Downloaded from GNOVELS.COM.NG This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG For feedback and support Facebook : https://facebook.com/gnovels Twitter : https://twitter.com/gnovels Telegram : https://t.me/gnovels TYPING 📲Fri, Dec 13/24 4:51pm YUSRAH MUSA ABUBAKAR✨✨✨. 💕MÏÑÏSTËR ÄSHRÄF💕 WHATSAPP NO:+234 8160983083 yusrahmusaabubakar@gmail.com A*W*A ANNURI WRITER'S ASSOCIATION 💫 Home of hospitality and harmony gidan karbar mutane hannu biyu da zaman lafiya ÀÑÑÙRÌ haske le'ka gidan kowa koda ma'kiya na kallon ka ramin kura sai'ya'yan. ____________________ ____________________________ ___________________________________ STÔRY WRITTEN ND EDITING YUSRAH MUSA ABUBAKAR ✍️Mrs Äl'ämëëñ Ähmäd çë. ¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶ I'm here to make you happy educated domin nifa I have no girman kai if you fushi dani to wallahi you are just 6atawa kan k lokaci. THINK BEFORE YOU DO Always be watchful don't take risk don't try to get lost try to protect your life always, be good be helpful people will like u to be a happy child like my daughter Fatima Zarah Ilham little Zarahn Aunty people will like u. °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° 📿BISMILLLAHIR RAHMANUR RAHIM📿 In the name of Allah the must benefits and the must merciful ALLAH THE MOST HIGH DOESN'T SLEEP ALLAH THE MOST HIGH IS PURE HE ACCEPT ONLY WHAT IS PURE we love our NABI no success without him he's the light of every darkness he's the mirror of our life he's the answer to every question he've no limits, ya rasulullah muna sonka fiye darai da iyaye da dukiya muna sonka fiye da dukka muradi na zuciya ANNABI mu mu ganka shine buri na zuciya lamince mu ganka ya mai salsabil da khausara. ÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷ SHORT STÔRY ÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷ 💦Yüsëëñ Sïr Äl-ämëëñ çë💦 PG____01&02 Zaune wani kyakkyawan farin mutum yake a wani office da takardu a gabansa yana dubawa a shekaru zai Kai shekara arba'in da biyar fari ne kamar ka ta'ba jikinsa jini ya fita a saman sa akwai katon photon sa banne a jikin bangon yana tsaye kamar ka kirashi ya amsa a qasan photon an rubuta sunansa da manyan ba'ki ASHRAF AHMAD da kyakkyawan murmushi na kwatance akan kyakkyawar fuskarsa sa, aiki kawai yake baya ko d'auke hannunsa ya huta sai lokacin da akai Kiran wayarsa sannan ya d'ago yana kallon wayar tasa ganin me kiran yasa yadan ja tsaki batare daya d'aga ba ya mayar da hankalinsa kan abinda yake yi har Kiran ya katse wani ya shigo amma ko inda wayar take bai sake kalla ba balle ya damu da ya d'auka saima saka wayar dayai a silent dan kada ringtone d'in yasa yayi mistake kawai yaci gaba da aikinsa. Tsaye wata cikakkiyar mace take tasha ado ta soke d'aurin kwali kallo d'aya zakai mata kasan yar duniya ce ranta a'bace tana kallon wayar dake hannunta gashi Kiran yana zuwa amma ba'a d'agawa Kuma tasan yana gurin yana ganin kiran huci ta fitar daidai ta sake Kira ya katse tai jifa da wayar tana zama akan kujera tare da dafe kanta tace. "Wai meyasa Alhaji Ashraf yake min haka wannan ai wulakanci ne nasan yana ganin kiran amma ya'ki d'agawa dan ya 6ata min rai meyasa zai min haka kodan yaga na damu dashi humm dole zan dau mataki a kansa kafin ya haukata min 'kwa'kwalwata haba wacce irin masifa ce wannan"?. Ta'be baki hajiya Bilkisu dake gefe tai tana kallon yadda fuskar qawar tata take dan'kare da ba'kin ciki da damuwa tace "kema wallahi Hajiya Sadiya kina da abun mamaki dole dan zamuyi tafiya saikin sanar masa kamar wani mijinki ina ruwansa da wannan harkar ki share shi mu tafi idan mun dawo koma menene saiki je har office din nasa ki same shi". Kai Hajiya Sadiya ta girgiza tare da furzar da huci tana cire glass d'in idonta tace "amma dai Bilkisu ke kanki sheda ce irin son da nakewa Ashraf ji nake kamar nayi hauka taya bazan damu da halin ko in kular da yake nuna min ba yadda nake binsa sau da qafa dan ya aureni ko ubana iyakaci kenan amma baya gani kullum labarin daya ne taya kike tunanin zan samu nutsuwa idan bai saurare niba"? Rausaya kai Hajiya Bilkisu tai tana cewa. "Humm kece fa kika d'au abun nan da zafi wallahi yadda Alhaji Ashraf yake bazai ta'ba sauraron kiba a haka kinsan meyasa? Ta fad'a tana kallon Hajiya Sadiya wacce ta zuba Mata ido jiran amsa cigaba hajiya Bilkisu tai da cewa "saboda kina yawan zubar da kimar ki a gabansa kina nuna masa kamar baki da aji kin zauce kin susuce da ace zaki iya da kin d'auke masa wuta kona wata biyu zuwa uku ne ki daina kiransa ki daina zuwa nemasa wallahi Ina fad'a Miki da kansa zaki ji ya kira wayarki yana tambayar kina lafiya amma kullum kina kiransa kina zarya a office dinsa taya kuwa bazai Miki wulakanci ba"?. Sauke numfashi Hajiya Sadiya tai tana kallon hajiya Bilkisu tace "amma taya kike tunanin zan iya share Alhaji Ashraf na wata uku batare Dana kirasa ba? Humm aiko kwana uku bazan iya ba balle wata uku so kike na mutu? domin ko sati nayi ban ganshi ko naji muryarsa sainayi rashin lafiya to kuma me kike zato idan aka ce yau rana ta fito ban daga waya na kirashi ba saidai a d'auke ni zuwa asibiti Bilkisu ni kaina bansan wanne irin so nake yiwa Ashraf ba hankali bazai kwatanto shiba misali bazai iya musalta shiba sannan kalmomi bazasu iya fad'ar saba kawai ki kyale ni nayi gwagwarmaya ta na samu soyayyar sa kuma burina a kansa shine na aure shi" tana rufe baki hajiya Bilkisu ta she'ke da dariya tana tafa mata tace "gaskiya ne saida ke qawata to Allah ya taimake ki ya soki nikam ina ganin hakan abu ne mai wuya domin kina kallon yadda naci ba'kar azabar soyayyar Alhaji Mukhtar amma qarshe ya barni ya auri wata balle ke da Alhaji Ashraf bai baki goyon baya ba ina tunanin yadda abun zai kasance da kamar wuya fa" ta karasa maganar tana yiwa Hajiya Sadiya kallon babu nasara a gabanta Kuma hakan zahiri ne a bayyane yake abunda take yi Mata hasashe gaskiya ne Alhaji Ashraf yasan Hajiya Sadiya da irin kalar rayuwar barikin da take na zaman kanta sannan dama gata babbar yar siyasa ce ko ina da ita ake shiga a fita dukkan wasu halayenta saidai ya baiwa wani labari shiyasa ko kad'an bai sake mata balle tayi tunanin zata samu fuskar dazai amsa mata gaisuwarta ma ko tayi zaton a gaba zata samu shiga a gurin sa inaaa!!! Never in history............... Ganin yadda tayi nisa cikin tunani yasa hajiya Bilkisu dafa kafad'arta tana d'an girgiza ta da sauri Hajiya Sadiya ta dawo daga tunanin da take tana kallon Hajiya Bilkisu wacce ta d'age mata gira tana cewa "wato kema kin fahimci hakan bazai ta'ba kasancewa gaskiya ba ko? To yanzu ya kamata ki daina wahalar da kanki a kansa ki tsaya ki saita rayuwarki ki kama kasuwancin ki kawai". Kai Hajiya Sadiya ta girgiza jikinta yana qara yin sanyi da karya mata gwiwar da hajiya Bilkisu take yi cikin rashin jin dad'i da walwala tace "a'a dan Allah Bilkisu kiyi shiru haka ki daina fad'a kar kisa zuciyata tai bindiga ko hawan jini ya kama ni abinda nace zai kasance alkhairi muna nan dake saina auri Ashraf ko yana so ko baya so ta hanyar halak ko haram tunda ni Ina sons........ shiru Hajiya Sadiya tai bata karasa ba sakamakon jin qarar takalmi ana saukowa daga upstairs tasan maybe Husnah ce ta shirya zata tafi school Kuma bata so ta ri'ka riskarta tana irin wad'annan maganganun juyawa tai tana kallon budurwar data sauko tasha kwalliya da handbag a hannunta bata rataya a kafad'a ba karasowa cikin parlon tai itama tana kallon Hajiya Sadiyan tace. "Momy zan je school". Kaita d'aga mata tana cewa "ok Husnah sai kin dawo". Bangaren da hajiya Bilkisu take xaune ta juya tana cewa "Ina kwanan Momyn Meelat"? Da fara'a hajiya Bilkisu tace "lafiya kalau Husnah ya kike"? "Ina lafiya Momyn Meelat" ta fad'a daidai zata wuce Hajiya Sadiya ta dakatar da ita da cewa "am Husnah zamuyi tafiya yau nida hajiya Bilkisu idan kin dawo daga school ki wuce gidan Hajiya Maryam ki zauna tare da ita idan mun dawo next week zan Kira ki a waya saiki dawo Kinga babu dad'i ki zauna a gida ke kad'ai" jin abinda Hajiya Sadiyan ke cewa yasa Husnah ta juyo fuska ba walwala tana cewa "Momy Ina Kuma zakuje har sati guda baku dawo ba dan Allah Momy ki rage fita da wannan yawace yawacen". Tana rufe baki Hajiya Sadiya ta sakar mata wata zazzafar harara tana cewa "kinga Husnah ki kiyaye ni akan irin wannan tambayar taki mara tushe Ina ruwanki da inda zanje wato abinda nake fad'a miki dabam kema wanda kike fad'a min dabam ko? Humm Husnah ke 'yata ce bana son ki ri'ka nuna kamar kina zargina dan haka ki kama kanki! ki kama kanki!! ki kama kanki!!! Sau uku na fad'a miki ko? Idan kunne yaji jiki ya tsira get to the point" ta karasa maganar cikin tsawa tana nuna mata kofar fita da hannu jikin a sanyaye Husnah ta juya ranta a'bace ta fice a parlon yayin da Hajiya Sadiya ta hau bala'i iri iri. "Ji yarinya da rainin hankali wato kenan maganata ta tabbata zargina take da wani abu nake aikatawa a 6oye ko? Tunda gashi harta fad'a lallai Husnah kina gaf dana 6alla miki qafa kici gaba da samun ido zanyi maganinki saina fasa idon gulmar inga da abunda zaki saka min idon haba ba dama kayi abun arziki idon yarinya yana kai kamar itace ta haifeka mutwww". Mi'kewa Hajiya Bilkisu tai tana gyara d'aurin kwali ta sake turo shi gaba ganin abun bana qarewa bane Hajiya Sadiya ta riga ta hauro tad'au xafi tace "kinga dan Allah d'auko gyalen ki mu fita hakan da kike sake 6ata mana lokaci kike yi ita wacce kike fadan a kanta batasan kina yi ba tunda ta fice saiki ha'kuri mu tafi kar lokacin mu ya fita" ta karasa maganar tana kallon yadda Hajiya Sadiyan take qara fusata sai data sake dannawa Husnah d'anyar ashar kafin ta juya tana hawa stairs d'in ta d'auko mayafinta da handbag suka fita a gidan. F.U.D ~🏙️Federal University Dutse🏙️~ D'alibai ne keta faman shiga maza da mata ta kowacce kofa dake school d'in daidai Husnah tayi parking wata farar mota mai qirar Mercedes-Benz mai ba'kin glass itama tai parking a kusa da ita kallon motar Husnah tai tana murmushi kafin ta bud'e kofa ta fita kusan tare suka fito da mamallakiyar motar hummm wata zu'ke'kiyar kyakkyawar budurwa ce sanye da bakar tsadaddiyar doguwar riga mai adon stone tayi Mata mugun kyau fara ce 'kar 'kar Kuma beauty no filter bata da qiba siririya ce amma ba irin can d'in nan ba tana da shape sosai a shekaru zatai ashirin da d'aya fuskarta sanye da qaramin farin glass wanda yasa fuskar tata ta sake kyau ga ba'kin gashi me kamar saje kwance a gefe da gefen fuskarta ta sanya lipstick mai walwali ko yaya ta motsa bakinta sai she'ki ga uwa uba dogon hanci da dimple duka 6arikan kumatu biyun suna lotsawa ko batai magana ba, bata tsaya rufe murfin motar ba da sauri ta taho yayin da Husnah itama da murnarta ta tafi gurin ta suna had'uwa suka rungume juna cike da farin ciki Husnah ta d'ago tana cewa. "Ke Nabilah Tajuddeen kin ganki kuwa"?. Ta fad'a harda d'an zaro ido