Downloaded from GNOVELS.COM.NG This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG For feedback and support Facebook : https://facebook.com/gnovels Twitter : https://twitter.com/gnovels Telegram : https://t.me/gnovels [1/8, 10:32 PM] Sha'awa: Hafsat Elham❤ Billy Galadanchi Labarin kauna. Haske writers Association. *Karku yi mamaki Idan nace muku Wannan littafin ma na sadaukar dashine ga Babbar Amiyata Hafsat Elham, wlhy ta cancanta ku yarda da kalamai na har cikin kasan zuciyana nake jiyo kaunarta,Ku yarda dani komai zan mata bazan taba biyanta alkhairanta agareni ba,dan Allah masoyana ku sota kuma ku kaunaceta tamkar yanda kuke sona* *Ina rokon Allah ya bani ikon rubuta alkhairi acikin Wannan littafin dazan rubuta yakuma sanya abin da zan rubuta ya amfane mu gaba daya* *Ina rokon duk wanda ya ya bude Wannan shafin ya taimaka ya karanta kul huwallahu kafa goma sha daya,ladan ya sauka ga yar uwata fad'matul zahra da yan uwa musulmi baki daya,na rasata kusan shekaru hudu yanzu nagode* 01 Sosai ran Elham yake b'ace ba kad'an ba,ji take tamkar ta juya ta wanke yaron daya taka mata farar socks d'inta tayi datti tunkan tashiga school ma da mari,aranta se mita take tana kyankyamin kanta sabi da tsabar tsanda da kyankyamin da Allah ya halicce ta dashi, a class sam kasa zama tayi da socks d'in,gashi sam ba'a bari Su zauna haka,tissue ta zaro a jakarta fara kal ta nade ilahirin kafafunta dashi sannan ta zura sandal dinta,wunin ranar gabaki daya a jaguje tayishi,driver din gidan sarkin fulanin Adamawa ne yazo daukarsu a school ita da feenah, ko kallon juna basuyiba a haka suka Shiga mota,suna isowa gida feenah tayi gaba zuwa cikin babban gidan,yayinda Elham tanufi b'angaren Masu gadin gidan tana tafiya tana dan saka hanky tana karkad'e kasan wandon uniform dinta tana guntun tsaki dagowar dazatyi ta hango yaa Abdul ya kura mata ido ya hard'e hannayenshi a k'irji se wani shan kamshi yakeyi,wani yamutsa fuska taja d'an siririn tsaki aranta tana mamakin yanda za'ace mutum kullum yana cikin dawaki ko k'yank'yamin Su bayaji ita sam bazata iyaba wlhy,se mayan kallo sekace wani d'an kauye......A d'aya bagaren kuwa na Abdul mamakin iyayi da kuri da k'yank'ya mi irin na Elham yakeyi yarinya ba kowa ba kuma ba yar kowa ba amma se kafirin iyayi da shegen gulman tsiya,banda gulma kaje skul ka dawo ai sauri zakayi ka raba jikinka da uniform amma ita tsabar kazanta wai hanky nata datake share fuskarta dashi kuma dashi take karkad'e dattin wando shi aganinshi Wannan babbar k'azan tace....da sallama tashiga gidan nasu mahaifiyar ta dake kokarin gyarawa akuya daurin da aka mata ta kalla yanda ta dage taketa damkar akuyar girgiza kanta tayi tace tana yank'wane fuska "Sannu Innah,ina wuni?" Dagowa uwar tayi taga yanda tayi kichi kitchen da fuska,ita abinma dariya ya bata tasani Wannan akuyar ne datake damk'a kuma wunin ranar bazataci abinda ma ta girka ba tace "Lapia lau Hafsatu harkun taso?" A tak'aice tace da ita "Ea Inna" tashige d'akin dayake mallakinta a gidan...duk da yake gidansu ba wani me muni bane amma sam bazakayi tsammanin cewar d'akin Elham yakai had'uwar hakanba,komai naciki pink & white har labulaye da gado closet nata center carpet tiles na dakin da komai ma,a kofar toilet dinta akwai towel shid'inma pink&white ne,ajiye jakar skul nata ta farayi sannan ta zauna kan kujerar k'walli d'aya dake cikin dakin ta zare takalmin skul nata ta cire Wannan tissue data nad'e kafanta dashi ta wurga a dustbin dake gefen kofar shigowa dakin wanda yake pink&white ne shima,mik'ewa tayi ta cire uniform nata ta daura towel d'inta na wanka zarar Su tashiga bathroom d'in dan karamin washing machine nata ta budesu ta wurgasu har inner wear's d'inta ma ta barsu anan sabida yana drying bayan ya wanke a tsanake tayi wanka wanda ankai 40 mnt ana yinshi sannan ta kai dubanta zuwaga dan mitsitsin agogon bangon dake toilet me kalar pink& white taga biyu ta gota da sauri ta dauro alwala tafito daga ban d'akin,wurin dazayi Sallah ma wani tashin kanshin turaruka yakeyi ga almiski ma kamshin shi se tashi yakeyi a haka ta janyo hijab fari k'al me kamshi ta tada Sallah tajima awurin tana addu'o inta har aka kira sallar la'asar sanda tayi Sallah sannan ta tashi,cikeda yanga ta zura wata doguwar rigar jallabiya baqa me adon duwatsu jajaye ta dauko red mini veil ta yane kanta dashi gaban mirror taje ta watsa turaruka na asalin masu kamshin gaske, sedai ba masu tashi bane masu sanyin kamshi ne se kazo daf da ita zakaji numfashin ka na shirin dauke wa ya mata rakiya,wasu takalmi ta saka masu d'an tudu suma black & red sannan ta janyo wayarta kiran iPhone 6+ ta kunna ta,tafito tsakar gidan,kallon ta maman tayi tace "Hafsat se ina haka?" Murmushi tayi tace "Zani gun momy Fulani ne,dasafe ban jeba" "To zancen abin ci fa Hafsat?" Yamutsa fuska tayi wanda Wannan ya zame mata d'abi'a tace " Innah na k'oshi" ,girgiza kai Innah tai tana jinjina k'yank'yami irin na Hafsat,sam abin baya mata dad'i yarinya sekace me shafar aljanai.....Dannan wayarta take tana tafiya a yangace status take dubawa kasancewar yau through out bata hauba, a hanyar dazata sadata da sashen momy Fulani taci karo da yaa Abdul,dan yamutsa fuska tayi tace dak'yar "Yaa Abdul ina wuni?" Ko kallon inda take beyiba yace "lapia" atakaice, haushi ne ya tarnak'e ta taja d'an guntun tsaki batare da sanin taba,Ashe ya jiyota,cike da dakakkiyar yace "Elham zo nan" rai a bace tazo kusa dashi ta sadda kanta a kasa tace "Gani yaa Abdul" yafi minti biyu yana Kallonta beyi magana ba,harta fara tsarguwa gashi iya k'uluwa ta k'ulu a ganin ta wani salon wulakncine yake shirin tsirowa dashi,se can har kwalla ya taru a idonta yace cikin izzah da isa "Wakike wa tsaki Elham?" Dago manya manyan fararen Idanuwan ta tayi dasuka Cika da kwallah ta saukesu a kanshi amma ta kasa magana,a tsawace yace "Dake nake magana wa kikewa tsaki?" Kwallar datake kokarin tarewa ne ya silalo a idonta da sauri ta sadda kanta k'asa manya manyan eye lashes d'inta lokaci daya suka jike suka kara bak'i da shek'i,ta kasa magana "Idan yanayin amsa gaisuwa tane bakyaso Na sauke miki ki huta karki kara gaidani,amma kinsani koba komai nafi karfin irinki tamun tsaki,balanta ina matsayin yayan ki" ta tsinkayi muryarsa yana fada, murya na rawa tace "Dan Allah Kayi hakuri yaa Abdul wlhy baran karaba" bece da ita komai ba ya wuce abinshi ya barta gun a tsaye, harga Allah taji kunyar abinta tamasa batai tsammanin zeji ba,hankalinta ya tashi ainun,gwiwa a sace ta juya zuwa cikin gidan "Da sallama ta Shiga parlor din bakowa se feenah dake shan romon kan rago,fuskarta ba Yabo ba fallasa suka gaisa tace " feenah momy fa?" Kallon raini feenah ta mata tace "wace Momyn?" Idan da sabo Elham ta saba bata biye taba tace "Momyn ki" dariya feenah tayi "Au momy na nazata bacin inna kinada wata momy bansaniba,aida tun farko sabida rage kokwanto sekice momyna" Murmushi tayi wanda ya kasance na yak'e ta nemi wuri ta zauna ta kurawa TV ido batare da ta ce kalaba,se can momy tafito, da fara'a dauke a fuskarta tace "Au Mamana dama kin shigo,yanzu nake cewa yau d'innan baki leqo minba sam ko lapia" "Lapia lau momy na tashi makarene kuma yanzu na dawo bansamu nayi Sallah a school ba" Murmushi tayi "Lallai kam nasan da babban dalili,kinmaci abinci kuwa?" Girgiza mata kai kurun tayi alamun a'a Momyn ta tashiga ciki batare da tayi magana ita kuwa feenah tace "Yana dai da kyau mutum ya godewa Allah da kalar cimar gidan ubansa,ace mutum se tsabar kwadayi baka cin abinda aka girka gidanku tsabar had'ama" ran Elham ya baci matuka sedai batace da ita kalaba,kasancewar ta dama bame yawan san magana ba,kawai mikewa tayi tabar sashen gaba daya zuwa swimming pool na gidan,cire ta kalmin kafarta tayi ta kwashe rigarta ta zura kafafuwanta aciki tana wasa da ruwan a hankali....kuka me karfi ya kwace mata ta zauna tayi abinta ma'ishi koda taji an dafa ta ta dago se ganin yaa faruk tayi yana kallonta,nad'e kafar wandonshi shima yayi ya zura kafafunshi acikin ruwan yace "Elham mesa ne bakya gajiya da kuka,ke sam abin kuka baya miki k'ank'anta,yanzu sanar dani menene nasani yanzu zakice ba komai" kallon shi tayi amma batayi magana ba kawai dai ta tsagaita kukan nata,rike mata hannu yayi yace "Ba kasafai nake san tsoma kana a personal life nakiba,amma kisani ina damuwa aduk lokacin da naganki a damuwa kema,dan Allah kirage yawan kukannan har zaki bata kya wawan idanuwanki my swt sis" Murmushi tayi sannan ta sanya hannu ta share hawayenta tace "karka damu yaa faruk zan dena Inshaa Allah" Murmushi ya sakar mata aka wuce wurin..... Washe gari tun 7 ta shirya ta wuce gidan momy Fulani,akan hanya ta hadu da yaa Abdul,dan durkuso tayi "Yaa Abdul ina Kwana?" Ko Kallonta beba balanta na ya amsa gaisuwarta,bata wani damuba ita tama matsu yabar kasar kowa ya huta,mutum se mugun girman kan tsiya,tana saqe saqen ta se ga yaa faruk a gabanta "Good morning beautiful" ya fada yana me sakar mata lallausan murmushin sa" murmushin itama tayi "Good morn sweetest bro ever and how was ur night?" Tsayawa Abdul yayi ya juyo ya kallesu se fara'a suke "It was sweet dear and u?" "Splendid" tabashi amsa tana kokarin barin wurin,hannun ta yariko,Shikuwa Abdul ya dauke kanshi daga dubansu yayi gaba abinshi......"Bazaki tsaya mu gaisa da kyau ba pretty?" Agogon dayan hannunta ta kalla tace "I'm going be late sweetest bro, w'll do that when I come back from skul" sake mata hannun yayi "OK cutee all the best" Murmushi tamasa tajuya kurun,Raihan dake tsaye daga garden tana kallonsu tace a ranta "Zakaci k'aniyarka wlhy yaa faruk,sena gayawa ummah abinda kake shirin yi" ta juya zuwa b'angarensu kallonsu Haj Fati tayi tace "Raihan Yaya kin gama shiri nki? " Sosa kanta tayi tace "Harma nafita na dawo?"" Mantuwa kika yine hala?" Zama tayi ta fuskanci ta "Ummah kinga yaa faruk bayajin maganar ki ko? Kinganshi can ko yanzu yana wa yar me gadi magana,baze taba iya rabuwa da itaba inhar ba tsaye kika tashi masa ba" nisawa tayi tace "Raihan ki barni dashi ze ganene wlhy dani yake zancen,tashi kiyi tafi yarki" mikewa tayi domin batasan tayi fashi jiyama ciwon ciki be barta tafi skul,dukkanin Su a wurin mota suka hadu susu hudu,ba wanda yayiwa dan uwansa magana haka suka d'unguma zuwa school,Raihan ce bayan sun sauka ta kalli feenah tace "Feenah muyi nan plss,ke kullum bakya taba raba hanya da talaka,talakan ma d'an masu gadi bakida labarin cewa annabi da kanshi yace munemi tsari da talauci,had'a hanya da talaka ma ni gani nake zunubi ne" feenah bata ce kanzil ba kasancewar itadin ma ba barinta Raihan tayi ba,Elham kuwa Idan da sabo ta saba da tsangwamar dukkansu,kazalika ire iren wayannan zantutuukan basa damunta, SS3 A take itada feenah yayinda Raihan take 3C, suna iska class yan class suka fara mss neat ta iso, yanzu zakuga iyayi cike da zolaya suke maganar Murmushi kurun ta musu ta zaro duster ta goge sit nata na zama da table sannan ta dauko wani fari se sheqi yakeyi ta shinfida sannan ta zauna,ihu suka saka suna dariya wasu na mamakin tsafta irin tata,Sune wayanda ba'a taba musu gwaninta. Yau bayan sun iso gida hanky d'in ta zaro tafara aikin karkad'e kafar wandonta,hanky dinne ya sub'uce mata adaidai lokacin data d'a goshi domin karkad'e wa,a daidai Wannan lokacin yaa Abdul yashigo ya zo wucewa hanky d'in ya saukar masa akan fuskarsa,cireshi yayi ya juyo a fusace wurgar dashi yayi akasa yad'ago yana Kallonta ita d'inma shi take kallo,rikicewa tayi ganin yanayin fuskarsa tace murya na rawa "Yaa Abdoul, dan Allah Kayi hakuri wlhy sub'uce mun yayi ban kuma san yanda akai yaje kan fuskar kaba" matsowa yayi daf da ita "Karyane Elham,tunda kika iya mun tsaki to my face komai ma zaki iya yimun,nasani sarai kinsani kika wurgomun Wannan kazanta ajikin,an gaya miki kowa k'azamine irinki,wlhy na tsaneki bakida kirki ko kad'an ko ganinki ma bana sanyi dalilinki zanbar kasar nan inkoma inda nafi wayo,and this should be the last concrete warning dazan baki akan Shiga sabgogina daki keyi, next time ko kallon inda nake kikayi wlhy se kinsha mamaki,now get out from my sight" tana kuka tabar wurin Sa'a taci bakowa agidansu hakan ya sanya kai tsaye tawuce dakinta ta rufoshi acan tasha kuka sannan tayi wanka ta gabatar da sallah ta kwanta lamo baccin ya dauketa....... Yaa Abdul yana tsaye yana Shafa jikin dokinshi Raihan tazo ta same shi, Murmushi me sanyi ya sakar mata yace "hii dear how r u?" Murmushin itama tayi "I'm fine yaa Abdul u?" Be amsa mata ba yace "ya akayi Raihan?" Dan Shafa fuskarta tayi tace "Yaa Abdul bakaga message nawa bane?" Murmushi ya sakar mata ya riko hannunta suka fitowar gidan dawakan yace "Raihan kiyi hakuri tafiyar nan tawa tazama dole ba yanda zanyi,kinsani company nakewa aiki kuma sun buqaceni yanzu,amma kin sani kullum zanna rika miki Waya so biyar arana kuma chat ma haka" sadda kanta tayi kasa tace "Allah yasa shine mafi alkhairi" "That's my beautiful wife,Allah ya miki albarka,momy ta aikeni anjima bayan magrib so ki shirya muje tare keda feenah zan muku siyayya.... Bayan isha ya shigo part din momy anan ya taradda Elham,gaida momy yayi cikeda girmamawai,Elham ma ta gaidashi ya amsa a dak'ile,yace " Momy list d'inkifa?" Murmushi tayi tace "Yana wurin Mamana tare da ita zakuje" murtuke fuska yayi yace "momy Idan zaki aika driver ya kaita mana" bata fuska tayi itama tace "Kaga Babana nafa kula kana takura mamana dayawa ka dauki karan tsana ka dora mata ji yanda ka ansa gaisuwar ta sekace ba kanwar kaba,yanda fa kuka dauki duniyar nan bafa haka take bafa tam,aiko dan darajata ka sota,itada feenah nace suje tare dakai Idan kuma bazakaje da Mamana ba Kayi tafiyar ka da kudinka banaso" durkusa wa yayi yashiga ban baki,arayuwar ya tsani yaga ya bata ran mahaifiyarshi,sassauta fushinta tayi tace "ke Elham jeki d'aki bamu wuri" bayan tafita ta kalleshi tace cikin taushin murya "Babana ya kamata ka fahimci Elham yarinya ce me hankali kuma sanin kankace agidan nan aka haifeta ta cancanci duk wani matsayi daga wurinka kodan kasancewar iyayenta masu nagarta,ina sone danni kawai kadauketa matsayin kanwarka kamar yanda ka dauki feenah kuma duk wani abu dazaka was feenah itaama kamata,kai mata wasa da dariya kuma ka saurari matsalolinta daidai gwargwadon yanda kakeyi wa feenah,Babana Wannan ita kadaice alfarmar danake nema a wurinka ina sone konbayan raina ka tallafi yarin yarnan Banso tashiga wata damuwa kabata dama ta kusance ka ta hakane kadai zaka san wacece Elham,Allah shine shaidata ina yowa ilham soyayya me tsanani Wannan rarrabewar kan naku da rashin jituwa,se inaga kamar uwarku daya ubanku daya kuke Wannan,wlhy Babana idanbhar kamun Wannan zan dinga zabga maka albarka daga nan har ranar mutuwa,kuma aljannah dakake nema awurina Idan har ka dena wannann kiyayyar wlhy namaka alkawarin daga ma kafar ka shige tun yanzu" nisawa yayi yace "kiyi hakuri momy ni dama ba kinta nakeyi ba kawai dai Yarinyar komai seta riqa nuna wa mutum k'yama sam bata ajiye kanta kusaba wlhy,amma duk da zan jata ajiki zan kuma nuna mata rashin dacewar hakan" godiya momy tamasa daganan taki rasu suka bar gidan,a hanya Raihan se yada magana takeyi ba wanda ya kulata,bayan sun isa mall din ya baiwa kowa 30k yace Su siya abinda suke so,ya kalli Elham yayi da sauri ta sauke kwayar idon ta kasa yace "Kizo muje kina kwasar kayan momy kina had'awa da naki " bin bayanshi kurun tayi batayi maganaba,Su kuwa Su Raihan sun zare suna can suna kwasar kayan maku lashe abinsu,ita kuwa seda ta gama siyawa momy duk abinda ta rubuta,tabaki wurin biya kud'i sannan tajuya wa nata,mamaki ne ya kama Abdul ganin takalmi kurun ta dauka me tudu se turaruka na 10 10k guda biyu,se kuma ta dauko clips na 4800 kwalli d'aya,kasa hakuri yayi yace " Elly Wannan abin kurun zaki siya?" Yamutsa fuska tayi wanda hakan ya zame mata d'abi'a tace " Yaa Abdul turaruka ne fa masu kamshi ina matukar sonsu dama nawa sun kusa karewa duk na damu" takarashe maganar tana yarfe hannaye nta ,Murmushi yayi yace "To clip's d'imfa me zakiyi dashi?" Ya tambaya yana me hard'e hannayenshi a kirji ya sanya Murmushi a fuskar sa wani langwabe kai tayi ta yamutsa fuska tace "to ai yaa Abdul Kaine baka siyawa kanka komai ba shine na siya maka" mamakin Yarinyar yakeyi duk da yake can kasan zuciyar sa yanajin tsananin tsanarta amma ta burgeshi godiya ya mata suka gama abinda suke suka bar mall d'in, kallon Raihan yayi yace "Bara muje wurin amadu me kajin hausa karna bar kasar ban Ciba" a haka sukaje yab siyawa kowa tasa,kallon kazar Elham tayi tace "Ayyah yaa Abdul ai da baka siyamun ba bana cin kazar hausa" wani dogon tsaki Raihan tayi tace "kaji jaka,ko ranar naji tana gayawa yaa faruk batacin kazar Hausa wai kwata takesha,ina agidan ubanki har kiwonsu ake seki kaiwa tsofaffi Su suci tunda ana kiwo tsabar maqo ba'a iyaci,yanzu gata Banza nan saci" tsawa yaa Abdul ya daka mata "Bakida hankaline Raihan? Ina komai ra'ayine? Tunda bata ra'ayi meye naki aciki,tsabar hauka seki sako iyayenta kina zagi,wlhy karna kuma ji ko ganikin zagi iyayen wata ma ba itaba,wannan ba tarbiyar damuka daura ku akai bane,and to be Frank I'm so very disappointed in you,Elham u should take hrt plss don't be angry,and do not take what she says to hrt,do forgive her,zan siya miki na turawa yanzunnan" Murmushi ta kakalo tace "Don't worry yaa Abdul its fine with me" kuka Raihan ta saka amma ba wanda ya kulata har sukaje gida,suna isa ta tattare kayanta tabar motar a fusace,ba wanda yabi ta kanta suka kwasa sukayi part na momy,acan Elham ta gayawa momy abinda yaa Abdul yaa basu kuma tamasa godiya da adu'a me yawa ta bashi clips data siya masa,momy taji dadi sosai.... Mom Nu'aiym [1/8, 10:32 PM] Sha'awa: *🌞HAFSAT ELHAM🌞* Billy Galadanchi Haske writer's Asso💡 Sadaukar wa ga k'awara Hafsat Abubakar qaya (Elham).                          02 Tana baro sashen momy Fulani taci karo da yaa faruk,hannayen shi yasa duka biyu ya daga ta yace "Kingan ki ba nayi se tsawo" d'an bata fuskarta tayi kasancewar batasan irin Wannan wasan daya ke mata hasalima batasan koda hannunta yake tab'awa gashi ta kula shi sam be dauki abin wani abin ba,tana yunkurin sauka tana wuntsila kafa yaa Abdul yafito daga part d'in,kallon mamaki yabisu dashi aranshi yana mamakin iskanci irinna Hafsat,sam bazakayi tunanin koda yatsa ka saka mata abaki zata ciza ba,d'an tab'e bakinshi yayi ya wuce Su,yayinda tana ganinshi taji wata irin kunya ta lullub'eta lokaci d'aya kuma ta dena yunkurin sauka daga jikinshi,sauketa yayi ganin yaa Abdul, b'ata fuska sosai tayi tace "yaa faruk dan manzan Allah kadena kokarin kai hannu jikina ko wane lokaci,nafa sanar maka banaso yanzu sabida Allah me kake so yaa Abdul yace?" Dariya yayi yace "Nadena princes Ni nasaba rayuwar turai wanna ba komai bane awurinmu" "To ai nan ba turai bane so seka maintaining kanka gaskia nidai Banaso" takarashe maganar cike da shagwaba,wanda ba karamin burgeshi tayi ba. yace yana kallonta "Elham bakice mun komaiba I'm sure kinga message nawa since morning"  Murmushi tamasa tace "yaa faruk kenan,kasani sarai bana bud'e phone nawa se 4 kullum,da yamma nagani trust me,and bansan me zance maka ba" kwai kwayar maganar ta yayi "kice Nima ina sanka yaa faruk mana" tufakan hannayenta ta saka ta rufe fuskarta sannan tace "Yaa faruk dan Allah ka dena kana bani kunya wlhy" "Naji yanzu jeki u ttxt me plss,and make sure u do that before going to bed" dan Murmushi tamasa tace "I'm not even sleepy @ all let's chat" Murmushi shima yamata yace "Fine then ping me if ur free" tafiya take tana Murmushi harga Allah tana kaunar yaa faruk,yafi kowa Santa agidannan me maraba ne da Fulani kurun suke nuna mta kauna fiye da shi,sun d'auketa tamkar yar uwarsu kuma jininsu kokuma Sune suka haifeta duk kuwa dayake itad'in ba kowa bace face 'ya awurin hadiminsu,a hadiman ma me gadi......bayan tayi wanka ta shirya cikin rigar bacci fara k'al ta tufke gashin kanta a tsakiya sannan ta saka hula a kanta ta kwanta,wayar ta ta dauka ta turawa faruk message "Sweetest I'm done" Murmushi ya turo mata yace "fine,that's good rose yanzu sanar dani menene amsarki zaki aureni?" Murmushi ita ma ta aika masa,sannan ta tura masa da hoton hrt,batai magana ba,hrt yakuma aika mata shima sannan yace "Rose mana sanar dani plss,I'm telling Idan kin amince gobe zanje na sanar da me Martaba kina kammala Wannan makarantar Abani matana muje gidana" Murmushi tayi tace "Zan aureka mana yaa faruk koda gobene na shirya wlhy" tsallah ya daka tamkar yana ganinta yace "I'm so much happy miss Rose,thanks a lot for loving me I really appreciate ur love" "I thank you too,charming" murna ce ta kama faruk yata mata hira da wasanni...... *Bayan sati biyu*       Fushi sosai Elham ta dauka da faruk sabida yayi kokarin tab'a jikinta kota karfin tuwo,ko hanya basa hadawa domin kuwa dasun hadu take sake hanya,Abdul kuwa wani abu ya tsare shi a Niger be koma ba sam satinnan dai yake shirin komawa,faruk ya damu ganin ko wayarshi bata d'agawa,yauma kamar da damuwar rashin faruk d'inta tashigo pool na gidan,harga Allah tana missing na faruk,kurun tana sone ta nuna masa kuskurensa Shiyasa take ta faman azabtar da har kanta ma,kamar daga sama taganshi akanta hannunta ya finciko ya juyota ta fuskance sa a bango yaje ya mannata ya daga hannayenta duka biyu ya manna a bangon ya riqe gagam yace "Tell me miss Rose? Why are punishing me like?" What the fuch did I do to you?" Kasa magana tayi kuma bata wani yi yunkurin kwace kanta ba,zuba masa manya manyan fararen Idan uwan ta tayi cike da tsoro,wanda shima din ita yake kallo....a haka yaa Abdul ya shigo ya samesu mamaki suke bashi shikam sam ba kunya a idonsu,ita ce ta ganshi kasan cewar shi faruk ya baiwa kofar shigowa baya,daga nan tafara cuku cukun kwace kanta "Yaa faruk plss let go of me" be sake taba illah ma ya kare riketa tamau ya zuba mata ido, a tunanin yaa Abdul sabida sun ganshi ne take kokarin basarwa ,tana hango sanda ya girgiza kai ya juya kurun, a fusace tace "Wannan mugun halin yasa kake kara nisanta kanka dani,na sanar maka haramunne abinda kake,niba muharra marka bace,ban riga na zama mallakinnka ba mene na tabamun jikina" a fusace ya saketa yafara banbami "Idan sabida wanna kike mun ihu zaki zama mallakina Hafsat,kullum magana d'aya bakida zance sena jikinki sekace kece kikafi kowa a duniya,wlhy nasan maganin ki,yanzunnan zanje na fadawa me martaba ina sone ya daura mun aure dake faqat shikenan?" Ya kura mata yana jira yaji cewarta,cikeda warning tace "Hakane bazan hanaka aikata Wannan ba,sedai fa ka sani karka kuskura na kuma ganin hannunka a saman jikina harsai ranar da aka daura auren namu,baka majin tausayina yaa faruk baka ganin yanda na rame duk sabida ina missing naka,simple abu ya gagareka" sassauta murya yayi "kiyi hauri miss Rose bazan karaba" daganan dai suka shirya Kansu yamata alkawarin baze kara tab'a taba. Zabura Umma tayi dajin zancen faruk tace "Au Wato dama faruku duk gargad'in nan danake maka baka saurara ta? Ina kataba ganin Sarki me jiran gado ya auri yar talakawa ,yar talawan ma yar me gadi! Wlhy faruk kobana numfashi kan auri Elham ban yafe maka ba" gigicewa yayi ya Hau ban baki da ban hakuri amma sam Umma bata sakko ba kara hawa ma takeyi tamkar wata farashi,wasa wasa fa kusan Kwana uku yana rokarta taki aminta,dolece ta sanya yaje wurin momy, ba karamin dadi momy tajiba mamanta zatayi auren Hutu dajin dad'i ,tace "Karka damu umarul faruk zanje da kaina gunta na mata magana da yardar Allah zata a mince,kaga dama na yayanka da Raihan muna jirane nan da watanni shida Su kammala skul inyaso se a hada gaba daya" godiya yayi yatashi yabar wurin cikeda murna,washe gari kuwan momy ta shirya zuwa bangaren Umma,gaisawa sukayi cikeda girmama juna tamkar ba komai a kasan rayukansu game da juna sannan ,gyaran zama Fulani tayi tace "Fulani Babba dama nazone in roki Alfarma awurinki akan zancen faruk da Mamana,dan Allah ki janye furu cinki ki barsu suyi auren Su,tunda addini da al'ada duk basu hana ba" wani mugun kallo ta wurga mata sannan tace "Kinga Fulani wlhy ko ubanwa zaki gayawa bazan sauya Wannan maganar ba,ke gani kike kamar bansan tuggun dakike kullawa ba? Kome nawa Kinbi kin kwace mun yatashi daga nawa ya dawo naki,bayan kin hade kai da mijinki kun kashe nawa mijin sabida ya Hau sarauta,yanzu kinzo kinaso ku daura Abdurrahman har dan munafurci wasu na kiranshi Yarima ,shine zaki zo sabida ki kara batawa faruk suna zaki hada shi da wata shegiyar talaka wai ya aura,a zatonki bansan me nake ba kokuma banida hankaline,duk muna funcinku ina kalonshi wlhy, kuma da yardar Allah bazakuci nasaraba faruk shine ze gaji sarautar ubansa,ko Raihan sabida banaso tashiga damuwa ne kasancewar ta mace kurun ya sanya na yarje mata auren Abdul" kura mata ido kurun momy tayi sanda ta kai aya sannan tace "Kinga Yaya habiba ba zwa nayi Kici mun mutunci ba,zancen kashe margayi me martaba dakike kuma kije mun barki da hukuncin Allah,zancen kuma sarauta dakike keta Shafa ni kina sane yarona bata shafeshi ba,Idan kuma har Allah ya zabeshi keda iyayi nki baku isa ku hana ba,auren Raihan da Abdul dakike magana ita Elham malama ba 'ya bace daki kece Raihan macece ai itama macence bakya duba damuwar dazata Shiga? Tsabar sonkai musulunci da kanshi yamana nuni a sassa daban daban,kuma hadisin ya inganta cewa imanin dayanku baya taba Cika Harse Idan ya sowa dan uwansa abinda yake sowa kansa,kekuwa taki yar kawai kika sani,wlhy kiji tsoron Allah" mikewa tayi a fusace "Kinga Nana barmun sashen na,borin kunya kikeyi Allah ya Toni asirin ku da wuri Wannan karon,wlhy inhar muddin ina numfashi bazaki taba cin nasaraba,nakara fada ko bayan raina faruk ya auri Elham dashi wayanda suka daure masa gindi Allah ya isa ban yafe ba,Idan gaskiyane ba mugunta kike shirin masaba ki baiwa Abdul Elham d'in ya aura mana" mikewa itama tayi "Naji Yaya habiba Abu daya nakeso ki rubuta ki ajiye wlhy Nima ko bayan raina ban yarjewa Abdul auren Raihan ba,dukkanin Su suyi asarar ababen kaunar Su,zan kuma tabbatar miki cewar ba mugun nufi araina domin kuwa aure ne Elham da Abdul anyishi an gama,ke kuwa Idan kin isa ki hada auren faruk da Raihan kema din kiyi auren huce haushi" zage juna sukayi tatas wanda da faruk da Raihan duk suna jiyosu, aikam hankalin dukkaninsu ya tashi,bayan Fulani ta wuce suka yita baiwa ummansu hakuri amma bata hakura ba.... "Koda momy takira Abdul dake birnin London tafada masa kasa yi mata musu yayi kasancewar sa me tsananin biyayya....gashi kuma bashida wacce ya tsana arayuwa sama da Elham" kuka sosai ya saka shikadai tamkar wani karamin yaro a ranshi yace "Ina zankai Wannan kazamar? Ina zan iya da yarinyar da faruk ya gama lalatawa gaba daya,kai wlhy gobe dolene nakira momy na bata hakuri,idan ta rabani da Raihan mutuwa zanyi"..... Kasancewar yau weekends yasanya Elham ke kitchen tana girki asaman risho,taba tsakiya da aikin tajuyo sallamr su Raihan itada uwarta,mahaifiyarta inna ma fitowa tayi dauke da mamaki a fuskarta tana musu Barka da zuwa , sheqeqe Umma ta kallesu tace " ke Asabe gunki nazo,wato sabida kinaso yarki dole setayi kud'i shine kiketa faman qaqa bawa faruk itako,kuma kunga bakuci nasaraba bazan taba bari me jiran gado ya auri yar matsi yataba shine kuka zago kuka koma gun Abdul mijin da kowa yasani Raihan dina ze aura,kuka asirce uwarsa tace yanzu Elham ze aura? To ban hana kuba amma wlhy ku kuka da kanku da abinda zan muku Idan kuka wa y'ata kwacen miji,faruk kuma baze taba auren yar masu Kwana a kofar gida bba".....ba karamin ,baci ran innah yayi ba da Wannan cin kashin bayan sun wuce tayita yowa Elham fada akan shishigin ta da samarin,amma ba ruwanta da zancen aurenta da Abdul domin kuwa uwarshibce ta nemi alfarma, ita kanma bataji Wannan labarin ba se yanzu,ga shi Innah tace ko wayar faruk ta kuma dagawa Allah ya isa,wunin ranar a daki tayishi tana kuka,bazata taba musawa momy ba kodan halaccinta agareta,kazalika bazata taba kaunar Abdul ba kamar yanda bazata taba iya dena san faruk ba. Mom Nu'aiym [1/8, 10:32 PM] Sha'awa: *🌞HAFSAT ELHAM🌞* Billy Galadanchi Haske writer's Asso💡 Sadaukar wa ga k'awara Hafsat Abubakar qaya (Elham).                            03 Washe momy na tsakiya da breakfast Abdul ya kirata,k'aidane Awurinta idan tana cin abinci bata magana,Wannan yasanya sam bata d'aga ba,se bayan data kammala sannan tayi kiransa back....gaisawa sukayi cikeda girmama wa,sannan cikin sanyin murya yace "Momy dama akan zancen Elham ne damukayi jiya,dan Allah momy ki yi hakuri,wlhy narigada na gama tsara rayuwata zanyine tane da Raihan,Idan akaimun haka ba'a mun adalciba" gyrana zaman ta tayi ta daura kafarta daya kan d'aya sannan tace "Babana Ashe kam kacika me hikima,kuma zuwanka a kasar turawa yayi matukar tasiri akanka,Ashe dai mutum da kanshi shine yake tsarawa kanshi rayuwar dayake so yakuma ga ta dace dashi banida Wannan karatun kuma agidan mu ba'a koyar dani irin shiba,wanda na sani shine Allah wanda ya halicci komai da kowa shine yake karawa bayinsa rayuwar data dace dasu ba wai Su bane suke tsarawa kansu,amma nagode daka sanar dani yanzu....zancen Mamana kuma Idan baka manta ba aiba tilastaka nayi ba,rokarka kurun nayi nace ka fitar dani kunya dacin zarafin da akamun,amma tunda tsarin rayuwar ka a hannunka yake,nagode maka kaje ka ci gaba da tsarin yanda kaso....abu na gaba kuma kaje na janye maka auren Elham sedai fa ko bayan raina ban yarje maka auren Raihan ba,seka shirya tsara wata rayuwar da wata ba itaba me tsari" kit ta kashe wayar gaba d'aya,jikinshi ne ya mace koda yakuma kiranta ta kashe wayarta.....Faruk duk ya gama kad'uwa shida Raihan yayinda Fulani Babba ta dauki k'iyayya me tsanani ta d'aura wa Elham da iyayenta,bata tsammanin zata iya bari faruk ya tab'a auren Elham,kazalika bazata taba iya barin rayuwar Raihan ya tagayyara ba beside koda faruk ze rasa sarauta ai Idan Raihan ta auri Abdul sarauta tamkar a hannunsu take,zasu Shiga malamai su mallakeshi kuma jikokinta su gaji sarautar daga baya,shirya wa tayi taje fadar me martaba....     Durkusa wa tayi har kasa ta kwashi gaisuwa,me matarba ya bukaci a basu wuri,bayan kowa ya fashe tayi gyaran zaman tamatelarta tace "Ranka ya dade me martaba dama nazone akan wata muhimmiyar magana,dangane da,zancen auren Abdul da Raihan, Haj Nana ce tace wai bazata tab'a bari Yaronta ya auri Raihan sabida wani dalili nata da ban sanshi ba,nikuwa a ganina da Abdul da Raihan duk abu d'aya ne abin beyi zafi har haka ba" jin tayi shiru ya sanya yafara magana Da daddaya tamkar baya sanyi "Habiba dukkanin abinda kika zomin dashi yanzu ina sane dashi,ki sani shi Allah ba'a masa wayo,ko kad'an abinda kikayi be kyau tuba,ai kodan darajar mahaifiyata kya duba ki bar faruk ya auri Elham,nine me yanke wa yarana hukunci akan wayanda zasu aura amma fa ki sani wlhy muddin kika hana faruk ya auri Mamana bazan bari Abdul ya auri Raihan ba,sabida Elham tafita bukatar taimako,kisani wanna umarnine na mahaifiyata akan inganta rayuwar Elham ko bayan Ranta,nasani cewar Idan na kuskura na had'a su kishi bazaki tab'a bari Elham ta zauna lapiya ba Wannan dalilin yasanya na ce shi Abdul ko yana so ko baya so ya auri Elham,Raihan kuma Baba karami na zab'a mata,Idan baki manta ba tun farkon dashi suka shirya Kansu kece kika hana kike turawa Abdul,nasani tunaninki Abdul shine ze gaji sarauta Shiyasa kikeso ki Aura wa Raihan shi toki sani ba sankai alamurana kazalika Abdul baya san sarauta sabida haka bazaki b'ata mana zumuncinmu ba sam,ko Nana,na sanar mata tuni bawai dan yanzu zancen faruk ya taso ba,na dade da sanar mata bazan bari akan Raihan zumuncin Baba karami da Abdul ya lalace ba labari yazo min cewar basa koda gaisawa kuma Abdul bashida gaskia tun farko yasani sun daidaita kansu,abin haushin ma har mu iyaye mun Shiga ciki daga zuwan shi ya b'ata komai kekuma habiba kika zuge yarki akan kwadayin mulkin da dukkaninmu a duniya zamu mutu mu barshi,ki sani wlhy Wannan karon bazan saurara miki ba,karna kuma jin zancen Abdul da Raihan,kuma lallai ne ta auri Baba karami,kusan shekaru 4 tana bashi wahala baku isaba" jin yayi shiru ya sanya tayi godiya kurun ta wuce abinta, rayuwarta ta baci,tsakani da Allah bataji dadin Wannan abin ba,dama kuma Raihan ba itace take san Abdul ba kwad'ai ta mata san duniya uwar tayi....jiki a sanyaye tashige part d'inta abin haushi kuma seta taradda Baba karami da Raihan suna zance ga dukkan alamu kiran dame martaba ya musu dukkansu yayi tasiri akan su,dama ga soyayya.      Abdul na zaune yana mamakin dalilin daya sanya momy ta dauki zafi har haka kusan kwanaki biyar bata daga wayar sa,ga d'ayan bangaren Raihan ma bata daga wayarsa,kullum cikin kiran Feenah yake,akan ta bashi momy amma sam momy bata karbar wayar,jin karar  shigowar message yayi a wayarshi koda ya duba Raihan ce "Salam yaa Abdul plss Kayi hakuri dani kamar yanda Nima na hakura dakai arayuwa,abubuwa ne iri iri daba kasan dasu ba,banajin dadin rashin daga wayarka amma nasani hakan shine daidai,ban guje ka sabida bana sankaba,wlhy ko kadan ba haka bane na dai gane kuskure na,sam ban kyautawa Baba karami ba,ina fata zaka fahimceni kuma Wannan baze taba mana zumun cin muba.Nagode Raihan." Nisawa yayi bayan ha karasa karanta message din yace a sarari..."Bazan taba dena sanki ba Raihan abu daya na sani tunda kika iya jin zaki rabu dani cikin lokaci kankani haka tofawa Nima zan hakura dake, Elham kuwa bazan taba Santa ba,zande aureta kurun sabida biyayya....   