi yayi cikin girmamawa, k'annen shi kuma suka gaida shi Abdul ne da Mama suka matso gaban shi cikin kuka da kunya da nadama Mama ta kalleshi tare da cewa. "Aliyu ka gafar ceni ka yafe min abubuwan da nayi maka a rayuwar ka ka yafe min ko zan samu sauk'i da yafiyar Allah, tabbas nasan na cutar da kai." Hannu ya d'aga mata cikin sanyi yace. "Ni na yafe Allah ya yafe mana, kai kuma Abdul aini a sanadi abinda kaso yiwa Meenarl ya zama sana din haduwata da iyayen na, dan haka kai kam yafiyar Meenarl zaka nema." Haka kuwa Abdul ya rarrafa gaban Meenarl da kakarsu yace. "Meenarl ki gafar ceni." Da sauri ta katseshi tare da cewa. "Haba dai Hamma Abdul wallahi tuni na yafe maka kaifa d'an uwana ne na jini na yafe maka Allah ya yafe mana baki d'aya." Gaba d'aya suka amsa da . "Amin! Amin! Amin ya rabbil izzati." Haka aka waste taron da Addu'a. Inna kuwa suna tashi taja hannun Meenarl suka nufi part ensu na musam man, shiko General dasu Ramadan d'akin Ammin su suka zauna suna d'an hira Ammi tasa Rayhana ta kawo musu Abinci sannan ta had'a nasu Inna kuwa takaici musu. A parlour ta same su Meenarl na konce Inna ta tasata a gaba tana cewa. "Na tabba yeki meke damun ki kink'i fad'amin sannan kinzo kin konta kina ta rawan sanyi ga fuskar ki duk a kumbure ki tashi muje d'aki kince ke a a ." Ammi na shiga ta zauna gefen ta cikin kula tace. " Bodd'i tashi ki zauna." Kai ta juya cikin rumtse ido dan gaba d'aya raunu kan sunyi tsami tunda ko parasitomol bata shaba, bata son yiwa Ammi musu yasa ta mik'e da k'er ta zaune a kaikaice sai kuma hawaye shar-shar. Ajiyan zuciya Ammi ta sauk'e cikin fahimta y'ar d'an uwanta ta tace. "Bodd'i meke damun ki gaya min ?." Sai kawai ta fara kuka cikin sanyi tace. "Ammi babu komai fa." Shiru Ammin tayi tare da kamo hannunta ta mik'e cikin kula tace. "Muje cikin d'aki ." "Toh" tace tare da tafiya a hankali tana d'ink'ishi Ammi kam da Inna shiru kawai sukayi dan sun gano da wata y'ar matsala. Suna shiga Bedroom d'in , shiko General ya shigo parlour Innan dan yaga shiru Ammi bata komaba tsoro yake jikar su ritsa Meenarl ta gaya musu wani abu, Inna ya kallah cikin tsuke fuska yace. "Ina Meenarl?." Ido ta tsura mishi cikin tuhuma tace. " Bata da lafiya kuma tace bacci take ji yanzu ta shiga ita da Ammin ka." Yana jin haka ya koma gefen ya zauna yana latsa phone enshi. Ita kuwa Ammin suna shiga bedroom d'in, toilet ta wuce ruwan d'umin ta had'a sannan ta fito tace. "Bodd'i shiga kiyi wonka zakiji dama-dama." "Toh" tace sannan ta shige, tana shiga ta samu ruwan d'umin ta gasa kanta da kyau dan koda Asuba da Hamman ta ya gasata ta d'an ji sauk'i sai kuma da ta dad'e a zaunen ne taji zafin ya dawo . Wonka tayi sannan ta kara amfani da ruwan zafin, tana fitowa ta samu Ammi ta kawo mata abinci tamkar mai jego, ta sata taci abinci da gasheshen naman da tayi mata mai romo-romo sannan ta had'a mata tea maikauri tasha ta kuma bata magungunan da tasa Ramadan ya seyo, sannan ta kalleta cikin