murmushi Nabilah tai tana cewa "meya faru"?. "Babu komai kawai gani nayi yau har kinfi kullum ma kyau anya kuwa Nabilah ba akwai wani sirrin da kike yiba fad'a min Nima na fara" dariya Nabilah tai jin abinda Husnan tace yasa ta kalleta tana cewa "kai Husnah kina da abun dariya me zanyi kuwa ba wani sirri wallahi da nake yi ni dama haka nake" kai Husnah ta girgiza tana cewa "a'a ba haka kike ba Beelat gaskiya yau kin zarta ko yaushe Allah ba da wasa nake miki ba yau kinfi kyau" murmushi Nabilah tai tana cewa "to nagode qawata muje ko" ta fad'a tana komata gaban motarta ta d'auko key da wayarta da kuma handbag d'inta suka shiga cikin school d'in tafiya mai nisa sukai kafin su shiga department d'insu fal suka samu gurin da d'alibai kowa ya inda yake zaune shiru hankalinsu nakan karatu sakamakon exam da za'ai musu suma zama sukai batare dasun kula kowa ba suka fara karatun karasowar wani lecturer tare da wata babbar malama itama kallon Nabilah yayi da d'an murmushi a fuskarsa yace. "Nabilah Sïr Tajuddeen". A bazata taji an Kira sunanta saidai tad'au murya domin babu a inda zaiyi magana bata ganeshi ba d'agowa tai tana kallon sa da ido yai mata magana d'an 6ata fuska tai a ranta tace "gaskiya gayen nan yaja yana matsa min fa bana son yawan maganar da yake min" daidai sun wuce ta bishi da kallo kafin taja qaramin tsaki tana cire glass d'in idonta ta mayar dashi cikin handbag d'inta tana mi'kewa ta kalli Husnah wacce itama ta d'ago tana kallon ta da mamaki tace "wai Beelat zuwa zakiyi"? Kaita d'aga tana cewa "eh zuwa zanyi amma wannan shine karo na qarshe da zanyi masa gargad'in kada ya sake kulani domin na fuskanci take-taken wannan lecturer saina fito na nuna masa 6acin raina a fili maybe daya rabu dani". Sauke ajiyar zuciya tai jin abinda Nabilan tace yasa ta mi'ke itama tana daukar tata handbag d'in ta rataya tana cewa "ok indai haka ne bake kad'ai zakije ba tunda kince Kinga alamar take-taken sa bai kamata ace na bari kin had'u dashi ku biyu ba Nabilah ina sonki kamar jini na bazan so wani abun cutarwa ya sameki ba" kai Nabilah ta jinjina cikin jin dad'in nuna kulawarta da Husnah keyi ta saki murmushi tana cewa. "Shikenan muje" Tafiya sukai suna zancen su da nishad'i harda dariya kamar wanda zasu kar'bo gift har suka karasa inda yace yana zaune ya d'ora kafa d'aya kan d'aya karasawa sukai da sallama ganinsu biyu ne yasa ya had'e rai ya d'aure fuska tamm ya kumbura kamar fulawar da yis ya mata yawa ya fara harare harare da muzurai alamar Husnah ta d'an basu gurin amma yafi karfin bud'e baki yace ta d'an basu gurin itama taga hakan amma ta share tana d'auke kai sake gyara zama yayi yana qare cika da batsewa wanda suma a nasu bangaren sunja sun tsaya kowacce ranta a 'bace musamman Husnah da kwata kwata bai kwanta mata arai ba har tafi Nabilan fusata ganin lokaci yana qurewa bai fad'a mata dalilin kiranta ba sannan su basu tafi sunyi karatunsu ba yasa Nabilah tace. "Sir Ahmad gani". Banza yayi ya'ki magana kusan mintu biyar ya sharesu had'a ido sukai suna kallon juna da idon sukai magana a tare suka kuya zasu bar wajen da sauri domin suje suyi abinda ke gabansu ko bari suyi taku baiyi ba muryarsa a hasale yace. "Nabilah come back here" ya fad'a cikin tsawa wanda yasa gabadayan su suka juyo suna binsa da kallon mamaki daidai ya taso yana gyara agogon hannunsa ya karaso ransa a mugun had'e yace "bamu wuri zamuyi magana" Husnah tasan da ita yake amma saita dake tana cewa "sister nace fa Sir Ahmad". "Ko wacece taki nace ki bamu guri". Tsaki Husnah taja a ranta kamar bazata bar gurin ba saboda yadda take matukar jin haushin sa amma sai ta juya tana barin gurin saida yaga wucewarta yaja tsuka yana mayar da kallonsa kan Nabilah wacce tai bala'in d'auke kai ta murtuke fuskarta yace. "Nabilah what is it"?. Shiru tai masa ko inda yake bata kallo saboda takaici saida ya sake tambayar ta karo na biyu amsar farko da zata bashi tace. "Sir Ahmad nifa Ina da wanda zan aura dan Allah ka rabu dani" ta fad'a tana sake had'e fuska zuba mata ido yayi yana kallon ta har kallon ya wuce misali ganin kawai lokaci zai 6ata mata tace "zan tafi" zata juya ya dakatar da ita "Nabilah" tsayawa tai a fusace ta juyo zatai magana ya girgiza mata Kai yana kara matsowa inda take kamar me shirin ri'ke mata hannu da sauri ta sake matsawa ya kuma binta karo na biyu ganin idan tai sake masa zai iya taba mata jiki yasa kamar walkiya ta juya fiiiii kafin ya farga har tayi nisa yaso yabita a baya amma saiya tsaya yana hard'e hannunsa ya zuba mata ido harta 'kule kafin yayi murmushi yana jinjina kai a ransa yana ji yana son yarinyar nan da aure da zata amince masa amma zai lalla6ata idan ta'ki hummm that mean war kenan dan wallahi bazai iya ha'kura da ita ba dole zaisan yadda zaiyi ko bai aureta ba zaiyi kokari yaga ya samu abinda yake so a wajenta juyawa yayi shima yana barin gurin. Husnah tana tsaye a bayan block d'in tana jiran Nabilah sai kuma ta ganta ta 6ullo a fusace tana sauri gyaran murya tai mata wanda yasa ta juyo da sauri tana kallon ta tare da sauke ajiyar zuciya ta waiga baya ko Sir Ahmad ya biyota karasowa Husnah tai fuskarta ba walwala tace. "Wai nikam dan Allah me Sir Ahmad d'in nan yake nufi bake da yake takurawa Beelat ni kaina na fara gajiya da wannan aikin banzar nasa kullum bazai bari kiyi abun arziki ba idan munzo school daga Kira sai Kira tsabar bulkumanci da sakalci Allah daga yau bazaki sake zuwa inda yake ba kome zaiyi domin naga d'anyar kan nasa ya wuce inda nake tunani haba jama'a" tsaki Nabilah tai tana cewa. "Share sa muje kawai indai yana da zuciya daga yau bazai sake kulani ba wallahi so yake yayi asarar takardar aikinsa domin matukar yaci gaba da matsa min zan hadashi da Daddy kawai ya dauka min mataki" Kai Husnah ta d'aga tana cewa "basai yaci gaba da matsa miki lamba ba kawai ki sanar masa a d'au mataki idan ma za'a bashi transfer lokacinsa baiyi ba saiya sani aikinsa zai 6ata muje kawai kar a shiga mana exam d'in ma muna nan" wucewa sukai kamar sun sani kuwa suna zuwa daidai lokacin shiga ko zama basuyi ba suka zarce cikin class d'insu,,,basu fito daga jarrabawar ba sai kusan karfe d'aya da rabi a ranar suna fitowa kowa ya fara alwala suna tafiya sukai sallah su Nabilah sun jima a gurin sallar domin saida la'asar tazo sukayi sannan suka taso Kai tsaye gurin motarsu suka nufa saida sukai sallama Nabilah harta bud'e mota zata shiga ta tsaya tana cewa. "Husnah dan Allah karki manta gobe ki fito da wuri tunda naji kince gidan kanwar Momyn zaki tafi" Kai Husnah ta d'aga tana cewa "ok sai Allah ya kaimu gobe ki gaida mun da Mum sosai Beelat" "ok bye" Nabilah ta fad'a tana shiga motarta itama saida ta Husnah ta wuce sannan tabi bayanta ita ta nufi Yalwawa Nabilah Kuma ta nufi Yadi ko a hanya tunanin yadda zata 6ullowa da al'amarin Sir Ähmäd takeyi amma ta bari a ranta tunda yau ta fad'a masa ya rabu da ita idan yaji shikenan idan baiji ba koda za'a 6ata masa paper saita fad'awa Daddy domin ya d'aukar mata mataki irin su Sir Ahmad ba mutanen da za'a zubawa ido bane domin shi mutum ne d'anye kuma ga6o ta tabbata matukar ta share bata fad'a anyi maganinsa ba uhmm tana tsoron abinda zai faru a gaba Allah ma ya kiyaye. Horn tayi a kofar gate d'insu me gadin dake zaune ta ciki ya tashi ya bud'e mata ta shiga sakamakon tana sa rai maybe zata fita da yamma yasa bata Kai motarta cikin rumfar parking d'in motoci ta barta a baya baya ta kasheta tana fitowa ta shiga ciki tsit parlon kamar ba kowa sakamakon Hajiya Fatima tana bedroom kuma TV ba'a kunne yake ba shiyasa parlon yad'au wani irin shiru shirun ma har yayi waya part d'inta ta wuce domin haka kawai taji jikinta na mata ciwo saida ta had'a ruwa me zafi tayi wanka ta sake sabon shiri cikin dinkin wata kyakkyawar atamfa anyi mata dinkin buba yasha stone yanata walwala ta kashe d'auri ta dau'ki agogo ta saka da takalmi harda d'an kunne da sarka kamar wacce zatai ba'ko ta feshe jikinta da daddad'an turare sannan ta dau'ki phone d'inta ta dawo parlor ganin kiran Husnah yasa tai murmushi tasan abinda zata tambaye ta amma sakamakon yanxu Hajiya Fatima ta fito tana parlon yasa bata bi kiran ba ta bari saita koma part d'inta yadda xatafi yin wayar a sake karasowa tai tana zama ta kalli Hajiya Fatima dake binta sa kallo tace. "Barka da gida Mami na fatan kin wuni lafiya"?. Kai Hajiya Fatima ta d'aga tana cewa "lafiya kalau na wuni ya gajiyar school ya exam"? "Alhamdulillah Mami ina Daddy ko bai dawo ba"?. "A'a ya dawo da wuri ma wanka yayi dai ya fita a gidan" ok kawai Nabilah tace tana d'age kafafunta daga kan carpet ta maida kan kujera ta tan'kwashe su bata sake cewa komai ba hankalinta nakan waya tana chatting d'agowa Hajiya Fatima tai tana cewa "amma Nabilah bakici abinci ba tun breakfast d'in safe shine kin dawo d'inma basaki mayar da hankali kici ba sai ulcer ta kama ki" murmushi Nabilah tai tana girgiza kai tace. "Ai Mami ulcer bazata ta'ba kama niba". Da mamaki Hajiya Fatima tace "meyasa bazata kamaki ba saboda da tana tsoron ki"? Dariya Nabilah tai tana cewa "a'a saboda 'kawata ce mun riga mun saba" "uhmmm" kawai shine abinda Hajiya Fatima tace tana kallon Nabilan wacce da gaske bazata ci abincin ba ta sake gyara zama tana mayar da hankalinta kan secreen d'in wayar tace. "Nabilah d'azu Daddyn ki yazo yana nemanki nace kina school amma ya aje Miki kyautar daya kawo miki gashi can akan dinning banma d'auke sa nasa a fridge ba sai kinzo ki gani da kanki yaso kin dawo kun gaisa har yace zai jira ki taso sai kuma akai kiransa a waya shine suka fita tare da Daddyn naki". Murmushi Nabilah tai tana d'agowa kalle ta domin tunda taji tace Daddyn ta tasan wa take nufi aje wayar tai cikin zumud'i ta mi'ke tana zuwa ta d'auko kyakkyawar ledar dake she'kin tabuntaka balle kumà abinda yake ciki ta dawo tana zama har lokacin da murmushi akan fuskarta ganin kayayyakin da suke ciki yasa ta sake fad'ad'a murmushin ta cikin walwala tace. "Wai Mami kina nufin Daddy Ash yazo gidan nan yau? Wayyo gashi bana nan". Zaro ido Hajiya Fatima tai tana kallon ta da mamaki tace "Daddy Ash kuma Nabilah abokin uban naki guda kike kira da Ash"? Dariya Nabilah tai tana cewa "to Mami ba sunan shi bane"?. "A'a ba sunan shi bane tunda ba Ashraf kika ce ba shi kuma sunansa kenan". "Ai Mami da Ash da Ashraf duk d'aya ne". "A gurinki ba amma ba d'aya bane tunda shifa ba yaro bane da saurayi ne saiki kirashi da hakan amma ubanki guda"?. "To Mami bakiji akace dakai wasa da baban wani gara kayi da naka ba shiyasa nayi hakan". "Au haba kenan yanzu zaki iya kiran naki tsohon da Daddy Taj ko? Tunda ai shima Tajuddeen yake". Hhhh dariya Nabilah tai tana fiffito da kayan zallar chocolates ne kala kala sai yogurts da ice cream da tsadaddun biscuits humm Hajiya Fatima bata bud'a taga mene a ciki ba amma tasan za'a rina kallon Nabilah wacce ta 6are wata babbar chocolate tana