Yau Kusan kwanaki goma sha d'aya fa momy bata d'aukar wayar Abdul,ya damu matuka,Wannan dalilin yasanya ya kira friend d'inshi zayyan ya sanar masa komai,gyaran murya zayyan yayi yace "Zancen gaskia moris maganar iyaye ba abin wasa bane,nifa iya gaskiya Na nake gaya maka ka daure wa kanka ka aure yarinyar,kasani Kaima momy tafisan ka fiye da kowa a yaranta mesa d'an wannan abin ze gagareka,macece fa a hankali zaka koyi santa insha Allah" dan nisawa yayi yace "Zandai aureta zayyan amma sam bazan tab'a Santa ba wlhy,kuma yazanyi da san Raihan ? Wlhy ina kaunarta" dan guntun tsaki zayyan yayi yace "Kaga nifa moris bana sanka da rigima,kaida kanka fa kace dani tajuya wa first love d'inta beside haka zaka bari ran momy yata b'aci mahaifiya uwa fa ? Kasani wlhy ka gyara tunanin ka tawa shawarar kenan" nisawa Abdul yayi yace "Yanzu ya zanyi zayyan?" "Zuwa zakayi ka fara  kiran Yarinyar a Waya,kuma ka daure kace ta hadaka da mahaifiyarka ka bata hakuri,ka sani fushin mahaifa wlhy Masifa ne moris" "Tayaya zan kirata ince tabani momy zayyan?, girmana ze fadi a gunta fa" tsaki zayyan yayi "kaje wurin tariyar girma ka b'atawa mahaifiyar ka rai,bawai nace ne kace ta baka momy kai tsaye ba,kurun kamata dabara,misali bayan kun gaisa ya skul,waye waye Idan kun dan taba hira se kace kana gaida momy kuma ta tabbatar ta sanar mata" "Zayyan tayaya zanyi hira da Elham dan Allah, ni harga Allah kazantar Yarinyar nakeji Wlhy" "Kaika sani ni kaga ina kan aiki se an jima" datse wayar yayi kan yace wani abin,shi kuwa yayi sororro yana kallon wayar,ya dade yana nazarin maganga nun zayyan kan daga bisani yakira Safeenah,lokacin ita da Elham ne zauna sunawa momy tausa,domin agunta Abdul ya gado k'yank'yami sam bata huldarta da hadimai,shiya sanya Fulani Babba ke cewa dan bata gada bane. Dagawa tayi cikeda girmamawa ta gaidashi sannan yace "ki sending mun Number din Elham yanzunnan kinji ko?" D'an kallon momy tayi kasance war ita sam bata san meke faruwa ba kuma dama tasu bazuwa tayi d'ai data Raihan ba sannan tace "To Yaya Yarima yanzu zan turo" momy ce ta bude idonta dasuke a lumshe tun sanda suka fara mata tausar tace "Me zaki tura masa kuma?" "Number din Elham yake so wai" gaban Elham ne ya fadi yayinda zuciyar momy tamata sanyi ganinta takusa cimma burinta....a d'aya bangaren kuwa Abdul ya baiwa Elham msd col har biyu bata dauka ba kasancewar wayanta nacikin gidansu ita kamma bata gidan tana gun momy,se bayan isha tashigo wanda bata mabi takan phone d'imba,tana gama wanka tabi lafiyar gado,can acikin bacci taji wayarta na ringing janyota kurun tayi ta daga ta kara a kunne,a tunaninta samra Ce tasani ita kadai ke mata Wannan iskancin,cikin muryan bacci tace "Samrah wai meye haka ne,kina yawan san takura ni wlhy,bacci fa nake" dan gyaran kwanciyar sa yayi sam be fahimceta ba yace "Hafsat ya gida?" Zabura tayi jin muryar Abdul tace "yaa Abdul ina Kwana ya aiki?" Murmushi rikicewar ta ha sakashi yace batare daya shirya zuwan furucinba "Hafsat ina Kwana fa? Sabida kurun ke kina bacci seki ce dani ina kwana, Toni ban ma kwanta ba balanta na gari ya waye" kasa sakewa tayi da dogon surutunsa tace "kuskure ne Kayi hakuri yaa Abdul" shiru dukkansu sukayi sannan yace "seda safe,gobe Idan kinje wurin yarki kice ina gaidata" Murmushi tayi itama tace "zan fada mata inshaa Allah nagode sosai" "Kinyi Alkawarin zaki fad'a d'in?" Ita dai binshi tayi da to a ranta tana tunanin yanda za'ayi ta sanar wa momy Wannan zancen, ahaka ta ajiye wayar tana nazarin dalilin kiran,ba wata kwakwarar dalili neman magana ne kurun. Da safe ya kasance asabar dan haka da wayarta ta tsala ado ta tafi part d'in momy,suna gaisawa tafara gyaran d'akin momy ko ina yayi kalkal sannan ta dawo gyaran parlor tana tsakiya da gyaran wayarta yafara ruri,dagawa tayi takara a kunne da sallamar ta,amsa ta yayi cikeda isa yace "ki ajiye duk abinda kikeyi kije part d'in momy ki kaimata Waya zanyi magana da ita" d'an wai gawa tayi ta kalli momy dake cin breakfast,tace masa tana me shigewa cikin dakin "yaa Abdul inajin nauyi fa mezan ce da ita,dan Allah ka kira yanzu phone nata yana kusa da ita" shiru yamata tayita hello hello,ba amsa can taji ya katse wayar,kiransa tayi back yaki dagawa har kusan so biyu,Sekuma taji ba dadi ganin cewar sam yaqi daga wayar kuma ta fahimceahi yana da saurin Fushi ta sani Fushi yayi,dawowa tayi parlor din taje dakyar tace "Momy dama yaa Abdul ne jiya yace na gaidaki,yanzu kuma yace na baki wayar kanna zo nan ya yanke ko zaki kirashi da wayanki dan Allah" momy gani tayi tamkar Abdul ya sanarwa Elham bata daga kiransa,kuma seta kula tamkar Elham ta damu Wannan ya sanya ta,dauki wayarta tayi kiranshi,jikin shi har rawa yake ganin ta kirashi ya daga,ko gaisawa basui ba yace "Momy dan manzan Allah kiyi hakuri, wlhy na gane kuskure na,na tuba momy wlhy zan auri Elham din dan Allah kimun gafara" nisawa tayi sannan ta tashi tashige dayan sashen daba kowa tace "Zan gafarta maka Idan kamun alkawarin zaka rika kiranta so uku a rana,zaka mata yanda kakewa Raihan sanda kake neman aurenta,zaka biya mata bukatunta Idan basufi karfin taba kuma zaka shigo next month" nisawa yayi yace "zan yi momy,wlhy zanyi nanda sati biyu ma Zanso inshaa Allah" sallama tamasa ta sauke qayataccen Murmushi cikeda nishadi ta koma parlor...... Hankalin Fulani Babba sam baya jikinta ganin fa dagaske me martaba yake kuma kowa ya goyo bayan hukuncin ta,ga faruk ya koma paris abinshi baya ma kiran Waya gida, gashi kuma Raihan da Baba karami sun kara d'inkewa Yarinyar taqi bata hadin kai tai bori tace dole se Abdul,duk tashige damuwa sosai. Wanin ranar Rabin shi Elham a wurin momy ta yishi,se bayan la'asar tabar gidan zuwa gidansu,Innah ta gaida inna ta ansata cikeda kauna tana kallonta ,ta yabawa yar yanda tayi jarumtar cire faruk a ranta gaba d'aya, takuma sani badan bata sansa ba,kurun dai Hafsat ne bata daukar wulakanci tasani wulakancin da Fulani Babba ta musu ne ya sanya ta fitar dashi aranta.....wuraren shidan yamma yakirata,da sauri kuwa ta d'aga wayar "Yaa Abdul Barka da yamma" seda yadanja fasali sannan yace "Lapia,karki karamun abinda kikamun d'azu bana so" shagwabe wa tayi tamkar zatayi kuka,wanda ita bata dauka komai ba tace "Yaa Abdul dan Allah Kayi hakuri wlhy bazan kara ba" wani yarrrr yaji ajikinshi lokaci daya abubuwan dake kai saqonni na fahimta acikin kwalwarsa suka dena aiki na na 1 mnt,dakyar ya tattaro nutsuwar sa yace "Naji" a takaice,gani tayi tamkar be aminta ba tace cikin wata shagwabar "Yaa Abdul plss mana,trust me bazan kara ba" kasala ce dabesan dalilin taba ta saukar masa ya kasa koda motsi bale yayi magana takuma cewa "yaa Abdul Allah fa nace" cikin muryar kuka,d'if ya kashe wayar yarasa dalilin dakesa kirjinsa ke dokawa dazaran tayi magana,yace aranshi "nifa momy tabani aiki Wannan kazamar jakar zata rainani ko ubanwa take wa shagwaba oho" ita kuwa tsaki taja tana share kwallar data sakko mata tace "Allah yaa Abdul bazan taba sanka ba,na tsaneka Nakuma tsani halayenka na jiji dakai,zan aureka kurun sabida iyaye nka". Mom Nu'aiym [1/8, 10:32 PM] Sha'awa: *🌞HAFSAT ELHAM🌞* Billy Galadanchi Haske writer's Asso💡 Sadaukar wa ga k'awata Hafsat Abubakar qaya (Elham). *A gaskiya kuna sakani farin ciki ba kadan ba,sena tattare dukkan nazari na da tunani,ababen dake sarquwa a kwanyana dan gane da aika saqon fahimta duk se su tsaya cak,ni kanyi mamaki matuka yanda kuke nuna kaunar ku ga rubutuna duk kuwa dayake nidin karamar su ce acikin marubuta.....a wani bangaren mamakine kan kashe ni duk na tuna a shafin farko na book nawa kuke fara comments,dan Allah ku yarda dani ina sanku har raina* 04 Wuraren karfe 9 na daren ranar ya kuma kiranta amma sabida hafsa tafishi zuciya ga kuma rashin daukar raini ya sanya taki dagawa,msd col biyu ya bata,ranshi yaji ya sosu ba bad'an ba, daba dan momy bace wlhy Wannan Yarinyar da tayi kadan yasani sarai tana ganin col nashi tamasa banza,amma zata fahimci baya daukar raini Idan tashigo hannun shi....a bangaren Elham kuwa ta kudiri niyyan bazata kara daukar wayar saba,tunda kullum burin shi ya bata mata rai,ita banda munafurci ma batasan meye na kiran taba,washe gari kuwa bata ma tafi da wayarta sashen momy ba haka taje saddan,ayyukanta tayi tazo ta zauna cin abinci tare da momy da feenah,wayar feenah ya soma ringing, dagawa tayi ganin yaa Abdul ne "Yaa Abdul ina Kwana" be amsata ba yace kije gidan su Elham ki kai mata Waya Kokuma kice da ita nace lallai ta kirani yanzu" tana kokarin sanar masa Elham na kusa kurun ya datse wayar tabe baki tayi ta kalli Elham tace "Elly ina wayan kine?"" Kallonta sukayi har momy,sannan tace "Tana sashen mu,agida na barta" dan yake tayi tace "Gwaramun me martaba ya kirani ban dauka ba nasan ze fahimci bana kusa akan yaa Abdul ya bani ko half msd c ne Idan akwai,ya tsani ya kira mutum yaqi d'agawa ko alama,yanzu kinga masifa yake wai na sanar dake ki kirashi yanzunnan" batayi magana ba shiru kurun tayi momy ce tace "ki tashi kije ki kirashi yanzu" mikewa tayi jiki ba kwari taje gidan msd col hudu ta tarar Nasa ,seta tsinci kanta da kasa kiranshi tsoro me tsanani ya shige ta,ta sani bazata iya gaya mai bakar magana ba amma fa batada juriyar wulakanci,tsaf zata kashe masa Waya Idan yanemi gaya mata ba daidai,daga karshe dai phone nata ta kashe gaba d'aya.... Ba ita ta koma part d'in momy ba se bayan isha sannan ta Shiga, suna wa momy tausa wayar feenah ta fara ringing tana dubawa taga Abdul ne,tana daga wa yace "Idan Elham tana kusa ki bata yanzu" batare da tayi magana ba ta mikawa Elham waya,tana karba tabar wurin seda tashiga d'akin momy sannan tace cikeda faduwar gaba "Assalamu Alaikum" cikin tsawa yafara masifa "Ke Elham me kika dauki kanki ne? Tun yaushe kike ganin col dina bakya dagawa kuma bakya kira back,kuma tsabar raini seki kashe wayar gaba daya,me kike tagama dashi kazama dake,ke badan umarnin iyaye ba da kin isa na rab'i hanyar dakika bima,iyayena naso su miki gata amma kina wulakanta musu yaro,ke bakisan halacci ba ko,dama mana tsinatacciyar mage ai bata mage,kisani wlhy talaka irin ki nafi karfin wulakanci daga wurinta,alkawrine nayiwa momy zan kiraki kullum so uku arana,dabadan uwa na uwa ba wlhy bazan kara kiran kiba,jaka kawai dabata san girman na gaba da itaba,kuma Idan kin isa Nakuma kiranki kimun banza,zan miki uzurin bakya kusa amma wlhy bazan miki uzurin rashin kirana back ba,idan katin wayane bakida zan miki VTU yanzunnan" kukane ya kwace mata,jin tana sheshekar kuka yasanya ya kashe wayar dak'yar ta iya saisaita kanta ta koma parlor d'in, momy ta zata wayar arziqi sukayi se washe baki taki,a daddafe ta gama abinda take ta koma gidansu,wanka tayi sannan ta kunna wayarta tayi adu'o in Kwanciya Sekuma ta kasa baccin ta soma kuka me tsuma zuciya,a haka ranar ta Kwana kuka tana mejin zafin zagin wulakncin da yamata,a rayuwar ta ta tsani a Rena mata iyaye da talaucinsu ko sabida kurun suna karkashin inuwarsu bashi ze basu damar wulakan tasu ba,mijin da zaka yana maka zagin na tozarci tunkan ayi auren hmmm...washe gari da ciwon kai ta tashi dama kuma sn fara final exam na kammala secondary skul,ranar ba skul basuda Exam kasa yin komai tayi,Wuraren 9 wayanta yafara ruri janyo wa tayi a wahalce,ta kara da kunne "Assalamu Alaikum" "Alaikissalama" ya fada cike sa isa "Yaa Abdul ina Kwana?" "Lapia kin tashi lapia?" "Alhamdulillah" tabashi amsa a takaice "meyake damunki Elham,muryanki wani iri?" haushi ne ya tarnake ta tace "Ba komai qalau nake" shiru yayi itama hakan kusan minti biyu,daga bisani ya datse call din, tsaki taja tace aranta kadaiji da rainin wayonka d'an masu kud'i. Haka rayuwa taci gaba da tafiya sam Elham batajin dad'in rayuwar ta, ta tsani Abdul ta tsani kalar wulakancin shi,ta tsani jin koda muryar sane,ta tsani tunawa da zancen auren sa gaba daya,duk sanda ta tuna cewar sun kammala exams gaba d'aya gashi taji ance me martaba ya saka bikin nanda watanni biyu setaji tamkar ta daura hannunta asaman kai ta zunduma ihu,ba karamin dad'i tajiba sanda akace zezo kuma ya fasa zuwa sabida aiki yamasa yawa sabida bata bukatar ganinsa.... Tafe take cikin doguwar bakar jallabiya me adon yellow stones, ga rigar tasha shape,d'an karamin cikinta daya lafe tamkar ba'a saka masa ko loma d'aya aciki,ga wadaccen kugunta daya ke kad'awa batare da tasaka shiba,tafiya takeyi tamkar tanajin tausayin kasa,fuskarta tayi fayau ba komai a cikinta se powder da lipbalm, kallo d'aya zaka mata ka gano sam bata cikin walwala,dadana wayarta take tana faking murmushin.....shi d'inma wayarsa yake dannawa hankalin shi yana wurin abinda yake se karo sukayi da juna take wayarta ta sub'uce a hannunta tafad'i a kasan interlock dake shinfide a wurin tare sukabi wayar har suna gwara kai,hannun tane yariga nashi kaiwa yayinda nashi ya sauka akan nata,lokaci d'aya wani shock ya sauka musu dukkansu atare suka d'ago suka kalli juna,a haka suka k'urawa juna ido tamkar wasu statues,itane tafara dauke kanta,yayinda shi kuwa da sauri ya dauke hannunshi daga nata,atare suka mik'e batare da kowa ya dauko wayar ba,Kawar da kanta tayi akaro na biyu tace "yaa Abdul Kayi hakuri ban kula kana zuwa ba" dukawa yayi ya dauko wayar ya mata kallon tsafta yace cikin gadara "Duk lokacin da kuke tafiya kuna maida hankalinku akan hanya kina jina?" Kai kurun ta gyad'a masa tana tunanin what on earth was he doing dabe mayarda hankalinshi akan hanyar ba shima,tana tsakiya da tunanin ta tsinkayi murya sa yana cewa "Wayar kinnan kai tsaye ta lashe screen Elham,ki shirya karfe 8 daidai ki sameni mota zamu fita" batare daya jiyo cewarta ba ya wuce abinshi kazalika be bata wayar taba dashi ya wuce, tab'e baki tayi itama ta wuce part din momy,a ranta tana mejin zafin lashewar wayar ta,harga Allah bataji dadi ba....feenah ce tace da ita "D'an bani aron wayarki Elham inaso nakira Ashraf ntwrk nawa ya dauke d'if MTN basuyi ba Allah" dan rausayar da kanta tayi tace "Yanzunnan nayi karo da yaa Abdul wayar ta cinye screen wlhy,tanama hannunshi" "Subhanallah wayar nan ko 9 month tayi kuwa? Amma banji miki dadi ba sam,yanzu me yace?" "Bafa abinda yace,kurun yace na shirya mu tafi wani gu anjima" dan Murmushi tayi tace "Allah sanya wata wayar ze siya miki,nasan shi da kyauta inba hakaba aike da irinta har abada" sarai ta gano abinda take nufi cewar iyayenta bazasu iyaba,bayaga laifin taba kasancewar tasani komai momy ce ke mata.......gidansu ta koma ta tsala wanka ta saka hadaddiyar atamfarta dinkin riga da skirt ja ya amsheta sosai,sosai ta murza dauri yasha steps ta feshe jikinta da turaruka masu sanyin kamshin,light makeup tayi ta yafa dan mitsitsin mayafinta a kafada,ta dauko yar cloche bag dinta da uban takalmi me tsini tafito cikeda yanga,karfe 7:56 tana wurin motar tsaye yayinda Shikuwa 8 dinnan ya karaso shi d'inma se tashin kamshi yakeyi,turarukansu suka hade suka bada wani kamshi me sanyin dad'i, dukkan ninsu sun shagala da kallon junansu,itane tayi saurin sadda kanta kasa tace "Yaa Abdul Barka fa fitowa" kallon ta ya d'anyi yace "yauwa" motar dayake komai nata is computerized kirar 508 ya bude da remote key nata suka shige,hanyar Hamdan phones ya dauka da ita suna isa yace ta fito,a yangace take tafi yarta ta catwalk ,shi harga Allah mamakinta yake yanda ta dauki kanta,kalli shigar datayi sekace wata yar Sarki,se yauk'i takeyi tamkar zata karye,d'an guntun tsaki yaja yabi bayanta,suna isa suka hadu da samrah da mijin dazata aura kamal,d'an gudu tayi wanda ya qayatar da dashi ta daka tsallah ta rungume samrah, "saam dazu muna chat wayana ya sub'uce mun ya lashe screen nayi bakin cikin baki kara samun hirarba" dariya sukayi tace "akwai gobe zan shigo gidanku saam dolene naji kanun labarai" yana daga nesa kusa da wasu samari yaji dayan cikinsu yace "Baba kalli inda Allah yayi yalwar kugu agun chic dincan me jar atamfa, tsinanniyar yanzu zamu zamuce munasan mud'an latsa ta nuna ita ta manya ce" rayuwar shi ce yaji ta masifar baci,barin wurin yayi yazo ya gasa da kamal da samrah yace "Elham akwai wanda ke jirana muje muyi abinda ya kawo mu,mutafi" sallama tawa qawar tata,sukaje wurin phones ya zaro mata iPhone 7 kurun yace muje" biyan kudin yayi,suka bar shop d'in, duk daba hira sukayi ba sanda zasu zo seta kula ya sauya fuskar sa zuwa bacin rai,gyaran zama tayi tace "yaa Abdul dan Allah ruwa nakeso" ko Kallonta beyiba har suka isa gida,kallonshi tayi tace " yaa Abdul nagode sosai Allah ya kar'a girma da budi" Binta kawai yayi da ido ya zaro wayarta ta dazu,yaciro sim card nata ya bata,karb'a kurun tayi tabar cikin motar,da sauri yafito yace " zonan Hafsat" zuwa tayi kusa dashi ta tsaya yace "Ba'a sanar miki anbiya sadak'in ki bane" shiru tayi rai abace yakuma cewa "Daga yau duk inda zakiji Sekin nemi izinina kuma Wannan guntun mayafin bana sanshi,lallai kiyi Shiga ta mutunci koda bazaki saka hijabi ba" batace komaiba ta juya,hannun ta ya damko ya juya da ita gaba daya ya daura dayan hannunshi asaman kugunta yace "Bakiji abinda nace bane zaki juya kiyi tafi yarki sekace ina magana da iska" numfashin tane taji yana zarya yana barazanar daukewa dakyar ta iya cewa "yaa Abdul dan Allah ka sakeni ba kyau fa wlhy" sakinta yayi ya riko hannunta gagam ya matso daf da ita har suna jiyo bugun zuciyar juna yace "Ohh Wato sabida niba faruk bane ko? Shi daidai ne ya murza ya kuma shade dukkanin jikinki yanda yaso, kisani wlhy badan najin komai na taba kiba,ke kinmun kazanta na yi Wannan dake ,kisani Kinyi gangan cin shigowa rayuwa ta,kazama kawai" ya sake hannun da karfi anan ta sake kwalin wayar da sim card din ta juya gida da gudu tana kuka.... [1/8, 10:32 PM] Sha'awa: *🌞HAFSAT ELHAM🌞* Billy Galadanchi Haske writer's Asso💡 Sadaukar wa ga k'awata Hafsat Abubakar qaya (Elham). 06 Kara matsawa yayi kusa da ita yace cikin sanyin murya "Hafsat dan Allah ki tashi muje,koso kikeyi kowa seya fahimci halin damuke ciki" dakyar ya iya furta kalaman ban hakurinnan,tunawa yayi da maganar momy datace karya kuskura ya b'ata ran mamanta,Shiyasa kurun yake rarrashinta kuma sarai ya sani feena seta gayawa momy cewar ga abinda ya faru,banza ta masa ya sanya hannun sa ya dagota,da sauri ta kwace hannun nata ta kara matsawa cikeda fusata,beta ba ganin ta harzuqa irin haka ba,d'an tattaro hakurin daya rage masa wuri daya yayi yace cikin d'acin murya "Hafsat kin sani ni d'innan ba sa'anki bane ko? Kuma sarai kin sani yarannan rainani zasuyi Idan har sukaga namiki magana kin k'i ji,plss mana hafsan momy Fulani,tashi ki shirya muje" murya na rawa cikin shagwabar daba ta ma san tanayi ba harda kwallanta tace "Allah ni yaa Abdul bazan biku ba,yanzunnan zaka disgani su feenah kuma sumin dariya,ni ba wanda yake sona kowa ma ya tsaneni" fashewa tayi da kuka shi abinma dariya ya so bashi,zuwa ya mikar da ita tsaye yace hannayenshi biyu duka a kafad'un ta "Bazan disgaski ba I promise,jiya d'in ma Aina ce dake sorry,kuma yau ma nan zan kama dakin Nima,waye ma yace dake ba me sanki? Kowa ma yana sanki Elly, baga momy ba dasu Inna?,plss kije ki shirya muje kinji?" D'an tsukakken bakinta ta turo takuma yamutse fuska dama wanan dabi at tace tace "kaje waje yanzunnan zan watsa ruwa na shirya mu tafi" Kallonta yayi yana dan kasalallen Murmushi yace "zan jiraki a parlor and plss karki wuce 10 mnt" daga nan ya bar d'akin a gurguje ta shirya cikin doguwar riga me santsi kalar sararin samani ya,ta yane kanta da guntun mayafi pink color, jakar ta yar k'arama kalar pink takalmi nta masu uban tudu ma pink ne,powder kurun tasaka da lipstick pink and purple dan tsukakken ba kinnan ya had'e karshe,kwalli ta saka take manya manyan fararen Ida nuwanta suka k'ara girma hasken su yakara bayyana,tasowa yayi domin yaga abinda ya tsaidata kusan 30 mnt,yasani su Ashraf ma sun gaji sabida kurun suna tsoron sane suka k'i kiransa,a daidai lokacin daze Shiga d'akin ita kuwa lokacin take kokarin fitowa,karo sukayi take ya bangajeta taje taga taga zata fad'i da sauri ya tarota jikinshi,kasa magana yayi ya k'urawa tsukakken mitsitsin bakinta ido,ita kuwa ta tsare shi da manyan idanuwanta yana kallon su kuwa ta lumshe su wanda hakan ba karamin saukar masa da kasala yayi ba,take kuma kamshin turaren ta ya gama rud'ashi,saurin saketa yayi yace "I'm sorry Elly, bansan kina zuwa ba" wara manyan idanu Wanga tayi akan nashi tace "Ba komai Nima ban kula kana zuwa ba I'm sorry" janye wa yayi ta wuce yabi k'ugunta da kallo gani yake tamkar danshi take Wannan rausayar,Murmushi yayi aranshi yace " yarinya bazaki rud'ani da Wannan rangwadar da shagwabar muna funcin dakike ba wlhy" koda suka fito kowa ya gama k'osawa Raihan ce sarkin baki tace a fusace "Wai mutum shiba kowa ba galadiman tsumma,yariqa d'aukar kansa wata tsiya,kawai zaki mana iko a karin banza ki barmu anan for more than an hour" batace komai ba,Ashraf ne me tuki,baba k'arami yana dayan gefen,yan matan susu uku suka Shiga baya,yayinda Abdul ya zaga gefen da Elham take ya zauna,lura yayi da yanda tsukakken tommy d'inta ya lafe ya kulleta yace "Elham have you eating?" D'an lagwabe kai tayi batace komai ba,Raihan ce yar iyayi tace " yaa Abdul bafa abinda Wannan taci tun zuwan mu anan,kasan halinta da k'yank'yamin masifa,yoghurt tasha jiya yauma haka" d'an Kallonta yayi ta d'auke kanta daga dubanshi yace,yana meso ya b'atawa Raihan rai karta gane baya san Elham,ko basason juna "Elham mesa? Ban hanaki zama da yunwa ba? Kalli fa yanda flat tommy naki ya k'ara shigewa ciki,Ashraf plss take us to a near by restaurant" d'an narkewa tayi harga Allah ita batasan cin abincin wani restaurant arna ne fa sukeyi kuma ba tsarki sukeyi ba tace "Noo plss yaa Abdul,zansha yoghurt I'm sure it will be OK" d'an mayarda dubanshi yayi kan hanya yace "Ashraf muje restaurant kawai" shiru ta masa ita harga Allah batasan cin komai na wuri,Mr Biggs ya kaisu kowa yafita shikuma ya riko hannunta haushi duk ya gama kashe Raihan,har k'arami ya fahimci hakan,shima hannun nata ya kama yace "kema zakici abinci ne habibty?" Da sauri tace zataci,koda sukaje suka zauna waiter yazo Elham se cewa tayi wai popcorn da ice cream takeso se fayrouz,hannunta Abdul ya riko yace murya k'asa2 "menene haka kike zama da yunwa? Sanar dani me Wannan k'walamar zasu miki' zuba mishi idonta tayi tace " I'm sure zasu k'osaddani,so worry not plss" kallon waiter din yayi yace "fried rice with fried chicken plss" juyawa yayi aka Wadata su da abinda suke buqata d'in,cikeda yanga Elham kecin popcorn d'in kai kace tilastata akayi,tana wani yamutsa fuska,itafa wannan abin dake baiwa mutane haushi akanta bata masan tana yin shiba,hasalima haka Allah ya halicceta,matsa kujerar sa yayi kusa da tata ya sanya hannu ya kwace kwalin popcorn d'in yace "Hafsat bazaki bari momy tace nazo dake Kano na bari yunwa ze halla ka ki ba,so maza bud'e baki shinkafa zakici" spoon din ta kaiwa kallo taga cewar na roba ne alamar dispose one ne,tamkar zatayi kuka ta wara bakin ya saka mata,tana tauna shinkafar tamkar mecin magani,shidai bebi ta kanta ba,haka yayita bata sanda taci kusan Rabi ya kara ebo wa ze bata ta janye kanta,kallonta yayi alamar me hakan yake nufi,ta langwabe kai kurun,kara matsawa yayi da spoon din bakinta ta karayi baya "Elham Sefa kin cinye shinkafar nan tatas" bata fuska tayi tace "yaa Abdul Allah na k'oshi kuma fa kagan inaso zanci popcorn na da ice cream" Murmushi ya sub'uce masa aranshi yace"kini babbiya kyadaiji dashi kike wani mun karairaya sekace anga ya miki ni Wannan yana tasiri ne akaina" ita kuwa aranta se cewa tayi "Mugu Wato sabida kurun suyi tsammanin yana kulawa dani,ta yanda ko aure mukayi nace yanamun wani mugun abin ba wanda ze yadda dani"bece komaiba,kurun ya mike yabar wurin Raihan se cab'e fuska takeyi,amota suka taddashi ya zauna inda yake zaune d'azu,tun daga nesa ya kurawa flat tommy d'inta ido,sosai yake mamakin duk abin cinnan data ci Tommy d'in nanan yanda yake dazu tamkar ba abinci aka zuba masa ba yanzu,Idan kaga tsukakken cikin bazaka yadda ka sanshi ke dauke da wayannan manya manyan Heeps da duwawun ba,dukta yanda ta cira kafarta tana tafiya ilahirin bayanta da gefen cinyoyinta motsi sukeyi,shi wasu lokutanma tsoro take bashi wlhy,a hankali ya d'aga idonshi zuwa dukiyar fulanin ta, yaa ilahi ya furta adaidai lokacin da suke kokarin shigowa motar ganin Raihan ta zago gefenshi yasanya yafito da sauri ya nufi shagon tamkar yayi mantuwa yaje ya dawo,ya zauna gefen Elham ya riko hannuta,wayarta yake kallo k'aya taccen pics nata data saka wall paper ya kurawa ido harga Allah yana san hoton,ba karamin kyawu hoton ya masaba,a haka suka isa shop na sammanin fatihu,mamakin yanda su feenah suka dage sunata kwasar kaya yakeyi ita kuwa ya kula she's too materialistic,and tana da high test ba komai bane yake burgeta sedai batada zalama, ta ebi jallabi yu masu kyau da tsada black ones dakuma coloured one's sunfi kala talatin,kawai taje ta zauna,kallonta Abdul yayi yace "Elham kin gaji ne?" D'an yamutsa fuska tayi tace "yaa Abdul ba gajiya bane ina wayannan sun isa" harara ya wurga mata yace sauran su Lace's fa da atamfa material,shaddoji?" Murmushi tayi "bana saka shadda sam,Lace's kuma da atamfa,hmmm aikawa nadan duba suma sun isheni" haushin tane ya cikasa yace "kinga bazaki hadani da momy ba wlhy,dukkanin kayan da kika eva sunfi kala hamsin ne? Kuma acewarta 150 set za'a miki nikuwa anawa ra'ayin 200 zanyi so maza muje har abinda be mikiba ki Zara,naga wasu dresses a shop na friend d'ina jiya suma muje ki kwasa" kallonsa kurun ta tsayayi,a haka yaja hannunta ya dinga jibagar kaya tamkar besan darajar kudaden sa ba,haka kowa ya siya kayan ba laifi,saura aka barwa gobe kurun...... Yamma sosai suka dawo masauki,Elham ce tafara yin wanka da Sallah sannan sauran ma sukayi,batare da sun sanar mata inda zasu ba, suka caba ado suka fice,bata wani damuba tayi kwanciyar a dakin tana dannan wayar ta,kira ne yashigo,taga bak'uwar lamba,d'agawa tayi da salkamarta,shi d'inma ya masa,suka gaisa yace "sunana Ibrahim,nine wanda namiki katsalandan jiya,ma ina sone muyi sallama,karna bar gari bamuyi sallama gobe asubar fari zamu juya zuwa abuja,Idan bazaki damuba mu hadu a inda na ganki jiya" batayi masa musuba ta saka dress ta roba da siririn mayafi sosai surarta ta bayyana a hakan tafito,zama tayi abinda ta sameshi suka kara gaisawa,yace dama ze mata sallama ne,yayi mata wa'azin yanayin shigarta a kaikaice sannan yace "Hafsat inasan sanin menene yakawo ki Wannan wurin ke kadai hotel ne fa" Murmushi tayi tace "Yaa Ibrahim ban t'aba zuwa hotel ba sam,Wannan ma daka ganni nida yayyu na maza nazo,dakuma yan mata irina susu biyu Munzo hada kayan lefene daga Adamawa muke,yan gidan sarkin Adamawa ne yayin da Nike yar me gadin gidan sarkin tuni,babban d'ansa zan aura,shine mukazo da kannensa maza da mata dayake auren gida Zakuyi dukkansu hadin kayan lefe" gyad'a kanshi yayi alamar gamsuwa da baya ninta yace "Se yanzu nakejin saukar nutsuwa akaina,da farko harga Allah na tsorata nazata cewar wani abinne yasanya kike gudo daga Allah ya albarkaci auren da Zakuyi, ina fatan zumun cinmun baze yanke daga nan ba" gyad'a masa kanta alamun ba abinda ze tsinka musu igiyar zumunci,ya zaro wani kwalin har guda biyu ya mik'a mata,godiya sosai ta masa,sukaci gaba da hira tamkar dama can sun saba,se dariya yake sakata,can ta hango Abdul ajikin mitarshi ya hard'e hannayenshi a k'irji yana kallonsu ya murtuk'e fuskarnan tamau,ta abin ma tsoro ya bata, sauri tayiwa Ibrahim sallama tajuya dakinsu....bayanta yabi yana zuwa ya banke kofar d'akin ya shiga,bata nan tana bedroom, kai tsaye yabita can fin cikota yayi yace a fusace. Mom Nu'aiym [1/8, 10:32 PM] Sha'awa: *🌞HAFSAT ELHAM🌞* Billy Galadanchi Haske writer's Asso💡 Sadaukar wa ga k'awata Hafsat Abubakar qaya (Elham). *Aunty Mejiddah Musa,Wannan shafin nakine kyauta duk ke kadai,na gode da kaunarki agareni* 05 Tana zuwa tayi Sa'a ba kowa kai tsaye dakinta ta wuce,fadawa tayi kan gado a rigin gine ta saka kuka me tsuma zuciya....duk'awa yayi ya dauki kwalin wayar da sim card d'in yabi bayanta dashi,da sallama ya isa gidan bakowa se k'anwarta Halima,tana ganinshi ta mik'e tsaye daga wanke kwanukan datake tace "Yaya Yarima Barka da zuwa ina wuni?" D'an kallon yanayin gidan yayi ba laifi Ba kazanta sedai warin dabbobin dasuke kiwo a gefe d'aya, yace "lapia ina Elham?" Dan Sosa kai tayi tace "Ni kadaice agidan amma inaga sanda nashiga Sallah kamar naji shigowarta bara na duba d'akinta" batare data jira cewar saba ta juya zuwa d'akin, dage labulen kofar tayi tace "Aunty Hafsat ga Yaya Yarima yana magana dake" d'an saisaita kanta tayi batare data juyo ba ta ce,banasan tsayuwa a waje,ki kawoshi cikin d'a kinnan" juyawa kurun tayi domin tasan da matsala taje ta kawo shi har kofar dakin tace ya Shiga.....A yanda ta kwanta kife haka yazo ya sameta still kukan takeyi mara sauti sosai,sosai yaji ba dad'i,harga Allah kukan mace na karyar masa da zuciya ya sani kuma sam be kyauta ba yanda ya sakar mata maganganu,Shifa Wannan kurin da nuna cewar ita watace shine yake bashi haushi dashi,dakin yafara bi da kallo komai k'al k'al,gashi bazakace d'akin acikin gidan yakeba se tashin kamshi yake ya hade da Air conditioner dake dakin,kai dubanshi yayi zuwa ga mirror nata,mamakin manya manyan turarukan dake kai yakeyi,albashin ubanta baze siye daya daga cikin suba,lallai momy ta sangartar da Yarinyar nan,a hankali ya tako yazo daf da ita zama yayi kan gadon ya sanya hannunshi ya d'ago ta,batayi musu ba ya dauki kafarshi ya daura har saman gadon ya juyota ta fuskance shi ya sanya hannunshi ya tallafo kanta ya sanya hannunshi ya share mata hawayenta,so yakeyi yace mata tayi hakuri amma girman kai ya hana,tausayinta yakeji amma yanajin kiyayyarta can kasan zuciyar sa,yayi iya yinsa harshen sa ya furta Kalmar hakuri amma ya kasa,ganin haka ya sanya yanjanyota zuwa kirjinsa,a hankali yake patting bayanta,shida ita bazasu fad'i tsawon lokacin da suka dauka a haka,kawai dai gani yayi jikinta duk ya mace dagotan dazeyi yaga tana bacci,mayar da ita yayi kirjinshi yana mamakin kanshi bayaso ya motsa yakasance bacci nta beyi nisa ba ta farka,yakusa 30 mnt tana jikinshi yana jin yanda har lokacin take shasheka tana sauke ajiyar zuciya, ganin baccin nata yayi nisa ya sanya ya kwantar da ita da kyau ya mik'e tsaye yana kura mata manya manyan dara daran inuwanshi,lumshe ido yayi yana mamakin dalilin dayasa yake Kallonta, waige waige ya soma yi a d'akin can ya hango sckool bag nata ya dakko ta ya zaro paper da pen ya rubuta dakyar "I'm sorry Elly,plss call me as soon as u wake up" ya dakko wayar ya zura mata layinta ya kunna sannan ya jona caji ya bar gidan gaba d'aya.. Wanka yayi ya shirya kwanciya,har ya Hau gado ya kwanta yayi adu'o insa Amma ya kasa bacci, duk motsi d'aya tunano yanayin da suka kasance atare dazu yake,dogon tsaki yaja yace a sarari "Wannan er iskar Yarinyar ta gama sabawa da maza,har ta samu damar yin bacci a jikina muna fukar banza,tagama nuna wa momy itadin ta kwarai ce" har bacci ya daukeshi yana mamakin kanshi yanda ya kasa manta Wannan moment din,dakuma yanda kwalwarsa keta tariyo masa uban tsallen da ta doka a shop dasukaje dazu,yarasa dalilin daya sanya tsallen ke bala'in bugeshi. Elham ba ita ta farka ba se asuba da mamakin kanta ta duba agogo,tayi mamakin baccin datayi iya saninta bazata tunano sanda tayi bacci sanye da kaya ajikinta ba,ga kuma fitila a kunne,tunano abinda ya faru tayi jiki a san yaye ta tashi taje tayi wanka ta daura alwala tazo tayi sallah,nan ta zauna tana ta adu'a, Idan aurenta da Abdul ba alkhairi bane kar Allah ya tabbatar dashi,tana aduar neman gafarar kwanciya da tayi ajikinshi har tayi bacci alhalin hakan ya haramta a tsakanin su,nan dai ta ga saqon shi,taga wayarta,banza ta mishi se Wuraren karfe bakwai da Rabi ta fito ta gaisa da mahaifiyarta ta daura musu breakfast soyayyen dankalin hausa da kwai,ta hada ruwan shayi ta kai dakin Innah sannan ta dauko nata tazo tadan tsakura,ta ajiye....wayar tane tana yana ringing tana dubawa taga Abdul ne,d'agawa tayi tamkar bata san magana tace "Yaa Abdul ina Kwana" gyaran muryarsa yayi "lapia lau kin tashi lapia elly?" Shiru tamasa yace "karfe tara ki shirya zamuje Kano dake da feenah da Raihan,se bayan sati d'aya zamu dawo Idan munje,zan koma ne nanda wani satin kuma da siyayyar da zamuyi" langwabe kai tayi tace "Yaa Abdul banida wanakken kaya fa,mafi akasarin dogawen riguna suna gun wanki plss Abari gobe mana,Idan na karbo" sosai ta bashi haushi yace "Kinga nifa ba laifi na bane,momy ce ta ce lallai yau zamu tafi so kije da kanki ki sanar mata uzurinki" da sauri tace "Kayi hakuri yaa Abdul bara kurin na ebi laces da atmfa,momy ta hana ni tara wanki fa,kuma kaga jiya na kammala exams ban samu na kaiba" "Karfe 9 ya miki a mota kinji bana san Wannan African time na kau yanci" kantayi magana ya kashe wayar sa ya kama hanyar part din momy,a gurguje taje ta sanar da Innah da Baba anan takejin seda aka tambayi baban ta ma,har hada ka yanta tayi ta fito waje kai tsaye part din momy ta nufa taje kusa da ita ta zauna tace " momy na shirya" Shafa kanta tayi tace "Allah ya kiyaye Mamana,dan Allah ki kula da kanki sosai ki tsare mutun cinki kamar yanda nasan kinayi,kuma ki kula da mijinki daidai gwargwado,kai kuma Babana lallai ka kular mun da Mamana amana ce na baka kakuma san yanda amana take ko" girgiza kai yayi,ta zaro wayar daya siya mata tace tana kallon momy tana Murmushi "Momy kinga wayar da yaa Abdul ya siyamun jiya,momy ki tayani godiya dan Allah jiya jiyannan tawa ta fadi ta cinye screen d'in" Murmushi momy tayi,har ranta taji dad'i tace "Angode Babana Allah ya saka da alkhairi ya kara bud'i" shima yaji dadin adu'ar ta matuka,a haka sukazo wurin mota dukkansu,Abdul ne ya kalli kannenshi Baba karami da Ashraf gasu feenah yace "Baba karami,Ashraf,feenah da Raihan ku karbi key din range dinnan ku biyo ni abaya,da mota biyu zamu tafi ni zan tafi da Elham" yana fad'a tamkar yayi kuka,Wannan tsarin momy ne,su kuwa masoyan dama haka sukeso se murna sukeyi zasusha hira soyayyah,Ashraf d'ane wurin yayan momy daya rasu kuma a hannunta yatashi, shine ze auri Feenah a yanzu haka yana aikine da kamfanin MTN,kayan lefe ne akace suje hadowa shine zasuje..... Yamma likis suka isa Kano,a Tahir guests palace hotel sukayi masauki,kallon Baba karami yayi yace"k'arami wayannan matan a kama musu suit Babba,ku kuma kujewa d'aki d'aya " kallon shi yayi yace "Yaya Abdul kaifa?" Wrist watch nashi ya kalla yace "Ba anan zan sauka ba ku dai ku zauna anan,kuma dan Allah banda shishirta,kusan wayannan yaran matsayin kannen ku suke ku kula da mutuncin su" haka kawai Elham taji ba dad'i tace tana shagwabe wa "yaa Abdul dan Allah kaima ka zauna anan" kura mata ido yayi nay'an dak'ik'u yace yana mayarda kallon shi ga Baba karami "Zan muku waya goben ku shirya early,zamu fita da range dukkanin mu" Da sauri ta sake jakarta tazo ta rike masa hannu "yaa Abdul dan Allah ka zauna anan hotel d'in" cikin fad'a ya warce hannunshi yace "ke Wannan wane irin rashin hankaline,kece zaki gayamun inda zan zauna kokuwa,bakida hankali" take idonta ya ciko da k'wallah su feenah suka kwashe da dariya sosai Wannan ba karamin bata ran Elham yayi ba,har ranta taji zafi.....bece komaiba ya ja motar shi yabar harabar hotel d'in, dakin da aka saukesu kowa tayi wanka aka kawo musu abinci suka ci banda Elham yoghurt kurun tasha tace ta koshi,silent ta saka wayarta ta fito waje,tasamu wurin flower bed dake zagaye wurin ta sadda kanta tana kuka me ban tausayi,kyakyawan saurayin datun fitowarta ita yake kallo yazo ya zauna wurin yace,cikeda iya tsara kalamai "K'anwata duk abinda yayi zafi magani nsa Allah,da Wannan kukan dakike dama zuwa kikayi kika daura alwala kika nafila ki mikawa Allah kukanki,kuka baya maganin kowace irin damuwa a rayuwa dan Allah ki sassauta kukannan my sister" a hankali ta d'ago ta kalleshi tana Murmushi tace "Nagode da kulawarka dan uwa,Allah yabar zumunci zan gwada inshaa Allah" Murmushi yamata yace, ko zaki taimakamun da phone number dinki,ina tare da mahaifina Munzo wa'azin kasa da akene kuma yanzu zamu tafi" batayi musu ba ta bashi number yabar wurin yana mata Murmushi, bata saniba komai daya faru akan idon Abdul ne. Cikin dare tasha kuka ba ka danba,washe gari kuwa kowa yashirya fita banda ita,sukace da ita tazo suje tace bazata ba,mamaki sukayi Raihan tace "wa kikeso ya zab'a miki kayan to? Banza ta musu sukayi tafiyarsu,koda sukazo mota yaga Batanan,yace dasu tana na? Wai tace bazata ba,bece komai ba ya nufi d'akin,kwance ya sameta yaje ya zauna kusa da ita yace " Elham I'm sorry kinji" kallonshi tayi tace what for" dakyar yace "about yesterday mana" juya masa baya kurun tayi ta soma. C [1/8, 10:32 PM] Sha'awa: *🌞HAFSAT ELHAM🌞* Billy Galadanchi Haske writer's Asso💡 Sadaukar wa ga k'awata Hafsat Abubakar qaya (Elham). This is just for u Hafsat,kince 2 pages to gashinan kyauta,plss be happy. 07 Uban waye kike zance dashi kullum a waje? A ina kika sanshi? Kuma ya akayi yasan kin zonan?" Rikicewa tayi gashi ya mata rikon da bazata iya daurewa ba,take ta fara zubar da k'wallah, "Yaa Abdul Kayi hakuri dan Allah wlhy anan muka hadu kuma gaisawa kurun mukeyi" wurgar da ita yayi yace "Anan kika sanshi dakika tafi ina kuka had'u? Wato iskancin naki na kula ba akan faruk kadai ya tsaya ba har wasu kartin banzan ko" kukan tane ya tsananta jin furucin shi, janyo ledar yayi yace yana bud'eta "har agogo ma yake baki da turare,shiya sanya kike mu'amala da turarukan dasuka fi karfin talakan ubanki, kin daukar wa kanki rayuwar datafi karfinki ,dole sekinyi abinda wasu masu kudin sukeyi shine kike bin maza ko,wlhy Wannan kaddararren auren da banka d'ad'd'iya irinki asarane,dabadan nayiwa momy alkawarin aurenki ko bayan rantaba ba ba kaddarar dazata sanya na aureki,kuma ki shirya wa kanki zaman kunci a gidana,banza kwad'a yayyiya Wama ya sani ko asircemun iyaye kukayi keda talakawan iyayenki dabasu san halacciba,banza jaka kalli shigar ki menene marabar da yar tasha haihuwar bakin kasuwa,wane me hankalin ne ze ganki ya zaci cewar ked'innan musulma ce? Wlhy an cuceni had'ani dake Hafsat Allah ya isa tsakanina dake, Sekin d'an d'ana kud'arki a hannuna wlhy" fusata tayi yanzu kam tamik'e tsaye tace tana me k'ank'ance idonta cikeda masifa "I have had enough now yaa Abdul! Nagaji! Nagaji! Kuma wlhy Nagaji! Duk iyakar abinda zakamun zan d'auka amma wlhy karka kuma sako mun iyayena,ba kinnan nawa dakake gani bashida ragowa,ni ba yar iska bace ba,kuma ban gada ba,jikina be taba haduwa dana wani ba dasunan zina kuma duk wanda kemun kallon mazinaciya na Barshi da Allah ciki kuwa harda kai,kasani wlhy badan ina sanka kodan wani abinka zan aureka ba,sabida darajar momy ne kawai dame martaba,naga alama abin naka nasan ya wuce gona da iri kana zagarmun iyaye to my face,ni ka sani iyayenka har abada iyayena ne, kuma duk wanda ya zagesu agabana se inda karfina ya k'are,sabida nasan darajar manya na,zancen zaman k'unci dakake cewa zanyi a gidanka Ai tunba Yauba na shirya wa hakan,bakada wani farin ciki karan kanka dazaka bani da har zanyi mafarkin zaman farin ciki agidanka,zancen yanayin Shiga I will admit it nayi laifi,kuma ina fatan kasan cewar Allah nawa laifin bakaiba so awurinshi nake neman gafara Ba kaiba,so na gode da tunatarwa,dan Allah karka k'ara zuwa inda nake,karka k'ara kirana awaya,kullum kamun d'aya daga ciki da bakin ciki nake kwana,dashi kuma nake tashi,ba abinda yafi mun ciwo irin wai ace mijin dazaka aura shine yake zargin ka....." Kasa karasa wa tayi ta durkushe awurin tana kuka me ban tausayi, Shikuwa jikinsane yayi sanyi,seyake ga koda hakane mazina ciyar ce cin zarafin yayi yawa,beside wane tsautsayinne yakaishi zagin iyayenta,shida kanshi yasani Baba hasan dattijo ne me kirkin gaske,sam bashida hayaniya shekaru kusan talatin yake gagi agidan,tun yana dan shekara 5 aka kawoshi gadi gidan kuma amana ta sanya haryau ba'a sauya wani ba,take yaji ya tsani kanshi kuma se wata zuciyar ke bashi watakil ma ba wani abin Elham keyi itada faruk ko wanin shiba,gwiwa asace ya juya ya bar d'akin gaba daga kansa ya kunce,basu feenah suka dawo ba se shad'a yan dare,zuwa lokacin zazzb'i me zafi yagama rufeta,kanta ba kad'an ba yake Sara mata,zuci yarta zafi takeyi sosai duk sanda ta tuna da maganganun Moris setaji tamkar kasa ta bud'e tashige sabida tsanar kanta da tayi,sosai wutar qiyayyar moris ta k'ara huruwa a birnin zuci yarta, ji take tamkar ta kurma ihu sabida tsananin zafin da kalamnshi ke mata a rai,kwanciyar sukayi batare da sun san meke damun taba,cikin dare Wuraren karfe hudu ta farka da wani razannanen ciwon kai,ga rawar sanyi tanayi jikinta yayi zafi rau tamkar gaushin wuta,dakyar tamatsa kusa da feenah ta d'an bubbuga bayanta,tsaki feenah taja tace dan La Elly rabu dani,bacci nakeji" haka tayita tashinsu basu tashiba,da asubar fari ta mike domin yin Sallah tana matukar ganin jiri,kasawa tayi taje ta kwata,Raihan ce ta tashi ta kunna fitilar d'akin ta dawo ta tashesu itama tashiga ban d'akin tai alwala,tana fitowa taga basu tashiba,ta kara tashin Elham aikam tana mikewa ta sulale wurin ta fad'i,da sauri Raihan ta tareta,jitayi jikinta zafi sosai ,tace "subhanallah Elham dama bakida lapia har haka baki sanar wa kowa ba?" Kasa ansata tayi,dakyar tace "Raihan ku kaini wurin Innah mutuwa zanyi kaina ze rabe gida biyu" feenah ma tasowa tayi tazo ta na tattab'a jikinta rikicewa sukayi ganinta galala,da sauri feenah ta janyo wayarta takira Abdul,yana d'agawa tace " yaa Yarima mun Shiga uku Elham zata mutu wlhy bata da lapia sosai, bata ma iya tashi faa" beyi magana ba ya kashe wayar dama yana d'akin kusa dasu daya kama jiya,aikam da gudun shi ya nufo dakin yayi knocking Raihan ta bud'e masa, yana zuwa ya dauketa ya dora kan gadon,sosai ya rikice jin jikinta tamkar wuta,yace da sauri feenah ta kira masa Ashraf Raihan kuma ta dakko masa ruwa me sanyi da towel,take yafara bata tapinsponge se rirrik'e sa takeyi abinda ya kula ma sambatu takeyi,Ashraf na zuzuwa da kanshi ya kwashe ta zuwa mota suka kaita wata alfijir hospital,likitan yace damuwa ce tamata yawa,jininta ke kokarin hawa amma dai be Hau d'inba,se an bata injection da k'arin ruwa,Abdul ya tsorata dajin Wannan zancen,kaddai maganganun shi na jiya neke daga mata hankali har haka!!! Koda akazo amata allura kasa Tsayawa tayi seda Abdul ya riketa, drip na karewa ta samu karfin jikinta aka sallamesu,Abdul da kanshi yake jinyar ta,Shifa arayuwa yanzu bala'in tausayin Elham yakeji ga masifar kunyar ta dayake ji,ita kuwa duk ta bud'i idonta ta ganshi tsanar sace ke kara ruruwa a cikin zuciyarta. *Bayan kwana d'aya* Yana zaune kusa da ita yana bata ayaba dakyar takeci amma ko kallonahi Bata sanyi yakuma kula da hakan,kallonta yayi cikin sanyin jiki yace "Elham dan Allah kiyi hakuri akan abinda na fada miki 2 back wlhy bacin Raine,abinda na fada bawai har raina bane" banza tamishi ta k'ara dauke kanta,yace "Dan Allah Hafsat kice dani kin hakura mana,nasani kalamai na ne suka jefaki a Wannan halin dakike ciki,dan Allah kiyi hakuri kinji" kuka tasaka masa,Shikuwa ayan kwana kinnan tausayin ta yakeji yarasa dalili wlhy gashi kuma bata bashi fuska,cikin rudu yace "kinga Idan zancen ne bakyaso kiyi hakuri na dena wlhy kinji Hafsat" kukan tane ya tsanan ta,harga Allah bata koda sanjin muryar Abdul wlhy ta tsaneshi..... Tir qashi ga alamafa Abdul ma ya jajibowa kanshi qiyayyar Elham matuqa,gashi shi kuwa yafara yin laushi,muje zuwa dai kuna tare da alk'amin mom Nu'aiym.... [1/8, 10:32 PM] Sha'awa: *🌞HAFSAT ELHAM🌞* Billy Galadanchi Haske writer's Asso💡 Sadaukar wa ga k'awata Hafsat Abubakar qaya (Elham).      *Mrs j moon mamar love,this page is for u and u alone,start dancing shoki,koda bansan wane team kike ba,nidai team Abdul moris sak*                           08 Zuwa yayi ya durk'usa daidai inda take zaune ya kamo hannunta ya rike,ta kwace hannun ta ta dauke kanta sannan ta rufe idanuwanta rufe,dafe kanshi yayi yana mejin zafin abinda ya aikata agareta,Shifa bawai yana Santa baneba,kurun dai tausayi take bashi kuma ya sani be kyauta mata ba sam iyaye ba abin wasa bane,matsawa yayi kusa da ita ya zauna yace cikin sigar rarrashi "Elham mana ki sassauta Wannan fushin dakike dan Allah,Idan muka koma gida kina haka momy zatayi zaton wani abin,ki sassauta wa kanki kinji,kumafa doctor yace damuwa ke damunki" cikin kuka tace "Yaa Abdul Idan ka fice mun daga rayuwa wlhy zan daina kuka,Idan kadena zuwa wurina,kadena kirana,ka dena damuwa da tawa damuwar,ka manta dani arayuwar ka wlhy zanji sauqi,dan Allah yaa Abdul ka taimakeni kace dasu me martaba bazaka aureni ba,wlhy banasan auren nan dakai,gwaramun na mutu ba aure dana auri wanda besan darajar iyayena ba yake mun kallon fasik'a yake wa iyayena dani kallon matsafa kuma masu kwad'ayi wlhy Yaya Abdul Idan aka daura mun aure dakai mutuwa zanyi,bazan tab'a manta muggan kalaman ka agareniba,Karfa ka manta har cewa Kayi wlhy ka tsaneni,dan Allah yaa Abdul.....kukane ya k'wace mata sosai,Abdul ya rasa ina ze tsoma ransa,tunda yake arayuwar sa be tab'ajin kunyar dayaji ba a yanzu,se yanzu yake gano d'imbin kuskuren daya tafka na kallon Tsakiyar idonta ya gaggasa mata maganganun marasa dad'i, musammamn tafuskar zagin iyayenta dakuma tsanar ta daya furta mata kanshi tsaye,menene ma ya aikeshi cewa ya tsaneta? Ko makiyinka na gaskia bazaka cewa haka agabanshiba,kallonta yayi idonshi har ya kad'a yayi jajir ita d'inma ta tsagaita kukanta shi take kallo, take ya hango tsanarsa k'arara acikin idonta,tashi yayi yabar d'akin  batare dayace kanzil ba,har wani duhu yake gani,yana zuwa d'akinshi ya kwanta se hawaye,gaba d'aya rayuwarsa ta masa k'unci shidai harga Allah bayasan Hafsat amma ya kasa gane tsakanin tausayinta da kuma kunyar ta Wanne yafi sakashi a k'unci a ce da girmansa da komai ya aikata abinda ko d'an shekaru baze aikata ba,wayarshi ya janyo ya dannawa Zayyan kira,suka gaisa sannan be b'oye masa komaiba ya masa bayani ya kara da cewar "A k'alla ni a ganina be dace na sako iyayen ta ba akoma menene,wlhy zayyan kunya nakeji,kuma na kula Yarinyar ta tsaneni matuka kofa kallona bata iyayi,zayyan koda bana san Yarinyar nan aure fa zamuyi? Kuma fa kaga banida tsarin mata biyu,bayaga haka ba saki tsakanina da Elham haka zamu yita zama?" Nisawa zayyan yayi yace "Moris Kaine kana da matsala wasu lokutan,nasha fad'a maka cewar yanda kake yi ba'a haka,nafasan Elham ba tun yauba,zan yadda da zancenka na iyayinta da kad'ifirin tsiya amma sam ni bana kawowa raina wai tana wanna abin,yanzu dai ka ajiye zancen Wannan k'iyayyar gefe ka rik'a rarrashinta kana bata hakuri,ninake gaya maka a hankali zaka koyi santa Ba kad'an ba" shimad'in nisawa yayi yace "Zanyi yanda kace,amma kam zancen soyayya tsakanina da Elham har abada,Bance ma kuma tana zinaba amma dai idona ya ganemin suna wasanni mara kyau da faruk wanda har abada bazan manta Wannan ba,kazalika baze barni na iya had'a makwancina da nata ba,kasancewar ina kyamar ta wlhy" tsaki zayyan yayi yace "Kanka akeji dai moris mace daice,wlhy tsaf zata rikita maka lissafi,a yanda na lura ma ta fara gigita mun kai" tsakin shima yayi yace "D'an rainin hankali kanka dai akeji wlhy" daga nan sukayi sallama ya koma ya kwata yana nazarin kalaman zayyan.....da yamma su feenah suka fita suda su Ashraf shi kuwa yazo d'akin wurinta,a zaune ya taddata saman sallaya tana adu'a ta idar da sallah,zama akan gadon yana jiranta,tana idarwa ta Kawar da kanta gefe d'aya tace "yaa Abdul ina wuni" da k'yar, d'an Murmushi yamata yace "Lapia lau Elly ya jikinki?" "Da sauqi" ta ansashi a tak'aice,nuna mata kusa dashi yayi yace "zoki zauna anan Hafsat" bata Musa masa ba taje ta zauna,ya ja hannunta ya riqe yace yana Murmushi "Nifa banga kina shirin Wannan bikin ba fa,duk gayunnan naki bazaki hada mana wani abinba" bataso ta bada shi ta kula hirar yakeso kuma duk dan ha Kawar mata da damuwa ne,Murmushi tayi tace "Yaa Abdul nifa banasan wani bidi'an yanzunnan zakaga ance nacika iyayi,walima kurun zanyi" hannunta dake rike da nashi ya matse sanda tayi k'ara kadan yayi dariya yace "kin Cika raki d'an wannan abin kikewa ihu haka,Nakuma sani bakyaso k'awayenki Su ganni fine fine bobo Su mak'alemun shiya sanya bakyason bikin" tafa kula so yakeyi ya mantar da ita abinda ya faru,bashida labarin cewa har abada bazata dena jin zafinsa da kiyayyar sa ba,kallonshi tayi tace " Ea mana Kaima kasan ai koda auren akayi Idan Nayi bak'i a d'aki zaka zauna" yaji dad'in yanda tad'an sake masa,hannu yakai daidai wuyan ta yatab'a yace yana kallonta ita d'inma shi take kallo "Har yanzu da sauran zafi jikinki Hafsat,dan Allah ki rage damuwa kinji" Murmushi tamasa itafa harga Allah yanacin albarkacin momy ne tace "Naji sauqi fa,kurun dai kwad'ayi nakeji wlhy" murmushin sa ya fad'a d'a yace "me kikeso Kici to?" Langwabe kai tayi tace "popcorn da ice cream" hancinta yaja cikin wasa yace "kwad'ayin kenan oya dress well mu tafi" mikewa tayi ta zare hijabin jikinta ta yane kanta da yalolon mayafi,kallonta yayi dress dake jikinta ya d'ameta da yawa ga heeps sun bala'in fito,wani iri yaji ajikinshi yace murya k'asa k'asa "Hafsat plss mana,yanzu Idan na barki seki fita a haka dan Allah? kowa fa ze gama kalleki" d'an Murmushi tayi tace a shagwabe "Yaa Abdul meye aciki dan Allah nafa saka mayafi" komawa yayi ya zauna yace " ki saka hijab kokuma mu fasa fita gaba d'aya " komawa tayi ta d'auki hijab d'inta ta saka tace "to muje na saka" "Yauwa ko Kefa? Kinma fi kyau ahaka Allah kuwa" a haka sukaje suka dawo tun a hanya ta shanye roba biyu na ice cream se kallonta yakeyi ko ajikinta,anan fa ta fara fyace hanci lokaci d'aya mura ya taso mata amma bata dena shaba,suna Shiga d'akin suka tarar dukkansu sun dawo har mazan suna kallo, har lokacin ice cream d'inta takesha,wara ido feenah tayi tace " na Shiga uku,yaa Abdul hope dai Elly batasha ice cream d'innan da yawaba momy fa ta hana,ranar damu kazo ma naga kinsha namiki shiru ne sabida d'ayane kurun" kallonta yayi yace "Bata shan ice cream sabida me to?" Kallon shi taku mayi tace "she's Asthmatic fa,kuma ire iren wayannan qanqarar sam basa bata lapia agida ma ko ruwa me sanyi ba'a bari tanasha" mayar da dubanshi yayi zuwa gareta yace "Hafsat hakane? Wannan fa rofa na ukune kinada hankali kuwa?" Turo baki tayi tana me fyace majina da tissue dake hannunta "kurun ni se'a riqa takurani,koma waye yana jin dadi bandani" nan take ya murtuke fuska dama Abdul akwai saurin Fushi "Danla can rufawa mutane baki,ke d'innan yar rainin wayau ce wlhy kinsan bakida lapia kike shan abinda ze cutar dake tsabar rashin sanin ciwon kai,maza bani ice cream d'in yanzu" tana shagwaba hadda doka kafa a kasa da k'un k'uni tabar wurin "Allah ni anbi duk an takura ni ice cream dinne bazan shaba kuma bayan kowa ma abinda yake so yake sha" galala ya saki baki yana kallonta harta bacewa ganinsa,kurun seyaji ta bala'in bashi Sha'awa,Binta baya yayi,ya zauna kusa da ita yace "Elham ni kuma kikewa k'un k'uni? Lapiyar ki fa nake dubawa" d'an rausayar da kanta harda kwallah "To Kayi hakuri bazan k'araba,amma plss ka bani na karasa shanye wa" Murmushi yayi yace "Zan dai hakura amma bazan baki ba gaskiya" kan wani cikinsu yayi magana har wayan ta ya soma ringing, Murmushi tayi ganin yaa Ibrahim a rubuce, da sauri ta daga wayar ta kwanta tana duban roof na d'akin a shagwabe tace "Lallai ma yaa Ibrahim,Wato se yau kake tunani,Allah ni Nayi Fushi bazan ma maka magana ba" wani d'aci ne ya tunkaro k'irjin Abdul tun daga kan dan yatsan sa har zuwa zuciyar sa da kwanyar sa,yana tsakiya da tunani yaji tana cewa "Ea mana Nayi bala'in missing hirar ka tun juya fa,Banyi dariya ba" da sauri ya mike yabar d'akin zuciyarsa she zafi take,wanda be san dalilin hakanba. [1/8, 10:32 PM] Sha'awa: *🌞HAFSAT ELHAM🌞* Billy Galadanchi Haske writer's Asso💡 Sadaukar wa ga k'awata Hafsat Abubakar qaya (Elham). *kandy  kishiyar Mrs j moon,Wannan nakine Mrs j moon k'awata ta roka abaki,wai kina kuka an bata kyautar page ke ba'a bakiba so chill Wannan nakine ki mata godiya lolxx*                                    9 Koda ta kammala wayanta ta juyo ya tafi,kwanciyar ta tayi bata kawo komai aranta ba,harga Allah ita be wani dameta ba,shi kuwa moris kasa koda kwanciyar yayi aranshi yana tunanin wanene Ibrahim? Hankalin shi ya tashi matuka,ya kasa gane mesa ya damu haka,wani barin na zuciyar sa yace dashi,kishi kishi ke damunka Abdul,yayin da d'ayan sashen na zuciyar sa yace dashi,kurun sabida zaka aureta ne bakajin dadin ganin tana huld'a da wasu mazan, "that's all" ya fad'a a sarari "Mema ze saka Nayi kishinta tunda ba santa nakeyi ba nikam" wanka yashiga ya fito ya saka jallabiya ya kwanta amma ya kasa bacci har karfe biyu na daren ranar idon sa biyu....cikin bacci Elham tasoma jin bata iya numfashi da kyau,dama kuma da mura sosai ta kwanta har tari takeyi,feenah ta tayar tace da ita "Feenah I'm sick,I cnt breath well,could u plss help me with my inhaler?" Mik'ewa tayi da sauri ta kunna side lamp d'in d'akin tace "Where d u keep it then,seda nace karki sha Wannan kayan sanyi amma bakyaji" kasa ansata tayi sabida abin ya taso mata sosai,ko ina feenah ta duba bata ga inhaler d'in ba,wayar ta,ta janyo takira Ashraf yana d'agawa tace dashi "Kazo yanzu plss Athsma d'in Hafsat ya tashi kuma gashi na duba ba inhaler d'inta" tashin baba karami yayi yace "Plss ka tashi muje gunsu feenah Waifa er matsalar nan Elham Athma d'inta ya tashi,shine zamuje muga halin datake ciki,zuwa sukayi suka yi cirko cirko akanta,se neman inhaler akeyi ita kuma tana fama da kanta, Ashraf ne yace " kaga K'arami kira yaa Abdul....." Yana zaune yana salati ya idarda da nafila kasance wa ya kasa bacci sabida tunanin Wannan Ibrahim da Elham ke waya dashi,yaji phone nashi na ringing,harta katse be tashi ba,harga Allah be kawo komai aranshi ba haka call d'in ya k'ara shigo yayi banza dashi,a tunaninshi wani balarabe ne dasuke huld'a dashi kasan cewar Su yanzu gari ya dade da wayewa,ganin fa Elham na shirin shrqewa ya sanya Baba karami ya soma danna mata k'irji,feenah ce tace "kunga dan Allah Kuzo mu kaita asibiti, Wannan athsma d'infa Idan ta tashi mata dole se anmata allura,da d'azu ne ma akaga inhaler ze sauka amma yanzu yayi nisa aminipilin injection kurun za'a mata ya sauka" Raihan ce tace "Hakane amma Inaga mu fara sanarwa Yaa Abdul koda ta zuwa d'akin sane tunda yana kusa" Ashraf ne yaje ya masa knocking,da mamakin sa ya bud'e ya k'urawa Ashraf ido,a rud'e Ashraf yace "Zata mutu wlhy yaya mutuwa zatayi" kallon shi yayi da mamaki dauke a fuskar "kai ka nutsu mana wacece Zata mutu?" "Yaa Elham ce fa Athma ya tasarwa,munyi kiran wayarka baka..." Ai bankeshi kurun Abdul yayi be tsaya ya karasa jin zancen ba,da gudu ya Shiga d'akin ganin k'arami na dannan mata k'irji ya sanya yaji wani bakin ciki ya taso masa,hawa kan gadon yayi ya dagota saman cinyar sa,gani yayi sam bata numfashi bata ma motsi rikicewa yayi lokaci daya ya kwasheta suka rufa masa baya seda ya sakata a mota sannan ya tuna da key,dagudu yaje d'akin ya had'o da wayanshi da ku d'ad'e,asibitin dasuka kaita ranar ya nufa,da sauri suka karb'eta aka danna mata ox da komai da injections,Abdul se zirga zirga yakeyi dawowa wurin Su Ashraf lokacin sun dawo sallar asuba yace "Waiku kuwa wane iskancinne ya hanaku kirana tun d'azu Idan da wani abin ya samu Yarinyar mutane me zakuce?" "Yaa munfa kiraka baka d'aga ba,ka duba wayarka" kan wani yayi magana doctor d'in yace "Patient naku ta farfad'o,dama kunsan case na athsma yana sauka da Wannan injection da sauri,sedai ku kiyaye abubuwan dake saurin tayar mata da asthma" da sauri yaje d'akin, yana zuwa yaje wurinta ya riko mata hannu "Sannu Hafsat ya jikin?" Murmushi tamasa tace yaa Abdul zansha ruwa dan Allah" da sauri ya bude robar ruwan dake gefenta ya daga ta,asaman jikinshi ya kara ta ya bata tasha,gani yaye ta lafe ajikinshi ya sanya be d'aga taba yace cikin sanyin murya "Elly bansan meyasa ba Idan bakida lapiya hankalina gaba d'aya yakan tashi,dan Allah na rokeki ki guje wa duk wani abinda ze kawo miki rashin lapia musamman irin Wannan,nafa Zata mutuwa zakiyi ki barni hankalina ba k'aramin tashi yayiba plss ki dena shan sanyinnan" mamakin kala manshi ne ya sanya ta d'ago ta kalleshi k'wallan datake kokarin tarewa ya sulalo,hannu ya saka ya share mata k'walar ya mayar mata da kanta saman k'irjin sa yana patting bayanta a hankali "Noo plss Elham banasan kina yawan kukannan Alhamdulillah kinji sauqi,koda inda yake miki ciwo ne?" Gyad'a masa kanta tayi alamar e,da sauri yace "sanar mun inane gayamun kinji,ina yake miki ciwo" janye jikinta tayi daga nata,ta kwanta tace "k'irji nane yakemun zafi,kuma se ina jin ribs nawa tamkar iska me sanyi tana Shiga cikin ribs d'in" kurawa dan tsukakken bakin ta ido yayi yanda take magana tana yamutsa fuska dukya gama burgeshi yace "zan sanar wa doctor yanzu I just cnt leave u in pain" Murmushi ta masa tace "Thank you" b'ata fuska yayi da wasa "Sabida na kula da Lapiyar matana kike wani cemun thank you bana so" Murmushi kurun tayi batayi magana ba. A daddafe suka karasa kwanakin biyu da suka rage musu suka dawo gida da yola,daga kaga Hafsat kasan batada lapia ta d'an rame,ba laipi Abdul yana kula da ita sosai,suna dawowa da kwana biyu ya wuce London...... Abdurrahman Allah yayishi da ilimin Zane tun yana karami,kuma Allah ya daukakashi har girmanshi Zane ba irin wanda bayayi,a London kampanonin dake k'era motoci yake zanawa mota,yayinda har kampanonin builder's yake zanawa gida,a yanzu haka yanada kampanin sa na kansa Abdul builder's dake birnin London,ba k'ananun kud'ad'e yake samu a harkar ba,ya kasance yaro ne d'an k'walisa meji da kansa ga tsananin k'yank'yamin masifa komai nashi CA's dashi....... Satinsa uku ga dawo,a parlorn sa yake yana kallo tayi sallama ta shigo kasancewar ya sanarwa feenah Idan tazo part din momy ta Turo masa ita phone nata a kashe yake,har qasa ta durk'usa ta gaidashi,da Murmushi d'auke a fuskarsa ya ce "Zonan ki zauna kusa dani Elham" batayi musuba taje a kujerar da yake ta zauna ya kalleta sosai ya janyo hannunta na dama ya rike yace "Elham mesa kika mun haka?" D'auke kanta tayi zuwa d'ayan side d'in tace cikin wata murya me sanyi "Yaa Abdul me na maka" karkatowa yayi gefenta ya daura kafafuwan sa gaba d'aya saman gadon yace "Yanzu ke baki masan me kika munba? sati na uku bana k'asar seki kama wayarki ki kashe gaba d'aya,abin takaicin ma nacewa feenah ta baki waya wai kin tafi gidan k'anwar mamanki,dagaske kin kyauta kenan Elham?" Sosai ta juyo ta k'ura masa ido,tana mamakin yanda yake rero kalamai tamkar da gaske,mutumin dayace ya tsaneta ina ruwansa da damuwa da inda taje" iska ya hura mata a ido,ta gyara zaman ta,sannan ta kalleshi ta k'ara ya mutsa fuskarta tace "kaga nifa sauqi namaka,ina dama ko tafiyar damukayi akan momy kake kulawa dani,yanzu baka gari menene ze dameka danna kashe Wayata beside ni a ganina wanda ka tsaneshi ai sauqin kane idan ya janye jikinshi daga naka" Hannunshi d'aya ya saka ya dafe kanshi yace "yaa salaam,Haba Hafsat wayene yace dake na tsaneki?" Murmushin yak'e ta masa tace "Yaa Abdul kenan,kasani matsalar furuci kenan ka furta akan idona kuma idanuwa na suna kallon naka sanda ka furta hakan na hango tsanar tawa k'arara a idonka da zuciyarka gaba d'aya" hannunta dake riqe a nashi ya matse sanda ta kwallah k'ara yace "Haba mana Hafsat,dan Allah ki dena furta irin wayannan kalaman kinji" kallonshi tayi tace "Ka gani ko yanzu fa ka kasa furta cewar ba k'iyayya ta aranka,kurun kace na dena zancen,naji Kayi hakuri bazan k'araba" juna suka k'urawa ido na yan dak'iku yayinda Abdul ya kasa gane ainahin meyakeji game da Wannan baiwar Allah ita kuwa tsanarsa fall a ranta sunan sa ma bata san ana anbata,shine ya Kawar da shirun dacewa "An sanar dani kince ke kurun a daura aure bakyasan wani bikin mesa ?" Kallonshi tayi dama taci d'amarar gaggasa masa magana tace "Ba bikin bane banaso auren nakane yake batamun rai wlhy banaso yaa Abdul,zargi na fa kake kuma kace ka tsaneni Wannan wane irin zama zamuyi,yaa Abdul bansan wazan sanarwa ba amma wlhy gabana fad'uwa yakeyi,tsoro nakeji" matsawa yayi kusa da ita ganin tana kuka,ya tallafo ta jikinshi,ita kanta mamaki takeyi yanda bata iya tureshi idan yazo jikinta. yace cikin rad'a "ki dena jin tsoro Elham,kuma gaban ki ya dena fad'uwa I promise to always be by ur side,dan Allah karki badani kowa fa jiran ranar aurena yakeyi,ki saki jikinki muyi bidirin mu kinji?" Bata yi magana ba kamar yanda bata bar jikinshi ba dan kanshi ya janye jikinshi daga nata........ba laifi Elham ta saki jikinta an cashe kuma na narke dukiya a Wannan bikin,sunsha gyara na musamman taciki data waje ba inda basusha gyara ba,fatar Yar fulanin yola se sheqi takeyi, komai iri d'aya aka saka musu ita da Su feenah..... *Bayan ankai Amare* Yan matan Amarya sun watse,ya rage Amarya kurun,Abdul ya daukar wa kansa alkawarin baze tab'a barin ya rab'i Elham ba,shi harga Allah kazantar ta yakeji,sannan kuma batada matsuguni acikin zuciyarsa sam,kazar Amarci yashigo da ita a hannu,ya mata sallama,batare da wata kulawa ba yace "Kici abinci kafin ki kwanta seda safe" daganan be jira cewar taba tafice daga d'akin,kuka sosai Elham tayi a Wannan daren,a ranta tace Wato dama ya kyalenine sabida agama bikin,yanzu nazo gidan na zama banza ko,daga nan ta kudiri niyyar cin ubanshi,kazalika ta dauki alkawarin baze taba ganin bacin rai a fuskar taba..... Mom Nu'aiym [1/8, 10:32 PM] Sha'awa: *🌞HAFSAT ELHAM🌞* Billy Galadanchi Haske writer's Asso💡 Vote me on wattpad@68billygaladanchi. Sadaukar wa ga k'awata Hafsat Abubakar qaya (Elham). 11 Washe gari bata bude kofa ba se karfe tara na safe,a parlor ta sameshi ta hade sosai cikin wata dress thee green color ,har kasa ba karamin kyau tamata ba,ta watsa pink lipstic dinta se tashin k'amshi takeyi,tana kallonshi ya D'auke kanshi daga dubanta da sauri,itama basarwa tayi tamkar bata ganshi ba ta wuce warta kitchen,bayanta yabi da kallo sannan yayi k'wafa yace "Dolene na d'auki girmana,yarin yarnan Zata rainani,ita kuwa ganin datayi ya shareta yasanya ta kudiri niyyar ramawa, ha d'add'iyar indomie ta dafa se tashin k'amshin curry takeyi tasha kayan lambu,ta soya k'wai da kifin gwangwani a had'e,tafito plate d'aya daman tayi tana wakar jirgin soyayya,cikin parlor d'in tashigo ta daura kan dining ta bud'e fridge ta d'auko lemon gwangwani da ruwa d'aya tazo kusa dashi ta zauna,ta kalleshi da d'an Murmushi tace " Ina kwana yaa Yarima? " yana wani tamke fuska yace "lapia lau" ataikace...murmushin ta kuma yi a ranta tace Kayi da gwana wlhy, tana kai lomar farko ta lumshe ido ta sanya hannu ta Sosa kunne tace "Garin dad'i na nesa wlhy" tana ci tana waqar jirgin soyayya abinta,ahaka wayanta yasoma ringing,saam ce ta d'aga tana ihu abinci a bakinta,saam tace "Banza me kike ci?" Dariya tayi daidai lokacin data had'iye lomar dake bakinta tace "Banza wlhy Wannan had'a diyar indomie damukeci a gida yau ma Nayi,ina loma ina tunawa da Rolex tsinanne Nike kawowa skul amma seya wawushe ya barmu,yanzu kuwa ni kad'ai inci karena ba babbaka" Murmushi saam tayi "beb I'm really missin those days wlhy ina, mijinki?" D'an kallonshi tayi da k'asan ido taga shidinma satar kallonta yake tace "mijina kuma? Ohhh kicemun yaa Abdul,yana nan qalau" tsaki saam tayi "wannan wane irin magana ne Elly watch ur tongue" tsakin itama tayi tace "Kinga nifa har yanzu Banyi wanka ba so,wlhy jina nake kamar a gidanmu,mantawa nake inada aure ma bare wani abu wai miji" bata rai saam tayi "Dan Allah ki dena karya jiki kinji,ba kyau abinda kike Wannan sirrin Kune be dace kina gayawa koda niba,nidai zancen yayin biki nane an fitar dubu goma sha biyu k'waya uku" ihu tasaka sanda ya kalleta tace "kaji manyan mata maganin k'ananun mata,d'an kara sending mun acc/number dinki plss zan miki sending yanzu,Choo biki on point* dariya sukai sunata hira kan daga bisani suyi sallama,ta zauna ta cinye indomie tatas tasha juice sannan tazo shan ruwa tana d'aga robar ruwan a bakinta ya taso a fusace ya dauke ta shuri atake ruwan ya tarwatse a parlor din, kallon mamaki tabishi dashi,kan tasamu bakin magana yafara masifa " k'azama kawai,shiya sanya nakejin k'yank'yamin ki wlhy,banda kina yar k'auye kuma jaka menene na saka robar ruwa agaba ki saka ta a baki,bazaki nemo cup ki shaba? Wannan qauyancin nan gaba idan Nayi bak'i a d'aki zan riqa b'oyeki karki yarfani da Wannan halin na yayan kauyawa dakike nunawa" Tunda Elham take bazatace taji abinda ya b'ata ranta irin Wannan ba,ko zagin farko daya mata bekai Wannan baqanta ranta ba,ace mijinka ya kalle kan yace ma y'ar k'auyawa? " Wato iyauenta ne ma k'auyawan plus jaka ita matarsa itace jaka,lokaci d'aya idonta ya ciko da k'wallah take ta fara kuka,murya na rawa tace "Yaa Abdul nice jaka? Nice iyayena suke qauyawa agareka?" Kurun seya wanketa da lapiyayyen mari,yace "ni ban ambaci iyayen kiba karki kuskura ki sauya mun magana kinji na gaya miki wlhy" dafe wurin tayi ta wara ido tana kallonshi zuwa yanzu ta gama tabbatar wa kanta Abdul baze tab'a santa ba,kuma tama fara tsoron sa,sabida tasan wata rana dukna tsiya zatasha,da gudu tawuce d'akinta ta banko k'ofa ko wayarta bata tsaya d'auka ba" acan tafi awa biyu tana kuka dama gwana ce a Wannan b'angaren,indai kukane.Taso ta kira saam setaga tamkar wannan tonon asiri ne agareta,amma fa Elham ta fusata daganan ta dauki k'udirin baze k'ara ganin haqwaran taba har abada, bazata fasa girka masa yaci ba amma fa ko inda yake bazata k'ara zama ba har abada,tsanar sa me tsanani ya addabi zuciyarta,har wani tafarfasa zuciyar tata ke mata, a haka taje ta watsa ruwa ta sauya kaya zuwa jeans 3 quarter da bingilalliyar riga pink colour,Yaukam ba makeup ta kalminma flat aka Saka, murtuke da fuska tafito dama duk fuskar ya kumbura idanuwanta ta sunyi jajir fuskar nan tayi jajir abinka da farar mace,a parlor ta sameshi ko kallonshi batayi ba ta wuce abinta kitchen,rice and stew tayi da salat ta soya kaza ta had'a musu mango juice tun a kitchen ta zuba komai nata a plate takai d'akinta ta dawo ta kai masa Nasa dining,ta zo inda tabar wayar ta,ta d'auka tace "Yaa Abdul abincinka yana dining" ko kallonta beyiba seda ta juya yace "yauwa" murya can k'asa dama yunwa yakeji sosai daurewa kurin yake,ga gogan da masifar k'yank'yami becin girki sena gida.... Haka kwana ki suka shud'e har sati biyu kowa tasa ta fissheshi yakeyi,tunda tazo gidan bata tab'a Shiga side d'inshi ba koda tashiga dariyar data kwana biyu ba tayiba ta dinga tsulawa tamkar wata zautacciya har tana rik'e ciki,ba wani abu bane ya bata dariya irin yanda taga komai Nasa a har gitse ga boxers da singlet nashi tsilli tsilli masu datti,laundry basket nashi gwanin ban tausayi,kan gadonnan kuwa tamkar inda akayi yaqi,sosai ya bata mamaki ace duk iyayi da tsafta irin nashi d'akinshin a haukace, a ranta kuma tace "Laifi nane ai its my duty wlhy,Harma naji kunyar kaina sosai" komawa sashenta tayi ta saka wandon maza irin k'ananun nan masu yanka ata gefen cinyoyi,wanda da kad'an suka wuce duwawunta,ta sako vest baqa tafito sosai ta gyare d'akin ta turareshi da turarukan masu daukar hankali,tashige ban dakin sanda ta wanke boxers din da singlet duk sannan ta wanke ban d'akin a ranta tace "Ko matar malam jabir ai da haka ta ciwo kansa"# wani haske Ummie Aisha. Tana idarwa tafito daga part d'in a parlor d'inshi suka had'u da sauri ya dauke kanshi itama haka ko kallon shi batayi ba tace " Sannu da zuwa yaa Abdul" a wulakance yace "Me kikemun a d'aki kokuma wata k'ulallaiyar ce yanzu" yafad'a a maimakon ya am sa gaisuwarta ,Ras taji gabanta ya fad'i sosai da sauri ta d'ago ta kalleshi sarakan kukan se hawaye,ita yanzu sosai yake bata tsoro wlhy,murya na rawa tace "Bafa abinda na maka part d'in na gyara kurun" juyowa yayi jin muryarta na rawa yace "Ubanwa ye yace dake ina bukatar hakan,Wato dariyar dakika ga ina miki shine har ya baki damar ki saka k'azamin hannun ki kina damkar mun kaya ko?" Mamakinta ne ya karu waiita yake kira k'azama,batasan yaa akayi ta tsinci muryarta da furta "Kayi hakuri plss yaa Yarima" tsaki yaja yayi gaba,ita kuwa d'akinta ta wuce se nana tawa kanta takeyi "Bazakiyi kuka ba Elham kin gaji wlhy,koda bazaki ramaba ki nuna masa cewar be damekiba,kuma karki fasa neman ladarki" a haka da k'arfin hali ta share k'wallar ta,Shikuwa a haukarshi wai basanta yakeyi ba wani asiri ta masa yake jin sha'awarta,wannan kuma ba wanda ke zugashi se abokinshi dakesan yayi kuskuren sakin Elham shiya aure Wato khamis,kuma yayi k'udirin baze dakata ba harsai ya cimma burinsa......Acan ma ta manta wayarta batare da wata farga baba bayan tayi wanka tasha gayu ta nufi part din,da sallamarta ta Shiga ta sameshi yayi d'ai d'ai a kan gadon yana danne dannen wayarsa,be ansataba itama kuma bata damuba ta dauki wayarta ta juya harta kai k'ofa yace "Ke zonan" gabanta ne ya fad'i jin yakirata da ke,lokaci daya kuma taji ranta yabbaci,Wato har takai baze iya kiran sunan taba?" Jiki a mace ta juyo ta tsaya wurin gadon batare datayi magana ba,cikeda isabba tare daya kalletabba yace "Visa naki ya zama ready,nanda kwana ki uku zamu wuce London ki shirya kayanki,kuma yau da dare zamuje gidan me martaba ki musu sallama gobe zamuje gidan Su momy ki musu sallama jibi da sa sassafe zamubi jirgi mu sauka a Lagos, Friday zamu d'aga zuwa London" shagwabe wa tayi,wanda itafa harga Allah bata masan tanayi ba tace "yaa Abdul dan Allah kamun rai,bikin saam next week fa,kabari idan aka gama mana" wani mugun kallo ya wurga mata,yace a fusace yana mike wa tsaye"wai nikam a zatonki zaki yaudareni da Wannan shagwabar munafurcin,kinga bokanku be Ciba shine zaku zomun ta wannan hanyar,wlhy wannan tafiyar ba fashi,kar kuma ki yarda wai sabida inaso zanje dake,takura ni akayi wlhy,banza kwad'ayayyiya danla can matsa ki bani wuri" tayi alkawarin bazata kuma yin kuka agabanshi ba wannan ne ya sanya ta masa murmushin yake wanda akace yafi kuka ciwo tajuya batare datayi magana...... Mom Nu'aiym [1/8, 10:32 PM] Sha'awa: *🌞HAFSAT ELHAM🌞* Billy Galadanchi Haske writer's Asso💡 Sadaukar wa ga k'awata Hafsat Abubakar qaya (Elham). 10 Abdul se zirga zirga yakeyi a d'akinshi ya kwasa bacci,ya rasa dalilin daya sanya zuciyar sa keta faman azalzalarsa akan yaje gun Hafsat,yanaga koba komai zataji sanyi,betab'a jin abokanshi sunce sun kwana d'aki daban daban da matansu ba musamman sabuwar Amarya, haka dai ya hakura ya kwanta dukda a wannan bacci sam be dauke shiba, da safe ma yaso Shiga d'akinta amma seyaji nauyin yin hakan....a b'angaren Elham kuwa Wannan rashin shigowar da safe ba k'aramin b'ata mata ranta yayiba,kuma ya kara nuna mata cewar ita da banza basuda maraba ko kad'an,sosai kuma taji ta qara sanarsa,tasani da faruk d'inta ne baze tab'a yi mata haka ba,wata k'ila ma sam zumud'i baze bari yabar kusa da itaba,kuka ta zauna ta saka ita kad'ai bame rarrashinta,tana Tsakiyar kukan wayanta ya soma bulayin neman agaji,dagawa tayi taga saam ce aminiyar ta da kukan ta d'aga bata boye mata komaiba,saam cewa tayi mata "Kinga ina gidan Aunty Husnah dama tace Zata baki tips na horar dashi sabida haka bara na bata,idan kina kuka kinma damu kenan" wayar aka baiwa Aunty Husna suka gaisa tace "Kinga Hafsatul Elham share hawayenki,yanzunnan zan saving digit naki a waya zanna riqa d'auraki akan service wlhy se yamiki magiya akan gwiwowinsa kekuwa alokacin zamu nuna masa cewar tabbas shayi ruwane,zamu tauna tsakuwa sabida aya taji tsoro kazalika zamu jefi tsuntsu biyu da dutse d'aya jal,Abu na farko danakeso dake shine ki cirewa rayuwar ki qiyayyar sa sabida mijinki ne zawarci masifa ne,sannan kuma qiyayya jafa'i ne wlhy, komai zece da iyayenki kansa yayiwa Allah ne masani,yanzu sanar dani kina da k'ananun kaya?" Tana share majina tace "Ea dama ni nafi shiri dasu da dogwayen riguna" Murmushi Husna tayi tace "Yauwa yar gari,inaso ki cire abinda yake halla ka matan hausawa Wato kunya,ki rataye a kwandon shara,mijinki Ne ba haramci ko tsirara kika fito masa,Ki fara dannan guntayen riguna da wanduna da d'amammun kaya kina rafka uwar kwalliya,na sanki da yalwar gashi ga jiki me daukar hankali,lallai ne ki rama wulakancin daya miki idan ya kawo kanshi domin dolenshi ma yazo,karki kuskura ya gane kinci ciwo,kuma ki masa girki na wuce sa'a,ina fatan dai kin koya agida kosai nazone?" Dan Murmushi ya sub'uce mata tace "A wurin momy Fulani ba kalar girkin daban koyaba,har na turawa ma sanda take a k'asar waje tana koyamun,kuma Alhamdulillah na dauke Su tsaf,sanda mukaje Kano Hutu ma da ita ta sakamu catering school na kusan 3 weeks har snacks muka koya,a school kuma Nayi food and nutrition da home economics" dariya ta bushe dashi tace "Kai Wannan zancen yamun dad'i yanzu dai dan Allah ki riqa wanka da ruwan miski,kuma had'in magarya da bagaruwa na tsarki ma ba dole se kanada aure ba,kurun ki daure kina had'awa zan aiko miki da butar k'arfe kina saka karan fari a ruwan da Jan miski Harma da farin kisaka ganyen d'od'oya idan baki dasu duk zan aiko miki,karkuma naji kina tsarkin ruwan sanyi wlhy,ruwan d'imi Sune ruwan tsarkin ki,kuma kina yawan wurga karan fari a bakinki seyayi laushi yana hana warin baki kinji?" Godiya sosai tayiwa Aunty husnah sannan tana Ajiya wayar ta yi dariyar mugunta sosai ta gano yanda Aunty Husna keso suci uban Yarima me jiran gado cikin ruwan lolxxx.... Tashi tayi tashige cikin toilet ta watsa ruwa abinta dama tanada farin miski momy ce ta bata kusan kwali uku,ta tsiyaya a ruwan se tashin kamshin miski takeyi tako ina,wata bingilallaiyar riga ta saka pure red me adon red stones agabanta,rigar iya karta gwiwa,gashi ta dameta ta d'ago da dukiyar fulaninta sun leqo waje ta baje gashinta batare data tufke shiba gashi bak'i wuluk se sheqi yake abinka da yar fulanin usul,ya sauka har gadon bayanta,a karonka na farko da ita zaka rantse cewar ba indiya ka gani,wani hula wanda bata rufe tsakiyar kai ta tsakiya ta zagaye kanta dashi ta sako gashin ta baya,janbaki me taken rubiwu ta saka a lips nata ta sanya kwalli me fito da blue color a take ta fara shanawa a fuska ma,kwanar turaren turarenta Na slim girl ta Shafa da sauran Su tomphord woman da daddy's girl ta saka sannan ta fito,a parlor ta taddashi yana zaune yana shan hot coffee yana kallo,cike da takun katsaita ta tinkaro inda yake,kamshin turaren tane ya shaida masa iso warta wurin,cup na coffee dazekai bakinsa ya dakatar yabita da ido,harga Allah be gane taba,murmushin ta me laushi ta sakar masa tace cikin wata hatsabibiyar murya "Ina kwana yaa Abdul dafatar ka tashi lapia" dak'yar ya saisaita tunaninsa sabida seda ma tayi magana ya tabbatar ita d'ince yace "Good morninh wify how was ur night" yafad'a yana kallonta wani wal tayi da ido tace "splendid yaa Abdul,kaifa?" D'an Murmushi yayi yace "Same as urs,u looking so wow" wani far tayi da ido "thank you yaa Yarima,me kake sha?" "Coffee,will u like some?" Yabata amsa yana kuma tambayar ta, Mik'ewa tayi daga zaman tace "No thank you,lemme prepare something for u to eat" wani Murmushi yayi "for me or for us?" Ya tambaya D'auke da Murmushi a fuskarsa,ita d'inma Murmushi tayi,tace "sure for the both us" "That's very good of u" bata kulashiba ta wuce se mazaya mazaunan ta takeyi,da kallo yabi Heeps nata,seda ya had'iya wani yawu me d'aci,sannan ya kawdda kanshi a daidai lokacin da ta b'acewa ganinshi,yace aranshi "Kinada diri Elham sedai bazaki dulmiyar dani ba,Wannan kad'ifirin naki a banza kikeynshi" A gurguje ta feraye dankali ta soye ta had'a kidney sauce ta soya k'wai,ta had'a ruwan tea,ta d'auka taje ta Jere Su a dining, ta zo ta zauna kusa dashi tace "Breakfast is ready" Mik'ewa yayi ba tare da ya kalleta ba yace "Shall we" shi adole ze D'auke idonshi daga kallonta,sabida Shifa ba wai yana santa bane kuma yaga alama so take ta d'aga masa hankali da Wannan k'ayatacciyar halitta me d'aukar hankali,kamar yanda be kalleta ba haka itama ta Kawar da kanta tace "sure" zaman cin abincin bameyin magana harsu ka kammala,dukkaninsu suna tafiya ne da tarbiyar momy ta rashin magana idan anacin abinci,yarigata kammala wa ya kalleta yace "Thank you so much,its soo delicious" Murmushi kurun tamasa ta bar wurin zuwa,parlour d'inta,acan ta baje tana cin kwakwa da dabino data gani a kitchen ta ebo dama cimar tane acewar Sophie G vitamin.....karfe d'aya ta tashiga kitchen koda ma ta duba yabar gidan be sanar mata ba Murmushi kurun tayi tace "A iya sanina dai duk wani namiji me mutunci idan ze fita ko Allah ya kiyaye ze nema agun matarsa amma banda Wannan,tunawa tayi da momy ta d'auki wayarta ta kirata,gaisawa sosai sukayi tace " Ina me gidan naki? " d'an Murmushi tayi cikeda kunya tace "yanzunnan ya fita momy" Murmushi itama Momyn tayi "Kuyi ta hakuri mamana,kiriqe mijinki hannu bibbiyu na sani dukkanku biyayya kikamun amma da yardar Allah zakuga sakamakon yiwa iyaye biyayya kuma zaku k'aunaci junanku ba kad'anba" godiya tawa momy,Momyn tace "ke Mamana kina da nutsuwa kinga yar uwarki feenah da masifa ta isheni wai aika musu da abinci ba nace aiba wacce ban koyawa girki acikin kuba so bazan wahalar da kaina ba" dariya tayi "momy se hakuri kinsan halin feenah akwai shagwaba" ahaka dai suka sha hira kan suyi sallama. Fried rice me yawa tayi da meat balls tayi salad na potatoes ta had'a zob'o se tashin kamshin karan fari yake da cucumbers, gidan gaba d'aya ya had'e da k'amshin girkinta,se Wuraren karfe uku ta kammala girkin,wanka tayi ta dauro alwala,tana nan har akayi la'asar ta tashi tayi salla sannan tashirya cikin wani rantsatsen lace pink colour me flowers red aciki,ba k'aramin karbarta yayi ba ya fito da figure 8 d'in tannan CA's da ita ta tufke gashin kanta tsakiya ta fito dashi ta baya,fuskar arna tasha makeup idan ka ganta tamkar ka sace ta ka gudu,uban takalminta me tsini ta saka red ta fito tana tauna chewing gum dake bakinta,sanda tazo tsakiyar parlor d'in takula da Abdul moris da friends d'inshi Su hudu, d'anja da baya tayi sannan ta gaidasu,kafe ta da ido yayi sanda take magana dasu,d'an mitsitsin bakinta yake kallo ga fuskarnan tasha makeup tamkar ta ziyarci wani makeup studio,tace dasu "Bismillah kuci abinci mana" zayyan ne cikeda zolaya yace "Dama mana kin isa muzo ki hanamu abinci aikinyi kad'an inba haka gobe zamu kara auro wata" dariya tayi har fararen haqoran ta suka bayyana tace "Aini kishiya se idan Anayi a lahira honey da kake gani ba kishiya a tsakanin mu ko ya kace honey?" Tafad'a tana me k'urawa Abdul ido tana dariya, yawunshi ya had'iya yace "Hakane sweery bazan miki kishiya ba har abada" cikin takunta na kasaita tajuya zuwa kitchen wani abokinsu yace da sauri batare dayasan tana jinsa ba"kai yanzu moris tsabar kai d'an iskane Wannan zangad'ediyar zakace bakaso shegen banza kawai" kawai moris seyaji haushi jin ancewa Elham zankad'ed'iya aranshi yace "data saka hijab da bazega surartaba har yace hakan,dining suka nufa Dukkansu ita kuwa koda ta karasa kitchen idonta ya Cika da kwallah aranta tace " Wato Harma friends nashi sunsan ni fankon ashana yafini daraja baya sona,ni ina kokarin nuna musu ana tare shi kuwa ba Wannan a tsarinsa ko?" Da k'yar ta iya saisaita kanta tafito tafara serving nasu tana dan Murmushi, lura Abdul yayi Wannan friend d'in nashi khamis ya matsawa Elham da kallo take yaji wani takaici dabesan dalilin saba,yabi heeps nata da kallo yaga tamkar ita ta dasawa kanta,yace "ki Barshi mana zan saka musu" Murmushi tamasa "Honey lemme just do it,its nothing ai" Noo u go and get us some fresh fruit's for me now" sake masa serving spoon d'in tayi tawuce cikin yangarta,Zayyan ya mikawa spoon din yabi bayanta,janyo hannunta yayi yana Shiga kitchen d'in ya rungumota ta hanyar rik'o k'ugunta ya sanya d'ayan hannunshi ya tallafo kanta ta bayan wuyanta,suka k'urawa juna ido na kusan second talatin itace ta fara d'an yamutsa fuska tana kokarin barin jikinshi,k'ara k'ank'ameta da kyau yayi yace "Elham me haka kikeyi?" D'an wara ido cikeda mamaki ta k'ara yamutsa fuska tace cikin shagwaba "Yanzu kuma yaa menayi" kara matseta yayi jikinshi yace "Kinganki kuwa,kalli jikinki Elham mesa baki saka hijabi ba? Kinga mazancen fa se kallonki suke" tsuke bakinta tayi sannan tace "Yaa Abdul to yanzu kuma baza'a kalleniba,kurun sabida kai ka tsaneni kowama so kake ya tsaneni?" Shiru yayi kuma be saketa ba yana nazarin kalamnta,cikin sigar rarrashi yace "Elham ki dena cewar wai na tsaneki,ba kyaufa kina cewa wai na tsaneki nifa mijinki ne" kara tsuke fuska tayi tace "kaga bafa ni bace nace haka Kaine da kanka kafad'a so yanzu me kakeso nace? Ni plss ka sakeni" sassauta riqon daya mata yayi yace cikin sigar rarrashi "Amma dai kin sani cewar ai ke matar aurece,dan Allah ko mayafi ne kisaka mana" gyad'a masa kai tayi alamun to,tama Zata sakinta zeyi se kurun ya kasa danne kwad'ayinnsa ya manna mata Sumba a kunci sannan ya saketa....juyawa kurun tayi tana mazaya masa k'ugu tana rangwa d'a anan ya tsaya amace......Koda dare yayi a parlor ta sako riga da wando na bacci gajeren wandon me aljihu ya fito da Heeps dinnan,ta baje gashinta me kyau kwantacce tazo ta zauna suna kallo tanashan fura daya kawonmata ba mewa wani magana,se Wuraren sha d'aya tamike tace "yaa Abdul I'm Danma sleepy,off to bed good night" Murmushi yamata "Bazaki bari film dinnan ya kare ba mu tashi tare?" Murmushi tayi ta cura hannunta cikin gashin kanta,tayi wata tsayuwa ta Turo k'afarta d'aya gaba tace tana yamutsa fuska"karka damu yaa Abdul bancinnan da gaske yake,idan ka tsayar dani wlhy anan zan maka bacci,kuma na tsani a tashe ni ina bacci" gyara kishingidar sa yayi "Bazanma tashe kiba cak zan d'a gaki zuwa room naki" tab'e baki takumayi ta yamutsa fuska tace "I will not like that either, so just lemme go,good night" bata jira cewar saba ta juya,tun a parlor d'inta ta rufe da key,beji dad'in hakan ba yaso tayata bacci yau,yayinda a d'ayan bangaren ta kudirta baze tab'a Shiga sashinta da sunan bacci ba" Tir k'ashi muje zuwa to,koya Wannan zaman ze zama,kuci gaba da kasancewa da alkalamin mom Nu'aiym. [1/8, 10:32 PM] Sha'awa: *🌞HAFSAT ELHAM🌞* Billy Galadanchi Haske writer's Asso💡 Vote me on wattpad@68billygaladanchi. Sadaukar wa ga k'awata Hafsat Abubakar qaya (Elham).   *Wannan shafin nakine Lil sis queen Miemie,Allah ya albarkaci rayuwar ki Ameen*                           12 A d'akinta takasa yin kuka, tunanin irin rayuwar datakeyi da Abdul take tana mejin tsoron kalar zaman dazasuyi idan har tabar k'asar ita dashi kurun, sukuku ta wuni ranar ba karamin tashin hankali take cikiba,da magrib suka shirya zuwa gidan a b'angaren momy suka sauka,kayakyawar tarba tamusu,sunsha hira ko wannensu ya ware ya nunawa momy ba matsala a tsakaninsu,daganan suka wuce part d'in Fulani Habiba then suka wuce part d'in me martaba, ya musu Nasiha sosai akan zaman lapia da mutun ta juna kuma sun d'auka har zuci agabanshi,koda zasu tafi sarqar gwal ya baiwa Elham dalleliya me dauke da zobuna da awarwa raye,ta zuba godiya ba adadi sannan suka fito kai tsaye wurin mota ya nufa da ita sanda taga da gaske yake sannan tamkar zatayi kuka tace "Yaa Abdul bamuje mun gaisa dasu Innah da Baba ba" wulakance ya kalleta "Au Baba me gadi wai,ina kinga da kanshi ya gaidani sanda muke shigowa kuma ai shine ya bud'e mana gate sabida duty d'insa ne,Kedai daki kaga ya dace ki gaidashi kije bazan hanaki ba,amma ni shi yake gaidani kuma Kema kin shaida hakan" wani bak'in cikine ya tarnak'owa Elham har wani d'aci takeji acikin yawunta haduye yawu tayi masu zafi sannan tace "Na sani ai Yaa Abdul bata yanda za'ayi me mulkin duniya ya gayar da me gadi,dama bance ka gayarda me gadi ko matar saba, amma y'ar me gadi ita ai tasan darajarsa kamar yanda tasan iyayen kowa,ta sani Babba babbane,sabida koba dan sun haifeta ba dole ta girmama Su" tana kaiwa nan ta juya,shi kuwa ya k'ura mata ido yana nazarin kalamanta....gaskiya Abdul akwai mugun hali,suk kalar zugae da khamis ke masa ai shima yanada hankalinsa be dace yanawa Elham haka ba....   Bayan kwana d'aya suka cira zuwa Lagos,har suka shirgi ba mewa kowa magana, ita ykamma tunda yaqi zuwa gaida iyayenta bata k'ara koda gaidashiba shikuwa ya nuna mata ko'a jikinshi,Suna hawa hanya gogan ya soma bacci ya daura kanshi a saman kafadarta,acikin baccin ya daura dayan hannushi saman cin yarta,ita dai batayi kokarin hanashi ba a haka har suka yi landing, hannunta ta saka tad'an bubbuga cibyarshi firgigit ya farka ganin shi ajikinta ya sanya duk yaji nauyi,shine ya rigata Mik'ewa yace muce, a hotel suka sauka d'aki d'aya ya kama musu badan yasoba,sedan yayiwa momy alk'awarin bazewa mamanta nisa ba har abada, Suna Shiga ta wuce  Bathroom sabida ta gaji towel nata ta dauka a jaka yana kallonta tashige labulen d'akin ta daura towel d'in ta dabe wuce duwawu kadan ba,ta fito ta shige wankan,tana fitowa tazo Shafa mai,koda take zuwa ya dawo dagashi se gajeren wando,girjinshi faffad'a ga wani yalwa taccen lallausan gargasa kwance luf a ilahirin jikinshi se sheqi sukeyi,farar fatarsa ta kara nuna wa acikin bakin gashin tayi luf luf a jikinshi,gabanta ne yayi mummunan wannan karo na farko data fara ganinshi a haka,dan sauri ta dauke kanta tazo tana Shafa mai,haka kurun yaja mata tsaki yace "Ke menene haka? Meye na zama daga ke se wannan towel bakida kunya ne ko bakisan bakida mara ba da tsirarara ba" kallonshi tayi batace k'alaba taci gaba da murza man shafawarta tamkar bada ita yake magana ba,k'wafa yayi ita kuwa tayi Murmushi,can kuma ta taso tazo kusa dashi ta sunkuya ta juya masa baya,sassauta towel d'inta tayi tace "Yaa Abdul plss ka shafamun a baya yana mun k'aik'ayi" kamar yace baze yiba se kuma ya lak'uci man ya murza a hannunshi,taushin lallausan hannunshi sanda ya sauka a wuyanta tad'an b'ank'are bazatace ga abinda taji ba awannan yanayin,yanayine na musamman da bata taba tsintar kanta acikiba me wuyar fassara,hakan take awurin Abdul tunda yake beji skin me santsi da laushi irin na Elham ba,Shafa man yake yana lumshe ido yakuma kasa dena wa sanda taga ze rikitar da ita tace cikin wata murya "Yaa Abdul har yanzu?" Lum sassun ida nuwansa ya sauke akanta yace "sorry network news nake kalla hankalina yana can" Murmushi tamasa tace "Tom na gode" wata hatsa bibiyar rigar bacci ta saka me had'e da wandonta iya cinya zip ne ta gaban rigar se faman janshi takeyi ya sak'ale tamkar Zata fasa kuka tazo kusa dashi "Yaa Abdul dan Allah ka rufe mun zip d'innan mana kaga fa se janshi nakeyi amma mak'ale" d'agowa yayi ya sauke idonshi daidai cikinta,flat tommy d'inta ya k'urawa ido yace aranshi "wannan Yarinyar anyi yar duniya" Tasowa yayi tsaye ya janyota ya manna jikinsu tamkar ze maidata ciki sannan ya d'an matsa kad'an ya kamo zip d'inta a maimakon ya ja zip d'in seya cura hannunshi cikin rigar ya shafi tommy d'in ta murya k'asa k'asa yace "Hafsat wai nikam yaushe rabonki da saka abinci a cikinnan,jifa yanda ya lafe" hannunta takai saman Nasa dake kan cikinta take ta k'ara masa wani shock ya D'auke numfashi tace "Yaa Abdul meye haka? Dan Allah ka dena banaso" idonshi da suka sauya launi sabida azaba ya sauke mata yace "Menayi kuma?" Shagwabe wa tayi "Dan annabi nidai ka rufe mun zip d'in yunwa nakeji" dakyar ya iya rufe zip d'in,a wahalce ya koma ya zauna,juyawa tayi tana dariyar mugunta a ranta tace "Indai ina duniya kuma muna tare seka duk'awa me gadi da ahalinsa wlhy" Har takai kofar fita zuwa parlor dake d'akin ta dawo "Yaa Abdul I'm hungry fa" k'ura mata ido yayi yace "Nasani yoghurt zakice kina wanka na saka an kawo miki" D'an lumshe ido tayi tace "But yau har da gasasshiyar kaza irin me d'awafi d'innan zanci plss,wasu lokutan idan akayi wa Baba megadi albashi yakan siyo mana" k'irjinshi seda ya doka jin abinda tace sarai ya sani dashi takeyi yace "Shirya mu taka anan bayan hotel nasan ana saidawa" da sauri ta wani daka tsalla tace "Yauwa bara na saka hijab kin na" Murmushi yayi yafara tariyo tsallen datayi yanda mazaunan ta ke girgiza san ransu,Shifa harga Allah ya kusa ajiye zancen Khamis gefe, idanma asiri suka masa aiba laipi bane danya kusanci matarshi kumama koda zasu rabu ai Gara yasan ya Mora,beside kyautuwa ma yayi a karya taba sakin matarshi,tunda ai zab:in momy ce,da wannan tunane tunanen har tace "Yar megadi na jiran Sarki me jiran gado,nafa kimtsa" beji dad'in maganar taba amma seya basar ya Mik'e kawai ya zura jallabiya rsa ya ce "muje" haka suka jeera suna tafiya ba mewa wani magana acikinsu,suna karya kwanar layin ya rik'e hannunta,kallon shi tayi batace komai ba,acan suka siyo suka k'aro juice suka juyo,har suka iso ba wanda ke magana,anan suka bace tare suka cin ye kazar tatas,mikewa tayi ta wanke baki ta dawo ta haye gadon ta kwanta abinta cikin nutsuwa bacci barawo shine ya sungumeta suka ware..... Ba ita ta farkaba se Wuraren karfe biyu na dare dama tana tsammanin zuwan period nata,aikam ciwon mara me tsanani ne ya tasheta,a razane ta tashi sai kuka,se Innah take kira tana yarfe hannaye,a k'asa ya kwanta dama saman carpet acikin bacci yaji kukanta ya farka da sauri yazo ya dagata ya daurata akan cinyarsa "Hafsat lapia menene ya sameki haka" tana kuka tace "Yaa Abdul na Shiga uku mtrl pain ke damuna mutuwa zanyi" tsoro yaji sosai ya rasa me ze mata,acikin rudu yace "Me ake baki Idan yana miki ciwo ne?" Kasa ansashi tayi tayita kuka se tambayoyi yake mata amma sa. Ta kasa amsashi sabida azaba,kan kace me wannan tafara amai me tsanani da gudu take zuwa toilet yin aman,a haka har kusan asuba dawowa tayi ta kwanta akan cinyarsa duk ya damu tanata kukan,hannu ya sanya yana d'an patting bayanta a hankali,da kad'an yaji shiru koda ya duba tayi bacci sosai ta bashi tausayi yalwataccen gashinta duk ya baje ya rufe mata fuska se gumi take had'awa hannu ya saka ya janye mata gashin a hankali ya sunkuya ya sumbaci goshinta yace "sorry my wife, u will soon be well" kasa d'agata yayi ya barta anan tana bacci nta har bakwai ta gota sannan ya lallab'a ya ajiyeta ya je sallah,kuma dawowa yayi kasan cewar flight nasu se dare ze tashi ya sanya ya shige cikin jikinta ya rungumeta sosai suka ci gaba da baccin Su,har cikin ransa yakejin wani dad'i jinshi ajikinta wanda ya kasa gane ko dad'in menene. *kumun uzuri Kuyi hakuri da wannan ina busy ne* Mom Nu'aiym ce. [1/8, 10:32 PM] Sha'awa: *🌞HAFSAT ELHAM🌞* Billy Galadanchi Haske writer's Asso💡 Vote me on wattpad@68billygaladanchi. Sadaukar wa ga k'awata Hafsat Abubakar qaya (Elham). 13 Basu suka farka ba se after 11,shine ya fara farkawa mamakin yanda suka k'ank'ame juna yakeyi,itama sarai ta farka amma seta kasa b'anb'are kanta daga cikinshi,haka kurun taji kwanciyar ajikinshi na saukar mata wata nishad'i dajin dad'i,duk sanda yayi yunk'urin tashi se yaga tana k'ara rik'eshi,gyara mata kwanciyar ta yayi ajikinshi ya rungumeta da kyau,k'urawa fuskar ta ido yayi yana murmushin dabesan dalilin shiba,hannunshi ya saka ya yaye mata gashinta daya rufe kyakyawar fuskar,idonta yake kallo yanda gashin idonta ya kwanta luf luf gasu zara zara,sumba ya manna mata a cute lips d'inshi.seda ta gaji da baccin k'arya sannan ta bud'e lumsassun idonta a hankali ta saukesu akanshi,Murmushi ya sakar mata ita d'inma ta mayar masa martanin Murmushi,yace "Sannu Elly how are u feeling now?" Wani narkewa tayi dak'yar tace "I'm feeling much better now but am seriously hungry" d'an gyara mata kwanciyar ya kuma yi yace "To ai ked'ince kin iya san jiki da yawa,baki bari ma na motsa ba balanta na na nemo miki abinda zakici nanfa ba gida bane" magana yakeyi d'auke da Murmushi a fuskarsa wanda shima besan tame ye yakeyi ba,lumshe ido tayi ta yamutsa fuska tace "Nidai abinda zanci plss" hannunshi ya d'aura akan gashinta yana shafawa a hankali yace "Elham to dake zan tashi kid'an tashi mana" a hankali ta raba jikinshi da nata tayi cikin toilet wanka tayi ta dawo d'akin ta tarar baya nan,ta zauna duk jikinta a mace yake ko man ta kasa shafawa, a haka yashigo ya sameta ta kwanta ta k'urawa saman d'akin ido,zama yayi kusa da ita yace "Chinese rice and meat balls, kokuma fried rice da paper chicken?" Turo baki tayi tace "Yaa Abdul shin kafa da safennan ni indomie zan ci" k'ura mata ido yayi yace " Elham a ina zan samo indomie yanzu? Dan Allah Kici wannan kiyi hakuri " batace komai ba ta sauko ta d'auki Chinese rice d'inta da meat balls ta fara ci sanda ta cinye tatas sannan ta sha lemo ta kalleshi "Yaa Moris kai bazaka ci abinci bane?" Murmushi ya sub'uce masa jin sunan data kirashi dashi yace "I'm OK nasha coffee yanzunnan" tashi tayi ta Shafa manta sannan tayi brush ta zo ta kalleshi tace "Yaa moris kaje parlor zan saka kaya" kwanta yayi ya bata baya yace "keda kika damu kya iya zuwa can ki shirya abinki ni ba inda zani" ya mutsa fuska tayi ta tab'e baki ta kwashi kayan taje parlor ta saka sannan ta dawo, wayarta ta d'auka ta juya zuwa parlor d'in taje ta kira Aunty husna,suna gaisawa tace "Aunty da kunya wlhy da kunya abinda kike cewa Senayi,jiyafa cewa yayi banida kunya" dariya Husna tai tace "kinga bawai rashin kunya nake Saka kiba gaskia ce kurun nake d'auraki akanta,kisani mijinki baze kawo kanshi gareki ba a wannan yanayin se kin janyo shi sosai ajiki,inasone ki saka abubuwan dakike a mizanin k'uruciya u stop being too serious kin gane ai?" Murmushi tayi tace "Yauwa Aunty Husnah na gode zanyi yanda kikace" daga haka sukayi sallama tana shigowa d'akin yace da ita " Elham zonan" batayi masa musu ba taje kusa dashi ta zauna yace "sanar dani menene ake baki idan kina kalar wannan ciwon dakikayi jiya? Na tsorata gashi bansan maganin dakike sha ba" d'an wara ido tayi irinna k'uruciya ta d'age kafad'unta tace "Lipton ake had'amun me d'acin gaske ba sugar kokuma nasha cock amma fa sam sedai yarage baya sauka kuma haka Innah tace se idan Nayi aure ze denamun ni banma yadda ba yanzu ita da momy duk haka suke cewa amma har yanzu be dena ba,gashi kuma Nayi auren kaga ni bara ma na kira momy na sanar mata Nayi auren amma mestral pain be dena munba" ta saka hannu ta janyo wayarta da sauri ya k'wace yace "ke bakida hankaline wai?" K'ura masa ido tayi irin cikin mamakin nan tace "Menayi kuma yanzu,ina Sune suka ce haka gashi yanzu nayi auren amma yamafi damuna" gano yayi kuruciyarta yayi yawa yace "How old are you Elham?" Kallonshi tayi tace "Kamanta kwana ki goma sha biyu na bawa Feenah August zan yi 17 nanda watanni shida masu zuwa yanzu ina 16/2 sha shida da Rabi" dariya ta sub'uce masa yace "Ban gaba jin inda mutum yace yana shekara kaza da Rabi ba just admit it ur just 16,kinga baki gane zancen Su momy bane suna nufin se i dan Kinyi aure kinada shekaru ashirin ne bazakiyi ba amma yanzu ur just 16 ai" dafe kirji tayi ta wara ido "yanzu kana nufin duk month Senayi haka se nan da shekaru uku da rabi?" Se kuma tasa kuka wiwi shi abinma dariya ya bashi janyota yayi yace "Kinga Elham bafa abin kuka bane,idan kin haihu ma kan nan da shekaru ukun ze dena" k'wace kanta tayi daga jikinshi tace tana kuka "Bayan Aunty Husnah data haihu tace da wahala daukan ciki sanda tazo aihuwa ma sumanta biyu Allah ni bazan haihuba" hannunta ya riqe "Yanzu dai ki dena kukan haka,idan mukaje London zance abaki maganin daze hana kiyi ciwon kuma tunda bakyaso ma bazaki haihuba so be it kinji?" Gyad'a masa kai tayi hadda share majina ya ce yana kwantar da ita "oya zoki kwanta da yamma zamuje yawo flight namu karfe 11pm ze tashi" wani patting bayanta yakeyi ita kuwa dama haka takeso sun shirya bashi wahala idan har ya kuskura ya kawo kanshi...... Ya Zata bacci takeyi jin yakira sunan ta kusan so biyu bata amsa ba,janyo wayar shi yayi yakira Khamis yana d'agawa yace "Khamis Yarinyar nan Zata rikitar dani wlhy,kaga k'uruciya zallah wai Ashe dama rashin zama wuri d'aya ne ya sanya ban gane tanayi ba nifa inaga bazan iya rabuwa da itaba sam wlhy" d'biar sace idan ba headphone tofa hansfree yake saka waya seji tayi khamis yace " Baba wlhy duk cikin tsafine wayannan mutane naji ana fad'in ko gadin dasu keyi agida nku shekara da shekaru asirce iyayenku sukayi dama so suke Su k'wace muku sarauta kaga idan ta haihu in one way or the other d'anta ze gaje sarautar daga nan kuma kaga Su sun zama jinin sarauta,wlhy ai kawai karka yarda da wani kirsa nata kuna zuwa kamata k'azafin bin maza ka Turo da takardar saki uku awuce wurin tunda ba gyara,ni dazaka bi magana na ma ka saketan yanzu ka Adana takardar dakunje da wata d'aya ka sako Shegiya ka turota gida" nisawa Abdul yayi yace "Khamis zanbi sha'awararka amma dai se idan zan korotan zan rubuta" sallama sukayi khamis se murna yakeyi, da yamma sukace yawo cikin dare suka cira zuwa birnin London...... Had'adden gidan dabata tab'a ganin irinshi ba ya kaisu taga hadimai turawa se kira masa sir sukeyi ana gaidashi,ahaka ya nuna mata d'akinta ya barta nan,yana wuce dama rata ne bata samu ba ta ciro wayarta takira Aunty Husna,suna fara magana yana danno kanshi domin shigowa d'akin,da kukanta take magana "AUNTY Husna nashiga ukuna,wani abokin Abdul me suna khamis naso ya mayar dani k'aramar bazawara,wai cewa ya masa asiri mahaifina ke musu danta gaji sarauta wlhy Aunty Husna mahaifina ko mahaifiyata sabida gudun irin wannan ba wanda yakesan aurennan kurun biyayya suka yiwa me martaba sabida k'imarsa ya wuce haka sannan kuma ya mutuntasu shi baya kyamar talaka wa ko kad'an,ni wlhy banasan yaa Abdul kodan wulakancin daya kemun Amma banaso na zama bazawar karfi da yaji,wlhy Aunty bamu masa asiri ba, mezamuyi da mulkin da zamu mutu mu Barshi a duniya? Me iyayena suka nema suka rasa dazasu ce dole se jininsu yayi sarauta,nifa a ganina Kobata hanyar ba idan Allah ya kaddara ze faru" nisawa Husna tayi "Nasan da tashin hankali amma kiyi hakuri,da yardar Allah baze sakekiba,sanar dani in details me kikaji da kunnen ki?" Kwashe komai na wayar dataji sunayi ta fad'awa Husnah ta k'ara dacewar "Sanar wa Abdul ne kurun banyiba,tunda suka zo gidana yake yawan kirana wai in kwantar da hankalina shi idan Abdul bayaso ze aureki,nace ina ka samo number na,wai Abdul ne ya ajiye wayarsa be saniba ya kwasa,idan shi Abdul besan darajataba shi ya sani,wai nayita yiwa Abdul rashin kunya idan ma ya sakeni shi ze aureni" mamakine yacika husan tace "har yanzu yana kiranki?" "Nasaka number d'inshi a black list ai,haka kawai se inga kamar Abdul ne ya turoshi dama ni bansan meyake tunani ba akaina" jinjina kai Husnah tayi tace "Ki nutsu ki saurereni so yake ya kashe miki aure sabida shi ya aureki,ai Abdul bazeyi wannan gangancinba sabida haka ki san abinyi koda bakya sansa ki koyar dashi yanda ze soki,bazamu bari yaci galaba akanmu ba kinji,anjima da kaina zan kiraki in sanar miki hanyoyi masu sauqin bi" godiya tayiwa Husnah ta kashe ta zauna tana hawaye da kuka me d'an sauti tana magana "Allah ya isa khamis wlhy,inajin muryanka na gane Kaine tunkan ya ambaci sunanka,kazafin daka mun se anwa yarka wlhy" juyawa Abdul yayi yana mejin zafin abinda khamis ya masa aranshi yace Senayi uwar khamis kuwa wlhy,dama burinshi ya had'ani da momy tome na masa,Kodai zargi nane ya tabbata so yake na saki Elham yaa aura? Dama mana ranar se kallonta yakeyi kuma seyata matsayin akan zasuzo gidana,k'wafa yayi yashiga d'akin da sauri ta goge fuskarta tace tana murmushin yaqe "Yaa Abdul yanzu nake shirin kiranka,yunwa fa na nakeji" kamo hannunta yayi yace "Elham kukan me kikeyi daga zuwanmu" k'ura masa ido tayi tace "Inna da momy nake missing da gida gaba d'aya" tausayinta yaji ga k'uruciya ga damuwa yace " keda kike da yaa Abdul d'inki a kusa mezai dameki kuma?" Murmushi tamasa kurin ya sanya hannu yaja hancinta yace "Idan na kuma jin kukannan bulala zan miki" maqe kafad'a tayi "ehmm ni banasan bulala fa ko askul idan za'a dakeni kula nake tayi inankiran momy" Jan hannunta yayi "muje our food is ready".... Da dare zasu kwanta se tsoro takeji ita kad'ai a d'akin gashi wani irin qatoton d'aki ne,b'ingilalliyar riga ta saka iya cinya tazo parlor d'in ta zauna,kallonta yayi yana danna laptop yace " Elly dear baki kwanta ba?" Murmushi tamasa sannan tace "I'm scared" "Of what Elham?" Murgud'a baki tayi ta tsuke fuska "I mean the bed room is very big can't sleep in there me alone" Murmushi yayi yace "Muje na tayaki kwana a d'akin kinji?" Binshi tayi abaya ya kashe laptop din ya kashe side lamp, edge d'in gadon taje ta kwanta tanata takure wa shi dariya ma tabashi,sanda ya bari tayi bacci sannan ya janyota jikinshi.... Mom Nu'aiym [1/8, 10:32 PM] Sha'awa: *🌞HAFSAT ELHAM🌞* Billy Galadanchi Haske writer's Asso💡 Vote me on wattpad@68billygaladanchi. Sadaukar wa ga k'awata Hafsat Abubakar qaya (Elham). *wannan shafin nakine mom humaid* 14 Wuraren k'arfe uku na dare ta farka,mamakin take sanda tazo jikinshi har haka,fitsari takeso tayi amma ta kasa koda motsi sabida yanda d'imin jikinshi ke saukar mata da kasala,a hankali ta ce "Yaa Abdul ka d'aga ni ina so zanje bathroom ne" be motsa ba sanda ta maimaita so kusan uku sannan ya bud'e idonshi a hankali ya sakar mata lallausan Murmushi dukda acikin duhu suke,hannu yakai ya kunna side lamp dake d'akin sannan ya sake riqon daya mata yace "Sorry na hanaki tashi bacci ne yamun nauyi" Mik'ewa tayi kurun ta gyara gashinta daya yamutse taje toilet d'in tayi fitsarin ta dawo,zaune ta taddashi tace "Lapia dai yaa Abdul?" Murmushi ya sakar mata " Ai komai Nisan dare idan aka tashe ni bana iya komawa baccin " b'ata fuska tayi tace "Ohhsh Allah dana sani ban tashe kaba wlhy,yanzu haka zaka yita zama kenan??" Kishin gid'a yayi yace parlor zanje inyi kallo kawai" zaunawa tayi kusa dashi tace "To nima zan bika muyi kallon tare" "Noo plss karki damu,ki kwanta kiyi baccin ki kinji" mak'e kafad'a tayi "ehmm ni bazan kwanta d'inba zanje mu zauna tare kawai" Mik'ewa yayi yace "if u insist" Murmushi kurun tayi tabi bayanshi,Jennifer's diary yake kallo dai itad'ima zama tayi se dariya sukeyi sabida anata yin abin dariyar,bacci ne yafara fizgarta,ganin tana d'ingishi ya sanyashi dariya ya janyota jikinshi kanta ya datura akan cinyarshi yashiga Shafa lallausar sumanta "Kiyi bacci Hafsat,bacci kikeji naga alama" batayi musuba tashiga lumshe ido,har cikin ribs nata take receiving saqonnin dayake aika mata,a haka bacci barawo ya kwasheta,gogan shima a zaune yayi baccin basu suka farka ba se 7 wannan ma ita d'ince ta fara farkawa k'urawa fuskarsa ido tayi tana mamakin kyakyawar fuskarsa har acikin bacci,tana so ta tasheshi yayi sallah,taga alama ma kwanciyar na bashi wahala sosai sabida a saman kujera kanshi ya tafi sosai kasancewar a k'asa suke,tuna wa tayi da yanda Husnah ta koyar da ita yanda zatana tashin mijinta a bacci,Murmushi tayi aranta tace zan iya kuwa?? A hankali ta tashi daga jikinshi ta sanya hannunta tana Shafa kanshi a hankali,bud'e idonshi yayi ya sau kesu a kanta,da Murmushi ta tare shi tace "Kayi Latin sallah yaa Abdul ka tashi" Mik'ewa yayi a hankali batare da yayi magana yabar gurin, itama ta miqe tawuce d'akin ta,wanka tayi ta shirya tsaf cikin wata doguwar riga mara nauyi me santsi da kyawun gaske kalar sararin samaniya ta tufke gashin kanta a tsakiya tayi masa style na donut, ta feshe jikinta da turaruka dama gashi tayi wanka da ruwan miski se tashin k'amshi takeyi tako ina. Parlor tafito har wannan lokacin be dawo ba,se can ya shigo cikin Shiga ta kananun kaya riga da wando,wandon jeans blue sa shirt kalar sararin samaniya shima yayi kyau matuka se tashin k'amshi yakeyi,zama yayi kusa da ita yace yana mai janyo hannunta "Ur looking beautiful Elham" Murmushi tamasa tace "u too" hancinta ya d'an ja "ohh Really?" Langwab'e kanta tayi tace "yea Kayi kyau sosai,ko wurin budurwar ka ta nan k'asar zakaje?" Murmushi yamata yace "Ai itane zatazo karki damu da wannan" cikeda isa ya nuna wannan,gabanta ne ya yanke ya fad'i ta yi Murmushi tace "zanji dadi idan na ganta kuwa" kallonta kurun yayi ya mik'e ya bar wurin...... Rayuwa tayiwa Elham k'unci kasancewar tunda sukazo bata sake saka Abdul a idon taba tun kwanan farko, tsoro me tsanani ya shigeta,gashi se yan matan turawa masu masa aiki take gani suna kai kawo a part d'in shi,takuma tambayi d'aya daga cikinsu inda yake tace mata fitar asuba yakeyi ya dawo late,yau kusan kwananta shida kenan bata ganshi ba abinda ta rasa amma batajin dad'in rayuwarta sam!!! Ganin ya Shigo da sauri ta miqe taje gunshi "Yaa Abdul lapia kuwa? Kwana biyu bana ganinka?" Hannunshi ya sanya ya tureta yace cikin maye "Zaman uwarki nake a garinnan dazakice Sekin ganni kullum,wlhy ki Shiga taitayinki" zaro ido waje tayi jin muryarshi se a sannan ta kula da yanayinshi sarkace k'atuwa a wuyanshi da wando iya gwiwa daka ganshi kaga zararre kuma a buge yake,kafin tayi wani yunkuri ya fad'o ajikinta,tare shi tayi sannan cike da k'arfin hali taje ta kwantar dashi a d'akin shi,wannan ne karo na farko data fara Shiga d'akin kuma ya tsoratar da ita, ko ina kwalaben giya ne da kwalayen sigari,bata tab'a zato cewar yana aikata wannan mugun abin ba,tausayin momy ne ya kamata tace a sarari murya na rawa "Wlhy nikan nashiga uku na,ya Allah ka kawo mun agaji" anan ta durqushe ta rushe da kuka me ban tausayi,kome yasa takejin tausayin Abdul oho...Tunawa tayi da yanda akeyi cikin films idan mutum yasha giya da sauri ta Shiga toilet nashi ta dauko towel da ruwan sanyi masu ice tazo tana Shafa masa akai a hankali,sanda ta kula yafara sound and safe sleep sannan ta kwanta a kusa dashi taci gaba da kukanta,bata masan me take wa kukan ba,wani abu takeji me d'aci har cikin ranta a wannan lokacin,a haka bacci ya kwasheta,se yamma ya farka tsoron abinda yayi ne ya dawo masa akai ganinta ajikinshi ya tariyo masa komai,dafe kanshi yayi yana kuka me sauti wanda kukanne ya tasheta,k'ura masa ido tayi sanda yayi me isarsa sannan ta dafa kafadar shi tace "Yaa Abdul dan Allah ka dena kuka" jiyowa yayi ya kalleta da jajayen idonshi yace "Hafsat dan Allah ki yi hakuri kuma ki rufamun asiri karki gayawa Su momy,wlhy bana neman mata giyar ce kawai kuma zan dena I promise" k'ura masa idonta tayi se hawaye kasa cewa tayi da shi komai,ta zauna zaman kuka awurin,janyo ta yayi ajikinshi yace "Hafsat ki tallafi rayuwata na dena shan giya,wlhy ba laifi na bane,nace dasu banson sarautar nan nafi buk'atar rayuwata cikin kwanciyar hankali amma sun kasa ganewa wlhy Hafsat bana so,zumunci yaqi saidai tuwa sabida sarauta,d'an uwa na neman ran d'an uwansa sabida sarauta,inaso na auri Humaira sun hanani sabida munafuncin sarauta,yanzu sun k'ara rabani da Raihan sabida nasu ra'ayin,Elham ki yarda dani banida burin tarwatsa rayuwar ki shiya san ya na gujewa aurenki bansan kalar muguntar dazasu miki ba, karkema Su rabaki da farin ciki na har abada,Hafsat wlhy na rantse miki banaso ki Shiga damuwa akaina,Banso ko kad'an kika zama cikin wayanda zasu d'and'ana muguntar gidan sarautaba" kasa magana tayi ya d'ago kanta ya sanya duka hannayenshi ya d'ago kanta ta hanyar Saka lasu a cheeks nata ta fuskance shi "Hafsat ki yarda da zancena nafi shekaru biyar ina d'awainiya da sanki cikin raina,wlhy Humaira da Raihan duk badan sun zamemin dole nake san auren suba, sabida kurun sud'in yan gidana,I really don't wannan drag u and ur family in to this mess,naso sosai kiyi aurenki inda zaki huta,momy ta kasa fahimta na,akanki kisane kawai bazan iya ba wlhy bazan juri ana neman tab'ar b'are rayuwar ki ba,ki sani ina sane nake zaginki nacin zarafi sabida kawai ki ce bazaki aure niba dan kisamu freedom me dorewa,ko bayan auren mu danake zaginki dan kawai ki kasa daure wa ne kice bazaki zauna daniba ki huta,ban tab'a zaginki Nayi bacci ba wlhy Hafsat duk sanda naci zarafinki bana iya bacci, sabida bakin ciki ni kanji natsani kaina amma ya zanyi.Tsakanina dan iyayenki biyayya ce me tsafta ki binci kesu kiji,tun ranar da muka taho yau gobe nakejin wasu maganganu daga gida wayanda bazan jura ba,Hafsat zan sauwaqe miki sabida inasan ki dauwa ma a farin ciki badan komai ba,idan ba wannan hukuncin na yanke mana ba wlhy bazasu barki ba Hafsat,sannan kuma bazan tab'a yin bankwana da giya ba idan nace zan rayu dake kina shan wahala,kuma soyayyar kice Zata halla kar dani idan har ban rayu dake amma na sani bakya sona ni kuwa farin cikinki shine nawa,sabida haka zamu rabu Hafsat ki guji yan gidan sarauta,anmiki asara mafi muni a yanzu haka,zuwa next week zan maidaki gida" k'ura masa ido kurin tayi takasa koda k"wak'waran motsi,Mik'ewa yayi yaje ya bud'e wardrobe d'in sa ya d'auko takarda ya miqa mata takardar yace "karanta kigani Hafsat,kuma kar kiga laifina koku zargeni wlhy k'aunace sila,kuma koda kin koma gida dan Allah ki guji faruk wlhy har cikin raina nakejin wannan tab'in dayake wa jikinki" Mik'ewa tayi jikinta se rawa yakeyi ta kasa bud'e takardar illah kallonshi kawai da takeyi cikin rashin fahimtar zancensa, janyota yayi jikinshi ya rungumeta sosai ya saka wani razanannen kuka daya tayar mata da hankali...... Hmmm to wai jama'a meyake damun Abdul,abin zantuttukan hankali yakeyi kuwa? Anya tun farko bamu kasa fahimtar Abdul ba kuwa? Muje zuwa dai kuna tare da alkalamin mom Nu'aiym [1/8, 10:32 PM] Sha'awa: *🌞HAFSAT ELHAM🌞* Billy Galadanchi Haske writer's Asso💡 Vote me on wattpad@68billygaladanchi. Sadaukar wa ga k'awata Hafsat Abubakar qaya (Elham). *Nafi, wannan shafin nakine kyauta,so chill* 15 Zare rungumar daya mata tayi ta tallafi fuskarsa da tafin hannunta tace cikin sassauta murya da sigar rarrashi "Com down yaa Abdul,ur a man plss try to look as one mana" k'ura mata ido yayi duk da hawayen basu dena tsiyaya daga idon shiba,tace tana me k'ara saisaita fuskarshi da hannunta "Yaa Abdul plss be like a man kaji,kalle ni plss dena kukan haka" zaunar dashi tayi sannan ta sakashi jikin kafadarta a hankali take Shafa bayanshi tamkar wani jinjiri,dagowa yayi yace "Hafsat yau zan sanar abubuwa da dama wayanda baki san dasuba arayuwa ta" gyad'a masa kanta tayi alamar yaci gaba..... "Koda na taso naganni a gidan me girman gaske,a labarin danaji Kakanmu wanda ya haifi mahaifina kashe shi akayi ta hanyar yi masa yankan rago, yanada mata Su hudu da kuma yara manya maza Su takwas,se kuma mata Su goma sha uku....Akwai k'aninshi Muhammad shine kadai gareshi dan uwa mahaifinsu Su biyu kad'ai ya haifa,bayan rasuwar sa kasancewar Kakanmu shine Babba se aka bashi sarkin garin,wannan abin ba k'aramin tayarwa mahaifiyar Su Muhammad hankali yayi daga nan ta k'walla fa ranta akan se Muhammad yayi sarauta.....Kakanmu a cikin y'ay'anshi takwas dinnan maza mahaifina shine na shida mahaifin Su faruk shine na biyar, kafin rasuwar kakanmu kuwa ansha fama da Baba Muhammad da mahaifiyarshi daga k'arshe dai sukayi nasarar yi masa yankan rago wanda agaban idon mahaifina hakan ta faru shida kanshi ya sanar dani,bayan rasuwar sa aka gane Sune amma se mutane suka k'aryata hakan,daganan aka bashi sarautar,sauran kishiyoyin kakata kuwa suka d'auki masifar san sarauta suka d'aurawa akan yayan su,daganan me martaba kakana yabar baya da k'ura sabida sune suka kashe Baba Muhammad da Kansu, a wannan lokacin se abin yazama rigima domin kuwa duk wanda yahau sarautar se an kasheshi haka yayyun mahaifina sukayita rasuwa har akazo akan Baban faruk,shine ma ya jima akan sarautar domin kuwa tun muna yara shina taso na gani akan sarautar,zancen da nake miki wayanda fa ake kashewa har matansu da y'ay'ayensu bawai barinsu akeyiba indai kin haifi yaro namiji sedai kiji ance guba yasha idan mace tace Zata motsa ita d'inma a kasheta mututus.....gidan sarauta yazama wani iri domin yayyuna maza guda biyu sace su akayi haryau ba labarin su mahaifiyata duk sanda kikaga tana kunannan dakike damuwa idan tana yinsa yaranta take tunawa,an halakasu duk dan sabida Karsu tasa su gaji sarauta, Ana haka muna aji shida a secondary akayi murdering mahaifin su faruk ta hanyar poisoning d'in sa,wanda haryau ya haddasa rud'ani akan cewa mahaifina shine ya kashe shi,da kunnena naji mamansu faruk na cewa lallai idan nayi aure sedai duk sanda matata tayi ciki su zubar dashi ta hanyar tsafi bazasu tab'a bari na haihuba,sedai ko na gaji sarautar yayan faruk su gada,wannan dalilin ne yasanya na nemi auren Humaira yayar Raihan aka hanani daga baya kuma na nemi auren Raihan ita d'inma ban samu ba,Karfa ki Zata sabida ina sansu ne wlhy kurun sabida nasani bata yanda za'ayi uwa ta cutar da 'yar ta hasalima wlhy banasan tarbiyar yaran,nafara sanki ne tun kina jss 1,Nakuma t'aba sanar da momy ki binci keta kiji amma duk sanda na tuna cewar zasu lahantamun ke su wurgaki cikin halin da ba nakiba senaji bazan iya ba,ahaka na koyawa kaina yi miki kallo iri d'aya da feenah sabida haka na fara jin sassauci,dazaki tariyo farko kece babbr k'awata banida Aboki yar hira seke,tun sanda na fara ganinki da faruk na d'aura aure da giya sosai,nasani rashin ki masifa ne a gareni, Naso Raihan bazan miki k'aryaba amma wannan a rashin kine nasoma sabawa da ita, bayan rashin ki kuma yanzu me martaba ya matsa akan rashin lapiyarshi wai ze sauka ya bani ragamar mulki,Hafsat ko kinsan hallakaki zasuyi bazasu bari kiga k'wanki a duniya ba,bayan nasani Baba Hashim yasha wahala kafin samuwarki Harma ya cire rai da haihuwa kuma bayanki seda suka shekara biyar basu samu wata haihuwar ba,sunci ganin jikokinsu sannan kuma kece zaki basu kulawa,idan kika Shiga damuwa yaushe zaki kula da kanki ma bare su,a yanzu haka an shaida mun tun dawowarmu nan da kwana d'aya an kashe Amir k'anina kuma labari ya riskeni ance saura ni dake!!!!! Hafsat ki yarda da k'addara wannan takardar saki d'aya ne aciki dana miki sabida na tserar da rayuwar ki daga halla ka plss ki fahimceni" shiru tayi ta k'ura masa ido nakusan minti biyar wanda shima d'in ita yake kallo,hannunta ya riqo ta warce da sauri ta mik'e tsaye ta juya masa baya yau kukanma ta kasa yi,cikin d'acin murya tafara magana "Dukkanin hujjojinka ababen dubawa ne,amma anya ka tausa yamun daka mayar dani k'aramar bazawara? Da kasan kanaso kan kareki daga hannun su aiba seka wulank'anta mun rayuwa ba,akwai wulakncin dayafi ka mayar dani k'aramar bazawara? Baka da labarin idan Kayi imanin da Allah cewar babu wanda ya isa yamaka abinda Allah be makaba kuma kanada adua ba wanda ya isa ya maka wannan mugun abin,wlhy na yarda da dukkanin abinda ka fad'a amma wannan sakin dakamun ya nunamun cewar tsantsar k'iyayyace ba wani so dakake mun se shirin tarwatsa rayuwata,nakuma gode k'warai" tasowa yayi a rud'e ya riqo ta ta kwace kanta da sauri "Bakada labarin cewar ni ba matarka bace? Kuma banida iddar ka ayau na wanke tsaf daga kanka,idan gobe naso aure na zanyi,sabida haka wlhy kaji na rantse maka wlhy karka kuma tab'ani,kuma yanzunnan zan kira momy na sanar mata" da sauri ya kalleta yace "ki rufamun asiri Elham karki sanar mata,amma ki kirata kimata gaisuwar Ameer,dan Allah dan annabi karki sanar wa kowa" hararar tayi tana me jin tsantsar tsanar sa "So kakeyi na k'urawa kaina ido a gida koso kakeyi na tabbata ban sanar wa kowaba,kana nufin cewar banaso nayi aure,aure zanyi dama ai acikin d'inbin masoya ka d'aukoni Ba maqiya ba,so namaka alkawarin acikin watanni biyu kacal zanyi aurena kuma kowa sena sanarwa ka sakeni" magiya yashiga mata ita kuwa ta saka wani kuka me ban tausayi,tanajin zafin mutuwar Ameer sun shaqu sosai kwanciya tayi tana ambaton sunan Ameer tana kuka...... Kuyi hakuri da wannan yau ban samu zamaba Mom Nu'aiym [1/8, 10:32 PM] Sha'awa: *🌞HAFSAT ELHAM🌞* Billy Galadanchi Haske writer's Asso💡 Vote me on wattpad@68billygaladanchi. Sadaukar wa ga k'awata Hafsat Abubakar qaya (Elham). 