kula tace. "Toh konta kiyi baccin ki." Toh tace tare da konci yar. Ammin na fita. General ya mik'e ya nufi cikin d'akin Inna na biye dashi a baya. Suna shiga Aliyun ya zauna gefen ta cikin tausayawa yace. "I love you so very very much sweet heart' sannu ko Minali na Allah ya miki albarka Allah ya faran ta miki kamar yadda kika faran tamin." "Amin ya Allah , Hamma na." Cikin rad'a yace. "Allah yasa baki gaya musu abinda nayi miki ba?." Cikin kunya tace. "Ban gaya musu ba Hamma na kuma har abada ba wanda zan gayawa dan wannan sirrin mune ni dakai kawai ba maiji." Murmushi yayi cikin Satan kallon Inna ganin hankalin ta baya garesu yasa, yayi sauri ya subbaci goshin ta tare da cewa. "A hubbuki ya Habeebatee." Murmushi sukayi su duka , sai Inna kuma ta matso gaban Meenarl d'in rik'e da y'ar k'aramar k'oriya tare da had'i na musamman had'in fulanin Gembu Membila cikin kula tace. " karb'i ki shanye." Ba musu ta karb'a ta zuk'eshi sannan ta fara lumshe ido alamun baccin haka yasa General shafa kanta tare da jamata blanket suka fita shida Innar.. Koda dare yayi fir Meenarl tak'i fitowa su koma dole ya hakura ya tafi. Washe gari kuwa a ranar aka d'aura auren Captain Sani da Nafeesat Doctor Jabeer da Rayhana, Inna kuwa da Meenarl sun samu mafakar kin Meenarl ta koma Jaji, Inna kuma sai faman tsuma jikarta take gashi duk had'in da za'a bawa amare sai an bata. Gaba d'aya sun hana General ganin matarsa gashi yanzu koda yaushe cikin begen ta yake. Anyi biki an gama duk bak'in sun watsa. Yau kwana 6 kenan Aliyu bai samu yaji d'umin matar saba, yanzu misalin karfe na 8 dare ya fito babban parlour nasu, gaba d'aya suna parlour sai Meenarl da bai gani ba bayan ya gaida iyayenshi cikin sunkuyar da kai yace. "Inna ina Meenarl?. Murmushi tayi ganin yadda ya tsuke fuska tace. " tana wonka." Shiru yayi kamar bai Jita ba a ranshi kuwa. hamdala yayi. Can dai yaga hankalin su baya kanshi sai yayi nor-nor ya zulle. Kai tsaye cikin d'akin ya shige yana kiran. "Meenarl! Habeebatee! sweet heart! sheriyel am." Shiru tayi tana toshe bak'in ta dan dariya ke son kubce mata, shi kuwa k'ofar ya turo hankali , itako idon ta a lumshe jin k'arar k'ofar ne ta bud'e ido, ganin shi ne yasa tayi sauri tayi baya jikin gini ta jingina. shiko cikin wani irin shauki ya matsota tare da turata jikin ganin cikin rawan jiki ya... By *Garkuwar Fulani* πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *BANDIRAWO* page 6⃣0⃣ *Na* *Aysha Aliyu Garkuwa* πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ *A madadin sauran 'yan uwa Fulani nake mik'a sak'on ta'aziyar mu da jaje ga yan uwanmu Fulani mazauna Gembu Membila tare da Jos akan rashin da akayi musu sakamakon mugayan yan ta'adda da sukayi ta k'ona musu rigogin su da sace musu dukiyoyin su tare da b'atawa yaransu mata yarintar su😭 uwa uba kashesu da akayi 😭, Allah ya karb'i shahadar wad'an aka kashe sun rabbi ya karemu mu saura da muke raye Allah ya bimana hak'k'in mu, Allah ya bawa gomnati