sha tayi ta d'an girgiza kai tana cewa "wai mutum ya girma shekara ashirin da yan kai amma saboda babu qani yasa suke shagwa'ba ki yanzu irin wannan kayan za'ki haka kamar 'yar yaye"? Dariya Nabilah tai tana mi'ko mata guda d'aya tace "Mami kema gashi ki sha wadannan chocolates d'in na dabam ne bana yara bane" kai Hajiya Fatima ta girgiza "a'a nikam bazan sha zaki ba kema da kike wadansu abubuwan ganin ba wani sai kene da kina da qani ko qanwa baza kiyi wani abun ba koda kud'i" murmushi Nabilah tai tana hade kayayyakin ta mayar dasu cikin ledar tace. "Shiyasa ya Sultan yake cewa wai Daddy's dina sune suka 6ata ni dashan abubuwa shiyasa ban damu da abinci ba shikam bazai yarda da wannan shaye shayen kayan za'kin ba dole ya koya min cin abinci". Jin abinda Nabilan tace yasa Hajiya Fatima cews "oh nina manta ma d'azu da safe kunyi sa6ani kina tafiya school sai gashi ya shigo gidan yana neman ki nace masa kin tafiya makaranta shima a lokacin hospital zai tafi dana fad'a masa haka sai kawai ya juya ya fita ban sani ba ko yaje"?. Kai Nabilah ta girgiza tana cewa "A yau ya Sultan yazo gidan nan Mami"? ta fad'a da surprise a fuskarta domin jiya da sukai waya ya fad'a mata zaiyi tafiya yau da safe ya akai kuma ya fasa d'an shiru tayi cikin nazari zuwa wani lokaci ta d'ago tana kallon Hajiya Fatima kamar zatai magana sai kuma ta fasa tana mi'kewa ta shige part d'inta ta d'auko hijab ta dawo parlon da mamaki Hajiya Fatima tace "Nabilah ina zuwa haka daga dawowar ki a school ko hutawa baki yiba balle kici abinci"? Kai Nabilah ta girgiza "no Mami na 'koshi zanje gidansu Daddy Mukhtar ne naji Yaya Sultan ya fasa tafiyar". "Amma me yasa bazaki kirashi a waya ba dole sai kinje kinsan ba jininku ne ya had'u da yaran gidan ba musamman Rasheedat harda ita kanta matar gidan Hajiya Salmahn to me zakije kiyo". "To ai Mami ba gurin ta zanje ko gurin yaran gidan ba ni gurin ya Sultan zanje". "Ok gurin Sultan d'in da zakije inace a gidan yake kuma d'anta ne ko asibitin doctor Sambon zaki bishi"? Hajiya Fatima ta fad'a tana qare mata kallo jiran amsa kai Nabilah ta girgiza tana cewa "a'a ba hospital zan bishi ba asalin gidansu zanje ba dad'ewa zanyi ba yanzu zan dawo". "Humm Nabilah kenan ni harna rasa bakin magana wai da gaske ke a zuciyar ki son Sultan kike bayan kina kallon irin zaman da mahaifiyar sa Hajiya Salmah keyi damu ga fitsara gurin 'ya'yanta amma ke duk hakan yayi miki a haka kike son kije gidan matsayin surukarta bayan kinsan har gobe bata goyon bayan Sultan akan neman aurenki da yake yi haba Nabilah ina kika Kai tunanin ki ya kamata ki tsaya guri d'aya kiyi nazarin abinda kike son aikataw.................... Bata karasa maganar ba akai kiranta a waya dan haka ta mi'ke tana shiga part d'inta domin ta amsa kiran a nutse ba kamar tana parlon ba shiru Nabilah tai bayan wucewar Hajiya Fatima ta fad'a cikin tunani ta sani har gobe Hajiya Salmah bata son ala'kar ta da d'anta Sultan amma tunda ba Sultan d'in ne ya 'kita ba itama bazata watsa masa qasa a ido ba zata aureshi kodan samun farin cikin su ita dashi ai tasan duk tsiya ba gida d'aya zai zauna da Hajiya Salmahn ba balle yawan fitina ta ri'ka tashi, sauke numfashi tana mi'kewa ta dau'ki ledar chocolates da key d'in motarta ta shige part d'inta domin ta samu tayi taga magriba tayi gara taje tayi sallah yau yadda take jinta a gajiyen nan barci zatai da wuri ko jikin nata ta samu ya daina ciwon inta tashi. *** Da dare har tayi shirin barci ta kwanta ko wayarta bata kashe ba tunanin ko Sultan zai kira kwanciyar ta da mintuna kad'an har barcin ya fara fisgarta kiran Sultan ya shigo da sauri ta bud'e ido tana tashi zaune ta d'auka ganin numbar wanda take tunani yasa saida taiwa secreen d'in wayar kiss kamar Sultan d'in take gani kafin ta d'aga tare da fara ido tana kashe murya tace. "Hello ya Sultan barka da dare". Shima a nasa 6angaren yana bedroom d'insa a kwance ya lullu'ba da bargo yana rungume da pillow ya sake gyara kwanciyarsa sosai yana murmushi yace. "Ya kike Baby na"?. "Ina lafiya ya Sultan ashe bakai barci ba naga goma ta kusa"?. "Eh taya kike tunanin zan iya yin barci bayan a yau ban sanya ki cikin idanuwan da zasu barcin ba tunda safe na wuni da kewar ki gashi ban samu na dawo gida da wuri ba dana dawo daga hospital Ina sauri bayan nayi wanka da sallah ko tsayawa cin abinci banyi ba domin kar dare yayi na samu nazo gurinki sai kuma nayi ba'kon bazata abokina Sameer ne yazo min ziyara tun daga Miyetti shiyasa ban samu nazo ba amma ya kike fatan kin wuni lafiya"?. Kaita d'aga kamar yana ganinta tace "lafiya kalau gaskiya nayi kewarka ya Sultan" ta fad'a a shagwa'be domin ba lefi ta riga data saba bata magana d'aya biyu saita saka shagwa'ba a ciki. "Nima nayi kewar ki Baby gashi yanzu idanuwa na suna son ganinki ba hali shiyasa nake fatan da naje Indian nan na dawo zanyiwa Daddy magana kawai a d'aura min aure dake ki dawo kusa dani sai hankali na yafi kwanciya dama kullum cikin kishi da fargaba nake kwana da'kyar nake iya barci idan na tuna kullum sai kin fita waje kinje school samari suna ganinki suna kalle mun ke kada wani banzan yaji kinyi masa ya tareki da maganar so ko ya biyoki gidan ku hummm wallahi saina 6alla masa 'kafa na zubar masa da ha'kora" . Hhhhh dariya Nabilah tai tana cewa "kai Yaya Sultan akwai kishi ji yadda kake magana da fad'a Kuma a misali na tambaye ka a bisa tsautsayi saika ganni tare da wani saurayin ina hira dashi ya zaka yi"?. Jin tambayar datai masa yasa ya zabura har yana cilli da bargon daya lullu'ba ya soma girgiza kai tare da dafe saitin zuciyarsa dake bugawa yace "nooo Nabilah please dan Allah karki kara fad'ar irin haka idan ba so kike zuciyata ta buga ba" zaro ido tai tana cewa. "kai ya Sultan ya zuciyarka ta buga kuma ni nayi ya? Kasan irin son da nake yi maka kuwa bana jin zan iya rayuwa idan batare dakai ba". Kaiya jinjina yana sakin murmushin da saida ta jishi a kunnen ta yace "yauwa ko kefa Baby nagode sosai yanzu ki kwanta kiyi barcinki saboda kada ki makara gobe idan Allah ya tashe mu lafiya maybe kafin na wuce hospital zan biyo ta gidan naku ki kula min da kanki". "Ok ya Sultan goodnight". "Shikenan mu kwana lafiya Baby". Sauke ajiyar zuciya tai bayan ya katse Kiran sai yanxu taji wani irin dad'i da iska mai sanyi tana ratsata sakamakon wayar da sukai amma da ta hana kanta sukuni lokaci guda ta koma kamar mara lafiya ita a zatonta ko laifi ma tayi masa domin ta sanshi da zuciya shiyasa duk abinda tasan zai 6ata masa rai bata yinsa ko menene qara gyara kwanciya tai tana sake rungumar pillow da murmushi akan fuskarta ta rufe ido tun tana tunani har barci ya d'auketa. ✨✨✨✨Saboda tasa abun a ranta ko barcin kirki batai ba sai mafarki iri iri har asuba sannan ta tashi duk jikinta ma ciwo yake da'kyar take takawa kamar mara lafiya ta shiga toilet tayo alwala ta fito tana saka kaya da hijab tai sallah bata tashi a gurin ba ta dau'ki al qur'ani ta bud'e ta fara karantawa a bayyane cikin zazza'kar muryarta me dad'in sauraro kafin gari yayi haske saida tayi izu biyar sannan ta rufe tayi addu'a ta shafa ta mi'ke tana mayar dashi inda ta d'auko kafin ta cire hijab d'in da kayan ta d'aura towel ta shiga wanka shaf shaf ta fito sauri take ta ta kammala shirinta sakamakon ta kwana da cewa Sultan zaizo kafin ya wuce asibiti haka ta tsara kwalliya mai kyau ta d'au wankan ala tsine uwar me 'karya hatta takalmin data saka a ranar yasan yau zatai muhimmin ba'ko d'aukar handbag d'inta tayi tana fitowa daga part d'inta tasan ba kowa a parlor yanzu idan ma ta fita sai iya 'yan aiki dan haka part d'in Daddynta ta shiga suna zaune tare da Hajiya Fatima suna zance ta shiga da sallama duk binta suke da kallo cikin mamaki yadda tayi kyau ta fito d'as da ita zama tai bayan ta gaisar dasu Alhaji Tajuddeen dahar lokacin yake kallon d'iyar tasa ya sauke numfashi tare da godewa Allah sannan yace. "Nabilah yau ko gasar kyau ake yi a makarantar taku ne? Naga kin d'au wanka kamar zakije gano shugaban qasa"?. Murmushi Nabilah tana kallon Hajiya Fatima dake mata kallon tasan saboda dawa tai wannan wankan tace "a'a Daddy zanyi ba'ko ne" da mamaki Alhaji Tajuddeen ya sake dubanta yana cewa "ba'ko kuma wanne iri Nabilah da wannan sassafen"? "Eh Daddy Yaya Sultan ne zaizo" ta fad'a tana d'agowa ta kallo Hajiya Fatima wacce ta d'an girgiza kai dama tasan sai shi murmushi Alhaji Tajuddeen yayi yana kallon ta yace "Ok yayi kyau Allah ya taimaka".. "Amin" Nabilah tace tana mi'kewa zata fita tace "na tafi school Daddy da Mami" ta fad'a tana shirin fita dakatar da ita Alhaji Tajuddeen yayi da cewa "amma bakiyi breakfast ba Nabilah zaki tafi ki jira su dafa Miki ko indomie ce kici kar ulcer ta kama ki" kaita d'aga "to Daddy bari naje kitchen d'in" saida ta bud'e kofa ta fita Hajiya Fatima ta kalli Alhaji Tajuddeen tana cewa. "Amma Alhaji nikam sai nake ganin abun nan kamar akwai damuwa a cikinsa fa ni Kuma bana son tashin hankali" da alamun tambaya Alhaji Tajuddeen ya kalleta yana cewa "abun me"? "Auren Sultan da Nabilah har yanzu bana jin farin ciki akan haka kuma ba kowa bane sila sai mahaifiyar shi lefin Hajiya Salmah ne domin tun farko itace ta 6ata abun Kuma nasan har gobe tana nan akan bakanta tunda ta rantse ta sake rantsewa ba karo d'aya ba cewa indai itace ta haifi Sultan a cikinta bazata bari ya auri Nabilah ba na rasa me yake damunta". "Oh akan haka ne hankalinki ya tashi dan ta fad'i wannan aiko tayi 'karya zan nuna mata kuskuren ta a fili ta hanyar aurawa Sultan Nabilah naga wanda zai hana kaf danginta idan basu taru basu isa su juya min ra'ayi ba balle ita maganar rantsuwa kuma tayi a banza idan anyi auren an gama sai tayi azumin kaffara domin indai kinga ba'ai auren nan ba to dama can Nabilah ba matar Sultan bace dan haka ki 'kyale ta shirmen banza take tunda shi yaron yana so an wuce gurin ai duk wani ihu bayan hari da zatai a banza bata Isa hana muyi abinda mukai niyya ba Mukhtar tun kafin yasanta nake tare da d'an uwa na tsawon rayuwar mu kinga sama takai wata bazata zo ta lalata mana zumunci da gur6ata mata ahli ba" kai Hajiya Fatima ta d'aga tana cewa "gaskiya ne shikenan Allah ya bamu ji da gani na gari bari naje naga wadannan sun gama aikin had'a breakfast d'in ne koda saura" mi'kewa tai tana fita domin ta gano. **Fitowar Nabilah Sultan ya kirata duk zaton ta yana gida saida ta fito main parlor ta ganshi a zaune yasha farar rigar likitoci yana sanye da glass a idonsa hankalinsa yana kan wayar dake hannunsa karasawa tai tana lekawa taga me yake gani har baisan ta fito ba cin karo tayi da photonta cikin mamaki ta tsaya kallon photon domin bata san ma dashi a duniya ba sai yau data gani da alama bata sani ba yayi Mata tunda hankalinta ya karkata xuwa wani gurin dabam murmushi tai tana jinjina kai kafin tasa hannu ta kar'bi wayar tana cigaba da kallon photon yayi matukar kyau d'agowa Sultan