17 Dangin Ibrahim kad'ai ake jira amma basu isoba,me martaba da kanshi yayi kiran sheikh Muhammad Adam,mahaifin Ibrahim amma abin mamaki se cewa yayi dashi "Ranka ya dade me martaba amin afuwar rashin kira,Allah yayiwa Ibrahim rasuwa yanzunnan,akan hanyar mu ta zuwa,kawai aman jini ya fara juyawar dazamuyi zuwa asibiti mafi kusa akace damu Allah ya karb'i abinsa,hankali nane ya d'auku dan Allah amana afuwa" Innalillahi wa Innah ilaihirraji'un" itace Kalmar da me martaba ya furta,"Ina rokon Allah ya jikanshi dan rahamarsa,inshaa Allah gobe zamu zo" godiya ya masa sukayi sallama,koda me martaba ya sanarwa mutane se al'ajabi ya kamasu,mahaifin Hafsat ne yace,Dan Allah tunda anrigada an tara mutane kuma dama mijinta na farko ya buk'aci koma warta dan Allah a d'aura dashi,k'anin me martaba ne yayi zumut yace "Da d'ina dakai Baba magadi haka iya had'iye kwad'a yinka,sarautar nan tunda ba gadar ta kayiba ai ka dena cusa jininka aciki ko?" Rayuwar me martaba ne yayi matukar b'aci dajin wannan zancen,mutane sun d'auki mutuwa ba'a bakin komaiba yanzunnan wani ya mutu amma basu da asara,lallai karshen duniya ne yazo,kallon Mahaifin Elham yayi yace "Ka wakilci ango nine wakilin Mamana" batare da b'ata lokaci ba aka d'aura auren.....kamar saukar aradu haka Elham taji sanda labarin mutuwar Ibrahim ya riske ta, Kuka kam ta shashi,amma tarasa dalilin daya sanya bataji zafi ba da aka mayarda aurenta da Yaa Yarima,da ita akaje gaisuwa har garin abj,yan uwan Ibrahim se kuka sukeyi musamman daya kasance mutuwar huji'a ce kamar daga sama,sosai suka bata tausayi ba kadan ba. *Bayan sati d'aya* Har akayi sati d'aya da d'aurin aure baisan inda kanshi yakeba,Elham kuwa duk tabi ta rame duk sanda aka barsu su biyu seta zauna tayita rusa uban kuka gani takeyi tamkar ze mutu ya barta ne,ranar wata alhamis ya fara kwara amai najini tamkar ranshi ze fita,ita kad'ai ce atare dashi tunawa tayi da yanda yan uwan Ibrahim ke bada labarin irin Amman dayazo masa nanjini nonstop kuma be tsayaba har sanda ya dauke sheda,rasa abinyi tayi da sauri taje ta d'auko alqur ani tafara karanta wa da k'arfi lokaci d'aya kuwa ya fara tsagaita aman,bata daka taba taci gaba da karatun sanda taga ya dena aman kwata kwata sannan ta ajiye alquranin tazo kusa dashi ta dafe k'irjinshi tafara tofa masa adu'o i kala kala na tsari,a hankali taga yana bud'e idonshi da sauri ta matsa kusa dashi tace "Sannu yaa Abdul ya jikinka?" Binta da ido yayi yana mata kallon rashin sani,adu'ar taci gaba da tofa masa har taga ya soma bacci cikin nutsuwar da tunda yafara wannan ciwon Bata gani a tare da shiba Mik'ewa tayi taje ta sanar da momy ta k'ara da cewar "momy me za'a hana akira malam uthman na meduguri se nakega abin kamar da iska aciki,dogon nazari momy tayi kan taje ta sanar wa me martaba,hakan kuwa akayi koda malamin yazo aljanai aka turowa Abdul a haka a haka akaso harya mutu,a binciken da malamin yayi wancen ma wanda ya mutu Wato Ibrahim shime same abune ya kashe shi kuma samu ne aka musu,amma Allah be bashi ikon gano wanda yayi wannan aikinba sedai ya bada adu'o I da kuma ruwan adu'a daze riqa sha kullum da du'oin da za'a masa dakuma wanda zena yiwa kanshi,Elham ce ta karb'i wayanda za'a na masa yayinda Abdul aka baiwa wayanda zeyiwa kanshi,gidansu aka maidasu na ainahin wanda tun farkon auren can suka fara zama..... Zaune yake tana bashi coffee abaki kasancewar har yanzu jikinshi be gama k'wariba yace yana kallon ta " Hafsat na gode sosai,na gode sosai Allah ya miki albarka,wlhy da baki dawo gareni ba nasani mutuwa zanyi" har Wannan lokacin hafsa bata gane komai ba game da son datakewa Abdul, kasancewar har gobe tanason faruk,wanna ya sanya ta sauya akalar zancen "Zakaci wani abinne?" Coffee dake hannunta ya karb'a ya a jiye sannan ya janyota jikinsa ya d'ago kanta ta fuskanceshi sannan yace "Ellyn yaa moris fushin ne haka har yanzu plss kiyi hakuri mana" k'uramasa ido kurun tayi batayi magana ba, batayi auneba taji bakinshi cikin nata taso sosai ta k'wace kanta amma ta kasa dole ta haqura,yafi minti biyu yana tsotsar bakinta,seda dan kanshi ya gaji ya saketa,da sauri ta sadda kanta k'asa sabida haka kurun taji wata kunya ta lullub'e ta,hannunshi yasa ya d'ago hab'arta yace yana Murmushi "Elham na kalle ni mana" duk'e kanta ta k'ara yi yana Murmushi yace "Kaddai kunya Elham na? Kiyi hakuri na dena miki I just couldn't take my ice off this fine lips of urs" batace komai ba ta tamik'e cikeda kunya ta bar wurin Murmushi yayi yana mamakin yanda yakewa Elham kallon wacce ta saba da maza amma wannan kiss kawai ta wani ji kunya Allah karya sanya zargin shi ya tabbata a kanta" zuwa tayi ta kwanta a bedroom nata,tarasa dalilin daya sanya ta kasa cire wannan moment d'in a ranta,da zaran ta tuna da yanayin da taji lokacin daya kama harshenta setaji wani Yarr har cikin ribs nata takejin wani feelings na shigarta,ba ita tabar cikin d'akin ba se la'asar kai tsaye kitchen ta wuce da sauri ta daura macaronie paper soup da beef souce, tana tsakiya da kwashewa yashigo bata saniba ta bayanta ya rungumeta ya daura hab'arsa sama wuyanta yace cikin wata siririyar murya "Elham na me kike girka mana,kika bar patient da yunwa har yamma Waike kunya ko? soon enough zanyi maganin wannan kunyar taki" kasa bashi ansa tayi ta lumshe ido ta bud'e su a hankali,janye jikinta tayi a hankali ta juyo amma bata bari sun had'a ido ba tace 'Kayi hakuri bacci ne ya sace ni" zagaye hannayenshi yayi a waist nata yace "Gwara daya dawo mun da Elham na,ba wanda ya isa ya sacemun ke" dariya maganar shi ta bata tayi Murmushi har hak'waranta suka bayyana gaba d'aya, d'an gyaran tsayuwa yayi still yana rik'e da waist nata yace "Elham na I'm hungry fa" hannayenta ta d'aura asaman nashi dake zagaye da waist nata ta langwab'e kai tace "To ka bani mintuna goma sha biyar yanzunnan zan kawo maka abincinka" saketa yayi ya juya bece ko maiba, a dining tayi serving nashi kuma tayi serving kanta,amma ga mamakinta yaqiyin koda loma d'aya ne da mamaki ta kalleshi duk yunwar dayake kira ya tasa abinci agaba yaqici "Yaa Abdul mesa bakacin abincinka ko baka son wannan naje na girka ma wani daban" kamar wani k'ank'anin yaro haka ya shagwabe "Ni bazan iya ci da kaina bafa" wani takaicin shi taji ya kamata amma a zahiri setayi Murmushi tace "Kona baka da kaina ne?" Murmushi yamata "Dama mana to waye ze bani?" Tasowa tayi ta zauna kujerar dake kusa dashi ta dinga ebar abincin tana bashi a baki cikeda nutsuwa dama mana maza ba kunya yakuwa hankad'e yayi narkar abinshi sanda ya k'oshi sannan ta koma taci nata... Da dare bayan ta shirya cikin rigar bacci mara nauyi tazo ta sameshi yana adu'a Sosa kanta ta d'anyi ta tsaya sanda ya idar,tasowa yayi ha zauna a bakin gadon tace dashi "Yaa Abdul ina so zanje na kwanta idan baka buqatar komai,na rigada na rufe ko ina na gidan" hannunshi ya saka ya janyota ta fad'a jikinshi kwantar da ita yayi akan gadon yaje daidai saitin kunnenta yace "Bana tunanin ina buqatar komai seke Elham na,yaya zaki tafi Kibarni ni kad'ai kin manta banida lapia?" Wani irin kasala ya saukar mata kasa cewa komai tayi har cikin b'argon ta takejin wani abu dabaza ta iya fassara ko meye ba,hannun shi yakai ya shafi mararta lokaci d'aya numfashin ta ya soma barazanar d'aukewa da sauri ta d'aura hannunta saman nashi se kuma ta soma kuka tace "Yaa Abdul dan Allah Kayi hakuri" hancinshi ya saka a saman nata yana gogawa a hankali batare daya janye hannunshi a saman marar tata ba,ita ma kuma ta kasa d'auke nata,sannan ya kai bakinshi wurin kunnenta yace "Menene yake sakaki kuka Elham na? Bakyaso nake zuwa kusa dakene ko me?" Cikin kukan tace "Nidai Kayi hakuri tsoro nake ji" sakinta yayi yaje kashe fitilar d'akin ya d'are kan gadon,janyota yayi sosai jikinshi ya lalubo bakinta yafara kissing nata passionately, kasa tureshi tayi kurin dai bata dena kukan ba,seda yagaji dan kanshi sannan ya pulling out,yace cikin sigar rarrashi hannunshi na saman kanta "Elham na menene? Bakyaso?" Gyad'a masa kanta tayi alamar e,janyota sosai yayi ya rad'a mata a kunne "To kiyi baccinki Na dena kinji,ko bakyason ki kwanta ajikin mijinki?" Banza ta masa yace "Ean Elham na bakyaso?" Cura fuskarta tayi acikin k'irjinshi duk da suna cikin duhu,cikeda shagwaba tace "To nidai ban ceba" Murmushi yayi ya k'ara k'ank'ameta a haka bacci me dad'in gaske yayi awon gaba da Dukkansu. Mom Nu'aiym [1/8, 10:32 PM] Sha'awa: *🌞HAFSAT ELHAM🌞* Billy Galadanchi Haske writer's Asso💡 Vote me on wattpad@68billygaladanchi. Sadaukar wa ga k'awata Hafsat Abubakar qaya (Elham). 16 Abdul kamma kuka ya saka ya zauna yana ta bata hakuri,dakinta ta koma ta k'ulle kanta,ta zauna tanata rusan uban kuka,tama rasa me zatayi,kiran momy tayi tayita kuka tamata ta'aziyar Ameer amma ta kasa gaya mata sakin da Abdul ya mata,bayan sun gama ta share hawayenta ta kira Aunty husna,komai sanda ta sanar mata,nisawa Aunty husna tayi tace "Kinga Elham,bazamu bari aurenki ya lalace haka a banza ba,karki kuskura kowa yaji wannan zancen, koda yace ze dawo dake karki yarda amma ki Barshi wlhy ze kawo kanshi ne,hujjojinshi basuyi karfin da zeyi wasa da saki har Hakaba,duk da yake yanada ban tausayi amma wlhy bazamu aminta ya lalata rayuwar kiba,yanzu ki nutsu Elham saki akwai ciwo ba kad'an ba, kuyita hakuri Koda yace ki dawo Nigeria karki yadda,ki roqa a sama miki makaranta anan" shiru tayi sabida tanaji wannan karon bazata bi zancen Aunty Husna ba kuma sam tama tsani ganin Abdul,se can tace "Aunty Husna nifa wlhy na tsaneshi bana san a gyara auren,ni sena sanar wa momy" sassauta murya husna tayi cikeda rarrashi "Haba Elham Karki yiwa momy haka mana,kinsan yanda take k'aunarki d'innan Zata iya yanke jiki ta fad'i ga kuma an mata mutuwar Ameer na damunta,dan Allah na rok'eki ki gyara aurenki da kanki batare da sanin kowa ba" nisawa tayi tace "Idan haka ne Aunty ina da shawara" "To ina jinki Hafsat" daga nan ta zayyane mata komai yanda take ganin za'ayi dashi,ta k'ara da cewar "Aunty wannan ne kad'ai hanyar danike ganin zamu bi,Abdul be kyauta wa kanshi ba aganina kuma beyi jarumta ba amaimakon yayi jarumta ya nemi mafita seya sakarwa yan uwansa ragamar rayuwar sa gaba d'aya" "To Elham ina fatan Allah ya sanya wannan tsarin namu yayi working kinji" sallama sukayi ta ajiye wayar cike da bacin rai,har kusan kwana ki biyar bata k'ara ganin Abdul a gidan ba da wannan take tunanin bata yanda za'ayi plan nasu yayi working,a maimakon ta kira Husnah,kurun se fushin zuciya ya d'ebeta ta kira momy ta saka mata kuka,cikeda wauta ta gaya mata komai tsaf daya faru,B'acin rai me tsanani ya ziyarci momy,rayuwarta ta b'aci,bak'in ciki ya lullub'e ta hankalinta ya tashi,kuka kawai ta saka ta kashe wayar,a fusace ta kira Number d'inshi..... Yana office zaune yana tunanin yanda zeyi da Elham so yakeyi yace ze maida aurenta amma yasani bazata aminta dashiba,yana tunanin yanda zeyi rayuwa batare da Elham ba,yanzu ya haqiqancewa kansa rayuwarshi batada wani amfani idan ba Elham,Mema zesa yayi wannan tunanin har ya biyewa san zuciyarsa ya saketa,yana tsakiya da wannan tunanin wayarsa ya soma ringing, gabanshi ne yayi mummunan fad'uwa ganin sunan momy domin kuwa basufi awanni biyu da gama wayar ba,yakuma sani banza bata kai zomo kasuwa,jiki a mace ya d'aga wayar.... "Baba na na gode da abinda ka sakamun dashi na sakar mun mama na da Kayi, ka mayar mun da ita k'aramar bazawara,ka tozar tar dani,baka dubi halin rashin Ameer danake ciki ba ka sakar mun yarinya,me kake so nace da iyayenta? Wlhy ka wulakanta ni fiye da tunaninka,kuma ka sani sena rama da yardar Allah Mamana Zata auri miji wanda ya fika lallai ka Turo mun ita as soon as possible sabida ta sanar dani ba iddar ka a kanta zamanku tare yanzu had'arine Babba ba k'arami ba" kafin yayi magana ta kashe wayar koda ya kuma kira wayarta a kashe gashi feenah bata gida yanzu bare ya kira ta bata,dafe kanshi yayi yata kuka tamkar k'aramin yaro,seda yayi me isarsa sannan ya tashi zuwa gida,d'akin Elham ya wuce kai tsaye ya tarar ta idar da sallah tana adua zama yayi harta idar,juyowa tayi ta kalleshi ta d'auke kanta "Hafsat mesa kika mun haka? Mesa zaki zab'i had'ani da mahaifiyata? Menene ban miki ba a rayuwa? Sabida kawai ki dauwama a farin ciki na sadaukar da nawa farin cikin,Ashe ban cancanci ki rufa min asiriba? Bayaga haka na gama yanke hukuncin zan kama aure na,Mesa bazaki fara tambaya na tsarin dana mana ba" wani mugun kallo ta wurga masa tace a fusace "Wlhy Kayi kad'an na kuma zama matar har abada,da kake zancen kama aurenka sekace wata tinkiya kokuma dabba,bakada labarin cewar Na gama idda,dole ne se an sake daura mana aure,kuma bana buk'atar k'arasa rayuwata da ragon namiji,mutumin daze bar ragamar gidansu ta lalace sabida rashin lissafi,aure na ya kare dakai har abada,banida iddar ka kuma Baba me gadi ya kaini islamiyyah,an sanar dani cewar idan idda ta yanke baza'a k'ara komawa aure ba se an d'aura kuma da waninka zan d'aura bada kaiba,na gama dakai har abada" duk girma irin na Abdul kasa daure wa yayi ya saka kuka "Elham wlhy bazan iya rayuwa batare dake ba,kuskure ne nayi kuma na gane kuskurene plss give me a second chance" dariya ta kwashe dashi "Off course I can give u one big another chance to destroy my life" matsawa yayi kusa da ita yace "Ba haka bane Elham,wlhy kece rayuwata gaba d'aya, banajin zan iya rayuwa baki" ka tayi magana wayarta ya soma ringing, dauka tayi taga yaa Ibrahim ne,d'agawa kurin tayi,t wani shagwabe murya "Yaa Ibrahim dan Allah fa tun yaushe na kiraka shine se yanzu kake kirana?" Daga d'aya bangaren kuma Murmushi yayi najin dad'i yace "Kiyi hakuri Rose kinji,inata aiki ne yanzunnan na shigo gida go lunch ban ciba" K'ara langwab'e murya tayi tace "Yaa Ibrahim kai kuwa seka riqa wani tunamun da yaa faruk na,shine yake kirana da Rose" Murmushi yayi shi yakasa gane kan Elham yanzu kuma tace dashi wai aurenta ya mutu,kuma batada Idda dama auren dole akayiwa dukkansu "Ehn love one tintin Kodai yanzu da yaa faruk za'ayi aurenne?" Dukda tasan cewar Abdul bawai yana jiyo me Ibrahim ke cewa bane,amma seta tsinci bakinta da furta Kalmar "Bazan kuma aure a gidan sarauta ba,indai yaa faruk ne na hak'ura gaba d'aya, kawai dai sunanne yake zuwarmun da good memories damuka kasance a tare,he's such a nice person,nasan da ace Shina aura,da Banyi zaman zawarcin k'uruciya ba a yanzu,baze tab'a saki naba sabida yana sona sosai" "To kiyi hakuri wata rana se labari,idan na kammala abinda nake zanyi kiranki" sallama sukayi ta wuce bathroom kai tsaye tana me jin zafin yanda zuciyarta keso ta bata kunya akan Abdul,mesa takejin tausayin sa ne?" Wannan itace tambayar data kasa samun amsarta tuni..... Juyin duniya Abdul yayi amma Elham takasa bashi fuska,hasalima zagine ke Shiga tsakaninsu,a haka a rikice ya dakatar da duk abinda yakeyi ya kwaso ta suka dawo Niger....... Zagi na wulakanci momy ta masa,yashiga magiya amma fir taqi saura rarsa,iyayenta sunyi bak'in cikin wannan wulakncin sedai wannan karon a wurin momy ta dawo da zama gaba d'aya,d'akin feenah shine ya zama nata,hankalin Abdul be kara tashiba seda yaga har me martaba Fushi yake dashi, shirya wa yayi yaje fadar me martaba,a durk'ushe yake agaban me martaba yana kwasar gaisuwa,daga gaisuwar kuwa me martaba yamata banza,seda ya raina kanshi sannan yace "Abba dama nazone akan zancen Hafsat,dan Allah a taimaka a dawo mun da ita,tunda saki daya ne,Inshaa Allah,wannan kuskuren baze sake faruwa ba" yafi mintuna sha biyar da gama magana me martaba be kulashiba,ga bahalin cewa komai,se can yace "Ina so kasani,mahaifiyata Hafsat ta kasance me rauni tun kafin zuwan tsufanta kasancewar batada lapia ko kadan,mahaifiyar Elham itace ke d'awainiya da ita kasancewar a b'angarenmu bamuda macen dazata kula da ita,bata tab'a gaji yawa da kulawa da itaba kazalika bata tab'a karb'ar sisin kwabon mu na ladan d'awainiyar da take da ita ba, alokacin datake fama da matsananciyar rashin lapiya Asabe baro mijinta take ta dawo ta kwana a wurinta,itace da kanta ta samo mata maganin hausan datayi ta sha harta samu lapiya,tafara tafiya bayan tayi shekaru takwas bata taka k'afafuwanta,sabida yaa d'aukar Mahaifiya ta matsayin mahaifiyarta tana haihuwa ta sakawa yarta suna Hafsat!!! Yarinyar da shekara da shekaru Allah be basu haihuwaba se daga bisani suka haifeta,soyayya me tsanani mahaifiyata keyiwa Elham wanda wannan shaida ne kowa yasani" "shiru yayi yad'anja fasali sannan yaci gaba " Anya Abdurrahman kayiwa Mamana adalci daka saketa da k'uruciya? Bakada labarin matsalar da wannan sakin ya jamun awurin Mahaifiyata akan na bada auren takwararta akan mijin dabe dace da ita ba? To ka sani gangan cin danayi abaya bazan k'ara maimaita irinshi ba har abada,Elham ta kawo mana yaron dazata aura me suna Ibrahim kuma mun bashi aurenta nanda sati biyu masu zuwa" zabura yayi tamkar wanda aka tsikara ya saka kuka agaban mahaifinshi "Dan Allah Abba kamun rai,na rokeku kubani wata damar nayi alkawarin zan gyara kura kuraina,na baya,zan kula da ita zan rayu da ita cikin Aminci" Murmushi me martaba yayi irinna manya yace "Abdurrahman ka rigada kafara haduwa da darasin rayuwa, da wannan zakasan muhimmancin tunani me zurfi kafin yanke ko wane irin hukunci" da kuka yabar wurin..... Sanye take da doguwar rigar less ash color tayi rolling da red d'in mayafi,fuskar nan tasha makeup tamkar babu abinda ke damunta,nan kuwa tunanin Abdul ya tayar mata da hankali matuka,tarasa nutsuwar ta gashi sam ta gayya ta gayyato Ibrahim a rayuwar ta bata taba zaton cewar ze gabatar da kanshi da sauri har hakaba, Dukda bata sonshi, amma a yanda Abdul ya wulakanta ta Zata koyawa kanta san Ibrahim ko yaya ne......kamar wanda k'wai ya fashewa aciki haka yake tafiya,a garden yazo ya sameta zauna kusa da ita,waigowa tayi ta kalleshi ta d'auke kanta gaba d'aya,cikin sanyi murya ya furta "Hafsat zuwa nayi muyi magana akan zancen aurenki da naji,dan Allah ki taimakamun karki barni" wani malala cin Murmushi tayi tace "Kamar yanda Kayi dogon nazari akan sakina kafin ka sakeni,haka nayi dogon nazari akan auren masoyina Na haqiqa,Abdul bakada hurumin dazakace wai na fasa auren shaqiqina na dawo hannun wanda bema san darajar iyaye na ba,inaso idan mafarki kakeyi toka farka,sabida bazan tab'a auren kaba" k'ura mata idonshi yayi da suka sauya launi zuwa jajaye yace murya na rawa "Hafsat nasani ban miki adalci ba ko kadan,kuma ban isa in hanaki komaiba,nasani wannan hukuncin dakika yankemun Na cancanci wanda yafishi,zan miki fatan alkhairi idan har kika zab'i yin hakan amma wlhy duk halin dana Shiga kece sila,mutuwa zanyi ada na hakura dakene sabida wasu yan dalilai,yanzu kuwa bayan munyi aure mun rabu na fahimci kece rayuwata tsaf zan mutu idan nayi rashin ki my Elly,ina miki....se kuma tari ya sarqeshi janyo handkerchief yayi ya tare wanda atake ya soma aman jini,gigicewa Elham tayi ganin wannan tashin hankali tazo ta riqeshi " Yaa Abdul Sannu,meke faruwa da kaine? Aman jini na Shiga uku " ganin fa be kulata ba kuma gashi se aman yakeyi ya matukar tayar da hankalinta,a rikice taje part d'in momy ta sanar mata,a tare sukazo aka kwashe shi zuwa asibiti Elham se kuka takeyi wanda ita kanta bata san kona meye ba,tsoro takeji karta rasa yaa Abdul d'inta wannan aman jini idan yayi irin shi so biyu toko tabbas tsaf mutuwa zeyi dominnko ba abinda ze hana wa jininshi tsiyayewa ta tas.....abin mamakin kuwa shine yanda doctors suka tabbatar musu cewar lallai daga zuciyarshi har b'angaren ulcer lapiyarshi qalau,me martaba be yadda ba yasanya aka masa general check up nan ma Lapiyar shi qalau.....haka ya shafe kwana ki goma cur besan inda kanshi yake ba idan kuma yasoma aman jini baya tsayawa seya kusa amayar da yayayen hanjinshi,Elham ita kad'ai setaje d'akinta tayita kuka daba tasan dalilin shiba,Gashi me martaba yace aurenta ba fashi sora kwana ki 4 tunda ba biki za'ayiba daurin aurena kawai kuma Abdul bashi bane angon kazalika ba waliyinta bane da har za'ace ajira warkewarsa,a yanzu an dawo dashi gida sabida likitoci basu gane komai ba,inda ake zargin asiri aka masa,momy dukta ya mutse ba itaba ba Elham ba,a haka ranar d'aurin aure tazo ba amarshi haka aka gangama daurin auren...... Mom Nu'aiym [1/8, 10:32 PM] Sha'awa: *🌞HAFSAT ELHAM🌞* Billy Galadanchi Haske writer's Asso💡 Vote me on wattpad@68billygaladanchi. Sadaukar wa ga k'awata Hafsat Abubakar qaya (Elham). 18 Tun asuba ta farka taga baya nan,ga alama ma sallaci yaje ita d'inma sallah taje tayi,ta wuce kitchen kai tsaye ta d'aura musu egeg yam with beef paper soup, ba jimawa ta kammala ta hada masa coffee ita kuma ta had'a kayan tea nata ,a dining ta Jere komai ta wuce toilet kai tsaye tana idar wa ta fito ta shafe jikinta da mai tafara sanya sure spray follewed by body splash nata,ta bayanta ya rungumota ta na tsaye ajikin mirror d'in rufe idonta tayi jin saukar hannunshi saman breast nata, dukda a saman towel ne seda taji wani yarrrr,bata gane menene yake mata yawo a duk sanda ya rab'eta irin haka,jikinta ta janye da sauri ta sadda kanta k'asa,hannunta ya janyo ta dawo jikinshi ya manna mata hot kiss a wuya yace "Elham na,ina kika Shiga ina ta nemanki?" Murmushi tamasa "Ina kitchen ne ina had'a breakfast" "Dama yunwa ya addabeni oya saka kaya da sauri muje muyi break fast d'in" yaudai Hafsatu kasa koda motsi tayi bazata iya saka kaya a gabanshi ba,kallonta yayi ganin tayi tsaye ta sunkuyar dakai "Bakiji ba nace ki shirya mu tafi ko" d'an ya tsanta ta saka a baki tace "Yaa Abdul ka bani wuri to mana,zan sameka a dining d'in" Murmushi yayi ya fice batare da yayi magana ba,yau ma sanda ta bashi abincin yaci sannan suka dawo parlor a saman cin yarta ya d'aura kanshi shi adole wai ga mara lapia, ita kuwa kunyarshi take ji matuka yanzu...... Tun da safe Hafsat ke fama da wani matsanan cin ciwon kai amma bata sanar masa ba da rana ma haka ta daure ta girka masu spaghetti da miyar Hanta kurun se ice tea, zuwa yamma kam Hafsat jiki ya tsananta domin kuwa kasa yin girki tayi,Shikuwa baya gidan yaje ya gaisa da mahaifanshi kasancewar jikinshi yayi k'wari.....sosai momy taji dad'in ganinshi agidan Ras da shi tace "Mamana fa? Ina fatar tana lapia?" D'an Sosa kunne yayi yace "Tana nan lapia lau momy tace ma na gaidaki ai" Murmushi tayi "To Babana kadaiji tsoron Allah ka kula da yar mutane tsakanin ka da Allah dan Allah na rokeka karka kuskura ka wula kanta musu 'ya,sunmaka halacci sosai" "Inshaa Allah momy zan kiyaye komai da kika ce zan kula da ita" al Barka ta zabga masa ya tashi ya fita......Koda ya dawo Elham bata parlor kuma yaje kitchen bata nan,kai tsaye bedroom nata wuce ya tarar ta k'udundune a bargo se rawar sanyi takeyi,da sauri ya Hau saman gadon ya d'an yaye duvet d'in "Hafsat lapia dai meya sameki?" Kasa bashi ansa tayi kurin dai taci gaba da zubar da zafafan hawaye,dagota yayi ya d'aura ta saman cinyarshi yaji jikinta zafi rau "Hafsat plss Sanar dani meyake damunki haka,jikinki zafi fa sosai" dak'yar ta iya cewa "Kainane yakemun masifar ciwo sarawa yakeyi tamkar ze rab'e gida biyu" kan ya kama yaji zafi rau yace "subhanallah Elly tashi muje asibiti,bazan barki gida da zazzabi haka ba gaskia" kasa cewa dashi komai tayi da kanshi ya saka mata doguwar riga ya kinkimeta se asibiti, zazzab'in cizon sauro ne ke damunta aka mata aluurai aka bata magunguna suka dawo gida abinsu,salar isha ma dak'yar tayi tayita ya samu tasha tea kawai suka koma d'aki suka kwanta,janyota sosai ajikinshi ya rungumeta yanata rarrashi nta se hawaye kurun takeyi sabida ita kad'ai tasan yanda kanta ke masifar Sara mata,har bacci ya d'aukeshi ita bata rutsa ba,can Wuraren karfe ukun dare kukanta ya tasheshi,"Hafsat har yanzu kanne?" Cikin kuka tace "yaa Abdul dan Allah ka k'ananun kaina ciwo yakemun sosai wlhy,kuma ka matsamun k'afana suma suna mun nauyi saramun komai yakeyi" haka ya tashi yamata kamun kai yashiga mata tausa sosai har jikinta ya sauka atake ta fara had'a gumi se bacci me nauyi yayi awon gaba da ita,adu'a yashiga yi mata seda yaji ana kiran Sallar asuba sannan fa yaje yayi alwala a d'akin yayi sallah sannan yaje ya soya kwai da plantain ya hada ruwan zafi,koda ya dawo d'akin ta farka amma bata tashi ba,hawa saman gadon yayi ya tab'a jikinta yaji ba zafi "Sannu Hafsat Kindai ji sauqi ko?" Murmushi ta sakar masa tace "Naji sauki sosai,amma daga kwance ina ganin jiri" "So nake namiki wanka sekici breakfast naki" zaro ido tayi waje tace "Allah ni zanyi da kaina" cikeda shagwab'a tayi wannan furucin har tana shura k'afa,be tsaya wani gaddama da itaba ya fara cire mata kaya jikinta yanayin yanda take jujjuya jikinta ne yafi tafiya da imaninsa tsirara ya mata sannan ya d'aga ta cak ya nufi ban d'akin da ita,acikin bahon wankan ya tsunduma ta ya sab'e ta tatas,se sussune kanta takeyi,da kanshi ya Shafa mata mai ya saka mata kaya ya daga ta se dining,shine ya bata abincin sanda ta k'oshi sannan ya ci Nasa,bayan sun dawo parlor se tausa yake mata tun tana lumshe ido har bacci b'arawo ya saceta se farkawa tayi ta ganta a cikin faffad'an girjinshi me cike da gargasa suna baccin a tare,kasa motsi tayi karta tada shi ta koma ta kwanta..... *Bayan sati Biyu* Jikin hafsat ya tsananta matuka,tasha maganin malaria kala kala amma duk a banza ciwon kai ne ya sakata a gaba babu k'auk'utawa,ganin haka momy ta kaita private hospital, duk ta rame tayi bak'i sabida azabar ciwon kai ko idonta bata iya d'agawa gwajin farko suka gano tana d'auke da cikin sati uku!!!!!! Agaban momy suka zo sukace da Abdul"Congratulations sir,ur wife is 3 weeks pregnant, Baza kuga daidai ajikinta ba se ta wuce trimester d'inta so se hakuri zamu bata magungunan dazasu taima kawa ita kanta da cikin dake jikinta" mutuwar tsaye Abdul yayi dagashi had Elham d'in yayinda momy se murna takeyi 'yarta nada ciki,Zata samu jika dama gashi feenah haryau shiru!!!!!!! Kai tsaye gidansu yace a amai dasu ze kula da ita,hakan kuwa akayi can aka sau kesu, Elham har lokacin kuka takeyi magungunan da aka bata ma watsar wa tayi, tarasa Inda Zata saka rayuwarta taji sauqi,a take ma taji ta tsani kanta tama kasa tunanin daya dace tayi, a d'akinshi taje ta taraddashi a zaune tana kuka ta duqa kusa dashi tace "Yaa Abdul wlhy summa tallahi ka yarda dani ba namijin daya tab'a sanina a 'ya mace,dan Allah Kayi hakuri" wata muguwar harara ya fara sakar mata sannan yace "A ruwa kika sha cikin dan kutmar uba? Wannan shine sakayyar soyayyar danake miki Hafsat? K'iyayyar daki kemun har takai matsayin da Zakije kiyi zina da aurena akanki? Wato sanda aka daura auren mu banida lapiya maza kikaje kina bi ko? Dukdan sabida bakya sona,cikinki sati uku ya nnuna cewar kinada igiyoyina akanki kikaje kina watsewarki da wanina,Allah ya isa ban yafe miki ba wlhy" kukan tane ya tsananta tace murya na rawa "Wlhy na rantse maka yaa Abdul bansan komai ba game da wannan cikin,ban tab'a aikata zinaba tun ina gidanmu balanta na kuma da aurena" shaqo wuyanta yayi yace "Baki tab'a zinaba a ina kika samo wannan d'an shegen? Wlhy Sekin sanar mun waye ubansa,sabida kinsan bazan iya gayawa momy da duniya abinda Ki kayiba shine yasanya kika zabi tozartar dani har haka Elham?" Sakinta yayi ta fadi cikin d'acin rai ya soma kukan shima,yana sambatu "Wlhy Hafsat ina masifar sanki,mutuwa zanyi idan ban rayu dakeba amma ya zanyi da wannan bak'in cikin da kika sakani? Allah ya isa wlhy bazan tab'a yafe miki ba" da gudu tabar sashinsa tana rusa uban kuka.... *Bayan sati uku* Hafsat har wannan lokacin bata samu lapiya ba,ciwon kai yaqi ci yaqi cinyewa,gashi batashan koda paracetamol ne,ta d'auki damuwa me tsanani ta saka a ranta,a d'akinta yashigo ya sameta tana aikin kukan data saba,kusan kwana ki biyu bata ganinshi,zama yayi kusa da ita yace "Hafsat ki sassauta wa rayuwar ki wannan kukan dakikeyi dazaki sanar dani waye uban d'annan data fiye miki" cikin d'acin rai ta d'ago ta kalleshi tace "shed'an shine uban d'annan ni banida bakin dazan iya kare kaina dashi awurinka amma ina rokonka dan Allah karka ce zakayi ta shan giya yanda naga kanayi wlhy zaka illata Lapiyar ka ne yaa Abdul,nfa daka gannin nan wlhy mutuwa zanyi,babu wanda ze yadda dani to meye amfanin rayuwata a yanzu?" K'ura mata ido yayi na y'an dak'ik'u kan ya tashi yabar wurin gaba daya..... A buge yashigo cikin gidan yana tafe yana maye,tareshi tayi tace dashi "Yaa Abdul wai dan Allah bazaka dena shan giyar nan haka nan ba? Haramun ne fa,kuma sarai ka sani wlhy" wanketa yayi da wani kyakyawan mari sannan ya Hau jibgarta baji Ba gani,tun tana iya motsi harta kasa,shurinta yakeyi tamkar ba gobe,dukya fasa mata baki da hanci se jini sukeyi sanda ya gaji sannan ya qyaleta ya wuce d'akinshi.... Dakyar ta rarrafa d'akinta takira momy,tana dagawa tace da ita "Momy dan Allah Kizo ki taimakeni yaa Abdul ze kashe ni?" Cikin rudu momy tace "ze kashe ki kamarya Elham?" Tana k'ok'arin yin magana kawai taji bata iya numfashi Athma d'inta ya taso mata gadan gadan,anan ta zube a sume..... Mom Nu'aiym [1/8, 10:32 PM] Sha'awa: *🌞HAFSAT ELHAM🌞* Billy Galadanchi Haske writer's Asso💡 Vote me on wattpad@68billygaladanchi. Sadaukar wa ga k'awata Hafsat Abubakar qaya (Elham).                            19 Dashi suka fara cin ka fito daga bed room d'inshi cikin halin maye,cikeda rud'u tace dashi "kai Babana Lapiyar ka kuwa? Meka wa yar mutane kuma meye haka kamar wanda yasha giya" dariya yayi irinta wanda yasha ya bugu yace "Momy ke bakya ganine Yarinyar nan tunda na aureta ban taba kwanciyar aure da itaba,yama za'ayi tace wai tana da ciki uban waye ma uban d'an?" Momy bata gare inda ya dosa ba,ta d'aura maganga nunshi a mizanin wanda yake cikin maye,tasan yanashan giya amma sam batayi tsamanin har yanzu be dena ba,wuceshi tai zuwa d'akin Elham acan ta tadda ta bata numfashi,aikam kinki mota tayi zuwa mota,ado driver yaja suka tai bata k'ara komawa takan Abdul ba abin duniya ya isheta yaronta ya daura aure da giya kuma kana kallon Elham kasan cewar dukan tsiya tasha abinma da kunya taje tana fada, A asibitin data kaita farko yauma can suka nufa,da sauri suka k'arbeta daura mata oxygen sukayi sanda ta farfado sannan suka bata test kala kala,ganin yanda duk tayi rama,bin cikensu ya nuna masu cewar typhoid ce tayi mata mummunan kamu,kuma itace take sakata wannan ciwon kan me tsanani,magunguna suka rubuta,suna zuwa zasu bata momy ta dakatar da doctor d'in tace "Dr magungunan nan basu mata k'arfi ba kuwa naga cikin nata beje ko ina ba k'arami ne" da mamaki doctor d'in ya kalleta yace "Ai dukkanin test sanda mukayi da muka dauki sample na blood nata,batada ciki fa" wani kallo da bazaka fassara wane iri bane momy tawa doctor din "wane irin zance ne wanan doctor sid? Baku bane last week bin ci kenku ya nuna tana da cikin sati uku?" Mik'ewa tsayi yayi ya duba file d'inta,abinda ya fad'o masa arai shine case dasuka gama solving jiya jiyannan akan wata Hafsat Elham Hashim, dafe kanshi yayi yamayar da dubanshi zuwaga khabbab yace "Dr khabbab I think she's the one,zo kaga sunan Hafsat Elham Hashim" matsowa Dr yayi yace "off course she's the one" mayarda dubanshi yayi zuwaga momy yace "Yaune muke shirin bin bayanku ta hanyar address dinku kasancewar tun jiya muke kiran wayar mijinta bama samu,wlhy wrong result aka baku,an samu kuskuren sunane yazo iri d'aya sak dana wata ita tana fama da matsalar ciki yayinda wannan ke fama da typhoid a matakinta na karshe a cutar da mutum,kunsan nan asibitin private ne lab d'inmu d'ayane dan Allah Kuyi mana afuwa,ita kanta waccen wlhy zuwa akayi da ita ta samu miscarriage seda mukayi bincike muka gano cewar magungunan typhoid ne suka mata nauyi,dan Allah kumana afuwa,ita d'inma se jiya tazo,kuma muna ganewa mu kaita neman layin mijin wannan amma be jeba" kuka Hafsat ta saka jin wannan maganar wanda shi ya hana momy zazzagawa drs d'in masifa iya son ranta,ta juyo ta rungume Hafsat tace "kiyi hakuri Hafsat inshaa Allah zaki samu wani me albarka" momy batasan Hafsat kukan dad'i takeyiba Allah ya wanketa,amma bata ce da ita komaiba,anan asibitin ta kwana yayinda momy ta koma gida ta Turo kanwar Hafsat d'in domin ta zauna da ita a asibitin.....da safe da kanta tayi kiran Abdul yaje ya sameta gida,cikeda nutsuwa ta kalleshi sannan ta kurb'i fresh milk dake hannunta tace "Babana na sani yaqi da rayuwa abune me matukar wahala amma shin kanada tabbacin wannan abin daka d'aukar wa kanka shine mafita? Baka ganin cewar idan kana sab'awa ubangijin ka har haka baze karb'i adu'ar kaba,kaida nake kallon Kaine zaka kawo sauyi a wannan masarautar shine zaka b'ige da aikata wannan mummunan barnar to Babana bazan maka fad'aba Nasiha ce nake maka akan kaji tsoron Allah abu na gaba kuma shine ina so ka d'auki k'addara,matarka daka narkewa k'oshi tana asibiti a kwance batada lapia typhoid ne ya matukar ci zarafin ta,wannan cikin damukewa murna da d'auki Ashe batada ciki,mistk din result din sukayi,suka bamu na wata Hafsat daban banita kasance war sure name nasu da sunan yazo iri d'aya,ita kuwa waccen suka bata na Hafsat wanda magungunan sukayi sanadiyar barar ma waccen baiwar Allah da ciki,anbata magungunan typhoid alhalin ciki ne da ita,kuma sse jiya suka sani,suce sunyita neman wayarka basu samu ba sunso sanar maka tun jiya" da sauri ya d'ago ya kalleta,lokaci d'aya k'irjinshi ya bala'in dokawa idonshi suka sauya launi zuwa ja sosai,ita uwa jin yayi shiru ta qara da cewar ."Abu na karshe da zan fad'a maka shine ko bayan Hafsat idan ka k'ara auren wata mata nan gaba ban yafe maka ba idan har ka daketa,karka kuma dukan mace wannan haline na la'antattun maza be kama cekaba wlhy ko kad'an se'a kiyaye,maza katashi kaje ka dubata ga abincin su can na break fast ka wuce musu dashi " kasa magana yayi sam, a haka ya mik'e jiki ba k'wari yabar gidan koda ya Shiga mota zama yayi ya dinga tariyo zan tuttukan momy se kurun ya fashe da kuka sanda yayi me isarsa sannan ya zaro wayarsa yakira zayyan, fayyace masa komai yayi ya qara da cewar "Zayyan ya zanyi? Wlhy masifar kunyar Elham nakeji na rasa meke damun kaina,mesa Banyi tunanin kaita wani asibitin ba,mesa kuma ban yadda da itaba sanda take ta mun ranstuwa? Yanzu yaya zanyi ina zan tsoma rayuwata? Da wane ido zan kalleta?" Nisawa zayyan yayi "Lallai wanna al'amarin akwai rud'u a cikinsa watak'il dabaka biyewa wannan bak'ar zuciyar takaba da tun a wancan lokacin kun cimma mafita,ni banida abinda zance maka yanzu,kawai dai ka bata hakuri Allah hasa Zata hakuran dts all" godiya yayiwa Zayyan ya kama hanyar asibitin,gwiwa a sab'ule ya Shiga d'akin da sallamar sa,sister d'in ta gaidashi ya ansata yaje ya zauna yace da Elham "Sannu Elham ya jikinki?" D'auke kanta tayi daga dubanshi gaba d'aya ta mayarda dubanta zuwaga d'ayan b'arin daban,lokaci d'aya hawaye masu d'imi suka gangaro daga idonta,Kallonta Asiya yayi yace "Asiya ko Zakije gida ne kiyi wanka ki dawo sena zauna da ita" bata masa musuba ta mik'e yace "ungo ki Hau adaidaita kinji" dubu d'aya ya bata ta k'arba ta wuce......tashi yayi yaje ya zauna a saman gadon da take ya riqo hannayenta duka biyu da sauri ta warce abinta har wani azaba taji a d'ayan hannunta me cannula, muryarshi na rawa yace "I knw I have wronged u Elham,but could u plss find a place in ur heart to forgive me? Wlhy wannan kuskure aka samu nasani ban kyauta ba daban zurfafa bincike ba amma kema kin sani akwai rud'u dan Allah kiyi hakuri my life partner" yanda ta rufe idonta harya k'araci maganarsa bata bud'esu ba,yafi awa d'aya yana bafa hakuri amma fir yaqi ce masa koda ci kanka,abinci ma yayi juyin duniyarnan taci amma taqi dukya bi ya rud'e matuk'a kuka kurun ya saka mata,har aka kira azahar shi da itane kurun a d'akin,momy ce dasu feenah sukayi sallama sukazo kallon shi momy tayi "Babana badai kana nufin cewar sabida kawai angano Ba Hafsat bace da cikin shine ka sakata agaba kana dirzar kuka,wannan wane irin haline wai? Su wayancen da k'addarar rashin yaronsu ta afka musu sabida rashin bada result daidai suce me? Sekai da bawai cikin bane ya zube dama babu shi? Dudu yaushe akayi aurenku ? Kasan tsarin Allah akanku? Danla ni matsa ka bani wuri ka wani zo haye gadon tamkar zaka maidata ciki" bece komai ba yatashi ya zauna akan k'aramar sallayar dake d'akin,se yamma su momy suka tafi..... Sanda Hafsat tayi kwana biyar sannan akayi discharging nata,har aka sallameta bata kulashi,kullum Awurinta yake wuni amma harya k'araci surutunshi da ban hakuri bata cewa dashi ci kanka,koda aka sallameta yace zasu wuce gida kuka ta saka ita lallai momy zatabi seta k'ara jin sauqi,hakan kuwa akayi momy ta wuce da ita gidan su....... A d'akin momy bayan yan dubiya sun watse dare yayi momy ta kalli Hafsat tace "Mamana don Allah sanar dani menene ya had'aki da Babana harta kai ga duka,dukda na ganshi acikin halina maye sanda naje gidan" Murmushi ta kakalo sannan tace "Ba komai momy". " kinga Hafsat tun kina k'ara marki nake tare dake I knw very wen ur telling the Truth,Karki mun k'arya sanar dani gaskiyar komai" se kawai ta saka kuka,kyar momy ta lallasheta tayi shiru,sannan tace "Dama fa momy ni tunda mukayi aure da Yaa Yarima ba abinda ya tab'a Shiga tsakanina dashi na auratayya shine kawai akace inada ciki.....daga nan kuma kuka ya k'wace mata,dak'yar ya tsagaita ta kwashe komai ta gayawa momy, nisawa momy tace " wannan abu kam sam beyi dad'i ba kuma Yarima ya tafka kuskure sabida komai yanada buqatar bincike,yayinda ke kuwa kikayi zurfin ciki,ai kamata yayi tun a asibiti kiyi magana semu k'arayin test kinga kin wanke wa kowa zargi amma ta yaya zamu gane gaskiyar lamarin bayan kinyi shiru? Kinga mijin kima zaton zeyi kin aikata ba saidai ba,amma shd'inma ya rafka kuskure sabida a yanda kike d'innan ni kaina zan iya shedarki,kiyi hakuri ki dena kuka kuma ki koma gidan mijinki ki yarda haka Allah ya tsaro miki taki rayuwar,kuma karkiji kunyar duk wani abu dazan gaya miki yanzu danake taqama dasu ake cewa na asirce mijina na hanashi aure.....sosai momy ta zayyane mata komai na yanda Zata kula da mijinta se sussune kanta takeyi. washe ta kira Abdul ta zazzaga masa wandon masifa sannan daga bisani ta had'asu duka tamusu Nasiha sannan ta hanesu gayawa wani wannan zancen kana sukaje suka gaisa da mahaifiyar Elham Abdul yamusu shatara na arziqi sannan wuce gida.... Love wan tintin... Ranar gaba d'aya Abdul kasa nutsuwa yayi shi harga Allah so yake ya angwance da matarsa,sallah ya saka sukayi sannan sukayi shirin kwanciya,Elham duk wani d'ari d'ari takeyi da Abdul,kallonta yayi ta wani takure a hijab yace "Yan matan moris yau baza'a mun kwalli yar bacci bane?" Tafukan hannayen ta saka ta rufe fuskarta sannan a shagwab'e tace "yaa Abdul nifa sam banajin bacci wlhy" Murmushi yayi yace aranshi ina ganin Yarinyar ta tsorata dani barin barta harta saba da wasanni na" "To muje parlor muyi kallo mana ehn" yafad'a yana kallonta da alamar wasa "To muje mana" Tafad'a bayan ta mik'e tsaye...takowa yayi yace yana k'ok'arin cire mata hijab "shi kuma wannan hijab d'in fa, kishiya tane?" Wani narkewa tayi Tafad'a jikinshi tana buga qafa a qasa cikeda shagwaba "Allah ni yaa Abdul karka cire mun bafa komai a jikina" sosai ta sungume hankalinshi sukayi habuja,d'aga hijab d'in nata yayi ya cura hannunshi ciki ya d'aura a saman waist nata,wani Yarr taji lokaci d'aya ta lumshe ido,hannunshi yasa ya zare hijab d'in wasu hatsabiban kayan bacci ya gani a jikinta riga k'arama da guntun wando Heeps d'innan sun zauna cas dasu ga dukiyar fulanin nan sun ciko sunyi sama,kasa d'auke dubanshi yayi daga nonuwanta, jefar da hijab d'in yayi ya riqo k'ugunta da kyau tazo jikinshi yakai bakinshi asaman breast d'in yabasu hot kiss wanda atake ya bata kunya,ta rufe idonta Shafa gashin kanta yayi yace "Haba y'an matan yaa moris ya zaki b'oye mun wannan kyakyawar shigar,ina ni Ki kayiwa? " sadda kanta tayi qasa tana Murmushi daga nan ya sanya hannunshi ya dagata cak zuwa parlor,a saman cinyarshi yayi mata matashin kai,ya cura hannunshi a cikin gashin kanta yana mata tafiyar tsutsa,gaba d'aya ya gama kashe mata jiki se lumshe ido takeyi a haka har bacci ya sureta.....mamakine ya kamata ganinta ajikinshi kuma ga haske ya mamaye d'akin alamar gari ya waye sannan dukkaninsu ba kaya ajikinsu,da sauri ta lalubo duvet ta rufe jikinta,wannan zaburar datayi ne ya farkar dashi,rufe idonta tayi ganin shiko ajikinshi be damu ta ganshi a hakaba,matsawa yayi daf da ita ya rungumota yace "Ke kintashi shine bazaki tashi kiyi salla ba,nifa tun asuba nayi sallah na" cikeda shagwab'a tace har lokacin idonta a rufe yake "shine ni baka tashe niba?" Murmushi yayi yace "ked'ince dason jikin tsiya kin kama kin wani qanqameni sekace za'a sace miki ni,dak'yar na samu na zare jikina kuma ma Aina tashe ki so biyu kene baki tashi ba" cura fuskar ta tayi a k'irjinshi cikeda kunya domin batasan me tayi ba acikin bacci,kamar zatayi kuka tace "shine kuma ka cire mun kaya nika tashi zanyi sallah ne" matse bakinta yayi yace "Zakiyi sallah d'in sena tashi,Kedai zaki tashi kije kiyi alwala rana na kallonki sakiyi salla" maqe kafad'a tayi "yaa Abdul bafa kaya ajikina dan Allah ka fita sena saka" bushewa yayi da dariya yace "kinga yan mata kayanki ma yana parlor naga kinata had'a gumi Shiyasa na ciresu,barima kiga" zare duvet din yayi ya sungumeta be dire ta ba se ban d'aki se yarfe k'afafuwanta takeyi tana shagwaba ga idonta a rufe ruf.....shi se dari yarta yakeyi kun yarta na bashi mamaki da dariya... Mom Nu'aiym [1/8, 10:32 PM] Sha'awa: *🌞HAFSAT ELHAM🌞* Billy Galadanchi Haske writer's Asso💡 Vote me on wattpad@68billygaladanchi. Sadaukar wa ga k'awata Hafsat Abubakar qaya (Elham).                         