kuma damar kula da Fulanin dake cikin tsaunuka da rigogi a matsayin su na 'yan k'asa suma a basu kulawa, Allah ya isar mana kan abinda bazamu iyawa kanmu ba* Kirjin shi ya manna da nata cikin lumshe ido tare da sauk'e ajiyar zuciya rugume ta yayi a jikin shi yana shafa gadon bayan ta tare dayi mata tafiyar tsutsa yana mai sinshuna wuyanta, Ido ta lumshe a hankali dan wani irin kunya da taji ya rufeta gaba d'aya ji take kamar ta nitse cikin k'asa zamewa ta rink'a yi a hankali har ta tsuguna a k'asa kife kirjin ta tayi a cinyoyin ta tafin hannun ta kuma ta rufe fuskarta, shima biyota k'asan yayi ya tsuguna yana fuskantar ta har cikin ranshi yake jin kaunarta na ratsashi haka nan kuma yake jin kunyarta na burgeshi dan tabbas ita kunya adoce ga d'iya mace matsota yayi murya can k'asa yace. "Meenarl ki tausawa Hamman ki mana wallahi na gaza samun sukuni a rayuwata a cikin kwana kin nan da kikayi nesa dani bana iya bacci cikin nitsuwa a cikin bacci na ko a ido biyu ke nake gani da marari, Meenarl nifa mijin kine meyasa kike son yin nesa dani?." Shiru tayi sai k'ara sunkuyar da kai tayi tana k'ara matse jikin ta, ido ya tsura mata tare da yin murmushi a hankali yasa hannushi tsakanin cinyarta da kirjin ta , ido ya lumshe da sauri tare da sauk'e ajiyar zuciya, itama ido ta lumshi da karfi tare da d'an zaro ido woje kan jin yadda gaba d'aya ya cusa hannayen shi kan kirjin ta yana mata wani irin salon mai tafiya da hankali gaba d'aya ya kashe mata jiki ya sakar mata wata iriyar muguwar kasala sai numfashi take fiddewa da sauri-sauri murya na rawa tace. "Hamma Aliyuuuuuuuu." Matsoto ya kumayi tare da mik'ewa da ita ya jingina ta jikin gini towel ya jawo a hankali ya d'aura mata shi a k'ugunta sannan ya juyota kirjin shi ya manna a bayan ta kanshi ya d'an sunkuyar ya cusa cikin kafadarta hannayen shi kuwa kirjin ta ya zagayo dasu cikin kasala yace. "Na,am Minalin Hamma Aliyuuuuuuuu meke faruwa ne?." Shiru tayi tana sauk'e numfashi, shi kuwa gaba d'aya ya susuce yana neman susutata kab shi ya manta a gidan su Abba suke ya mance cewa a toilet suke bare ya tuna a part d'in Inna suke bare daya samu itanma ta narke mishi a jikin shi sai faman mak'aleshi takeyi tana shafa sajenshi tare da rugume shi. Su Inna kuwa ana watsewa hiran ta shigo Part inta kai tsaye bedroom ta shige cikin yin mik'a alamun bacci ta had'awa Meenarl had'in data saba had'a mata tana gama had'awa ta juyo kan gadon ido ta mutsike ganin Meenarl d'in bata kan gadon cikin mamaki tace. "Toh ina take." Sai kuma ta fara kiranta cikin d'aga murya tana. "Bodd'i ! Bodd'i! Kai Bodd'i! Ina kike ne?." Ita kuwa Meenarl a cikin toilet d'in cikin sanyi tasa hannun tana mannawa General bel d'in shi d'aya fara kuncewa cikin sanyi tace. "kayi hak'uri Hamma kaji Inna na kirana gashi dare yayi kuma kace zaka koma cikin Jaji." Kamota ya kumayi cikin lok'osa kai kamar yaro yace. "Ni dai a,a wallahi na gaji mutafi tare kawai In ba so kike na shiga wani halin