yayi yana kallon ta daidai ta zauna yace. "Gimbiya sarautar mata kin gama shiryawa ne school xaki tafi"?. Kaita d'aga "eh na gama komai tafiya zanyi" mi'kewa yai yana cewa "ok muje na kaiki da kaina yau dama badan aiyuka sun min yawa ba kullum nine zan ri'ka zuwa ina kaiki amma hakan za'ai saina ri'ka fitowa da wuri yadda bazan makara a hospital ba muje" ya fad'a yana yin gaba mi'kewa tai tana bin bayansa har gaban motarsa ya bud'e Mata ta shiga sannan ya zagaya shima ya shiga yana tada motar suka bar gidan hankalinta nakan waya bata fargaba har suka je kwanar gidan yarima Saida taji ya tsaya ta d'ago ganinsu a inda batai tunanin zuwansu yanzu ba tasan maybe Husnah bata cikin makarantar tunda jiya tace mata Momyn ta tayi tafiya idan an tashi a school gidan 'kanwar Momyn nata zata wuce kafin ta dawo tuna hakan datai yasa ta kalli Sultan tana cewa. "Ya Sultan please dan Allah muje ka shiga Yalwawa kota sabon titin I.M.G (ai em ji) ne ka d'auko qawata a gidan qanwar Momyn ta" jin abinda tace yasa shi kallonta yace "amma tun da baki fad'a min ba da nabi ta wajen Hasinah hotel sai na 6ullo ta titin gidan man Awajil ai zaifi min sauri saboda karna makara a zuwa hospital yau Ina da aiki sosai gashi saida kika bari na kusa school d'in gaskiya bazan shiga Yalwawa ba" ya fad'a zai wuce ya shiga school d'in cikin shagwa'ba tace "ya Sultan kawai aje ni anan zan karasa cikin school d'in da 'kafata" ta karasa maganar tana shirin bud'e murfin motar ta fita ya dakatar da ita. "Meyasa bazaki bari na karasa dake ba zaki tafi da 'kafa"?. Turo baki tai tana qin kallonsa saida ya sake maimata tambayar dayai mata sannan tace "to bakace baza muje ka d'auko qawata ba kuma bani da kamarta fa" dafe kai yayi domin gaskiya idan tace saiya yi mata haka zata takura shi amma baida wani za6i tunda baya son 6acin ranta d'agowa yayi yana kallon ta yadda ta cika ta batse ga hannunta har lokacin yana ri'ke da murfin motar jira take ya bata amsa zai daukota kota fita sauke ajiyar zuciya yayi yana cewa. "Ok sake murfi ki gyara zaman ki muje na d'auko miki ita shikenan hakan yayi miki koda 'kari"? Sakin murfin tai tana murmushi tace "yauwa ko kaifa ya Sultan shiyasa kake burgeni nake sonka akwai sau'kin hali" shima murmushin yayi Mata suna tafi suna hira kamar ba yanzu ta gama had'e rai ba har suka shiga anguwa bayan sunje kofar gidan yayi parking zata fita yace. "Nabilah" tsayawa tai tare da juyowa tana kallon sa a marairaice yace "please karki dad'e" yadda yai maganar yasa tayi dariya tana tsokanar sa itama cikin marairaice murya tace "bazan dad'e ba ya Sultan" ta fad'a da sauri ta fita tana dariya ganin yadda ya zaro ido shiga gidan tai da sallama a zaune ta samu Hajiya Maryam a waje tana lissafin kayan da tayo sari bayan sun gaisa tace. "Momy Husnah fa jiya tace min anan zata kwana yau ko"? Kai Hajiya Maryam ta d'aga tana cewa "eh tana nan shiga wannan d'akin tana ciki" to Nabilah tace tana shiga a kwance ta samu Husnah lullu'be da bargo kamar mara lafiya tsaye tai a bakin kofa tanai mata kallon mamaki kafin ta karaso tana cewa. "Haba Husnah yada kwance karma kice min baki shirya ba"?. Murmushi Husnah tai tana gyara kwanciya ta fuskanci Nabilan sosai tana cewa "ban dad'e da tashi ba kin gani tun daga sallar asuba na koma barci sai yanzu na tashi ko wanka banyi ba balle breakfast ki shigo man ki zauna idan na shirya saimu tafi" zaro ido Nabilah tai tana cewa "waye zai karaso ya zauna ya jira kin amma ba dani kike ba kinsan irin cakwakiyar dana had'a a waje ya Sultan nefa yau yaje gidan mu shine yace zai kawo ni school d'in har munje kwanar gidan yarima na rokeshi muzo mu daukeki da'kyar ya amince yana cewa zai makara a zuwa hospital Kuma yanzu nazo baki shirya ba humm yau akwai ya'ki idan muka fita so kike yace bazai sake kawoni school ba saidai idan munyi aure" Nabilah na rufe baki Husnah tai dariya tana tashi zaune tace. "Yanxu fa ya kika ganni"?. K'are mata kallo Nabilah tai a shirye take tsaf takalmi kawai zata sa da mayafi tace "oh wato dama kin shirya amma shine kika wani kwanta sad'e-sad'e kamar majinyaciya"? Mi'kewa tai tana d'aukar mayafinta da handbag d'inta ta d'auko takalmi tana cewa "eh man naji lokacin da kike cewa small Mom Ina nake lokacin Ina zaune zan sanya mayafi shine na kwanta da sauri na lullu'ba dan na tsokane ki" "ok taho muje kar ya gaji nasan zai iya tafiya ba karamin aikinsa bane niko da kika ganni ban fito da ko sisi ba" ta fad'a tana ri'ke hannunta suka fita sallama taiwa Hajiya Maryam sannan suka nufi bakin gate suka fita harya gaji da zama a motar ya fito yana jingine ya hard'e hannuwa a 'kirji karasowa sukai Husnah tai gaida dashi bayan ya amsa ya kalli Nabilah ya kalli agogon dake d'aure a hannunsa yana cewa. "To yanzu kam bazan samu damar kaiku ba ku tare d'an napep ya kaisu school ni zan wuce saboda idan nace saina kaiku zan makara da yawa" jin abinda yace yasa Nabilah shagwa'be fuska tana cewa "kai dan Allah ya Sultan ka kaimu bafa nisa daga nan ko a qasa idan mutum yabi ta cikin maja zai iya zuwa" tana rufe baki yace "ok to kubi ta majar mana ai yanzu zakuje Kinga amsa wannan in tafi" kud'i ya mi'ko mata amma ta had'e rai taki kar'ba ita saidai ya kaisu kaiya jinjina yana mi'kawa Husnah yace "ku tari me napep ya kaiku" kar'ba Husnah tai shi kuma ya bud'e mota ya shiga yabar gurin Nabilah tana kallo yabi ta titin mechanic village har ya 'kule kallonta Husnah tai tana cewa. "Kiyi hakuri Nabilah nice sila badan kince yazo ku d'auke niba da duk hakan bata faru" kai Nabilah ta girgiza tana cewa "haba Husnah ki daina d'orawa kanki lefi tun kafin mu had'u dake nasan halin ya Sultan saidai na fad'awa wani ko su Rasheedat qaninsa basu isa fad'a min wasu halayen nasa ba karki damu muje" wucewa sukai suna tafe suna hira sun d'anyi nisa suka tsare me napep suka hau ya kaisu daidai ya tsaya sun fita motar Sir Ahmad ta shigo makarantar tsayawa yayi a saitin su yana sauke glass d'in motarsa cikin mamaki daya tabbatar Nabilah d'ince sannan ya mayar da glass d'in yana jan motar yayi gaba saida suka biya me napep sun juya sun fara tafiya Husnah tace. "Ke Beelat bakiga Sir Ahmad yadda yake mana wani irin kallo ba daga ni har ke to me yake tunani a kanmu"? ta'be baki Nabilah tai tana cewa "oho masa nasan ganin mu dayai a napep ne zaiyi tunanin ko mu irin 'yan qaryar nan ne masu aron kaya da aron mota dan mu burge mutune ace mu wasu ne aina gane manufar sa tuntuni sharesa nai" kai Husnah ta jinjina tana cewa "humm kedai bari kawai Beelat Allah Allah nake gayen nan yabar cikin school d'in nan tunda ranar na biyo ta wani block suna tsaye su uku naji kamar yana fad'a musu zai nemi transfer ya koma yanki garinsu ya gaji da zaman arewaci" Cikin murna Nabilah tace "ya tafi d'in man da nafi kowa jin dad'i wallahi domin dama ya takura min mtwwww" ta karasa maganar tana jan zazzafan tsaki dariya Husnah tai tana cewa "uhm mutum ne shi me naci sai kace maye amma badan haka ba irin had'e masa ran da kike yaci ya daina kula ki". "Karma ya daina Ina daidai dashi zansa ayi maganinisa". Sun kusa shiga department d'insu suka ci karo dashi har yakai motarsa parking space ya dawo tsaki Husnah tai tana cewa "kiga maye nasan ke zaiwa magana tunda naga ya zubo mata wadancan idanuwan nasa" tabe baki Nabilah tai lokacin har sun kusa had'uwa tace "yaiwa kansa magana dai amma bani ba domin bazan sake kulashi ba idan ban fito masa a mutum nace masa mutunci ba bazai gane abinda nake nufi ba" tana rufe baki yana karasowa cikin muryarsa da 'kwararriyar hausa ba yace. "Nebilah Sir Tejuddeeen". Had'e rai tayi batare data amsa ba suna kokarin wucewa yace "Nabilah" ko sauraron sa batai ba kamar ma bada ita yake magana ba haka suka manna masa hauka suka wuce tsaye yayi a gurin ya kasa gaba ya kasa baya ganin yadda ta yarfa shi a gaban wasu d'aliban kai ya jinjina yana nuna saitin inda suka shiga da yatsa yace. "Heyemm Nabilah Nabilah ni kikewa shariya kike wulakanta ni bakisan koni waye ba amma zan sanar dake ta hanyar 6ata sunanki a gari dana mahaifin ki idan nayi haka na tabbata zaki fini jin ciwon abinda kikai min na soki da gaskiya kin 'ki zan karbe abinda kike takama dashi na matantakar taki sannan na bayyana lokacin faruwar hakan a gari muje zuwa kici gaba da mun shariya zan nuna miki ke ba kowa bace a cikin Dutse" ya karasa maganar yana fita daga cikin school d'in ya gangara wani gidan cin abinci dake opposite d'in makarantar domin yayi breakfast. Yauma jarrabawar da sukai taci lokaci domin har 'karfe uku da rabi suna ciki basu samu damar fitowa ba sai karfe hud'u sannan suka fito a gaggauce kowa yayi alwala sukai sallar azhar da la'asar suka mi'kewa suna fita a gurin humm kamar wanda suka sha maganin gano indai zasu fito su baro department d'insu to zasu had'u da Sir Ahmad abun kamar had'in baki saidai wannan karon ko inda suke bai kalla ba yayi gaba kallon juna sukai bayan wucewar sa suna murmushi kai Nabilah ta jinjina tana cewa. "Kai alhamdulillah har naji dad'i wallahi da naga ya share ni haba yanzu ne zan sake a school d'in nan Allah yasa ya kusa tafiya ma na karasa hutawa". "Amin domin Nima nayi mamaki da naga ya wuce wallahi na d'auka zaiyi miki magana humm dama irin su Sir Ahmad saika fito ka nuna musu 6acin ranka a fili suke ganewa ne amma koba komai yanzun ma kin samu salama ko nace mun samu domin nima yana shiga hakki na yana mugun takura min kiranki da yake yi". "Komai yazo karshe ai tunda yayi fushi nasan na huta Allah yasa bazai sake kwana cikin Dutse ba a yau ya koma yankinsu". "Amin Beelat Allah yasa" Husnah ta fad'a harda yafa hannu a fuska fitowa sukai bakin titi tuna babu wacce tazo da mota yasa Husnah ta bud'e handbag d'inta tana ciro kud'in da Sultan ya Basu su hau napep d'azu dubu biyu ne wanda ya kawosu d'azu sun bashi d'ari biyu yanzu saura dubu d'aya da d'ari takwas mi'kawa Nabilah kud'in tai tana cewa. "Kar'bi sauran kud'in nan Beelat" Kai Nabilah ta girgiza"no Husnah jeki dashi" da mamaki Husnah tace "Kuma da me zaki hau napep kije gida"? Murmushi Nabilah tana dafe kafad'ar ta tace "Karki damu kije kawai idan mun sauka zan shiga na amso kud'in a gurin Mami na kawo masa ke kuma kinga Momyn ki bata nan" sauke numfashi Husnah tai tana girgiza kai itama tace "ai kuma a gurin 'kanwarta nake kawai ki karfa Beelat". "A'a Husnah kije dashi nace" "nifa bazanje dashi ba dan Allah ki kar'ba" "ok shikenan bani iya d'ari biyar tunda kin matsa" dubu d'ayan Husnah ta mi'ko mata bata kar'ba ba tace "ni d'ari biyar nace miki" d'an dafe goshi Husnah tai tasan tunda ta ture akan d'ari biyar d'in nan bazata karbi sama da hakan ba mi'ka mata tayi sannan sukai sallama kowa ya tare napep yayi anguwansu.........