20 Sanda ya wanke ta tatas sannan ya barta tayi alwala,ta dauro towel ta fito se wani kunya takeji a haka ta zura jallabiya tayi sallah,kai tsaye kitchen ta wuce ta musu samosa bread da spaghetti bolognese ta had'a masa coffee sannan ta dawo d'aki light makeup tasaka sannan ta sanya less ruwan Zuma ta murza d'auri ta feshe jikinta da turaruka sannan ta fito kai tsaye d'ankinsa ta wuce,a gaban mirror ta sameshi yana taje sumar kanshi,d'auke kanta tayi daga dubanshi sannan a hankali tace "Yaa Abdul Barka da kwana" ajiye brush d'in yayi ya juyo yana Murmushi sosai ya mata kyau,Sanye yake da jeans black da rigar sa asalin fara qal kirar kamfanin mk ya dirza agogon gold a hannunshi se tashin k'amshi yakeyi,matsowa yayi kusa da ita ya rungumo ta jikinshi sannan ya kalli kyakyawar fuskarta yace "Blossom kullum k'ara kyau kikeyi,narasa wane kalar kaya ne yafi miki kyau,kinga idan kika saka k'ananun kaya seki fito kamar wata baturiya,idan kuma kika saka Jallabiya seki dawomun balarabiya sak idan kuma kika saka kayanmu na hausawa sena kasa wai hausa Fulani nake gani kokuma kanuri" tsura masa ido tayi harya gama wannan rattaben sannan a hankali ta sauke idonta k'asa tace "Yaa Abdul breakfast is ready" hannunshi ya saka ya d'ago hab'arta yace "Blossom bakya san kallona,har yanzu fushin kike dani?" Batayi magana ba Murmushi kurin tayi be saki hab'ar tata ba yace "Blossom dan Allah kiyi hakuri komai ya wuce Allah bana cikin nutsuwa ganin wannan halin da kike ciki,kalli fa na miki kwalliya bakice namiki kyau ba ko sabida ban saka takalmi bane?" Dariya ta masa har haqwaran ta suka bayyana tace "Kayi kyau mana yaa Yarima nifa dana shigo banma gane kaba,na Zata wani balarabe ne Ashe miji nane?" Dariya yayi yace "Kin iya tsoka na faa blossom, kuma kinga nifa bana so kike laqabamun wani yaa Yarima yaa Abdul, ki sama mun suna me dad'i daza kina riqa kira na dashi" Murmushi tayi sosai tace " yaa Abdul ni bansan me zan ce ba fa,wane suna kake so na kiraka dashi" "Kece da kanki zaki nemo nima ban saniba" dariyar dai tamasa "Muje kaci breakfast mana" bece komai ba ya saqala hannunshi a nata suka wuce,shine da kanshi ya bata taci sannan yaci,daga nan suka dawo parlor suna kallon wani film na hausa.       Da dare ma wanka tayi ta caba kwalliya cikin doguwar rigar dress red color bata saka d'an kwaliba tufke kanta kurun tayi da Jan ribon,bayan ta gama dafa musu tuwon semo da had'addiyar miyar egusi taji ganda kifi da nama,se tashin k'amshi takeyi ta had'a mu sugar cane and lemon zest drink se tashin k'amshin dadi yakeyi,lomar sa ta farko ya lumshe ido yace "Blossom idan kinsan irin wannan dad'in zaki riqa girka wa ki dena kawoni dining kurun ki ajiyeni a qasa,idan ba haka ba kuwa Allah fad'owa zanyi " sosai maganarshi ta bata dariya,dariyar kuwa tashiga yi har tana riqe ciki,shi kuwa yana dariyar yana kallonta ba k'aramin burgeshi takeyi ba tana dariyar,sanda yace "Au dariya ma kike mun,zan rama ne nine zan mana lunch Allah idan kika kuskura kikaci daddad'an girkina sumewa kurin zakiyi" dariya ya qara bata jin zancensa aikam tafara mar dariya har tana durqushewa take lomar datakai bakinta ya sarqeta nan take ta soma tari ba k'ak'autawa idonta yayi jajir,tasowa yayi ya tallafeta yana bata ruwa dak'yar ta samu ya tsaya mana,ama abin da ya bashi haushi still suna cin abinci tana masa dariya kuma taqi magana "Blossom dama haka kike da dariyar k'eta? Allah yau zan shayar dake mamaki zaki tabbatar sunana Mr.chef" tana dariyar tace "Tom yau kuwa zanga Mr. chef meze dafa mana" Murmushi yayi yace "Shawarma da hand sandwiches zan miki plus mango and milk shake,yau d'innan zan tabbatar miki ban zauna turai a banza ba" dariyar taci gaba dayi "idan ina bacci na karka tasheni se idan ka tabbatar ka kammala mana lunch" shidai banza ya mata,daganan zuka wuce bed room bacci....... Ba ita ta farka ba se Wuraren karfe d'aya sallah tayi tawuce parlor kai tsaye se sauri takeyi tamakara girki a tunaninta wasa Abdul keyi,aikam tana zuwa kitchen ta tarar yama kammala girka komai se tashin k'amshi gidan keyi, Juyowa yagi ya wara hannayenshi yace "common sleeping beauty" Murmushi tamasa amma kunya ta hanata k'ara sawa jikinshi dakanshi ya tako yazo ya rungumeta,ya rad'a mata a kunne "Blossom nagama fa,yau zakici best girki ever" Murmushi tamasa kurun seta tsinci kanta da lafewa ajikinshi ta saka hannayenta bayan waist nashi "Yaa Yarima I'm so hungry" Tafad'a har tana doka k'afanta a k'asa cikeda shagwab'a, d'ago habarta yayi da hannunshi yace "Look blossom taimako d'aya zaki mun ki bani 15 mnt nayi sallah ke kuma ki had'a table kinji" Murmushi tamasa tace "Alright u go and pray and I will set d table" sakinta yayi bayan ya manna mata kiss a kumatu yabar kitchen din.....mamakine ya kamata ganin yanda ya had'a Shawarma da hand sandwiches d'in ga kuma mango and milk shake a manyan cups guda 4 saka biyu tayi fridge sannan ta gyara sauran a dining, kan ya fito kuma taje tayi wanka da ruwan miski ta feshe jikinta da manya manyan turaruka ta saka doguwar rigar jallabiya kalar wine color ta d'aura d'an kwalin ta kalar sararin samaniya tayi kyau matuk'a,a yanga ce take tafiya harta iso dining d'in k'amshin turaren ta ne ya sanar masa da zuwanta, da sauri ya juyo lokaci d'aya ya mik'e yaje ya rungumeta sauke ajiyar zuciya yayi yace a hankali "blossom kina kashe ni da wannan wankan naki me d'aukar hankali,wlhy ki yarda dani lada kike samu kuma ina matukar jin dad'in haka,k'amshin turarenki banajin kalarshi ko ina se a wurinki sanar sani Wanne irine zanje nawa CEO na campanin babbar kyauta" Murmushin ta me sanyi tamasa,sannan cikeda shagwaba tace "Yaa Abdul zanji shawarma yawuna se tsinkewa yakeyi" saketa yayi yana dariya "yanzunnan sekice zaki mun kuka,muje na Kici" bata masa musuba kurun sukaje sanda taci guda biyu sannan taci sandwiches d'in ta shanye mango and milk shake duka sannan tace "Man wane shop ka siyo Wannan shawarmar? Murmushi yayi yace " Moris Shawarma shop" kwashe wa tayi da dariya sannan yace "ki shirya da yamma zamuje yawo kinji" A green color suka je yawo se hirar su suke suna dariya,tana ganin Shawarma tace Zata ci,yace "Blossom ki bari Kici wani abun daban da akwai agida fa" maqe kafad'a tayi "Noo ni wannan zanci yanzu idan kuma naje gida Senayi warming wancen naci" aikam koda ta fara ci setace bataso wai nashi yafi dad'i, sanda suka gama shan iskar duniya gab da magrib zuga biya ice cream shop suka siya sannan suka wuce gida direct..... Bayan sallar isha,suka dawo parlor suna hira abinsu,Elham ta saka wani wando iya cin yarta sannan kuma ga bingilalliyar riga gashi batada bra niples nata sun gama tayarwa gogan da hankali, gashi ta baje yalwa taciyar sumarta se tashin kamshi takeyi,kasa hakuri yayi ya dawo kusa da ita,hannunshi ya sanya ya janyota ta kwanta a saman k'irjinshi ya cura hannunshi acikin sumarta yana mata wasa dashi a hankali,kasa hanashi tayi zuwa wannan lokacin idan ba cikin jikinshi tajita ba batajin daidai,yau d'in ma bacci taketa so tayi har goma ta gota amma a yan kwanaki biyunnan ta soma sabawa da kwanciya a jikinshi seta kasa,ganin zatayi bacci a haka ya sanya ya sauketa yaje ya rife ko ina yazo parlor ya kashe kayan kallo ya dagata se bedroom nasa....Kwantar da ita yayi bayan ya kashe fitinar d'akin lokaci d'aya ya sanya hannun shi ya zare mata guntun wando,gaban tane ya fad'i tace murya na rawa "yaa Abdul dan Allah ka dena" bakinshi yakai daidai kunnerigarnan "Haba blossom bakyason kiji dad'in bacci,kayan nan taku raki kurun zeyi" ta bud'e baki Zata magana ya cura bakinci a nata harshenta ya janyo ya dinga tsotsa tamkar ze tsinkashi yakai minti biyar yana saukar mata da kasala sannan ya janye bakinshi daga nata yace "Ki tashi zaune mana ki cire rigarnan na sakaki a jikina kiyi bacci" cikeda shagwab'a tace "yaa Abdul ni ka bani wandona plss" hannunshi ya d'aura aka lips nashi yace "shhhhhhh blossom bana san gadda ma fa" shura k'afa tasoma yi cikeda shagwab'a "yaa Abdul dan Allah fa" cikin y'ar tsawa kad'an yace "Blossom if there say a word again I will slap you fa,just sit down and raise up ur hands" tashi tayi zaune tana kallonshi acikin wannan d'an hasken na deem light,zunb'uro baki tayi tana yamutsa fuska ta daga hannunbya zare yar muna fukar rigar dake jikinta,gaba d'aya kunya ce ta gama da matsalar ta musamman dataga yana cire kayanshi mayarda idonta tayi ta rufe,sannan ta kwanta rigingina cikeda kunya, kashe deem light d'in yayi sannan batare da tayi auneba taji lallausan harshensa da lips d'inshi a saman breast d'inta,d'imau cewa tayi gashi lokaci d'aya ya saukar mata da kasala wani irin masifaffen dad'i ne ya ziyarceta da bazata iya fasssara yanda take jinshi ba wani abune yake fizgarta tun daga kan d'an yatsanta na k'afa har saman kanta,dak'yar ta iya bud'e bakinta tace "Yaa Abdul zaka kashe ni" sake mata breast d'in yayi ya matso da kanshi wurin kunnenta yace "Kashe ki kuma blossom dame zan kashe ki?" Cikeda rad'a yace haka mik'a tayi daba tasan dalilin taba tace "Dan Allah kadaina mun magana a kunne" be kula taba ya kuma kai bakinshi wuyanta yarfe hannayenta tayi duka biyu tace "Nashiga uku" nanma be kula taba yaci gaba da lasarta dukta inda yaso Elham,se murk'ususu takeyi tarasa dalilin dayasa ta nemi nutsuwar ta ta rasa, bakinshi ya kuma kaiwa kan breast dinta ya dan na musu kyakyawar tsotsa lokaci d'aya numfashin ta yafara up and down,d'ayan hannunshi kuma ya d'aura asaman d'ayan breast d'in ba shiri ta d'aura hannunta saman kanshi tana Shafa, Allah Sarki Abdul cikeda k'warewa ya sarrafa Elham da wasanni masu sanya nishad'i dajin dad'i mara misaltuwa,a hankali yazo ze saukewa kanshi wahala kuma yar garin bata yi masa musu ba,lapiya lau be cutar da ita ba cikeda sanin darajar 'ya mace ya kuma duba kasancewar ta k'aramar yarinya ya lallab'a abarsa har ya cimma burinsa,sedai fa yasha raki Elly kuka tayita masa tana magiya,koda ya dawo nutsuwarsa albarka ya d'inga zuba mata,ganin ya sameta cikakkiyar mace me gard'in gaske,koda ya haske d'akin da fitila rufe fuskarta tayi da tafukan hannayenta,ganin duk ya b'ata wurin da jini ya sanya ya d'aura towel ya zauna yace "Hafsatul Elham ina roqon Allah yayi miki albarka ba adadi,Allah ya albarkaci rayuwar ki da rayuwar zuriyarki,yanda kika faranta raina Allah ya faranta rayuwar ki daga yau har abada,Hafsat kin burgeni a wannan zamanin d'aid'aikun matane kurin za'a samu da kare Kansu irinki,yau na k'ara tabbatar wa kaina ina d'aya daga cikin mazaje mafi Sa'a a rayuwa,Allah ya barmu tare blossom" batace komai ba saida ta gaji kuma harga Allah kunyar abinda yashiga tsakaninta dashi takeyi "Blossom ki tashi na gasa miki jiki kinji?" Cikeda shagwab'a tace "Yaa Abdul zanyi da kaina plss" sarai ya sani gaddama Zata tsaya masa,wannan ya sanya ya d'agata zuwa bathroom a bahon yadireta acikin warm water sannan ya wanke ta shima yayi wankan yasanyata tsarkake kanta agabanshi domin ganin iyawarta,yane zanin gadon yayi sannan ya wuce d'akinta suka kwana acan cike da farin ciki..... *Bayan sati d'aya* Cikeda zumud'in kasancewa tare da juna suke tare,yau fitar yamma sukayi Sunje gida,lapiya lau suke hira a mota,suna isowa k'ofar gidan Elham taga wata qatuwar halitta dabazata iya tantance meye ba tayo kanta,da sauri ta kwallah k'ara tayi bayan Abdul ta koma tace "Nashiga uku yaa Abdul wlhy ga wani abunan ze kasheni a k'ofar gida" dubawa yayi bega komai ba yace "Blossom ki nutsu nifa banga komai ba" dagowar dazatyi takuma ganin abin aikam ta ruga seda ya riqota,wasa wasa fa gaba d'aya ta haukace sekace me shafar aljanai waya yayi momy tazo anfi awanni biyu amma taqi Shiga ciki,dole suka koma da ita gidansu name Marta ba,duk sanda Abdul yazo kusa da ita seta saka masa ihu kamar wacce taga wani abin tsoro gaba daya ta fita hayyacinta.... Mom Nu'aiym [1/8, 10:32 PM] Sha'awa: *🌞HAFSAT ELHAM🌞* Billy Galadanchi Haske writer's Asso💡 Vote me on wattpad@68billygaladanchi. Sadaukar wa ga k'awata Hafsat Abubakar qaya (Elham).                              21 Momy nifa na damu sosai,Shiyasa naketa gudun wannan auren da baiwar Allah nan,yanzu gashi sunaso su firgita y'ar mutane,kuma abun haushin nine batasan koda gani wlhy" "Babana ka kwantar da hankalinka Mlm na Maiduguri nakan hanya fa,inshaa Allah komai zezo da sauqi" shiru be tankaba sabida bashida abin cewa d'in.....da yamma Mlm yazo,a d'akin datake kwance aka kaishi domin ya dubata  ,adua aka Shiga yi mata da karatun alqur'ani amma abin mamaki ko gezau ba tayiba,kallon me martaba Mlm yayi yace "Wannan asiri ne kuma suna sane da zuwana,dama abin tsoratar da ita kurun yakeyi bawai ajikinta yake zama ba,an sanya mata qiyayyar mijinta ne dakuma gidanshi shi gaba d'aya wata halitta yake zo mata me matukar ban tsoro sabida haka inaga se zuwa gobe zamuyi maganin abin" godiya sukayi masa Abdul ranshi a bace yake wayene yakeso ya rabashi da farin cikin rayuwarsa Ellyn sa,aikam idan ya kamashi seya yabawa aya zaqinta..... Dama ya baiwa kallamu motarsa akai masa wurin wanki se kurun yayi amfani da d'aya daga cikin ta gidansu,ya wuce gidansa domin dauko wani sako, mamakin ganin khamis na magana da me gadinsa yayi matuka,k'in karasa wa yayi har k'ofar gidan,parking yayi daga gefe ya tsaya yana kallonshi harya gama bashi wani qulli a Leda yana nuna masa yanda ze bad'a mamakinsa ne ya qaru ganinfa ya Ciro kud'ad'e ya baiwa me gadin,yana gurin harya masa sallama yabar wurin kai tsaye shima yafito daga motar har yana had'awa da gudu ganin me gadin yashiga cikin gidan yana kunce k'ullin,labewa yayi yana kallonshi ya barbade tundaga kan inda yake parking har zuwa matattakalar dazata sadaka da k'ofar Shiga gidan,yana dawowa gate ya ganshi atake rashin gaskiya qarara ya bayyana a gareshi,murtuk'e fuskarshi yayi yace "Ard'o me kakeyi acikin gidan ne?" D'an Sosa kanshi yayi yace "Ban d'aki naje yallabai" miqa masa key na cikin main Gidan yayi yace "A parlor Idan ka Shiga zakaga jakar computer na saman kujera ka dakko mun" muzu muzu Ard'o yayi baya son shiga,Abdul yayi yai dashi yaqi,aikam a waya yakira Baba k'arami da Ashraf ba'afi mintuna goma sha biyar ba se gasu sun iso a tare, "Yaa Yarima lapiya dai" agaban Ard'o ya zayyane musu komai,yace yanzu kunga na aikeshi yaqi Shiga menene shawarar ku?" Ashraf ne yace "Na rantse da Allah seya taka masifar daya barbad'a ta koma masa" atake kuwa ya kira wani Friend d'inshi soja,suka zo suka dannamai bindiga dole yana kuka ya taka,aikam yana dawowa wurin yafara soshe soshe haukan tuburan Ard'o ya haukace,seda suka d'aureshi,kai tsaye kuwa akaje aka kamo khamis sojojinnan suka Hau jibgarshi da kanshi yayi confess ganin zasu aika dashi gaba da lahira....wani soja da haushi ya isheshi bindiga ya kwala masa yace "Wancen Ibrahim da da ze auri Hafsat,dakuma Abdul Kaine Kayi asiri har wancen ya mutu ko?" Gaddama yayi aikam suka Shiga dukanshi dole ya fad'a waida so yayi duk su mutu sabida yanaso ya auri Elham,take aka wurga hege ga hukuma akan yayi kisan kai yana kuma shirin haukatar da wani akan mace.....abinda yafi baqanta wa Abdul rai shine ciwon daya sakawa Hafsat,seda aka kama har bokan dake masa wannan mugun aikin ya karya komai shima yaga kanshi court d'an banza mushiriki.... *Bayan kwana biyu*      "Momy nifa na tsorata da garinnan,abin ya wuce cikin gida amaka asiri harda na waje,abun ai yayi yawa wlhy,gaskia ni London zan d'auke Hafsat mu tafi Yafiye mun kwanciyar hankali" Murmushi momy tayi"Ba wanda ya isa ya hanaka tafiya da matarka duk inda kaga dama ammafa kasani ko ina kuke se ku riqe Allah,dan ka bar katsar bashi bane,lafiyar Allah zakana riqa nema muku ako da yaushe ana yawaita karanta alqur'ani me girma ana adu'a, sannan kuma seta mirmire zaku tafi" b'ata fuska yayi "Momy wane irin mirmirewa kuma wai,tafaji sauqi ni next week naso mu tafi" rik'e baki tayi "ohh ni Allah ya raka taki gona Abdul,matarka ce idan ma kaso ka d'auketa Ku tafi yanzu,kumama kai anan Zata zauna seta gama mirmirewa zuwa jibi" da sauri ya dago ya kalleta amma ya kasa magana ita kuwa dauke kanta tayi kamar bata ganshiba,tama bar wurin Shikuwa kai tsaye bedroom nata ya wuce yana qunquni....a kwance ya taddata ta rufe idonta tamkar me bacci,bayanta ya kwanta ya rungumota ta baya,a kunne ya rad'a mata "Blossom I really missed you,gashi kuma momy ta hana intafi dake gida yau" da sauri ta Turo shi ta tashi "yaa Abdl momy fa,Karfa taganka anan dan Allah ka fita" janyota ya qarayi "Haba blossom ki nutsu mana nida matana haka kawai zaki takurani kice bazan yi yanda naso da ita ba" kamar zatayi kuka tace " Yaa Abdul ni inajin kunya dan Allah Kayi hakuri" b'ata fuska "Look blossom I'm in need of u,and if u dare say a word I will slap u,comon hug me now" Qunquni tashigayi "Allah ni yaa Abdul gwanda mun marin da momy ta ganni a jikinka,kurun seka sanya tanamun kallon mara kunya" k'ura mata ido yayi cikin B'acin rai sannan batare dayace komai ya mike zebar mata d'akin,kasa hakura tayi da gudunta taje ta rungemeshi ta baya hannayen ta duka biyu a saman k'irjinshi tace tana kuka "Hubby plss don't be angry with me,I missed you so very much" mamakin kalamanta ya sanya ya tsaya beko motsa ba kamar statue haka ya tsaya,ita kuwa a zatonta duk fushin ne dayake, ta gabanshi ta zago ta kama kunnenta duka biyu "Kamun horo me tsanani nikama zaneni amma karkace zakayi Fushi dani kaji?" Tana maganar ne cikin kuka kad'an hawayen idonta na kwaranya,shi kamma ya kasa komai anhankai cikin kasala ya janyota jikinshi, Harshensa ya saka ya lashe mata hawayenta yace "Bazan tab'a zanekiba blossom har abada komai girman laifin daki kamun kuwa amma fa tsaf zan zaneki Idan kina mun asarar wayannan tsadaddun hawayen naki,so banda kuka kinji?" Ya fad'a yana riqe da hab'arta,sauke lumsassasun manyan ida nuwanta tayi a k'asa da suka sauya launi,gashin saman idon yajiqe da hawaye ya kwanta shifshif dashi,a hankali ta d'aura hannunta d'aya asaman k'irjinshi tana wasa da botirin rigarshi cikeda shagwab'a tace "To ni idan kana Fushi dani zanta kukane fa,so idan kanaso na dena kuka ka dena Fushi dani kaji" ba k'aramin burgeshi tayiba,ga kalaman ta sun sakashi rud'ani beside wannan k'urciyar data nuna ya burgeshi cikeda wawta take maganar,a wuyan ta ya d'aura hannunshi yasoma murzashi a hankali yana mata wani kasalallen kallo daya saukar mata da kasala,d'auke da Murmushi a fuskarsa yace "Blossom I'm really sorry for making cry,bansan idan ina Fushi yana sakaki kuka ba,bazan qara Fushi dake ba kinji?" Jujjuya idonta tayi sannan ta yamutsa fuska tace "Sure?" Murmushin shi ya fad'ad'a "sure blossom" Sekuma ta qara narke fuska tamkar zatayi wani kukan,cikeda shagwab'a tace "Zaka mun kalar wannan Shawarma d'in na ranar plss?" Kallon agogon hannunshi yayi yace "Blossom its already late fa,kiga yanzu 7 ya gota" Turo baki tayi sosai wane zatayi kuka,cikeda shagwab'a tace "Allah ni idan bashiba bazan ci dinner ba kuma yau" dafe kanshi yayi "Oh my God blossom rigima ne dake wlhy,kinga muje season seven na siya miki nasu ma dad'i" kwantawa tayi ajikinshi a hankali tace "Idan banaka ba na qoshi zan kwana da yunwa na kawai" hannunshi ya sanya ya ture d'an kwalinta yafara shafar gashin kanta a hankali "Blossom idan zaki rakani gida zan miki Kizo muje" bata kawo komai a ranta ba ta zura hijab,dama momy tabar b'angaren aikam suka fice kurun.....Shawarma d'in ya mata da milk shake,ta zauna ta tankad'a sosai aikam se hamma bacci yazo,kallonshi tayi "Hubby ka kaini wurin momy bacci zanyi" d'agata yayi cak zuwa bedroom d'inshi ya kwantar da ita akan gado,hannu ya sanya ya cire mata d'an kwali,sannan ya soma k'ok'arin rabata da doguwar rigar atamfar dake jikinta,hannunta ta saka ta riqe nashi tace "Yaa Abdul bafa anan zan kwana ba wurin momy zani,haka tace se na kwana biyu zan dawo" Murmushi yamata yace "Nimafa ta sanarmun,amma ai kya bari zuwa k'arfe tara na maidake yanzu fa 8:30 kuma kinga rigar nan nauyi Zata miki idan baki cireba" harga Allah bata kawo komai aranta ba "Tom bara na saka k'aramar rigana da akwai anan,plss idan 9 d'in yayi ka tashe ni kaji bacci nakeji" Murmushi ya kuma mata yace "Yauwa Blossom na,ur always shining,jeki ki saka" bata damu ba taje wardrobe hadda lab'ewa bayan murfin wardrobe d'in ta saka rigar iya cinya tazo kwanciyarta tayi Shikuwa ya kashe fitilar yabar iya deem light shima rage kayan jikinshi yayi zuwa boxer's kawai,ya kwanta ta bayanta,a hankali ya sanya hannunshi ya janye rigar tata har d'an guntun pant d'inta kalar gold ya bayyana,hannun ya sanya ya shafi mararta lokaci d'aya kuma ya kai bakinshi a wuyanta yana lasa a hankali da harshensa me d'imi,zuwan bazata wannan saqon nashi ya mata lokaci d'aya nutsuwar ta tabar jikinta,wani bank'arewa tayi tace cikin murya can k'asan mak'oshi "Yaa Abdul zaka kashe ni" bece da ita komai ba haka zalika be dena abinda yake ba,hannunshi ma dayake murza mararta dashi yaja zuwa kan breast nata ya Shiga Sosa mata nipples nata,kawai Elham kuka ta saka masa,hannu ya sanya ya birkitota ya sanya hannun shi d'aya ya d'ago habarta yace "Blossom ban sanar miki banasan kukannan ba yanzu menene abun kuka,wani wurin ne yake miki ciwo? Girgiza masa kanta tayi alamar AA,yace to menene meya sakaki kuka?" Cikin shagwab'a tace "wannan abin mana" kamar be fahimce ta ba yace "Menene wannan abin?" tana kukan tace "wanda kake mun yanzu mana" k'ara rungumota yayi yace a hankali "Blossom menene bakyaso aciki,me kike jine?" K'ara zumb'uro baki tayi ta yamutsa fuska "Yaa Abdul nifa ji nake kamar mutuwa zanyi wani abu nakeji fa" Shafa sumar kanta yaso mayi "Blossom wannan abin da kikeji fa dad'i ne ba mutuwa bane,mutuwa ai batada dad'i Elly,ki dena kuka Kizo muyi wasa kinji" batace komaiba kurin dai ta lumshe idonta ne,tana saurarenshi yana sarrafata yanda duk yaso,kuma seta tsinci kanta da mayar masa da martani batare da tasan me take ba,a haka har suka biyawa junansu buk'ata, da kanshi ya taya wanka,tace zataje gidan momy yayita mata dabara har bacci ya d'auke ta ajikinshi..... Mom Nu'aiym [1/8, 10:32 PM] Sha'awa: 🌞HAFSAT ELHAM🌞* Billy Galadanchi Haske writer's Asso💡 Vote me on wattpad@68billygaladanchi. Sadaukar wa ga k'awata Hafsat Abubakar qaya (Elham). 22 Shine ya fara farkawa lokacin sallah asuba,be tasheta sabida yasan akwai rigima a qasa,alwala yayi ya gudu masallacin dake layinsu domin gabatar da sallah,yana fita ba jimawa ta farka aikam fitila ta kunna ta qurawa agogon bangon dake d'akin ido,da mamaki ta tashi,da sauri taje tayo alwala tayi sallah ta zauna zaman jiran shigo warsa,koda yashigo tasowa kurun tayi tafad'a jikinshi tana kuka,shikam abin dariya yabashi saboda yasan dawan garin,rungumeta yayi sosai yana patting bayanta a hankali,ganin bazatayi shiru ba ya sanya ya d'agota cikeda kulawa yace "Kuka kuma this early morning blossom meya sameki,ko cinnaka ne ya cijeki?" Tana shashekar kuka tace "Yanzu ni me zance da momy? Allah ni bazan ma koma gidanba" Murmushi yamata yace "Kinga blossom ki dena kuka bacci ne mafa ya sureni nima, ai kinsan dana maidaki,kuma momy Zata fahimta kinji" share hawayen nata tayi tace "Toni yaa Abdul ai inajin kunya yanzu fa dagata gammu zatace Munzo muyi wannan abin ne" gintse dariyar sa yayi yace "Blossom aibazama tayi wannan tunanin ba,kurin dai zatace mun tafi ba sallama ne kuma zance bacci ne ya sure mu,ki kwantar da hankalinki ki dena kuka kinji? Me kikeso Kici na d'aura miki da kaina?" Hannu tasaka ta share hawayenta tace "Banajin yunwa na koshi" Jan hannunta yayi zuwa saman gadon ya d'aurata a saman cinyarsa ya saqala hannunshi saman bayanta yace "Blossom na plss ki daure Kici abinci Allah momy bazatace mana komaiba,haba mana se kace ba miji da mata ba,zakisha chocolate?" Gyad'a masa kanta tayi tace "Zansha mana da waffles ma" Murmushi yayi "Yauwa Inada chocolate da yawa a d'akina zan had'a miki waffles d'in yanzunnan kuma idan kika gama cin breakfast da kaina zan baki chocolate" kallonshi tayi "Toni yanzu bazanci komai ba se wannan Shawarma d'in da hot tea" dafe kanshi yayi yazeyi da Elham dolenshi ya had'a mata Shawarma d'in,dagata yayi ya kwantar da ita yace "Oya ki kwanta idan na kammala zanzo na tashe ki kinji" batayi musu ba sabida baccin be gama isarta ba.....sanda ya kammala yayi wanka sannan ya tasheta kallonshi tayi ta zumburo baki ta yamutsa fuska "Yaa Abdul ka tashe ni ina bacci na me dad'i mafarkin ka fa nakeyi har zaka sakamun Shawarma a baki" dariya yayi "To kiyi hakuri Kizo zan baki a bakin" tashi tayi zaune tace "yaa Abdul zakamun wanka? Yau gajiya nakeji" dafe kanshi yayi yace "Blossom nafayi wanka na,ni zaki b'atan wanka" qunquni taso mayi "Allah ni Idan bazaka munba bazan maci breakfast d'in ba,kumafa kasan banida lapia fa shine zakace nayi da kaina" Shifa har tsoron rikicin Elham yakeyi yanzu,gashi har wani dena kunyar shi takeyi ta masifar iya zuba shagwab'a da rikicin tsiya "Oya tashi ki rage kayan jikinki na miki wankan inyaso idan kin shirya maci breakfast d'in" matsowa tayi kusa dashi ta d'aga mata hannayenta sama alamar ya cire rigar,be musa ba ya cire mata rigar ya soma mata cakulkuli,aikam ta soma kwasar dariya dak'yar ta tsagaita dariyar datake tace masa "Allah na tuba yaa Abdul, dan Allah Kayi hakuri ka dena" dena mata cakulkulin yayi yace "Gobema kya k'ara gantsarewa kina mun rigima oya muje ban d'akin" rungume k'irjinta tayi da hannayenta,wai ita a dole lallai kunya takeji,shikam wannan wawtar ta Hafsat na bashi masifar dariya be kulata ba ya wuce gaba abinshi zuwa ban d'akin bayanshi tabi tana dariya,sanda yasake wani wankan shima sannan suka dawo d'akin zamanta tayi akan bed,waigowa yayi ya kalleta "Blossom bakajin yunwa ne wai? Ki shirya mutafi mana" maqe kafad'a tayi tace "Yaa Abdul nika sha famun mai kuma ka sakamun kaya,banida lapiya fa" girgiza kai kurun yayi yazo ya Shafa mata man ya zura mata wata guntuwar riga iya gwiwa sannan suka juya zuwa dining.... Acan ma seda yasha fama da ita shi kuwa se biyewa shirmenta yakeyi,bayan sun kammala dak'yar ya lallabata ta shirya suka je gidan momy wai kunya takeji...... Agaban momy Hafsat ta kasa had'a idonta dana momy se sosai kai takeyi,momy kuwa tayi Kici kicin da fuska,bayan gaisuwa momy bata qara cewa dasu komai ba,duk sun tsargu,Abdul ne yace "Momy dama na dawo da Elham ne har jibin,jiyane bacci ya sureni,kuma tayita tashina na maidota amma baccin yaci k'arfina" wata uwar harara ta wurga masa "Da kukaje gidan ubanme ya kaiku? Shine zaka nuna mun ka isa ka d'auke matarka ku gudu banma sani ba ko kaiga me mata? To kaje can da ita ni bazan yadda ta zauna mun kazo ka mun rashin kunya" Sosa kai yayi "momy kiyi hakuri dan Allah" "Kabani hakuri wani laifin kamun,Allah maza ka dauki matarka ku barmun gida,kuje gidan naku da kuke d'oki" matsawa Elly tayi kusa da momy kanta a sunkuye "Momy dan Allah kiyi hakuri Allah kuwan yaa Abdul yaqi ya dawo dani" harara momy ta wurga mata "Da igiya yajaki kuka tafi kenan?" Shiru tayi ta saka kuka,ganin haka yasanya momy sakkowa daga domin fushin da takeyi ta rarrasheta sanda ta dena kukan sannan suka koma gidansu bisa umarnin momy,lura Momyn tayi da matsala idan ta riqe masa mata...... Da yamma yana wasa da yan yatsunta na k'afa lokacin ta tasashi gaba da rigima akan seya ja mata 'yan yatsunta, wayarshi ya soma ringing,inspector mansur ,ya furta bayan ya daga wayar "Yallab'ai wlhy fa khamis ya gudu bamusan ya akayi yagudu ba" tsaki yaja lokaci d'aya sarautar ta motsa "ida ya gudu meye ruwana aciki ,wlhy Sekun nemoshi mutumin dake iyayin kisa Zakuyi sakaci dashi harya gudu daga hannunku?" "Yallab'ai laifin yarane kuma munyi informing na commissioner yanzu haka yace abaka tsaro an Turo yan sanda susu goma zasu yi gadin gidanka" bece komai ba ya ajiye wayar ya fara masifa "Dan Allah meya sanya en sandan Nigeria basuda hankali kuma basusan kan aikinsuba,tayaya criminal irin wannan me murder case and another attempted murder case ze gudu daga hannun su,this is unbelievable,I don't even trust there word's may be dasaka hannunshi aciki and I promise they will pay for it" rik'e hannunshi tayi tace "Come down hubby,kanata masifa menene ya faru?" Cikeda fusata yace "Haba mana Hafsat,tayaya zasuce wai khamis ya gudu sekace wanda yake ajiye a kasuwa,yaya zasuyi Saka cin da haka ze faru? Wlhy zasu ganene idan wani abin ya biyo baya" hannunta da d'aura saman wuyanshi cikeda kulawa "Hubby plss come down zasu nemo shine,kuma inshaa Allah ba abinda ze faru se alkhairi kaji" k'ura mata ido take ta hango masifa a idonshi wannan ya sanya tabar masa parlor gaba d'aya,ita kanta k'arfin hali kawai takeyi amma k'irjinta na dukan uku uku sabida tsoron abinda ze biyo baya,tana nan ya dazo ya sameta "Blossom kinji wani labari mara dad'i kuma,wai khamis yayi hatsari da motar sa a hanyar sa ta barin garinnan kuma anje jikinshi kusan rabewa biyu yayi,wlhy duk Senaji jikina ya mutu Allah koda nake jin matukar haushinsa amma mutuwar nan ta dakeni har raina" zabura tayi tana salallami tace "Allah uban giji ya jikan khamis da rahamar sa,Ashe dama ajaline yake kiransa bawan Allah,nidai kam na yafe masa duk abinda yamun " Abdul dai bece komai ba shiru kurun ya mata.... *Bayan kwana goma* Yanke mata farce yakeyi da nail cutter yana mitar rigima irin nata,"ace mutum shi komai nasa rigima ne,yankan farcen ma Senayi dagaske kice ke bazakiyi da kanki ba tsabar shagwab'a Allah momy ne ta sangartar dake" Turo baki tayi "Allah nifa tunda mukazo garinnan ka wani dena sona ni London d'in ma ba dad'i ka mayar dani gida" dariya yayi yace "jiya jiyannan fa muka zo kuma yau da yamma zamuje yawo so karki damu zakiji dad'in London sekince bazaki koma Nigeria ba" bata tanka mishi ba dai har suka gama.... *Bayan wata biyu* Kwance take ajikinshi Wuraren k'arfe biyu na dare ta sashi a gaba da rigima "Allah ni ya Abdul seka mun Shawarma da creamy La bee's, bazan iya bacci ba yunwa nakeji" hannun shi ya sanya ya shafi fuskarta a hankali "Blossom meyasa kike da rigima ne wai,kisha yoghurt mana,I promise danayi sallan asuba zan had'a miki" shura k'afa ta somayi tana kuka "Ni idan ka gaji dani ka maidani gida sarai nasan wannan yunwar tawa bazata bari nakai safeba kuma youghurt bata k'osar dani" tashi yayi zaune bacci fal idonshi yace "muje na tashi Margie ta had'a miki" (house help nasu) "Idan ba naka ba bazan ciba Allah" bece komai ba yatashi yaje kitchen dama sunada Shawarma bread shapshap ya hada mata da Creemy d'in ya kawo mata zama tayi ta fara shan creamy ta zauna ta cinye Shawarma din duka biyu,aikam tana idarwa se Amai,shi duk hankalinshi ya tashi ganin aman yaqi tsayawa,se Wuraren k'arfe biyar sannan tasamu bacci tausayi ta bashi ya kasa komawa bacci ya zauna zaman jiranta yayi sallah yaje ya had'a mata wani Shawarma d'in da mango juice koda yazo hartayi wanka kallon Shawarma din kurun tayi ta d'inga kwara amai dak'yar ya lafa,koda ya kamota su dawo d'akin ki tayi "Yaa Abdul dan Allah ka fitar da abin cinnan kan na koma d'akin bana sanjin warinshi sam" ya kasa ganewa kanta sam tausayinta tamkar yayi kuka koda ya dawo harta kwanta tallafota yayi "Blossom what's wrong with you all of a sudden, me yake sakaki amai wani wurin yana miki ciwo ne?" Shiru ta masa ta kasa ansashi sanda ya kuma tambayarta sannan tace "Bana san warin wannan Shawarma d'in da komai ma" subhanallah ya fad'a shawarma d'in nawane bakyasan warinshi kuma? Tome zakici?" Shiru tayi nanma "Blossom what d u want to eat? Just tel me I will go and prepare it my self right away" "Yaa Abdul I'm not hungry,i don't feel like eating anything" shiru yayi ya qura mata ido,sosai mamaki ya kamashi ganin batayi minti biyu dagama magana amma harta soma bacci,ba ita ta farka ba se after 12 noon, koda ta farka baya d'akin kai tsaye dining ta nufa kasancewar tanajin maso faffiyar yunwa,wanda a had'e yake da kitchen sabida ginin turawa,tana isowa wurin taji warin abincin da house help dinsu ke girka wa se wani aman ya taso ta dinga kwara rawa ba k'auk'autawa tun tana iya riqe kanta harta kwanta kasa a galabaice... Maggie ce ta taimakabta kaita dakinta ta gyara wurin Abdul yafita, aikam tana komawa d'akin se bacci koda Abdul ya dawo Wuraren la'asar tana bacci tun lokacin,Maggie ce ta sanar masa abinda yafaru "Kina nufin blossom bataci abincin dana hada mata ba,kenan yau gaba daya ba abinda taci?" Girgiza masa kai tayi alamar hakane da kanshi yaje ya tasheta amma ina baccin takeyi cikeda wahala,seta bud'e ido Sekuma takoma baccin,ba ita ta farka ba se Wuraren magrib ta gota kad'an da uwar yunwa ta farka wannan ya sanya ta sauka zuwa dining da gudu,a parlor taga Abdul Murmushi kurun ta masa ya taso da sauri ya rungumeta "Blossom Sannu ya jikin? Wai inane yake miki ciwo haka?" "Ba abinda yake mun ciwo nidai zanci abinci" dining ya jata ya soma zuba mata grill fish da sauce se kuma spaghetti, tunkan tafara cin abincin tasoma jin zuciyarta na tashi haka ta daure ta yanki kifin taci,aikam tunkan ta had'yeshi ta soma danna amai, haka tayi amai me yawa kuma a wurin bacci ya sure ta" zuwa yanzu ya fara tsorata musamman da wannan baccin be kawo komai a ranshi ba se mugayen dake binsu da jifa tuni,wanan ya sanya be mayi tunanin kaita asibiti ba anan yake mata aduua da karatun qurani a ruwan zamzam yake mata adua tana sha,wasa wasa Elham sanda tayi kusan kwana biyar a haka dukta rame tayi fari,sauqinta ma tanashan fresh milk da yoghurt su kadaine basa sakata amai ga uban bacci a wuni bata had'a awa uku a farke neman abinci ne kawai ke tashinta.... Yau kuma Elham rigimar lemon tsami takeyi wai da kwad'on rama,andaina samo lemon tsami amma ba zancen kwad'on rama besan inda ze fara nemo mata rama a London ba se rarrashi nta yake amma taqi dena kukan dak'yar ta yadda yamata waffles instead shima baya sakata amai... Mom Nu'aiym [1/8, 10:32 PM] Sha'awa: *🌞HAFSAT ELHAM🌞* Billy Galadanchi Haske writer's Asso💡 Vote me on wattpad@68billygaladanchi. Sadaukar wa ga k'awata Hafsat Abubakar qaya (Elham). 23 Riqe yake da ita tanata uban amai,shi kamma yakasa hakuri k'wallan dayake tarewa ne ya silalo,gani yakeyi tamkar anaso ne a raba Hafsat da rayuwarta sabida ya sani tako ina binsu akeyi da bak'ar mugunta,wanke mata bakinta yayi ya dawo d'aki ya kwantar da ita,abinda yafi komai tsoratar dashi shine wannan baccin datakeyi tamkar matacciya aduk sanda ta kammala amai,wanda duk tabi ta rame tayi wani mugun fari har ja takeyi,sabida abinci baya zama a acikinta,wayanshi ya janyo ya dannawa momy kira tana d'agawa yace tamkar wani k'aramin yaro "Momy wlhy zasu kashe mun Elly na,kin ganta kusan fa sati biyu bataci batasha komai taci se amai,sannan kuma ga uban bacci awuni befi tayi awa biyu a farke ba,Allah momy ni na tsorata" nisawa momy tayi domin kuwai sarai ta fahimci ciki ne da hafsa,tace "Babana kunje asibiti kuwa??" "Momy nasan asiri ne mezamuje asibiti muyi??" "Kaga Babana ba'a haka,zatafa iya yiyuwa ba asirin bane ka yarda da Allah mana da khaddararsa wlhy Ko kad'an banji ajikina cewar asiri bane sam,sabida haka lallai yanzu yanzu ka kaimun Mamana gun doctor" cikin sanyi yace "Ina fatan hakanne momy,bari muje" daga nan sukayi sallama ya ajiye wayar,ba tashinta da beyiba amma bata tashiba dolenshi ya qyaleta ahaka ya d'agata zuwa asibitin, Koda Dr ya gama bincikensa se dawowa yayi da fara'arsa ya kalli Abdul dama abokinshi ne,dukanshi yayi a qirji yace "congrats dude u'll soon be a father" shi be gane inda ya dosaba riqe masa hannu yayi yace "Dr Michael what are u saying,waz wrong with her" dukanshi ya kuma yi "Ur wife is one month pregnant,wahalan datake sha kenan Buh zamu bata magungunan daze taimaka ya tsayar da aman dakuma nacin abinci bacci kuwa se yanda Allah yayi" murna a wurin Abdul ba'a magana ko kadan,ihu ya saka ya d'aga Michael yana jujjuyawa dashi......tun daga ranar Abdul ke baiwa Elham extra care ba qaqautawa Alhamdulillah kuma taji sauqi tayi kyau abinta idan ka ganta bazakace cikin ta yayi 4 month ba sabida ko kad'an be taso ba dama abinka ga doguwar mace,zaune tayi tanashan ice cream abinta datayi ordering daga green three tana sha,a ta bayanta taji an warce da fad'a yace "Wai Elham se yaushe zaki fara jin magana nane? Kinsani wannan ba me kyau bane ga Lapiyar ki dama prince na dake cikin ki,gaskia yau dai munyi fad'a bazan miki doki ba da tausa" Turo baki tayi "Ni komai seka wani ce prince prince,inaso Inshaa dad'i na amma kafisan wannan prince me qaton hanci dani Allah ni wurin momy zan koma" hancinta yaja kad'an "kece dai me qaton hanci ba prince dina ba,kuma wannan ice cream karna k'ara ganin kina shanshi kinmaji na gaya miki" bata rai tayi sosai taqi kulashi,wunin ranar har dare bata kulashi,kuma juyin duniya yayi amma taqi cin abinci dole ya haqura ya qyaleta,cikin dare ta tasheshi "Ka tashi yunwa nakeji,zanci noodles me yaji sosai" a takaice ya mike cikeda bacci a idonshi "idan kika kuma tashina ina bacci Allah sekinsha mari,bazan dafa noodles d'inba ina ba yanda Banyi dakeba kika k'icin abinci shine dan iskanci zaki zomun da wani raini ina bacci na" sosai ta tsorata da kalamnshi,sabida be tab'a yi mata haka ba,batace masa Komaiba ta koma takwanta shima kwantawar yayi dama acikin bacci yake masifar dama ya kwana da takaicin ta yau ta wahalar masa da prince dinsa dayake fatan samu,tashi tayi taje parlor ta kwanta tanata uban kuka shi gogan ma besan tanayiba baccinsa yakeyi,Koda ya farka da asuba bata nan,ya Zata fushin ne ya sanya ta gudu d'akinta bebi ta kanta ba yaje yayi salla abinshi,tunawa yayi da abinda ya faru daren jiya,da sauri ya zabura ya sani yau akwai yaqi, yaje room nata bata can,ya dawo parlor anan ya ganta a kwance tana rawar sanyi,mamaki yakama shi da sauri yaje wurinta,dagota yayi yace "Subhanallah blossom jikinki zafi sosai meya sameki?" Batace masa komai ba se kukan dataci gaba dayi tana rawar sanyi" hannunshi ya d'aura a saman kanta yaji wani masifar zafi da gudu ya kwasheta zuwa bedroom yafara bata taping sponge seda yaji jikin ya sauka,kanya gama tayi bacci ma,qura mata ido yai yana mamakin rigima irin nata,bata jima tana baccin ba ta farka,dashi ta fara tozali da sauri d'auke kanta,hannun shi ya saka ya juyo da fuskarta tana fuskantarsa "Blossom plss kiyi hakuri kinji,yanzu sanar dani menene kikesan Kici?" Banza ta masa yafi 10 mnt yana mata magana amma ko cikanka bata ce masa ba,tashi yayi a k'ufule yaje kitchen ya had'o mata noodles ya kula yunwa ce ke d'awainiya da ita,mugun b'ata fuska yayi sanda ya shigo ya tadata zaune ya ebo abincin ya bata,kauda fuska tayi cikin d'aga murya yace "Hafsat wlhy I will slap u right away,karki mayar dani a bokin wasanki mana,maza bud'e bakinki Kici abinci" tsorata tayi da yana yinsa wannan ya sanya ta wangale bakin ya zura mata ci takeyi tamkar batason ci,Shikuwa se gimtse dariyar sa yakeyi karta raina shi sanda ta cinye tatas sannan ya zuba mata milk shake ta shanye shima rungumeta yayi sosai ya ce cikin sanyi "I'm so sorry blossom kin saka namiki tsawa" batace masa komaiba sabida bacci kanya ankare harta soma minshari abinta..... *Baya wata biyar* Hafsat kam dukta kumbura sakamakon watan haihuwarta daya tsaya,shi tausayi ma take bashi wlhy,ga abin ban tausayinma momy ta hana koda Innah a sanarwa tanada ciki sabida mata basa iya kama bakinsu kuma tana tsoron munafurcin siyasa itama tasan wahalar datasha,dako da adu'ar uwa ta samu, "Blossom me qaton ciki zamuyi selfie" Murmushi tamasa sannan tace " Kaga ni ka matsa zan zauna,wayene zeyi wani selfi yaronka na ciki ya k'ara mun k'aton hanci" Murmushi yayi ya d'aurata akan cinyarsa yace "kinga nifa banasan k'azafi ke d'innan sanda kina yarinya me qaton hanci ma ake ce dake,kurin da kika girmane kika soma packaging kina saka makeup Allah da bazaki ganuba"bata kula shiba ita dai yau sauyi takeji ajikinta na musamman kuma haka kawai ta tsinci kanta da kasa gaya masa,Murmushi yaku mayi " blossom ya dai zakisha fresh milk ne?" Girgiza masa kai tayi alamar Noo da mamaki ya kalleta yace "Blossom yau kene kike gudun milk Kodai bakida lapiya ne?" Murmushin karfin hali ta qaqalo "Noo I just don't feel like taking it now" Murmushi yayi ya qura mata ido yana nazarinta ga mamakinsa gumi takeyi bece mata komai ba ya gyara mata zamanta ya rungumeta,can anjima seta cafko hannunshi ta riqe gam,saukar da ita yayi yace "Blossom look @ me" Ba msu ta kalleshi "Are u sure ur alright?" K'walla ta soma yi"I'm not sure yaa Abdul " kamo hannunta yayi "inane yake miki ciwo den?" "Nima ban sani ba,baya nane tamkar ana datsamun and dts all" bece komai ba ya d'aga ta se asibiti.... Allah Sarki k'uruciya Ashe labor take domin kuwa basufi 30 mnt da isaba ta sunkuco rangadeden yaro sak ubanshi,Abdul dukya gama rudewa,lokaci d'aya ya dauki san duniya ya daurawa yaronnan,batada wani problem yasanya aka sallamesu, waya yayi ya sanarwa momy aikam kan kace meye Wannan gidan sarauta ya d'auka cewar Elham ta haihu,kowa se murna yake Haj Habeeba dakanta ta roqa me martaba a sakawa jinjirin sunan yaronta daya rasu Ibrahim tun yana qarami,hakan kuwa akayi yaro yaci suna Ibrahim ana kiranshi da sultan,dama momy ta turawa Hafsat kanwarta itane ta kula da ita har yaron yayi watanni uku,sannan suka shirya zuwa domin kawowa me martaba da Fulani jikinsu su ganshi..... *Nigeria* Ba k'aramin so Abdul akewa sultan ba duk inda zashi tare suke zuwa koma ina ne,ga yaro qarami amma ya shaida ubansa kowa nasan sultan,wani yanmaci lokacin Satinsu biyu da zuwa k'asar Abdul nawa sultan wasa a parlor haryayi bacci anan ya shinfideshi ya Shiga domin watsa ruwa Ita kuwa tana kitchen.......koda Abdul yadawo bega sultan ba kwallawa Elham kira yayi tazo "Blossom kaddai kitchen kika kaimun sultan kinsanfa akwai zafin gas acan" hannu tasa tad'an shafi fuskarta sannan ta yamutsa fuskar "Yana d'akin ka daiko ni ban dauke shi ba" wasa farin girki domin kuwa kaf sun duba ba sultan ba labarinshi ba k'aramar hauka cewa Abdul yayi ba me gadi ya shaqa akan wayaga yashigo yace dashi "wata motace ta shigo irin waccen shudiyar ta Haj,ina ga abokankane domin mazane,ganin wanin yayi ciki ya sanya nashiga ban d'aki koda na fito harsun tafiyarsu" nan take Abdul ya soma kuka bashiba ba Elham ba haka ya kira momy duk aka taru aka Shiga damuwa. Mom Nu'aiym [1/8, 10:32 PM] Sha'awa: *🌞HAFSAT ELHAM🌞* Billy Galadanchi Haske writer's Asso💡 Vote me on wattpad@68billygaladanchi. Sadaukar wa ga k'awata Hafsat Abubakar qaya (Elham).                             