ba." Zatayi magana kenan ta kuma jin kiran Inna ido ta zaro cikin shafa kanshi daya manna da kirjin ta yana murzata ido ta lumshe tana. "Wayyo Hamma na zaka zautar dani, kaji fa Inna na kirana." Zare bakin shi yayi a hankali ya kuma manna hannushi kan kirjin nata ido yatsura mata cikin rad'a yace. "Kai wannan tsohuwar fitinar ta nada yawa, ki amsa mata mu huta daga nan bazan fitaba sai tayi bacci." Ganin bayi da niyar saketa yasa cikin d'an daga murya tace. "Na'am Inna yanzu dai nashiga ban fara wonkan bama ke kam kiyi konci yarki." "Toh in kin fito ga maganin ki kisha." "Toh" kawai tace, sannan ta kalli General da ya susuce a kirjin ta murya can k'asa tace. "Allah k Hamma zanyi kuka fa." Hannun ta yajawo ya cusa a jikin shi murya a raunane yace. "Ni fa zan iya rasa lafiya ta plxx Minali na mukoma gidan mu ba kowa a can dagani sai ke." A zahiri taji tausayin shi so Amman kuma tana tsoron shi. Rugume juna suka kumayi tare da newa Kansu sassaucin abinda ke damunsu su suduka biyun. Ita kuwa Inna kan gado ta zauna tana yin addu'ar konciya kenan Ramadan ya shigo daga parlour yake ta kiran. "Hamma Aliyu! Hamma Aliyu! 11:55 pm baka tafiba , Abba na kira kazo ka tafi tunda kace ba kwana zakayi ba." Tunda yaji Abba ne ke kiran shi ya d'an saketa cikin kasala ya manner bel d'in shi tare da manne boturan rigarshi hannun shi yasa ya tallabo habarta cikin so ya had'a lips ensure a dai-dai lokacin kuma Ramadan ya sakezuga mishi kira. "Hamma Aliyu." ba tare datuna komai ba yace. "Na'am gani nan zuwa." Inna kam ido ta d'an fitar cikin mamaki ta sake cewa. " Bodd'i. " Cikin mantuwa Meenarl d'in ma tace. "Na'am." Tana amsawa kuma sai suka ankara da cewa Inna da Ramadan sun gane su suduka biyu suna cikin toilet d'in, Ido Meenarl ta zaro tare da cewa . "Hamma ka amsa." Shi kam General kunyace da takaici suka rufeshi wai mutun da matarsa a maidashi kamar b'arawo. Bai kulata ba sai lips enta ya murza iya son ranshi sannan yasaketa yana haki kamar wanda yayi gudun pampalak'i idonshi yayi jazir fuska a murtuk'e yace. "Meenarl bakya tausaya min keda gidan ki kin wani dawo gida kin zauna kin barni kamar mara mata." Sai ya juya ya fice fuska a murtuk'e . Shiko Ramadan dama tunda yaji suna tare da Meenarl ya fice abinsa. Itama Inna sai ta konta ta lumshe ido kawai . Shiku General a General d'in shi ya fito dan tabbas yaji kunyan abin. A bakin gate ya samu Abba, cikin girmamawa ya mishi saida safe sannan ya tafi. ranshi cike da k'una. Ita kuwa Meenarl gaba d'aya sai taji tausayin shi ganin yadda ya koma gashi ranshi ya bacci da ita. Shiyasa itama sai kawai ta tsinci kanta cikin bak'in hali, Tana fitowa Maganin tasha sannan ta fito parlour a hankali take kiran. "Ya Ramadan." Ramadan kuwu da yanzu ya fito part d'in Ammi shi parlour Innan ya nufa, yana zuwa yace . "Bodd'i mene na kira a daran nan?." Fuska a tsuke tace. "Ni ka kira min Hamma Aliyu a woyar ka." Ka ya sunkuyar dan dariya ke son kubce mishi , ki ranshi yayi