✍️Mrs Äl'ämëëñ Ähmäd çë😘. Mu tsaya mu kwana anan Sai Allah ya tashe mu cikin masu rai da nisan kwana da lafiya insha Allahu zan d'ora muku littafin minister Ashraf amma kafin nan Ina so naga comments masu yawa wanda harsai na gaji da dubuwa. YUSRAH MUSA ABUBAKAR GIMBA MUHAMMAD KA'ABU. ✨🥀Mukamin ka da girma yake me ka'abu da zahidu ka taka daidai uban gidana ya rasulullah. ✨🥀A baitin sunanka ne ya al Aliyu ina tawassuli da annabin nan almakiyyu sirrin wadatuwa wanda ya zama madaniyyu albarkacinsa nazo kai mini a qawiyyu ka kara bani dama in wake nuru zatullah. ✨🥀Ranar kowa yana kasa kai ko kana buraka ma'iku rundunar Allah na bayanka suna ta gaisuwa da sallamar su a gare ka ranar dukkan annabawa ne fadawanka ashe kwa zamusha kallo matsayin rasulullah💓🌹. Sai mun sake had'uwa a gaba masoya na masu yabo a gareni godiya sosai sosai godiya🌺. Tnks for your supports🔥 we will meet again. #Vote #Comments #Share #Fallow 2~Allahummu salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil Mujahidina. TYPING 📲Fri, Dec 20/24 7:44am YUSRAH MUSA ABUBAKAR ✨✨. 💞MINISTER ASHRAF💞 WHATSAPP NO:234 8160983083. Mai son magana dani kai tsaye a tuntu6e ni ta wannan numbern. ANNURI WRITER'S ASSOCIATION 💫 Home of hospitality and harmony gidan kar'bar mutane hannu biyu da zaman lafiya ÀÑÑÙRÌ haske le'ka gidan kowa koda ma'kiya na kallon ka ramin kura sai'ya'yan ta. STORY WRITTEN ND EDITING By ✍️Yusrah Musa Abubakar Mrs Äl'ämëëñ Ähmäd çë maman little Zarahn Aunty. Bismilllahir Rahmanur Raheem. Ya rabbana salli ala khairul ala biman ala alal samawatul ula bi izini rabbi him alam. 🕋🕌🕋 It's Friday don't forget to recite suratul al-khaf may Allah open the door of success for us and our family we love our NABI no success without him he've no limits ya rasulullah muna sonka fiye darai da iyaye da dukiya. 3~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil Shahidina. 💦Yüsëëñ Sïr Äl-ämëëñ çë💦 PG_____03&04 Hajiya Salmah tana zaune a parlor tare da 'yan matanta Sultan ya fito daga part d'in shi zama yayi yana gaida ita kamar bazata amsa ba saboda haushinsa da take ji akan maganar jiya da sukai da mahaifinsa saida ya sake gaida ita a karo na biyu sannan ta amsa da'kyar yaji amsuwar d'an girgiza kai yai zai mi'ke ta dakatar dashi "Sultan Ina zakaje"? "Umma zanje wani wurin ne" jin abinda yace yasa ta had'e rai tana sake qare masa kallo yadda yaci uban wanka tace "shi gurin da zakaje bashi da suna"? "A'a" "to ina zakaje"? D'an shiru yayi domin ya sani matukar yace mata gidansu Nabilah zaije bayan bala'i dazai least gurin ta saiya sha ruwan ashar iri iri.................. "Sultan ba dakai nake ba amma kayi min banza"?. Sauke numfashi Sultan yai domin gaskiya Hajiya Salmah irin iyayen nan ne masu mugun takura akan abinda ba sune sukai ra'ayi ba cikin d'an tunani yace "Umma zanje gidansu Nabilah ne" ya fad'a yana d'agowa yaga halin da take ciki da wani irin 6acin rai yaci karo wanda saida yayi dana sanin fad'ar dayai saidai shi mutum ne wanda bai iya 'karya ba kuma baya 6oye-6oye yafi son komai a zahiri "Sultan" yaji muryar Hajiya Salmah ta kira shi amma da yanayi mara dad'i amsa mata yai Kuma yasan mezai faru tunda harya ta'bo wannan maganar. "Wato Sultan dama da nace maka ka daina son wannan yarinyar nan baka daina ba ko? Wai Sultan uban me ka gani a jikinta ne wanda ya burgeka tun yaushe nake maka maganar 'yar gidan 'kawata Hajeer kaje ka ganta nasan zatai maka ubanme ita wannan shegiyar Nabilan ta fita dashi amma ka'ki saboda maita wallahi Sultan indai Ina raye saika auri Hajeer domin ita nake so ta zama suruka ta uwar 'ya'yanka itace tafi dacewa dakai gaba da baya amma kana sane kake kautarwa, humm to bari kaji tunda ka nace sai tsinanniyar Nabilan ba na 'kyale ka kaje kayi gaban kanka amma bada yawu naba sannan daga yau na cire hannu na a cikin lamarin ka kabi uban naka kuje ku karata tashi ka bani gu" Jin abinda tace yasa Sultan ya girgiza kai cikin damuwa yace "Umma dan girman Allah kiyi ha'kuri ki fahimce ni wallahi bazan iya goge son da nake yiwa Nabilah bane dazan iya dana ha'kura da ita nabi za'bin naki amma duk da haka idan kin amince zan auri Hajeer d'in bayan na auri Nabilan" ya karasa maganar yana kallon ta tare da jiran amsar me zata ce masa. Kaita jinjina cikin 6acin rai itama tana kallon shi tace "Sultan nifa bari kaji kwata-kwata auren Nabilah d'in ne bana so kayi na tsaneta bana son koda ganinta balle ta zama suruka ta ka gane idan zaka auri Hajeer ka aureta idan kuma bazakai ba shikenan na amma nidai na fad'a maka babu hannu na babu sanyawar albarka ta" Hajiya Salmah na rufe baki Rasheedat dake gefe ta d'ora da cewa "wallahi Umma bake ba ni kaina na tsani yarinyar nan ko ganinta bana so kina gani fa saboda ita nabar FUD na ha'kura na dawo Poly amma Yaya kake neman d'auko ta ka kawota cikin mu gaskiya bana so ka auri wacce Umma tace domin Hajeer school d'in mu d'aya na santa sosai kuma kyakkyawa ce itama mukam ita meke so hum'um Nabilan banz........................ Tana rufe baki taji saukar zazzafan mari a fuskarta wanda yasa a gigice ta saki 'kara tana mi'kewa tsaye da gudu ta shige part d'insu a fusace Sultan yabi bayanta domin ya tsani raini shi mutum ne me zuciya tunda har ta taso masa da 6acin rai Hajiya Salmah ko tayi magana saiya kai kandaminsa da gudu Rasheedat ta shiga bedroom d'insu tana kuka domin Marin yayi mugun shigarta gashi da zafin hannu humm batasan ya biyota ba sai gani tayi ya banko 'kofa ya shigo 'kara ta fasa tana d'ora hannunta aka cikin kuka tace "dan Allah Yaya Sultan kayi ha'kur............ Bai bari ta karasa bashi ha'kurin ba domin bashi yazo nema ba idan da zai iya ha'kura tofa da bai biyota ba belt d'in dake d'aure a wandonsa ya zare cikin 6acin ran da ya riga ya taso masa akan lamarin ya soma shimfid'a mata a jikinta ihu take sosai tana bashi ha'kuri ko sauraron ta baiyi Hajiya Salmah dake parlor ranta yayi mugun 'baci amma ko matsawa batai ba jin ihun Rasheedat ya'ki 'karewa yasa 'kanwarta Amrat ta mi'ke tana nufar bedroom d'in gabadaya ya hargitsa musu d'akin tsayawa tai a ba'kin kofa tana kallonsu ba damar da zata bashi ha'kuri domin ganin yadda ya d'ame da dukkan karfin sa yake sakarwa Rasheedat belt d'in sauke ajiyar zuciya tai tana karasa shiga da karfi tace. "YAYA SULTAN". Da sauri ya juyo had'e hannuwanta Amrat tai tana cewa "dan Allah Yaya Sultan kayi hakuri dan Allah ka 'kyale ta dan girman Allah insha Allahu Allah bazai hanaka za'bin ranka ba bansan meyasa Nabilah bata yiwa Umma da Aunty Rasheedat ba amma nikam a nawa 6angaren bana jin komai kuma ina sonta domin koba komai 'yar uwata ce dan Allah kayi ha'kuri ka daina dukanta" ta karasa maganar tana dur'kusawa a kasa ganin haka da jin furucinta yasa Sultan bai sake kallon koda inda Rasheedat take kwance tana rusa kukan azaba ba sai belt d'insa daya mayar yana fita daga bedroom din mi'kewa Amrat tai tana zuwa inda Rasheedat ke kwance ta d'agota tare da zaunar da ita a bakin gado ta shiga toilet ta d'ebo ruwan d'umi da karamin towel ta dawo a kusa da ita ta zauna tana d'und'uma mata duk inda taga shacin belt d'in ya fito domin ansha allura da mai kamar jiki ya tsage jini ya fito saida ta gama ta mayar towel d'in ta dawo daidai Rasheedat ta mi'ke tana jan 'kafa ta nufi gaban wardrobe kai Amrat ta girgiza tare da cewa. "Aunty Rasheedat kin gani ko kiga yadda kika jawowa kanki matsala kema kinsan Yaya Sultan baya d'aukar wargi meyasa zaki shiga cikin maganar su ki bari dai Umman data isa dashi ta fad'a masa amma ke mene naki a ciki ba shine yaga yana sonta ba zai zauna da ita meye matsalar ki da hakan idan ke batai Miki ba shi kuma yana son kayarsa saiki rabu dashi ya auri za'bin ransa ba gara Nabilan ba akan ita wancan Hajeer d'in da kike cewa kin santa school d'inku daya idan kin santa kinsan halinta ne"? Jin abinda Amrat take fad'a yasa Rasheedat ta sakar mata wata uwar zazzafar harara batare datai magana ba ta'be baki Amrat tai tana ci gaba "yanzu tsaya nayi miki misali a kanki yadda kike son Mustapha sai ace ki rabu dashi ko Kuma ace mahaifiyar sa bata sonki kamar yadda Umma bata son Nabilah zaki ji dad'i haba Aunty Rasheedat kema ki tuna fa gidan wani zaki tafi ba'a gidanku zaki tabbata ba kuma bakisan halin dangin mijin da zaki aura ba ko tanan bai kamata ki ri'ka sukan Nabilah ba a rubuce yake abinda kaisai anyi maka shin ke bakya tsoron hakan wacce irin rayuwa ce wannan"?. A fusace Rasheedat ta juyo tana cewa "fita min a d'aki dan bura ubanki idan nayi auren kije kisa ayi min abinda nayi mtwwww" taja dogon tsuka tana sauya kayan jikinta tare da nufar gado ta kwanta tana lullu'ba domin lokaci guda taji wani irin sanyi me yanayi da zazza'bi nason kamata taji ya fara rufeta jikinta ya dau'ki zafi Amrat tana tsaye tana kallon ta bata sake cewa komai ba Kuma bata fita daga d'akin ba sai gaban mirror data nufa tana zama tare da d'aukar wani book da yake aje ta fara karantawa. Hajiya Salmah tana zaune Sultan ya fito zai fice wata uwar harara ta sakar masa cike da jin haushin dukan da yayiwa Rasheedat akan Nabilah kuma tasa a ranta indai tsautsayi yasa Nabilah ta aureshi sai tasa Rasheedat ta rama dukanta ganin yana shirin fita tace "Sultan zo min nan" dakatawa yayi yana sau'ke numfashi kafin ya juyo yana dawowa har gabanta ya zauna a kasan carpet cikin ladabi yace "gani Umma kiyi hakuri idan na 6ata miki rai" wani kallo Hajiya Salmah tayi masa tana cewa. "Oh Ashe kasan kayi min lefin? Lallai Kam Sultan wai kana hankalinka kuwa ko Kuma asiri sukai maka domin wannan son da kake nunawa 'yar yarinyar nan ba 'kalau ba yanzu tsabar rashin hankali kaga irin dukan da kayiwa Rasheedat akan wata banza can gefe dan kawai kin hada kakanni dakyau Sultan yayi maka kyau tashi kaje ka auri Nabilan Allah ya baka sa'a". Jin abinda tace yasa Sultan girgiza kai yana cewa "dan Allah Umma kiyi hakuri abinda ya faru idan hakan danai ya 6ata miki rai ki yafe min" ta'be baki tai tana kau dakai tace "ka tashi kaban guri nace ko? Idan kaga dama karka sake kwana a gidan nan daga yau ya tattara ka koma gidan su Nabilan" humm matsalarta kenan auren Nabilah da zaiyi ya sani shine yaja duk wannan damuwar bai sake cewa komai ba ya mi'ke yana fita 'kwafa Hajiya Salmah tai jin tashin motarsa alamar hospital zai tafi yasa ta mi'ke tana shiga part d'inta ta Kira 'kawarta a waya tana d'agawa ta soma magana. "Hello Hajiya Suwaiba wai ya batun mu na auren Hajeer da nace miki Ina nemawa Sultan nifa gaskiya yaron nan yana neman d'ora min hawan jini shiyasa nace ki barta tazo ko sati d'aya tayi min su had'u dashi ya ganta tad'an ri'ka shige masa da haka maybe kinsan mace tuni zata juya ra'ayin sa ya fasa auren wancan matsiyaciyar yarinyar". Daga can 6angaren Hajiya Suwaiba tai murmushi tare da jinjina kai tana cewa "ayya 'kawata kiyi hakuri wallahi Hajeer yanzu bata da lokaci ne Daddyn ta yana gari idan har ba komawa yayi ba bazai ta'ba bari taje wani gu tayi koda kwana bane shiyasa kikaga bata zoba amma ki qara ha'kuri zuwa wani lokaci idan ya koma insha Allahu da kaina zan kawo miki ita har