24 Zaman dirshan Abdul yayi ya qurawa Hafsat ido ganin ba'a ga sultan ba kwana uku ya sanya ko magana batayi kuma batacin abinci,shi d'in ma ba abincin yake ciba amma dai yafita dauriya kodan kasantuwar sa namijine oho,kyakyawan murmushin k'arfin hali ya sakar mata sannan yace "Blossom na plss kimun magana mana,nace Meyene kike sn ci na girka miki da kaina?" K'ur tamasa da ido kawai batace kanzil ba,hannu ya sanya ya tura hularsa bayan kansa ya shafi sumarsa "Innalilahi wa inna ilaihiraji'un" itace Kalmar daya keta nanata,tashi yayi yabar wurin batare daya qara cewa komai ba,d'akinshi ya Shiga ya rusa uban kuka tamkar wani k'aramin yaro abubuwan sun had'e masa ga rashin sanin halin da sultan Hake ciki,gashi kuma Elham ko magana batayi bata kuma cin abinci,sanda yayi me isarsa sannan yazo ya dagata cak zuwa d'akin barcinsu,kwantar da ita yayi ya daura kanta saman hannunshi cikeda rarrashi yafara magana "Hafsat dan Allah ki sassauta wa kanki yau kwanaki nawa bakyacin abinci kuma bakyawa kowa magana,dan Allah na rokeki ki nutsu kiyita adua,wlhy kina k'aramun damuwa ne mara misaltuwa,idan dai baso kike na haukace ba dan Allah Kici wani abin" kuka kawai ta saka ta rungumeshi k'ank'ameshi sosai tayi "Yaa Abdul Nashiga ukuna har yanzu fa ba koda labarin sultan,wlhy zautar dani zasuyi idan ba'a nemomin sultan ba mutuwa kawai zanyi,me wannan d'an ta tsitsin yaron ya aikata wa mutane,yaa Abdul dan Allah ka taimaka ka nemonin sultan d'ina" k'ara matseta yayi ajikinshi yana jin zuciyar na masa tafarfasa lokaci d'aya kuma yanajin tamkar zuciyarsa Zata Faso k'irjinsa ta fito har cikin b'argonshi yakejin tausayin ta matuk'a wanan damuwar da hafsa ke ciki na cikin abin da ke qara harzuqa Abdul,rarrashinta yashigayi har bacci ya d'auketa" Wuraren k'arfe d'ayan dare me gadin gidan yaji motsi ana k'ok'arin bud'e k'ofar gate d'in a hankali yazo ya wuce jikin k'ofar gidan ya tsaya wayanshi ya janyo yakira Abdul,ya sanar masa,betashi Elham ba amma sarai taji sanda yake wayar kasancewar dukkanin su bawai baccin sukeba sedai dayake bacci b'arawo ne yakan sacesu wani lokacin suna tsaye a lab'e ya samu nasarar bud'e k'aramar k'ofar gate d'in da buhu D'auke a hannun shi ya ajiye ze juya Abdul yace me gadin ya bishi da gudu me gadin ya bi bayanshi kan yakai k'ofar ya rafka masa uwar sandarsa,take ya fad'i wurin a sume,Shikuwa Abdul da sauri wurin buhun yayi wari ne yabugi hancinsa tunkan ya qarasa bud'e Buhun daurewa yayi ya haska fitilar wayarsa ya qarasa bud'e Buhun "Innalillahi wa inna ilaihirraji'un" itace kalmar dayake ta nanata wa yayinda yayi mutuwar tsaye warin ma ya denaji sabida ganin gawar sultan harta fara zagwanyewa,Elham da tunda yafito take binsa isowa tayi wurin batare da sanin saba,ganin sultan a haka Abdul a tsaye ya sanya ta ture Abdul da hanzari ta wawusheshi,mamakine ya kamata ganin fatarshi ta sab'ule ga uban wari alamomi sun nuna yafi kwana biyu da mutuwa, baka ma gane shine seka kula da kyau,hauka cewa tayi ta soma sambatu kankace meye wannan tafita hayyacinta dak'yar Abdul ya riqeta yana bata baki,kallon shi tayi acikin hasken fitilar wayarshi a daidai lokacinda me gadin ya dawo wurin da gudunshi "Kaga yaa Abdul kalli sultan na,sun kashe shi fa kalli mutuwar wulakanci,kalli yana warin gawa kalli yanda fatar jikinshi ya zagwanyewa daga jikinshi, anya kasan wahalar da yaronnan yake sha kuwa?? Wlhy baka sani ba cewa akayi damu gawa zafi takeji idan ana mata wanka ma,kalli sultan fatar shi duk a sale kalli idonshi,wlhy zafi yakeji yaa Abdul ka tasheshi mana,sudais na be mutuba wlhy" jijiigata yayi yace "kiyi hakuri Elham dan Allah ki nutsu mana,kiyi hakuri kinji" batace komai ba ta k'ura masa ido,se kuma ta kwashe da dariya cikeda hauka tace "Mesa ba zaka tasheniba ina bacci, yaya zaka barni ina bacci ina wannan mugun mafarkin, dan Allah yaa Abdul muje ciki mana" ganin tana wannan abin ya tsoratar dashi matuk'a....miqewa yayi shima ya kamo hannunta "Elham na plss mana me haka?? Ki nutsu kiji ni da kyau haquri zakiyi kinji k'addara ta riga fata an rigada an cucemu se hakuri" dukan k'irjinshi tayi "so kake kace dani wai ba bacci nake yiba,da gaske kake wannan sultan nane wannan,kalli fa da kyau wlhy wannan kalarshi tsanwa ne ni kuwa sultan na fari ne qal" kurin seta sake saka kuka,a haka ta sulale a wurin bata koda motsi.....me gadin ya kalla yace "waye wancan" "Wlhy yallab'ai sale ne?" Da mamaki ya kalleshi yace "wane salen kake magana?" "Sale dai sale wanda ka sani yallab'ai" d'aga Elham yayi zuwa mota yazo ya kai gawar sultan ma yana matsar kwalla,yace da me gadin ya fara d'aure sale sannan ya watsa masa ruwa,zashi asibiti ya Turo police anan d'in........ Sosai Abdul ya girgiza jin cewar kan Elham ya tab'u saka makon wannan abin daya faru da ita,sosai abinda ta gani ya girgiza ta Baza suce bazata warke ba amma fa sam Baza suce ga tsawon lokacin dazata d'auka ahaka ba,sedai abinda Allah yayi,kuka Abdul ya sakawa momy sosai sam zuciyarsa bazata iya d'aukar wannan abin ba,wanda ya kawo gawar kuwa anyi anyi dashi Amma sam yaqi magana.... A firgice Elham ta farka tana kurma uban ihu tana sambatu "Wai cewa suke dani Sultan ya mutu ni sam sultan d'ina be mukuba yaa Abdul me shine shaida agabanshi nabashi mama yasha,se kuma tasaka kuka tasoma kokarin kunce d'aurin da aka mata, sosai ta baiwa Abdul dake kusa da ita tausayi yasoma sharar k'wallah " Wlhy sun kasheshi kisan wulakanci fa ko binnewa beci albarkacin suka masa ba,gaskia nima sena kashesu,kuma bazan binne suba sesun dawo k'asusuwa sena mayarda su...sekuma ta kwashe da dariya...Abdul barin d'akin kurun yayi cikin tsananin k'unan rai ilahirin mutanen dake d'akin kuka sukeyi na matukar tausayawa Elham. Mom Nu'aiym. [1/8, 10:32 PM] Sha'awa: *🌞HAFSAT ELHAM🌞* Billy Galadanchi Haske writer's Asso💡 Vote me on wattpad@68billygaladanchi. Sadaukar wa ga k'awata Hafsat Abubakar qaya (Elham).                             25 Zaman nutsuwa sukayi a gaban me martaba suna sauraren abinda zece yayinda yayi mintuna biyar suna saurarensa batare da yayi magana ba se can yayi gyaran murya xanna ya gyara zaman alkyabbar sa yace cikin nutsuwa "Abubuwa da dama sun faru a wannan masarautar,kuma sanin kanku ne wayannan abubuwan ba masu dad'i bane,dukda yake sace sultan da akayi bawai acikin nan Gidan aka shigo aka sace shiba amma sarai ganin sale da gawar jaririn ya sanya mun tabbatar cewar daga wannan masautar ne,tunda kuwa sale shekararshi kusan talatin da biyar koma fiye da haka anan gidan, koda ya zo nan shekaru nsa basu wuce sha biyar ba har tsufa yazo masa gashi muna tare,yanzu wannan d'anyen aikin ya janyowa mahaifiyar sultan kamuwa da cutar tab'in hankali,tofa ku sani na rantse da Allah mabuwayi duk wanda na kama dasa hannun shi aciki ko waye shi saina hukuntar dashi,sale na nan na saka an kawo mun shi a masarautar nan da kaina zan bincikeshi yana nan a tsohon prison na masu laifi a masarauta gobe da yardar Allah zan bashi azaba mafi muni da Zata saka yayi magana koda beso ba, Mamana kuwa idan visa dinsu ya zama ready zuwa wani watan zan turata India adubamun k'walwarta" jin yayi shiru Haj habiba tace "yallab'ai har yanzu munkasa gane dalilin kirannan da aka mana,bansaniba ko satar da kisan jinjirin ya shafi nida iya laina ne?" Wata mahaukaci yar tsawa ya daka mata wacce a lokaci d'aya ta razanar da ita matuk'a bama itaba d'auka cin mutanen dake wurin "Wlhy Habeebah zan nuna miki isa da k'arfin mulkin dana keda shi,idan baki saniba na sanar miki cike nake dake FAM kuma wlhy bazanci b'ata lokaciba wurin ganar dake kuskurenki kinji na fad'a miki,maza tashi ku bani wuri dukkanku" jiji a sab'ule dukkansu suka mik'e se adu'o i sukeyi na tonuwar asirin duk wanda ya aikata wannan mummunan aikin..... Wuraren k'arfe biyu na dare me martaba har lokacin be runtsaba yana nan yana zagayen gidan shida fadawanshi guda biyu, B'acin rai sam baya barinshi bacci tun faruwar wannan mummunan abin,muryar dayaji ne ya sanya ga dakatar dasu da hannu tare da nuni da hannu akan cewar su dakata "Kaga burshi Me martaba fa na sanar maka da gaske yakeyi wannan karon,so yake ya dauko mana rigima,sabida haka wannan babbar damace agaremu dawowar da akayi da sale gida prison na nan gidan,zuwa zakayi ka bashi zab'i Kodai na mallaka masa dukiya me yawa ya koma inda ba wanda ya sanshi kokuma ka kasheshi" kallonta burshi yayi yace " Haj nifa nasan halin saleh,yanda yasha burin adama dashi idan an samu nasarar kashe Yarima faruk yahau baze tab'a barin wannan masarautar ba,ki bani dama kurun na kasheshi" shiru yad'an ratsa wurin kan tace "Burshi wlhy kaga nifa harka da kisan kai ba santa nake ba,sanin kanka ne ko sultan d'innan bawai da gangan na kashe shiba hasalima dan kanshi ya mutu nida bansan a kashe kowa,ko yayyun Yarima ai gidan marayu na kaisu bana san harka da kisa karka kasheshi adai fitar dashi daga garin kota karfin tuwo ne" Sosa sumar sa yayi "Barin je in sumar da masu gadin in jashi kawai mubar nan" baya da baya me martaba ya koma seda burshi yayi gaba sannan suma sukabi bayanshi acan suna kallonshi ya wurga wata farar Leda yaja da baya had'e da toshe hancinsa,daya daga cikin fadawan dake tare da Sarki ne ya koma ya tashi wasu bardawa shi kuwa me martaba da daya suka lab'e wani wuri,shida sale suka fito sad'ad'a suka wuce Sarki ma suka bi bayanshi suna zuwa gate se gani sukayi fadawa sun zagayesu take aka kama Shegu...... Koda momy taji komai a bakin me martaba gigicewa tayi ta saka kuka dak'yar ya riqeta akan kartaje wurin habeeba har wannan lokacin ita habeeban batasan an damqe su sale ba kuma bata masan me martaba Yaji komai ba police kawai ya sanya akawo su zasu mata tambayoyi dole se ta fad'i inda takai yaran farko Wato yayyun Abdul sannan tayi bayanin zancen sultan menene laifinsa na sace shi kuma menene laifinsa na kasheshin da tayi......." Hannun Elham acikin na Abdul ya qurawa fuskarta ido data kumbura tayi ja jajir se sheqi takeyi na wahala bacci takeyi sakamakon allurar baccin da aka mata sabida ta samu nutsuwa tamkar matacciya lokaci zuwa lokaci takan kwab'e fuskarta tamkar me shirin yin kuka kota yamutsa fuskar wanda dana hakan d'abi'ar datane,tausayinta sosai yakeji se adu'a yake ta tofa mata haka yakeyi daman dare da rana bashida aikinyi se zaman mata adu'a yana sharar k'walla,yau kusan wata d'aya kenan da faruwar wannan al'amarin kuma har yanzu bata sauya zaniba, Haj Habeeba dai a binciken da akayi dukkanin yayyun Abdul datakai orphanage susu biyu sun rayu acan sedai gabaki d'ayansu sun bar orphanage d'in sunyi aure da yan uwansu na wurin sun fara aiki, ba kad'an ba momy tayi kuka ace kana d'an Sarki ka b'uge da rayuwar gidan marayu tsabar san kai irinna Habeeba da rashin imani,abin bak'in cikimma wai D'ayan me suna jabir Allah ya masa rasuwa yabar matarsa da yaronsu d'aya,se kabir ne aka samu wanda yayiwa Habeeba Allah ya isa cikin buhu buhu........A hankali ta bud'e idonta ta sau kesu akanshi Koda suke a lumshe,a wahalce tace "Yaa Abdul yunwa nakeji sosai ka bani wani abin,se inajin jikina tamkar wata mara lapiya" da sauri ya miqe jin tayi magana irinta masu hankali da sauri yazo ya d'agata yace "me kikeso Kici blossom?" Narkewa tayi ajikinshi sannan tasaka masa kuka "wai yaa Abdul da gaske ba mafarki nake ba sultan naga gawarshi jiya??" Qara qanqameta yayi yace yana kukan shima "Blossom kiyi hakuri ba mafarki kikeba,haka Allah ya tsara abinshi" wani kukan ta kuma fashewa dashi me ban tausayi... *Dan Allah Kuyi hakuri da wannan yan kwana kinnan bana samun zama* Mom Nu'aiym [1/8, 10:32 PM] Sha'awa: *🌞HAFSAT ELHAM🌞* Billy Galadanchi Haske writer's Asso💡 Vote me on wattpad@68billygaladanchi. Sadaukar wa ga k'awata Hafsat Abubakar qaya (Elham).                            26 Sosai me martaba yayi murnar samun Lapiyar hafsa,matsala d'aya ne ta kasa kwantar da hankalinta abincinma taqi ci yanzu tunda aka tabbatar mata da mutuwar sultan kuma a hanyar data ganshi take kuka,me martaba da kanshi ya shirya yaje asibitin domin har wannan lokacin asibitin basu sallameta sunce se sunga yanda jikinta ya qarayi,a saman kujerar da masu zuwa duba marasa lapiya ke zama anan me martaba ya zauna ya fuskanci Hafsat sosai ya tattare nutsuwar sa akanta yace bayan yayi gyaran murya "Mamana yaya Lapiyar jikinki? Ina fatar kin samu sauqi?" Sunkuyar da kanta tayi qasa cikeda kunya sannan tana hawayen data kasa tsaidasu tace "Naji sauqi ranka ya dade jiki Alhamdulillah" sake yin gyaran murya yayi yace "Na sanar miki karna kumajin kin kirani da wani sunan bayan daddy,Aini mahaifinki ne" murmushin k'arfin hali tayi cikin hawayenta tace murya na rawa "To daddy" shiru ya d'an ratsa d'akin na wani lokaci kan yace "Mamana ko kinsan cewa Allah mahaliccin dukkan komai shine da kanshi yake rayawa kuma shine yake kashewa alokacin dayaso kuma yayi muradi,kamar yanda yake Talauta wa a sanda yazo yakuma azurta a sanda yayi muradi,kana ya fitar da rayayye a cikin matacce kuma ya fitar da matacce a cikin rayayye?? Shin kokinsa ubangiji shiya keda iko akan dukkan kuma shine qadirin ala manyasha'u,kokina labarin cewar agaban idona akayiwa mahaifina yankan rago?? Shin Hafsatu bakida labarin cewar acikin k'addarori na rayuwa taki k'addarar ta fad'o ne acikin mafi sauqin d'auka?? Labari ya riskeni cewar tunda Allah ya baki Lapiyar ki bakyacin abinci bakida aiki se kuka,Anya Mamana kinwa adalci kuwa? Anya Hafsatu kin godewa Allah akan manya manyan ni'imominsa akanki? Ashe ba wani babbar ni'ima bane Allah ya baki na samun lapia ba sanda kika Zata ba? Ashe ba babbar ni'ima bane agareki kin tashi kiga dukkanin Dangin ki suna farin ciki da samun Lapiyar ki?? Shin ko kinsan cewar mutane da dama dasuka samu irin matsalar ki a rayuwa suna nan suna yawo akan titi,bola da juji Nanne makwancinsu, abincin su a bola ruwan shansu a bola sannan kuma suturun su ma daga juji,sabida kasawar Dangin su daga lalurarsu ya sanya ko damar zuwa asibiti basu samu ba,Ashe bakya kulawa masu irin laurarki koda me basu sadaka basa samu sabida kasancewar ana qyamarsu kuma ana tsoron su,lallai Mamana ki farga kuma kiyi istigfari ki godewa Allah da ni'imominsa masu tarin yawa akan ki,ki kuma gaggauta neman gafarar Allah domin kin kasa jure guntuwar kaddarar dabata taka kara ta karya ba,sultan koda a kar kashin kulawar ki yake tsaf Alla ze karb'e abinsa idan lokacinsa yayinda,nasani mutuwar yaro akwai zafi amma shin ko kinsan tanadin Mad'aukakin Sarki akanki??" To akul d'inki karnaji kuma narka ga kin qara saka damuwa aranki inshaa Allah zaki samu wasu 'ya'ya masu alkhairi da tarin albarka arayuwa kuma da yardar Alla sultan ze zamto daga cikin yara masu ceton iyayen su a gobe qiyama". Godiya tashiga yi masa da adu'a gamawa da duniya lapia, sosai yaji dad'i ya mata sallama sannan suka juya shida fadawa nsa........ *Bayan kwana biyar* Tun bayan da me martaba ya zo ya mata fad'a taji komai ya sure mata,ta mayarda lamuranta ga Allah take aka sallameta a asibiti, komawarsu gida ma ba karamar nutsuwa ya saukarwa Elham ba sabida mijinta yana matukar kulawa da ita,yauma kamar kullum da kanshi ya dafa mata Shawarma da pineapple drink ne sanyi,shine da kanshi yake bata tana ci sanda tayi dam,sannan yace "Blossom idan Kinyi sallan isha semu kwanta ko?" Kallonshi tayi La langwab'e kai sannan tace "Hubby kafin na kwanta wanka nakeso kamun kaga sanyi ake jikina kuma bayasan sanyi,ruwan zafi sosai zakamun wanka dashi seka shafamun mai den ka sakamun kayan bacci sannan kuma ka rarrasheni nayi bacci" murmushin sa me laushi ya sakar mata sannan yace "blossom duk wanna aikin ni kad'ai?"zaro ido tayi sannan ta shagwab'e fuska ta Turo baki " Ea mana kai kad'ai fa ko bazaka mun ba?" Mikewa yayi "waaa ni na isa?? Wannan ai dolene na miki har brush ma zan miki kannan" miqewa yayi har ya kusa Shiga d'aki ya juyo ya kalleta"blossom to muje mana" maqe kafad'a tayi "Ni bazani dakai naba,sedai ka d'agani zuwa bedroom d'in" dawowa ya d'auketa ya manna mata Sumba a wuya "Blossom wlhy rikicin ki seke amma yau d'innan zanyi maganin rigimar nan taki,sabida kwana biyu kinga ina raga miki ko?" Batace komai kurin dai ta yamutsa fuska ne,da kanshi ya mata wanka ya shirya ta sannan shima yayi wankan ya shirya kwanciya, fitilar d'akin ya kashe musu sannan ya kwanta suna fuskantar juna janyota kurin yayi ya rungumeta ajikinshi sosai amma ba abinda yakeda niyyar mata,ba kad'an ba Ellyn yaa moris tayi missing uncle baby d'inta cikin sanyin murya da shagwab'a tace "Uncle baby" hannunshi yafara d'aurawa akan waist nata shima ahankali yace "Aunty baby ya akayi ne?" Hannu tasaka ta daki bayanshi da wasa cikeda shagwab'a tace "Nice kuma Aunty baby Allah kuwan banaso?" D'an tsikarin ta yayi seda ta zabura sannan yace " to sanar dani Elilin moris me Nene?" K'ara matsawa tayi jikinshi sosai sannan tace "Bakinka da harshenka nakeso kabani aro" Murmushi yayi koda suke a duhu yace "Nabaki aronsu in nayi magana dame?" Sarai yagane inda ta dosa neman magana yakeyi,shura k'afa ta somayi "Dan Allah fa yaa Abdul wlhy matsu" hannunshi ya zura acikin yar rigar baccinta ya kaiwa dukiyar fulaninta cafka, yasoma murzawa a hankali,kasa hanashi tayi sabida wani irin desire takeji a wannan ranar bakinshi ta kama da kanta ta soma tsotsar harshensa tana mayarda numfarfashi kaikace cinye harshen zatayi shima d'in wannan kissing nashi datakeyi passionately ba k'aramin tayar masa da abubuwa sukayi ba,kuma yasha mamakinta domin wannan ne karanta na farko data masa haka,dan kanta tayi pulling out,sannan ta saqala hannunta a wuyanshi,tace cikin wata murya dabe tab'a ji tayi magana da ita "Hubby zaka barni nayi ganda nakeso dakai?" Hannunta dake wuyanshi ya d'aura nashi akai yana murzawa a hankali "sure u can my princess I'm all urs" k'ara matsawa tayi jikinshi ta manna masa wani kiss a k'irjinshi sannan lokaci d'aya ta tuna da hudubar Aunty husna " Elham wlhy karki cuci kanki ki samo tamkar wata hoto a wurin mijinki,komai sedai shi ya miki,kinga d'an breast d'innan na maza ma kamawa kake da baki kana wasa dashi da harshe kuma kana sha,sa annan kuma yan tagwayensa biyu na qasa ma wasa akeyi da su kuma ana ebe kunyar bayan amarci a tsotse masa su tatas,tako ina Abi da harshe ana lasa kuma hura masa kunne ana zura harshe a hankali ana wasa dashi aciki,dan Allah banda cutar kai a zare kunya" tunawa da wannan ya sanya ta saka harshe ta soma wasa da niples nashi tana lasa tana tsotse su,take ogan ya rikice harga Allah be san da wannan salon ba,bata inda bata zura harshenta tana lasar sa gaba d'aya Abdul yagama rikice wa yama rasa ina ze saka Elham sambatu yake mata tamkar wani zautacce ita kuwa tarasa mesa ta nemi kunyar ta tarasa kuma tamkar yana tunzurata wannan ihun dayake yi,dan kanta ta sakeshi kafin yayi wani yunkuri tuni ta d'areshi ta zura abar da kanta wannan ranar dai da kanta tayi aikin sunnah na neman lada....(saura kuma wata ta biyoni pc tace nayi iskanci,daga abun arziqi) Koda suka sauka dukkansu se wata uwar kunya ta lullub'e ta,bargo ta saka ta rufe jikinta yana kunna fitilar d'akin ta rufe idonta, d'agota yayi ya d'aura ta akan kirjinsa yace "Blossom na bazan tab'a manta alkhairanki agareni ba yau kin shayar dani dad'i wanda yafi dad'i dad'i,sanar dani a wace makarantar aka koyar dake rikitar da k'walwar mutum" hannayenta ta saka ta rufe fuskarta,hannunshi daya ya saka ya janye hannunta dake kan fuskar "Blossom kunya kuma,ai baki isa ba,wto a duhu shine kika rufe babin kunyar kikasha dad'inki shine yanzu zaki wani maqale wai kunya" Murmushi tayi "Dan Allah yaa Abdul nika qyaleni" "Naji zan qyaleki amma sekin yimun irin kiss d'in d'azu hot one d'innan" shagwab'a tashigayi da kanshi ya mata wanka ya gyara wuri har bedsheet ya sauya sannan ya rungume abarsa suka fara bacci"..... *Bayan watanni hudu* A London Abdul se fama fad'a yakeyi da Elham akan zuwa Niger "Allah ni bazan kuma wannan garinba sena haihu,baka ganin wahalar danake sha kuma fa,har yanzu ba abinda akayiwa Fulani Habeeba watakil ma idan ta ganni da ciki tayi asirin dazayi a zubar kaga nifa bazaniba,kuma ai bance dakai wai ni zanyi missing naka ba idan ka tafi abinka" Murmushi yayi yace "Haba blossom, dan Allah kiyi hakuri, to kinga tunda kin dauka haka barin sanar miki dalilin tafiyar momy ne fa batada lapiya kusan kwanan ta biyar a asibiti" zabura tayi kuma seta saka hawaye "Dama momy batada lapiya shine baka sanar dani ba?" Rarrashinta yashigayi harta haqura sannan washe gari suka dauki hanyar Niger.. Tun daga k'ofar gate d'in gidan jikinshi yayi sanyi ganin dandazon mutane kuma ga alama zaman karb'ar gaisuwar mutuwa akeyi kallon driver yayi yace "Kai me nake gani haka?? Waye ya rasu?" D'an kallonshi driver d'in yayi yace "yallab'ai dama ba'a sanar maka ba?" Cikeda rud'u yace "Meyene ba'a sanar mini ba?"....... Mom Nu'aiym [1/8, 10:32 PM] Sha'awa: *🌞HAFSAT ELHAM🌞* Billy Galadanchi Haske writer's Asso💡 Vote me on wattpad@68billygaladanchi. Sadaukar wa ga k'awata Hafsat Abubakar qaya (Elham).                            27 Kan wani yayi magana Elham ta saki wani razananniyar qara "Nashiga uku momyyyyyyy......" Dafeta yayi yace "Haba Elham menene abin ihu Bakima ji waya rasu bafa" ganin bata hayyacinta se kukan take taqi ta kulashi ya sanya ya tallafota jikinshi "Jijjigata yayi yace " Blossom ki nutsu mu Shiga cikin gida tukunna kinji" hannu ya sanya akan lips nashi ya girgizawa driver d'in kai alamar karya fad'a waya rasu d'in,sosai yashiga rud'ani kasancewar besan waye ya rasuba idan ko momy ce lallai da babbar matsala,a haka dai ya d'aura ta akan kafad'arsa suka Shiga ciki,a parlor momy mutane sunyi yawa har bazaka iya ratsasu ka shiga cikiba,juyawa sukayi da nufin zuwa sashen su aikam se ganin Fulani Habeeba sukayi da icce qaton gaske "Wlhy bazan yadda ba yanda ya Turo aka kashemun faruk daga dawowar shi haka shima zan kasheshi Mugu kawai azzalumi" hafsa da Abdul da suka kasa gane inda zancenta ya dosa se suka tsaya sororo suna kallonta,da gudunta ta saka wannan uban sandar ta kwad'a wa Abdul a kai,take ya zube wurin a asume,kallonta Hafsat tayi cikeda rud'u sannan ta mayarda dubanta zuwaga Abdul dake kwance jini na masa zuba a kai,durqusawa tayi tama kasa kukan dayazo mata duk wani tunani nata ya tsaya chack baya yi gabaki d'ayan jinin dake zagaye ajikinta yakai saqonni cikin kwanyarta ya dena yawo,a hankali ta saka hannu ta jijjigashi "Yaa Abdul" ta kira sunanshi a hankali ganin be motsa ba ya sanya ta dafe cikinta atake tasoma ganin jiri,isowar momy kenan da sauri tayi kansu,dafata Elham tayi sannan cikin kuka tace "Yaa Abdul momy wlhy zasu kashe mun shi,kalli fa Haj Habeeba ta kwala masa wannan mugun iccen,na rantse da wanda rayuwa ta take hannunsa idan ta kashemun. Yaa Abdul na sena kasheta nima,sekuma ta qara dafe cikin koda ta kalli kafafunta tafara bleeding over,wani sabon kara ta k'walla take itama ta zube wurin asume,mutane sun riqe Haj Habeeba ana mata Nasiha amma ta kafe lallai seta kashe Abdul,kai tsaye momy sawa tayi aka wuce dasu asibiti tana sharar kwallah tabi bayansu........Allah ya tsare Elham bata samu miscarriage ba Abdul kuwa buguwane kawai,shine ya soma farkawa ganin momy akanshi ya sanya a hankali yace " momy dan Allah sanar dani wai meya ke faruwa ne ??" Kallonshi tayi cikeda ban tausayi tace "Babana wlhy qaddarorine,kaga Faruk ne ya dawo jiya da safe ni bama nida lapiya, wlhy da safe koda hadimansa suka je b'angaren sa ganin ya jima be fito ba Sefa gawarsa suka tarar an dab'a masa wuqa a qahon zuci,shine fa Habeeba ke ihun Kaine ka kasheshi karya gaji sarauta" dafe kanshi dake Sara masa yayi "Wai ita wannan matar yaushe ne zatayi hankali,bazata barni ma Inji da mutuwar wulakancin gudan jinina ba seta zomun da wani salon iskanci wlhy wannan karon ko me martaba be isa ya hanani hukunta Habeeba ba abinta ya isheni,na shiga uku Farouq yanzu ya zanyi...." Rarrashin sa ta soma yayi seda ya hakura sannan yace "Momy ina Elham ?" Dan shiru kan can tace "Elham zazzabi takeyi tana wancan d'akin am bata gado" zabura yayi ya zare qarin ruwan da aka d'aura masa "Momy ta kani na ganta mana dan Allah ina ne d'akin?" Tana yunkurin hanashi amma ina seda yafita dole ta bishi sukayi d'akin, koda sukazo baccinta takeyi amma yaqi komawa d'akin sa sanda ta farka,a gaban momy ya rungume abarsa suka fara hawaye "Blossom na menene? Meya sameki haka?" Tama manta da wata momy hannun ta ta saka a saman wuyanshi tana shafawa a hankali "Bayan wannan matarne takeso ta kashemun kai,kagafa wannan qaton sandar ta buga maka,Allah ni idan har ta qara tab'aka sena rama maka muguwa ma da ita" rungume abarsa yayi ita dai momy murmushi kurun takeyi Elham ce takuma cewa "Yaa Abdul gobe zamu tafi London din ko?" "Noo princess sekin haihu tukunna" shagwab'a ta soma yi wanda ya sanya ba shiri momy tabar musu d'akin ganinfa dukkansu ba wanda yasan da zumanta acikinsu "Hubby wai ni waye ga rasu ne? Nagane momy ai d'azu tamaji sauqi" k'ara rungumeta yayi sosai "Habeebty se hakuri faruk ne akazo har cikin masarautar nan aka kasheshi jiya" zabura tayi ta dafe k'irji sosai ta sona kuka dakyar ya rarrasheta tayi shiru,sosai taji wannan mutuwar ta faruk musamman dayake ita dashi basuyi rabuwar dadi ba sam. A haka dai aka kammala zaman jana'iza yayinda Habeeba ta daurawa Abdul alhakin kisan faruk wanda kowa yasan haukanta takeyi sabida tun farko shi Abdul baya san sarautar balantana ma yayi kisa akanta......... Har cikin Elham yashiga watanshi na haihuwa suna Niger wannan umarnin mahaifin Abdul ne, wata rana da yamma Elham ta tashi da labor ita kad'ai Abdul yaje Kano amma a ranar ze dawo da kanta takira momy ta sanar mata tanajin labor ne yazo mata aikam cikin ikon Allah segashi momy da kanta ta karb'i haihuwar agida sabida koda tazo har kan baby ya soma shirin sulmiyowa ta sunkuco little princess d'inta kyakyawa me matukar kamanni da ita,har sumar kan babyn irin nata tayo,cikeda murna aka sanar a fada take agun me martaba yayi umarni da azo masa da babyn aikam take yabata kyautar wani katafaren kamfanin sa na saqa,kuma ya bata sunan momy,dama a fada suke zama tunda cikinta ya tsufa,se Wuraren 9 Abdul ya qaraso a fusace yazo gidan yana zuwa yaganta zaune a parlor itada wasu hadimai "Sannu da zuwa yaa Abdul?" Tace dashi tana me kallonshi ko duban inda take beyiba yace "yauwa" atakaice ya wuce ciki abinshi,mamakine ya kamata ta miqe ta baiwa dayar babyn ita kuma tabishi ciki yana daga cikin wardrobe tace "yaa Abdul lapiya dai kashigo cikin gida ranka abace?" Cikeda fusata yace "Bansaniba tsabar rainin hankali shine tun karfe hudu nake kiranki amma baki daga ba kuma har yanzu baki kirani back ba,ko kinaso...ya zaro kanshi daga wardrobe d'in yana mata magana atake yayi hooking gani ba ciki a jikinta,da sauri yazo ya riqeta da mamakinshi yace " Blossom yadai?" B'ata rai tayi "kaci gaba da masifan da kake mana,banda haka ina fama da labour zaka zo kanamun masifa,Allah ni banmasan inda na wurgar da phone naba,kuma fa nasha wuya,shine kokace ina Baby" wara idonshi cikeda mamaki "Blossom wai da gaske kin haihu? Wlhy babu wanda ya sanar mun hasalima ban lura ba ciki ajikinki ba se yanzu,me kika haifa mun ina babyn?" Murmushi tayi "Baby girl tana hannun hadima adama" wani uban tsalle ya daka yana ihun murna da gudu ya ruga parlor hadimanma sunsha mamakin yanda ya manta da wani girman kan mulki ya sungume y'arsa yana tsallen murna.. *ku taya Nu'aiym da adu'a wlhy bashida lapiya* Mom Nu'aiym [1/8, 10:32 PM] Sha'awa: 🌞HAFSAT ELHAM🌞* Billy Galadanchi Haske writer's Asso💡 Vote me on wattpad@68billygaladanchi. Sadaukar wa ga k'awata Hafsat Abubakar qaya (Elham).                           29 Zanen Elham ta duqufa tanayi na wani kata faren kamfanin da za'a bud'e a qasar Saudi wanda aka baiwa Abdul kwangila Shikuwa haka kawai yace lallai itace zatayi wannan zanen,yau kusan sati biyu tanayi,tausayinta yaji yabata wahala har kusan k'arfe biyu na dare tana abu d'aya dafa kafadar ta yayi yana daga kwance yace "Blossom mana ki kwanta inyaso da safe kya qarasa kinji?" Batare data dakatar da abinda takeyi ba tace "Hubby sauramun befi 30mnt ba plss kabarni na k'arasa" bece komai ba ya kwanta abinshi..... Lokacin da Abdul yaje gabatar da wannan zanen aka karb'a cikin jin dadi be boye musu ba akan cewar matarshice tayi zanen lokaci d'aya suka buqaci ganinta inda suka jinjina wa k'okarin datayi tare da kyaututtuka masu tsoka ciki kuwa harda gida sukutum kuma suma d'auketa aiki a babban kamfaninsu na Zane Zane, wannan abu ba karamin dad'i yayi Abdul ba alokaci d'aya ya nema mata gurbin karatu a jami'ar dake birnin London tafannin Zane,tana karatun tana aikinta haka suka rayu da juna cikeda Aminci kuma princess har wannan lokacin tana wurin momy susu kad'ai suke zaune  a london d'in suna sha'anin su,wani yammaci suka shirya zuwa yellow London Beach, dogon wandon jeans ta saka blue sa top red,sannan ta daura qatuwar rigar sanyi light brown a sama ta saka hula brown da shade ruwan k'asa shima, ba k'aramun kyau tayi shima kusan irin shigarta yayi suka d'auki hanya a beach elham matashin kai tayi da cinyar shi tana cin strawberries,hannunshi ya d'aura a saman kanta yace "Blossom dama fa inaso muyi wata magana dake" batare data baiwa abun muhimmanci ba tace "To bismillah ina jinka" d'an shiru yayi sanda ta qara cewa "Enhm hubby inajinka menene?" "So nakeyi ki haqura da karatun nan da kikeyi" sarqewa tayi da Berry d'in da takesha ta miqe da sauri ta juyo ta kalleshi "meya faru hubby? Meya sameka? Meye zesa na dena karatuna ? Wani abin na maka ne? Kokuwa dai haka kawai?" A rud'e ta jero masa wayannan tambayoyin, d'an murtuqe fuska yayi yace "Ba abinda kikamun kawai dai banaso ne ya isheni haka ke har aikin ma ki dena banaso" shiru tayi ta qura masa idonta da a wannan lokacin har sun sauya launi zuwa ja tamkar gaushin wuta,dak'yar ta furta "Yaa Abdul dan Allah kayi hakuri ka barni na qarasa karatuna kuma inajin dad'in aikina" harara ya wurga mata "Bazan haquraba naga alama kinaso ki maidani qaramun mutum sabida haka daga yau dukka biyun na dakatar dasu bazaki yiba" kasa riqe hawayenta tayi "Yaa Abdul lapiya lau fa muka fito daga gida kuma bansan menene ze shafi aiki na da karatuna da sauri haka ba mena maka?? Sauramun shekaru biyu kacal fa na kammala" k'ara tamke fuska yayi "Nasani sarai lapiya lau muka fito kuma ai wannan ba wai shawararki nake nema ba umarni ne nake baki,daga yau na dakatar dake daga zuwa skul d'in aikin ma ki rubuta resignation later ki basu,ke gaba d'aya ma Nigeria zaki koma da zama, shekaru biyun dakike cewa Sune suka rage miki bansan abinda zaki zamar mun ba idan na barki kika karasa sabida haka bazakiyi ba" zaro idonta tayi waje cikeda tashin hankali "Yaa Abdul to yanzu nikam mena zama arayuwa?? Konayi maka wani laifin ne hala?" Tsawa ya daka mata "Ba abinda kikamun kurin dai bazakiyi bane,kuma kinji na fad'a miki Karki k'aramun maganar skul d'innan kuma kafin hutun dakika d'auka ya qare lallai kiyi resigning" bata qara cewa komai ba haka ta share hawayenta a zuciyarta tana da d'a nanata innalillahi wa Innah ilaihirraji'un ba adadi,har suka bar wurin ba wanda ya kuma qara cewa komai,koda suka je gida kowa part dinsa ya nufa,a can Elham ta zauna ta dirza kukanta ma ishi,ko bayan isha bata fito ba haka Shina bebi ta kanta ba sabida abinda tamasa ba karamin b'ata ranshi tayi ba,yaga alama idan yayi wasa London din Zata haukatar masa da ita......washe gari ma bata fito ba sabida bataji dad'in yanda ya wofintar da itaba bayan kuma ba haka ya saba mata ba kuma ba rashin kunya ta masa ba,a part nata kurun tasha fresh milk ta shirya zuwa skul se time da takeda lecture sannan ta fito,a parlor ta same shi taje ta durkusa kaman yanda ta saba tace "Sabahul khair  hubby" kallonta yayi fuskarsa a daure yace a dakike "kin tashi lapiya?" "Lapiya lau zan tafi skul ne inada test" da mamaki ya d'ago ya kalleta amma seyayi kokarin Kawar da mamakinshi yace "Allah ya sanya ayi a Sa'a"  "Ameen" tace a taqaice taje ta dauki key a inda suke ajiye key na motocinsu tafice,wannan abin ba qaramun tunzura Abdul yayiba aranshi yace "Wato ma ban isa ba kenan? Lallai kuwa zan shayar dake mamaki" ita kuwa harga Allah bata dauka komai ba batayi tsammanin kawai sabida yace Zata dena zuwa skul ba shikenan Zata dena zuwa ta Zata zeje skul d'inne ya sanar musu Zata dakata tukunna,da wannan tayi hakan, wannan kenan. *Washe gari*       Koda Elham tayi wanka tazo ta d'auki key ba key kona mota d'aya a wurin dasuke ajiye Key's na motocinsu d'akinshi ta nufa nanma bayanan,d'aga wayarta tayi tayi kiranshi yana d'agawa suka gaisa tamkar ba komai tace "hubby ba key na mota ko d'aya awurin ajiyewa?" "Ina dukkanin motocin nine na siya da kudina?" Mamaki maganarshi ta bata a hankali tace "To hubby me kuma ya kawo wannan maganar?" Katse kiran kurin yayi batare dayayi magana ba  ita kuwa tabi kan wayar tata da kallo,sam bata fahimci inda ya dosa ba kuma ta kasa gane kan wannan fushin nashi batasan dalilin suna zaman zaman su lapiya ze tsiri masifa ba,haka tayita fama har sukayi wata fiye da d'aya baya kulata,wannan ya sanya tayi resigning dukda company d'in basuso hakan ba Amma ba yanda zasuyi kasancewar tamusu alqawarin bayan gama karatunta zata dawo wa aikinsu.......A parlor yana zaune yana karatun news paper yana kurbar coffee a hankali ya d'aura k'afa d'aya kan d'aya da madubi Sanye a idonshi tazo ta zameshi,kusa dashi ta zauna a k'asan kafafunshi tace cikin sanyin murya "Yaa Abdul dan Allah magana nakeso muyi dakai" beko kalli inda takeba bare ta saka ran ze saurareta hawayene ya soma sintiri a akan fuskarta takuma cewa "Yaa Abdul dan Allah Kayi hakuri wlhy nayi dukkanin abinda kakeso, karatun ma Kaine kawai nake jira kaje ka dakatar dani" rausayar da kanshi yayi D'auke da Murmushi akan fuskarshi me nuna irin kanki akeji kenan sannan yace yana me zummar barin wurin "Hafsat dama ke nake jira kiyi Hutu muje gida,so na kammala shirye shiryen da komai ranar Tuesday zamu wuce" kukan tane ya tsananta taje tasha gabanshi tana kuka ta qanqameshi "yaa Abdul wayene yake k'ok'arin shiga tsakanina dakai? Mena maka arayuwa dana cancanci wannan horon,ai kinnan dakaina na dakatar dashi karatunnan kuma qarashen hukuncinka kawai nake jira dan Allah Kayi hakuri" hannunshi ya saka ya b'amb'areta ajikinshi sannan yace bayan ya qura mata ido "A zatonki kin fini wayo,a tunaninki kin fini kwarewa a rayuwar turai a tsammanin ki bazan tab'a gano mugun abinda kike aika tamun ba,Toki sani wlhy nasan komai sabida haka kije can da taurin kanki,ina watannin mu biyu a haka baki damu ba,kinfi damuwa da karatunki,kinfi mayar da hankalinki akan neman ilimi to kije na dena hanaki karatun aikin kuma kije kiyi tayi ba ruwana dake da rayuwar ki gaba d'aya wlhy,ke har yanzu girman kanki kikeji da ganin Kud'in watace,so please kiyi sha'aninki" daga nan ya wuce ya barta gun a tsaye tana famar rusa uban kuka,gashi ta kasa nunawa kowa damuwarta. *Nigeria* Tunda suka isa momy ta hadasu da Princess suzo da ita,Abdul idan ba cikin mutane ba ba ruwanshi da Elham,ko abincinta baya ci,kallo daya me hankali ze mata ya gano sam bata cikin kwanciyar hankali,ko mahaifiyarta ta fahimci hakan kuma data tambayeta setace da ita stress din karatu ne ke damunta,dukda bata yarda ba amma haka tayita hakuri ta qyaleta, tafito daga gidan mahaifiyar ta zuwa sashen momy ga had'u da raihan haka kawai taji gabanta na faduwa cikin dakiya ta tsaya Su gaisa,bayan sun gaisa kamar abun arziqi sekuma Raihan ta kalleta tace "Elham sekuma mukaji zance mara dad'i Ashe yaa Abdul aure ze qara? Ni wlhy se yanzu ma nakeji biki saura sati uku,da har inajin haushi zai auro miki yar talaka wa sekuma na tuna duk k'anwar ja ce,Allah ya sanya alkhairi acikin bikin" haka Elham taji wannan zancen tamkar saukar aradu aranta tace "Aure kuma? Nashiga ukuna,dama akan wannan yaa Abdul ke wulakanta ni ? A fili kuma se tace tana me tattaro nutsuwarsa da kokarin wanzar da yalwar murmushin yaqe a fuskarta " Hakane Wlhy kinji dai abin alkhairi, nima kuma Senayi godiyar Allah sabida Sa'a had'aka kishi da 'ya'yan masu kisan kai wlhy gwara maka yan uwanka talakawa da basu san tashin hankali da hadama akan mulki ba" sumsum Raihan ta wuce batare da ta koma magana ba,anan tabar princess ta wuce gidansu a rikice,tana tuqi tana kuka duk tabi ta rud'e ta gigice, a d'akinshi ta wuce ta sameshi yana waya,zama tayi kusa dashi tana sharar k'wallah harya idar,kallonta yayi yace "Ke lapiya meye haka?" Tana sheshekar kuka tace " Yaa Abdul waida gaske zaka k'ara aure? Da gaske nanda sati uku aurenka ban saniba" tsaki yaja irin dama akan wannan kike mana kuka,gincirawa yayi yace yana Murmushi "Ea Hakane aure zanyi kuma nan da sati ukun,Meyene aciki to?" Zare ido tayi tace tana me riqe masa kafa "yaa Abdul mena maka zakamun hakan dan Allah Kayi hakuri,wlhy idan kamun haka mutuwa zanyi bana san kishiya tsoron ta nakeyi bazan iya had'a ka da wata ba" miqewa yayi a fusace "ke meye haka? Sabida wannan borin zaki zauna kinamun kukan raini,ubanwa ye yace ki aika tamun abinda kikemun tsabar mugunta, to dolene na auro uwa ta gari wa y'ay'ana wadda Zata kulamun da princess kuma ta haifa mun da yara masu tarbiya kuma na gari kekuma meye nawa na miki yanda kikeso karatu kikeso da gayu da bariki nikuma haqiqanin sunna nakeso na raya ta usuli bawai shirmen kiba" wani razanannen qara ta saka da kuka me ban tausayi...... Mom Nu'aiym [1/8, 10:32 PM] Sha'awa:      ☀️Hafsat Elham☀️ HASKE WRITER'S  ASSO. Wattpad@68billygaladanchi. Sadaukarwa GA qawata Hafsat  Abubuakar qaya.                                  30 Ethan abun duniya ya isheta,ta Kasa gane inda zancen Abdul ya nufa kome Tamasa ai bata cancanci wannan d'anyen hukuncin  ba, shin Anya Kuwa Abdul Yasan Abinda yake shirin   aikatawa? Da sauri ta miqe  ta zari key na motar ta ta nufi fada tuqin  takeyi Kawai amma Sam hankalinta baya Kan abinda takeyi se uban Kuka takeyi bata tab'a Zata cewar haka azabar kishi yakeyiba ji takeyi tamkar zuciyarta zata faso qirjinta ta fito wani tafarfasa da d'aci zuciyarta ke Mata ikon Allah ne kadai yakaita fada lapiya, Ko lucking  car batayiba ta afka cikin gidan  Kai tsaye part din mommy ta nufa, a parlo  ta Sameta itada Abdul Suna hira Kai tsaye Saman cinyoyin mommy ta d'are ta soma Kuka da sambatu "mommy Dan Allah Kiwa yaa Abdul magana yamun rai idan wani abun namasa yayi hakuri wlhy banason kishiya banso ya had'ani da kowa, karatun Kuma da bayaso shima na  dena bazan ma koma qasar ba" kukan takeyita baji ba Gani,d'agota mommy tayi " Elham Karki Zamo cikin mataye Marasa yarda da k'haddara ina  tunkafin kuzo me gidanki ya sanarmun Kinsan komai, shine kuma Yanzu zaki biyewa mutane su rikitar dake a karin banza,ina nan ina faman saka Miki albarka akan yarda da khaddarar dakikayi Ashe ba haka bane zaki biyewa mutanen banza su kaiki su Baro,to ki Sani zamu b'ata dake kishiya ba abun gudu bace 'yar uwace kuma abarso,karna kuma ganin kin Tashi hankalinki  Akan zancen kishiya  tunda mijinki Yana qaunarki, Maza  tashi ki koma dakinki yanma nayi" mamakin Jinwai tun Kan Suzo ta Sani  takeyi amma batace da mommy  komai ba Tamata godiya jiki ba k'wari ta Kama Hanyar waje tun a Hanya kafin taje gun mota take ganin Jiri ya soma kwasarta har Abdul yafito tana nan bata qarasa gun Mota ba tana tafiya tana bin bango tana layi ,ta bayanta ya tsaya Yana  nazarinta Harga Allah badasan ranshi zeyi aurennan ba amma yana mamakin sanda Elham tayi wayewar aikata abinda ta aikata ba wannan kadai zeyi ya rage jin zafinta aranshi, da k'yar ta isa mota koda tashiga ma sam batasan me yakeyiba, Allah shiyake halittar mata da mishi amma Elham tana daga cikin mataye Masu azababben kishin tsiya, da k'yar ta iya yin rivers  ta harbawa motar wuta ,mahaifinta ma dayaqi yarda  ya dena aikin gadin  binta yayi da Kallo harta bacewa ganinsa ganin yanda batako tsaya sunyi sallamaba kuma yaga ta sharara da wani uban gudu na Allah ya kiyaye....... Ganin haka ya sanya Abdul juyawa ciki aranshi yana Mata  aduar sauka lapiya.      