sannan ya mik'a mata woyar sannan ya fice. Kan 3 str ta konta tana ji woyar na ringgin bai d'aga ba har saida ya kusa tsinkewa sannan taji yana cewa. "Menene kuma Ramadan?." Ajiyan zuciya ta sauk'e a hankali tace. "Hamma nice fa." A kufule yace. "Menene zaki kirani me zai cemin?." Cikin sanyi tace. "kayi hakuri Hamma na ka gafar ceni naga kamar ranka ya b'aci dani." "Baki da matsala dani ai shiyasa ki ke min abinda kike so kina sane inada muradinki a kusa dani bakya sonane ai shi yasa." A marairai ce tace. "kayi hak'uri Hamma na wallahi ina sonka." Murmushi yayi tare da jin dad'in furucin ta a zahiri kuma cewa yayi. "A a kam." sai kawai ya kashe woyarsa . Ita kuwa Meenarl haka ta kwana cikin damuwa, da asuba kuwa kusan da addu,a ta tashi a firgice dan mafarkin da tayi Hamman ta ya rasu tana zubda k'ollah ta gayawa Inna. Daga nan kuma ta wuni cikin bak'in hali. haka ta wuni har dare koda Inna ta matsa mata da naci da tabbayar dalilin ta na had'a fuska kawai sai ta kama zubda k'ollah wasa-wasa Inna taga Abu fa zai zama gaske har ta fara sheshshek'a haka yasa taje ta kira Ammi. Ammin na zuwa ta sata a gaba cikin lumana tace. "Me yake miki ciwo Bodd'i?." Kai ta girgiza cikin zubda k'ollah tace. "Babu komai Ammi zuciya tane ke tsinkewa." Ido Ammi ta tsura mata sannan tace. "Toh meyasa zuciyar taki tsinke wa?." Kai ta sunkuyar cikin Murza yatsun k'afarta tace. "Ammi nayi mafarkin Hamma ya rasu ne, kuma tunda garin ya waye ya Ramadan keta ki ranshi baya d'agawa." Sai kuma hawaye cur- cur . Ita ko Ammi murmushi kawai tayi tare da cewa. "Toh bari inzo." Itako Inna harararta tayi tare da cewa. "Toh kice komawa gun mijin ki kike so mana haka kawai ki tsiran mani bak'in hali wato shegiyar tsohowa ta shiga tsaka ninki da mijin ki ko?." Ita dai cib d'in ta sai hawaye. Ita kuwa Ammi d'akin Abba ta nufa cikin murmushi tayi mishi bayani. Shima dariya yayi tare da cewa. "Kune baku san shak'uwar dake tsakanin Haiydar da Meenarl ba da kun sani da bazaku rik'eta ba, yanzu-yanzu kusa Ramadan ya mai data d'akin ta gidan mijin ta." "Toh" Ammi tace ta fice tana murmushi. A parlour ta samu Ramadan da Abdul suna zaune sunata. hirarsu aiken Abba ta gaya musu sannan ta tasasu a gaba har parlour Inna. Suna zuwa tace. "Inna Abban su yace Ramadan ya mai data gidan ta yanzu." Inna kam rai a had'e tace. "Toh gata nan aini Bodd'i ta bani mamaki wato Aliyu yafi mata ni yaushe ma kika sanshi? ." Ita kam Ammi dariya kawai take musu sannan tace. " Bodd'i tashi ku tafi maza maza kar Abba ya fito ya samu baku tafi ba." Cikin sanyi ta mik'e abinta tabi bayan su Ramadan har sun fita Inna ta kuma biyota da yar robar had'in tace. "Gashi ki sha kije ki sameshi daram tunda ya fimiki ni." Karb'a tayi murya na rawa tace. "Nagode Inna kuma ni ina sonki Hamma Aliyu baifi mini kuba dan bashi da lafiya ne shiyasa." Murmushi Inna tayi sannan sukayi sallama . A motar tayi ta shan had'in nata Ramadan da Abdul ko hirarsu kawai suke. Suna sauk'e ta