gida ya ganta haba kawata wazai 'ki hada jini dake saidai idan ma'kiyin ki" sauke ajiyar zuciya Hajiya Salmah tai cikin jin dad'i tana cewa "yauwa 'kawata nagode sosai saina ganki". "Ok saina zo". Sauke waya Hajiya Salmah tai tare da fitar da huci tana cewa "kai jama'a har naji dad'i wallahi Kai Kuma Sultan zan nuna maka matsayin karfin girman ikon uwa kaje ka auri za'bin naka nima zan tilasta maka ko baka so ka auri za'bina sannan nasa ta wulakanta Nabilan mu had'u mu 'kutata Mata wanda da 'kafarta zata gudu daga gidan wallahi tallahi sai tayi nadamar aurenka dani suke zancen muje zuwa" ta karasa maganar tana fita ta shiga part d'in su Amrat ta gano ya yayiwa Rasheedat da jikinta domin tana parlor tana jiyo 'karar belt d'in idan ya sauke Mata a jiki. *** Tafiyar Hajiya Sadiya Dubai ita da 'kawarta Bilkisu Basu dawo ba sai saida sukai sati uku abin ya baiwa Husnah haushi ranta ya 6aci ganin kullum lamarin mahaifiyar tata kara ta6ar6arewa yake ranar data dawo ko zama basuyi ba Hajiya Bilkisu ta qara janta suka tafi wani gurin inda bata san ko ina bane Saida suka qara kwana biyu sannan ta dawo Husnah tayi kuka da halin Hajiya Sadiya tayi ba'kin ciki ta ha'kura addu'ar ta kad'ai Allah ya shiryeta ta daina wannan yawace yawacen tayi aure tssha ganin manyan mutane da alhazawa suna zuwa gurin ta amma ta'k za'bari d'aya ta aura kawai ita duniya ne a gabanta. Yau weekend ne bataje ko'ina ba tana gida sakamakon Husnah ta fad'a mata zata zo tare da 'kawarta su gaisa da kanta ta shiga kitchen ta had'a kayan ciye-ciye na alfarma ta gyara dinning table tsaftace parlor taci wanka itama ta d'au kwalliya ta kashe d'auri kamar zata muhimmin ba'ko ta hakimce akan kujerar parlor tana kallon yadda less d'in jikinta yake walwali da she'ki da dubban kud'ad'e,, waya ta d'auka tana bud'e data tayi sa'a kuwa Alhaji Ashraf yana online murmushi tai tana kiransa video call amma harta katse baiyi picking ba ta sake kira bai d'aga ba dama tasan za'ai haka ha'kura tai ta katse datar tare da mi'kewa tsaye ta saita wayarta ta ri'ka d'aukar zafafan salfie saida ta gama sannan ta sake bud'e datar ta tura masa photunan tare da cewa. "Ina sauraron amsa please Ashraf idan ka samu lokaci dan Allah kazo gidana idan bazaka samu dama ba ka fad'a min inda zan sameka ina so zamuyi magana" ta tura masa sending tare da zuba ido taga ya bata amsa amma shiru ga alamar ya gani nan amma baiyi Mata reply ba zazzafan numfashi ta sau'ke tare da mi'kewa ta goya hannunta a baya ta fara zaga parlon cikin tarin tunanin taya zata shawo kan Alhaji Ashraf ya sota ya aureta itakam tana matukar sonsa kuma tana burin aurensa sannan tana fatan mafarkin ta ya zamo gaskiya agogo ta kalla ganin kusan awa uku da tafiyar Husnah d'auko Nabilah amma har yanzu shiru komawa ta tana zama akan kujerar data tashi kawai tayi tsam domin ta gaza gane meke damunta a halin yanzun kawai kiran Husnah ta danna taji itama idan bazata zo da 'kawar tata ba ita zata fita domin hankalinta ya tashi da shariyar da Alhaji Ashraf yayi Mata yanzu so take ta fita su had'u ko zata samu taji salama a ranta. Husnah tana zaune a gefen gadon Nabilah tana kallon yadda take kwalliya a shafa nan a shafa can d'an murmushi tai tana mi'kewa tace "please Nabilah ki tashi muje kinga Momy tana kirana taga dad'ewar tayi yawa gashi ke Kuma kin 'ki gama kwalliyar kamar zakije gano shugaban qasa gashi banga komai a fuskarki ba banda lipstick" juyiwa Nabilah tai tana kallon ta kafin ta mi'ke tana d'aukar mayafinta da handbag d'inta tace "na gama muje" hanyar fita suka nufa Husnah na cewa "yauwa sis ko kefa kullum ina fad'awa Momy ke shine yau tace tana so na Kai mata ke ta ganki muje" ta karasa maganar suna ri'ke hannun juna kowa da murmushi a fuskarsa suka fita parlor zaro ido Nabilah tai ganin wanda yake zaune yasa tace. "Daddy Ash dama kazo gidan nan ban sani ba"?. D'agowa Alhaji Ashraf yayi ganin Nabilah yasa yace "Baby dama kina nan amma shiru banji motsinki ba sanda nazo ko kina barci ne"? Murmushi Nabilah tai tana kallon Hajiya Fatima datayi mata da'kuwa tana cewa "wato Nabilah fad'ar Daddy Ash d'in nan ya shiga bakin ki ko zaki iya kiran naki uban da Daddy Taj"? dariya tai tana d'an rufe baki tai tana cewa "yi hakuri Mami na sha'afa ne Daddy ina kwana"?. "Lafiya kalau Baby ya kike"?. "Ina lafiya Daddy ranar na dawo daga school na tarar ka kawo min kaya nagode Allah ya qara arziki". "Amin Baby ina zuwa wannan 'kawar kice"?. "Eh Daddy 'kawata ce sunanta Husnah Sahah". Jin abinda Nabilah tace yasa Alhaji Ashraf kallon Husnah yana sake maimata Husnah Sahah a ransa oh kodai yarinyar Hajiya Sadiya Sahah ce ita? Ko ba'a fad'a ba ga kama nan ya gani bai sake cewa komai ba ya jinjina kai kawai daidai Nabilah ta mi'ke tana yiwa Hajiya Fatima sallama cewa zata je gidansu Husnan kumà ba jimawa zatai ba,,, suna fita Alhaji Ashraf yace. "Amma Fatima ya akai kukai sake har Baby take mu'amala da yarinyar Hajiya Sadiya Sahah"?. "Meya faru kasan mahaifiyar tane"? Hajiya Fatima ta fad'a cikin fargabar me Alhaji Ashraf d'in ya hango bayan taga sha'kuwa a tsakaninsu kaiya d'aga Mata yana kallon Alhaji Tajuddeen yace "kwarai Fatima nasan mahaifiyar ta Hajiya Sadiya Sahah ba mutuniyar kirki bace ai kai ka santa Tajuddeen Kuma kasan halayenta meyasa ka bari har Nabilah take 'kawance da 'yarta baka tsoron abinda zai biyo baya"? Kai Alhaji Tajuddeen ya girgiza yana cewa "wallahi Ashraf ban sani ba ko a mafarki bansan suna zumunci da wata 'yar gidan Sadiya Sahah ba sai yau da na gansu tare Kuma bansan ita bace sai yanzu data fad'i sunanta badan haka ba ban wani ganeta ba tunda bata kama da mahaifiyar ta". Huci Alhaji Ashraf ya fitar yana cewa "Gaskiya banji dad'in wannan al'amarin ba bana so ace Nabilah wani abun rashin dad'i ya faru a kanta saboda haka dole ne a tari abun tun wuri da zafi ake dukan 'karfe sannan ice tun yana d'anye ake tan'kwasa shi yanzu abinda ya kamata idan Baby ta dawo ka sameta cikin nasiha kayi mata magana ba cikin zafin rai ba dan na sanka da saurin hawa kabi a hankali kayi mata bayani yadda zata fahimci manufarka sai ta ri'ka ja baya a sannu da haka da haka saita janye jikinta daga na wannan yarinyar kafin wani abun muniya wanda bama fata ya faru" ya karasa maganar yana kallon Alhaji Tajuddeen wanda ya jinjina kai cike da gamsuwa domin maganar gaskiya ya san Hajiya Sadiya Sahah yasan halinta ba ba'kuwarsa bace dole ya dakatar da Nabilah tunda yaji wacece Husnah daga Ina ta fito sauke ajiyar zuciya yayi yana mi'kewa yace. "Shikenan na fahimta muje zan dau'ki mataki bari saita dawo". Mi'kewa Alhaji Ashraf yayi yana kallon Hajiya Fatima da itama ta mi'ke yace "ok Fatima na wuce gida daga can" kaita d'aga tana cewa "baza ka dawo kayi lunch anan ba"? "Eh tacan zan wuce gidan munyi magana da wani mutum jiya zaizo daga government house zamu gana shine dalili bari muje kinga kira ma yake yi maybe ya sauka kuma baisan inda zamu had'u ba" ya karasa maganar yana juyawa 6angaren Alhaji Tajuddeen yace "muje" fita sukai yana d'aga kiran Hajiya Fatima kam shiru tayi cike da tunani da rashin jin dad'i domin Nabilah ta matukar sha'kuwa da yarinyar nan rana d'aya ba lefin tsaye ba na zaune ace ta rabu da ita ta daina yi mata magana ba fad'a ba komai bayan school d'insu d'aya sun saba gaskiya abun baiyi daidai ba bari Alhaji Tajuddeen ya dawo ta sameshi ta bashi wata shawarar Allah yasa zai yarda. ***Husnah da farin ciki a fuskarta suka shiga parlon Hajiya Sadiya har lokacin tana zaga kujerun dake parlon da waya a hannunta tana sake Kiran Alhaji Ashraf amma bai d'aga ba idonta yayi ja ranta yakai 'kololuwa wajen 6aci ganinsu yasa ta sassauta fushin dake cin ranta tana d'an sake fuska da murmushi tace. "Sannu da zuwa bismilllah zauna" ta fad'a tana bin Nabilah da kallon cike da mamaki ta zuba Mata ido zama Nabilah tai cikin ladabi ta gaida ita amsawa Hajiya Sadiya tai tana kallon Husnah wacce bakinta ya'ki rufuwa tace "ki kaita dinning Ina zuwa" to Husnah tace suna mi'kewa suka tafi can domin itama Nabilan taji dad'in hakan sai tafi sakewa akan suna gaban Hajiya Sadiya ga wani kallon 'kurulla da take mata sunan zaune suna hira da dariya abinsu Hajiya Sadiya itama ta karaso gurin ta samu guri ta zauna tare da cewa Husnah tai serving din'ta mi'kewa Husnah tai ta had'a Mata komai kafin ta koma ta zauna amma me Hajiya Sadiya ta kasa nutsuwa taci abincin yadda ya kamata haka kawai ganin Nabilah ya tada Mata hankali kuma batasan dalili ba aje spoon d'in hannunta tai tana kallon Husnah tace. "Husnah wannan yarinyar daga Ina kuka taho tare a wanne gidan take gani nake kamar nasan wani me kama da ita a cikin manyan mutanen mu kuma wanin ba kowa bane sai professor Alhaji Tajuddeen"? ta karasa maganar tana sake qarewa Nabilah kallo cike da mamaki. Itama Husnah kallon Nabilan tai tana cewa "eh Momy kin fad'a daidai wallahi 'yarshi ce sunanata Nabilah Tajuddeen". Murmushin ya'ke Hajiya Sadiya tai tana cewa "ayya Allah sarki ai jini baya 6uya kallo d'aya nayi mata na gani, ashe itace qawar taki"?. "Eh Momy qawata tace sosai banda kamar ta kaf cikin qawaye na munfi shakuwa da ita". Kai Hajiya Sadiya ta jinjina tana cewa "Masha Allah gaskiya kinyi dacen qawa naga itama kamar ba ruwanta irin yadda kike dama haka kike so" 'yar dariya Husnah tai tana kallon Hajiya Sadiya tace "ai Momy yadda kika san 'yan biyu idan mukai abu wani lokacin haka muke a school kuwa ba d'alibai ba hatta malamai sun gane mu saboda bama rabuwa saidai idan tashi akai har twins ake ce mana" ta karasa maganar suna had'a ido da juna sukai murmushi wanda akan idon Hajiya Sadiya haka kawai taji gabanta na fad'uwa lokaci guda ta tsinci kanta cikin wata iriyar fargaba to meya faru meke damunta meyasa daga ganin wannan budurwar ta nemi nutsuwarta ta rasa?sauke wani kalar zazzafan numfashi tai tana sake kallon Nabilah a karo na ba adadi ganin yadda suke hira a tsakanin su lallai akwai so da shaquwa mai karfi runtse ido tai jin yadda zuciyarta ke harbawa kafin ta mi'ke tana barin wuri domin tasan ganin Nabilan ne ya jawo Mata haka to amma akan wanne dalili shine tambayar dake cin ranta harta shiga bedroom da sauri ta rufe kofa tana d'auko waya ta kira numbern Hajiya Bilkisu tare da fatan Allah yasa tana kusa tayi sa'a kuwa tana d'agawa cikin 'kaguwa tace. "Ke Hajiya Bilkisu kin ta'ba ganin 'yar gidan professor Tajuddeen ne ko a wani wuri"?. Daga can 6angaren hajiya Bilkisu dake zaune tare da wata hajiya suna lissafin manyar ma'kudan kud'ad'e tace "eh bana ce ba kona taba ganin nata na manta kinsan 'ya'yan manyan nan ba barinsu ake suna fita ba saida 'kwak'kwaran dalili a Ina zan ganta ked'in had'uwa kukai"?. "Ina muka had'u nida tazo min har gida". A zabure hajiya Bilkisu tace "har gidan ki kuma to waye ya kawota kodai Alhaji Tajuddeen d'in ne suka zo tare to amma me zasu zo yi gurin ki ma ko tare da Alhaji Ashraf d'in suke"? Kai