Yana nan zaune wayar mommy ya soma ringing,d'agawa tayi ganin baquwar lamba ya sanya ta ajiye bata d'agaba ta mayarda dubanta Zuwa gareshi tace "Babana lapiya dai ka tafi kuma ka dawo? " Sosa kanshi yayi yace " Kawai Naji bazan iya zuwa  gidan Yanzu ba" kan tace wani abu wayar yafara ruri a Karo na biyu,ganin Sunan Elham NE,  da Sauri ta d'aga "Mamana ya akayi? " muryan namiji tajiyo "Haj bame wayar bace tayi accident  Anan kan Hanyar government  house kuma gata a kwance sedai ace Allah ya sauwaqa, Yanzu zamu wuce da ita babbar asibitin kwararru ta jiha shine muka Kira ganin Kamar number dinkine a sama kuma munma Kira wacce Muke tsammanin ta mijintane amma be d'aga ba" miqewa momyn tayi da salati d'auke abakinta "Malam injin dai Tana da rai? " ta wurgo masa wannan tambayar "Haj bazan iya cewa komai ba, Sabida banida masaniya,kurun dai na kula she's unconscious" a gigice ta ajiye wayar  ta Kalli Abdul "Babana tashi muje ba lapiya, Elham tayi accident  a Hanyar government  house" haukace mata ne  kurun beyiba amma Kam ya kusan zaucewa, Kasa tuqin yayi kurun yafito ya tsaya yana tunanin wane Hali Illy take cikin, seda driver yazo yajasu,suna zuwa wurin da akayi accident  d'in Abdul ya dakatar dasu Kallo daya Abdul yayiwa motocin guda biyu zufa ta keto masa Sam dazaran kaga Motan Elham Kasan akwai Marsala, fitowa yayi yaje wurin mutanen dake tsatsaye a wurin " Malam Dan Allah meya faru? " ya tambaya bayan ya musu sallama "AI malam wlhy wani mummunan hatsarine ya afku, wata yar matashiyar budurwace tazo dagudu k'addara ta afka mata Kasan wani lokaci idan ajalin mutun yazo bayan Sanin me yakeyi kurun baiwar Allah nan tayi maja da waccen motar ta ibar yashi kaga yanda motar ta ta dawo wlhy malam bakaga yarinyar ba gwanin ban tausayi ni inaga wlhy ko aure batayiba amma mutuwa tazo mata a bazata" wara idonshi yayi ya dafe k'irjinshi dake masa zafi yajuya zuwa mota maganganun da mutumin ya fad'a suna masa yawo aka, ya Kasa gaskata zancen mutumin,koda yashiga motar suna masa maganr kasa amsasu yayi kukan ma ya gagareshi a haka har suka k'arasa asibitin, shine ya fara fitowa daga cikin motar ya nufi cikin asibitin..... Kallon nutsuwa likitan yayiwa Abdul kan yace " Yarima tun kafin faruwar wannan accident d'in binciken mu ya nuna mana cewar matarka na cikin matsanancin damuwa, Zama mu iya cewa shine yayi sanadin wannan accident data Samu Sabida Tana d'auke da matsanancin ciwon zuciya Wanda akalla zefi shrkaru goma acikinta faruwar wannan abun ya sanya gaba d'aya ya taso mata lokaci d'aya had'uwar sa kuma da wannan accident yasanya kuma lokaci d'aya zuciyarta ta buga!!!" cike da razani Abdul ya d'ago ya kalleshi "Bugawar zuciya fa kace doctor? Mekenan Kake shirin sanarmun? Kuma ni iyakar sanina matana batada ciwon zuciya mema ze haifar mata da ciwon zuciya??" tasowa likitan yayi ya zago ya dafa kafad'arsa yace "Abdulrahman ko bansankaba bazan make k'aryaba balantana muntaso Dakai tun Muna Tara atare, ba dalilin maka haka,abu na gaba kuma ka sani matarka wannan ciwon ya jima ajikinta Danma Tanada qananun shekarune ya shekaru ne ya sanya be bayyana kanshi ba,na tabbatar damuwane ya haddasa mata wannan accident d'in Sannan kuma fad'uwar gaban data Samu yamun faruwar wannan Al'amarin shine ya haifar mata da Bugawar zuciya sabida a zahirin Gaskia bataji wasu raunuka masu yawaba dazasu kaita ga wannan abinba, buguwane kurun Se goguwa kad'an" nisawa Abdul yayi cikeda damuwa "To Yanzu doctor Meye abinyi?" shima doctor d'in nisawa yayi kan yace " Tsakani da Allah Abdul duk duniyarnan babu Wanda ze iya sanar maka halin da matarka zata kasance daga Yanzu zuwa kowane lokaci Allah ze iya bata lapiya kazalika daga Yanzu zuwa ko wane lokaci zata iya Rasa rayuwarta!" miqewa yayi "Haba Dr marwan ai ba'a Yankewa mutum hukunci irin haka, nasan Allah shike rayawa da kashewa amma Dan Allah ka taimaki rayuwar Hafsat da ikon da Allah ya maka kaji" Sosai likitan Yamasa bayani akan ciwon Nata sannan Yakoma d'akin da take ya qura mata Manya Manyan idonshi yana sauke siraran hawaye a hankali aranshi yanajin zafin abubuwan daya aikata agareta gani yakeyi tamkar ciwon zuciyannan Nata shine sanadi,momy ce tazo ta dafashi Taja hannunshi zuwa cikin d'akin tanemi sanin Meke damun Elham yana kuka ya sanar mata komai da doctor ya fada masa, ya qara da cewa "Mommy wlhy nasani nine Sila,wata qila zafin qaryar dana mata ne nace dake tasan zanyi aure batasan da zancen ba dawowarnan namune dazu takeji abakin Raihan, kuma Nafi watanni uku Bana kulata akan naga Tanasha qwayoyin Hana d'aukar ciki na sanya ta dakatar da aikinta na kuma tilastata barin zuwa makaranta, sabida taqi dena zuwa makaranta ya Sanya nadena shiga harkarta kuma na dakko zancen aure batare da sanin taba,hasalima yarinyar dazan aura ban Santaba seda Nazo nan Moh ne yanemamun ita dukdan na baqanta Ranta a zatona batasan haihuwa danine sabida taga qaddara na yawan fad'awa zuri'armu, Yanzu abinda doctor kecemun dama Anaso suna d'aga wa haihuwa qafa sabida condition nasu lapiya bata wadacesuba" Sosai mommy ta zazzaga masifa daga baya ta saka kuka sabida batasan yanda zatayi ba inhar Elham ta rasu ....... *Bayan Sati biyu* Elham taji sauqi Alhamdulillah, sedai har wannan lokacin batawa Abdul magana, idan ze shekara yana mata magana sedai ta tasashi agaba da kuka, bata ce masa ci Kanka amma takan d'an tab'a hira dasu mommy, Suna yawan kwantar mata da hankalin Kamar yanda doctor yace, a haka har taji sauqi ta warke Sarai aka sallameta....... A yanda Elham ta zata yau saura Kwana uku d'aurin auren batada labarin cewar tun Ranar datayi accident mommy ta Hana wannan maganar kuma Koda bata hanaba abun gaba d'aya ya ficewa Abdul akai,tana zaune a parlo ta gama Shan magungunan ta tana kubar fresh milk a hankali,zuwa yayi ya zauna kusa da ita yajanyo hannunta ya cura a nasa "Blossom ya jikinki?" da dan mamaki ta kalleshi kasancewar tasan ya dena kiranta da wannan sunan, a hankali ta kalleshi ta saya d'an murmushi a fuskarta sannan tace "Ango kasha mai Yanzu Kake shigowa" murmushin Shima yayi "Angon hafsatul Elham ba" bata kulashiba Yakuma cewa "Blossom Dan Allah kiyi hakuri ki gafarceni abin da na miki,wlhy Sam banzata akwai dalilin ki Nashan k'wayoyin Hana d'aukar cikiba kuma zancen auren danamiki Shima na janye har abada" gyaran murya tayi tukunna tace cikeda nutsuwa " Bance ka fasa auren kaba sabida ni nayi kad'an na haramta maka abinda Allah ya halatta akanka sedai Nasha mamakin sauyawar halayenka akan laifin da bakayi bincike akanshi ba,sabida ina tunanin damuwar dazaka Shiga idan har Kaji cewar ina cikin wannan halin na ciwon zuciya na boye makane sabida Karka shiga damuwa Nabi sha'warar doctor ne nayin tsarin Iyali sabida condition nawa,nakuma kasa sanar maka sabida kurun Karka gano ciwon dake damuna kashiga damuwa, Ashe Kai a wurinka ba haka bane kana iya watanni baka kulani zabida Kawai Dan wannan abin,amaimakon ma kazo ka sanarmun laifin dana maka Seka dauki wannan matakin" D'an dakatawa tayi sannan Taci gaba " Dama kaje ka auri wacce kayi niyyar auren Danni wlhy bazan zauna dakaiba kaficemun arai kuma karkayi tunanin samuna akusa" tana gama fad'ar Hakan tamiqe tabar wurin,da ido kurun ya bita bezata words Nata har zuci bane....... Wasa Farin girki fa Wuni d'aya cur ba Elham ba kayanta ya zaga gida da dangi kaf be gantaba kuma wayarta akashe hankalinshi ya tashi Matuka bashiba bar mommy...... Mom nuaiym [1/8, 10:32 PM] Sha'awa: ☀️Hafsat Elham☀️ HASKE WRITER'S ASSO. Sadaukarwa GA qawata hafsat Abubuakar qaya.   Vote me on wattpad @68billygaladanchi.                               31 Zaman dirshan Abdul yayi agaban mommy "Amma babana Kaima da kanka kasani Sam baka kyautawa mamana bako?  Namijin kirki baya tab'a  Yiwa mace yanda kayi,kaine babba agareta kyautuwa yayi kan zauna ka nusar da ita kuskurenta amma ka dauki fushi batare da sanin ainahin meta maka ba, Yanzu Hafsat ta girma ta mallaki hankalin Kanta na tabbatar bazatayi abinda ze cutar da itaba,ba inda zanje nemanta kuma wlhy bazan tab'a  nema maka yafiyartaba sabida kayi Hali irinna qaranta gaba d'aya kayi Hali irinna mutane Marasa dattako musamman dakayi shirin aure bada sanintaba kuma kazo kace ta sani, ni maza bansan jin komai ka bani wuri" yana cikin qunan rai na Rashin hafsatul Elham,yatashi kurun batare da yayi magana ba Yabar  wurin, Kai tsaye part  nasu ya nufa ya tarar mahaifin hafsa na gida,cikeda girma mawa ya gayar  dashi bayan nan ya sunkui Dakai sannan yace "Baba dama zancen Elham yau kwana biyu kenan bata gidana kuma tun ranar data tafi Nazo Nan Inna tacemun  bata nan kuma bata wurin mommy na duk dangi na zaga Sosai bata nan gashi ta Rufe wayanta baya tafiya" nisawa Abbanta yayi sannan yace " yallab'ai naji wannan labarin tun kusan kwana biyu da suka wuce abakin Fulani k'arama hakuri shine kadai  abinda zan iya baka kuma Insshaa Allah  zan Saka a Nemo ta duk inda take zan  kuma mata fada sosai sedai dan Allah ka sanya gaskia da Amana a dukkanin lamuranka abaiwa aure haqqinsa" godiya yayiwa baba sannan yamasa sallama ya tafi, kamar kullum yauma kasa Bacci yayi yana Famar tunanin Elham.....Elham zaune tana breakfast agidan Aunty husna,husnan ta shigo a d'akin  tanemi zauna kusan da ita tace "Hafsat Yanzu inaga lokaci yayi da zaki Buda wayarki hakanan,  Yanzu wannan horon ya wuce Sena gaba kuma naqin d'aukar  waya idan ya kira" murmushi  tayi tace "Tom auntie barin kunna" batafi mintuna biyu da buda wayarba mommy ta kirata jikinta na rawa ta d'aga "mommy Ina kwana? " da murmushi d'auke a fuskarta tamkar  Elham  d'in  na gabanta ta amsata " lapiya qalau mamana, nace fushinnan harda ni acikinta?  Tunda kika tafi ban qara jinki ba ko waya ernan?? " cikeda jin kunya tace "Momy Dan Allah kiyi hakuri wayar ne ba caji" "Ba komai Elham kuma Naji dadin yanda kikayi gwara ki Nuna masa kuskuren sa,laifinki d'aya  tunda kika tafi baki neme Niba,kinku masan hankali na baze kwantaba inhar bansan halin dakike cikiba, Yanzu kina ina?" "Ina gidan Aunty husna mommy yayar Saam,dan Allah kiyi hakuri" murmushi  mommy  ta qarayi  " Ba komai Elham, Lallai kiyi zamanki seya gane kuskurensa bakuma zan sanar kowa nasan Inda kikeba" godiya yayiwa mommy sannan sukayi sallama.... Messages  na Abdul ba'a ma maganarsu sannan kuma ga voice messages ,yana ganin delivery report na messages  nashi ya tabbatar ta bude wayarta ya shiga kiranta baji ba gani,har kuka yayi sanda yaganta online  yayi mata magana tayi banza dashi, DAGA bisani kuma tayi blocking  nashi gaba d'aya, wannan qara tabbatar masa cewar Lallai Elham ta dauka da zafi.....     *Bayan kwana biyu* Abdul duk ya gama haukacewa sabida Yanzu yama dena samun wayar Elham kwata kwata,yagama tara qasumba yayi fayau ya rame, a bangaren Elham Kuwa phone Nata ya fad'a cikin kofin ruwan shayi zuwa Yanzu taqosa taga mijinta abin qaunarta,amma tanajin kunyar Aunty husna sabida ba hakan suka tsara ba....Tare da husna suka fita zuwa babban shop na siyar da wayoyi me suna season 7,domin tana so ta sake waya tun a hanya Abdul yayi kicibis da fuskarta take yabi bayan motar ta husna har shop d'in  waya ta d'auko kirar Samsung Galaxy j5 tazo Domin  biya da POS nasu karaf Abdul  ya Janye kwalin ya turawa mutumin hade da zaro Kudi a aljihunshi yace nawane?? Biya yayi ita kuwa ta bishi da ido kurun tana kallonshi cikeda mamakin yanda akayi yasan inda take,  kasa magana tayi bayan ya biya yaja hannunta tana turjewa amma ina yariqeta gagam,husna dai sebin bayansu tayi tana murmushi, daidai motarshi yakaita yace tamkar yayi "Na rikeki da Girman Allah kishiga motarnan Zamuyi magana" ko motsawa batayiba kurun dai ta qura masa ido tana qoqarin tare kwallar dake shirin silalo mata,tarasa dalilin daya sanya ganinsa ya saukar mata da wata irin ni'ima da kasala ga wani irin Farin ciki daya mamayeta,kannewa kurun takeyi,yayi magana harya gaji amma ko Motsi bata yiba,husna dake bayansu Itace tace " Hafsat namiki izini dakibi mijinki gobe Zanzo gidan naki kuma zan aiko miki da kayanki yau bayan isha" turo bakinta tayi cikeda jin haushin hukuncin  Aunty husna " Ni Allah aunty husna bazan wani bishiba  zuwa zanyi ya dinga bani wahala akarin banza banciba ban Shaba" b'ata fuska husna tayi "Hafsat ina wasa Dakene nace kibi mijin ki yanzu" tana zumb'ura baki tana qunquni  tabude  gidan baya  tashiga Shima ya zaga dayan gefen ya zauna,ya zaro dubu d'aya  ya miqawa driver  yace "Kaje gidan zamuzo daga baya" ba musu ya karb'a yafita, shikuwa ya mayarda dubanshi zuwaga Elham ita dashi suka qurawa Juna ido na kusan mintuna biyar batare da kowansu yayi magana ba,Abdul dukya birkice ya rasa ta ina ze soma magana ma  ita Kuwa se ruwan hawaye take tsiyaya, da k'yar  ya iya daurewa ya tallafota k'irjinshi se patting  na bayanta yaso mayi cikin sigar rarrashi a hankali yara d'a mata a kunne "Blossom I'm so sorry, Dan Allah ki yafeni wlhy bansan haka bane, Nima daurewa kurun nakeyi ina miki abinda namiki  bawai Asan raina bane, na rokeki kiyi afuwa agareni ki dawo muci gaba da rayuwarmu ta aure cikin jin dad'i" bata iya cewa dashi qalaba kurun dai bata dena kukan ba, dakyar ya lallaab'ata tayi shiru suka dauki Hanyar  gida bamewa wani magana acikinsu,tana zuwa d'akin ta tashiga ta kwanta kan gado tana rusar Uban kuka, Ahaka yashigo ya sameta zuwa yayi ya kwanta a bayanta ya rungumota ta baya yace cikin sigar rarrashi  "blossom  could u plss find a place in ur heart to forgive me?  Could u plss let all dat happened  and let bygone be bygone?,blossom  I beg of you  with all my heart  to please  forget  everything" batai magana ba duk wannan surutun daya gama rattabawa,kuka kawai ya saka mata da iya k'arfinsa tamkar wani qaramun yaro,mamakine ya kamata jin yana mata kuka hadda jiniya lokaci  d'aya jikinta yayi Sanyi ta miqe tsaye zuwa tayi ta tsaya gabanshi ta sanya hannayenta ta tallafo kanshi,be dena kukan ba kuma besamu Damar cewa komai ba, a hankali tace itama tana  kukan " hubby plss kukafa? Noo plss ba girman ka bane, Allah trust me komai ya wuce awurina" be iya dena kukan ba kurun dai ya taqaita sautin kukan,ganin ya kasa dena kukan ya sanya lokaci d'aya  tayi shutting  bakinsa ta hanyar manna Nata da nashin tana tsotsa a hankali bashiri yabiye mata sunfi 30mnt suna abu d'aya tamkar bazasu qyale juna ba,itane da kanta tayi pulling out  sannan ta sakala hannunta cikin sumar kanshi tana shafa a hankali,murya na rawa tace "I so much miss u hubby, Nafi watanni biyar banji d'umin jikinka ba, nasha wahalan rashinka kusa Dani, wlhy yaa Abdul duk Girman laifin dana maka idan ka qara mun horo irin wannan bazan tab'a gafarta maka ba, zan barka har abada" matsowa yayi da ita jikinshi yana hawaye har cikin b'argon sa yakejin qaunarta na ratsa shi " wlhy blossom bazan qaraba,har Abada bazan qara gudinkiba nafiki shan wuya dabana tare dake, Dan Allah promise me that you will never leave me ever again " qara cura kanta jikinshi tana me shaqar daddad'an qamshin jikinshi data jima bata jishiba,a hankali ya soma sarrafata cikin salo na qwarewa bata wani tsaya yangaba sabida Harga Allah Hafsat tana cikin matayen dabasa jurar rashin namiji kusa dasu,kuma wannan lokacin data d'iba ita kadai tasan irin wahalar datasha akan rashin sahibinta kusa da iya, a wannan Daren Kuwa kasa qosawa sukayi da juna sabida dukkansu Sunji ajikinsu...... *Bayan shekaru hudu*      A London  princess  zaune tana koyawa qannenta Amir da Amira homework da aka basu a skul,yarinya er shekaru bakwai se qoqarin ba kadan ba,ita kuwa masifar qaunar twins masu matukar kamada Elham takeyi, ta dawo London sabida karatunsu......Zuwa Yanzu Elham ta samu matsayi Sosai awurin aikinsu tayi Kudi daidai gwargwado,harta siyawa mahaifinsu gida yabar aikin gadi......      A parlor tana zaune tana shan milkshake Abdul ya shigo,hannu ya saka ya warce cup d'in ta bayanta da wasa aikam ta diro Tabi bayanshi suka kwasa a guje se daki,ajiye cup d'in  yayi ya kamata yashiga shafarta tako ina take itama ta biye mishi suka shiga faranta ran junansu,tana wasa da sumar kanshi tace "Hubby shekaru uku,plss kabani guzy baby yau dinnan  , i really wanna have a baby again" laquce mata Hanci yayi yace "Elham har Yanzu bazaki dena shed'ana bako? Bakya jin kunya na kike cewa na miki cikiba? " murmushi tayi tace "kaga ni idan yanga kakeji ko bazaka iyaba kwanta na hau" Dariya suka saka dukkansu sannan yace "Allah yau senayi Maganin bakinnan naki".......    Yayan Abdul shine aka radawa sarautar garin nasu,yayinda sukaci gaba da rayuwarsu cikeda jin dadin rayuwa da kaunar juna, Elham d'auke take da ciki na watanni biyar se fatan sauka lapiya...... Tammat bihamdillah.. Inda nayi kuskure Allah ya gafarceni, Inda kuma nayi daidai Allah yasa ya amfanemu baki d'aya. Mom nuaiym ce👌☀️Hafsat Elham☀️ HASKE WRITER'S ASSO. Sadaukarwa GA qawata hafsat Abubuakar qaya.   Vote me on wattpad @68billygaladanchi.                               31 Zaman dirshan Abdul yayi agaban mommy "Amma babana Kaima da kanka kasani Sam baka kyautawa mamana bako?  Namijin kirki baya tab'a  Yiwa mace yanda kayi,kaine babba agareta kyautuwa yayi kan zauna ka nusar da ita kuskurenta amma ka dauki fushi batare da sanin ainahin meta maka ba, Yanzu Hafsat ta girma ta mallaki hankalin Kanta na tabbatar bazatayi abinda ze cutar da itaba,ba inda zanje nemanta kuma wlhy bazan tab'a  nema maka yafiyartaba sabida kayi Hali irinna qaranta gaba d'aya kayi Hali irinna mutane Marasa dattako musamman dakayi shirin aure bada sanintaba kuma kazo kace ta sani, ni maza bansan jin komai ka bani wuri" yana cikin qunan rai na Rashin hafsatul Elham,yatashi kurun batare da yayi magana ba Yabar  wurin, Kai tsaye part  nasu ya nufa ya tarar mahaifin hafsa na gida,cikeda girma mawa ya gayar  dashi bayan nan ya sunkui Dakai sannan yace "Baba dama zancen Elham yau kwana biyu kenan bata gidana kuma tun ranar data tafi Nazo Nan Inna tacemun  bata nan kuma bata wurin mommy na duk dangi na zaga Sosai bata nan gashi ta Rufe wayanta baya tafiya" nisawa Abbanta yayi sannan yace " yallab'ai naji wannan labarin tun kusan kwana biyu da suka wuce abakin Fulani k'arama hakuri shine kadai  abinda zan iya baka kuma Insshaa Allah  zan Saka a Nemo ta duk inda take zan  kuma mata fada sosai sedai dan Allah ka sanya gaskia da Amana a dukkanin lamuranka abaiwa aure haqqinsa" godiya yayiwa baba sannan yamasa sallama ya tafi, kamar kullum yauma kasa Bacci yayi yana Famar tunanin Elham.....Elham zaune tana breakfast agidan Aunty husna,husnan ta shigo a d'akin  tanemi zauna kusan da ita tace "Hafsat Yanzu inaga lokaci yayi da zaki Buda wayarki hakanan,  Yanzu wannan horon ya wuce Sena gaba kuma naqin d'aukar  waya idan ya kira" murmushi  tayi tace "Tom auntie barin kunna" batafi mintuna biyu da buda wayarba mommy ta kirata jikinta na rawa ta d'aga "mommy Ina kwana? " da murmushi d'auke a fuskarta tamkar  Elham  d'in  na gabanta ta amsata " lapiya qalau mamana, nace fushinnan harda ni acikinta?  Tunda kika tafi ban qara jinki ba ko waya ernan?? " cikeda jin kunya tace "Momy Dan Allah kiyi hakuri wayar ne ba caji" "Ba komai Elham kuma Naji dadin yanda kikayi gwara ki Nuna masa kuskuren sa,laifinki d'aya  tunda kika tafi baki neme Niba,kinku masan hankali na baze kwantaba inhar bansan halin dakike cikiba, Yanzu kina ina?" "Ina gidan Aunty husna mommy yayar Saam,dan Allah kiyi hakuri" murmushi  mommy  ta qarayi  " Ba komai Elham, Lallai kiyi zamanki seya gane kuskurensa bakuma zan sanar kowa nasan Inda kikeba" godiya yayiwa mommy sannan sukayi sallama.... Messages  na Abdul ba'a ma maganarsu sannan kuma ga voice messages ,yana ganin delivery report na messages  nashi ya tabbatar ta bude wayarta ya shiga kiranta baji ba gani,har kuka yayi sanda yaganta online  yayi mata magana tayi banza dashi, DAGA bisani kuma tayi blocking  nashi gaba d'aya, wannan qara tabbatar masa cewar Lallai Elham ta dauka da zafi.....     *Bayan kwana biyu* Abdul duk ya gama haukacewa sabida Yanzu yama dena samun wayar Elham kwata kwata,yagama tara qasumba yayi fayau ya rame, a bangaren Elham Kuwa phone Nata ya fad'a cikin kofin ruwan shayi zuwa Yanzu taqosa taga mijinta abin qaunarta,amma tanajin kunyar Aunty husna sabida ba hakan suka tsara ba....Tare da husna suka fita zuwa babban shop na siyar da wayoyi me suna season 7,domin tana so ta sake waya tun a hanya Abdul yayi kicibis da fuskarta take yabi bayan motar ta husna har shop d'in  waya ta d'auko kirar Samsung Galaxy j5 tazo Domin  biya da POS nasu karaf Abdul  ya Janye kwalin ya turawa mutumin hade da zaro Kudi a aljihunshi yace nawane?? Biya yayi ita kuwa ta bishi da ido kurun tana kallonshi cikeda mamakin yanda akayi yasan inda take,  kasa magana tayi bayan ya biya yaja hannunta tana turjewa amma ina yariqeta gagam,husna dai sebin bayansu tayi tana murmushi, daidai motarshi yakaita yace tamkar yayi "Na rikeki da Girman Allah kishiga motarnan Zamuyi magana" ko motsawa batayiba kurun dai ta qura masa ido tana qoqarin tare kwallar dake shirin silalo mata,tarasa dalilin daya sanya ganinsa ya saukar mata da wata irin ni'ima da kasala ga wani irin Farin ciki daya mamayeta,kannewa kurun takeyi,yayi magana harya gaji amma ko Motsi bata yiba,husna dake bayansu Itace tace " Hafsat namiki izini dakibi mijinki gobe Zanzo gidan naki kuma zan aiko miki da kayanki yau bayan isha" turo bakinta tayi cikeda jin haushin hukuncin  Aunty husna " Ni Allah aunty husna bazan wani bishiba  zuwa zanyi ya dinga bani wahala akarin banza banciba ban Shaba" b'ata fuska husna tayi "Hafsat ina wasa Dakene nace kibi mijin ki yanzu" tana zumb'ura baki tana qunquni  tabude  gidan baya  tashiga Shima ya zaga dayan gefen ya zauna,ya zaro dubu d'aya  ya miqawa driver  yace "Kaje gidan zamuzo daga baya" ba musu ya karb'a yafita, shikuwa ya mayarda dubanshi zuwaga Elham ita dashi suka qurawa Juna ido na kusan mintuna biyar batare da kowansu yayi magana ba,Abdul dukya birkice ya rasa ta ina ze soma magana ma  ita Kuwa se ruwan hawaye take tsiyaya, da k'yar  ya iya daurewa ya tallafota k'irjinshi se patting  na bayanta yaso mayi cikin sigar rarrashi a hankali yara d'a mata a kunne "Blossom I'm so sorry, Dan Allah ki yafeni wlhy bansan haka bane, Nima daurewa kurun nakeyi ina miki abinda namiki  bawai Asan raina bane, na rokeki kiyi afuwa agareni ki dawo muci gaba da rayuwarmu ta aure cikin jin dad'i" bata iya cewa dashi qalaba kurun dai bata dena kukan ba, dakyar ya lallaab'ata tayi shiru suka dauki Hanyar  gida bamewa wani magana acikinsu,tana zuwa d'akin ta tashiga ta kwanta kan gado tana rusar Uban kuka, Ahaka yashigo ya sameta zuwa yayi ya kwanta a bayanta ya rungumota ta baya yace cikin sigar rarrashi  "blossom  could u plss find a place in ur heart to forgive me?  Could u plss let all dat happened  and let bygone be bygone?,blossom  I beg of you  with all my heart  to please  forget  everything" batai magana ba duk wannan surutun daya gama rattabawa,kuka kawai ya saka mata da iya k'arfinsa tamkar wani qaramun yaro,mamakine ya kamata jin yana mata kuka hadda jiniya lokaci  d'aya jikinta yayi Sanyi ta miqe tsaye zuwa tayi ta tsaya gabanshi ta sanya hannayenta ta tallafo kanshi,be dena kukan ba kuma besamu Damar cewa komai ba, a hankali tace itama tana  kukan " hubby plss kukafa? Noo plss ba girman ka bane, Allah trust me komai ya wuce awurina" be iya dena kukan ba kurun dai ya taqaita sautin kukan,ganin ya kasa dena kukan ya sanya lokaci d'aya  tayi shutting  bakinsa ta hanyar manna Nata da nashin tana tsotsa a hankali bashiri yabiye mata sunfi 30mnt suna abu d'aya tamkar bazasu qyale juna ba,itane da kanta tayi pulling out  sannan ta sakala hannunta cikin sumar kanshi tana shafa a hankali,murya na rawa tace "I so much miss u hubby, Nafi watanni biyar banji d'umin jikinka ba, nasha wahalan rashinka kusa Dani, wlhy yaa Abdul duk Girman laifin dana maka idan ka qara mun horo irin wannan bazan tab'a gafarta maka ba, zan barka har abada" matsowa yayi da ita jikinshi yana hawaye har cikin b'argon sa yakejin qaunarta na ratsa shi " wlhy blossom bazan qaraba,har Abada bazan qara gudinkiba nafiki shan wuya dabana tare dake, Dan Allah promise me that you will never leave me ever again " qara cura kanta jikinshi tana me shaqar daddad'an qamshin jikinshi data jima bata jishiba,a hankali ya soma sarrafata cikin salo na qwarewa bata wani tsaya yangaba sabida Harga Allah Hafsat tana cikin matayen dabasa jurar rashin namiji kusa dasu,kuma wannan lokacin data d'iba ita kadai tasan irin wahalar datasha akan rashin sahibinta kusa da iya, a wannan Daren Kuwa kasa qosawa sukayi da juna sabida dukkansu Sunji ajikinsu...... *Bayan shekaru hudu*      A London  princess  zaune tana koyawa qannenta Amir da Amira homework da aka basu a skul,yarinya er shekaru bakwai se qoqarin ba kadan ba,ita kuwa masifar qaunar twins masu matukar kamada Elham takeyi, ta dawo London sabida karatunsu......Zuwa Yanzu Elham ta samu matsayi Sosai awurin aikinsu tayi Kudi daidai gwargwado,harta siyawa mahaifinsu gida yabar aikin gadi......      A parlor tana zaune tana shan milkshake Abdul ya shigo,hannu ya saka ya warce cup d'in ta bayanta da wasa aikam ta diro Tabi bayanshi suka kwasa a guje se daki,ajiye cup d'in  yayi ya kamata yashiga shafarta tako ina take itama ta biye mishi suka shiga faranta ran junansu,tana wasa da sumar kanshi tace "Hubby shekaru uku,plss kabani guzy baby yau dinnan  , i really wanna have a baby again" laquce mata Hanci yayi yace "Elham har Yanzu bazaki dena shed'ana bako? Bakya jin kunya na kike cewa na miki cikiba? " murmushi tayi tace "kaga ni idan yanga kakeji ko bazaka iyaba kwanta na hau" Dariya suka saka dukkansu sannan yace "Allah yau senayi Maganin bakinnan naki".......    Yayan Abdul shine aka radawa sarautar garin nasu,yayinda sukaci gaba da rayuwarsu cikeda jin dadin rayuwa da kaunar juna, Elham d'auke take da ciki na watanni biyar se fatan sauka lapiya...... Tammat bihamdillah.. Inda nayi kuskure Allah ya gafarceni, Inda kuma nayi daidai Allah yasa ya amfanemu baki d'aya. Mom nuaiym ce👌 [1/9, 1:16 PM] Billy Galadanchi: *🌞HAFSAT ELHAM🌞* Billy Galadanchi Haske writer's Asso💡 Vote me on wattpad@68billygaladanchi. Sadaukar wa ga k'awata Hafsat Abubakar qaya (Elham).                          28 Zama yayi ya qurawa fuskar babyn ido "Blossom kinsan Allah princess dake take matukar kama ni bana iya babban ta inda ajikin ta ba irin naki bane,Allah saka miki da alkhairi kin kawomun Little princess na lapiya" Murmushi kurun ta masa ya qara cewa "Blossom baba da Innah sunci kujerar hajjin bana da na umrah Inshaa Allah,ke kuwa kyautar ki me tsoka ne kuma zamune yawon zaga duniya se inda maina ya qarqare" murmushin takumayi tace "Kaji daddy ma yayi wa baby kyautar kampani guda daya duk ita kad'ai?" Murmushi yayi yasan mahaifin shi ze iya "Allah ubangiji ya saka maka da alkhairi ya d'auka kaka yakuma sanya ka gama da duniya da kuma iyayenka lapiya Ameen" hannunta ya murza tare da nasa "Thanks for the warm prayers blossom, Allah ya sama miki da alkhairi kuma ya miki albarka" murmushin dai me sanyi ta kuma sakar masa "Ameen ya Allah hubby na I love you" da sauri ya d'ago ya kalle ta "Blossom me kikace?" Bata fahimci inda ya dosa ba tace "yaushe?" "Blossom do you really mean it?" Sake kallonshi tayi da mamaki dauke a fuskar ta "wai mene?" "That you love me mana?" Dariya tayi "Sure mana I do,mesa ka tambaya?" Ihun murna ya saka ga miqe sa princess a hannunsa...."princess u mean everything to me,wlhy ke alherice ranar zuwanki duniya ranar naji Kalmar dana jima ina muradin ji daga Elilina, thank you Allah for blessing me with d light of my life, thank you so much Elham wlhy na dad'e ina so naji wannan Kalmar daga gareki,I love you too beyond expectation,words cnt tell how much I love blossom " dariyar dabatasan dalilinta ba ta tsinci kanta tanayi,had'esu yayi ya rungume....... *Bayan wata biyar*      "Blossom nidai zanaennan daki kamun yayi wlhy inaga kawai zan ajiye nawa na basu wannan nakin Allah motar Zata had'e ba k'arya" Murmushi tamasa "wai da gaske yaa Abdul yanzu seka biyemun nifa wlhy kurun nature nane son Zane ko a school sena zauna nayita yin zane na na shirme iri iri,ko wannan fa nakan nake gani idan kana zanen motar ko gida shine na zana nawa" hannunta ya kama "Blossom trust me wlhy ke d'innan kinada tulin baiwa a kanki ki yarda dani ba wasa wannan zanen naki zeyi masoya kuma nasani zasu yi mota sak zanen kinnan its so unique and classy" Murmushi tabishi dashi ya kwashe takardun yace office ya zaune ya mayarda zanen tsaf kan system  yayi kyau matuka...... Ba k'aramun dad'i yajiba sanda oganshi ya karb'i aikin yakuma yaba masa sosai, koda ya shigo gidan d'agata yayi sama yana sowa dak'yar ya direta ta "Blossom wlhy Kinyi kin gama had'e ni,wai kinsan Oga yace zanen yayi,2016 d'innan ita zasu fara lunching kuma har meeting akayi an haska zanen kuma kowa ya yaba,blossom ur a blessing to me,dan Allah zoki ga wannan zanen na gidan da kikayi shima,wlhy fitar dashi zanyi" k'ura masa ido kurun tayi cikeda rashin gaskata zancensa,tace "Hubby are u serious?" "Wlhy da gaske blossom, na sanar miki Zane baiwa ne kuma Allah ya rigada ya baki so yanzu kullum kece zaki riqa tayani aikin Zane,kuma dukkanin abinda na samu a wannan zanen zamu rabashi biyu ni d'aya ke d'aya sabida aikin kine" b'ata fuska tayi , "plss ya Abdul karmu soma haka dakai,Allah de ya sanyawa dukkanin ayyukanka albarka Ameen" Murmushi yayi ya saka mata albarka ba adadi.   A gida kuwa me martaba ya dage tukuru wurin koyarda sabon Yarima har kokin mulki,sabida yarjewar Yarima Abdul akan yahau kan karagar mulkin mahaifinsu sabida shi sam bashida Sha'awa kuma shine Babba agidan ko bayan hakan,ba laifi yana ganewa kuma yanada hankali sosai ga ilimi da Allah ya wadatashi dashi na boko dana arbiya kasancewa gidan marayun daya tashi suna basu ilimi ba wasa. *Bayan shekara d'aya*      Da Kansu suka zo gida daga London somin sun yaye Princess, suna so su kawota wrin momy dama abisa umarnin ta,sunji dad'in zuwa Nigeria wannan karon matuka,satinsu uku suka wuce umrah daga can kuma suka haura Dubai se chilling dinsu sukeyi kasancewar princess tana wurin momy, kwance hafsa take saman k'irjin yaa Abdul tana wasa da kwantaccen gashin dake kwance luff a k'irjin nasa,harshe takai takai lashi kan nipples d'inshi cikeda zolaya tasan seya motsa,tayi yinkurin barin jikinshi,janyota yayi yana dariya "blossom kin isa kuwa? Ai yanda kika fara neman tsokanar nan sekin k'arasa shi" d'an dukan k'irjinshi tayi "kaga nifa yaa Abdul bazan iya da jarabanka ba,sabida haka kurun ka k'ara aure ina zan iya da wannan fitinar" dariya sosai yayi yace "nine jarababben anan ko? Ke bakya ganin yanda kika daddage kika nacemun duk Kinbi kin jarabe ina ko yanzu zagaye ne kikayi kinaso shine kika lalubo ni da dubaru" Turo bakinta tayi sosai "wlhy Allah jifa banaso yaa Abdul nifa dama wasa nake maka" hancinta yaja "Naji wasar kikemun zoki kwanta nima wasa nake miki" kwanciya tayi nesa dashi amma batace komai ba harga Allah taji matukar kunya daya gano lagonta,kuma ji take tamkar yau bazata iya bacci ba Idan har bata kasance tare da hubbyn ta,banza shi kuwa yayi da ita sabida sarai ya gano ta so takeyi su kasance atare, Sunfi awa kowa shiru ita azatonta ma yayi bacci kurin seta Saka kuka se sheshekar kukanta yajiyo,matsawa yayi ya juyo da ita ta fuskanceshi " yaa Salam blossom meye abin kuka kuma me aka miki" share hawayen nata tayi ce "ba komai kainane yakemun ciwo" sarai ya sani k'arya takeyi kurin tana yine sabida batasan yanda zatayi da sha'awar shiba data adda beta,bece da ita komai ba kurun rungumeta yayi ya manna bakinshi a nata,ba shiri ta biye masa Sunfi 20mnt suna abu d'aya kaikace ze cire mata bakin gaba daya ita kuwa tamkar wacce taga wani abinci haka take tsotsar harshensa,da kanshi yayi pulling out "Blossom nabaki maganin ciwon kan ya  isheki kuwa?" Batayi magana kurun ta fara saukar masa kasala a haka har suka gamsar da junansu,dariya ya soma yi mata bayan komai ya natsa "Ni blossom bana ganewa kan wannan ciwon kan naki,kowa idan yana ciwon kai zakiga yanashan pain reliver amma Kefa sam kullum Salon naki ciwon kan a jikina kike cire pain reliever d'in,ni zuwa ma zanyi in qara aure,idan namiki kwana biyu naje nayiwa amaryata kwana biyu,jara banki nann yayi isheni zaki ta tsemun jinin jikina" zumburo baki tayi "Allah ni bazaka mun wata kishiya ba,kumama bakai bane ba kake wani hanani kanka sekace wani abun k'a ida kullum kai se bayan kwana biyu,ni Nafiso kullum" dariya yayi harda k'walla sannan yace "Amun afuwa blossom zan riqa yi kullum so biyu bama d'aya ba,ni dariya kika bani wlhy kin gama cemun jarababbe Ashe kece haka, dama da kanki kikeyi kenan" dukan k'irjinshi ta d'ingayi da wasa cikeda shagwaba "Allah ni yaa Abdul ka dena banaso" kwasarta yayi yanaci gaba da dariyar se toilet ya direta   (Mata dan Allah adena b'oye wa namiji idan ana buqatarsa wlhy cutar da kanmu mukeyi, akarin banza bayan Allah da kanshi shine yabamu damar moruwa da ni'imomin dake jikin junan mu matuqar muka kasance ma'auta,tom itadai hafsa ta taimaki kanta wollah) Dan Allah kumun uzuri,wlhy yau dak'yar nayo wannan,ayyukanne sukamun yawa Downloaded from GNOVELS.COM.NG This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG For feedback and support Facebook : https://facebook.com/gnovels Twitter : https://twitter.com/gnovels Telegram : https://t.me/gnovels