suka rakata har bak'in parlour suna tura k'ofar ta bud'u ganin haka yasa Ramadan ya kalle ta cikin. Murmushi yace. "Toh madam saida safe mu zamu koma." A kunyace tace. "Toh Allah kiyaye hanya." Suna tafiya Ita kuma ta shige cikin parlourn. A hankali take takawa tare da yin salama. Shi kuwa General tunda ya fito wonka ya konta a k'asa kan carpet yayi rufda ciki yana jin zafin yadda aka rik'e mishi mata a haka bacci ya saceshi. A hankali ta shigo cikin d'akin ganin shi a konce yasa ta karisa gunshi da sauri tana zuwa ta zauna a hankali ta fara ki ranshi tana d'an tab'a kirjin shi. Kiran forko da tayi ya farka amman sai yayi shiru yana jin yadda take shafa kirjin shi sai kuma yaji ta fara kuka a hankali tare da manna kanta a kirjin shi tana. "Hamma! Hamma na ka bud'e idonka wallahi ina sonka karka mutun kaga gani na dawo kusa da kai." Rugeme ta yayi tare da had'e bakinsu wuri d'aya kissing d'in ta ya rink'ayi a buk'ace cikin sanyi yace. Meenarl kin matar da zuciya ta da sonki ki taimaka karki sake yin nesa dani." Kanshi ta shafa cikin kuka tace. "Hamma na nayi mafarkin ka mutu gaba d'aya hankali na ya tashi." Rugumata yayi yana cire mata rigar jikin ta yace. "Meenarl ki dena yin kuka ki k'addara a ranki sai lokacin yayi zamu rabu." Daga nan kuma ya canza salon d'aga ta yayi cak sai kan gado. Gaba d'aya sun rikicewa juna dan itama Meenarl tsumin Gembu yana aiki, ta biye mishi sai juya juna sukeyi. A hankali ta rik'e Hannannu shi jin ya mata rumfa da kirjin shi cikin tsoro tace. "Hamma na ina jin tsoro zafi." Kanta ya shafa murya can k'asa yace. "Insha Allah ba zaki ji zafiba zan biki a hankali." "Toh Hamma a hankali fa". tace mishi cikin rawan murya . Haka suka raya wannan daren cikin kaunar juna da soyayya General ya murji gara iya son ranshi, Ita kuwa Meenarl ta zuba mishi ranki da shogoba da sakalci, shiko duk ya susuce mata, daga nan kuma Meenarl ta zama 'yar hannu bata wasa da buk'atun Hamman ta.... *Bayan shekara 1* Haka rayuwata tayi ta juya musu cikin so da k'aur juna. Dr Jabeer da Raihana ma rayuwata tayi musu dadi suna rayuwa cikin tsab tacecci yar soyayya. Captain Sani ma da Nafeesat suma Alhamdulillah. Su Bappa kuma su Abba sun hanasu komawa Gembu Membila sai suka sa aka kwaso rabin dukiyar su aka ajiye a rigogin dake kusa da kadunan rabi kuma suka barsu a can lokaci-lokaci suna zuwa membilan ziyara, tare da Lari mai kambun baka inda a yanzu ta nitsu ganin yanzu itace abin tausayi ta nitsuba ta tuba don Allah su Bappa rayuwa tayi dad'i. Mama kuma tana ta tuba da istik'ifari da azumi dan neman yardar Allah. Zuriyar su Alhaji Ibrahim mai dala suma Alhamdulillah sun samu konciyar hankali . *Bayan shekara hud'u* Ramadan ne tsaye a tsakiyar parlour General Aliyu da Meenarl suna shirya y'an yaran su guda 2 Namijin shine babba sunan shi Adnan sai mace Ita kuma sunan ta Hannah yara kyawawa masu kwarjini, sai wasu yara biyu dake mak'ale da General Ashraf 'yar Dr Jabeer da Raihana, sai Affan