Hajiya Sadiya ta girgiza tana cewa "a'a ba tare suke ba tab Alhaji Ashraf ne zaizo gidana inda nake amma kema dai fad'a kike saboda dad'in zance ko? Hum ni bama wannan ba kinsan abinda ya bani tsoro ina kallonta naji gabana ya fad'i yanayi na ya sauya zuciyata tahau bugawa da qarfi da sauri shiyasa ma na Kira ki me hakan yake nufi dan kawai naga yarinyar zanji haka"?. Shiru Hajiya Bilkisu tai zuwa wani lokaci tayi dariya cike da tsokana tace ''kodai kin fad'a tarkon son mahaifin ta ne professor Alhaji Tajuddeen idan ba haka ba meyasa xakice dan kawai kin ganta sai hankalin ki ya tashi haba Hajiya Sadiya kina da son d'orawa kanki damuwa dan Allah ki sassauta wannan abun tsabar son da kikewa minister Ashraf ne shiyasa idan kika ga makusancinsa sai kiji gabadaya kin nemi nutsuwarki kin rasa tunda kinga Daddyn Nabilan da kike magana a kanta abokin Alhaji Ashraf d'in ne sosai ba'a ganin tsakaninsu Kuma ance aminta ce mai qarfi tun suna matasa har zuwa d'agowarsu amma kinga ta inda suka bambanta shi Alhaji Tajuddeen yayi aure domin ga zahiri nan kinga 'yarsa a gabanki sa6anin Alhaji Ashraf da bai ta'ba furtawa mace kalmar soba shiyasa ma kike matukar shan wahalar sa domin baisan yadda zafin so yake ba bai ta'ba yinsa yaji yadda ake ji ba dan haka kullum nake gargad'inki ki ri'ka masa uziri kinji qawar kina binsa a sannu harya fahimci menene so ya fuskance ki". Sauke ajiyar zuciya Hajiya Sadiya tai cikin jin d'an sassauci sakamakon wannan maganar da hajiya Bilkisu tai Mata tace "kwarai haka ne kin fad'i gaskiya qawata nagode sosai da nuna kokarin ki gareni". "Ok karki damu zan Kira ki yanxu akwai abinda nake yi saboda ina son jibi zanje Dubai na saro kaya ne". "To shikenan na gode Bilkisu" Hajiya Sadiya ta fad'a tana kashe Kiran tare da manna wayar a 'kirjinta tace "kai alhamdulillah har naji dad'i wallahi da ina neman rud'a kaina a banza bari na koma kar Husnah taga na barsu bayan taxo da ba'kuwa" aje wayar tayi tana fita har lokacin suna zaune inda ta barsu suna hira da dariya sosai babu wata matsala suna cikin nishad'i zama tai batare da tace musu 'kala ba kawai ta d'ora kafa d'aya kan d'aya tana kallon Nabilah a fisge idan taga kamar Nabilan xata ganta sai tai saurin d'auke kanta har kusan magriba sannan ta mi'ke zata tafi gida Hajiya Sadiya ta bata kayan kwalliya da doguwar riga me tsada harda handbag domin kayan sana'ar ta kenan godiya Nabilah tayi mata Husnah tayi Mata rakiya zuwa harabar gidan inda tayi parking da motarta bayan sunyi sallama ta wuce gida. Hajiya Fatima tana parlor a zaune Nabilah ta shigo tare da zama tana aje ledar hannunta tace "barka da gida Mami na" kallonta Hajiya Fatima tai tana cewa "yauwa kin dawo"? Kai Nabilah ta d'aga tana mi'kewa tace "eh Mami ga tsaraba ma ta bani doguwar riga da kayan kwalliya harda handbag". "Ok an gode mata kije ki aje kayan ki dawo dama Daddyn ki yana nemanki tun d'azu yayi tunanin kin dawo nace a'a". "Ok bari na dawo yana gida ne"?. "Eh ya dawo yana part d'insa". "To tsaya na aje kayan naje" ta fad'a tana d'auka ta shiga part d'inta tana ajewa ta fito ganin bataga Hajiya Fatiman ba yasa ta shige part d'in Daddyn nata a zaune ta samesu da sallama ta shiga tana zama tare da gaisar da Alhaji Tajuddeen amsawa yayi yana kallonta tare da sauke numfashi saboda tunani ta Ina zai fara yi mata maganar da Alhaji Ashraf ya fad'a masa taya zaice ta daina mu'amala da Husnah ta ruwan sanyi batare da 6ata ran dukkan su biyun ba? sake kallonta yayi yana cewa. "Nabilah a ina kuka had'u da wancan yarinyar Husnah Sahah ko a school d'in"?. Nabilah tayi mamakin jin tambayar da Alhaji Tajuddeen d'in yayi mata batai tunanin abinda zai fad'a ba kenan to meyasa ya tambaye ta? Kaita d'aga tana cewa "eh Daddy a school muka had'u da ita". "Shekara nawa da had'uwar ku"?. "Tun farkon shigata school d'in muka had'u muke 'kawance da ita har yau kuma ina jin dad'in zama da ita domin tana da hankali". Sake sauke ajiyar zuciya yayi a karo na biyu yana cewa "da akwai sha'kuwa a tsakanin ku"?. "Eh Daddy sosai ma ni bayan ita bani da wata 'kawar na yarda ita kamar yadda itama ta yarda dani nasan bazata ta'ba cin amanata ba har abada". "Ok Masha Allah shikenan tashi kije Allah ya tashe mu lafiya" Amin Nabilah ta fad'a da fara'a a fuskarta duk da batasan me tambayar da Alhaji Tajuddeen ya mata ba ta mi'ke tana fita Hajiya Fatima ta kalleshi tana cewa "amma Alhaji meyasa baka fad'a mata wata magana ba ka bari ta tafi taji kana cewa masha Allah me hakan yake nufi ko ka fasa hanasu mu'amalar"? Kai ya jinjina yana cewa "eh gaskiya Fatima bazan iyaba ba dan komai ba na gani Nabilah tace min sun dad'e tare kuma ki tuna shekaru uku baya da suka wuce xuwa yau yanzu da nake miki wannan maganar ki gani kin ta'ba ganin wani hali mara kyau Wanda Nabilah ta koya ko tayi wanda ya sa6a hankali ta'ba yi kece zan tambaya domin kin fini zama tare da ita"?. Kai Hajiya Fatima ta girgiza tana cewa "a'a ban ta'ba ganin wani abu sa6anin hankali ba gaskiya bata ta'ba zuwa da wani sabon al'amari gidan nan da sunan a gurin 'kawa ta koya ba". "Ok to kin gani saboda haka hanata mu'amala da yarinyar akwai damuwa me yawa dun riga sun sha'ku sun saba rana tsaka nace ta rabu da ita ba wani hujja abun xai mata barazana sannan zata nemi dalilin hanata kawance da yarinyar nace mata me? Bani da bakin magana tunda kika ga har Allah ya kawo mu yanzu bakiga ta koyar da ita wata mummunar d'abi'a ba to insha Allahu inada tabbacin babu wani abu dazai faru kawai kibar maganar ya wuce shi kuma Ashraf nasan yadda zanyi dashi" kai Hajiya Fatima ta d'aga tana cewa "to shikenan Allah yasa alkhairi tsakaninsu Allah yasa su cigaba da amfanar da junansu Allah yasa tarayyarsu tayi amfani koda a gaba ne" amin Alhaji Tajuddeen yace tare da mi'kewa ya shiga bedroom cewar zaiyi wanka mi'kewa Hajiya Fatima tao tana bin bayansa ta had'a masa ruwan. MRS ÃL'ÅMÉÉÑ ÁHMÃD CË. Rayuwar daba Annabi SAW ba rayuwa ba dakai na fake rasulullah ban fake da kowa. 💓Na kirayi sunan Allah mamallaki me mulkin dukkan halittu marashin mataimaki auwalu akhiru zahiru bad'inu ya madaukaki ka karan dubun basira badan halina ba. Tnks for ur supports 🔥 nagode sosai masoya we will meet again sai mun sake had'uwa be with me at always my lover's. 4~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil khaifina. TYPING 📲Thu, Jan 2/25. 3:13pm YUSRAH MUSA ABUBAKAR🤘💓💯. 💕MINISTER ASHRAF💕 ÀÑÑÙRÌ WRITER'S ASSOCIATION 💫 Home of hospitality and harmony gidan kar'bar mutane hannu biyu da zaman lafiya ÀÑÑÙRÌ haske le'ka gidan kowa koda ma'kiya na kallon ka ramin kura sai'ya'yan haka taken mu yake. ××××××××××××××××××××××××××××× ++++++++++++++++++++++ ******************* STORY WRITTEN ND EDITING °°°°°°°°BY°°°°°°°° ✍️ Yusrah Musa Abubakar YUSEEN SIR ÄL'ÄMËËÑ ÄHMÄD ÇË. YMA DUTSE NEW WORLD🌏 sabuwar duniya kuzo kuyi kallo dad'i yana Jigawa garin ilmi garin addini zaman lafiya Jigawa. 5~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil D'a'inah. WhatsApp no:234 816 098 3083. yusrahmusaabubakar65@gmail.com ¶~¶~¶~¶~¶~¶~¶~¶~ ©®YMA DUTSE BISMILLLAHIR RAHMANUR RAHIM. 💦Yüsëëñ Sïr Äl-ämëëñ çë💦 PG_____05&06 Washe gari ba school Nabilah a bedroom ta wuni bata fito ba tana karatun exam kanta yad'au zafi domin ko kiran ta da Sultan yayi sama-sama sukai magana akan yadda hidimar graduate d'inta zai kasance da abinda zatayi yace zuwa jimawa zai kawo mata d'inkin dayai mata da sauran abubawan da zata bu'kata kafin ta aje wayar taci gaba da karatun ta bata fito part d'inta ba sai bayan sallar magriba sannan ta d'auko hijab ta fito tana bud'e kofa Sultan ma ya bud'o kofar parlor tsaye sukai suna kallon juna daga baya kowa ya rufe karasowa Nabilah tare da zama tana kallonsa kafin tace. "Yaya Sultan yau meye sirrin"?. "Sirrin me"? Ya tambaya cikin mamaki yana kallon ta shima murmushi tai tana tagumi kamar me tunani kuma har lokacin bata daina kallonsa ba tace "gani nayi kayi kyau sosai yau kamar ango wallahi". Jin abinda tace yasa ya murmusa yana cewa "kin fad'a daidai ai dama angon ne saura wata d'aya fa auren namu haka d'azu Daddy ya fad'a min yace fatan na fara shiri nace masa na gama komai balle ke" dariya Nabilah tai cikin farin ciki tace "au wai kai harsun fad'a maka lokacin bikin amma ni ban sani ba"?. "Eh idan kin sani me zakiyi"?. "Amma ko bazan yi komai ba ai zan gayyaci 'kawaye na ko"?. "To daga gayyatar 'kawayen naki ina shikenan komai saidai a miki"?. "Me za'ai min"?. "Kema kin sani". "Ni ban sani ba kawai ka fad'a min". "Da gaske baki sani ba"?. "Kwarai ban sani ba". "Ok shikenan zan fad'a miki amma ba yanzu ba sai nan gaba". "Gaba kamar yaushe"?. "Kamar lokacin da kika bu'kata fad'a min abubuwan da kike so ayi a bikin mu wanne irin tsari zakiyi sannan wanne kalar kaya da make-up zaki d'auka"?. "Humm ai Yaya Sultan na d'auko buri da yawa nifa a bikin nan so nake mu gwangwaje Ina so ka kama mana moderling event center sannan ga gyaran jiki da wedding gown Ina son guda biyar saboda sati zamu d'auka ana biki tunda kaga bayan ni Daddy da Mami na basu da wani d'an da za'ai shagali dole ne a gyagije sosai ko"?. D'agowa yayi yana kallon ta kamar me kallon mirror sai kuma yayi murmushi yana jinjina kai yace "as you wish duk abinda kike so shi za'ai miki madam". Cike da murna Nabilah tace "da gaske zakai min duk abinda na lissafa maka"?. "Eh Nabilah kinfi karfin komai a gurina nifa Nabilah koda raina akace na bayar madadin ki zan bada ina yi miki so a zuciyata wanda bazan iya kwatanta girman saba kawai saidai nace ina son ki". Sauke ajiyar zuciya Nabilah tai itama cikin tsananin son da take masa tace "Yauwa Yaya Sultan nagode da nuna kaunar ka gareni na sani samun wanda zai soni kamar yadda ka 'kaunace ni zaiyi wuya ka nuna min gata ka bani duk abinda nake so a rayuwa fatana Allah ya barmu tare" da sauri Sultan ya d'aga hannu sama harda shafawa yace "Amin Nabilah wallahi wannan addu'ar taki bakiji yadda ta sanya min nutsuwa da sanyi a zuciyata ba burina naga ranar dazan bud'e ido na ganki a gidana matsayin matata". "Insha Allahu Yaya Sultan kamar yaune zakaga lokaci yazo". "Ai Nabilah gani nake yanzu kamar lokacin baya gudu". "Yana gudu man kawai dai kaine baka ganin hakan". "To meyasa ni nake ganin baya gudun"?. "Saboda ka 'kagu kaga ranar bikin mu shine dalilin dayasa koda lokacin yana gudu kai baza kaji yana gudun ba". "Haka ne zan tafi domin jiya nazo gidan bakya nan sai iya Mami tace min kinje anguwa gurin 'kawarki". "Eh naje gurin wannan 'kawar tawa wacce kwanan baya nace muje Yalwawa ka d'auko ta naje gurin tane jiya da safe na dawo bayan magriba". "Ok muje ki taka min" ya fad'a yana mi'kewa itama mi'kewar tayi suna fita tare har jikin mota ta rakashi anan ma sun dad'e suna hira kamar bazasu rabu da juna ba kafin da'kyar sukai sallama amma duk da haka saida taga tashin motarsa me gadi ya bud'e masa gate ya fita sannan ta juya tana