d'an Captain Sani da Nafeesat wanda sun bawa ya Amir shi tunda shi bai samu haihuba Nafeesat kuma tana da wani cikin, Ramadan da Abdul ma sunyi aure yanzu haka Ramadan zai kwashi yaranne su tafi gidan shi dake kusa da gidan Dr Jabeer a cikin gida jen dake cikin asibitin Cika.. Suna gama shirya su Adnan ya subaci kumatun Abba shi tare da cewa. "Abbana sai mun dawo." Murmushi yayi ya kawo Hannah ya subaci goshin ta yace "Allah ya kaiku lafiya." Gaba d'aya suka suka amsa da Amin sannan ya subaci Ashraf da Affan. Daga nan suka fice suka tafi suna tsalle shima Ramadan binsu yayi a baya yana murmushi suna fita. General ya rugume Minalin shi sukayi cikin bedroom kan gado suka kwanta tare da mak'alewa juna cikin rawan jiki General ya cusa hannushi cikin rigarta baki na rawa yace. "Alhamdulillah lillahi Alah kulli halin nagodewa Allah d'aya bani *'YAR FULANI* danayi garaje sai *NAYI NADAMA* a rayuwata *MI WASMITI*, lallai tabbas , *NAMIJI BAYA KAD'AN* , Amman fa a gun matarsa tamkar yaro yake, haka zai sa *ATAUSAYAWA JUNA* daga nan sai mace ta zawo , *BANDIRAWO* a gun mijin ta har su juye su koma , *Bandirab'e*."``` Ido ya sura mata tare da cewa. *"Habeebatee arafti hesh?* (Mosoyiyata kinsan me?)." Kai ta girgiza mishi tare da turo mishi k'irjin ta. A hankali yace. *"Kunti anxifu ala sa'irin nisa* (kin zamo gwanar tsafta akan sauran mata), *kanat wa'in kuntu fil maktabee la'ajidu reeha jismik* (ya kasance ko ina office k'amshin jikinki nake ji) *Alal hak'ik'ati li ajali haza nasarta k'albee* (Gaskiya ko akan wannan kinyi nasarar zuciyata) *kulla yaumin kuntu fee k'issati hubbuki* (Kullum ina cikin labarin sonki) *laisa Lee misluki Abadan* ( gareni baki da tamka)." Sai ya kuma susuce kan surarar jikin ta, tare da jawo musu blanket. Itama hannu tasa tana mishi wani salon so tare da cewa. *"Uhmmm axeexee ai antallaxee allamanee haza min k'abli kalli shai,wa li karamatika laa shai'u sa'aba minnee* (Uhmm me gidana ai kaine ka koyamin wannan, kafin komai kuma ni a wajen biyayyarka babu wani abin da yake zama me wahala a wajena), *Farhatu li haazaka ya axeexee* (Nayi farin ciki da samunka ya me gidan)." Rugume juna suka yi Ita kuwa Meenarl jawoshi tayi kanta tare da rad'a mishi. *"Xaujee i'ilam kama kanatil d'a atika k'ahree alayya kazalika k'ahree alayya tarkeexu farhak* (Mijina kasani kamar yadda biyeyyar ka ta zama wajibi a kaina haka ya zama dole in kula da farin cikin ka. ") General kam wani irin ruguma yayi mata tare da rufesu da blanket suka rufu kirib... Garkuwa ma bata sake jin me suke fad'iba *Alhamdulillah ala kulli halin na godewa Allah daya bani damar gama wannan littafin lfy kamar yadda na fara lfy* Alhamdulillah Alhamdulillah Alhamdulillah Bye sisters By *GARKUWAR FULANI* Downloaded from GNOVELS.COM.NG This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG For feedback and support Facebook : https://facebook.com/gnovels Twitter : https://twitter.com/gnovels Telegram : https://t.me/gnovels