komawa ciki ganin har lokacin babu alamar Hajiya Fatima kawai taje dinning table d'ebi abinda take so ta koma part d'inta balle jiyan Alhaji Ashraf bayan dawowar su ya taho mata da kayan chocolates masu yawa shi take sha shiyasa ma bata fito ta nemi abincin ba. *** ***Humm tun ranar da zasu gama exam d'in final suka fara shigulgula da kid'a-kid'e kamar a gidan DJ wadanda basa rawa ma ranar saida suka girgiza balle wanda ya saba abun ba'a magana 'yan mata ansha lalle an dau kwalliya kamar ranar zasuyi partyn da sun tsara zasu kama Hall daga baya sai sukace suyi abubuwan su kawai a cikin makaranta yafi suna fitowa daga d'akin exam suka saki ihun murna musamman samari abubawa iri iri tun ranar suka sha kid'a-kid'e kafin washe gari kowa yasha wanka ala tsine uwar me 'karya haka ranar suka taru suka sake gwangwajewa. Duk abinda suke Sir Ahmad hankalin sa yana kan Nabilah tun data shigo school d'in ya kafeta da ido duk wani motsi da zatai yana binta da kallo saida ya bari lokacin tashi ya kusa ya mi'ke ya yana zuwa inda take tsaye tare da Husnah da sauran 'kawayen su tana ganinsa saida taji gabanta ya fad'i ta rasa meyasa batasan koda hangoshi daga nesa balle yazo inda take ko yayi mata magana saidai tuna daga yau shikenan ba sake ganinta zaiyi ba kuma dama shima state d'insa xai koma yasa kawai ta share batun tabar 6acin ran daya taso mata karta 6ata ranar farin cikinta da damuwa................... "Nabilah Sir Tajuddeen happy graduation". Taji muryar Sir Ahmad d'an kallonsa tayi a fisge tace "na gode" tana fad'in haka ta ri'ke hannun Husnah tana janta alamar subar gurin su sake shiga cikin d'alibai ya dakatar da ita. "Nabilah ina so zamuyi magana ko minti biyar ne domin maybe daga yau baza mu sake had'uwa dake ba" jin abinda yace yasa taji wani sanyi da dad'i ya rufe ta tasan kila gobe ko jibi zai ware hakan yasa ta saki hannun Husnah tana cewa "bari na dawo" ta fad'a suna wucewa da harara Husnah ta raka bayan Sir Ahmad domin ta matukar tsanarsa musamman wannan takurar da yake yiwa Nabilah yana mugun 'kona mata rai. Can cikin makaranta suka shiga inda ya kasance shiru ba kowa suka sami gurin zama suka zauna Nabilah harda d'ora kafa d'aya kan d'aya ta fuskance shi tunda tasan duk tsiya daga yau shikenan ko a tunani bazata tuna Sir Ahmad ba domin tunanin sa zai ri'ka dawo mata da takurar dayai mata............... "Nabilah". "Na'am Sir Ahmad". Kaiya jinjina yana kallon ta yadda tayi kyau ta tsaru yace "Nabilah na fad'a"? D'agowa tai tana masa kallon mamaki da alamun tambaya tace "me"? Da ido ya nuna Mata kwalliyar jikinta yana cewa "kin yi kyau sosai yau har bansan yadda xan kwatanta miki ba" jin abinda yace yasa cike da jin haushi Nabilah taja tsaki a ranta amma a fili ba yabo ba fallasa tace "tnks" ta fad'a tana sake kawar dakai daga kallon da yake mata. Gyara zama yayi yana cewa "Nabilah kinsan meyasa na kiraki ina so ne nayi miki tambaya ta karshe daga yau shikenan na sani idan har ba kin amince ba basake had'uwa zamuyi dake ba har abada please Nabilah dan Allah ki amince min ki yarda ki soni ki aureni wallahi ina sonki so na gaskiya da aure ba yaudara ba" yana rufe baki Nabilah ta soma girgiza kai tana cewa. "A'a Sir Ahmad dan Allah nima kayi ha'kuri ka fahimce ni ina da wanda nake so kuma shi zan aura". "No Nabilah zuciyata bazata iya ha'kuri dake ba ina matukar sonki ki fahimta please Baby Nabilah Kinga I love you bana jin dad'in wannan shariyar da kike min idan jan aji ne dajan rai na gama jawuwa ki fad'a min kalmar so Nabilah". "Dan Allah Sir Ahmad ka gane gaskiya nake fad'a maka domin bazan yaudare kaba ina da wanda zan aura". "Ki rabu dashi Nabilah ki bar batun sa ki 'kyale shi kingan ni nan zan baki komai da kike bukata da jiyar dake dad'i da kud'i masu yawa ki rabu da wancan ki aure ni pls" ya karasa maganar yana shirin ri'ke hannunta a zabure ta mi'ke ganin yana neman d'ora mata hau ta matsa baya ranta a 'bace tace. "Wai me kake yi haka na fad'a maka da wanda nake so amma ka'ki ganewa ko ana so dole ne wannan wacce irin rayuwa ce dan Allah ka rabu dani ka 'kyale ni haba" tana fad'in haka ta juya fuuuu tabar gurin. Da kallo ya bita tare da kad'a kai yana sakin wani irin murmushin takaici kafin ya mi'ke yana tafe shi kad'ai yana magana da zuciyarsa har tuntu'be yake yi "meyasa zaki min haka Nabilah ina son ki meyasa kika kasa fahimta waye wanda zaki aura a ina yake dole na nemoshi dole nayi magana dashi ko yana so ko baya so saiya barmin ke ta halin tsiya da masifar da zata sameshi idan har bai bar min keba to shima bazai ta'ba auren kiba saina wulakanta ki na 6ata al'amarin saina sa ki kuka da ba'kin ciki ba keba hatta danginki sai sun shiga tashin hankali zan rabaki da abinda kike tunkaro dashi a jikin ki sai naga karshen 'karya" dariya yayi shi kad'ai yana jinjina ya koma ainishin inda ake shagalin amma babu alamar Nabilah maybe tana baro gurinsa ta fita a school d'in ta'be baki yana d'aga waya ya kira wata budurwa da kamar minti biyar tazo cikin 'kaguwa yace. "Nazzi yaya kin samo min"?. Murmushi tai tana d'aga kai tare da mi'ka masa wayarta tace "eh na samo maka amma da'kyar a gurin wata student 'yar classmates d'insu ce saida na bata kud'i masu yawa kafin itama ta shiga cikin lad'iban ta nemo min" kaiya jinjina yana amsar wayar ya zubawa numbar wayar Nabilah ido kamar ita yake kallo daga baya ya d'auko tasa wayar ya dau'ki numbar yayi saved sannan ya mi'ka mata yana cewa. "Ok nagode Nazzi muje nayi dropping d'inki a gida saina wuce idan lokaci yayi zan neme ki kece zakiyi min aiki". Murmushi tai daidai ya bud'e mota ya shiga itama ta shiga d'ayan site d'in tana cewa "amma sakamakon irin wannan aiki ina karbar kud'ad'e fa masu yawa domin kasan aikin sayar darai ne kai kanka sheda ne kasan wace Nabilah kasan mahaifin ta ba 'yar 'kananun mutane bace idan tsautsayi yasa a wajen aikin aka samu akasi bansan wanne hali zan shiga ba". Kai Sir Ahmad ya d'aga yana cewa "nasan 'yar waye ita shiyasa zan bi ta hikima na 6ata mata rayuwarta kamar yadda ta bakanta raina ta hanyar 'kin amincewa 'kudurina kin gane? karki wani damu ina tare dake babu yadda za'ai su gane zamu had'a baki tare da Danual komai zai kasance a sirrince ina kammala aiki na zamu tattara kayan mu harke mubar Dutse ko koma state namu acan za'ai bikin auren mu ni dake" kaita d'aga masa cikin jin dad'i domin tana mutuwar sonshi amma dalilin Nabilah yasa baya bata lokaci yanzu kuma da yaga Nabilan tayi masa nisa dole ya dawo gurinta. Nabilah kam 6uya sukai ita da Husnah sai bayan sallar la'asar suka bar school d'in sakamakon Sultan ne yazo d'aukar Nabilah tun a cikin school d'in sukai sallama tana cewa mata sai ranar biki zata zo mata fitarsu ba jimawa Husnan itama ta dau'ki motarta ta nufi gida daidai tayi parking taga Hajiya Sadiya ta fito hankali tashe ranta a 'bace hatta mayafinta yana kafad'arta bata samu nutsuwar yafawa ba da sauri ta nufi parking space idonta a rufe ko ganin Husnah batai ba wacce ta tsaya kamar sanda cike da mamaki tana binta da kallo harta bud'e mota zata shiga Husnah tace. "Momy". A firgice Hajiya Sadiya ta juyo tana kallon Husnah da jan idonta domin batai tunanin ita bace bataso ta dawo ta sameta bata fita a gidan ba amma hakan ma bazai hanata fita ba batai magana har Husnah ta rufe murfin motar data fito ta karaso gurin Hajiya Sadiyan ta kalleta sosai kafin tace. "Momy meya faru ina zuwa yanzu haka magriba tayi naga ranki a 6ace"?. Shiru Hajiya Sadiya tai ta rasa me zatace mata dan haka kawai tace "eh akwai inda zanje ba zama zanyi ba yanzu zan dawo ki kula kar kije ko'ina" ganin tana shirin shiga mota Husnah tace "Momy dan Allah karki fita yanxu Ina zakije ne a wannan daren"? Husnah ta fad'a ranta duk babu dad'i a fusace Hajiya Sadiya ta juyo tana cewa "gidan mataccen ubanki Sahah Bilal zanje yanzu kin gane inda zanje"? Karasa maganar tana kallon yadda Husnah ta zaro ido jin abinda tace ganin batai magana ba yasa taja dogon tsuka tana shiga motar da 'karfi ta rufe tare da yi mata key ta fita daga rumfar aje motocin ta nufi gate tare dayin horn me gadi ya bud'e ta fita Husnah tana tsaye tana kallo saida taga me gadin ya mayar da gate ya rufe sannan ta sauke wani irin zazzafan numfashi idonta fal da hawaye ta koma gaban motarta tana d'auko handbag d'inta ta cire key d'in motar kafin ta rufe ta shiga gidan cike da tsananin damuwa. Hajiya Sadiya tana fita daga mopal-base government house ta nufa da mugun gudu burinta kawai ta had'u da Alhaji Ashraf ko hankalinta zai dawo jikinta tsabar tsaron dake gidansa ba'a barta ta shiga ba ba'kin ciki kamar zai kasheta gashi ta kira numbern wayarsa yafi a kirga ta'ki ya d'aga tana tsaye ta jingina a jikin motar ta kifa kanta cike da damuwa da tashin hankali zuwa bayan sallar isha kusan karfi tara taji motoci suna parking da sauri ta juya tana kallon gurin motocin gidan Alhaji Ashraf ne daidai an bud'e kofar babban gate d'in gidan sun fara shiga Hajiya Sadiya ta cije yatsa cike da takaici tasan yau ko mutuwa zatai bazai saurare taba saidai ta barwa gobe, akan idonta suka gama wucewa kafin aka mayar da gate aka rufe runtse ido tai ba zato taji hawaye yana zuba kaita jinjina tare da nufar motarta ta shiga ta koma gida a parlor ta samu Husnah ko iya shiga part d'inta batai ba tunda taga fitar Hajiya Sadiyan ganin ta shigo yasa zubur ta mi'ke tana kallon yanayin rashin walwalar dake kan fuskarta tace. "Momy ina kika je"?. Wani irin kallo Hajiya Sadiya tai mata jin tambayar data jefo mata batare data motsa koda lips d'inta ba kuma bata tsaya ba ta wuce part d'inta da kallo Husnah ta bita tana sau'ke ajiyar zuciya itama ta shiga nata part d'in tunda tasan ko tayi uwa yata maye ayau Hajiya Sadiya baxatai mata magana ba saidai gobe idan ta huce........✍️ AYI HA'KURI YAU TYPING D'IN BABU YAWA. YUSRAH MUSA ABUBAKAR✨✨ ✍️MARUBUCIYAR Yarima abdul-maleek Rayuwa biyu Safreeyyah D'an millionaire Minah-Umer Dama kece Yarima Aryam Husnah ko Badiyat Royalty Tajuddeen Aryam Zuciyar Aliyu ce Me kamar sarki And now minister Ashraf🤟. MRS ÃL'ÅMÉÉÑ ÁHMÃD CË. Mai tambarin yma dutse new world me alfaharin jihata ce ko'ina nake inda zan zarce a cikin Nigeria muke da gada mun taka kan dutse birnin daraja daya batse ga haske🎆 ga adon Dutse 🏞️. See you tomorrow morning. We will meet again. Be with me at always my lover's. 6~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil Taibanah. ∆Saleem Musa Abubakar ∆Naja'at Musa Abubakar ∆Fatima Musa Abubakar ∆Aishat Musa Abubakar ∆Abubakar Musa Abubakar. @YUSRAHMS CE. ••• ••• Official By=== === === === ✍️ YÚSRÃHMS CE. 14~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil Muttaqinah. Downloaded from GNOVELS.COM.NG This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG For feedback and support Facebook : https://facebook.com/gnovels Twitter : https://twitter.com/gnovels Telegram : https://t.me/gnovels